Showing 78001 words to 81000 words out of 110071 words
ta kalla mace da namiji da shi ma nurse din tace.
"You are fired! Ni zaku ci wa amana ku batawa yarinyata suna ta rasa miji"
Mamaki ya kamasu domin ko kadan su likitocin basu su ka fitar da zancen ba. Namijin ya cire whitecoat dinsa ya bugata da kasa.
"Asibitin ma da kike yin kudi da guminmu amma kin kasa biyanmu halak dinmu yadda ya kamata? Meye bama yi domin cigabansa amma albashinmu bai taka kara ya karya ba. Mtswwww" ya juya a fusace.
Cikin kankanin lokaci wurin ya kaure da surutu. Da gangan ma saboda samun dama da yawansu suka yi ta cewa anyi fyaden kuma magana yanzu suka fara. Kusan mutum hudu ta kora daga aiki harda kukanta ta gurgura Qareeba dakinta.
Asibitin ko ina maganganu ke tashi hatta dakunan patients. Gashi ta kori likitoci biyun da suke on call a lokacin shiyasa komai ita ake kira.
Su Dahiru sun iso asibitin dukkansu suka shiga reception suna kiran azo a taimakawa Ade. Dr Tani kai ya dau chaji kamar zata zare gashi yau mutane da dama ake ta kawowa.
Da gudu gudu ta sauko ance mata emergency idonta ya sauka akan Dahiru. Sakin fuska tayi kamar ba ita ba.
"Dana daga ina haka ba yau ake kawo amarya ba? Ko ka biyo ganin Qareeba ne"
Ade ya nuna mata batare da ya amsa ba "ki duba mamana faduwa tayi har yanzu bata farfado ba"
Matsowa tayi da sauri ta nuna daki aka kaita aka kwantar. Ta duka kanta tana tambayar me ya sameta Iya ta rike mata hannu tana kare mata kallo "DaftaTani?"
Dr Tani ta gyada kai ta dago ta kalli Iya kamar ta san fuskar nan.
Bata yi aune ba taji an shako wuyanta ta baya. Tana juyawa Yaya ta watsa mata yatsu biyar ta rike kumatu a gigice. Baba bai ce komai ba haka Inna domin sun ganeta suma.
Dakin yayi tsit suna mamakin wannan abu. Dahiru Yaya ta kalla idanu rufe da bacin rai
"mu bar asibitin nan tun kafin Sa'ade ta farfafo ta sake sumewa saboda bakinciki"
Cikin tsananin mamaki yace "Yaya kun santa ne?"
Baba ne ya nunata "Dahiru wannan matar ita ce ta bada shaidar karya a kotu aka saki yaron nan gashi yau a karo na biyu ya sace Mawadda a ranar aurenta"
Dr Tani tayi mugun kaduwa. Iyayen Mawadda ne yarinyar da ta canja duka evidence dinsu na asibiti karshe aka kori karar BB.
Hayaniya ta tayar da Ade abin mamaki Dr Tani ta gani a kusa da gadon. Da sauri ta tashi tana zubar hawaye ta gama jin me suke cewa tace
"Karasani ki ka zo yi yadda ki ka watsa mana rayuwa shekarun baya? Ku kaini gida gara na mutu da ta tabani"
Bacin ran Dahiru bazai misaltu ba. Idanunsa tamkar gauta sun kara kankancewa. Wani mugun kallo yake yiwa Dr Tani wanda ya karasa razana ta soma ja da baya don a ganinta wannan kallon nasa kadai ya fassara mata zai iya karar da numfashinta a duniya batare da yayi nadama ba.
"Dahiru ka tuna zaman da muka yi a baya kayi hakuri ban san kuna da alaka ba. Ka gani yadda nima yazo ya yiwa 'yar uwarka Qareeba"
Fuska babu alamun annuri yace "kina nufin mutumin da na hana ya yiwa 'yarki fyade shine wanda ya yiwa matata a shekarun baya?"
Ta zaro ido "matarka kuma?"
"Mawadda nake nufi ko kin manta sunanta yadda kika manta cutar da kika yi mata da iyayenta?"
Jikinta yayi mugun sanyi ta gyada kai. Dahiru kamar ya zare haka yake ji a wannan lokacin. Kusan kowa a dakin tsoron yanayinsa yake ji.
"Ban taba nadamar taimako ba musamman idan musulmi na yiwa. Amma a yau Dr Tani nayi, naji a raina ina ma ban je gidanki ba a wannan ranar yadda ya dandanawa Mawadda bakinciki inama ya yiwa taki 'yar kiji yadda su Ade suka ji. Kina babbar makiyata ace nayi zaman aiki a gidanki...Ya Allah" wasu zafafan hawaye ya goge.
Attahir ya yunkura ya riko hannunsa ya kwace da karfi ya daga zai mareta.
Tsawar Baba Prof ce ta dakatar dashi "DAHIRU!!! Bamuyi maka wannan tarbiyar ba kada ka yarda ka daki matar wani"
Sauke hannunsa yayi zuciya na tafasa ya sake matsawa daf da ita har lokacin ta kasa magana sai faduwar gaba.
"A yau na auri Mawadda kuma a yau BB din da ya kusa yiwa taki 'yar fyade ya saceta bayan abinda yayi mata 8 years ago. Kiyi addu'a Tani, ki tsananta addu'a domin ni Dahiru Ishak nayi miki alkawari idan ya kuskura ya sake maimaita kusantar iyalina wallahi babu wanda ya isa ya hanani mayar da tsinannan asibitin nan naki toka kinji na fada miki. Sai na kona shi da duk wanda ya rage a cikinsa" ya kare maganar da kada yatsunsa biyu a gaban fuskarta suka yi kara.
Durkushewa tayi a kasa ta hada hannuwanta biyu "don...."
Attahir ya yatsina fuska ya kada mata yatsa "kada ki bata bakinki babu wanda zai yafe miki. If I were you zan sallami duk wanda yake asibitin nan don na san dan uwana baya magana biyu."
Tare suka fice da Dahiru iyayensu suna kallonsu sun kasa yi musu magana. A jikin bango Dahiru ya ga Qareeba tana wani irin kuka saboda sai a yau komai ya warware mata. Mummynta tayi karya ne kawai don tayi aure. Ko kallo bata ishe shi ba ya wuce ga wani bala'in zugi da hannun damansa yake yi saboda targadensa da ya fama.
*****
BB da abokansa suna ta sheke ayarsu sun yi biris da Mawadda da take bugun kofar iyaka karfinta kamar zata ballata. Kuka take yi haikan tana hadashi da Allah ya duba darajar aure ya saketa ta tafi.
Tafi awa daya tana bugu tun tana roko har ta koma fada da nasihar yaji tsoron Allah.
Gajiya tayi ta koma bakin taga ta leka. Karfe ne ta waje ko ta sauke glass din babu damar fita. Bata ma san wace unguwa bace saboda a hanya rudewa tayi tana ta buge bugen kofa da magiya bata kallon ina suke bi. Ta dai kula wurin akwai karancin gidaje sai filaye da kango.
Iyayenta da Dahiru take tunani tana kara kuka. Ta san duk inda suke hankalinsu ba a kwance yake ba. Gashi tun a hanya su ka karbe mata jaka. Da suka iso ya zagaya zai daukota tace ya barta zata shiga da kanta. Banda tsoronsa da ya gama mamayeta tana kyamar ya tabata da kazantarsa tana matar Dahiru.
Kofar taji ana tabawa bugun zuciyarta ya karu.
BB ne ya shigo yasha wanka harda gyaran fuska ga shadda da hula yana ta kamshi. Ledar hannunsa yaje gabanta ya ajiye ta matsa baya da sauri ta sake mannewa da bango.
Murmushin gefen baki yayi mata "wai duk amarya sai ta yi pretending tana tsoron miji ne? Ni fa na sani kuna so tsabar gulma ce kawai ace muku nagari"
Bata ce masa komai ba ya dauko ledar ya bude kaza ce a ciki tana tiriri da kamshi.
"Ga fa abin arziki kazar amarci matso mu ci tun da zafinta"
"Ko maita nake yi bazan ci abin hannunka ba ko da yunwa zata kasheni"
Ya kada kafada "suit yourself" ya fara ci kamar shine mayen.
Bayan ya gama ya dauko juice a cikin fridge dake dakin ya tsiyaya a kofi ya haye gado yana sha.
Ran Mawadda ya soma baci ta yarda BB mahaukacin gaske ne da taji yace "amaryata yau fa daren farko me ki ka tanadar min?"
Neman makami take yi ido rufe bata samu ba yana kallonta ta gama dube dubenta ta gaji ta dawo tsakiyar dakin ta durkusa gwiwoyi a kasa "don Allah ka taimaka ka barni na tafi gida. Me nayi maka haka da zafi ka kasa hakura har kake bibiyata?"
Dariya yayi yana buga kafa "ashe zaki saduda my baby. Sonki nake yi amma saboda kwarewa wurin cin amana ki ka auri wani ba ni ba. Ga sadakinki nan ki dauka a waccan drawer din domin nima na aureki daga yau. Ki kwantar da hankalinki mu zauna lafiya"
"Baka da hankali ne?" Tace cikin daga murya.
"Kin tafi dashi kin barni da dakon sonki a raina. Mawadda ki karbeni a matsayin miji zan rike ki da gaskiya"
Me kuma zata ce masa tunda alamu sun nuna bashi da hankali ko kadan.
Tashi yayi ya fita bai dade ba sai gashi da kayan bacci.
"Daga ni sai ke muka rage amaryata kowa ya tafi yau an bar mana gidan kiyi wanka don yau ranarmu ce."
Bata yi masa musu ba ta karbi kayan ta shige bandakin. Rufe kofar tayi da mukulli ta zame a kasa ta rizgar kuka. Burinta ta bude ido ta ga Dahiru a gabanta. Tana nan zaune sama da rabin awa taji BB ya soma bugawa yana cewa ta bude.
Da farko kamar lallami ya fara sai gashi ya rikide yana zaginta ta uwa ta uba yana cewa hakurinsa ya kare.
Rasa wurin buya tayi ta gama tsorata tana jin numfashinta kamar zai dauke. Robar watsa ruwa ta dauko ta tsaya daga gefen kofar yana budewa ta rafka masa a kansa iya karfinta ta fita a guje tayi sa'a dakin a bude yake.
Kofar gidan an garkame ta kasa budewa ya biyo bayanta yana kiranta. Kitchen ta hango ta shiga babu kayan kirki a ciki da sauri ta rinka jan drawers tayi sa'ar dauko wuka.
BB ya shigo daga bakin kofa ya tsaya "kinsan bani da kyau Mawadda. Ki ajiye wannan haukan mu zauna lafiya kafin na tuna miki da waye BB."
Wukar ta saita a wuyanta har yanzu tana kuka amma kokari take ta dake zuciyarta domin idan tsoro yayi galaba ta suma shikenan zai sami yadda yake so "da ka tabani BB gara na kashe kaina"
A karo na farko da yaji tsoro kenan. Duk wahalar da yasha meye ribarsa idan ta mutu.
Ja yayi da baya "ajiye wukar kizo muyi magana. Ga wayarki nan" ya fito da wayar daga aljihunsa sannan yace "kizo ki kira ko ma wa zaki kira don baki isa na kaiki gida ba"
Jiki na rawa ta yar da wukar sannan ta taho bakin kofar ta mika hannu "bani"
Cafkota yayi yana kokarin hadata da jikinsa ta suka soma kokawa yana shirin fara yi mata muguntarsa ta duka ta dage ta kai masa wani naushin hauka a kasan mararsa sai gashi ya saketa ba shiri yana kurma ihu kamar mahaukaci. Wayarta ta dauke ta koma dakin ta rufe tana numfarfashi.
*****
Su Baffa sun iso daga Tariwa gidan Mal.Fatihu ya cika da 'yan jaje kamar ba dare ba. Dahiru da Attahir suna kofar gidan a mota bayan sun gama magana da 'yan sandan da suka zo.
Hannunsa da ya soma kumbura Attahir ya kalla "don Allah ka amince muje a gyara hannun nan kaga har ya fara kumburi"
"Ka barshi baya min ciwo"
"To idan ba'a gyara ba me zaka dauki 'Yar uwarmu idan ta dawo? Kada kace min da kafarta zata hau saman nan kana biye da ita"
Murmushi Dahiru yayi "nagode Attahir"
"Da me?"
"Komai ma, amma ka tafi wurin Nawal don Allah"
Daure fuska Attahir yayi "iyakar amintar tamu kenan Dahiru? Kana cikin wannan yanayin in shiga dakin amarya inyi me?"
Marwanu ne ya kwankwansa gilas din motar yace su shigo ciki akwai baki.
Da su ka shiga Dr Tani ce tare da mijinta da Qareeba da bata iya tafiya sosai sai an riketa. Ko zama Dahiru baiyi ba ya fita abinsa. Tana kuka ta shiga basu hakuri har take nuna musu Qareeba da labarin abin da BB yayi mata.
"Kinsan ance komai nisan jifa kasa zai fado. A da baki damu da halin da wannan iyali zasu shiga ba da abinda kika yi musu. Sai dai gashi tun a duniya kina ganin sakayya" cewar Baffa
Dr Auwal ya tayata basu hakuri da basu taimako wurin neman 'yarsu domin su ma neman BB din suke.
******
Loba boy ya sami wani gefe ya tsaya ya kira Garwashi.
"Oga hasashenka fa ya zama true"
Garwashi ya ture yarinyar da ke kusa dashi a wani club a Kaduna ya matsa gefe.
"Ina sauraronka me Danmani yake yi?"
Kwanaki biyu da suka wuce kafin Garwashi ya koma Kaduna ya ga Danmani da sabuwar waya. Yana tambayarsa sai cewa yayi cikin kudin da suka raba ya siyo. Garwashi ya karba yana gani shi kuma Danmani shaf ya manta da hotunan Mawadda da ya daukowa BB. Batare da nuna fushi ba yayi saurin rufe folder din hotunan ya cigaba da dube dube amma zuciyarsa ta bashi babban yaron nasa ya ha'incesu ne shiyasa da duka suka yi shirin komawa Kaduna yace yana da uzuri sai Garwashi ya rabu dashi amma ya bar Loba boy yana binsa a boye.
Shi Loba boy ya jima yana harin mukamin Danmani yana son zama na hannun dama sai yanzu dama tazo.
Garwashi ya gama jin bayaninsa na satar amarya ya kutuntuma ashar "kai baka wurin nace zamu yi mata solidarity saboda 'yar uwa ce 'yar Kano ce?"
Loba boy an sami yadda ake so zai ture gwamnatin Danmani yace "Oga alakar tafi haka ma. Sai da abin ya faru na gane ashe dangin matar kawuna ce"
"Bana son shafta Loba boy. Ita da suke Bebeji kai kuma Dawakin kudu?"
"Oga ashe baka sani ba Bebejin daga jikin Dawakin kudu aka yanketa lokacin mulkin sojoji"
Garwashi rai ya baci kuwa jin haka yace "kace dai wannan rigimarmu ce ta famili lallai Danmani don wulakanci abin kuma harda tabo gida"
Loba boy ya cigaba da ingiza shi yace kada yayi komai gobe da sassafe zasu taho Kano.
******
Sun cika alkawari kuwa domin karfe goma da rabi ma a garin Kano tayi musu. Zama suka yi kamar wasu 'yan sanda suka gama tsara yadda zasu sulala Danmani kamar tafasasshen nama.
******
Yadda Mawadda bata runtsa ba haka su Dahiru suka kwana tare da iyayenta. Gari na wayewa suka koma ofishin 'yan sanda aka sanar dasu ana bincike sosai su cigaba da addu'a.
Hannun Dahiru ya kumbura Baba da kansa ya nemi mai gyara aka matsa matsa ya shigo ciki lokacin ya matsawa Attahir shima ya tafi gidan Baba Prof ganin Nawal.
An gama gyaran Attahir ya dawo yaci karo dasu Garwashi a kofar gidan. Wai saboda kada ace musu 'yan daba shine duka su biyar suka sako manyan kaya burum burum kamar wasu barayi.
Hannu Garwashi ya mikawa Attahir suka gaisa yace sun kawo taimako ne suna bukatar izinin ganin iyayen amaryar da aka sace ko babanta.
Attahir ya hade rai "kun zo damfara dai to ayi gaba mun yafe"
Garwashi ya rage murya yace sun zo da bayani ne akan BB. Janyo shi Attahir yayi suka yi ciki sauran na biye dasu.
Baffa yace "wadannan fa?"
Garwashi yace yana so a rage jama'a ko su sami wuri da zasuyi magana babu takurawa domin aikinsu na bukatar sirri. Ba don sun yarda ba sai don ganin Dahiru ya tada hankalinsa yace a sauraresu suka tashi suka koma dan falon nan. Wuri ya cunkushe Attahir yace ko zasu koma gidansu ne tunda Garwashi yace baya son hayaniya a bakin aikinsa. Mamaki suke yi amma ga dukkan alamu dai bai yi kama da irin malaman bogin nan ba. Rankayawa suka yi gidan Baba Prof aka zubawa su Garwashi idanu.
Dariya yayi ya soma musu bayanin kansu da haduwarsu da BB da kuma sa hannun Danmani da suke zargi.
"Zamu taimaka saboda munyi alkawarin solidarity ga 'yar uwa. Kuma ashe ma dangin matar kawun wannan ce ta wajen kakarta mace ko? " ya nuna Loba boy.
Inna da Iya suka kalli juna. Iya tace "ko kece naga kamar yana da billenku?"
Innar Fatihu ta rufe billenta da sauri "meye haka ne TaRasulu?"
Baba Prof yace sun basu dama amma idan suka ga ranin wayo su shirya zasu damka su wurin 'yan sanda ne.
Garwashi ya dubi wani yaronsa ya ce masa fara.
Yaron ya bukaci shiru banda ko da tari ne sannan ya kunna wayarsa ya bude recorder ya karkace kai sai gashi ya fara muryar Nasiru Salisu Zango
_"a yau ne kuma majiyar inda ranka take dauke da labari mai cike da al'ajabi inda iftila'i ya afkawa wata amarya. Amaryar dai wadda danginta suka bukaci a sakaya sunanta wasu bata gari ne suka yi sama da fadi da ita kamar allura an nemeta an rasa a cikin zugar kai amarya. Yanzu haka iyayenta da sabon ango suna cikin gagari suna rokon duk wanda yake da wani bayani da zai taimaka wurin ganota ya nemesu ta wannan lambar waya da zan bayar. Angon harda alkawarin kyauta mai tsoka ga wanda ya sada shi da amaryarsa. Ga dai yadda mukayi da angon"_
Matashin da baifi shekaru ashirin da shida ba ya sake karkata ya kyabe fuska kamar mai kuka sai ha murya ta fito a raunane
_Don Allah ko waye ya dauketa kada ku cutar min da mata. idan kudi kuke so zan bada miliyan daya da rabi ga duk wanda ya taimaka ko yaya ne_
Daga nan ya sake komawa muryar Zango _"to Allah shi kyauta amma ga dukkan alamu lokaci yayi da za'a fara daukar rijistar masu zuwa daukar amarya."_
Kusan kowa sakin baki yayi bayan yaron ya gama Garwashi ya kira Danmani yasa wayar a speaker. Dahiru da Baba suka matso kusa yayi musu alama da suyi shiru.
"Oga ya kana lafiya?"
"Kai Danmani kana Kano abu irin wannan ya faru baka fada mana ba sai wani ne cikin abokai na yace yasan ina da network ya turo min rakodin din"
Danmani ya dan tsorata "ban gane ba Oga"
Garwashi ya rage murya "kaga yanzu nake ji an sace wata amarya jiya angon yayi alkawarin miliyan daya da rabi. To nafi son muyi aikin nan mu biyu a kyale su Loba boy yadda kake ta bani shawara"
Tashi Danmani yayi jiki na bari bayan Garwashi ya kunna recording din da ya manna da wayarsa ya gama ji. Yace masa "ance Kano ta rude mutumina kowa na son nemota, ni kaina sammako nayo na shigo gari kazo mu hau aiki"
Danmani mayen kudi wanda shine babban lagonsa yace "Oga ina jin fa mutumin nan BB ne ya sace matar da ya tura mu aiki a kanta. Haka kawai hankalina bai kwanta dashi ba bayan ya bamu kudin nan har gidan da yake nabi bayansa rannan. To amma daga baya na share. Kana ina ne mu hadu sai mu nemi angon. Sai dai banji lambar wayar ba"
Garwashi yayi murmushin saurin kama Danmani "bari naje gidansu mu tabbatar sai na sameka a cikin gari mu wuce"
Babu wani dogon tunani Danmani ya amince. Shi akan kudi dama kansa toshewa yake. Dahiru ne ya bawa kowa mamaki da yazo