Showing 6001 words to 9000 words out of 40610 words

Chapter 3 - MAH~ NOOR (MY FIRST WIFE) BY MRS USMAN-1.txt

06 Mar 2025

3507

ta tare da kiran ta da hannu. "Ki min tausa"
Wani irin girma kanta yayi tare da wani bada sauti na musamman, yau ita ce zata yiwa daya daga cikin young billionaire boys na naija. Jin wani irin karsashi ya shigeta, a hankali ta isa bayan shi, tare da fara mishi tausa, a sannu a hankali. Take mishi, yana aiki tare da lumshe idanun shi. Karar wayar shi tayi wacce take saman table din Office din, ya kai hannun shi ya d'auka.
         Lion Man! Ya gani, murmushi ya sake sannan ya kunna tare da sakawa a amsa kuwa.
"Barka dai Lion!"
"Tiger!" Ya kira sunan cikin wata irin kasalalliyar murya, juyawa yayi ya kalli Tasleem, da sauri ta tashi ta koma daya daga cikin kujerun cikin office din, ta zauna wasu gray colour, ta daura daya akan daya.
"Lion! Kana bukatar wani abu ne?"
         Shiru yayi, yaki bashi amsa. Sai da ya kuma maimaita abinda yace sau uku kafin yace mishi.
"Please ka daina min ihu,"

       "Ok what do u need? Ko kana bukatar zafaffan Yan mata zasu jiyar da kai dad'i." Wani irin iska yaja tare da yaji, sannan yace.
"No need, yan bautar ƙasan sun iso ko? And ka zab'a min daya a cikin su.  Wanda zai taimaka min da aiki Insha Allah ina hanya kowani lokaci."

       "Ok boss!"
Karamin tsaki yaja, jin ya kira shi da boss. Yana kashe wayar ya kalli Tasleem, yaga itace ta dace da Office din Mr Mahir, murmushi yayi sannan yace." Hey" da sauri ta mike tare da isa gurin shi, ta Cigaba da aikin, yana wani juyar da wuyar shi

         Zuwa gabanta yayi tare da zuba hannun shi duk biyu a aljuhun wandon shi.
"Zaki iya aiki da kuwa, akwai brother na, da zai dawo dan haka ki nutsu karki janyo ya kore ki "

Gyada mishi kai tayi, sannan ta juya zata fita yace mata.
"Kice Aeesha tazo."

     .... Ciki ciki ta amsa mishi, tana me fita a ranshi yace.
"Hmm!"

Muna tsaka da aiki tare da Badar ta shigo, tsaki tayi sannan ta juya ta zauna tare da cewa, "kije Mr Nazzir yana kiranki."
          Mikewa nayi na fita, kallonta Badar yayi yace.
"Kina kishi da ita ne?"
Wani kallon banza tayi mishi tare da wani gatsine face, kafin ta Cigaba da abinda take.

.. ina shiga ya kalle ni, tare da nuna min gurin zama na zauna.
"Ko zaki zauna a Office dina kina tayani aiki?"

      Shiru nayi kafin nace mishi.
"Kayi hakuri! Ba zan iya zama da wani namiji a guri guda ba, domin duk yadda aka zauna mace da namiji sai ka samu na ukun su iblis ne! Am sorry service muka zo ba kebewa ba!"

Ina gama gaya mishi haka na mike tare da barin Office din. Murmushi ya sake tare da cewa.
"Dama nasan da haka."
Tunda na koma muka cigaba da aiki, tare da nuna min wasu abubuwan na kamfanin, har aka yi break, muka nufi gurin cin abinci. Ban iya cin kome ba, sabida da kunya nayi ta cusa abinci a gaban mutane. Abinda bai tab'a faruwa ba yau shi ya faru. Zuwan Mr Nazzir gurin cin abincin.
.     Ya amso shima ya zauna a kusa da ni,
"Ko baki murna da gani na ne?"
"A'a," na fada da sauri."toh kici mana" yace min,
"Ban iya cin abincin a gaban jama'a bane." "Ok, idan babu kowa zaki iya ci?"
    "A'a ba sai haka ba, zan ci a Office."
"Toh muje office dina!"
"No...no, nan ma yayi."
D'ago kai yayi sannan ya kira wani security yana tawowa ya sunkuyar da kanshi, suka yi magana.
Mutumin na d'aga kai, ya kalli yadda kowa yake juyawa yana kallon mu, sannan ya bude murya yace.
"Kowa ya bar nan, kuje Office din ku, ko gurin da kuke ku ci abincin ku, ku bar nan cikin minti biyar."
     Cike da mamaki, ake kallona, sannan suka shiga daukar abincin su. Suna fita, irin ransu a b'acen nan kallon zaki sani Tasleem tayi min.

        Nima mik'ewa nayi ya rike tiren abincin yana faɗin.
"Zauna muci."

"Amma!"
Hannun shi ya saka a baki tare da lumshe idanun shi, dole na zauna na fara cin abin ba wani abu bane, snacks ne sai namar kaza da kuma juice, ganin juice din shi nayi ba irin namu ba, dan haka ma ɗan saci kallon goran, na cigaba da cin abincin, guda daya naci. Sannan na goge bakina na mike ko inda yake ban kalla ba, na barshi zaune.
"Hotness! Ina zaki?"

     Cak na tsaya, kafin na juya tare da nuna mishi agogon hannuna, min cinye lokacin mu. Har mun shiga na aiki. Table baki yayi tare da mik'ewa, ya biyo ni.
"Baki ce min kome ba!"
"Da aka yi me?"
Na maida mishi tambayar shi,
"Baki tambaye ni, Number na ba"
"Bashi ya kawo ni ba! Abu nazo yi, kuma idan na gama zan kara gaba."
"Tare zamu kara gaba?"
Juyawa nayi na kalle shi, sannan na wuce inda zai kai ni office din Badar, muka shiga aiki, shigowa yayi yaga yadda nake mai da hankali ga bayanin da Badar yake min, a hankali ya iso tare da sunkuyawa yana kallon laptop din, sannan ya tab'a wani gurin, yadda ya kwanto ya bayyana yasani jan kujeran kamar zai fadi.
"Sorry! Kimar hijab dina nake karewa;" na fada mishi haka a hankali, lokacin da ya juya yana kallona, murmushi yayi sannan yace.
"Karki damu!"
Tab'a mouse na laptop din nayi, tare da kai arrow din side din da yace ai yarda a shiga ba, yana ganin haka ya yayi maza ya kai hannun shi kan nawa, da sauri na juya. Girgiza min kai yayi, janye hannun nayi tare da yarfe hannun. Kamar na tab'a wuta,
"Bana son ki tab'a gurin, tsohon gurin sarrafa abubuwan kamfani ne yanzun baa cika amfani dashi ba. Badar kayi mata bayani, har da Tasleem yadda zasu fahimta."

Yana gama fadar haka ya fice abin shi,.yana fita,.itama tana fita.
"Noorh, kin san Allah zaki b'allo min August, wannan side din ba'a shiga, sannan na gaya miki karki na barin yana tab'a ki, Kinga kamfanin nan, mugun guri ne! Mutane da yawa sun mutu sabida wannan kamfanin, yan bauta ƙasa irin ki sun mutu, sai samun gawar su ake a gidajen su.

       Noorh, jami'an sirri sun mutu, kuma su kan su kamfanin suna da goyan bayan gwamnatocin kasar nan domin idan aka zo campaign, suna bada gudummawar su na fitar hankali. Sabida asalin mai kamfanin yayi hidimar siyasa, kuma har yau ana siyasa a cikin gidan su. Dan haka ki kula koda anyi wani abu b'oyewa suke."

    "Amma kasan abin shan mu dana shi ba ne iri daya bane. " Buge min baƙi yayi, tare da magana kasa kasa.
       "Baki da hankali, kiyi kokarin dakatar da nazarinki idan ba haka ba, sunanki gawa."

    Ya faɗa min tare da Cigaba da aikin shi, shiru nayi tare da rike goshina ina kara tunanin rubutun jikin lemon kwalbar, ina kara juyar da lumshashen idanuna, a hankali na sauke akan  da sauri na bude idanuna, tare da kallon shi kasa kasa nayi da muryana kamar karyaciya nace.
"Abin."
"Hm" yace min tare da mik'ewa ya nufi wani daki, bai fito ba sai karfe sha biyu saura, yana fitowa ya kalle ni.
"Sannu!"
"Yawwa!". Can ya cigaba da abinda muke, ban ga Tasleem ba har kusan karfe ɗaya muka fita sallah, muna dawowa, na sameta tana wasu dube dube a wayarta.

"Tasly!" Ture hannuna tayi, cikin wani irin kallo, sannan ta mike tana faɗin.
"Karki min karuwanci,  karuwa kawai. Da kika tafi office din MD."
Ture ta nayi cikin bakin ciki, tare da nuna ta da yatsa, kawo hannu tayi zata murɗe min yatsar na kama hannunta, na juyar da ita, sai shegen baki babu karfi.
"Karku kuma kira na da kalmar karuwa, dan wallahi zan baki mamaki, ni ban iya niman maza su soni ba, halitta tace, duk wanda ya zauna dani sai ya bukaci haka a tare dani.

   Sannan da kike cewa, naje office din Mr Nazzir, kece zaki gayawa kanki haka, Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, yace idan dayan ku ya jefe ku da kalmar da ya kasance muzanci ne da b'atanci, kuma bai nemi yafiyarku ba, idan har baku aikata ba, Allah ba zai tab'a kyale shi ba har sai ya aikata abinda ya gaya muku, dan haka ki nemi yafita, domin ba zan yafe ba." Na cigaba da murde mata hannunta tana kuka.. shigowar Badar yace.
"Subhanallahi! Noorh! Saketa bana son shirme!" Ture ta nayi ta fadi.
Ya d'ago Tasleem tana kuka kamar wacce aka saka mata wani abu.
"Me ya faru!" Zuciya ta hanani bashi masa tace mishi.
"Hm! Fisabillahi! Kome Noor, kowa Noor! Babu wanda ya dame da how am feel, she take my position! Ta dauke hankalin kowa, d'azun kaga yadda MD ya kore mu sabida ita, Why sai Noor ?" Tana gama fad'ar haka ta dauki jakarta ta bar Office din.

        ..... Bata kula Mr Nazzir da yake bakin kofar ba, ni kaina kuka nake, tare da ɗaukar jakata, zan bi bayanta, yace min.
"Ki dawo kiyi muku sign, sabida asan kun zo kun fara abinda ya kawo ku."

     Zuwa nayi, na cika mata tare da nawa, na fito ina zuwa naga ta tafi, wani irin kuka ne yazo, ya tsaya a gabana.
"Zo na kai ki"
Kallon shi nayi, sannan na shiga motar ina yi ina share kwalla na, har muka isa gidan, ya har cikin gidan ya kai ni,sannan ya tsaya tare da mika min tissue, na bude tare da cewa."thanks!"
Na ficce abuna, tunda daga bakin kofar shi gidan cikina ya murɗa, dan na hango ta tana kuka a jikin window..
Ina shiga ta juya gurin Mommy, cikin kuka tace..
"Mommy shine ya kawo ta, Mr Nazzir Abu Aswad, Mommy na shiga uku mutuwa zanyi don Allah Mommy ku kore A'isha daga gidan nan!"

#Vote
#Comments
#Share😍😘🌹
https://my.w.tt/fpBMaONrHbb

MAH~NOOR✧✧
My First Wife♡
Chapter 0️⃣5️⃣
MrsUsmaa400
Free book
For You Jikar kulu

BISMILLAH RAHAMANIH RAHEEM

~#HB Family~

Wani dan iskan rawa jikina yake tare da zaro idanu waje, cikin karaji tace.
Fitar min a gidan Ubana, bana son kuma ganinki, bana so? Bana kaunar ganinki, fita ko na saka a kashe min ke!"
   Ta shiga turani da karfin tsiya, hawaye ke tsiyaya a idanuna, a hankali momy ta tako tare da zuwa gaban mu, ta kifa min mari.  Kafin ta kuma d'ago kaina.
       "Ke! Kike niman hanyar da zaki wargaza farin cikin Baby Queen?"
Bakina na rawa nace mata.
"A'a momy wallahi ba  yadda take tsammani bane, wallahi babu kome a tsakanin mu, kawai tana zargi ne don Allah kiyi hakuri wallahi ba zan kuma shige mishi ba."
          Kallona a hankali tana danne zuciyarta ga abinda yake tinxirata, gani take me zai hana ta lalata fuskar da mutane suke rawan kai akan shi. Idan ta tuna kuma yadda dangin Mahaifiyar Noor suke mahaukatar masu kuɗi ne, sai taji jikinta yayi sanyi. Dan tasan tana tab'a lafiyar Noor kamar ta kashe yarta da ranta ne.
     .Sake ajiyar zuciya tayi sannan tace mata.
"Karki kuma sakewa naga kin fita zuwa HB. Company idan kuma na fahimci haka toh zan lalata miki."
"Insha Allah ba zan kuma ba kiyi hakuri don Allah."
   "Wuce ki bani guri."
Da sauri na bar falon tare da hayewa sama, ina wucewa suka bini da kallo.
"Momy!"
"Bana son ci da zuci, idan muka mata wani abu kece zaki fara faduwa, idan muka barta kece zaki moreta. Dan haka ki zuba mata ido, zan barta ta koma amma kafin nan kin shigewa Mr Nazzir.

Yadda babu wanda ba zai san kuna soyayya ba, karki sake ki bada damar da wata zata gane cewa kina jin haushin Noorh, dan haka ki shige mishi. Insha Allah akwai wata mata mari, tana hada magani na musamman, sabida irin su Mr Nazzir.

        ---
A hankali na zube a bakin gadon,  na fashe da kuka. Tare da dafe goshina..ina kuka ina karawa, sai da nayi ya ishe ni sannan na mike na cire kayana na shiga ban daki nayi wanka tare da alola na fito.

           Na saka dogon riga, tare da hijab nayi sallah. Sannan na kwanta a kan abin sallah. Ina sauke wasu kwalla masu shegen zafi. A hankali har barci ya dauke ni.
      ---
Lagos.
A duniya Allah ya halicci mutane da halayyar su daban daban, wasu zaka samu suna masifar son sanyi wasu kuma suna son zafi, haka wasu kuma suna matukar son ruwa. A cikin wannan dabi'ar Mr Hamoud Boualem ya gina Iyalin shi. Mutum ne mai matukar kaunar ruwa. 

        Shi yasa da ya tashi gina gidan shi ya gina a bakin tekun Lagos, a banana island. Inda ya saka ka je har kasar Kuwait aka zano mishi hoton wani dankarerren gida, me mugun kyau, inda ya sanyawa gidan sunan.
Narrabeen beach housa. Yayinda mutane kewa gidan lakabi da honey house, kasancewar gidan guda hudu ne a cikin unguwar.

   Gida na daya gidan Shi da iyalin shine, kafin rasuwar shi. Four bed room ne, sai kitchen guda biyu da falo uku.

    Hajiya Maryam itace matar shi, daga ita bai kara aure ba, ita daya ce tal. Hajiya Maryam tana da yara biyar namiji ɗaya sai mata uku.
Mahir shine babba, me shekara talatin da uku, sai Hadiya. Wacce take da shekara shirin da takwas. Tana aure a lekki. Sai Suhaila wacce take da shekaru ashirin da hudu, tana karatunta na karshe a Calgary.
    Sai Adeemah wacce shekarunta Ashirin da daya, tana karatun a jami'ar Abti Yola, sai yar Uwarta su Alishbah. Itace take secondry school, ss2.
        Mansion din cike yake da ma'aikata, wanda suke karkashin kulawar mahaifiyar Mahir, kasancewarta babbar  Judge na garin lagos.
Mace mai addini da Sanin ya kamata, sannan bafulatana ce gaba da bayanta, dan ko Hausar ta har yanzun bata ware ba. Gidan.
       Sai Mansion na gaba, gidan Barraq Abu Aswad, Mahaifin Mr Nazzir Abu Aswad. Kanin ne ga Hamoud Boualem, wanda suka kasance Uwa daya.

     Dan kimanin shekaru saba'in idan ka ganshi ba zaka ce ya kai haka ba, tare da matar shi Sahiba, yaran su uku.

          Nazzir shine babba, sai Nurul Sahar, sai kuma  Zoolfa. Suna da mugun ji da kansu, basu cika son mutane suna zuwa gurin Hajiya Maryam ba, toh ya zata yi ita na mutane ce, Hamoud Boualem asalin su yan kasar algeria ne. Wasu damuwa irinta zumunci yasanya Hamoud Boualem ya bar kasar shi ta Haihuwa,

   Ya dawo Naija da zama, lokacin da  yazo ne ya nemi inda zai fara kasuwanci sai ya zabi zaman yola, a can ya hadu da Hajiya Maryam, har suka yi aure.  Ana suka haifi mahir, sannan ya kafa kamfanin shi na soft drink, Sabida yana da asalin babban branch din shi a Kasar shi ta Haihuwa. Wato Algeria.

.... Bayan haihuwa Mahir suka tafi Algeria anan suka samu family house din su ya kuma tarwatsewa, sakamakon matsalar  cikin gidan su, a cikin mutanen da suka bar gidan har da dan uwantar su. Shima ya bar garin biskira. Haka ya dame shi sosai,. Da zai koma ne ya tafi garin bechar inda mahaifiyar shi take aure, ya daukota da kanin shi Barraq Abu Aswad. Mahaifiyar su mai suna.

   Hadiya, tazo ta zauna dasu lokacin Hajiya Maryam tana karatun ta akan lawyer. Haka suka ci-gaba da zama a Yola har matar Barraq ta haihu lokacin Mahir na da shekara biyu har yanzun suna tare da Hajiya Maryam.

       .... A hankali kome na family yake tafiya cikin tsarin Ubangiji, sabida Mr Hamoud Boualem yana bawa kowa damar yayi abinda yake so. Har Mahir da Nazzir suka girma, aka kai su makaranta mafi tsada da kyau wato king Abdul azeez Saudiya. Acan suka fara karatun su har suka kai matakin digiri.

         Anan ne kuma suka raba jaha, domin shi Mahir yana son aikin tsaro, yayinda Nazzir ya zabi kasuwanci. Mahir ya tafi College of militry USA. Inda ya samu degree din shi a fannin binciken sirri, sannan ya kuma sake samun degree na biyu, akan yaki da ta'addanci. Dan haka ya dawowa gida Najeriya hukumar sojojin ƙasar suka dauke shi a shashin sirri.
        
     Amma daga baya ya ajiye aikin bayan wani irin tashin hankali da akayi a ƙasar naija, wanda aka samu fada tsakanin bangarori biyu na ƙasar, yanzun haka ya ajiye aikin baya damuwa da kowa, sai kasuwancin shi da kamfanonin mahaifin shi musamman wadanda suke dakon mai dasu.

      Mahir yana da matukar kirki amma bai da mutunci kasancewar yayi aikin soja, abu kadan yake fusata shi, bai cika hayaniya ba, har yau Mahir yana da mafarkin akan wata mace da suka haɗu. Amma ya manta inda suka haɗu.

      Mutum ne da ya kasance miskili,. Bai da magana amma yasan kan mugunta, domin idan yana gari. Yana da Office a cikin gidan shi, akwai wani a cikin gidan mahaifiyar shi.

       Idan aka mishi abinda bai masa ba, zai iya hana kowani mai aiki  barci a ranar, ya saki kuyi ta aikin da babu. Idan yana barci ba a hayaniya a cikin gidan su ko gidan shi. Atleast dai bai son kwaraniya, shi yasa ya ajiye aikin militry, yace aikin militry bana mutane irin shi bane.

           ......
Sauran Mansion din kuwa, sun hada nashi dana Nazzir. Duk cikin gidajen gidan Mahir yafi na kowa haduwa da haska Mansion din sabida gidan sama ne da fuskar gidan yake kallon taku, sannan Bayan anyi building gidan, amadadin katanga wasu irin Glass me mugun kauri aka saka a jikin gidan Amadadin bango.

           Anyi tsarin gidan farin paint ne, yadda haka falon gidan guda hudu ne, kamar yadda dakunan gidan suka kasance huda uku.
        Falon shi na farko wanda yake sama kayan cikin kujerun falon ba wasu dayawa bane amma gray colour ne, sai dan gurin shakatawa, wanda daga falon kana hangowa, kuma kana hango tekun Lagos. Sannan shima falon yan me dauke da dinning table kujeru guda ukku

      Sai na biyu, shima multicolour ne, amma a kasa yake, sannan akwai littafai, tare da frame na wall, da dinning table, sai yan wasu drower masu shegen kyau na jikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login