Showing 57001 words to 60000 words out of 110071 words

Chapter 20 - GUMIN HALAK Hausa Novels by Maman Batul.txt

24 Sep 2025

1929

Ga kama gida da yake son yi shima basu gama zabar unguwa ba.

Attahir ya nuna masa hoton wasu akwatuna masu kyau da yake son zaba cikinsu.

"Ba don ka tsaya ruwan ido ba kaga kamata yayi komai muyi tare. Akwatunan nan so nayi na saya mana iri daya amma kada a saya har su fita yayi baka tsayar da mata ba tuzurun Haj Mama"

Dahiru yayi dariya "yanzu ma ai komai taren muke yi. Mata kuma kasha kuruminka Haj Mama ta kusa dena yi min korafin rashin aure ana kirana tuzuru"

Dundu Attahir ya kai masa yana cewa yaci amanarsa tunda bai sanar dashi da wuri ba. Labarin sake haduwa da Mawadda ya bashi domin kuwa amincinsu yasa ya sanar dashi rayuwarsa ta baya. Attahir na murna da wannan al'amari Dahiru ya sako zancen Anti Qareeba. Sunci dariya musamman Attahir wanda yaso kwarai ace yana wurin
"Da na wanke 'yar rainin wayo. Ni ka tabbata mamanta likita ce kuwa ba irin dafta dinnan da ake karawa gaban suna bace don ado?"

"Baka da kirki har asibiti gareta fa"

"To ai abin nasu ne ba ko kunya, gaskiya idan ka auri Qareeba sunan 'ya'yanka sorry. Tun wuri ma ka sani irin hadin zumuncin nan bazan yarda ba kada a cuceni a hada ni da jikoki 'yan ahirin"

Yana fada ya tashi a guje don Dahiru bayansa ya bi suna dariya. Haj Mama tana shigowa taja tsaki tana girgiza kai.

"Allah nagode Maka. Kattin maza maimakon su kawo min yaransu in rinka jin hayaniyarsu ina bari bari shine da kansu suke cika min kunne. Kodayake gara kai Attahir, wani yana nan sai sayen kaya da takalma yana kwalliya."

Dahiru yayi dariya yasan dashi take. Iyalin gidan nan suna kaunarshi suna nuna masa soyayya tamkar jininsu. Attahir ne yayi mata albishir da an kusa gabatar mata da suruka ai kuwa ta washe fuska tana murna.

Bayan fitarta ya matsawa Dahiru ya kamata su je ya ganta ya kara wasa mata dan uwansa don tayi saurin amincewa.

Tagumi Qareeba ta rafka tana zaune daga ita sai zani da tayi dauri ya leko ta kasa sai wata vest da hannut daya ya sabule. Ko wanka bata yi ba tun safe. Rashin mijin nan fa yana damunta sosai.

Dr Tani ce ta shigo dakin rike da leda ta dora mata akan cinya.

"Qareeba bana son wannan damuwa da kika shiga 'yan kwanakin nan"

"Kiji Mummy fa na rasa mijin aure ya bazan damu ba? Dashiru ya gujeni saboda wulakancin da kika yi masa da." Ta kare da tura baki.

Bakin Dr Tani ta doke "shashasha karshenta ma Dashiru kika rinka kiransa a gabansa ba dole ya gujeki. Yanzu dai bude ledar nan ki duba"

Ihun murna ta saka bayan ta bude . Material ne mai matukar kyau da tsada. Kamar yarinyar da aka yiwa kyautar bazata tace
"Mummy nawa ne?"

Zama Dr Tani tayi sannan cikin murna itama tace "ki tashi kiyi wanka ki kai dinki. Next week sunday Babawo zai zo wurinki. Ya dawo kuma da maganar aure"

Sakin kayan tayi "Cabdi sai kace wata mara aji Mummy? Sai da ya gadamar dawowa za'ace yazo neman aure. To ni na wuce ajinsa wallahi Dashiru nake so ki fadawa Daddy kawai"

Ranta ya soma baci don Qareeba bata san yadda ta zubar da nata ajin bane saboda nema mata miji.
"Dahirun me, har nawa yake kuma me ya taka? Banda ma lalura shi har zai taba yin arzikin da zamu roki alfarma wurinsa ne?"

Har ranta Qareeba bata so ana fadin abu mara dadi ga Dashirunta yanzu. Daukan kayan tayi ba don taso ba ta ajiye akan gado ta shiga wanka.

Da ta shirya ta fito ma kana ganinta kasan an bata mata rai. Dr Tani bata son biye mata dama ina su ina Dahiru dan mutan Tariwa. Kawai dai taso amfani dashi ne lokacin da babu kowa. Ita ba wai kudin su Haj Mara ne ya dameta ba kamar son 'yarta tayi auren da zai bawa duka danginsu 'yan bani na iya mamaki. A yanzu ansa musu ido kamar su kadai suka fara haihuwar 'yar da ta rasa miji.
******

Yadda Attahir ya matsawa Dahiru dole ya kira Mawadda ya sanar da ita zai zo da dan uwansa su gaisa.

Tana kwance tana hutawa sanda ya kira. Taji dadin jin zaizo don kwana tayi tunaninsa da kuma tunanin maganarsu da Baba. Ya zama dole ta yaki zuciyarta ta dakatar da alakar da take tunanin zata kare a ciwon zuciya. Shawarar Dr Imran zata bi da yace ta yawaita addua amma duk da haka zata yi kokari wurin janye masa.

"Sai ana magana dake ki shiga tunani. Shirun na mene?" Dahiru ya fada don ya fara ganeta da yawan tunani yanzu.

Mikewa tayi kafin tace "tunanin saurayina, sai dai kazo zan baka labari yau zance naje"

Sai da ya fito daga falon ya iya amsawa yadda yaji wani bala'in kishi ya taso masa abin har mamaki ya bashi.

"Me kika ce?"

Muryarsa ta fahimtar da ita yadda yaji sai kuma ta soma karaya.
"Asibiti naje ba na fada maka ina zuwa checkup ba"

"Mawaddatan wa Rahma!"

"Na'am inji larabawa"

"Bana son wannan wasan don Allah da gaske zance kika je? Likita ne saurayin naki?" Yayi magana cikin cijewa.

Sosai ransa ya baci da kishin da ya rufe masa ido. Bai jira ta ansa masa ba ma ya nanata mata zuwansu yanzu ya kashe wayar.

Hannunsa yasa ya rike bakinsa da habarsa idanunsa suka kankance. Karshe ya koma ya dafe saman motar Attahir da hannuwansa biyu ya dukar da kansa yana kallon kasa.

Attahir da yaji bai dawo ba ya fito ya sameshi a haka. Kafadarsa ya dafa hakan yasa shi juyowa suna kallon juna.

"Me ya faru?" Attahir ya tambaya don kallo daya zaka yi masa ka gane baya cikin nutsuwa.

"Wai ni Mawadda zata cewa taje zance? Likitan da yake dubata saurayinta ne. Wallahi bazan iya sake rasata ba Attahir. Na sota sosai a baya amma yanzu ni bansan yadda zan kwatanta maka kaunar da nake mata ba. Ban taba son wata mace ba sai ita kaima shaida ne"

Motar Attahir ya bude suka shiga sannan ya kalli Dahiru "calm down bro, har ka manta rabonka da ita ne kake tunanin yanzu komai zai zo da sauki kamar ba'ayi ba?"

"Nayi zaton itama tana sona....na tabbatar ne ma. Baka ji yadda kalamanta suka tsaya min a rai ba"

Attahir ya jinjina kai "ashe haka kake da kishi Dahiru? Lallai Mawadda sai tayi a hankali"

Shiru kawai yayi Attahir yaja mota suka fita. Lokacin da yaji labarin anyi mata fyade abu daya ne a ransa wato aure. Sai dai yafi kowa sanin me ya jima yana dannewa har mutane suke masa kallon kamar mutum marasa damuwa a rai. Ko Mawadda baya son ta san yadda yake burin haduwa da mutumin da yayi mata fyade. Ko ranar da tace masa taje Kaduna da ya bagarar da zancen yayi ne kawai saboda yadda yaji abin zai fama masa tsohon ciwonsa. Soyayyarta da son sanyata cikin farinciki sune suke dakushe bacin ransa da kishin da yake damunsa game da kaddarar da ta sameta.

Suna fitowa daga gidan daidai lokacin Qareeba ma ta fito zata kai dinki. Dahiru ta hango jiki na rawa ta zuke glass ta soma kwala masa kira. Ganin bai ji ba yasa kawai tabi bayansu.

Attahir yana ta kwantarwa da Dahiru hankali kafin su tsaya a gidan mai ya sami nutsuwa sosai.

Ana zuba musu mai Attahir yana waje kusa da me zuban man yayin da Dahiru yake zaune ya kwantar da kansa jikin kujera hade da lumshe idanu.

"AHIRIN" Qareeba tace da karfi tana tsaye daga waje saitinsa.

A firgice ya bude ido yayi tozali da ita. Tsabar rudewa ma ya manta ina yake ya taso da karfi ya buge kansa. Dama gashi rai a bace abu ya tarar masa.

"Lahhhh Dashiru sannu kaji" tace da ya fito.

Attahir kawai ya gani a gefensu yana murmushi don tana cewa Ahirin ya zagayo ya kuma gane ko wacece.

Kin kulata Dahiru yayi Attahir yace "Anti Qareeba daga ina haka"

Habawa dadi kamar ta saka ihu ta rabe jikin mota ta rufe fuska da mayafi irin na jin kunyar nan. Dahiru kansa sai da yayi murmushi sannan yace.

"Mai kika zo sha kema?"

"A'a na fito zani wurin dinki ne na hango ku shine na tsaya mu gaisa" ta sake amsawa tana ta fari da idanu.

Attahir ya gimtse dariyarsa "ko dai dan uwana ya hure miki idon ne naga yana ta kadawa"

Dahiru ya watsa masa harara ita kuwa ta kuma sunkuyar da kai "Kai dai baka da kunya da alama. Dashiru ashe kana bawa 'yan uwanka labarina gashi har ya ganeni. Don Allah ka ajiye komai ka dawo su Mummy sun amince da soyayyarmu. Yaya sunanka ne?" Ta kalli Attahir.

Yayi dariya "Ni Attashir nake"

Sakin fuska tayi "sunanku kusan daya da My Man"

"Kut..." Dahiru yace tsabar mamaki wai my man, sai dai bai sami damar karawa ba Attahir ya sakar masa dundu a baya yana masa sannu wai ya kware. Shi kuma yana make tasa dariyar da tarin karya.

Duk ta rude "Man sannu wayyo me ya sameka haka? Attashir do something mana!"

Attahir dariya taci karfinsa Dahiru bakinciki ya turnuke shi zata tara musu mutane an fara kallonsu ya ma kasa magana sai biye masa da yayi yana duka bayan nasa.

Qareeba ranta ya baci da dariyar Attahir ta karbi purewater ta bawa Dahiru sannan tayi masa wani kallo da ya kara tunzuro dariyar tasa. Bakin gwargwado yake kokarin boyewa ta sake kallon Dahiru.

"Sannu Man ko zaka zo na mayar da kai gida. Bana jin hankalina zai kwanta idan na barka da wannan dan uwan naka. I am sorry to say amma kamar yana da matsalar brain ko?"

Yace cikin gatse "haka kike gani?"

"Sosai kuwa , ka kware amma ya rinka dariya haka. Kada ku rinka raina lalura inji Mummyna gara ku kaishi asibiti"

Dahiru ya kamo Attahir shima kamar yayi dariyar sai dai so yake kawai ta tafi "haka muke fama dashi amma gara ki tafi don daga dariyar nan abin nasa gaba zai kara. Jeki kawai zan kaishi gida"

A tsorace ta matsa gefe "akwai number din malamin da aka kira yayi min karatu kwanaki ko na baku? Ni dai an tabbatar bani da aljanu amma wannan...mtsw..akwai serious problem"

"Sai nazo zan karba" Dahiru yace ya danna Attahir a mota wanda dariya ta sa ya soma hawaye.

Qareeba na ganin ya goge ido tayi baya tana sake cewa Dahiru yayi a hankali ya kunna motar suka yi gaba. Itama juyawa tayi tana adduar Man dinta ya isa gida lafiya.

Har suka tsaya a danja dariya suke yi. Attahir sai ya kalli Dahiru yace "My Man" sai su sake kwashewa da dariya.

"Man da gaske fa idan ka auri Woman babu zancen auren zumunci tsakanin 'ya'yanmu. Wai ji ko kadan bata ma fahimci ita ce abar dariyar ba"

"Ai baka ga komai ba. Ni da na zauna a gidan nasha kallo wani abin shiru ake yi kawai"

Har suka isa gidansu Mawadda suna dariyar Anti Qareeba.
******

Yanayin da Dahiru ya amsata da ajiye waya ya tsaya mata a rai. Jiki a sanyaye ta fita falon da take sauke shi ta sami Marwanu a kwance kan kujera yana bacci yazo hutu. Tashinsa tayi tace ya kwashe kwanukan abincin da ya soma tarawa daga zuwansa.

"Bako zaki yi ne Yayata ta kaina?" Ya tambaya yana daga gira.

"Jere zamu yiwa amaryarka dai" ta bashi amsa fuskarta ba walwala.

Tattare kayan yayi harda fesa wani turare da take hadawa na daki. Yana fita ya tambayi Ade me aka yiwa Mawadda tace itama tun jiya ta kula yanayinta ya sauya. Yaya tace sun sawa 'yarta ido a barta ta sarara.

Ba dadewa Dahiru ya sake kiranta yace sun iso. Har yanzu yana jin ba dadi saboda maganarta ta dazu kuma taji hakan a muryarsa. Ji tayi kamar tasa kuka da tayi tunanin me zaiyi kuma idan ta tabbatar masa da ya dena zuwa da sunan ganinta gabadaya.

Marwanu ne shigo dasu yana ta murnar ganin Dahiru. Sai da ya fita Mawadda ta shigo ta zauna a inda ta saba , bakin kofa.

Attahir ta gaisar ta dauke kai kamar bata ga Dahiru ba. Shima wayarsa ya shiga dannawa yaki kallonta.

Attahir yayi gyaran murya kamar suna jira duka su biyun suka kalle shi hakan yayi sanadin haduwar idanunsu. Mawadda ce ta soma kawar da kai gabanta yana faduwa. Ta rasa gane wane irin so take yiwa wannan Dahirun daga sake haduwarsu. Shima a nasa bangaren neman fushin ma yayi ya rasa amma sai ya basar ya kawar da kai.

Attahir ya gyara zama yana dariya "Fushin masoya da dadin kallo bari na dauka a waya ko na sami abin kallo da nishadi"

Murmushi Mawadda tayi "ayi haka Dan uwanmu? Ka tambayar min shi dai ko nayi masa laifi ne daga wasa"

Dahiru ya tabo "ka fada min me 'yar uwarmu tayi maka daga wasa ka shigo kana wani hade rai"

"Ta fada maka wurin wa taje zance har take iya fada min nida tace na tsaya iya yayanta kawai"

Juyowa yayi ya maimaita tambayar tace cikin murya mai rauni tana shirin kuka "ni wasa nake masa kace yayi hakuri bana so mu rabu haka"

Wata irin juyowa Dahiru yayi ya kalleta kafin ya sake cewa Attahir "kaji zancen rabuwa ma take min."

Attahir tashi yayi ganin abin ya soma zama na gaske "ni nayi nan idan kun gama sai ka kirani"

Matsawa tayi ciki ya fita ya barsu su kadai. Daga ita har Dahirun an rasa me cewa komai. Kusan minti uku kafin ya kawo karshen shirun nasu

"Duba wayarki nayi miki text"

Sai da ta harare shi ta duba wayar.

*Bazan iya rabuwa dake ba akan me zaki rinka zancen rabuwa?shi kuma wanda kika je wurin nashi yayi miki ganin karshe gara ki sani tun yanzu ina da kishi*

Sai da ta karance sakon tsaf sannan ta dago kai "an sami matsala fa, ni ban iya karatu ba"

Sake rubutu yayi yace "duba yanzu na tabbatar zaki iya karantawa"

Wayar ta sake kallo ta saki baki.

*nima ina sonki*

Bakinta yake ta kallo tana cije lebenta tana wani kyakkyawan murmushi tayi rubutu sannan tayi masa alama da ya duba tasa wayar.

*yaushe nace ina sonka?*

Ajiye wayarsa yayi kusa da ta Attahir da ya bari a kan kujerar sannan yace
"amsar abinda kike boyewa a zuciyarki na baki"

"Kace in fara turare a gidan nan na hadu da mai gani har hanji" tayi maganar cikin dariya.

"Ni tawa maitar tafi karfin turare idan na kama sai na...na dai yi shiru ki karasa a zuciyarki"

Kunya taji sai kuma tace "Allah Yayanmu ka iya rigima daga wasa duk ka tayar min da hankali."

"Kin tabbata har zancen rabuwar ma wasa ne?" Yace yana kafeta da ido.

Kokarin fahimtar dashi ta soma yi matsalolin da zasu iya tasowa daga dangi wanda bata so a maimaita irin na da.

Gabadaya maganganun bata masa rai suke yi don baya jin zai sake hakuri yadda yayi a baya. Sai da ya bari ta gama bayaninta kamar tayi kuka don ba karamin dauriya take yi ba yace

"Kiyi ki gama zille-zillen a daukoki a kawo min gidana"

Attahir ne ya tuna da wayarsa ya koma zai dauko.

Yadda Mawadda take a zaune kusan kan kafarta daya a takure Dahiru yace ta gyara zamanta mana bata gaji bane a haka. Tashi taso yi don itama ta gaji din kafar tayi tsami shi kuma Attahir ya taho bai ma kula ba ya kusa bugeta tunda a bakin kofa take. Motsin da taji yasa tayi baya ta zauna daram ba shiri.

Dahiru na ganin haka ya taso da zafin nama saboda ta kusa buguwa da kofa. Yadda ya taso ya bala'in bata tsoro dama gashi yamma tayi gari ya soma dubu. A lokacin babu abinda yake yawo a kanta sai BB balle da taga Attahir duka su biyun kasa gane kowa tayi sai mugun faduwar gaba ta sa ihu a razane har cikin gidan babu wanda bai ji ba.

Marwanu ne a gaba Baba ma ya taso yana sauri duk da yanayin jikinsa. Attahir dai gefe yaja yayin da Dahiru yayi yunkurin taimaka mata ta tashi don kwanciya tayi gabadaya ta cure jikinta wuri guda tana kuka.

"Don Allah ka rufa min asiri kar ka sake" take cewa da rokon kada yayi mata fyade.

Dahiru ja yayi baya zuciyarsa na kuna sai hawaye yake wanda bai ma san yana yi ba don tashin hankali.

Baba na zuwa ya zauna a gefenta yasa hannunsa mai lafiya ya rike hannunta daya sosai "bude idonki Mawadda nine"

Kuka take har yanzu tana surutai yasa Marwanu ya dago masa ita shi kanshi tasa muryar rawa take "ki kalleni Baba ne Mawadda"

Da kyar Dahiru yace "Wallahi babu abinda nayi mata. Faduwa tayi shine nayi niyar taimaka mata ta tashi"

Su Yaya suna son zuwa Inna ta hana tace su bari a shigo da ita tunda akwai baki a wurin.

Magana ta rarrashi Mal Fatihu ya cigaba sai a hankali ta bude idanun da ta runtse "Baba BB ne ya biyoni ko?"

"Bashi bane Dahiru ne kin ganshi can tsaye kin tada masa hankali" ya nuna mata inda Dahiru yake tsaye yana mai takaicin rashin damar taimakonta da tsinewa wannan BB din ko waye shi.

Attahir kuwa abin ba karamin tausayi ya bashi ba. Da taimakon Marwanu Mawadda ta tashi ya rike mata hannu kamar yarinya suka koma cikin gidan tana ta waigen Dahiru. Shima din ita yake kallo yana kara so da tausayinta.

Baba yace su zauna yana murmushinsa na manya yace "kada ka damu nan da 'yan kwanaki zata warware. Wannan yana daga cikin abubuwan da mukayi ta fama dasu a garin nan. Idan ka kula bata taba wuce bakin kofa duk inda yake da maza. Ko ni mahaifinta dakina indai ina ciki wallahi iyakarta kofa sai nayi kamar bangane ba"

"Amma Baba babu wani taimako da zamu iya yi mata ko asibiti?"

"Duk munyi Dahiru al'amarin ne sai a hankali zai wuce kila. Ban sani ba ko ta fada maka nace ku hakura da juna."

Da sauri Dahiru ya kalli Baba shi kuma ya cigaba da cewa "ina jinka tamkar dan cikina domin samun namiji irinka sai an tona. Kaso Mawadda lokacin da duniya ta juya mata baya na tabbatar bazata taba samun kamarka ba. Amma yau ka ganewa idanunka kadan daga tabon da yaron nan ya bar mata."

Runtse ido Dahiru yayi kawai don bakinciki.

"Har kullum ka dauki gidan nan gidanku amma na soke zancen aure don samun maslaha a rayuwar ku biyun"

Gabansa Dahiru yazo ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login