Showing 18001 words to 21000 words out of 22403 words
Chapter 7 - SARAUNIYAR KYAU Takun Tsakiya FREE PAGE'S BY Nanah KD.txt
kuma aka yi rashin Nasara mutane suka shiga tsakani ko?."
"Yes of course haka fa nake nufi."
Jiddarh ta bata amsa. Nan dai suka ci gaba da shan fira ko wacce tana bada labarin abin dariya tamkar waɗanda suka yi one Year ko fiye da haka da haɗu wa, bacin sau biyu kawai suka taɓa haɗu wa.
Sai da Afeefah ta kammala waya da Jiddarh sannan ta kuma dan nawa Daddyn ta Mister Mai Kyau dake Jamus kira dan tayi kewar sa sosai.
"Assalamu Alaikum Daddy wato shi ne koka kirani ko?. Ae nayi fushi ma."😩
Afeefah tayi maganar cike da tsantsan shagwaɓa ga Daddyn nata.
Ƙayataccen Murmushi Mister Mai Kyau ya yi daga yadda yake zaune a hamshaƙe saman kujerar sa ta alfarma cikin haɗaɗɗen ofishin sa dake hawa na ƙarshe cikin katafaren company nasa dake can Germany (Jamus).
"Wa'alaiki Salam WarahamatuLlahi Wabarakatuhu. Kaina bisa wuya Shalele uzurori ne suka yiwa Daddyn ki yawa sosai, shiyasa ban samu na kiraki ba, sannan ae nayi tunanin Zaynerb ta dawo ne, kodai ba yau ne zata dawo daga Kano State ba?."
Wani irin bugu na tashin hankali kuma mara dalili zuciyar Afeefah tayi jin Daddy ya ambaci Zaynerb, ita fa wallahi shaf ta manta yau Zaynerb zata dawo Abuja, cikin sauri ta ciro wayar daga kunnenta ta duba Time 4:50pm hankali a tashe ta mayar da wayar kunnen ta tana faɗin.
"Subhanallah, Daddy Anty Zaynerb fa bata dawo ba, nifa gaba ɗaya na manta yau zata dawo, kuma tun jiya da muka yi waya da ita ta ce Yau zata dawo bamu ƙara waya ba fa, wayyo Daddy tsoro nakeji kar wani abu ya sama Anty Zaynerb na..."
Jin yadda Afeefah take maganar hankalin ta a mugun tashe ne.
Yasa Daddy saurin tarar ta da faɗin.
"Ki kwantar da hankalin ki wata ƙilama Zaynerb ɗin ta fasa dawowa Abuja yau ɗin ne fa, amma dai gudun zargi riƙe waya, barina tuntuɓi Uncle Sagir naku muji."
Da "Toh." Kawai Afeefah ta amsa masa amma bata tunanin zata iya kwantar da hankalin ta, bacin batasan halin da Zaynerb Yayarta take ciki ba.
Tsuru tsuru Lailah da Deejarh harma da Haleesat wacca tashin ta daga Bacci ke nan ta fito palon a gaɓar da Afeefah take faɗin Zaynerb bata dawo ba.
"Assalamu Alaikum Babban Yaya. Yau Harkokin Kasuwanci sun bari an tuna damu ke nan, tun da naga kira da Yamma nan."
Uncle Sagir ne duk yake waɗannan maganganun cike da farin ciki na ganin kiran da Ɗan uwan na sa ya yi masa.
"Sagir ba wawan ne a gabana yanzu ba, wai nace Zaynerb ta fasa dawowa Abuja ne, sai ta ƙara kwanaki ko kuwa, Afeefah ta kirani tana faɗin Zaynerb bata ƙari so ba har yanzu."
Cikin sauri Uncle Sagir ya katse Daddy da faɗin.
"Zaynerb kuma wata Zaynerb ke nan, wai dama ba tun jiya Zaynerb kuka ce ta koma Abuja ba?."
Ya yi tambayar yana kallon Mah'fuz dake zaune gefansa yana jin abin da ke faruwa.
"Zaynerb kuma Abhu anya kuwa, ae Zaynerb tun jiya tabar nan, ta ce zata koma Abuja, babu yadda bamu yi da ita ba, akan ta tsaya gari ya waye saboda a jiyan babu Flight, amma Zaynerb taƙi ji saboda taurin kai da Yammacin ta ɗauki Driver da mota suka nufa Abuja, gashi kuma har yanzu Drivern bai dawo ba..."
Duk wannan maganar Mah'eesha ce take zubosu a lokacin da ta ƙari sa shiga cikin palon mahaifin nasu sannan ta a je masa kayan maƙulashe da ta kawo masa saman center table.
"Inna-lilahi-wa-inna-illahir-raji'un, na shiga ukuna Daddy kanaji fa wai cewa suke Anty Zaynerb ɗita tun jiya ta kamo hanyar zuwa nan, gashi kuma har yanzu batazo ba, Daddy tsoro nakeji kar'a cutar min da Yayata Daddy please kayi wani abu kaji Daddy i'm begging you please Dad say something to me pleased......"
Ƙari sa maganar Afeefah tayi cikin tsananin kuka muryarta na fita da kyar kuma cikin wahalar fitar numfashi.
"Subhanallah Afeefah menene nakeji kike faɗa ne, wai kina nufin Zaynerb bata dawo ba, inna-lilahi-wa-inna-illahir-raji'un menene ke nan yake faruwa i'm so confusing fa."
Uncle Sagir ne yanzu ya yi maganar jin muryar Afeefah da kuma irin abin da take faɗa.
"Afeefah! Afeefah!! Kina jina kuwa, please kiyi magana mana?...."
"Na'am Daddy ina jinka domin ban mutu ba, tukunna amma muddun ba'a nemo min Ƴar uwata Zaynerb ba. Tabbas Daddy zan iya mutuwa a kowane irin lokaci...."
"Subhanallah Afeefah kina da hankali kuwa kin san menene kike faɗa, nace ki kwantar da hankalin ki Zaynerb ba ɓata tayi ba Insha Allah za'a ganta kinji Shalele ta!?...."
Tanaso tayi magana sai dai abin da ya tokare ta a maƙushi shi ne ya hanata yi magana.
Ji take a maqwoqwaronta tamkar ana jajjagen yaji a ciki duk yadda taso tayi magana abin cutura ya yi.
Zubewa tayi a ƙasa sumammiya yayin da bakinta yake fitar da wani irin kumfa tamkar wacca tasha poison.
Da gudun tsiya gaba ɗayan su tun daga Haleesat da Lailah har da Deejarh suka ƙari sa kanta suna kiran sunan ta cikin tsananin tashin hankali.
Sai dai ina Afeefah ba jinsu takeyi ba domin kuwa tashin hankalin da ta shiga ne yasa ciwon ta yake ƙoƙarin tashi.
*TASHIN HANKALI*
*WANDA BA'A SAKA MASA RANA*
Tofa fi ye da haka gaba ɗaya Ahalin Mai Kyau suka shiga domin kuwa Afeefah ciwo ya tashi kuma yazo da mugun gardama.
Yayin da ita kuma Zaynerb an tabbatar da saceta akayi. Sai dai a yadda labarin yaje musu bawai ita kaɗai kidnapper's ɗin suka sace ba harda wasu mutanen.
A Ranar da abin ya faru M.MK ya dawo ya biyo ta private jet. Nasa ya dawo ƙasa Nigeria cikin tsananin tashin hankali domin kuwa abin haɗe masa biyu ya yi ga ciwon Afeefah wanda baya jin magani ga kuma ɓatar da Zaynerb tayi. gaba ɗaya yabi ya fita hayyacin sa, danma wani abun Maleek ne yake yi da kansa musamman akan binciken nemo inda Zaynerb take.
Gaba ɗaya Ahalin sam basa cikin kwanciyar hankali na abin da yake faruwa, tsawon kwanaki uku ke nan da sace Zaynerb kuma babu ita babu labarin ta, sannan kidnapper's basu kira sun faɗa adadin kuɗaɗen da suke so a basu ba.
Wanda hakan yasa aka fara zargin da wuya idan saboda kuɗi suka yi Kidnapping nata.
Babu shiri gaba ɗaya Ahalin Uncle Yusuf suka tattaro suka dawo Abuja Gidan Mister Mai Kyau da zama har zuwa Ranar da kidnapper's ɗin zasu kira su faɗin Abin da suke so.
A 6angaren Momy Rafi'at kuwa za'a iya cewa tafi kowa shiga tsananin damuwa na sace Zaynerb da aka yi da kuma ciwon Afeefah.
Sai dai na ciki na ciki, Dan ita kaɗai tasan Gadar Zaren da take shiryawa
*WANNAN KE NAN*
*KAƊAN DAGA CIKIN IRIN HALIN DA AHALIN MAI KYAU SUKA SHIGA SAKAMAKON KIDNAPPING ZAYNERB DA AKAYI*
*ZAYNERB*😣
"Na kammala fa."
Tayi maganar tana kawar da idanunta da kallon sa, sai dai cikin rashin sa'a suka shiga cikin na Yarinyar da yake tare da ita kuma ta ambaci kanta da matar sa.
Rumtse idanun nata tayi ƙam tana nuna kalar baƙar wahalar da suka sha hannun waɗannan kidnapper's.
A lokacin da ɗaya daga cikin su ya sanar police sun sama labarin wurin suke, cikin gaggawa gaba ɗaya kidnapper's ɗin, suka tattara mutanen da suka yi Kidnapping, cikin wasu motoci tamkar awaki haka suke zuba mutane a motocin. Sannan suka bar wurin dasu, tsawon kwanaki biyu suna tafiya dasu suna shiga dasu cikin tantagaryar daji, sannan bayan shafe kwanaki biyu da sa'o'i suka ƙari so da su wani ƙurman gida ƙaton gaske cikin dajin.
Sosai mutum zai yi mamakin ganin irin wannan gida a daji.
Cikin gidan suka shishshiga dasu Zaynerb kamar wasu awakai, sannan ne aka fara neman wanda zai cire wa Aasief harsashin dake ƙafarsa, da muka wata Budurwa ita ma da alama tayi musu taurin kai ne, suka harbeta a kafaɗa.
A lokacin cike da Qwarin gwiwa Zaynerb ta ce dasu ita likita ce saboda haka zata iya kula da masu raunuka.
Ba tare da ɓata lokaci ba suka ware ma ta wani ɗaki a cikin gidan sannan suka kai ma ta kayan aikin da zata buƙata.
Nan ne fa da shigarsu ta fara ƙoƙarin cire masa harsashin.
Ta sha wahala sosai sannan da kyar ta samu ta cire tana haɗa uban haɗa gumi sannan take cewa da shi ta kammala.
A hankali ya janye ƙafar tasa yana rumshe idanu saboda azaba.
"Karka damu na haɗa maka da Allurar kashe zafi, zuwa anjima zaka nema zafin ka rasa."
Zaynerb tayi maganar ba tare da ta kallesa ba, bayan ta buɗe idanunta sannan ta ƙari sa wurin ɗayar Budurwar da aka harba a kafaɗa.
Cikin taimakon Allah Zaynerb ta samu tayi ma ta treatment da ya kamata, sannan ta kalleta tana ƙare wa irin shigar dake jikin Budurwar kallo, ta tambaye ta
"What is your name?."
Tayi ma ta maganar da turanci ne dan ta fahimci da wuya idan tanajin Hausa
"Samiupter D'Souza..."
Budurwar ta bata amsa.
"Daga wata ƙasa kike, kuma menene ya kawoki nan ƙasar, sannan garin ya ya waɗannan mutanen suka yi Kidnapping naki?."
Zaynerb ta jero ma ta tambayar kamar wata ƴar jarida idanunta akan Budurwar da ta kira kanta da ' Samiupter '.
"Ƙasar Indiya nake yanki kudanci, nazo Birthday Party na ƙawata ce, a hanyar mu na zuwa Abuja daga Kano waɗannan mutanen suka yi garkuwa damu, kuma sun kashe Ansha, dama tare da ita nake. Ta ce zata rakani Abuja saboda ban san kowa anan ƙasar ba."😭
Cikin kuka Samiupter ta ƙari sa bawa Zaynerb labarin muryarta har dashewa tayi saboda tsananin tashin hankali da wani irin hali da take ciki.
Rungumo ta Zaynerb tayi tana lallashi cike da tausayin ta.
Yayin da shi kuwa Aasief ido ya zubawa Zaynerb ɗin yana kallon ta.
Neelarh kuwa tuni baccin wahala ya yi gaba da ita tana daga gefen sa ta jingina da kafaɗarsa.
"Zaynerb kin canza sosai kamar bake ba, kuma ban san dalili ba, kece kika yimin laifi, amma ni kika ɗaura wa laifin..."
A hankali Zaynerb ta juya ta kallesa jin irin maganar rainin wayo da yake son kawo ma ta, ranta a ɓace ta basa amsa da faɗin.
"Aasief kaine ka canja ba kamar yadda na sanka ba, ka canja daga Aasief mutumin kirki dana sanka, gaba ɗaya halayyar ka basu yi ba, ban taɓa tunanin ka da irin halin da na tsinceka ciki ba a wancan lokacin, ka rasa wacce zakayi Alaƙa da ita sai wannan Arniyar Erisha haba wallahi ka bani mamaki ba kaɗan ba."
Zuwa lokacin kansa ya fara ɗaurewa da kalaman Zaynerb, sam bai fahimci abin da take nufi ba kwata kwata.
"Kiyimin bayani yadda zan fahimta, nifa cikin ruɗani kawai maganganun ki suke jefa ni, dan ban san inda suka dosa ba sam."
Wannan karon kallon sa tayi da kyau idanunta na cika tab da kwalla take faɗin.
"Haba mana Aasief ya kakeso ka mayar dani shashasha ce, ko an gaya maka wancan Ranar da kace na sameka Gidan ka banga komai bane?."
"Me kike nufi ne Zaynerb, wacce Ranar kuma?."
"Kaji ko ƙara raina min wayyo kakeyi fa, wancan Ranar mana da dare da saƙon ka ya shiga wayata kana faɗin nazo Estate naku gidan ka, ko kuwa dai ka manta Ranar?...."
Dafe kansa dake mugun sara masa Aasief ya yi wani tunani tana ɗar suwa a Ransa, cikin sauri ya kalleta don ya ƙara tabbatar da tunanin sa, yake tambayarta da faɗin.
"Ina jinki a Ranar menene ya faru da ki ka zo Estate bayan kin ƙari so Room nawa, menene ya faru, please Zaynerb Tell me anything everything, please ki faɗa min duka abin ya faru da kuma wanda kika gani?."
Cikin tsorata da irin yanayin da ya fara shiga, idanun sa sun yi jajur na ɓacin rai Yayin gaba ɗaya jijiyoyin kansa suka tatashi, kai kana ganin sa kasan ransa ya yi matuƙar ɓaci.
Bai damu da kalar raɗaɗi da kuma jinin da ƙafarsa da aka harba take fitarwa ba, ya miƙe tsaye ya ƙari sa wurin ta.
Jijjiga ta yake yana roƙon ta akan ta faɗa masa abin da ya faru a lokacin, ihu da kuma maganar da yake ma ta da ƙarfi yana jijjiga kafaɗunta ne, yasa Neelarh da Samiupter suka farka daga ɗan baccin da ya fara ɗaukar su a firgice suna zazzare ido cike da tashin hankali.
Wani irin ban ko ƙofar akayi Sannan wannan ƙaton Gardin wato Gaddafi ya shigo ɗakin cikin ƙatuwar muryarsa kuma cike da bala'i yake faɗin.
"Wani mara rabon ne, yake mana ihu anan wurin, da alama ya gaji da rayuwar sa ne..."
Ya yi maganar ne yana ƙari sawa wurin da Aasief yake a durƙushe bai dena jijjiga Zaynerb yana faɗin ta faɗa masa gaskiya ba.
Cike da tsantsan mugunta ƙaton Gardin yakai hannu ya finciko Aasief ya miƙar da shi tsaye sannan ya saita bakin bindigan hannunsa a ta bayan Aasief ɗin yana ƙoƙarin juyo da shi.
Cikin Wata kalar da fusata da zafin nama Aasief ya juya gaba ɗayansa sannan ya dunƙule hannayen sa yakai ma masa wani wawan naushi a ido.
Zubewa Gaddafi ya yi ƙasa cike da azaba idanun sa na fitar da jini.
Bin sa ƙasan Aasief ya yi Dan bala'i, yana kai masa naushi a fuska ta wurin da ya tabbatar yana masa rauni, cikin wata kalar murya kakkausa yake faɗin.
"Dan uban ka ina tambayarta abin da ya faru shekaru biyar baya, shi ne zaka shigo tsakani da wannan jahilar Muryar taka, wato dama bakasan haushin ka nake ji ba, kaine ka harbeni ko zakaci uban ka yau."
Maganar Aasief yake yana kuma kai masa naushi a ta ko'ina na fuskar sa, Aasief bai dena dukan Gaddafi ba har sai da yaga ya daina motsi alamar ya suma...
Sannan ya dakata sannan cikin fitar da huci na mugun ɓacin rai ya juya kamar wani kububuwa yana kallon Zaynerb wacce ganin abin da yake yi, yasa idan banda rawa babu abin da gaba ɗaya ilahirin jikinta yake yi, tun kafin yace da ita komai ta fara masa bayani.
Cikin lokaci ƙanƙani Zaynerb ta koroma Aasief gaba ɗaya bayanin abin da ya faru lokacin da taje Room nasa, ta faɗa masa irin tashin hankalin da ta shiga da kuma irin maganar da Erisha ta faɗa ma ta.
*Aasief*
Wani wawan naushi ya kai ma bangon ɗakin wanda har sai da gaba ɗaya ɗakin ya amsa.
Idan banda huci babu abin da Aasief yake yi tunda yake a Duniya ransa bai taɓa ɓaci ba irin na yau.
Wai ashe duk waɗannan shekarun da aka kwashe idan Zaynerb zata tuna sa, tuna sa take yi a matsayin Mazinaci mayaudari....
Inna-lilahi-wa-inna-illahir-raji'un
Zubewa ya yi a ƙasan idanun sa na fitar da ruwa.
Miƙe wa ya yi a fusace ya fara zagaye ɗakin faɗi kawai yake.
"Saina kashe Leo, Tabbas da hannuna zan kashe Leo da wancan kafirar Erisha ko tabbas sai nayi musu KISAN GILLA."
Tabbas indai lissafin sa ya tafi dai dai yadda tunanin sa ya basa ke nan dai Leo da Erisha su ne suka shirya komai na abin da ya faru tsakanin sa da Zaynerb...
"A wancan Ranar ba Ni ne na turo Miki da wannan saƙon ba, domin kuwa sace wayata akayi a Ranar, nasha wahala sosai wurin neman ta amma ban gani ba, haka na haƙura na nufi hanyar komawa gida cikin motata a hanyar ne na haɗu da Accident, ban farka ba sai washe gari na ganni a Room na ga Leo a gefe na, yana faɗa min wai a Hanyar sa na komawa gida ne, ya ganni nayi Accident shi ne kawoni gida..."
Shiru Zaynerb tayi tana sauraren abin da yake faɗa ma ta kuma yana ma ta maganar bada kakkaurar murya ba, cikin murya ma dai dai ciya yake ma ta bayanin.
"Dama Leo yasan Estate naka ne?."
Zaynerb ta tambaya har lokacin jikinta bai bar rawa ba, ga kuma siraran hawaye da suke bin fuskarta.
"No bai sani ba, kuma a lokacin ban tambaye sa ta ya akai ya sani ba."
Da bata amsar, miƙe wa ya yi tsaye yana gogen jinin dake fita a ƙafarsa.
"Ku taho muje..."
"Ina ke nan?."
Zaynerb ta tambaya tana kallon sa cikin faɗuwar gaba.
"Barin nan zamuyi, ada banyi niyyar guduwa ba, amma wannan labarin da kika bani yasa na yanke shawarar mu gudu saboda banaso Leo yakai Yammacin yau bai mutu ba."
Zaro ido Zaynerb tayi cikin tashin hankali bakin ta na rawa take faɗin
"Mu-mummtuwa fa kake faɗa....."
*ABUJA*
*Haleesat*
Baya tayi ta jingina kanta da kujerar motar ta, idanunta akan Babban Ofishin bincike reshen manyan laifuka dake Abuja. C.I.D.
Sosai ta shiga matsanancin tashin hankali da kuma damuwa na sace Zaynerb da kuma rashin lafiyar Afeefah.
Wanda sanadin haka ne koda University bata samu taje, cikin haka ne wata ƙawarta ta bata shawarar zuwa ofishin c.i.d. domin basu report duk da cewa shima Daddy yana iyakar bakin ƙoƙarin sa haka ma Maleek.
Ranar ta fito daga bathroom ta duba wayarta nan ne taga message da Maryam ta turo ma ta, cikin hanzari ta buɗe ta fara karantawa.
"Sunan sa Suhais Sulaiman Interval, just 'Interval' aka fi sanin sa da shi.
Rank Officer.
Batch Number T3,783 :: D8... Specialization.
Shekarun sa Twenty something.....
D.O.B......
Iya kar abin da na sani akan sa na faɗa miki, kije wurin sa Insha Allah zai taimaka da nasa binciken domin shi ɗin qwararren Jami'i ne wanda yasan makamar aikin sa, sannan bayada wata matsala."
Ajiyar zuciya Haleesat ta sauke a lokacin bayan gama karanta saƙon.
Nan ba tare da ɓata lokaci ba tana gama shiryawa ta ɗauki mota ta tuƙa har zuwa Babban Ofishin.
Koda isarta ofishin ta nema a haɗa ta da shi.
Da farko Jami'in ƙi ya yi, amma tana faɗa masa Wanene mahaifinta a ƙasar, cikin rawar jiki ba tare ɓata lokaci ba, shi da kansa Jami'in ya kaita har gaban Yallaɓan Officer Interval, sai dai kuma menene zai faru bayan ganin sa da Haleesat tayi?.....
*What Next*
_______💓💓💓
The Nainarh Kd
💓💓💓_________
Sam Haleesat ta kasa nutsuwa tayi masa bayani yadda ya kamata a lokacin, sakamakon ganin wannan jami'in ba kowa bane fa ce, Mutumin da ta haɗu da shi a Mashaya, kuma tayi Drawing face nasa As masoyinta sannan kuma take ƙaunar sa har tayi masa laƙani da Souvenir....
Doguwar ajiyar zuciya taja bayan ta kawo nan da tunanin nata sannan ta saka hannu ta buɗe motar ta fito.
Kai tsaye office nasa ta nufa domin kuwa shi da kansa yace ta dawo yau akan binciken nasu.
Sallama ɗauke a bakinta ta shiga cikin haɗaɗɗen ofishin.
Amsa wa ya yi ƙasa ƙasa idanun sa akan Laptop dake gaban sa, ba tare da ya kalle ta ba.
Zama tayi ƙoƙarin yi a kujerar dake fuskantar sa, sai dai jin muryar sa da tayi ne yana magana, yasa ta miƙewa tsaye da sauri tana sakin Murmushi domin