Showing 81001 words to 84000 words out of 110071 words
ya rungume Garwashi yana masa godiya tun ba'a ganta ba. Jiran minti shabiyar suka yi bayan anyi notifying 'yan sanda amma basu sanar dasu su waye Garwashi ba domin sunyi musu halacci.
Danmani doki ya hana shi sakat ya kira Garwashi yace su hadu a hanya. 'Yan sanda suka yi basaja akayi akayi Dahiru ya zauna ba'a sani ba ko suna da makamai ya dage sai yaje.
*****
BB yayi kwanan izaya don ya daku fiye da tunaninsa. Gumi yake ta yarfewa a nan falon ya kwana a yashe. Mawadda tana daki tana kuka bayan tayi sallah. Wayarta ta kalla ta sake fashewa da wani kukan. Ashe fanko ce ya cire batir din.
Da kyar ya tashi ya rarrafa ya dauko wayarsa ya kira Bobo yace yazo ya kaishi asibiti. Sannan ya koma kofar dakin yana bugawa yace idan bata bude ba har ya bude da kansa zai bata mamaki.
Jikinta yana rawa tana tsoron kada ya bude ya sake maimaita abinda yayi mata ta danne kofar tana kuka. Wannan mutum ya zame mata masifa.
A waje kuma Garwashi da Danmani ne suka sauka daga babur din da Danmanin yazo dashi a kofar gidan. Daga bayansu batare da saninsa ba su Dahiru ne da 'yan sanda.
"Oga ko zaka bani lambar mijin nata na kira sai su taho. Jikina yana bani ita ce amaryar kuma tana gidan nan" Danmani yace cike da zumudi.
"Nima jikina ya bani dan ubanka" Garwashi ya shake masa wuya nan da nan su Dahiru suka fito.
'Yan sanda suka zagaye su Garwashi ya nuna Danmani "wannan ne dan daban da nake fada muku da hannunsa aka saceta yace tana gidan nan"
Danmani ya zaro idanu "Oga nine fa, karya yake shine shugabanmu"
Dahiru yayi murmushi ya ce da Inspector din "wannan dan agaji ne da ya taimaka mana"
Wani sergent ne ya ingiza Danmani cikin motarsu aka saka mai ankwa sai rantsuwa yake tare suke da Garwashi.
Gate din suka buga wani buzu ya bude a zatonsa abokan BB ne don ya san wane irin mutane yake yiwa gadi. Bude baki yayi zaiyi ihu Attahir ya toshe shi sannan shima 'yan sanda suka tura shi waje suka shiga.
Bugun farko a kofar BB yana daga kwance ya baje yana shan iska saboda azaba yace kofar a bude take.
Kamar daga sama ya ga 'yan sanda da su Dahiru sun shigo. Su Baba ma ashe sun biyo bayansu sai gasu ya tashi da sauri babu wurin gudu.
Kansa Dahiru yayi hannusa ya hana shi dukansa yadda yaso. BB yasan yau dai karyarsa ta kare bashi da sauran mafaka ya soma dariya "ka biyomu ne ka sami sudin da na rage maka? Jeka tana ciki jiya ta shayar dani soyayyar ban mamaki"
Wani kukan kura Dahiru yayi da hannunsa na hagu ya doki bakin BB sai ga hakora uku a take sun zubo. Ya kuma danne shi a kasa yana duka Attahir yana taya shi.
Inspector zai hana Garwashi yace "Yallabai ka auna ka gani idan matarka ce"
Su Dahiru sun yi masa mugun duka don ma 'yan sandan suna hana su tare da su Baba da Baffa.
Ligi-ligi aka daga shi baki na jini yace "wallahi nima sai an bi min hakkina"
Inspector din ya kalli abokan aikinsa "ku cikinku waye ya ga wanda ya cirewa mutumin nan hakora?"
Girgiza kai suka yi kowa yace bai kula ba. Garwashi yace shi ya gani tuntube yayi ya fadi.
Mawadda tana cikin daki a takure don bata jiyo su saboda gidan kato ne taji ana buga kofar dakin.
A tsorace tace "wallahi idan ka shigo zan kasheka nima na kashe kaina"
Dahiru yayi ajiyar zuciya ya dora hannu a jikin kofar ya jingina "Mawaddatan wa Rahma"
Ji tayi kamar tana mafarki ta taho jikin kofar da gudu itama ta jingina "Yayanmu?"
"Matarmu!"
Wani kuka ta soma amma na farinciki ta bude kofar da saurinta.
Dahiru yana tsaye ta bude suka hada ido. Zukatansu ke bugawa da soyayyar da suke yiwa juna. Gani take yi kamar mafarki take Dahiru yazo cetonta.
A hankali ta tako gabansa tasa hannu ta shafa fuskarsa don kawai ta tabbatar ba gizo yake mata ba. Lumshe ido yayi yau ranar farko da hannun Mawadda ya taba jikinsa ya kama hannun ya sumbaci tsakiyarsa.
Rufe ido tayi wasu hawayen masu dumi suka gangaro tace "kaine?"
"Nine?"
"Ka tabbata ba mafarki nake ba?" Ta sake tambayarsa yana matsowa gabanta.
Ba tare da ya dauke idanu daga kanta ba yace "Mijin Mawadda ne a gaban Matar Dahiru"
Jikinta na rawa ta rasa da yadda zata kwatanta farincikinta Dahiru ya janyo hannunta "come here"
Yace yana rungumeta tsam a jikinsa. Kusan a tare suke sauke numfashi yana kara matseta a jikinsa. Samun kanta tayi da jin kunyarsa balle da ya dago habarta da yatsunsa biyu ya kusanto da kansa kasa yana kokarin hada lebensa da nata.
"To ya isa wallahi baka isa ba kuma" Attahir yace ya wani kanne ido daya yana kallonsu da daya idon.
Dahiru ya sake riko Mawadda ta barin hannunsa mai lafiya ta sa hannayenta ta rufe fuska ya harare shi "sa ido kowa yana falo meye na biyoni har nan"
"Gani nayi zaka wuceni. A ka'ida ni aka fara daurawa aure amma ko dan kiss dinnan na hakura dashi ina maka *_SOLIDARITY_* shine kai kuma zaka min solo. 'Yar uwarmu welcome back kinji muje daga waje wurin su Baba"
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰21
*Batul Mamman*💖
Sai da suka kusa kofar gidan Dahiru ya saki hannunta ba don yaso ba. Wurin Baba tayi a guje ta fad jikinsa tana kuka. Abinka da mutan karkara ga rashin sabo sai yayi ta sunne kai cikin kunyar su Baffa. Ita kuwa kuka take bilhaqqi. Ganin haka Baffa yace su shiga mota su koma gida domin ta sami nutsuwa.
BB suka ga an fito dashi yana tafiya da kyar ga fuska ta dame babu kyan gani. Da farko tsoro ya fara ji da aka tura shi cikin motar 'yan sandan. Sai daga baya da ya tuno mahaifiyarsa zata yi komai domin fito dashi yayi wani munafukin murmushi. Baya jin duk kudin da mutanen suke dashi sun kai mahaifinsa. Kudin mahaifinsa kuwa Hajiyarsa sai yadda tayi dashi.
Gabadaya suka dunguma zuwa gidan Baba Prof tunda kowa yana can. Daga waje aka tarbesu tsabar farinciki sun kasa jira a shigo da ita ciki. Yayyenta su Bilki da kanne su Saifullahi duka suna gidan ana kukan murna. Rafi'a ce kawai tun da akace an ganta Yaya tace ta tafi gida tayi girki mai rai da lafiya. Maman Nawal ma da Babanta ba'a barsu a baya ba.
Ba ko kunya Mawadda ta makale Ade bayan ta gama rungumar su Yaya da 'yan uwanta. Bata taba tunanin zata tsira daga sharrin BB da wuri haka ba. Bayan an zazzauna an sake jajantawa juna su Yaya suka ce gara su wuce gida da ita a samu tayi wanka taci abinci.
Haj Mama ta bata rai "Amarya fa tazo kenan sai dai ku yi hakuri zata kawo muku ziyara idan taji dama-dama nan da kamar sati guda. Nan za tayi wankan da cin abincin ko 'yata?" Ta kare da murmushi tana rike da hannun Mawadda.
Sunkuyar da kai tayi tana mai jin kunyarta. Dahiru na jin haka ya tashi yayi waje Attahir ya biyo bayanshi.
"Kaima fa ya kamata muje muyi wankan nan muci abinci"
Sai da ya harare shi yace "baka ji ba wai a nan zata zauna har sati, kila kai ba ka da matsala za'a baka matarka ku tafi"
Dariya Attahir ta rinka masa ya kuwa kara bashi haushi.
"Da nasan hakane dazu da na kyaleka kun dan..."
Kansa ya ga Dahiru yayi ya nuna masa hannunsa "yau fa kaine za ka ji jiki don ni kam hannu biyu gareni"
Dama sun saba da wasan bin juna tun farkon zuwan Dahiru gidan ya fahimci Attahir yana da tsokana. Kofa Dahirun ya nuna masa.
"Ko dai kaje ka fito min da matata ko kuma naje na janyota kuma ince kaine ka fada min ance nazo na janyota"
"Da gaske kake ko wasa"
"Ana wasa da angon da aka hana amaryarsa ne?"
Attahir ya kada kai "a'a"
"To ka taimakeni idan ba haka ba muje gidan a kasa wurinku zan kwana kasan mara lafiya sai da jinya" yace yana dariyar mugunta.
Attahir ya san ko bai kwana ba Dahiru zai iya zuwa ya zauna don kawai ya takura shi. Bata fuska yayi yace "na shiga uku inji mata. Yanzu me zan ce musu?"
"Oho ina nan" yace yana juyar da kansa gefe shima yana dariya.
A falo kuma bayan Haj Mama tace Mawadda zata kwana a gidan Baba Prof kallonta yayi ya dubi su Baffa "kunji halin mata wai a barta sati daya, mijin nata kuma fa? Mafi dacewa su dauki matansu su wuce gida Allah Ya bada zaman lafiya"
"Banda abinsu ma me ya rage kuma" inji Baffa.
Innar su Dahiru ta nuna itama tafi son a barta taje gida "yarinya duk wahalar da tasha ku barta taje taji dumin iyaye a kaita daga baya
Wata karamar muhawara suke neman yi 'ya'yansu suka tashi suka basu wuri.
Baba da kansa da ya kula zancen yaki karewa kowa na kawo dalilinsa yace ya amince ta bi mijinta babu damuwa.
Baba Prof yayi murmushi "Yauwa Mal Fatihu ka gama magana bari a kirawo su dai muyi musu nasihar da bata samu ba jiya su wuce"
Hamdala Attahir ya rinka yi da yaji an chanja shawarar ya kirawo Dahiru da Nawal dama Mawadda tana wurin.
Baffa da Baba duk wanda aka ce yayi magana sai yace ya barwa Baba Prof wannan huruminsa ne domin gabadayansu ya mayar dasu tamkar 'yan uwansa har da Baba da bai dade da sani ba.
Godiya ya fara yi ga Allah SWT da Ya dawo musu da Mawadda lafiya sannan yayi musu nasiha akan zaman lafiya da juna da biyayya ga mazajensu. Matan ya kalla kowacce kai a kasa suna hawaye saboda nasihar tasa ta kashe musu jiki.
"Hadin kanku shine hadin kan mazajenku. Ku sani ku ba kishiyoyi bane sannan samun mazajenku ba daya ba saboda haka kada muji kada mu gani wai rigima ta tashi saboda kinga wance da zani naki mijin bai saya miki ba. Zama irin haka idan kuka tsarkake zukatanku yafi komai dadi ku zamewa juna 'yan uwa. Amma idan aka tsiro da kyashi da hassada wadda sukan bullo a rayuwar zaman tare to baza'a je ko ina ba gayyar zata watse. Allah Ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyiba. Kuma Allah Ya hada mana kawunanku"
Falo ya kaure da "AMIN"
Mawadda da Nawal suka kare kukansu suka yo waje tare da 'yan uwansu.
Attahir ya karbi mukullin motar Dahiru yace zai tuka su duka saboda hannunsa washegari zai dawo daukar tasa.
Nawal ta zaga zata shiga baya Attahir yace ta dawo gaba "mutumin nan hararata fa zaiyi ta yi yace na hanashi zama kusa da matarsa. Ki dawo gaba kawai"
Murmushi suka yi ita da Mawadda suka shige bayan yana ta magiya. Dahiru ya shiga gaba yana masa dariya "so kake ta biye maka ta zauna ka jefamu a rami ko?"
Suna tafe suna taba hira a tsakaninsu mazan don Mawadda da Nawal kowacce ta fada duniyar tunani da fargabar sabuwar rayuwar da zasu tunkara a yau.
Yaya ce ta kira Dahiru da wayar Saifullahi tace Marwanu zai kai musu abinci daga gidan Rafi'a kada su saka matansu girki. Godiya yayi mata ta sake tambayarsa yaya 'yarta babu matsala ko.
Murmushi yayi yace babu ko ya bata ne sai taji kunya tace a'a. Ba'a dade ba sai Ade ma ta kira itama dai so take taji yaya Mawadda take ya maimaita mata yadda suka yi da Yaya a kunyace ta ajiye wayar da yace zai bata itama.
Murmushi yayi yadda suke son 'yar tasu ya burge shi da irin zaman amanar dake tsakaninsu kamar ba kishiyoyi ba.
Layin gidan nasu kusan duka sababbin gidaje ne harda titi har kofar gidan. Dakin maigadi dai babu kowa Dahiru ne ya bude Attahir ya shigo. Wurin ajiye mota zai ci motoci hudu ma ga borehole da katon tanki a jikin katanga daga karshen gidan.
Gidan nasu tun daga waje yayi kyau. Kofa ce daga can karshe a kasa ta karfe wadda ta nan bene ne kawai zuwa saman inda su Dahiru zasu zauna.
Suna fitowa kowacce ciki ya duri ruwa sai rabewa suke a gefe. Attahir yace " 'yar uwarmu Allah Ya bamu alkhairi bari mu shiga ciki"
Kanta a kasa tace "to mungode Allah Ya saka da alkhairi"
Nawal ta kalleta kamar tayi kuka ganin yadda mijin nata yake ta rawar kai duk ta firgice. To itama Mawaddan dauriya ce kawai ta kalleta tayi murmushin dole.
Dahiru ya kama hannun Attahir "Dan uwa Allah Ya saka da alkhairi"
"Ka ji ka da wani zance sai da safe kaji"
"Sauran sallolin yau an yafe maka jam'i ne?" Dahiru ya amsa yana tsokanarsa sannan kowa yayi gaba matarsa tana biye dashi.
*****
Da sallama ta shiga gidan wani hadadden kamshin turaren wuta ya ziyarci hancinta. Duka turarukanta hatta humra da kanta ta hada saboda yanzu ta gama kwarewa. Kullum jikinta cikin sassanyan kamshi yake yau da gobe sana'arta ta janyo hakan balle kuma tana amaryarta guda.
Katon falon nasu suka shiga wanda aka kawata da kayan alatu na zamani. Daga gefen inda kofar kitchen take harda dinning table da kitchen cabinet. Kalle kallen dai ba yau ba ta samu wuri akan kujerar mutum daya ta zauna a takure.
Kujerar gefenta Dahiru ya zauna ya mika hannu ya riko hannunta daya. Jikinta taji yayi sanyi fiye da yadda taji dazu da suka hadu ko don lokacin tana tattare da fargaba ne.
"Mawaddatan wa Rahma yau gaki a gidan Dahiru a matsayin matarsa. Babban burina ya cika ina fata zamu zauna lafiya mu rike juna tsakani da Allah"
Kanta a kasa tace "In sha Allah."
Irin kararrawar nan mai sallama ce ta doka sallama a falon. Daga wajen kofar hawa saman Dahiru ya saka saboda kada a buga basu ji ba idan kofar saman a rufe take. Mike yayi yace mata yana zuwa. Fita ta ga yayi bai dade ba ya dawo rike da kwandon abinci.
"Marwanu ne ya kawo"
Hannunsa na dama ta kalla har yanzu da kumburi ga dukkan alamu yana masa ciwo ta tashi ta karbi kwandon ta ajiye a kan dinning table.
Har lokacin yana tsaye "bari na nemo plates to tunda kin karasa min wannan ladan"
"A'a barshi zan duba" tace tana dan waige. Plates ne masu kyau da cokula, kofuna da jugs a cikin kitchen cabinet din da yake manne a bango daga bayan table din komai a jere yadda ya kamata. Budewa tayi ta dauko plates biyu, da sauran kayan bukata ta ajiye.
Gani tayi ya ja kujera daya ya zauna tace "in zuba maka?"
Ya tsareta da ido ganin jikinta ya soma rawa amma tana ta kokarin boye masa "ki zuba mana dai"
"Na'am?" Tace a sanyaye tana mai fargabar kada ta fara wannan abin don tunda ya tsayaba wurin table din taji zuciyarta ta tsinke.
"Kinji me nace ko yau ma kurumtar ce ta tashi?"
Cije lebenta tayi tana karfafawa kanta gwiwar kada ta tsorata yaji babu dadi shi kuma ya kawar da kansa yana mai tuna maganar da Inna tayi masa jiya bayan daurin aure. Ita ma kuma Yaya ce ta fara yi mata bayanin yanayin da Mawadda kan shiga idan ta kebe da namiji na tsoro da firgici.
_"Dahiru kai ba bako bane game da sanin wacece Mawadda. 'Yar shawara zan baka ka sani cewa soyayya daban sha'awa daban. Duk son da take yi maka kasan kaddarar da ta afka mata a baya har yanzu tana iya tasiri a kanta. Idan kana son samun nutsuwa da kwanciyar hankali a gidanka ka fara neman kusanci da yarda daga matarka kafin ka bijiro mata da wani abu daban. Ina fata ka fahimceni. Idan kaje mata lokaci guda tana iya alakanta hakan da wannan lamari na baya ku zo kuna samun sabani"_
Wannan sune kalaman Inna gareshi kafin ya baro Tariwa. Ya gamsu da su dari bisa dari ya kuma san cewa hakan shine zai sanya shakuwa a tsakaninsu.
A plate daya ta zuba musu abincin dayan kuma ta zuba soyayyan naman kaza.
Kallonta yayi ya sake kallon abincin "kin tabbata zai ishemu? Ina jin yunwa sosai"
Bata ce komai ba ta kara musu. Tana gamawa ya sake hada komai a cikin kwandon "bari na kaiwa su Attahir"
Jin haka tayi murmushi saboda tayi wannan tunanin sai dai kuma tsoron kada ya zama kaiwar akwai takura.
Inda ya barta ya dawo ya sameta. Kujera yaja ya zauna sannan yace ta zauna ganin ta tana tsaye har lokacin.
"Matarmu kinsan me nake so dake?"
Ta girgiza kai a hankali tana jin alamun hawaye mara dalili.
"Don Allahi ki cire komai a ranki ki saki jikinki. Ban aureki domin na takura ki ba duk da nasan cewa da wahala idan kowacce amarya ba haka take yi ba. Amma kinga mu special case ne."
Yadda yake daga gira yasa ta murmushi tace "kamar yaya?"
"Kinga dai ke da rana tsaka kika tare, gashi ango ya shigo ko kullin kazar al'ada babu. Sannan kin shigo gidanki babu irin kwalliyar nan ko inji kamshiki tun daga kasa"
Kallon kayanta tayi mayafin duk ya yamutse shi kuma ya nuna mata fuskarta a jikin wayarsa ta kode idanu zuru-zuru. Ita kanta ta bawa kanta dariya wai amarya kenan.
Turbune fuska tayi cikin shagwaba "ai kasan me ya janyo hakan"
"Na sani shiyasa nace miki komai namu daban ne. Saboda haka nake so daga yau har ranar da tayi miki ki dauke ni a matsayin yayanki, kaninki ko abokinki. Duk wanda kike so ki zaba. Ni kuma zan jira ki zuwa lokacin da kanki zaki dawo dani miji."
Sunkuyar da kai tayi ya ga hawaye ya diga akan tafin hannunta.
"Kina so muyi fada ne?"
"A'a"
"Na soke kuka a gidan nan daga yau. Idan kika kuskura na kamaki kina kuka zaki sha mamakin abinda zanyi"
Goge hawayen tayi ya taso ya dagota tsaye sannan ya rabata da jikinsa ya daga waya "hoton tarihi zanyi mana"
Hannu biyu tasa ta rufe fuskarta "naki wayon wallahi bazanyi kyau ba"
"Zakiyi mana" yace yana ta daukarsu tana kaucewa har ya sami wanda duka su biyun suke dariya.
Zama suka yi cin abincin ya dauki cokali da hannun hagu yana satar kallonta "ni gashi hannun daman yana ciwo, hagun kuma ban wani iya amfani dashi sosai ba"
Sam bata kawo me yake son yi ba tace "daurewa zakayi Yayanmu nasan kana jin yunwa"
Marairaicewa yayi "sosai ma amma kinsan Annabi SAW yayi hani da cin abinci da hannun hagu"
Ajiye cokalin da ta rike tayi ta dago