Showing 3001 words to 6000 words out of 37326 words
Chapter 2 - WACECE ITA COMPLETE HAUSA NOVELS BY Hauwa M Jabo.txt
sati uku da magana matar tazo ta
tafi da ippatu birni ta mata dinki kala biyu Dan
kar taje Gidan daga shigarta a koresu , aka hada
da yan kayan sallarta. Ippatu tayi kukan rabuwa
da qauyensu Dan batason zuwa aikin da
za'akaita sun rabu da dijee da rukayya sunata
kuka sai birni......
WACE CE ITA..?? 8
Na Hauwa M. Jabo
*******************
Bayan sun isa birni matar da nikaina Jabo
bansan sunantaba takaita gidanta, tasa tayi
wanka ta saka kayan da ta dinka mata, suka
kwashi hanya takaita gidan da zatayi aiki, ippatu
tunda ta shigo birnin sokoto take qauyanci ganin
sabuwar duniya ya hanata kula da fadan da
matar take mata bare ta mata rashin kunya,
data shigo gidan Alhaji Habib nan kallo ya koma
sama, gidane da idan na tsaya muku bayaninsa
zan bata lokacine, duk unguwar ba gidan da
yakaishi girma, ga lambu a gidan shuke shuke
manyan itatuwa swimming pool ne, gurin ijiye
motoci ga abubuwa nan kala kala, ataqaice dai
Gidan dai ya hadu, ippatu tana shiga palon
santsin tayis ya kwasheta ta xube qasa tiiiiim..!!
Wata Yar budurwa da matar gidan suka saka
dariya, taji haushin dariyar da aka mata ta daure
fuska abinta, badan yau tazoba da sai ta tsula
musu rashin mutunci su har sun isa su mata
dariya.!!?
Matar data kawota ta riqa hannunta suka
qarasa palon suka zauna, sanyin ac tuni ya fara
shigarta ta fara rawar dari sai qarar haqoranta
kikeji kakaf. kakaf, alhaji yace a kashe ac din
baquwarsu tanajin sanyi.! haba Abba wallahi
zafi akeyifa wani Dan saurayi ya fada yana
yatsina fuska alamar zafi! Alhajin dakanshi
yatashi ya kashe ac ya dawo ya xauna. Wacce
ta kawoni ta fara musu bayanina kamar yanda
goggo ta mata bayani, taji qaryarda goggo ta
zuba tayi yawa ta kasa haquri Dan ita ba'aqarya
gabanta, tayi charb ta chabke ta fara zuba,
goggo ba itace mahaifiyataba mahaifiyata sun
rabu da mahaifina tun ina qarama mahaifina ya
rasu shekara kusan biyu da suka wuce kum.....
Keeee, keep quiet mana ya fada yana mata
kallon wulaqanci, chikin tsawa ya fadi maganar
ta gane keep quiet dan lokacinda tana boko
kamin a korota Malaminsu yana yawan fadar
haka idan ana surutu kuma daya fada sai kowa
yayi shiru, shima malaminsu da qarfi yake fada
kamar yanda wannan ya fada, ta dallamai
harara hadi da yimai kallon banxa ta zubar.
Kaiiiii abba u see? Kaga yanda take kallona
kuwa,?
Farhaan yakamata ka riqa haquri mana, da
zuwan baquwa zaka tsaneta haka, kada ka
manta da ita zaka zauna.. farhaan ya juyar da
kai gefe gaskiya dady bana tunanin xan iya
zama da wannan, kalletafa!! wata kyakyawar
dattijuwa ta kalleshi wallahi kayi kadan wannan
itace ta qarshe ba chanji. Duk maganar. da
suke da englsh suke yinta, Ya bata fuska ya
tashi yabar musu guri yar qanwarshima ta bi
bayanshi suna gunagunai da turanci,
Matar data kawoni ta basu haquri tace kuma
kada in qara magana, ganin maganata kamar
itace ta haifarda rigima sai nayi shiru bawai dan
raina yasoba, taci gaba da musu bayani inajin
tana qarya amma ba halin magana......
Mujeee zuwa muji yanda iffat za'azauna a gidan
aiki, da wannan hali nata......M jabo
.......
[4:00PM, 4/27/2015] .: WAYE ITA..?? 9
Na Hauwa M. Jabo
Wacce ta kawoni Ta qare bayananta na qarya
dana gaskiya da goggo ta kitsa mata....
Kyakyawar matar tace Allah ya bamu ikon riqeta
yar marainiya da ita, dama yaron mune muka
nemowa mai aiki, duk wacce aka kawo sai su
sami sabani dashi kusan mai aiki 13 ana
kawowa suna samun sabani, shine yanxu yace
asamo mai qaramar yarinya tunda aikin nashi
bashida yawa yace bayason Yar cikin qari sabida
sauran daga qazamai sai barayi sai yan iska sai
marasa kunya da sauransu, shi kuma baya iya
zama dasu amma wannan yarinyar ni tamini
sosai, ammafa sai ta zama mai haquri Dan
farhaan akwai fadin rai da fushin bala'e sai kina
haquri kinji yan mata? Ta amsa da to kamar da
gaske, ya sunanki da sauri nace ippatu. Matar ta
maimaita iffaah suna mai dadi! Sai naji tafi kowa
iya sunana yanda ta fada ta wani juya baki,
"kunsan bahaushe baya banbanta "P""F" duk
daya yake kiransu" Maman farhan ta mini nasiha
ta kira yarta farahnax amma shiru bataxob,
dakanta tace muje in nuna mini dakinki da zaki
zauna, tashin hankali koni Jabo dakin ya burgeni
bare wata yar qauye irin iffaaah...
An gaya mata aikin da zatanayi, zata gyaramai
dakinsa tattara mai kaya takai ma mai wanki ya
wanke, ta wanke bayi, ita zata riqa tashinsa da
safe yaje skull. Hummm iffaat kam sarkin bacci
wa zata iya tayarwa daga bacci, Naji matar
gidan ta burgeni cox batada gyama kuma ba
wulaqanci haka mai gidan amma su hatsabiban
yayan yan wulaqanci ne tasan ma korarta zaiyi
Dan bazai iya zama da itaba.
********
Kwanan hajiya Fati hudu da iffaaat anyi sa'a ba
wanda ya tsokaneta bare ta rama, yau zasu bar
naija su koma UK da yarsu farahnax, akabar
farhan da iffaaat a gidan. Da gani jininsu ko
kadan bai haduba amma ba yanda ya iya
mamarshi harda rantsuwa akan cewa bazai
chanza taba, dole yayi haquri koda na shekara
dayane, ya fahimchi yarinyar batada kunya dole
ya saitata.!!
Bayan tafiyar su hajiya ya dawo daga rakiyansu
da yayi a airport ya shigo gidan,
Keeee come here, taxo gabanshi tamai qiqam
kamar ice ta tsaya, Oyaaaa get seat tazauna
bawai ta gane mi ya fada bane kawai a
makarantar boko kamin a korota taji maliminsu
na cewa seat down ta gane cewa acikin biyun
daya na nufin zamame tunda yana fada kowa
yake xaunawa, haka yana cewa come here sai
taga anje gun malami. sai itama tayi hakan,
akayi Sa'a ta gane farhaan ya dauka tanajin
English ganin ya mata Dan biyu ta gane sai ya
fara bayani Hausa da turanci saida yayi yayi
yace have u get me.? Yaga ko motsi batayiba,
ya qara tambaya shiru kakeji yagane aikin banxa
yayi, keee ya daka mata tsawa. Kina jina?? eh
inaji. to mi nace?? Ta harareshi mi kace kuwa?
Duk maganar da nayi bakiji abinda naceba. Ta
tabe baki ai ban dauka dani kakeba to da uban
wa nake, zanci ubanki fa.! ta miqe zunbur ta
nunashi da yatsa kada ka qara zagar min baba
sabida ya rasu idan ka qara zagin babana zan
rama masa kaji na fada maka. Ta murguda baki
ta maka mai harara... Farhaan kam gaskiya
tamai yawa ya tsaya yana kallon baqauya tazo
tanamai rashin kunya har gida wai kuma Yar
aikinsa, anya kuwa tasan WACE CE ITA anan
gidan? ba shakka batasan WACE CE ITA ba nine
xan Sanar da ita WACE CE ITA a gidannan, baice
mata komaiba yaci gaba da kallonsa....
[4:00PM, 4/27/2015] .: WAYE ITA..?? 10
Na Hauwa M. Jabo.
Ta kalleshi in tafi?? Yayi banza da ita, ta qara
tambayar sa yayi mata banxa, ta kama hanya
zata tafi ya daka mata tsawa, ki dawo ki tsaya
nan, taja ta tsaya kusan 30mnt tana tsaye, ta
gaji zata zauna ya hanata Idan kika zauna sai
na kakkaryaki, tayi tsaki, ta kauda kai, ya qare
abinda yakeyi ina miki magana zakice baki dauka
dake nakeba ko?? To waye a dakin da zanyi
magana dashi? Ta kalleshi a wulaqance da chan
dakake maganar dawa kakeyi?? sau nawa ina
ganinka kana daura hannu a kunne kanata
magana ko kuma kayi yare kana dariya, wani
lokaci ai wata waya kake sakawa a kunnenka
kayita magana kai kadai duk da uban wa kake
magana?
Kaga yanzuma na dauka da ubanda kake
magana farko dashi kakeyi yanxu .
Zunbur ya miqe yayi niyyar mammaketa sai ya
tuna da abinda ummanshi ta fada mai "ban
amince ka daki yar mutaneba marainiyace duk
abin da ta maka kamin waya zan mata magana"
sai ya koma ya zauna ya dun qule hannu itako
tana tsaye ta riqe kunkuminta kamar mai jiran
danbe, ya kalleta wata mummuna qazama da
ita, ya rasa abinda zai fada mata ta gane WACE
CE ITA. ya harareta yaja dogon tsaki, to ki
zauna, ta zauna ya maimata bayanin da ya mata
da dazu, shima dai iskancine yazai ijiye baqauya
kamar wannan yana mata English to amma ai da
yayi na farko ta gane, ya akayi ta gane? Koma
yane ya rage nata..
Yace Inada abokai mata da maxa, kuma ko
wanne yana zuwa nan gidan suna kwana wasu
suna wata daya wasu suna sati biyu idan sunzo
suma duk abinda kike min suma zaki musu
hadda girki idan suna buqata zaki musu. Ni ban
iya girkibafa Malam.! Gidanku basu koya miki
girkiba ? Eh basu koyamin ba, ta fada cike da
tsiwa,sai yayi banxa da ita ya fahimci yarinta na
damunta amma zai gyarata a hankali, ya nuna
mata WACE CE ITA a gidannan, OK ya rage naki,
haka zaki girka musu in sun buqata, tayi banza
dashi Dan tunda take bata taba yiwa goggo
girkiba cox batama zauna gidaba bare tasan
yanda ake girka abinci. Ko girkin murhu bata
iyaba bare na gas, ya qara jaddada mata abinda
umma tace bata ba fita waje, ba wasa da masu
gadi, ba ruwanta da kowa aikinta kawai. za'ayi
shegiya kuwa.!
Yaqare fada mata abinda zai fada mata ta tashi
ta shige dakinta.
Tunda tazo gidan a Leda take kashi sai ta saka
bola idan yayi yawa ta fitar dashi sabida duk
dube dubenta bataga masai a gidan ba, shi yasa
dakinta yake wari Dan bata damu da gyara
komaiba, gurinda kawai akace ta gyara dakin
farhaan take gyarawa....
[4:00PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 11
Na Hauwa M. Jabo
********
Ranar farko da farhaan yayi baqo wani abokinsa
da sukayi karatu a UK. Tare sunyi missing din
juna, farhaan yanata addu'a kada wannan
kucakar ta fito ta kwafsa mishi Dan ya lura
kanta rawa yakeyi ba kadanba, suna tsaka da
gaisawa sai gata ta fito. Kamar an korota daga
daki, Ku tashi zan goge nan gurin! Ta fada ba
tareda ta kallesuba, Tafara share palon, meene
kebakiga inada baqo bane,? maza ki bacemin da
gani har ta fara shara tajiyo tsawan da ya daka
mata ta miqe tsaye, tana yatsina fuska kai
bakasan lokacin aiki na bane da zaka kwaso
tarkacen abokanka kazo dasu Ku hanani aiki..!
Habawa Ya wanke ta da mari tashin hankali..!
ta dauki bokitinta na ruwan dattin data goge
sauran guraren dasu, ta watsawa abokinsaA
fuska, tunda shine silar adaketa, ta matsa daga
nesa tana jiran hukuncin da za'amata da Wanda
itama zatayi Dan bata yafiya, dukansu sun rasa
abinyi abokinsa ya fara bala'e ya zaka zauna da
mahaukaciya farhaaah, bakasan hadarin
hakabane? Wannan wata rana zata iya kasheka
wallahi, tana shigowa palon nagane batada
hankali, Kaine Mara hankali baniba tana zazzare
ido kamar lecturer ya titsiye jabo a clss bata iya
karatuba, farhaan zaije gunta abokinsa yariqe
hannunsa, cool down my man. Akwai banbanci
tsakanin mai hankali da mahaukaci nasan da
tanada hankali bazata taba yimin hakaba, muje
daga ciki inyi wanka in chanja kaya kawai.
Baqin ciki ya hana farhaan magana ya rasa
yanda zaiyi, Dole ya nuna mata WACE CE ITA a
gidannan. Abokinsa yaja hannunsa suka wuce
daki ita kuwa hajiyar tachi gaba da aikinta.
((Allah ya tsaremu da aikin jahili da baqauye.))
ta gyara gunda ta jiqe da ruwa kamar bata
zubarba, aikin ma fa yinsa kawai takeyi amma
ba abinda ta iya bayi ruwa kawai take sakawa
ta dauraye duk da cewa umma ta nuna mata
wasu abunuwan, gadonsa kuwa sai Wanda ya
gani da yake shima gwanine gun shiririta haka
yake kwanciya akan gadonsa shi warine kawai
bayaso.
Bayan abokinsa ya tafi ya kwala mata kira ta
fito ya nunata da yatsa wallahi yau sai kin bar
gidannan Dan ba gidan ubanki bane, ko in
hallakaki matsayaciya kawai, tofaaa ran ta ya
baci ta tsani a zagi babanta ta kebe baki, ai bani
nakawo kaina gidan na ubankaba, ubanka ya
kawoni sai ka bari idan ubanka ya dawo sai ya
maidani gidan ubana kamar yanda ya daukoni,
ta fada cike da gadara da rashin tsoro. Sai ya
saki baki yana kallonta ta juya ta koma dakinta
ya bita da kallo,
Ita kanta tasan zata iya gayawa farhaaah ko
wace irin magana amma bata taba kawo ta kulla
masa sharri ko daya a zuciyantaba, haka kawai
yake bata tausayi kajifa..
Maamanshi ya kira, umma wallahi yau sai na
babbala wannan qazamar yarinyar batada
amfanin komai, umma dai nata bashi haquri dan
tasan zai rina, nan ya kwashe duk abinda ya
faru ya gayawa umma ita kanta umma ta jinjina
wa wannan yarinyar da Karen aikinta. amma
bata nunawa dantaba ta bashi haquri da kuma
yimai kashedin ya fita hanyarta Kuma kada ya
qara sa mata hannu, tace yakaiwa iffaaat waya,
waye iffaaat umma?? Itayarinyar mana,
baimasan sunantaba sai yau, kullum da yake
kullum da keee yake kiranta ya kwala mata kira
ta fito ya bata waya yaga dai batasan wayaba
bata Masan yanda ake amfani da wayarba sai
kawai ya sa speaker, taji ana kiran sunanta a
ciki, farko ta dauka radio ne yake magana sai
taji ana kiran sunanta habawa.... Ta wugar da
wayar Da gudu ta koma daki jikinta na rawa abin
ya bashi dariya sosai, sai ya bita dakin yana
shiga wani qarni da wari ya tarbeshi ya kasa
numfashi ya dawo Palo ya qara kiranta dagyar
tafito, ni kaina Jabo abin ya bani mamaki Dan
kuwa iffaaat ko lokacinda aka kaisu police
station bataji tsoronda taji yanxuba Ashe Akwai
abinda take tsoro.......
Mujeee zuwa muji ta'addancin da zatamai kamin
tafara..
[4:52PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 12
Na Hauwa M. Jabo
Ta samu guri ta rakube nesa dashi, ya daure
fuska ki karba umma zatayi magana dake, ina
ummar? Magana take kuka kuka Ya zanyi
magana da ita? Ki karba nace jiki na rawa duk
ta rude ta karbi waya, ki daura a kunne takuwa
danna waya a kunne,tayi mutuwar tsaye, Tana
tsoron kar ta jata, wayar ma a juye ta daurata
sai ya shareta, to kiyi magana, kamin tayi
magana sai taji an sake kiran sunanta har zata
wurgar da wayar sai kawai ta daure ta amsa, jiki
na rawa, sundan gaisa, nan dai umma ta mata
magana akan ta daina yiwa yayanta rashin
kunya duk abinda yakeso ta mishi, ta amsa da
to zata daina, amma hajiya kice ya daina
dukana,!! gaban abokansa yake dukana kamar
jakar gidansu, duka.!? Eh, kuma kullum saiya
zagi margayi babana bayan na fada mishi
babana ya rasu yadaina, amma kullum saiya
zageni, kwallata ta cika mata ido batason a zagi
babant ko kadan. umma taji haushi sosai ta bata
haquri tace zatamai magana,daganan tadan
bata labari har tana dariya, tama manta da
tsoronda takeji,, haushi ya kama farhaan ya kira
amata fada, ta bige dakai qaranshi, har tanata
dariya, tana dariya shiko ya qura mata I do yana
kallon haqoranta da sukayi wani tsatsa, ta qare
ta kawo mai tana dariya ya kalleta ke wai laka
kikeci hala,kinga yanda haqoranki sukayi tsatsa
kuwa? Ta harareshi, ba laka naciba kashi
nakecii, tayi tsaki ta wuce dakinta, ya bita da ido
cike da takaicinta to waima miye amfanin kiran
umma da nayi? Gashi ba abinda ya chanza! Kalli
ko second goma ba'ayiba ta qara yimin rashin
kunya, shima yayi tsaki lallai an hadashi da
qaddara kuma umma tace sai ta dawo
za'achanzamai ita, nanda shekara daya kenan
lallai zaici uban yarinyar nan kuwa, dole ya nuna
mata WACE CE ITA, a duniya ya rasa horon da
zaimata taji haushi ko zata Dan natsu, ya kira
kukunsu yace daga yau kada ya qara yin girki da
ita, okay sir,
******
Da yamma mutuniyar taku ta tashi daga bacci
ta nufi kitchen taga wayam ba abinci da Rana
ma batachi komaiba yanxuma bataci komaiba,
tana tsaye saiga farhaan ya shigo, abincin sa a
shirye kamar yanda aka saba hadamai amma ba
nata ta kalleshi fuska a yatsine, Ina abincina?
Nine mai miki girki? Ko ni nasaba girka miki?
Karki manta kema yar aikinace so ki kula kisan
abinda kikeyi a gidannan ya bone. Ta kalleshi
rai a bace to dan ina Yar aikinka sai akayi mine?
Sai kada in nemi abincinda zanci? Ta kalleshi Ni
yanxu mixanchi ? Yana kai spoon a baki ya
tauna ba tare daya kalletaba Kici halinki ko ki
girka da kanki idan kin matsu,.! Tofa yau
za'aqure iffaaat yan mata......
[5:00PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 13
Na Hauwa M. Jabo
Ta kalli kitchen din ko za'akasheta ba abinda
zata iyayi a bayan buda fridge ba abinda ta iya,
kuma ga wasu abubuwa kamar fridge akai taga
ana girki. Za'ayi shegiya kuwa.ta kalleshi taga
yana kai loma hankalinsa kwance., tayi tunanin
ko ta barar mai da abincin da yake ci a jikinsa
sai kuma ya bata tausayi, kawai saita rakube
saida ya kammala Wanda ya rage shi tacinye....
****
Tafiya ta kama farhaan zuwa Lagos, ya tafi
satinsa daya baidawoba. tun ranar da ya tafi
batachin abinci saidai tabuda fridge duk abinda
taga nacine ta dauko ta chinye, cikenta ya
lallace kullum tana hanyar bayi, to anachin
abinda ba'asaba Chiba wasu kuma ba bisa
Qa'ida ake cinsuba duk wani abu da tagani mai
Dan gishiri gishiri da zaqi zaqi ta gama dashi.
Kaihar saida ta qare chiye chiyen takai batada
abincin da zatachi yau.
kwananta biyu bataci komaiba yunwa na
Neman ta hallakata.. tunda tazo gidan bata
taba koda fita wajen Palonba daga daki sai Palo
sai kitchen, batamasan qofar da ake fitaba...
Aranta taji ta fita haka ta biyo hanya tabi nan ta
leqa chan har tayi karo da qofar fita, ta baya ta
fita, Habawa, tayi murmushi taga S pool aranta
tace wato gidan nan hadda qaramin kogi sukeda,
ta waiga ta hango lanbu komai yaji fruit duk sun
nuna wasu sun fado a qasa Habawa tayi ciki da
sauri taci ayaba son ranta saida ta qoshi,
sannan ta kwance Dan kwalinta tayo guxuri ta
fito har zata wuce taga yanda ruwan nan sukayi
sky colour sai suka bata sha'a ta tu6e ta fada
tayi wanka sosai gata gwanar iya ruwa, gashi,an
Dade ba'ahaduba ta Dade a ruwan sannan ta
fito, dama tunda umman su farhaan ta tafi
batayi wankaba kwana goma kenan, ta fito cike
da nishadi an samu banxa, dagyar ta gane
hangar komawa daki taje ta chanxa tufafi tunda
wayannan sun jiqe, tana zaune Palo a qasa ta
miqe qafafu ta saka fruits dinta tsakiyar qafafu,
tanashan mangoro abin sai Wanda ya gani,taji
qamshin turare hadi da dariya koda ta duba
farhaan da wata mata yar gayu da qananan jaya
a jikinta tasha attach fuskannan tasha fenti
bakinnan yaji janbaki, ta rurungumo farhaan,
tana mai shagwaba suna ta dariya, sun bata
haushi haka kawai, ta miqe da dariyanta
tagaishesu a tunaninta matarsace, matar ta
mata kallon tsana da gyama ta kalleta a
wulaqance ta zubar, hooney miya kawo almajirai
a gidannan bayan kace min ba kowa dagakai sai
masu aiki biyu. Wai itama mai aikinace, .matar
ta wani jaa da baya honey wannan din?? Aiko
hanyar databi bana son nabi tana magana
ayangace tana wani rungumoshi, ran iffaaat ya
bace tuni tasha magani aranta tace Dan an
samu an gaishesu suke yiwa mutane wulaqanci
ba matar shi bace ko uwarshice tamin iskanci
zanci zan rama, taja wani dogon tsaki,ta
murguda baki ta wucesu, hooney kana kallo mai
aikin gidanku abinda ta mini...??
[2:48PM, 4/28/2015] .: WACE CEE ITA..?? 14
Na Hauwa M.Jabo
Kiyi haquri tanada matsalar gwagwalwane, ta
wani zare ido kana nufin mahaukaciya kake
rayuwa,?? Haba Hoooney wannan ai gangancine
ta fada da qarfi, har saida iffat tajiyota, ta waigo
ta zare ido gasu masha Allah idonta, ido cikin
ido tace; waye mahaukaciya?? Rufee ta rungume
farhaan da qarfi kiyi haquri badake nakeba, rufee
dai taji tsoro, hankalinta ya tashi qarshe taqi
zama gidan tace sai dai ya kaita hotel Dan
bazata zauna da mahaukaciyaba ta hallakata.!
Haka dai rufee ta hana farhaan zama gida duk
gajiyar daya kwaso saida yakaita hotol, kuma ta
hanashi dawowa kar mahaukaciya tamai illa sai
gobe da dare ya lallabata ya dawo gida, iffaaat
dai fruits dinta takeci dare da rana amma taji jiki
ba kadan ba har ta chanxa kala, kullum tana
hanyar bayi tana gudawa.
Dan ma Allah yasa ba irin zainb khalifa bace mai
shegen ci da ba haka ba..
********
Yana isowa ta fashe mai da kuka wallahi saika
maidani gida!! angayamaka banida gata zata
ijiyeni ba abinci wallahi saika maidani gidanmu
ta riqe mai gefen riga tana kuka, anyi arziki
bataci kwalarshibama. sai yanxu ya kula da ta
Dan chanza kamar ta tame ta qara duhu ya tuna
da cewa ya hana abata abinci.! Girjinsane ya
buga to me takeci tsawon kwana 9?? Ya kalleta
sai kuka take sai ta