Showing 54001 words to 57000 words out of 82398 words
tsaye gurin sultan yanufa akai masa iso lokacin anwatse sai gobe a shaida hukuncinda zai iya yankewa.
Kallonsa yarima yayi cikeda takaici da baqin cikin yanda yasan sultana bazata aikata hakan ga yayansa ba amma ya yarda haryana iya tunanin yanke mata hukunci
Kai tsaye yace,
Amatsayina na uban magaji zan kar6i mulkin mineelik har lokacinda zai girma ya karbi da hannunsa.
Wani irin murmushin takaici sultan yasaki batareda yakallesaba yace,
Mulkin mineelik da za6ar mai mulkin na mutum 'dayane yanxu dan haka ka rasa damarka,
Mahaifiyarka kuma koni bazan iya kubutarda itaba idan har bincike ya nuna da hannunta aciki.
Yana fadar haka ya shige tabarsa zaune idanuwansa na kadawa jajir.
Duk inda tashin hankali yake masarautar na ciki dan shi kansa sultan jinjina alamarin yake aransa yana jaddadawa yana kuma fatar bincike yasa kar asamu hannun sultana aciki.
Acikin daren babu kalar azabar daba'a bawa mamaniba tace Jakadiya tasaka ta.
Jakadiya aka hau bawa baqar azaba amma daqyar take iya furta babu saka hannunsu aciki.
Acikin daren saqon neman sulhu da sassaucin hukunci yazo daga masarautar Libya dakuma wasu masarautun duk sai alamarin yasake girmama ya sake cabewa sultan gashi komene adaren ne sbd gobe dolene zai yanke hukunci.
Nuratu datun jiya take kuka da tashin hankalin halinda mamani ta fada koda bincike yazo kanta ba qaramin rikicewa tayiba saidai tafada musu komai na dangane da zancen dasukaji su Jakadiya nayi da sultana itada rumanah akan basuso ta haifi namiji.
Atake aka kaiwa sultan wannan zancen hankalinsa ya matuqar tashi saidai har lokacin yanada wasi wasin zancen ga asirinsu na 6oye daya fara shigowa cikin zancen Wanda tonuwar dolema yayi gaggawar yanke hukunci sbd kar maganar ta bankado atake ya yanke hukuncin kisa ga dukkaninsu ukun gobe.
Acikin daren hankula suka masifar tashi jin anyekewasu sultana hukuncin kisa washe gari.
Duk wata zuriar masarautar tun acikin daren suka fara isowa musamman 'yayan sultana da kuka sunyisa na zuci dana fili hankalinsu amatuqar tashe yake.
Yarima maheer Kansa ya rufe adaki duk yanda yake tunanin masifar ta wuce nan abu 'daya yasani bazai mahaifiyarsa ta fuskanci hukuncin kisar wulaqanciba.
Kwance take lamo idanuwanta jajir ko kukan bata iyayi duk abinda yake faruwa bata saniba sbd ta hana abar kowa shigowa gurinta.
Ahankali taji antsaya akanta batareda tadagoba ta lumshe ido tareda budewa taji muryar suhailat cikin wani irin yanayi tace,
Nazo neman alfarma agurin sbd kece kawai zaki iya tsayarda abinda ke shirin faruwa.
Tashi zaune tayi ahankali batareda takalli suhailat dinba
Itama suhailat sauke kanta tayi sbd batason kallon rumanah dan ganinta ke tuno mata da ba itace zuciyar mijintaba.
Hawayene suka gangaro mata tasaka hannu ahankali tashare taci gaba da cewa,
Nice uwar datai rashin abu biyu lokaci daya kuma zuciyata cike takeda neman adalci,
Ina roqonki amatsayina na uwar data rasa 'da da mahaifarta akan adalci zanso ganin anmin adalci saidai bazanso akashe Wanda bashine mai laifinba sbd mai laifin zai cigaba da aikata 6anna aboye har wadda tafi wannan.
Cikin dasashiyar murya da sanyi tace,
Adalcin nima nake nema amatsiyana na marainiyar da aka raba da iyayenta dakuma uwar da aka rabata da 'danta tun bata gama warkewa daga zafin naqudarsaba.
Asubar fari yashigo dakinta idanuwansa da yanayinsa suka karya mata zuciya ta dauke kai daga kallonsa tareda mayarda kanta kan gwiwoyinta.
Tsayawa yayi agabanta zuciyarsa cikeda baqin cikin kasancewarsa shine zai roqi wani yabasa sarautarda shine ya gada saidai yasan kubutarda ammynsa na nufin ya karbi sarautar ayau yazamo shine zai yanke hukunci sbd yagano sultan sbd 6oye wani sirrinsa yakeson yanke hukuncin da gaggawa ayau.
Kallonta yayi da idanuwansa dasukai jajir yace,
Inason kibani sarautar mineelik ayau.
Kallonsa tayi da sauri da jajayen idanuwanta dake budewa daqyar sbd kumburi.
Juya mata baya yayi yace,
Ki shirya ina jiranki kafin lokacin yanke hukuncin su ammy yayi.
Ficewa yayi tabisa da kallo zuciyarta na harbawa.
Cikin wani irin yanayi na sabon tashin hankali ta 'dauki abeel hassan ta fito palo takalli nuratu dake rakube tun acikin daren tana jiran fitowarta tayi kuka har batada qarfin yin wani.
Kai tsaye tace,
Meke faruwa?
Da sauri nuratu ta tashi ta zube gabanta tana hawaye tace,
Ina neman afuwa akan shaidar dana bayar akan sultana da jakadiya gashi zasu rasa ransa sanadin shaidata saidai wlh ina rantsuwa da rayuwata mamani bayin kantabane sakata akayi saidai wlh bansan wayake sakataba dana fada nan fitardasu sultana dan haka ashirye nake da daukar hukuncinki.
Da wani irin sabon baqin ciki da takaici takalli nuratu saidai takasa cewa komai ta nufi qofa ta fice kai tsaye sashen suhailat ta nufa.
Zaune take a dakinta taqurawa akwatinanta data saka Carolina hadawa ido idanuwanta jajir.
Tsayawa gabanta rumanah tayi tareda miqa mata abeel hassan idanuwanta na cikowa da hawaye tace,
Duk duniya ayanxu kece kawai na yarda dake akan 'dana sai Ammy dan haka ina riqonki daki riqesa har sai lokacinda kikaji zuciyarki ta gamsu da adalcin dazan baki,
Na miki alqawarin duk Wanda yakeda hannu aciki ayau zai fuskanci hukuncinsa.
Ficewa tayi kai tsaye ta nufi sashenta tashiga wanka zuciyarta na wani irin zafi tana fitowa tagansa tsaye cikin 'dakin idanuwansa jajir ya kalleta ta 'dauke kanta tareda isa gaban madubi ta zauna.
Cikin zafi ya jawota gabansa cikin 'daga murya yace,
Me kike nufi da abinda kika fadawa suhailat?
Bata kallesaba tace,
Kubutarda uwata.
Sakinta yayi da sauri tareda kallon cikin idonta yace,
Kinsan abinda kike fada?
Kinsan abinda hakan ke nufi?
Bana buqatar ki shiga komai abu 'daya nace kiyi shine ki bani matsayin danace inaso....
Kallonsa tayi da jajayen idanuwanta cikin rawar murya tace,
Nima bana buqatar ka saka kanka cikin ha'dari dan haka bazan taba baka mulkin mineelik ba koda hakan na nufin rasa rayuwatane....
Riqota yayi da qarfi tareda girgizata yace,
Idan kina sona bazaki taba bari ataba mahaifiyata ba sbd itace rayuwata dan haka dole zaki bani mulki.
Hawayen dasuka cika mata idone suka gangaro mata ahankali tace,
Namaka alqawarin babu abinda zai samu uwar data haifi halitta mafi soyuwa arayuwata kozan rasa raina.
Shiga jikinsa tayi ahankali tareda rungumesa hawaye na tsinke mata.
Rintse ido yayi tareda rungumeta ahankali ya furta,
KECE RAYUWATA UMMU-RUMANAH BULAMA.
Dagowa tayi takallesa hawaye far in ciki na tsiyayo mata saidai bazata iya cewa komaiba.
Ruwan kan table din dake tsakiyar dakin ta dauka tareda kaiwa bakinsa tana tsiyayar hawayen tausayinsa dana kanta.
Ahankali yasha yana kallon cikin idonta.
Ahankali ta furta,
Karka gujeni kome zanzama arayuwa dan allah,
Ko bayan raina kayi kayi alqawarin tunawa dani.
Lumshe ido yayi jikinsa na mutuwa idanuwansa na fara gani dishi dishi a firgice yake kallonta sbd gano wani abune tabashi saidai kafin yayi wani yunquri ya zube kan gadon ta durqusa ta gyara masa kwanciyarsa tareda shafa fuskarsa ta miqe.
Dukkanin wani maison sheda hukuncin sultan na cikin qasar da wajenta sun hallara sultan na fitowa guri yayi tsit ya zauna kan kujerar mulkinsa atake aka fito da mamani da jakadiya dukkaninsu babu mai iya tsayuwa sbd azaba da 'daurin dake jikinsu.
Kukan baqin ciki Jakadiya takeyi sbd irin mutuwar tozarcin dazasuyi tareda sultana.
Mamani na ganin masu jiran umarni sun tsaya akansu da takobuna suna kashe ido sbd laifi da qyallinsu hankalinta yatashi tabude ido daqyar tanason magana kaleeb ya take mata kai.
Ana jiran ana fitoda sultana cikin wani irin ama aka sanarda fitowar uwar magaji.
Atake kowa yayi tsit sultan yayi saurin kallon qofar
Tafito cikin wata irin doguwar ethiopiany royal gown red colour mai tsananin tsawo da adon black stones wuyanta da kanta na kyallin farin zinari kallo 'daya zakayi mata kasan tana cikin baqin ciki.
Cikin wainda ke tareda ita Dan tsaron lafiyarta ta kalli gefen daya jiki na rawa ya fidda bayananta dake rubuce jikin fatar rubutu ya miqawa sarkin na'din sarautar mineelik.
Budewa yayi tareda fara karanto da qarfin muryarsa yanda duka alummar dasuka halarci gurin zasuji.
"" NI UMMU-RUMANAH BULAMA MATAR YARIMA MAHEER UWAR MAGAJIN MINEELIK AYAU KWANA 'DAYA DA NADIN SUNAN MAGAJIN MINEELIK NA SAUKE SULTAN ABDULSHAMS ABDALLAH DAGA MULKIN MINEELIK NA KARBA HAR ZUWA RANARDA 'DANA MAGAJI ABEEL HASSAN ZAI KARBI MULKI DA HANNUNSA.."""
Tsit koina yayi sbd firgici da mamaki
Sultan da adama kusan atare suka miqe tsaye tsabar firgici.
Ammy da ake fitowa da ita kadan ya rage ta yanke jiki ta fadi sbd jiyo sanarwar.
Jiki na rawa sarkin nadi tareda duk sauran sarakuna da wazirai suka miqe ta nufi kujerar mulkin mineelik gabanta da numfashinta na fita da sauri
Sultan dayayi mutuwar tsaye ya zare hular mulkin ya miqawa sarkin gida atake aka dauko kayan rantsarwa aka rantsar da ita atake ta zauna kujerar mineelik aka saka mata hular.
Lumshe jajayen idanuwanta tayi wani irin baqon yanayi mai qarfi na shigarta
Wani irin qarfin zuciya da taurin zuciya taji yana shigarta tsawon lokaci ahaka duk anyi tsit anajiranta.
Ahankali ta bude idanuwanta dasuka bushe nan take tagyara zama takalli inda sultan yake zaune yana kallonta cikin isa shima yanajiran jin nata hukuncin ta juyo takalli indasu mamani suke cikin daga murya tace,
Akawo abinda mamani tafiso aduniya.
Cikin gaggawa aka jawo nuratu aka durqusar tsakiyar gurin kai tsaye tace,
Ku yankata agabanta uwarta idan bata fadi Wanda yasakataba cikin seconds uku.
#mamuhgee.
*_TARAYYA_*
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*34*
Not edited.
Arazane sultan,adama,ammy,da baqin sarakunan dasukazo suka kalleta
Babu Wanda ta kalla acikinsu tayiwa kaleeb kallo 'daya idanuwanta na sake bushewa cikin gaggawar cika umarninta kaleeb ya daga shar6ebiyar takobinsa mai cire kai lokaci 'daya ya 'dora a wuyan nuratu dake hawaye ta qurawa rumanah ido.
Numfashin wahala mamani ta fitar cikin tashin hankali ta bude baki zatai magana adama datai mutuwar zaune tayi sairi tashi tsaye jikinta na wata irin tsuma zatai magana rumanah ta 'daga hannu batareda takalleta tace,
Duk Wanda yayi magana batareda hukunci ya gama tabbatuwaba abakin rayuwarsu ko wanene.
A gigice adama tasake kallonta cikin wani sabon tashin hankalin takoma ta zauna zufa na karyo mata jikinta na wata irin tsuma.
Tayar da ita akayi tana numfashin azaba takalli takobin datake qyalli a wuyan nuratu takuma tabbarda yankata din za'ayi.
Ahankali rumanah ta 'dagawa kaleeb kai alamar yacika aiki.
Atake ya 'daga takobin cikin wahalalliyar murya mamani tace,
Gimbiya adama ce.
Cak kaleeb ya tsaya sbd harya 'dora takobin a wuyan nuratu harma saida ya'dan yanketa.
Arazace sultan yakalli adama data jiqe jagaf da zufa jikinta na tsuma tanason kare kanta gashi ance duk Wanda yayi magana bbakin ransa kuma tasan tsaf rumanah zata iya sbd tasan abinda ka cikin karagar zaifi shigarta kasancewarta mace dan haka zatafi rashin tausayi da imani.
Sarakunan dake gurin duk ita suke kallo cikin mamaki yayanta kuwa kuka suka fashe dashi gashi babu ikon ko qwaqwaran motsi.
Rufe ido rumanah tayi wani irin yanayi na tsuma zuciyarta gawar 'danta da iyayenta tana mata yawo ido da irin tozarcinda ammy ta fuskanta akan hakan
Fuskar maheer ce ta fado mata da irin tashin hankalinda tagani ataredashi tsakanin jiya zuwa yau ta bude idanuwanta dasukai jajir tace,
Ni sarauniya ummu-rumanah bulama na halastawa takobin kaleeb adana jinin adama kisheer ayau agaban mijinta da 'yayanta tareda sauran alumma duk Wanda ko a fuska ya nuna hukuncina baimasaba a shayar dashi dafi daidai irin Wanda adama tashayarda qannen magajin mineelik.,
Baiwa mamani arufeta mai rubuta tarihi yaje tabasa tarihin sarauniya rumanah arubuta atarihin mineelik tana gamawa bazata qara minti biyar aduniyaba a shayar da ita Kofi 'daya na daafin macijin dayafi kowanne kaifin dafi,
Sultana zaarah da jakadiya sunfita da zargin da ake musu.
Sultan abdulshams arufesa a turakarsa babu shiga babu fita aabisaga zarginsa na qoqarin yanke hukunci batareda bincikeba harsai angama bincike akan niyarsa sultana zaarah ce kawai keda damar shiga da fita agurinsa sai yarima maheer.
Arikice sultan yakalleta ransa na mummunan 6aci da baqin ciki ace rana 'daya cikin mintunan dabasu wuce biyarba baiwa wadda bama asalin 'yar qasaba ta saukesa akan mulkin daya gada iyaye da kakanni,
Ta yankewa matarsa kisan wulaqanci agaban dubban jama'ar dasuke shakkar ko kallon inda yake sannan yanxu tace arufesa a turakarsa wannan shine tozarci mafi muni arayuwa...
Yanxu ta karbi mulki idan tagano shine asalin dalilin mutuwar iyayenta akwai masifa sosai sbd yanda sihirin karagar nan ke shigarta nan cikin qanqanin lokaci zata zamewa kowa masifa mai matuqar hadari musamman shi saidai duk masifa duk balai bazai bari yayi mutuwar wulaqanci a hannuntaba koda hakan na nufin hada hannu da balain da aka binne shekaru tun kafinsu.
Kama adama akayi aka fara janta tayi saurin kwacewa ta isa gaban rumanah ta zube tana kukan tashin hankali jikinta na mugun karkarwa saidai takasa magana sbd umarninda rumanar tabayar ko kallonta rumanah batayiba ta kalli su kaleeb atake suka fara yiwa adama jan wulaqanci.
Jikin ammy ne yadauki rawa cikin sabon tashin hankali take kallon rumanah tana girgiza kai sbd matuqar tafara mulkinta ayau da zubarda jinin wani to tabbas zaiyi wuya bata zamewa mutane abin tsorobas.
Qoqarin isa gurin rumanah din tayi aka dakatar da ita ta hanyar tareta tayi saurin kallon rumanah data rufe idonta tanajin wani irin baqon yanayi shigarta.
Cikeda rashin imani da tausayi kaleeb ya daga takobinsa yacire kan adama data mutu tana ihu da fizge fizge.
Tsit gurin yayi sbd tsoro da firgici sbd duk mulkin sultan ba'a taba kashe mutum agaban alumma ba sai yanzu nantake kowa yaji tsoro da fargaba tareda tashin hankali na shigarsa atake kaleeb ya 'daga takobinsa dake 'digar jinin adama sama ta bude idanuwanta ahankali takalli jinin dake diga qasa ahankali tasauke ajiyar zuciya ta miqe tsaye.
Cikin wani sauti da babban sauti sarkin na'di yace,
Dogon zamani MINEELIK ASSULTANA UMMU-RUMANAH UWAR MAGAJI.
Juyawa tayi wasu irin samudawan masu bata tsaro da kuyankinta mata suka mara mata baya tashige.
Tafiya kadan tayi ta tsaya cak sbd abinda takeji ajikinta
Wani irin abu takeji kamar yana tafiya da motsi ajikinta ta dafe qirjinta da takejin yana quna.
Ammy tayi saurin nufota aka sake tareda
Rumanar ta 'daga musu hannu daqyar alamar subarta ammyn tayi saurin qarasowa kafin tayi yunqurin ta6ata sukaga ta yanke jiki ta fadi jini na fita ta hancinta atake hankalinsu yayi masifar tashi ammy na qoqarin 'dagota suka gansa kansu idanuwansa jajir jijiyoyin sun firfito ya durqusa ya dauketa ya nufi sashenta da ita cikin qanqanin lokaci aka zuba wasu irin tsaro tundaga qofar sashenta har zuwa qofar masarautar atake labarin halinda take ciki ya yadu nan mutane suka sake shan jinin jikinsu atake aka rufe duk wata qofar shige da fice dake mineelik aka dauko duk masu bada maganin sarauta na asalin gargajiyarsu nanda nan aka hau dubata suna qoqarin tabbatarda abinda suke tunani.
Cikin wani irin tashin hankali da damuwa yake,
Zafi sosai yakeji acikin xuciyarsu akaro na farko dayaji zuciyarsa na karaya akan abu saidai yasan mutuwace kawai zata rabasa da rumanah dan haka duk abinda zata zama ayanxu ashirye yake daya sadaukar da rayuwarsa akan cetota daga masifar dake tattare da wannan karagar.
Jini ne sosai yake fita ta hancinta ahankali tafara wata irin jijjiga jijiyoyin jikinta suka ringa firfitowa Kore sosai nan take hankalin su negasi(masu maganin gargajiyar qarnin baya na sarauta) ya tashi
Maheer da idanuwansa sukai mugun rikidewa yayi saurin nufarta zai rungumota cikin wani irin sauti negasi yace,
Karka kusanci inda take ko kusa a wannan yanayin hadarine mai matuqar gaske dankuwa dafine yake yawo ajikinta yanxu idan jininta yafi qarfin dafin zataci qarfinsa ta tashi idan kuma dafin karagar yafi qarfin jininta shikenan sai hakuri sbd har abada bazata koma daidaiba zata zama rabi hankali rabi nakashe.
Cikin wani mumman tashin hankali ya dafe goshinsa akaro na farko yaji idanuwansa suna qoqarin tara hawaye ya fito dakin baya gani sosai sbd tashin hankali
Ahankali yaji andafasa yana juyowa yaga suhailat rungume da abeel baisan sanda ya fada jikintaba ta rungumesu gaba daya shida abeel din hawaye na gangaro mata cikeda tausayinsa dana rumanah taso tafiyarta ayau saidai ganinsa Cikin halinda bata taba ganinsaba yasata jin bazata iya tafiya tabarsa a lokacinda yafi buqatarta,tabbas idan tanada wata qaddara arayuwa to soyayyar maheer ce dan haka kamar yanda zai sadaukar da rayuwarsa gurin kulada rumanah duk halinda zata shiga mai kyau ko mara kyau to itama zata zauna ta sadaukar da rayuwarta gurin kula dashi da zame masa garkuwa duk lokacinda zai nemi hakan.
Ammy dake zaune tareda sauran 'yayanta yayun yarima sun biyu da Jakadiya da sauran masu tsaro da jiran tsammanin halinda ake ciki ta rafka tagumi zuciyarta na harbawa da qarfi sbd tasan me hakan ke nufi dan kuwa rumanarsu tariga ta tafi sbd idan har komai yagama shiga jikinta duk abinda yafaru shekara da shekaru tun kafa mineelik zata gani Wanda shine idan kaga masifun dake ciki yakeda wuya baka haukaceba idan ka farka.
ASALIN MINEELIK.......
#mamuhgee
Kuyi manage na fitane so mu kama gobe.
_*TARAYYA*_
_wattpad@mamuhgee_
_Haske writers association💡_
*35*
Not edited
*Asalin Labarin mineelik*
Soyayya da cin Amana haÉ—i da Yaudara suka, kafa daular, asalin masifar ya fara ne, daga ranar laraba ga watan maris 1836. Mafarin rigimar daga mutane huÉ—une, jigogin masarautar, Musaman Sultan Jamal wanda shi ya haifar da kome....
Tafiya suke a gajiye ga dare ya fara rabawa, yunwa da kishirwa ya addabesu, dan haka suka yanke hukuncin da zaran sun sami, wani guri a can gaba zasu yada zango kasancewa sun fito daga yanki sham, fatauci duk cikinsu babu wanda yake iya magana sai Jamal, sabida Allah yayoshi mutune magananne, da kuma son raha,
"Kayyasa! Ajani karda ka gaji da tafiyar dan naga kaman rakuminka ke janka ba kai kejanshi ba."
"Wai shin Jamal baka gajiya da magane, haba tun da muka fito kaiÉ—ai ke surutu gaskiya kacika surutu kayi mana hakuri haka dan yunwa muke ji." inji Kojo.
"Shi kenan kojo nayi shiru kuma bazan sake magana ba, amma kusan matuƙar muka ce zamu shiga Ehtophiea a wannan daren akwai damuwa mu yada zango anan gaba."
Shirun da sukayi ya tabbatar da amincewar sauran.
Tafiya sukayi sosai har suka isa dajin kurfa, wanda yake cike da ababen tsoratarwa, É—an tafiya kaÉ—an sukayi É—ayansu amari yaga wani irin Haske mai tsananin kyalli cikin duhu ya ware ido sosai yasake kallawa domin kuwa ya tabbatarda mage yake gani mai shegen hasken nan kamarna zinari cikin zaquwa da fargaba yace.
"Ku dakata naga wani abu, kamar Zinari."
"Amari nima nagani tsoron siffar abin yasani shiru gashi can kamar mage ko?" Inji Jamal,
Linzamin rakumarsu suka ja, suka tsaya Jamal da Amari suka sauka, daga bisa rakumansu, Ajani da Koja suna tsaye suna kallonsu, tafiya sukayi me É—an nisa suna niman Zinarin basu ganshi ba,
Tsaki Ajani yayi wanda ya