Showing 21001 words to 22238 words out of 22238 words

Chapter 8 - SAUYIN YANAYI Free pages -WPS Office.txt

kashe wannan bakin naki, maima mutane kukan banza?"


Wani irin bak'in ciki ne ya rufe Nanah, data na dama wallahi saita kashe duk wani d'an Ta'adda dake wajan yanzu, to amma bata da damar hakan.


Sakinta yayi yana maido dubansa inda Auta yake.


Ya wani k'ankance ido ya ce "ni wai miye ma anfanin tahowa da wannan yaron?, ai da an rage masa wahalar duniya, an aikasa can kiyama".


Zare ido Nanah tayi tana jin wani sabon tashin hankali na saukar mata.


Tafiya suka farayi suka bar wajan da Nanah take. Suna magana, ganin haka yasa Auta rungume Nanah dake d'aure kamar wata akuya.




Ba abunda y'an Ta'addar suke sai shan tab'a da giya. Ga y'an matan da suka dad'e da satowa suna faman dafa masu abinci, wasu ma sun maida su k'aruwan k'arfi da yaji, sun maida su kamar wasu matansu.


K'iri-k'iri sai kaga k'aton gardi, daya ji sha'awar mace, zai d'auki mace kamar kayan wanki yayi cikin wata rufma da ita, ya biya ma kansa buk'ata, ya kuma tashi ya zuge wandonsa. Yadda suke afka masu kamar wasu dabbobi.


Yadda Nanah ta lura da yawan matan wajan suna sato sune kawai dan su rink'a masu bauta, da biyan buk'atarsu kawai. Hakan yasa Nanah shiga wani sabon tashin hankali marar musaltuwa.


Motsi kad'an tana nanik'e da Auta, wadda ji take kamar ta mayar dashi ciki.


Wata irin yinwa ta fara addabar wa'inda suka sato, ciki harda Auta, ya fara kuka, yana gaya ma Nanah yinwa yake ji. Dan rabonsa da abinci tun jiya cikin dare gashi har gare ya waye rana na neman fad'uwa.


Wasu hawaye ne suka shiga zuboma Nanah na tausayin Auta, ita dan ita zata iya zama a haka, zata iya jurewa na d'an wani lokaci, kai zama ta iya hakura har zuwa wata safiyar. Shifa?, yaro ne.


Gashi anbi an wani d'aure mata hannu, tana son rarrashin Auta, tama rasa wacce kalma zata fara basa hakuri da ita.


Kukan da Auta yake ne ya fara isar y'an Ta'addar. Hakan yasa wadda Nanah bazata tab'a manta sunansa ba, Mai suna Tajo ya nufo inda suke.


Duk duniya idan akwai wadda ta tsana to bazai wace wannan Tajo ba, shine ya rabata da farin cikin rayuwarta, wato Innarta, shine ya ruguza masu rayuwa, shine ya rabasu da jigwan rayuwarsu. Da tana da dama saita kashe Tajo kamar yadda ya kashe Inna.


Da jajayen idonsa yake kallon su Nanah, ganin irin kallon da Nanah ke aika masa dashi, na tsananin tsana da fusata, yasa Tajo shekewa da wata dariya yana nuna Nanah da hannunsa.


Can ya tsagaita dariyar yana kallon Nanah da ba alamar tsoro yanzu a cikin idonta. Ya ce "keee uban mi yaron nan yake so ya ishemu da kuka?".


Shuru tayi bata da niyar magana ga Auta daya k'ara balun d'in kukansa.


Haushi abun ya bama Tajo, hakan yasa ya d'auke Nanah da wani gigitaccan mari. Wadda yasa taga giftawar wasu taurari. Duk da haka taji zafin marin daya kai mata, amma tayi shuru tana kallonsa da jajeyen idonta da suka kad'a sukai jawur.


Ganin fa bazata tanka masa ba, yasa Tajo jawo Auta ya daka masa tsawa yana cewa "kaii kayi ma mutane shuru ko yanzu nasa wuk'a na yanka maka wuya wallahi"


Auta bai daina kuka ba, majina da hawaye duk sun b'ata masa fuska.


Wani dogon tsaki Tajo yaja yana shafa sumar kansa, ya d'an daga kansa sama, sak'on d'aya biyu....... Kawai ya kaima Auta wani bugu a saman kai, nan take Auta ya zube a sume.


Wani sab'on kuka ne ya kufce ma Nanah tana kiran sunan Auta iya k'arfinta, duk tunaninta ko mutuwa yayi.


Cikin muryar kuka take magana tana kallon Tajo cike da tsana ta ce "ku sani Allah bazai tab'a kyale ku ba, Allah saiya isar mana akan zaluncin da kuke mana. K'aramin yaro ma baku kyale ba, tsabar baku da imani, Allah ya isarmu wallahi bamu yafe ba".




Dariya Tajo ya saki yana matsowa inda Nanah take, ya damko wuyanta yana cewa "au ashe kina magana y'an mata?, na d'auka ai kurma muka d'akko. Dama mu ai bamu ce ku yafe ba. Ya ishe mu da kukan banza ne, shine na sashi yin baccin dole, kin gane?, zai farka ai ba mutuwa yayi ba, amma ki sani ya sake mana irin haka, to zaibar duniya ne gaba d'aya. Ya kamata ki kula, bama son damuwa ne".


Wani abu mai d'aci Nana ta had'iye a mak'oshinta tana bin Tajo da kallo. Ji take inama tana da dama data shak'e masa wuta shima harsai ya daina numfashi.




Cikin dare Nanah tajiyo kukan Auta daya farka, sanyin dake cikin dajin ne ya farkar dashi, ga kuma inda yake kwance tsinnaku duk sun cijeshi a jiki. Da sauri Nanah ta kira sunansa a hankali. Da lalube ya k'araso inda Nanah take, yana zuwa ta rufe masa baki da tafin hannunta data samu Tajo ya kwance mata shi, d'azo daya gama gaggaya mata magana.


A hankali Nanah ta ce "dan Allah Auta kayi shuru, kayi hakuri kaji?, zuwa safiya za'a baka wani abu kaci, kana kallo mutanan nan basu da imani fa, kana so ka mutu ne?".
Da sauri Auta ya girgiza mata kai.
Ta ce "to yawwa ka daina kuka idan baka so kaji?".


Ba yadda Auta yayi dole tasa yayi shuru ya mak'ale a jikin Nanah.


Suna haka, sukaji ihun wata matashiyar yarinya, daga jin yadda take ihun tana neman taimako, zaka san cewa so ake a keta mutumcinta ne.


Yadda Nanah ke jin yarinyar na cewa "wayyo Allah, ku taimaka min zai kashe ni, na shiga uku ina zan kai wannan mutunin, zai lalata min rayuwa dan Allah ku ceceni".


Waro idonta Nanah tayi tana kallon wata ruffa da abun ke faruwa hasken fitila ta gani a wajan, ihun yarinyar na fitowa daga cikin rufar. Tana iya jiyo yadda suke kokowa da yarinyar, tana son kwance kanta. Tana jin shi kuma yadda yake ta kai mata maruka ba k'ak'k'autawa.


Allah sarki yarinyar duk da irin dukan da yake kai mata so kawai take ta kwaci kanta, sai kuka take tana kiran azo a taimaketa.


Ganinfa tana son b'ata masa lokaci, gashi duk ta ji masa ciwo yasa ya harzuk'a bai san sadda ya d'akko bindiga ba ya sakar mata harsashi.


A mugun rud'e Nanah ta toshe kunnuwanta had'e da k'ara rungume Auta daya fasa wata gigitacciyar k'ara yana sumewa a jikin Nanah, domin harga Allah ya mugun tsorota sosai. Nanah tama rasa wane hali take ciki, duk ta rud'e ta fice daga yaccinta. Ga Auta da bata jin motsinsa a jikinta, ga yarinyar da tana da tabbacin ita ce aka halba. Tana iya jiyo yadda D'an Ta'addar ke ta'asarsa saman kan yarinyar duk da halbinta da yayi, amma tsabar mugunta da rashin imani a haka ya afka mata.....




_________________________
Mike shirin faruwa ne da Salma wai?, ya rayuwar Salman zata kasance a nan gaba ne wai?, shin Momy wacce irin zuciya ce da ita ne ta rashin imani?, kaiii wannan Mama ma akwai y'ar kwal uba fa🤭. Shin wai tsaya ma Hajiya zata amince da aurar da ake son d'aura ma d'iyarta wadda bata san dashi ba?, Yaya Salma zata ji idan taji an d'aura mata aure da wani, waninma wadda bata tab'a gani ba?...*KAIII JAMA'A AKWAI CAKWAKIYA A BOOK D'INGA, NA TSAYA A NAN DOMIN NIMA INA SON SANIN DUK AMSOSHIN NAN*
_________________________




*To a nan na kawo k'arshen Free pages*


*Game son ci gaban book d'in nan zai biya D'ARI BIYAR NE KACAL*


Ta wannan account number d'in.
8130479973 Fatima Rabi'u Opay bank


Saika turo shaidar biya ta wannan number d'in 08130479973

6
7
8

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login