Showing 78001 words to 81000 words out of 82398 words
qasar Ethiopia ba kuma daga masarautarsu.
Washe gari cikin manyan motoci suka dunguma zuwa garinsu kutti dan sake tabbatarwa.
Sai tsakiyar dare suka isa kuma acikin daren aka tara duk dattijan garin dasukasan su bulama da asma'u tun zuwansu garin da duk abinda yafaru.
Kuka sosai alhaji babaye yayi dayaji irin rayuwar da 'dan uwansa da matarsa sukayi saidai kuma yanzu babu abinda yakeson gani kamar 'yar dan uwansa.
Daga alhaji babaye sai khaleefa suka koma sbd khaleefa jirgi zaibi yakoma bazai iya tafiyar ruwaba kuma sauran binciken da tabbatarwar idan sun haduda rumanah zasu qarasa tabbatarwa.
Koda suka koma gida sosai hajiya yakurah taso bin khaleefa suje tare saidai maigidanta yace tabari yadawo daga China saisuje gabaki dayansu da haka khaleefa yatafi sbd ciwo dake neman kwantar dashi sbd bai qaramar wahalaba yasha a tafiyar.
A yau saqon haroun ya iso gareta an kammala aikinta.
Shiru tayi bayan fitar Jakadiya sbd tunanin yaya maheer zai karbi zancen sbd dole tana buqatar aiwatarda abinda tayi niya dan tanaji jikinta yasaki sosai jininta qarewa yakeyi sbd tsananta da abin yafarayi ajikinta sbd jinin dataqi zubarwa har lokacin tasan daf take da rasa hankalinta dan wata irin zabura dake kamata yanzu duk da tana qoqarin boyewa ammy da maheer tanaji abin yafara cin qarfinta.
Kallon abeel dake kwance jikinta tayi zatai magana jini ya digo ta hancinta ya sauka kan fuskarsa tayi saurin goge masa tareda ajiyesa ta dauki tissue tana dafe kanta da jiri ke juyawa dashi.
Durqusa gurin tayi tana fidda wani irin nishi cikin azaba tsawon mintuna kafin tasamu taci qarfin abin tana kiran sunayen Allah harya lafa kafin tayi wani yunqurin miqewa ya turo qofar dakin yashigo cikin nutsuwa idanuwansa kanta yana kallon tissues din gabanta dasuke lalace da jini hakama hancinta zuwa bakinta duk jini.
Saurin goge hancinta tahau yi saidai kuma atake jinin yasake 6allewa ta rintse ido cikin wani irin hali tafara nishi mai wuyar fita.
Da wani irin gudu ya qaraso gareta tun kafi yakai hannunsa gareta idanuwanta suka fara qoqarin rufewa yayi saurin tarota jikinsa yana kiran sunanta da qarfi.
Ganin tana neman fita hayyacinta yasa ya bude bedside drawer dinta yadauko maganin da negasi yabayar ariqa bata idan jinin yazo mata ya bude gabaki daya ya zuba mata abaki cikin tashin hankalin saidai jinin bai tsayaba amma idanuwanta sun bude tafara qoqarin tashi tana karbar tissue din dayake qoqarin kaiwa hancinta tace,
Banda lokaci inason sanardakai abinda nake ashirin aikatawa ayau sbd banason na mutu abanza batareda na tsayarda abinda ke faruwaba.....
Wani irin tari tayi jini mai tarin yawa ya fito bakinta kamar amai
Atake ya rungumota abinda bai taba ba arayuwarsa hawaye suka gangaro masa yafara girgiza kai yana hanata magana..
Girgiza masa kai tayi awahalce tace,
Taimakeni na shirya muje mukawa qarshen matsalar sbd 'yan baya su samu nutsuwa da kwanciyar hankalin gudanarda mulkin adalci.
Kasa motsi yayi saidata saki kuka ahankali tana kallonsa cikin rawar murya tace,
Karka manta ka min alqawarin tsayawa dani dan kawarda matsalar data lalata farin cikinmu dana wainda basujiba basu ganiba.
Cikin wani irin hali yace,
Na miki alqawari amma banda sadaukar da lafiyarki ko rayuwarki meyasa z......
Rufe masa baki tayi cikin wani irin yanayi tace,
Mu barwa Allah zabi zai mana mafita.
Amatuqar wahalce ya taimaka mata ta shirya sbd tuni alummar mineelik da kewayenta suka hallara sbd mahimmin saqon daza'a bayyanar garesu.
Duk yanda yakeson daurewa kasawa yayi lokacinda zasu shiga inda dukkanin jama'arta zasu ganta jawota yayi ya rungume da qarfi cikin rawar murya yace,
Kisani har abada bazan saki hannunkiba zamu fuskanci duk abinda zai tunkaromu atare, ummu-rumanah bulama kece zuciyar maheer abdulshams so please fight this battle for my love...
Ajiyar zuciya tasauke ahankali tareda zamewa daga jikinsa tana riqe hannun ammy dake hawaye gefenta Jakadiya dake gefensu tayi saurin miqawa ammy tissues ganin jinin yanason sake tsananta.
Ammy dakanta ta goge mata tana danne kukanta.
Murmushi tasaki tareda riqe hannun ammyn ta karbi tissue din tana goge hancinta zuwa bakinta da hannunta dake rawa sbd ko tsayuwa daidai bata iyayi abinda yafi daga hankalinsu kenan.
Sultan ma aranar da safe ta bayarda takardar sakinsa dan haka shima tuni ya fito ya halarci taron tareda sauran dattijawon masarautar duk da ayau jikinsa a sanyaye yake da abinda yake faruwar saidai a safiyar yau 'din ya gana da dukkanin 'yayansa dasuka zo dan halartar wannan taro kuma ganinsu ayau din da maganganunsu sun sanyaya jikinsa sunbar zuciyarsa da dana sani musamman maganganun maheer dayayi masa gameda mutuwar iyayen rumanah...
Hakan yasa ya ajiye dukkanin makaman yaqinsa akawo qarshen masifar duk da su sunriga sunbi sahu.
Tana fita ko ina yayi tsit dukkanin alummar gurin suka nutsu ahankali haroun yabada umarni nan take aka bayyanarda wata irin sabuwar karaga mai tsananin kyawu da kyalli mai daukar ido atake dukkanin jamar gurin mamaki da tsoro yakamasu musamman maheer dabaisan da hakanba yakalleta da sauri saiyaga tana qoqarin danne abinda takejine dan daidaita nutsuwarta yafasa maganar dayayi niyya ya damqe hannunta dake cikin nasa sbd har lokacin a tsaye suke taredasu ammy da jakadiya da masu tsaron lafiyarta.
Cikin wata irin budaddiyar murya sarkin fada haroun ya bude wata irin zungureriyar takarda mai daukeda tambarin masarautar mineelik dake daukeda saqon assultana yafara karantowa kai tsaye da qarfin muryarsa yanda kowa zaiji.
"""" NI SARAUNIYAR MINEELIK UMMU-RUMANAH BULAMA AYAU SHA BIYU GA WATA NA BIYAR A SHEKARA TA DUBU BIYU DA UKU NA SOKE KARAGAR MINEELIK DAN KAWO QARSHEN MULKIN ZALINCI INA GABATAR MUKU DA SABUWAR KARAGA GA WANNAN MASARAUTA...HAKA KUMA AYAU SHA BIYU GA WATAN BIYAR SHEKARA TA DUBU BIYU DA UKU NI UWAR MAGAJI SARAUNIYA UMMU-RUMANAH NA SAUKA KAN MULKIN MASARAUTAR MINEELIK TAREDA 'DORA SABON SARKI ABDALLAH ABDALLAH AMMED""
Atake dukkanin gurin yadauki wata irin kabbara da koke koken farin ciki da sbd wannan wani irin babban alamarine yazo musu na sauyi daga mulkin azaba musamman Abdallah Abdallah ammed mahaifin khaleefa mutum ne dazai kawowa rayuwarsu sauyi na adalci gashi shikansa baisanda zancenba.
Tsit aka sakeyi lokacin wasu irin majiya qarfin bayi kusan goma sha biyar suka ciccibo karagar mineelik Wanda keda wani irin girma tareda hularta.
Wani irin baro mai tsananin girma da fadi daukeda wani irin mahaukaciyar tukunta mai tsananin tiriri yaran negasi kusan su ashirin da biyu suka turo aka ajiye tsakiyar filin harabar.
Ta lumshe idanuwanta dasuka fara rufewa suna gani dishi dishi ta budesu daqyar ta iya 'daga hannu ta bada umarni atake haroun yabada umarni aka 'daga karagar aka saka ciki atake tafara nitsewa tana narkewa cikin ruwan dalmar tun tana gani dishi dishi sbd jinin daya balle hancinta atake idanuwanta suka rufe ruf ta yanke jiki ta zube gurin jini na qarasa balle mata ta hanci da bakinta.
#mamuhgee
*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers associationš”_
*45*
Not edited.
Saki jikinsa yayi sbd wutar data daukewa jikinsa da wani irin qarfi ammy ta jijjigasa tareda kiran sunanda da qarfi ya durqusa tareda jawota jikinsa ya dauketa gabaki 'daya yabar gurin da ita.
Anso tsayarda nadin sarautar amma haroun ya fitarda saqonta na gaba dake cewa duk abinda zai faru kar a tsayarda nadin dakuma takardarta tagaba dake cewa a raba mara masarautar biyu a rushe Rabin a gina masallacinda yafi kowane girma a qasar Ethiopia.
Hakan yasa aka cigaba da nadin yayinda sultan dake zaune har aka gama bai motsa daga inda yakeba saida aka watse aka gano ya rasu zaune agurin gakuma jinin da aka ganin ya digo daga hancinsa.
Lokacinda su negasi suka rufu akanta dan ceto rayuwarta alokacin ne aka zo da saqon rasuwar sultan Wanda ya girgizasu ya qarasa wargaza dukkanin sauran nutsuwarsu musamman ammy data kasa riqe kukanta maheer yayi saurin rungumeta yana riqe nasa hawayen sbd Allah yasani yana qaunar mahaifinsa duk mugun halinsa sbd koyaya ya zama mahaifinsane.
Cikin qanqanin lokaci rasuwar sultan da halinda assultana take ciki tareda canza karagar mineelik suka yadu 'yan jaridu da kafafen yanda labarai sukaiwa masarautar wani irin dandazo ana yada abinda ke faruwa.
Dukkanin iyalan marigayi abdulshams sun halarto cikin tsananin baqin cikin wannan rana data riskesu musamman 'yayan marigayiya adama dasuke ganin sun rasa uwa da uba.
Da maraice akai jana'izarsa inda dubban alumma na nesa dana kusa suka hallara inda yawan jama'arsa yasa maheer jin sanyi sanyi aransa tareda yiwa mahaifinsa adduar samun rahamar Ubangiji.
Duk damuwar dayake ciki ta halinda rumanah take ciki bai koma gurinta ba sai dare bayan an watse.
Kai tsaye sashen ammynsa ya nufa inda ya tararda ita tareda sauran 'yan uwansa ya qarasa kusada ammyn ya zauna yana kallonta cikin nutsuwa da tausayawa ya riqo hannunta ahankali ya iya furta,
Allah yaji qansa ammynah.
Kwantarda kanta tayi kafadarsa tareda cewa "amin" da muryarta data shaqe kafin ta 'dora da fadin,
Kaje gurin rumanah dan sanin halinda take ciki duk da meenah da jakadiya na gurinta.
Jinjina kai yayi jikinsa na qara sanyi da tuno wani tashin hankalin dayake ciki.
Lokacinda ya isa sashenta har lokacin bata farfado ba sai jinin daya tsaya Wanda suke sakaran jinintane yayi matuqar qasa sosai.
Zaune ya kwana gabanta yana mata addua cikin wani irin hali dabai ta6a tsintar kansa aciki ba.
Washe gari koda akaga bata farkaba hankula sukai matuqar tashi musamman da jikinta yayi wani irin fari fari Kore Kore ga 'yan jarida dasuka kasa suka tsare a masarautar sunason ganawa da sarauniyar data kafa sabon tarihi a qasar daba tataba.
Duk wani kalar likiti na turai da gargajiya an nuna qwarewa amma abu yaci tura gashi alamunta na sake 6aci ranar da akai uku aranar gabaki dayansu suka tattara suka nufi Georgia..shi,ammy da jakadiya data samu 'yancin rayuwarta itama sai sauran 'ya'yan da kowace takoma inda take aka bar sabon sultan dan gabatarda mulkinsa cikin aminci.
Suna sauka kai tsaye motar asibiti tazo daukarsu aka wuce asibiti dasu cikin tashin hankalinda yafi na farko sbd saki jikinta daya farayi.
Matsayinsa a babbar asibitin garin yasa ana isa da ita dukkanin likitocin dake nan suka taru aka fara qoqarin gano matsalar cikin gaggawa cikin tashin hankali da mamakin yanayin matsalarta sbd basu taba cin karo da irin hakanba.
Ammy daqyar ta iya zama gida saidai gabaki 'daya hankalinta da damuwarta na asibitin gabaki daya cikin kwana ukun ta rame tayi wani irin sanyi ko doguwar magana bata iyawa.
Har gari ya waye likitoci na kanta duk wata dabararsu da qwarewarsu sun nuna dan ganin ta farfado saidai Sam bata farfado ba saidai fatarta data fara komawa daidai sbd jinin da aka saka mata kusan leda biyu hakan yasa suke sakaran idan fatar ta gama komawa daidai ta farka.
Daqyar yake iya hadiye yawun bakinsa sbd tsananin bushewar bakinsa da maqoshinsa,
Duk wata nutsuwarsa da tunaninsa sungama barin jikinsa idanuwansa tuni suka qanqance ko gani bayayi sosai da idonsa dukkanin abokanan aikinsa sun tausayawa halinda yake ciki shiyasa suma gabaki daya hankalinsu tashe yake da ganin ta farfado 'din.
Khaleefa aranarda suka wuce aranar yasauka Ethiopia ya tararda abinda ke faruwa kasa kwana yayi duk da rashin lafiyarsa washe gari yabi jirgin asuba sbd yasan aminin nasa na tsananin buqatarsa.
Har yamma bata farkaba khaleefa ma saukarsa garin alhaji babaye yakirasa sbd news din dasuka gani gameda abinda yake faruwa a qasar nan yaqara yasanardasu abinda yake faruwa nan hankalinsu yayi matuqar tashi suka fara shirye shiryen tahowa cikin gaggawa.
Qarfe goma na dare ta bude idanuwanta dasukai wani irin shigewa sukai nauyi da ja.
Atake dukkanin likitoci suka sake hawa kanta cikin gaggawa da nuna qwarewa tareda fatar samun nasarar sanin matsalarta.
Kasa miqewa yayi sbd saki ga gabobin jikinsa sukayi sbd fargabar abinda za'a fada masa saidai khaleefa ne ya dafasa yana jinjina masa kai alamar qwarin gwiwa ganin halinda yake ciki.
Wasu sabbin dogayen hours suka 'diba suna qoqarin gano matsalar wadda suka gano daga qarshe wadda tayi mummunan 'daga hankalinsu haka suka ringa fitowa jiki amatuqar mace zuciyoyinsu ba dadi sbd dukkanin hotunansu da test test dinsu sun tabbatar musu da abu 'daya.
Dr Edward ne yafito qarshe yana zare glasses dinsa yakalli maheer da khaleefa yace,
Can we talk in my office pls..
Tashi tsaye maheer yayi tareda kallon qofar dakin da take yakalli Dr Edward din yana rintse idanuwansa da abinda za'a fada masa yace,
Just tell me dr Edward I c........
Dafasa Dr Edward yayi cikin tsananin tausayi ganin daqyar yake iya bude bakinsa yayi magana cikin sanyin murya yace,
I'm really sorry Dr m.a shams matarka ta rasa gangar jikinta bazata taba gara aikiba ma'ana tanada rai tana gani tana numfashi tanaji saidai bazata iya motsa jikintaba ko kadan bare magana har abada.
Wani mugun jirine ya dibesa khaleefa da Dr Edward sukai saurin nufarsa zasu taresa ta rigasu taresa cikin kulawa da tausayawa.
Khaleefa ne yakalleta cikin mamaki Dr Edward kuwa jinjina mata kai yayi alamar ta kula da maheer din yana buqatarta fiyeda koyaushe.
Shikuwa idanuwansa na ganinta baisan sanda ya sake fadawa jikinta yana qoqarin tsaida hawayensa saidai Sam basu tsaiduba saida suka zubo ya sake qanqameta yana cewa,
Suhailat please pray for me wlh zuciyata zafi takeyi I just can't live without her sbd wannan ma baida banbanci da mutuwa agareta.
Murmushin tausayinsa tasaki cikin sanyin murya tace,
Insha Allah zata warke
Nayi maka alqawarin zamowa majingini agareka duk lokacinda kake buqatata wannan alqawarin yananan haryanxu kuma nayi alqawarin cika makashi har qarshen rayuwata kuma zan tayaka jinyarta harta ji sauki sbd sonka shine qaddarata maheer abdulshams..
'Dagowa yayi kalleta da idanuwansa itama hawayen takeyi tana murmushi ahankali yaji wata irin soyayyarta mai tsafta tashiga zuciyarsa akaro na farko cikin wata irin rawar murya yace,
I love you suhailat sbd kece hasken rayuwata dakike tallafoni koyaushe.
Wasu hawayene suka gangaro mata ta rintse ido tana kwabar zuciyarta dake neman shegala da kamansa datasan ta samesune sbd nuna qaunarta ga rumanah saidai matuqar qaunarta ga rumanah zata jawo masa soyayyar mijinta to tabbas ta shirya samun soyayyar mijinta ta hakan.
Duk yanda ya 'daga hankalin likitocin asibitin akan abinda sukace dole ya dangana yadauki qaddara sbd result din dayane.
Ko ammy saidata kwana ta yini tana kukan halinda rumanar ke ciki da Wanda yashiga sbd gabaki daya ya birkice musu ko abinci sai ammyn tayi kuka yake iya shan abu mai ruwa ga suhailat data zamo batada wata hidima saita kula da dukkaninsu sbd sundawo gida.
Idan yazo ya zauna kusada ita haka zai riqe hannunta cikin nasa ya qura mata ido
Itadai hawayene kawai ke iya gangarowa ta gefen idonta musamman idan ammy tasata gaba tana kuka kokuma shi idan yazo ya zauna yasaka gaba ya qura mata ido tana iya hango mawuyacin halinda yake ciki.
Ranarda su hajiya yakurah suka iso aranar kuka yadawo sabo ganin halinda 'yarsu dasuke 'dokin gani take ciki...
Ko alhaji babaye dake dattijo saida ya zubarda hawayen baqin ciki da farin ciki.
Akwance take itama amma hawayene keta bin gefen fuskarta suna zuba Wanda hakan yaqara bawa kowa tausayi.
Duk da akwai Carolina sosai suhailat ke wahala sbd lalurar rumanah din.
Kusan satinsu alhaji babaye biyu kafin shi ya koma yabar haj yakurah dataqi dawowa tana jiran isowar mijinta dazasu tafi tareda rumanah sbd gwada nasu na addinin.
Satin alhaji babaye daya da tafiya alhaji mukhtar mijin haj yakurah ya iso kallo 'daya yayi mata yagano lalurarta Allah takeson akomawa sbd lalurace ta iska nan take suka yanke shawarar tafiya da ita maheer kai tsaye ya nuna rashin amincewarsa
Saidai ammy dataga yana mutuwar tsaye kullum sbd lalacewa da rayuwarsa ke nemanyi dan ko aiki bai taba fitaba koyaushe yana gida ga suhailat data zamto abar tausayi gurin qoqarin kulawa dashi da rumanah duk ta rame tausayinta da qaunarta yasa kai tsaye ta zaunar dashi cikin nutsuwa ta fahimtar dashi kuskuren dayake jefa rayuwarsa da iyalinsa ciki dan haka yabar rumanah aje da ita ya tsaya ya gyara mu'amalarsa da rayuwar aurensa da suhailat.
Sosai jikinsa yayi sanyi kuma yasan matuqar yanason gyara rayuwar iyalansa ta inganta saiya boye soyayyar rumanah kwata kwata dan haka zai danne Zuciyarsa yafara daga yanzu.
Da haka ya amince aka tafida rumanah din amma hardashi suka tafi saidaya kwana biyu yadawo dan qoqarta gyara mu'amalarsa da suhailat.
Koda yadawo su ammy da jakadiya tareda abeel sun komawarsu Libya dan haka gidan dagashi sai suhailat sbd su amah ma suna Mali tabarosu dama itakadai tazo.
Aranar daya dawo lafiyayyan tarba tayi masa cikeda Dari darin yanda zai dawo yayi rayuwa a inda babu rumanah.
Ganin yanda take kama kanta dashi duk sai yaji ya muzanta ya tattaro jarumtarsa ya danne abinda ke ransa ya riqo hannunta ahankali tareda jawota jikinsa yana kallon fuskarta dake kallonsa yasaki qayataccen murmushi yajata suka zauna bakin gadon dakinta daya shigo yasameta hartayi shirin bacci zata kwanta.
Kallonsa takeyi tanason gano damuwarsa saidai takasa ganin komai sai murmushin dayake sakar mata
Wani irin sanyi da farin ciki taji na shigarta ahankali kenan kalamansa daga zuciyarsa suka fito lokacinda yafada matasu.
Rungumesa tayi da sauri tana sakin hawayen farin ciki ta murmushin jin dadi.
Dagota yayi tareda zare mata riga yana murmushi yace,
Banyi wankaba so yau kece zakiyi wannan aiki.
Noqewa taso yi tana murmushi yayi saurin riqeta yana kallon cikin idonta ya girgiza mata kai ahankali yace,
Don't make that mistake again suhailat.
Kallonsa tayi tareda jinjina kai takama hannunsa ta nufi hanyar toilet dinta dashi suka shige.
Aranar wata irin rayuwa suka gudanar data mantarda suhailat dukkanin damuwarta ta dah inda sukai alqawarin dora sabuwar rayuwar aure ta fahimta,soyayya qauna da aminci atsakanin su uku da 'yayansu daga yanxu.
**
Ahankali ake gudanar da adduoi da sauran abubuwan addini tareda sauke al-qur'ani da sadaka ana fatar samun sauqi.
Kulawa sosai da wata irin qauna da soyayya suke mata kaf zuriar banda zuriar gidansu aqeel data gama tarwatsewa babu wani nakamawa acikin zuriar gidansu shiyasa koda sukaji 'yarsu bulama tadawo kuma a nakashe kota kan zancen basubiba.
Su kuwa haj yakurah tamkar 'yar data haifa da cikin ta takejin rumanah duk wata kulawarta da dukkanin hidimarta takoma ta rumanah shima alhaji babaye kullum saiyazo gidan sbd yayi yayi tabari rumanah takoma gidansa taqi yarda tabari.
Watanta hudu a Nigeria yazo dubata babu adadi duk tareda suhailat suke zuwa Wanda itama tanajin farin cikin ganinsa da suhailat sbd ganin hankalinsa ya 'dan kwanta sosai duk sukazo idan zasu tafi daurewa kawai yakeyi yakoma sbd alqawarin adalci daya daukarwa kansa.
Ammy kuwa kusan tamafi maheer din zuwa kuma takan dade idan tazo.
Ahankali tafara samun sauqi sbd wasu gurare dasuka fara motsawa ajikinta Wanda hakan ba qaramin farin ciki da qwarin gwiwa yasakasuba nan aka sake maida himma ga sauke al-qur'anai da sadaka da adduoi.
Ba'a rufa wata biyu da fara motsinta ba tafara magana ahankali har tana iya tashi zaune da kanta ta tashi.
Lokacinda wannan saqon ya iso masa aranar suhailat