Showing 18001 words to 21000 words out of 22238 words

Chapter 7 - SAUYIN YANAYI Free pages -WPS Office.txt

naji Hajiya na cewa. "Salma ya kamata fa ki aje typing d'in nan haka nan, ki d'an huta, idan kika gama littafin nan, ki d'an huta, kamin ki d'ora wani"


Sai kuma na sake jin Salma ta ce "Hajiya ai hutu ba yanzu ba, tunda ina da lokaci yanzu so nake sai nayi littafi kusan goma ko biyar tukunna zan huta. Dan har gasar Hikayata nake so na shiga shekarar nan"


A haukace Mama ta mik'e tana cewa "kutumar Ubancan, ai ko bazai tab'a yiwuba wallahi, dole na d'au mataki, dole ne gobe naje garin Hayin fari, wajan Mlm, dole ne sai Salma ta nemi wannan basirar rubutu littafin ta rasa, dani suke zancan wallahi".


Maryam ta sake kamo hannun Mama tana cewa "Mama kiyi a hankali dan Allah, kar wani yaji, nasan dama zaki d'au mataki ai, shi yasa zuciyata ta kasa yarda ba Salma bace tunda naji sunanta, na ce ni ko saina binciko, ashe-ashe b'oye mana ake dankar mu gane",


"Hmm dole zasu b'oye mana, amma yanzun ma ba makara nayi ba wallahi".






*Gurbi K'aramar Hukumar Jibia Katsina State Nigeria*




Tagumin da Nanah ta zafga ne, tun fitar Saminu take jin wata fad'uwar gaba, Allah ya sani tunda Baba ya rasu take jin irin haka, kuma har yanzu bata sake ta ba.


Inna dake mata magana tun d'azo, ganinfa kamar bama jinta take ba, yasa Inna mamakin miye Nanah take tunani har haka ne?. Ace duk uwar maganar nan da take bata ma jinta ashe?.


Saida Innar ta dafa kafad'arta, ta d'ago a d'an zabure tana kallon Inna.


Inna tana kallonta, ta nisa ta ce "Nanah lafiyarki kuwa?"


Ai kawai Nanah saita fashe mata da kuka. Tana jin wani abu ya tsaya mata a wuya.


Hankali a tashe Inna ta ce "Subhanallahi ke Nanah miye hakan kuma?",


"Inna tsoro nake ji wallahi. Inna ina tsoron mutuwa yanzu wallahi, bana son k'ara rasa kowa Inna"


Wani murmushin manya Inna ta saki tana cewa "haba ke kuwa Nanah ai mutuwa dole ce, ga duk mai rai. Ki kwantar da hankalinki insha Allahu sai Kinga y'ay'anki harma da jikoki, kinji bana son ganinki cikin wannan halin kinji?"


Goge hawayenta Inna tayi. Nanah ta sakar mata murmushin yak'i wadda bai kai zuci ba.




Cikin dare Nanah ta kasa runtsawa ko kad'an ga Auta dake kwance a jikinta, sai Inna dake gefensu. Tana baccinta hankalinta kwance.


Murd'awar da cikin Nanah yayi ne tasa ta sauk'e Auta daga jikinta, domin zuwa ban d'aki, haka nan taji wani zawo-zawo ya kamata.
Da sauri ta nufi ban d'aki.


Tayi mamaki ba abunda taci amma cikinta ya b'aci domin zawo tayi mai ruwa ma kuwa.


Bayan ta koma ta kwanta bata fi minti biyar da kwanciya ba, ta sake jin cikinta ya katsa.


Wani d'an tsaki taja tana dafe cikin nata. Fitowarta kenan zata d'auki buta, ba zato ba tsammani kawai taji K'arar halbe-halben Bindigogi kota ina suna tashi a tsakiyar garin nasu.


Cikin Nanah ne ya k'ara hautsinawa, ji tayi tana niyar sakin kashin a wando tsabar tashin hankali.


Zaro ido tayi hankalinta a mugun tashe tama k'asa koda motsawa a inda take. Sai da taji saukar maganar Inna itama hankalinta a tashe tana cewa "keee Nanah kinji abunda naji kuwa?, kodai kunne na ne kawai ke jiyo hayaniyar mutane da halbin Bindigogi?"


Nanah ji tayi kamar bacci take Inna ta farkar da ita. Bakinta na kyarma wajan cewa "mun shiga uku Innna, inama yau muka bar garin nan, na shiga ukuna, bana son mutuwa yanzu, bana son rasa kowa yanzu, wayyo Allah Inna ki taimaka mana, Inna ina zamu gudu?, Inna kina jifa gida-gida suke shiga".




Ai kawai Inna itama saita ji wasu zafafen hawaye na zubo mata. Auta dake gefen Inna ya rungumeta yayi shuru kamar wadda baida baki, shima kansa hankalinsa a tashe yake.




Banko k'ofar gidan da akai ce tasa Nanah da Inna zabura suna curewa waje d'aya. Ba abunda ke fita a bakinsu sai Addu'a, sosai Nanah ta rungume Inna da Auta.


Abunda ya shigo gidan nasu ne ya k'ara hargitse masu kwakwalwa.


Nanah kuwa zawon data ke rik'ewa ne ya samu damar kufce mata a wando. Zubewa kawai sukai a k'asa su duka. Ba abunda jikinsu yake sai rawa.




Ganin wasu Y'an Ta'adda sun kai su biyar fuskokinsu duk a rufe rik'e da wasu Bindigogi wadda tunda aka haifi Nanah bata tab'a ganinsu da idonta ba, kai hatta Inna ma, sai dai su kallesu a cikin Film.


Wata tsawa aka daka masu yasa su Inna runtse idonsu ba shiri suna fashewa da kuka.


"Keee ina mai gidan nan yake?"


Bakin Inna na rawa take cewa "mai gidan nan ya rasu da dad'ewa"


Zagaye gidan suka farayi suna bincika ganin babu wani namiji cikin gidan yasa wani Babba cikin y'an Ta'addar ya ce "kaiii Tajo, ka kashe min matar nan, yarinyar nan kuma ku taho min da ita, da wannan yaron"


Wata irin kururuwa Nanah ta saki tana ihu iya k'arfinta take cewa "na shiga ukuna, na lalace, dan Allah karku kashe min Innata, gara ni ku kashe ni, daku kashe ta, wayyo Allah dan Alla...... Maganar Nanah ta tsaya cakkk sak'on d'aya biyu...... Jin saukar k'arar Bindiga a kunnanta, kamin ta gama tantance waye aka halba, taga Inna ta zube a jikinta babu alamar sauran rai a tare da ita. Domin a saman kanta Tajo ya saita bindiga ya halbeta nan take.


Yadda kasan batun-batumi haka Nanah ta koma. Hatta da d'an yatsan hannunta baya motsi. Tana iya jiyo kukan Auta yana girgiza Gawar Inna dake yashe a k'asa.


Tana dai jin sadda wani ya sab'eta a bayansa, daga nan bata sake sanin mike faruwa ba.


Shima kansa Auta tasa k'eyar yaron sukai suna zaginsa suna turasa da bakin Bindiga.


Auta yana gani aka tasa su gaba aka bar gawar Inna. Auta yana ganin yadda y'an Ta'addar suka kaso mutane da yawa, dake cikin garin naso. Wasu suka d'ora su a Mashina, wasu a mota, wasu ma a k'asa, an d'aure su da igiya, kamar wasu dabbobi, yana gani akasa Nanah kan wani mashin, shima aka jefasa cikin wata bayan mota, suka fara tafiya cikin dokar daji mai duhun gaske, sunyi tafiya harta wuce hankali, tun yana iya gane ina suke har ya rasa ganewa, tun idonsa biyu suke tafiya har wani wahalallan bacci ya d'aukesa............


*SAUYIN YANAYI*








Share Fisbilillahi
*©ZAHRA ROYAL STAR 🌝*






*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*






*EPISODE* 9-10 END OF FREE PAGES






*MAMA* POV




"Mlm so nake a lalata mata basirar rubuta littafin data fara. Ina so asa mata rashin kwanciyar hankali tare da farkai masu ban tsoro, ta yadda bata da wata natsuwar rubutun bare harta k'irkiri wani labari"


Mlm dake kallonta da jajayen idonsa, ya saki wani murmushi yana cewa "wani hanzari ba gudu ba Hajara"


"Ina jinka Mlm"


"Akwai wata k'awarki Asiya hakane?"


"Kware kuwa Mlm Asiya k'awarta ce Unguwa d'aya ma muka taso da ita ai"


"Yawwa to zata kawo miki ziyara a yau d'in nan. Zata zo da wani fahimmin zance, duk yadda zakiyi kiyi domin aba Asiya aurar Salma. Indai kina son ganin bayan Salma, to ki tabbatar Abbansu Maryam ya amince da abunda Asiya tazo dashi"




"Mlm na kasa fahimtarka fa?"


Murmushin gefen baki ya sake saki kamin ya d'akko wata kwarya cike da ruwa ya nuna cikinta, yana cewa "ki kalla tsakiyar kwaryar nan"
Da sauri Mama ta kai dubanta a cikin kwaryar abunda ta gani ne ya bata mamaki.

Da d'an mamaki take kallon Mlm.
Mlm ya ce "miye kika gani ciki?"


"To Mlm mutum na gani, kwance bashi da lafiya, kamar mai shirin komawa maciji, jifa fatar jikinsa yacce take komawa tana sabulewa kamarta aljanin maciji, masu komawa mutane, irin wadda nake kallo a cikin fina-finan India"


"To kinga wannan mutunin shine za'a aurama Salma shi, zata zauna da mahaukaci har rayuwarta ta lalace, bata tsinana komai a duniya ba, tazo a wahale zata koma a wahale".
Wata shewa Mama ta saki harda su bud'a tsabar dad'i.


Ta k'ara duba cikin kwaryar tana cewa "ai Mlm dole ma Abbansu Maryam ya amince da wannan batu. Abu d'aya zaka min kasa shi ya amince kawai idan na masa zancan, karma yayi min gaddama".


Mlm ya d'akko wani k'ulli ya mik'a ma Mama yana cewa "kinga wannan?, ki tabbatar kin sa masa a abinci yaci, kamin ki kai masa maganar, na tabbatar zai amsa bai shirya ba. Sana ita kuma zamu sa mata rashin natsuwar zuciya bata da lokacin ma rubuta wani littafi"




"Idan kamin haka Mlm ka gama min komai ai"


Mama ta fad'a tana bud'e jakarta ta fiddo da wasu kud'i, tana dank'ama Mlm sai washe baki yake.




*Unguwar Dubantu Hadejia Jigawa State Nigeria*




"Hajiya yau ne fa na tura labarina na gasar Hikayata, kimin addu'a"


"D'iyar albarka Allah ya bada sa'a kinji"


"Amin Hajiyata"
Cewar Salma tana kallon Hajiya da murmushi kwance akan fuskarta.




Ahmad ne yayi sallama ya shigo hannunsa rik'e da wata leda.


Zama yayi kan d'aya daga cikin kujerun parlon yana kallon Salma dake mik'a masa gaisuwa, ya amsa yana cewa "Salma kina shan magungunan ki kuwa?"


Murmushi ta saki tana jin dad'in yadda Yayan nata yake bata kulawa sosai. Ta ce "eh man Y Ahmad Ina sha"


"To amma naga kwayar idonki ta canza kala tana son komawa d'orawa?"


"To nima ban sani ba, amma dai duk ina sha akan lokaci yadda ya dace"


"Abinci fa kina kiyaye cinsa?, kin san fa ba kowane abinci ne ya kamata ki rink'a ci ba?"


Hajiya ce tayi gyaran murya tana cewa "Ahmad kenan, kaima kasan ba komai take samu ta ci yadda ya dace ba, kai dai kawai Allah yasa mu dace ya bata lafiya kuma"




Shima ajiyar zuciya ya sauk'e yana mik'a ma Salma ledar hannunsa ya ce "anshi wannan ki samu kici, ki ajema Ismail sauran"
Da murmushi sallama ta amsa tana godiya.


Tashi yayi ya fice daga d'akin.
Bayan fitarsa Salma ta bud'a ledar tana kallon abunda Yayan nata ya sayo mata. Su kankana ne dasu Ayaba, da dai sauransu.
Sosai Hajiya tayi murna dan ya kamata Salmar ta rink'a shan abubuwa irinsu dama.




Sallamar da ake rafkawa a tsakar gidan ce, sawa Maryam fitowa daga d'akinsu.


Ganin k'awar Mama Asiya ce yasa ta cewa "Inna Asiya sannu da zuwa, ai ko yanzu Mamar ta dawo daga unguwa, Allah yasa zaki tadda ita, bari na kira miki ita, tana d'akin Abba"


"Yawwa y'ar albarka kira min ita, akwai magana yau ai",


Bata tsaya jiran jin sauran abunda Asiyar ke cewa ba tayi gaba ta shiga d'akin Abban.


Zaune ta iske Mama sai wani iyaye take ma Abba yana biye mata.


Ganin Maryam ta shigo d'akin yasa Mama dubanta tana jiran jin miya kawota?.


Maryam ta ce "dama Mama Inna Asiya ce tazo ",


"Kai ai ko nasan da zuwanta, bari jeki gani nan zuwa",


Maryam na fita Mama ta dawo da dubanta wajan Abba tana cewa "kaji abunda nake gaya maka ko?, dama na ce ma zata sake dawowa ne, domin tana so ayi abun da wuri"


Abba ya nisa ya ce "kin ce yaron bashi da lafiya zata je kula dashi ne, za'a d'aura auran domin gudun faruwar wani Abu?, to amma a can zatayi karatu ne ko kuwa?",


Kallon takaici Mama ke aikama Abba, yadda yake shirin mata musu, duk da ta basa abinci da abunda Malaminta ya bata, kuma ya ci, dan yana kanci ma.




Ta ce "eh man zasu sata mana, babu abunda zata nema ta rasa. Ai kaga gara ma taje can tayi mai dalili, kai ka huta da kashe kud'inka akanta. Kuma tazo karatun ta kasayi kayi asarar kud'i akanta, tunda kasan ai ba k'ok'ari gareta ba, asarar kud'i kawai zakai, gara can taje tayi karatun acan"




"Kuma fa hakane Hajara. Ai kawai na amince, ko gobe suka zo za'a iya d'aura auran babu wata damuwa"


Wani almurin murmushi ta saki. Tana cewa "yawwa Abbansu Maryam shi yasa fa nake k'ara sonka, akwai saurin fahimtar mutum. Bari naje wajan Asiyar na sanar da ita abunda ake ciki"




Tana gama maganar ta fice daga d'akin.




"Ahh ahh Asiya yada zama waje kuma?, ga d'aki"


Cewar Mama data fito daga d'akin Abba, ta iske Asiya zaune a waje.


Asiya ta ce "wallahi kawai zama nayi nida Maryam muna d'an tab'a fira, ina Khadija ne ni kam?, ban ganta ba"


Mama ta ce "wallahi Khadija sun fita ita da wadda zata aura sunje wata sayayya ne"


"Ahh kai Masha Allah, kice an samo mana siriki kenan?"


"Ai kuwa dai, na nunawa a sa'a kuwa"


"Ayyiririiii, kice mun kusa zuwa aikin hajji?".


Dariya Mama ta saki tana kamo hannun Asiya suka shige d'aki Mama na cewa "ai kuwa dai, gamu can a k'asa mai tsarki"


Zama Asiya tayi tana cire gyalanta ta k'ara natsuwa ta ce "kinga akwai fa magana a bakina sosai",


Dariya Mama ta saki tana cewa "tunkan kizo na riga da na gama da matsalar, domin nasan zancan daya kawo ki"


Cike da d'unbin mamaki Asiya ke duban Mama, ta kasa hakuri ta ce "kamarya ban fahimta ba?"


"Hmmm Asiya kenan, Malami na nasa yayi min duba, har ya sanar dani zuwanki, da abunda zaki zo min dashi, tunkan kizo, na riga da na sanar da Abbansu Maryam, akan wannan zancan, kuma na gama shawo kansa, kawai abunda zance miki shine su turo ayi auran kawai"


Rik'e baki kawai Asiya tayi tana kallon K'awar tata, shaid'aniya uwar shaid'anu. Yo idan ba shaid'aniya ba, waye zai haka?.


Kamo hannunta Mama tayi tana fiskewa ta ce "ke karkiyi wani mamaki fa, kamar kin manta wace ni?".


Ture komai Asiya tayi tana cewa "tunda kin gama da wannan, kema tukaicinki babba ne, idan abun ya kasance"


"Baki da damuwa komai zai kasance yadda muke so".


Dariya suka saki a tare harda tab'a hannu.




*Copa Cabana Estate Lokogoma District Abuja Nigeria*




Waya ce manne a kunnan Momy suna waya da Asiya.


Daga cikin wayar Asiya ta ce "Hajiya an gama komai fa, yanzu haka wakilanku kawai zaku turo a d'aura auran, ku tafi da amarya"


"Da kyau, haka nake sonji. Zan turo miki naira million biyar, ki d'auki naira million biyu, kiba wacce tayi hanyar abun ya yiwu, naira million d'aya, shi kuma Abban yarinyar ki basa cik'on naira million biyun"


Wata shewa had'e bud'a Asiya ta saki tana cewa "saike Hajiyarmu, uwar gida, a gidan Alhaji Bin Muhammad daga ke ba k'ari, Allah dai ya biya".
Dariya kawai Momy ta saki tana kashe wayar. Ba'a jima ba kuwa saiga message na account number na Asiyar. Nan take ta tura mata kud'in gaba d'aya.




Zaune take a gaban Daddy bayan ta gama koro masa jawabin abunda take so ayi.
"Daddyn Salman, ina ganin yarinyar ita ce ta dace da zama da Salman, domin yarinyar tana da hankali da tunani, zata zauna dashi tsakani da Allah badan komai nasa na duniya ba, domin duk sauran da yake aura duk dan kud'insa ko kyansa ke rud'arsu".


Daddy ya aje wani biro dake hannunsa yana rubutu a wasu takardu ya ce "kina ganin ita yarinyar ba'a danne mata hak'k'inta ba?, kin sanfa yadda rayuwar yaron nan take ciki"


Kamo hannun Daddy Momy tayi cike da kissa ta ce "ba wani danne hak'k'inta da akai. Hasalinma taimakonta akai, saboda ita kanta tasan ko a hanya bata isa ganin Salman ba, yaro mai kud'i ga kyau ga nasaba, komai ya had'a, kawai wannan ciwon ne ke basa matsala a rayuwa, kuma da sannu komai zai shige, idan komai ya wuce ita ce da riba nake gani ai"


Wani murmushin jin dad'i Daddy yayi, yaji dad'in yadda ta fahimtar dashi, kuma ya fahimta sosai. Inda daga k'arshe ya ce "to ita yarinyar y'ar ina ce?, yaushe kuma kike ganin za'aje domin tabbayo auran nata?"


"Y'ar Hadejia ce, kuma tabbayo aure duk bai taso ba, d'aurasa kawai za'ai, domin duk na gama da wannan, yanzu haka Abban yarinyar yasan da maganar, ku kawai yake jira"


"Ai shikenan tunda abu yazo gidan sauk'i. Zanje da kaina tare da wasu manya dana aminta dasu a d'auro auran zuwa gobe insha Allahu".


Cike da farin ciki Momy ta baro part d'in Daddy. Tafe take tana maganar zuci.
"Hmm Alhaji kenan, kaifa gani kake kamar son d'anka nake ko?, ina duk duniya ba abunda na tsana yanzu kamar shegen yaron can naka, amma da sannu zan kawo k'arshensa".




*NANAH* POV




Wani irin sansanin y'an Ta'adda ne su Auta suka tsinci kansu ciki. Auta ba abunda yake sai kuka yanata neman inda zai hangi Nanah.


An zube su wani waje duk ciyayi ga rana ta kwanyare.


Kowa ka gani wajan sab'anin y'an Ta'addar cike suke da tashin hankali.


Kamar ance Auta ya waiga ya hango Nanah dake d'aure a jikin wata bishiya har yanzu a sume take bata farka ba. Gashin kanta ya sakko ya rufe mata fuska.


Da gudu Auta ya nufi inda take, yana aikin kiran sunanta.


Wani d'an Ta'adda ne ya matso ya kwasa masa tsawa, yana cewa "kaiii ina zaka je haka?, koma inda kake kar yanzu na fasa maka kai da wannan Bindigar"


A tsorace ce Auta ya ke duban D'an Ta'addar. Amma duk da haka tsaye yake inda Nanah take ya rik'e tsintsiyar hannunta sai jijjigata yake.


A hankali Nanah ta fara motsa hannun nata, kamin komai nata ya fara dawowa dai-dai, dashi-dashi take ganin mutane, hatta muryar Auta sama-sama take iya jiyota, kamin ta ware idonta akan Auta.


Auta ko jin Nanah na motsa hannunta yasa shi sakin murmushin k'arfin hali yana sake kiran sunanta.


Kallon Auta take kamar wacce ta samu tab'in hankali. Kamin komai a hankali ya fara dawo mata, duk abubuwan da suka wakana a daran jiya.


Tana gama tunanowa ta fashe da wani irin kuka mai k'arfi jikinta na rawa, ta kama leb'en bakinta ta cije tana durzar kuka. Ganin yadda take kuka yasa Auta ma fashewa da kuka.


Wani daga cikin y'an Ta'addar ne ya k'ara matsowa inda suke, bai tsaya wata-wata ba, ya damk'e gashin kan Nanah ya jashi zuwa baya da k'arfi, har saida ta saki wata k'arar azaba. Fuskarta ce ta bayyana.


Hawaye duk sun b'ata mata fuska. Cike da rashin imani yake kallonta ya ce "zakiyi mana shuru a wajan nan, ko sai na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login