Showing 21001 words to 24000 words out of 25431 words
Chapter 8 - Mahaukaci ko boyayyen masoyi complete by Maryam Yarmawa .txt
itama Aziza kuka tasaki tana"yar uwa Ashe zamu sake haduwa a rayuwa"kuka suka kara fashewa dashi... Momyn annur ne tashigo tana"haba daughters ya isa kar kanku yayi ciwo, sakin Aziza minal tayi ta nufi wajen momyn annur ta rungumeta tana gaisheta... Aziza dake rike da baby malika ta hangout safwan yana tsaye sai murmushi yake nan ta shaidashi tace"kamar safwan nake bani".... Cikin Myrna safwan yace bakiyi karyaba nine safwan dai na minal, Dariya tayi tace "kaikam akwai zolaya"...
Nan aka bude sabon shafin hirar rayuwa, sai raha ake cike da annashuwa yau Gidan marayu kowa sai farinciki yake minal sai rarraba ido take ko zataga Annur (Allah sarki minal sarkin hakuri, haka akeso mutum ya kasance a rayuwa, ga yafiya)...
Momyn Annur ce ta shiga lallashin minal da tayi hakuri ta koma dakin Annur... Inda harda su safwan
Kuka minal take tana itafa bazata komaba,Aziza ce tace minal idan har don safwan ne karki damu mun daidaita kanmu... Dukan wasa minal ta kawo mata cikin kunya tace"wallahi kefa yar uwa sai a hankali,bakida dama dama
Dariya da murna kowa yafara, nan dai mony suka roki hajiya Mairo da tabar su sutafi da minal, dakyar hajiya Mairo ta yarda nan... Momyn annur tayiwa su hajiya Mairo da hajiya hanne dumbin Alkhairi da Alkawarin kowani wata zata dinga taimakawa marayu... Kuka kam Yara da manya na Gidan marayu sun sashi minal kuka takeyi saboda tasan zatayi kewarsu... Haka Yaran kowa ya dinga Aunty zanbiki.. Minal sai takara fashewa da kuka tamkar karamin yarinya... Har kasa ta durkusa tana godewa hajiya Mairo da sauran matan Gidan... Nan suka shiga motocin Alfarma sai Gidan annur,tafkeken gate din aka bude musu suka yada zango cikin Gidan.... Annur dake kwance a falo da drip a hannunsa yanajin karar motocin ya fincike drip din ya nufi kofar dazai sadashi da harabar Gidan.. Fitowar sa keda wuya, aka budewa minal mota...santalelen chocolate color kafartane yafara fitowa daga mota... Sannan tafito tafiya take cike da nutsuwa , ta kara kyau,kalar skin dinta chocolate yakara fitowa tayi kyau sosai har wani sheki take... Turus Annur yaja ya tsaya yana kare mata kallo.itama cal ta tsaya azixama da mommy suka tsaya..hawayene yafara shatata a idanuwanshi, blue eyes dinsa yajuye yazama brown... Doso inda minal take yayi, wacce tuni ta hade rai itama zubar da hawaye take... Yana zuwa ya zube agabanta tamkar zaiyi shige kasa cikin muryar kuka yace"minal! Wallahi kunyarki nake, narasa yanda zanyi na Kali idanuwanki ince ki yafemin na rasa da wacce kalma zan baki hakuri... Minal I just know I can't leave without you.. Ruhina, rayuwarta, jinina, dukiyata fansace a gareki, kiyi hakuri ki yafemin ko bazaki komo gareniba pls minal kice kin yafemin"... Yana gama fadin haka ya rushe da kuka maicin rai.... Minal ji tayi an dafota tabaya juyowar da zatayi saudat tagani tana zubar da hawaye cikin muryar kuka tace
"Na dauka dan talaka Ba mutane bane, nadauka mulki da sarauta sune jin dadin rayuwa, Amma sai na lura bisa tunani na Duk shirmene, komai na duniya banzane, Duk abinda yafaru tsakanunku da Annur nice sanadi, ni nayi kulla-kulla... Da ace mata da Dama zasu zama kamarki da sun morewa rayuwa.. Minal kiyi hakuri ki koma dakin mijinki,na gayawa annur Duk irin abubuwan Dana mulla miki, ki koma ki zauna ke kedai badanmu ba ko dan yarinyarki.. Ki yafemin domin duniya ta koyamin darasi yanzu narasa mahaifana kuma narasa annur har abada "....
Cikin kidima minal ta Kali saudat... Sannan ta fashe da kuka tace"wallahi Aunty bakiyimin komai ba, kuma na yafemiki idan harma kinyimin... Rungumeta saudat tayi tana godiya sannan tace'"ni nabawa su Momy da Aziza address din inda kike, Tunda sun samoki Alhamdilillh, zan iya yafiya yanzu Tunda kun yafemin... Nan daisukayi bankwana inda Saudat tahau motarta aka bude mata gate tafice daga Gidan....
Aziza ce takaraso wajen tace Haba ya Annur dan Allah katashi ba girmanka bane kana rokar wannan kwailar...
Minal ce ta kalleta tayi wani dakuwa t share hawayenta... Da hannunta masu taushi ta durkusa ta tallafo annur ta rungumeshi tana "sugar kaima bakayimin komaiba ka yafemin..Allah ma Muna masa laifi yana yafe mana balle mu, na yafe maka"... Farinciki ne yarufe annur yakara rungumeta cikin muryar dady yace"omg dagaske kike matar mahaukacin masoyi, nagode Allah ya biyaki da Aljanna"... (Summa manta da awaje suke)....dasuka Ankara nan kunya ya kamasu annur ya waske ya saki minal sannan ya karbi babynshi a hannun momy... Yarinya tazo hannun ubanta sai Dariya take... Nan annur ya ga Kama tayi dashi sak har fatarshi... Nan yafara kissing dinta sannan yayi mata adu'oi a kunnenta... Ya rungumeta suka shiga ciki....
*KANO CITY*
jikin Abba yakara Zafi ya rikice, hasiya da luba sai kuka suke rizga yayinda mama saicin tuwonta take tana"yo to ai kudena wahalar da kanku kuna zubar da hawayenku a banza ai mahaifinku abinda ya shuka shi yake girba.. Ke kuma luba saboda Allah da annabi duk mazajen da kuka aura Duk tsinannu ne, kinje kin auri dan dambe, gsshi ya ragargaza miki fuskarki kin dawo harda saki uku kema, yanzu gashi kin dawo gida, to wallahi kowacce takama sana'a bazan iya ciyar daku ba... Cikin kuka haseeya tace"mama yanzu da tsohon cikin zankama sana'a"
Cikin fada mama tace yo Dama dan ubanki haka zan zauna dake ina ciyar daku da cikin dan danfarar nan.. Ai duk ke kika jawo mana wahalar nan.. Gashi yanzu gidansu minal mike ciki, Gidan Dama yafara rushewa, yanzu idan sun dawo wayasan inda zamu dosa? Aiko cikin gobe zaki haihu ne wallahi sai kin Kama sana'a.. Matar madamfari kawai haihuwarku wallahi batayin ranaba..... Bata gama rufe bakinta ba taji sallamar..mai sallamar ce tashigo
Kara mama tasaki tana"umman Aziza"
💥MAHAUKACI KO BOYAYYEN MASOYI💥
85
By maryam yarmama
*masoya daga Cameron, niger, chad da sauran garuruwa, ina mika sakon godiya musu kaunar dakuke nunamin, nagode Allah yabar zumunci*
*SHAFIN KARSHE*
*ABUJA CITY*
Nan aka kara maida auren minal da annur, zokaga irin farincikin da suka shiga...bikin gargajiya akayi inda su minal da annur suka zaka kayan sarauta.. Minal taga gaga wajen dangin annur dayake da daya tilo, kuma ga dangi masu tarin tawa... Ana gama da kwana daya aka daura auren safwan da aziza... Bawani buduri akayiba saboda safwan yace shi bayason ayi wani buduri, Aziza kam taci burin akwana bakwai ana budurin bikin amma sagwan yaki haka ta hakura, su Aziza anshiga sawun manya, sunsha kuka suda minal lokacin da akazo daukar aziza domin akaita gidanta
"Cikin shekshekar kuka minal tace"Allah sarki umma, inama kinanan, kizo kiga yanda yaranki suka zama, rushewa tayi da wani irin kuka maicin rai sannan itama aziza tadinga kuka, su hajiya mairo ne da momyna annur sukata basu baki, dayake agidan su annur akayi taron biki.... Dakyar aka banbare aziza daga jikin minal inda aka kaita gidanta dake abuja crown exculisive gida tamkar Aljannar duniya.. Aziza ta tsorata da ganin wannan gidan...(dama gata da uwar buri aranta)...... Nandai amarai suka tashan amarcinsu... Inda annur da minal suka kara kyau da gogewa, annur baya zuwa ko'ina, kitchen tare suke shiga, komai tare sukeyi sun zamto abin sha'awa ga kowa.... Annur kam yazama tamkar cingum yace bayason borori a gidansa
Kwance minal take akujerar falonta tayi matashi da cinyar annur, shafa kanta annur yake cikin so da kauna yana kallon kyakyawar brown din fuskarta yace "babyn yakamata ace munje kano, mun binciko gidanku sannan mufara binciken inda zamuga umma".... Nan idon minal yakawo ruwa tace" heartbeat wallahi ba irin binciken da bamuyi ba, kaga umma har yanzu, amma ni a raina kullum inaji zamu sake haduwa da umma, sannan ko badon umma ba inason inje kano in nemi numbansu ummi kawata, domin mu dinga sada zumunci,.... Kuka ta fashe dashi yayinda annur yafara lallashinta cikin salon riritawa ya mantar da ita duk wani kunci da take ciki........ Annur da minal kenan... Mahaukaci da mahaukaciyar masoya.... Nan dai suka yanke zasu rankaya kano gobe, harda Aziza da safwan........
KANO CITY
Cikin hawaye umma tace"ladi nice ba wata ba, yanaga kun dawo nan, meyasu Abbansu haseeya, ina kuma yarana innalillahir wa"inna ilaihir raji"un,... Ina kuka kaimun yayana? Badai kun koresu a gidan daya rage shine gatanmu ba...
Cikin kuka mama ta kalli umma tace" umman minal kiyi hakuri, ki yafe mana, muma bamusan inda sukeba, tun lokacin da Abba ya daurawa minal aure da wani mahaukaci, sannan ya kori aziza daga gidan bankara jin labarinsu ba... Kiyi hakuri.... Kara umma tasa ta sunkuya a wajen tana"Abba ka cuceni! Me mukayi maka a rayuwa da zaka saka mana da irin wannan abin, dan uwanka imran mijina ya kaunace ka da zuciya daya, ya jawoka jikinshi, amma ka kasa rike mishi yaya"nashiga uku nawa yakare, nikam bazan iya rayuwa ba yarana ba.... Zaman dirshin tayi... Yayin abba dake kwance yake kallonta yana matse hawaye ga cikinshi sai kara kumburi yake"...... Dakyar ya iya cewa... "Dan Allah kiyi hakuri, nima nemansu nake in nemi yafiyarsu, kiyi hakuri ni nayi miki kurciya kika fita hayyacinki, ki kabar gida da yaranyi... Mijinki ma ni na kasheshi don in mallake dukiyarshi.....na zalunceku, nasan Allah bazai taba yafemin ba.
Salati umma tasa yayinda inna ladi ta fashe da kuka... Kowa kuka, lubaba dake tsaye itama tayar da butar hannunta tafashe da kuka tana"Abba baka cancanci zama mahaifinaba, nayi nadamar saninka a rayuwa kanayin komai cikin son zuciyarka, to yanzu ai kaga karshenka
Dakyar umma ta tashi da niyyar fita daga gidan,inda ta yanke shawarar gwanda tashiga gari ta nemo inda yaranta suke... Nan taji duniyarma yana juyi da ita, zubewa tayi a wajen sumammiya...
Annur da minal rike suke da hannun juna, inda malika tana hannun yar aikin maisuna hajara, tafiya suke acikin airport ga bodyguard da dogarai suna take musu baya.. Annur sanye yake da blue din suit wanda ya amshi farin fatarsa, itama kuma minal sanye take da dogan rigar abaya dark blue, sannan tayi rolling, sunyi masifar kyau duk inda suka wuce sai an gaishesu domin prince annur sananne ne, Gashi kuma dan wasan kallon kafan da akeji dashi ne.... Nandai suka wuce inda passenger suke zama kafin jirginsu ya tashi.... Basu dade da zamaba Aziza da safwan suka tawo suna rike da hannun juna... Su Aziza anzama manyan mata sai takun kasaita ake, ita sanye take dadogan riga amma nata red ne, shikuma safwan sanye yake da shadda shampo, sunyi kyau sun kara gogewa... Suna zuwa aziza ta rungume minal cikin farincikin sannan ta karbi malika a hannun hajara tana"thats my baby".... Sannan ta kalli minal tace"matar mahaukacn masoyi yayane".... Dariya duka suka fara yayinda annur ya kalli aziza yace"yayarmu ai wannan tsohon labari ne"gaskiya kina kwafsa mana
Azixa tace"ai nikam bazan mantaba yanda nasha bulala, a hannunka, inw zan manta, wai bakaji kunyar zamanka acikin dattiba"
Sosa kai annur yayi yace"ai sone ya kawo haka, kuma nason yanzu duk duniya bawata mace da zata soni kamar my heart minal, shiya duk wani dukiyata, rayuwata komaina na mallaka mata and yau shine ranar dazan gaya muku nine boyayyen masoyin da kuke nema.... Mamaki yacika minal,, kafin suyi magana amfara kiran passenger... Nan suka shige cikin jirgin sai kano, ba wanda yasamu damar yiwa kowa magana har suka sauka a Aminu kano Airport
KANO CITY
Haseeya da tsohon ciki tana suyar awara a kofar gidan yayinda lubaba ke siyar da kunnun tsamiya... Mama ce ta leko tana musu masifar kar wacce ta karo aiko abata ruwa acikin gida, su siya da kudinsu.. Jiniyar dankara-dankaran motoci sukaji... Nanda motoci kusan guda goma suka faka a layin... Nancikin mama ya duri ruwa tana fadin"munshiga uku, kardai gwamnati ne tazo ta fitar damu daga gidan...duk da unguwarsu minal dan babban layine haka bai hana makota fitowa su ganewa idonsu meke faruwa.... Lubaba da hayakin iccen murhun ya balbalesu, tashi sukayi tsaye suna karewa motocin kallo,kowa da abinda yake aiyanawa a ranshi, cikin sauri bodyguard suka fito suka fara bude motocin tsakiya... Dogarai ne suka fito suna "takawarku lafiya, jinin sarauta, takawarka lafiya dan sarki, magajin sarki.... Bude wata hadaddiyar mota ash colour sukayi... Annur ne yafito hannunsa dauke da malika yana, kissing din goshinta"nan akafara binsa da kallo yayinda dogarai suka bude dayan part din suna wa minal kirari"takawarki lafiya, matar yarima kuma surkar sarki, Allah yaga bayan makiyanki, Allah yaja kwana hajiya minal".... Dabadan ance minal bace to tabbas da lubaba da haseeya sun karyata.... Mama ce tasaki baki tana goge idonta wai shin gaskene ko ba gaske bane"wannan kamar minal, Amma kuma ai taji ance matar sarki kodai batan kai akayi"..mama sai kara raba ido take .. Aziza da safwan aka budewa mota suma suka fito.... Nan minal ta sanya fara'a a fuskata tana kallon kaskon awaran suyarsu minal tace "Ahaba wa nake gani kamar su lubabatu da haseeya "ai sunajin ta ambaci sunansu suka karaso suka rungumeta suna fadin "minal kece".fashewa sukayi da kuka mai tsuma zuciya... .... Cikin mamana ne yabada wani sauti"kurrrrrr bashiri ta shige gida tadau buta, tashiga bandaki domin tasan wannan bakomai bane fyace gudawa.........
Aziza ce ta karaso wajen tana musu kallon hadarin kaji tace"ai saiku saketa karta shafa muku warin talauci, kunga ai karuwanci yayi rana, tunda gashi munsami maza a bariki.... Maganarce ta doki dodon kunnensu, shiru sukayi duk jikin kowa yayi sanyi.... Lubaba tace "Aziza dan Allah mu yafi juna, Adaina dawo da hannun agogo baya"......
Aziza tayi yar dariya tace"haba matar manya, au kinyi laushi kenan, ina mijin naki yake,ke kuma haseeya ina biloniya din naganki da ciki kina sana'ar awara a waje, anya lubabar dana sani ce kuwa..... Cikin bacin rai lubaba taso kawar da zancen da fadin.... Minal ummanku tana cikifa,... Kukan dadi minal tasa, tayi cikin gidan yayinda kowa ya rufa mata baya...... Abbane kwance a tsakiyar gida akan taburma, rana sai dukansa yake, tundayafara rashin lafiyarnan daga mama har su lubaba wulakantashi suke, ko abinci zasu bashi saiya roka, saukin abinma tunda umma tadawo gidan ita takedan kula dashi, itama tace tanayine don Allah......... Muryar minal da aziza yaji suna kiran umma! Umma ina kike.... Turus sukaja suka tsaya ganin wani tamkar Abba yana kwance, ga ciki ya kumbura suntum......
Ummq ce ta fito daga daki hannunta rike da carbi, kuka tafara... Minal da aziza suma kuka suka fara... Suka nufi wajenta ta rungumesu, sunata kukan farinciki... Safwan yana gefe suda annur suna kallon matayansu yanda suke cike da sha'awar yanda suke kaunar mahaifiyarsu.... Saida su minal da umma sukayi kuka mai isharsu.... Muryar Abba suka tsinkaya yana "waye nakejin muryarsu tamkar su minal
Minal ce ta juyo tana "Abba mune, bakada lafiyane... Cikin dauriyace minal nine kunga yanda Allah yazamar daniko, hakkinku shike dawainiya dani, naci amanar mahaifinku minal dan Allah ku yafemin.... Zama sukayi a taburman da luBaba ta shinfida musu... Abba yakara fadin minal dan Allah ku yafemin"cikin kuka minal tace wallahi ni dama Abba ban rikeka a zuciyaba ni na yafe maka, kullum adu'a nake maka Allah yasa kagane, har yanzu ina kaunarka kuma ina kallonka a matsayin abbana, kuma duk nasan rudin shedane ne yake dawainiya dakai, wallahi na yafe maka, annur dake zaune a gefe da safwan a wani taburmar cikin murmushi ya kalli minal yana godiya a ranshi BISA wannan babbar kyautar ...
Abba Godiya yayi yayinda ya kalli Aziza dake ta faman harararsa tana tsaki kamr ta dokeshi takeji yace"Aziza na cutar da rayuwarku, nasan kona mutu bazan sami rahamar ubangijiba "..cunno baki Aziza tayi tana"yo ai wannan tsakanikane da ubangiji, Amma nikam bazan taba yafewa macuci irinka ba, kuma Allah ya isa bamu yafeba, duk abinda kayimin kabuga kirji kace bazamu cigaba ba, yo yanzu kirjin waye yake ciwo... Gashi kafara gani, kaine ka daurawa minal auren mahaukaci domin mu tozarta, Amma Albishirinka ka tona ramin mugunta ka fada aciki, kullim tunaninka yanda zaka kuntatawa marayun Allah, gsshi yadawo kanka domin mijin minal dan sarkine kuma jinin sarauta, kuma dan wasan kallo na africa ne... Sannan nikuma ina auran shararren doctor wanda ya shahara ciki da wajen kasa, to yanzu daka buga kirji kace saidai mu kare a karuwanci da kaskantarcyar rayuwa, tsakaninmu dakai waye yanzu yake jin jiki... Nikam wallahi ban yafe makaba, kuka aziza ta fashe dashi yayinda ta kalli umma tace"umma kiyi hakuri idan harna bata miki rai, inajin zafi a raina akan abinda mutumin nan yayi mana.....
Jinjina kai umma tayi tana"Aziza nayi tafiya ta kwana daya baci basha, kafafuna sun kunbura, hankalina ya gushe, karshe wasu yar rugane suka tsinceni, sukatayimin magani, harna warke kullum, kuka nake ina kiran sunanku kuda minal, karshe dai dana gama warkewa, nace zan taho kana, dakyar suka barni nataho nakarbi addreshinsu inda suke, zuwana gidan nan shine nagasu abba sukecemin basu san inda kuke ba... Nandai nafadi na suma! Karshe dai na hakura ina adu'ar Allah yadawomin daku duk inda muke, ni kaina na yafewa abba ko bakomai yaci darajar abbanku daya rikeni amana".... Nan kowa yadau kuka, mama tana kuka itama ta dinga rokar gafara
Aziza ce ta juyo ta Kali mama tace"ai mama kece da abin kuka yanzu, kuma duk dan hakkin daka raina shi zai tone maka ido, mamah billionaire nake aure yanda KUKAYi fata ba haka ya kasance ba.....
Su lubaba da haseeyan da kuka dau buri a kansu ina musu fatan Allah ya sakasu a danshinmu... Kasa dakai mama tayi gumi yafasa zubo mata, ba shiri takarajin cikin yabada wani sauti kurrrrrr, nadamar abinda tayi takeyi nan tafashe da kuka ta tashi tadau buta tayi bandaki ta dinga zawo 😂😂shikam safwan tsiwar matarshi Aziza ne yake burgeshi
Nan dai umma takara yiwa Aziza fada domin tasan halinta tun tana yarinya da lafiya nan dai aka yafewa juna... Inda har hira ta barke tsakaninsu, har Abba ya tsomo baki, anata raha...
Su annur ne, suka koma gefe sukayi shawarar fitar da abba waje....