Showing 90001 words to 93000 words out of 110071 words
tayaki?"
"Jeka kaci abinci" ta kakaro maganar da kyar.
"Mawadda ina son ki!"
"Wallahi nima ina sonka Yayanmu" ta fada tana kallonsa.
Kallon juna suka tsaya yi kafin ta nuna masa kofa da yatsanta.
"Ko baki ce ba tafiya zanyi ko don tseratar da kaina daga soyewa"
"Me zai soyaka ana zaune kalau?"
"Ke mana da idanunki masu hanani sukuni"
Kofar ta sake nuna masa ya fice yana dariya ita kuma ta cigaba da aikinta cikin tunanin mijinta abin son ta Dahiru.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰24
*Batul Mamman*💖
Annurin fuskarta ne ya bace bat kamar anyi ruwa an dauke ta hade rai "me kace?"
Dahiru an sami abinda ake so ya wani kashingida akan kujera ya basar "cewa nayi zamu je neman auren Anti Qareeba"
Wani abu taji ya tokare mata a wuya ta tashi ta shige daki ta barshi a wurin. Shafa kansa yayi wanda gashinsa irin na Fulani da suka gada wurin mahaifinsu har ya fara taruwa ya ce "Allah nagode Maka Mawaddata tana sona"
Kusan minti uku tana daki tana kuka. Aure ko wata bai cika ba Dahiru yake fada mata zaije neman aure. Don karfin hali harda cewa taje wurin Nawal wato ma dare zasu raba. Yanzu haka Attahir zaiyi mata duk irin girmamawar da take masa. Shi kuma Bilya karshenta matarsa ce ta fada masa tayi mata ba daidai ba da suka zo shine zaice ayi mata kishiya. Allah Sarki rayuwarta daga wannan sai wannan. Amma tayi alkawarin daurewa bazata taba bijirewa Dahiru ba. Wani matsanancin tausayin kanta ne ya kara kamata ta kifa kai akan filo tana kuka haikan kamar yau za'a kawo mata amaryar.
Dahiru ya taso yana rangaji abinsa don shi idan ya ga alamun kishinsa a idanun Mawadda wani kara sonta yake ji. Kukanta ya jiyo kafin ya bude kofar yaji gabansa ya fadi. Da sauri ya tura kofar ya ganta kwance a tsakiyar gadon tayi rub da ciki sai sautin kuka ke tashi.
Gadon ya hau yayi kokarin juyata ta makale jiki.
"Subhanallahi Mawadda me ya sameki?"
Shiru tayi tana mamakin rainin wayo na maza. Yanzun nan ya juyar mata da duniyar farincikinta shine kuma yake tambayar me ya faru.
"Don Allah fada min. Baki da lafiya ne?"
Nan ma babu amsa. Duk yadda zaiyi taki shiru sai da kyar ne ma ya samu tace masa ya rabu da ita ya tafi wurin wadda yake so. Sai lokacin ya harbo jirginta ya danne dariyarsa ya gyara zama daga gefenta ya bude baki sai jiyo shi tayi kamar yana kuka.
Da farko ta zaci wasa ne ta kyale shi sai daga baya taji ya bude murya yana neman cika mata kunne. Jiki na rawa ta tashi ta ma manta da nata kukan "menene?"
Kara sauti yayi ta saka hannu akan bakinsa da sauri ta toshe ga nata hawayen na zuba cikin muryar kuka tace "Yayanmu me ya sameka kuma?"
Ya kwabe kyakkyawar fuskarsa ma'abociyar saje wanda ya hade duka gefen fuskarsa.
"Ba ke bace kike kuka kuma na tambayeki kinki yi min magana"
Harara ta dalla masa idanun nan kamar su fado ya daure iyakar dauriya kada yayi mata dariya.
"Kishiya fa kace zaka yi min ba dole nayi kuka ba" ta fada tana turo baki.
Sake bude baki yayi harda daga murya ta dora hannu a ka tana salati "so kake a jiyo mu ne?"
"Gara wasu daga waje su zo su rarrashemu duka mu biyun tunda ni baki son nawa"
Hawayenta ta goge da sauri ta tattaro wani murmushin dole ta yaba a fuskarta "na dena don Allah kaima kayi shiru idan aka shigo ai kunya zaka bani"
"Saboda kada kiji kunya kike son nayi shiru....Allah Sarki Dahiru bawan Allah" matso kwalla yake ta son yi abu ta gagara yana ta kikkifta idanu.
"Ba haka bane, ai kai dinne kukan naka har yafi nawa"
Yatsanta karami ya kama ya murda da nasa yana murmyshi "na dena amma kiyi min alkawarin kin dena zama kina kuka ke kadai."
"Nayi" tace ba don ta so ba.
"Ranar da ki ka karya idan na kamaki hukuncinki shine nima kukan zan tayaki in bude murya banda su Attahir makotan hagu da dama duk sai sunji sun shigo"
Ta zaro idanu "kace Allah"
Ya matso kusa da ita "ko a gwada ne?"
Girgiza kai tayi da sauri "rufa min asiri"
Janyota yayi jikinsa suka kwanta ya rungumeta "kukan me kike yi to daga tambayata ina zani?"
Sai da taja hanci ita a dole abar tausayi tace "aure kace min zaka nema na Anti Qareeba anjima"
"Don nace zani neman aurenta ba ina nufin nemawa kaina ba. Solidarity zanyi mata na hadata da Yayanmu Bilya"
Dariya ce ta kwacewa Mawadda farincikinta bai buya ta tashi ta zauna ta goge hawayenta tas "Yayanmu ka rinka bayani dalla-dalla ko don gaba. Kaine baka yi yadda zan fahimta ba amma yanzu komai ya wuce kamar iska"
Hannunta ya riko ta fada kansa gabadayanta fuskokinsu na kallon juna "don Allah kema kina jin yadda nake ji akanki? Sonki nake sosai"
Bayan hannunta tasa ta shafi gefen fuskarsa "nima haka"
Ya sake narke mata a jiki "Kema me?"
"Abinda kace mana"
Noke kafada yayi yana kara matseta "ni gaskiya a'a ki fada yadda na fada"
Kallonsa tayi yadda ya koma mata shagwababbe tun bayan aurensu. Duk wani ture turen baki ya iya ya sata yin abu ko babu niyya.
Wani abun idan yayi har mamaki take wai Dahirunta ne tun na da can ko kuwa. Komai yayi burgeta yake yi shiyasa idan ya fita sai taji kamar bata da lafiya. Wani dan tunani tayi ta tashi zaune da sauri tana ture shi.
"Me kuma nayi yanzu?"
Bata rai tayi "wallahi ba haka ake yi ba Yayanmu"
"Har yanzu ban fara yi miki yadda ake yiwa amaren bane?" Ya fada yana kamota.
"Ni ka kyaleni bana so"
Muryarsa da take matukar so mai tayar mata da tsigar jiki ya sake ragewa yana turmurmusata "Uhm uhmm ni ina so"
Hawaye ne ya digo mata dama ta iya saurin kuka "ya zaka rinka yi min hakane?"
Ganin abin nata na gaske ne ya dena wasan ya zama serious "what is wrong?"
"A iya sanina mata ne suke shagwaba amma tunda nazo gidan nan kullum kaine kake yi duk ka tare komai. To ni me zanyi don Allah" ta fada tana ware hannuwanta tayi kicin kicin da fuska.
Sai da yayi dariya mai isarsa har ta kule ta fara kai masa duka yana karewa yana cigaba da dariyar yace "idan nayi ki rarrasheni"
"Haka akeyi dama?"
"A gidan Dahiru da Mawadda ba" ya riko hannayenta da take kokarin dukansa dasu.
Kwafa tayi tace "har fa huduba aka yi min akan na rinka maka"
Cikin tausayawa yace "Allah sarki kice a baki wata satar amsar wannan dai na riga bari ma ki gani"
Zillewa ta soma yi ya kankameta suka kwanta yana dariya tana masa kukan shagwaba.
"Iyyeee ashe kin iya, kara sautin muji"
Rasa yadda zatayi dashi tayi duk abinda tayi sai ya mayar na tsokana. Wayarta ce ta soma ringing ya miko mata. Sunan Nawal ta gani amma muryar Attahir.
Muryarsa ta nuna yana cikin damuwa yace "Mawadda ina Dahiru?"
Kansa a cinyarta sai shige mata yake ta kasa magana da kyar tace "gashi nan"
Ajiyar zuciya yayi "bashi please"
Wayar ta dora masa akan kunne ya hada da hannunta ya rike. Attahir yace "dadinta dai nima ina da tawa matar amma Allah sai na rama. Kace karfe biyar zamu fita amma gashi shida saura kwata ina ta waya baka dauka"
Sai lokacin ya tuna wayarsa na falo. Attahir yana ta mita ya rinka dariya yana bashi hakuri. Idan yana tare da Mawadda baya sanin lokaci ya ja sosai.
Kafin ya ajiye wayar Attahir yace "kuma sai na fadawa Yaya Bilya me ka tsaya yi"
Kashewa Mawadda ido yayi ta kawar da kai tana murmushi yace "me nayi"
"Abinda zuciyarka ta raya maka" ya amsa da shakiyanci.
Jikin Mawadda ya sake makalewa ya sassauta "kai Attahir har kasa naji kunya"
Attahir ya hau salati "shikenan Dahiru ya lalace"
"Muka lalace dai"
Mawadda ta juyo da sauri ya dora hannu akan bakinsa yana duka sannan ya cewa Attahir ya bashi minti goma yana zuwa.
Kaya ta dauko masa yadi mara nauyi sky blue da hula mai fari da blue itama. Yana shiryawa yace mata shi dai baya son fitar ko yace musu sai gobe.
"Idan ka fasa ma bazan zauna a gidan ba saboda munyi fada"
Turare take fesa masa suke maganar ya karbi kwalbar ya ajiye "duk kin tayar da kwantacciyar soyayya zaki koreni. Haka zan tafi kina yi min gizo"
Kunya ce ta kamata ta rufe ido ya juyata tana kallon madubin.
A daidai kunnenta yace "bude ido ki tayani ganin matata"
Kanta ta kalla ta ba kanta dariya. Dahiru na bayanta yayi kyau sosai ita kuwa kayan jikinta duk sun gama yamutsewa saboda yadda ya tumurmusata akan gadon. Gashin kanta ya fita daga cikin ribbon din shima ya baje ko ina.
"Ji yadda ka mayar dani kamar sabon kamu"
"Sababbin kamu dai....amma na kin gane" ya kashe ido yana rike da hannunta suka je falo.
"Kije kasa bana son ki zauna kiyi ta tunani na kewata na damunki"
"Wai ni yaushe ka zama haka ne?"
"Tun lokacin da na fara ganinki. Sani ne bakiyi ba. Hmm bari naje kada mu tsinci Attahir a bakin kofa"
Bakin kofar kasa ta raka shi zai fita ta riko hannunsa "i will miss you"
"I know"
Ya saka idonsa cikin nata ta runtse nata da sauri. Hannu yasa a bayan kanta ya matso da ita ya shiga kissing dinta kamar wanda za'a kwace masa ita. Horn Attahir yayi da karfi ta ture shi ba shiri ya fita.
Yasha tsiya a mota tun yana ramawa har ya kama bakinsa ya tsuke don duk bakin da yayi yanzu still Attahir ya dama shi ya shanye.
******
*Kwana biyu da suka wuce*
Kamar ta durkusa a gaban mutanen biyu don magiya da roko. Fito da kudin da bata san adadinsu tayi ba.
"Bobo ga wannan ka bashi kuma na rantse idan ya fito min da Babawo a yau zan kara masa"
Bobo aminin BB wanda a gidansa aka ajiye Mawadda lokacin da suka sato ta. Mahaifinsa babba ne a gwamnati ya taso cikin gata da sangarta kamar BB din. A halin yanzu iyayensa ko keyarsa basa son gani saboda abubuwan kunya da ya jawo musu a unguwa da gari. Shiyasa ya karasa kangarewa duk abinda yasan zaiyi karshe ya komawa iyayensa baya bata lokaci wurin aiwatarwa kawai don ya bakanta musu. Uwa uba BB baisan zafin kudi ba yana sakar masa sosai.
Haj Mara da taimakon kofur Pascal wanda ta jika da kudi ta sami damar ganin BB shine ya bata numbar Bobo yace ta neme shi su fitar dashi.
Sunyi iya yinsu sun rasa hanyar kubutar dashi suka rasa mafitar da ta wuce hada baki da Kofur Pascal.
Kudaden hannunsa ya shafa yaji da nauyi ko da bai kirga ba.
"Hajiya kada ki damu. Nayi miki alkawarin zaki dauki yaronki ku tafi"
Wani abu da ya jima akan kirjinta taji ya sauka. Mutumin da ta bawa miliyan uku domin yayi musu visa ya bace a doron kasa don kuwa ta neme shi ta rasa. Kudaden hannunta sunyi mugun kasa amma bazata karaya ba. Idan Babawo ya fito sai su koma wani garin da zama. Zata ja masa kunne akan mata ko ta sami wata yar masu karamin karfin ta aura masa kowa ya huta.
Sun gama tsarin komai don Bobo master planner ne. Ko satar Mawadda shi ya kawo idea din yadda za'ayi. Wannan karon ma ya baje basirarsa ta kulle kulle kamar wata mace.
*4:07pm Police Station*
Kofur Pascal yana ganin abokan aikinsa mutum uku da suke teburin karbar korafi na farko da an shigo station din sun bingere da bacci ya kira Bobo yace ya shirya idan komai ya tafi daidai yanzu BB zai fito domin kamar yadda ya fada musu an shiga meeting akan case din wasu barayi. Sa'arsu daya cell din BB shine na farko ana shiga kuma an raba shi da Danmani saboda dukan da yake masa ko da an hukunta shi. Bude shi yayi ya fito sai wari yake ga ciwukan jikinsa jini ya bushe ya dankare. Da sauri sauri suka fito saboda yana kallo security dinsu ya zaga bandaki saboda murdawar ciki a dalilin abinda ya saka masa a fura.
Suna fitowa inda wadancan ke bacci guda cikinsu ashe baccin baiyi nisa ba amma bashi da kuzarin daga koda yatsa sai dai ya ga fitar BB da Pascal wanda ya kawo musu youghurt mai sanyi da aka sakawa maganin bacci.
A guje Bobo ya fizgi mota suka bar wurin shi kuma Pascal ya koma ya kwanta cikinsu kafin su DPO su fito daga meeting.
Ruwa da abinci wanda Haj Mara ta bada domin yaci kafin su iso inda zaa dauketa su wuce Kaduna ta tattare abinda zata iya su nausa kudu Bobo ya bashi. Kamar tsohon maye haka ya ringa gabzar abincin nan ko taunawa babu. Sai da yaji cikinsa kamar zai fashe yayi wata muguwar gyatsa.
Idanu a kekashe bayan Bobo ya gama yi masa bayanin komai yace "bazan bar garin nan ba sai na lahanta munafukin nan da ya aure min mata. Ko baccin kirki bana iyawa saboda tunanin suna can suna cin amanata"
Dariyar mugunta Bobo yayi "nasan zaka bukaci hakan BB shiyasa rannan nazo station din na bi bayansa bayan Pascal da ya fito da kai ya tabbatar min shine mijinta. To cut the story kit nasan gidansu"
"Muje gidan Bobo"
"What? Yanzun nan? Haba ka bari kaje wurin Hajiyarka idan an natsa kwana biyu ka dawo muje a gabansa wallahi ayi mata aiki"
"Idan banje yau ba bacin rai sai ya kasheni kafin 'yan sanda. Muje da wannan kazamin jikin a gaban idonsa ka daure min shi ya ga yadda ake nunawa mace soyayya"
Tafawa suka yi Bobo ya karkata mota sai unguwar Rijiyar zaki. Suna zuwa gidan Attahir da Dahiru suna fita. Gilashin motar Dahiru saboda tint ne sai suka yi zaton Mawadda tana baya suka shiga binsu har gate din gidan Dr Auwal. Ciki suka shiga da motar su BB suka jira a waje don yau sai ya wulalanta Mawadda da mijinta zaiji dadi. Haj Mara tana ta bugo wayar Bobo amma BB yace kada ya dauka bata plan zata yi.
*******
Da rawar jiki Dr Tani ta fito bakin nan har kunne tana ta murmushi.
"Menene haka 'ya'yana zaku tsaya daga waje. Ku shigo nan gidanku ne ku ba baki bane"
Murmushi suka yi a tare suka bi bayanta. Bayan sun gaisa ta tashi da kanta kawo musu abin sha sai bare-bare take bata son abinda zata batawa Dahiru yanzu ko kadan kuwa. Yaron yana burgeta inama nata ne ko mijin 'yarta.
Tana kawo musu ta tafi kiran Qareeba wai tazo sun zo dubata ne.
Itama da sauri ta tashi Dr Tani tace "yi hankali cikinki bai gama warkewa ba"
"To Mummy zabar mim kayan da zan saka"
Murmushin Dr Tani ya fadada ta dauko mata wani hadadden material ta saka. Fuska tasha kwalliya tana zuba kamshi suka fito tare.
"AHIRIIIINNN" tace tana saukowa baki bude.
"Anti Qareebaaaa" shima ya fada yadda tayi suna dariya shi da Attahir wanda sai lokacin ta kula dashi.
"Attashir ashe tare kuke"
"Eh wallahi Antinmu yaya karfin jiki?"
Sun gama gaisawa a mutumce suna dan taba hira Bilya ya kira yace ya iso dama cewa yayi zaizo da motarsa saboda yana da uzuri daga nan.
Attahir ya fita shigo dashi. Dahiru kuma yace da Dr Tani yana son magana da ita.
Qareeba na zumbura baki ta tashi ta basu wuri.
Hankalinta a dan tashe tace "lafiya dai ko?
"Akan Anti Qareeba ne"
"Dahiru zaka aureta ne?"
"A'a" yace da sauri.
Jikinta a sanyaye tace to me ya faru.
"Hajiya duk abubuwan rashin jindadin da suka faru tsakaninmu basu sa na dena tausayin Anti Qareeba ba. Ni da ke da mutane da dama kowa yasan tana son tayi aure"
Kwalla ce ta ciko a idanun Dr Tani "wallahi Dahiru ko waye yanzu yazo nemanta idan yana da sana'a zan bashi ko don kallon da ake yi mata na wadda aka yiwa fyade. Yar uwarka bata jin kunyar fada min tana son auren nan kaga idan bata yi ba sai mu sami matsala"
"Ko da dan uwana ne kuma makanike?"
Yawu ta hadiya ta kalli idanun Dahiru wanda suka matukar tsorata ta ranar da yace zai kona mata asibiti.
Bakinta yana rawa a hankali tace "makanike?"
Ya dage gira yana jiran ya gani ko zata fadi magana mara dadi su tattara su bar gidan. Duk halin shirmen Qareeba yana ganinta da wani dan mutumci tun bayan abinda BB yayi mata kuma ba don tozarci yake son hadata da dan uwan da bashi da kamarsa ba. Don ko me ya zama yau Bilya ne mafari.
"Eh makanike mai mace daya da 'ya'ya biyar. Yana da kirki fiye da zatonki kuma mutum ne mai tsananin hakuri....and yes yana da garejin kansa yanzu da mota ba yaron kowa bane"
Ga tsananin mamakinsa hawaye ne suke saukowa hadaddiya kuma rikakkiyar 'yar boko Dr Tani.
"Ko a cikin 'ya'ya Dahiru ka fita daban. Nagode kuma in sha Allahu zan baku mamaki a kotu. A shirye nake na rasa komai don ganin bayan Haj Mara da BB. Allah Yasa tayi masa yayan naka"
Murmushi Dahiru yayi wanda ya karawa fuskarsa kwarjini da kyau.
"Kada ki damu da wannan in sha Allah"
Tare suka koma falon lokacin Attahir ya shigo da Bilya. Kana ganinsa ka ga jinin Dahiru saboda kama da suke yi. Dukkansu suna da tsayi musamman Bilya da Danlami da suka rankwafa kadan. Shiga yayi ta kamala yayi kyau kallo daya zaka gane mutum ne mai sanyin hali.
Tunda suka shigo Qareeba ta kasa dauke ido daga kansa don sai da Dr Tani ta zauna a gefenta ta dan daki gefen kafarta tayi firgigit ta dago.
Sun gaisa da Dr Tani a take ya kwanta mata. To ita wane sauran zabe zata zauna bayan duka isharar da tayi ta gani a kwanakin nan.
Dahiru ne ya fara mikewa "Hajiya zamu je wurin Baba Prof mu dawo sai mu wuce gida"
Qareeba ta dago da sauri "dukkanku Ahirin?"
"Yayanmu Bilya zai jiramu a nan ba jimawa zamuyi ba"
Tayi wani fari da ido "no take your time fa sai na zauna dashi kada a barshi shi daya"
Bilya yana jin haka ya daga ya kalli Dahiru. Anya zai iya da wannan tunda yazo dama ta kafe shi da idanu.
Cikin sanyinsa da ya janyo masa raini a wurin Furera yace "ko dai na biku ne"
Qareeba taji kamar ya mareta daga zuwa sai tafiya "don Allah ka tsaya mu sake gaisawa sai na raka ka gidan. Ba nisa daga nan"
Attahir ya kunshe baki yayi waje Dahiru ya biyo bayansa "ba