Showing 15001 words to 18000 words out of 24136 words
Chapter 6 - YAR BAUTAR KASA COMPELET DOCUMENT BOOK.txt
gudu kabarni bacin kasan banajin daɗin rayuwa idan baka?"
"dalla yimim shuru se zuba yake kamar famfon daya lalace,niba wannan ce tasa nakiraka ba,tambayarka zanyi,yanzu ka amince kanason salma ko baka aminceba?"
Shuru najeeb yayi kanshi na mishi zafi zuwacan de yadaure yace.
"Don Allah barrister kada kabari salma tashiga tsakanina dakai,dan wlh azahirin gaskiya ni bana son salma bantaɓa sonta ba kuma bazan taɓa ba har abada,nide kawai nasan ina jin tausayinta"doctor yaƙarasa maganar yana kuka.
kabeer bece masa komaiba yakashe wayarshi,koda najeeb yaji yakashe wayar wani kukan ne yasake ƙwace masa.
Haka rayuwa taci gaba da tafiya,najib cikin tashin hankali,salma cikin tsana da tsangwama ta mutanan gari.
gaba ɗayansu sunyi baƙi sun lalace,bama kamar najeeb wanda gaba ɗaya yazama tamkar mahaukaci kuma ya rasa meke damunsa,ba irin gwajin cututtukan da beyiwa kanshiba amman results ɗaya yake samu,zuciyar shi nason wani abu.
Amatsayinshi na likita yasan matsalace babba to amman yarasa gano abinda zuciyar tashi takeso bare yabata.
Kabeer ne zaune agaban mahaifin salma suna tattaunawa,da ganin yanayinsu kasan sunɗan jima da fahimtar juna.
(abinda me karatu be saniba shine,kabeer tsawon wata guda kabeer ya kwashe yana zuwa gurin mahaifin salma yana bashi haƙuri,)
murmushi mahaifin salma yayi sannan yace.
"kabeeru kenan,to ay ko wani kazo nemawa auran salma zan bashi bare kuma kai da kanka,dan haka ka kwantar da hankalinka,inde kashirya kaje kasanar da magabatanka,azo ayi maganar,amman katabbatar kafaɗa musu komai game da salma".
godiya kabeer yayi sosai,daganan kai tsaye katsina yawuce gurin iyayensa,yamusu bayanin komai be ɓoye musu ba.
Dayake mahaifinshi malami ne me tsoron Allah,be ƙi ba.
Sati guda tsakani iyayan kabeer sukazo aka tsaida maganar,suka biya sadakin salma,
Bayan tafiyarsu mahaifinta shima yaje yayi bincike akatsinan yatabbatar da mutanen kirki ne
Wata guda tsakani,jamaa suka taru domin shaida ɗaurin auran salma da kabeer,
yan unguwar se gulma sukeyi,sabida suna ganin shima auran fasawa zaayi,sede ga mamakinsu anɗaura aure lafiya antashi bawani tashin hankali,ataƙaice ma har dangin angon sun koma gida.
Anata ɓangaren,salma kuwa,ta ɗauki auranta da kabeer da matuƙar muhimmanci ko kaɗan bata ƙin auran,sabida ko ba komai yacireta daga ƙuncin datake ciki.
Haka aka cigaba da shagalin biki kowa se murna yake,karfe huɗu aka kawo motar ɗaukar kaya,akaje aka shirya gidan amarya a unguwar malali GRA dake kaduna sabida kabeer dama kaduna yadawo da aykinshi,yayin da gidan uwargidanshi kuma yake a gomna road.
Yasha fama da Aisha matarshi kamin ta Amince ya auri salma.dan cewa tayi sede yasaketa.
Gidan amarya ba laifi yayi kyau sosai,daidai namasu ƙaramin ƙarfi,duk da cewa gidan namasu babban ƙarfine amman iyayenta sunyi ƙoƙarin tsara gidan da abinda Allah ya hore musu.
ƙarfe takwas nadare,motocin ɗaukar,amarya suka iso,inda aka ɗauki amarya tana ta kuka zuwa gidan mijinta kabeer.
ikon Allah.
surbajo for life.
*🙆🏻Y'AR BAUTAR K'ASA*
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*22*
Haka ƴan kai amarya suka watse suka barota tana ta kuka.
Misalin sha ɗaya na dare ango yashigo ɗakin shi kaɗai,hannunshi ɗauke ɗa ledar kaji.
Sallamah yayi yashiga,bakin gadon yaje yazauna,yayi shuru,ita kuma se kukan ta takeyi.
Zuwa can de yadaure ya matsa kusa da ita,mayafin kanta yacire yajawota jikinshi yafara rarrashinta,da kyar yasamu tayi shuru,
Dakanshi yaɗauko plate yazuba kajin yadunga bata abaki har ta ƙoshi,daga haka brush sukayo da alwala sukayi sallah sannan suka kwanta.
Jawota jikinshi kabeer yayi yarungume sukayi bacci.
Haka rayuwa taci gaba da tafiya,kabeer kullum cikin nuna ma salma soyayya yake ba abin data nema tarasa,itama sosai take nuna masa kulawa,
Tuni yase mata mota yasiyawa iyayenta gidan dasuke ciki yasa aka gyara masu gidan sosai,
Rayuwa tayiwa salma daɗi sede abu ɗaya ne yake hanata jin daɗin giɗan mijin,shine rashin kusantarta da kabeer bayayi,ita kuma macece me ƙarfin shaawa,amman haka ta haƙura dan ko maganar bayaso tamishi,se ya ɓata rai yace mata shi badan haka ya aure taba,ganin ranshi na ɓaci Ne yasa tadena yimasa magana ta koma faɗawa Allah damuwar ta.
Tuni salma tamance da wani najeeb arayuwarta.
Anashi ɓangaren najeeb yakoma kamar mahaukaci ko aski bayayi gashi duk yacika masa fuska bashida natsuwa duk a firgice yake.
Yanzu sauƙinta ɗaya suna waya da kabeer harma yabashi address din gidan shi dake kaduna.
Yaude Abujar tayiwa najeeb zafi dan haka shiryawa yayi yanufi Kaduna gurin Kabeer ko zeji daɗi.
Koda ya iso kaduna,se yacintsi kanshi dazuwa gidan su salma,koda ya isa yaci saa babanta yananan,dan haka gurinshi yanufa duk da sauyar gidan tabashi mamaki.
baban salma be gane najeeb ba seda najeeb ya gabatar da kanshi.
Da sauri yajawo shi jikinshi yarungumeshi yana faɗin.
"najeebullahi najima inason ganinka amman Allah be nufa ba se yanzu,kayi ciwone naga ka lalace haka?"
Kuka najeeb ya rushe dashi yana ƙara rungume baban yana neman gafarar shi abisa rashin kunyar daya masa.
Dariya baban yayi sannan yace.
"najeebullahi,bakamin laifiba,ko fushin danayi dakai rainane ya ɓaci ba komai ba,amman yan zu bana tare da ɓacin ran komai,nayafe maka tun tuni"
har cikin gida yashigar dashi gurin mahaifiyar salma dakyar ta amince tayafe mishi,haka shima sahabi dakyar ya amince,daganan ne najeeb ya buƙaci ganin salma,itama yabata haƙuri,cikin faraa mahaifinta yace.
"wai ay salma shekararta guda kenan agidan mijinta,ay tayi aure"
Jirine yafara ɗaukar najeeb kamin wani lokacin yazube ƙasa sumamme,a gigice suka ɗebo ruwa suka shiga yayyafa masa,be jimaba ya farko yana wani gunjin kuka ,ƙafar mahaifinta yariƙe yana kuka yace.
"baba meyasa ka aurar da salma? meyasa baba?"
tambayar sosai tabashi mamaki,amman se yace,
"sabida ta isa aure shiyasa na aurar da ita,danko calender ce ita watarana zan gaji da kallonta nayaga kona ƙona"
Najeeb kasa magana yayi,cikin fushi yamike yafice daga gidan suna kiranshi amman ko waigowa beyiba yaje yashige motarshi yatada daita yabar anguwar.
yana tafe yakira kabeer yace mishi gashinan zuwa gidan shi.
Sosai kabeer ya firgita da zuwan na najeeb,kamin yayi wani yunƙuri najeeb ya iso gidan.
jin nucking yasa kabeer daurewa yaje ya buɗe masa ƙofar,yana buɗewa najeeb yarungume kabeer ya rushe da kuka dakyar kabeer yajashi zuwa cikin falon suka zauna,cikin kuka najeeb ke faɗin.
"kabeer iyayen salma sun cuceni,sun aurawa wani salmata,kabeer ina zan saka rayuwata,?"yaƙarasa maganar cikin matsanancin kuka.
a daidai lokacin salma tashigo falon sabida tajiyo sautin kuka daga ɗakinta,sanye take cikin riga da wando three quater tayi kyau sosai,har ta shigo falon basu saniba.
Najeeb ne yafara ɗsgo kanshi arazane sabida yajiyo ƙamshin salma,koda ya waigo ido cikin ido sukayi shida ita,azabure ya miƙe ya nufeta tana ja da baya da sauri kabeer yace.
"kada ka kuskura kayi gangancin taɓamin mata"ya faɗi sanda ya ƙarasa ya rungumo salma jikinshi,ita kuma se wani ƙara shigewa jikinshi takeyi.
*Tassssssssssss*
Najeeb yaɗauke kabeer dawani gigitaccen mari,sannan yaje yacukumi kwalarsa,yace.
"kada ka kuskura kasake maimaita wannan kalar wasan agabana,nakiran salma matarka"
Tassssssssss.
yaji shima an ɗaukeshi da mari,koda ya waiga salmace sannan tace cikin ɓacin rai.
"wannan ne ganganci mafi muni dazaka kumayi agabana na marin mijina,kai waye dazaka shigo har gidanmu kana cimana mutunci?"
Tsananin mamaki najeeb yakasa magana bakinshi rawa yake kamat mazari,da kyar yace.
"kina nufin kabeer shine wanda kika aura?"
"kana mamakine?"kabeer yabashi amsa.
"kabeer kagama dani duniya da lahira,bani da wani abu dazan iya yimaka,kayimin abinda ko maƙiyina baze yimin ba,duk wani abu dazanyi maka baze gogemin duhun dakasa azuciyata ba"
Be jira abinda zasuce ba yafice da gudu ya faɗa motarshi,da gudu kabeer yabi bayanshi dan yasan komai ze iya faruwa inyabarshi yatafi,sedr kamin ya iso najeeb yafice da mahaukacin gudu,daga gidan,
Da gudu kabeer ya koma cikin gidan ya ɗauko key din motarshi shima yatada yabi bayanshi,
Gudu suke sosai yayinda najeeb ko gabanshi ba sosai yake ganiba,a haka har suka iso gadar Abuja junction,wanda najeeb yajima da sumewa a motar dan haka,kabeer se gani yayi sunyi taho mu kara da tirela,wanda hakan yajanyo motar najeeb ta faɗa ƙasan gadar wacce ƙasanta titine,wata tirelar ce tayi tafiyar yaji da motar ta wancakalar da ita gefen titi.
Ihu kabeer yakeyi,iya ƙarfinsa,yafito daga motarshi,da gudu ,jamaa suka riƙeshi dan kan titi yahau be saniba.
Da ƙyar aka ciro najeeb acikin motar,wanda dagani base an faɗiba babu alamun rai atattare da[truncated by WhatsApp]
*👩🏻💼YAR BAUTAR KASA*
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*23*
Emergency aka tafi da gawar najeeb,wacce ke ta faman zubar da jini.
Kabeer ko ihu yakeyi gaba ɗaya yafice daga hayyacinshi,
Likitoci ne akan gawar najeeb suna bincike,cikin ikon Allah sesukaji jijiyar bayan kunnenshi na bugawa.
Da sauri suka jawo kayan ayki suka shiga ceton ranshi,inda cikin nasara bugawar zuciyarshi yadawo,amman da sauri da sauri,alamar dake nuna zuciyar bata da lafiya.
Tsawin awanni uku numfashin shi yaƙi daidaita,duk wani abu da suke tunanin yimishi sunyi amman abun yaci tura.
Gwaje gwaje suka shiga yimasa,anan suka fahimci akwai abinda yakeso be samuba,dan haka da sauri suka nufi kabeer,wanda ke birgima akasa kamar yaro,suna zuwa ɗaya daga cikinsu yace masa.
"we dont have enough time,only one hours remain for your patient,based on our investigation,we find out that there was something he needed on this earth urgently,and he couldn't obtaind it,but if you know the actual thing he needed,you are free to bring it right now,Becouse that is the only solution to save his life"
Tunda likitan yafara magana kabeer yake gyaɗa kai kamar ƙadangaren,yana gama saurarar su yajuya da wani mahaukacin gudu,ya faɗa motar shi,ko murfin be jira yarufe ba ya finciketa da mahaukacin gudu se a hanya ya rufe murfin.
Cikin minti goma ya iso gidan shi,koda yafita be jira yarufe motarba,ya ruga da gudu zuwa cikin gidan.
A falo yasami salma se kuka take yi fuskarta tayi jazir,yana shiga tamiƙe da sauri tace.
"ya kashe kanshi ko?,don Allah kasanar dani a halin dayake ciki jikina yana bani wani mummunan abu yasami doctor"taƙarasa maganar tana kuka me nuna zuciyarta nacike da fargaba.
Jawota yayi da ƙarfi yana shirin ficewa da ita waje,da sauri ta ƙwace takoma gefe tace.
"ina kakeso ka kaini?"
Hawaye ke zuba a idon kabeer kamar ruwa yace.
"salma gurin najeeb zan kaiki"
"a matsayinsa nawa agurina dazaka kaini gurinshi"
"salma najeeb yana sonki,kuma kema kina sonshi don Allah ki taimakeni kar na rasa najeeb,in wani abu yasameshi bazan yafewa kaina ba"kabeer ya faɗi yana kuka.
"tun wuri ka gyara maganarka ni ba son najeeb nakeba tausayins kawai nakeji,ni mahaukaciyar inace zanso mutumin da besan mutuncin iyayena ba?"
"ƙaryane salma,wlh kinason najeeb,kullum dasonshi kike kwana kike tashi,najeeb yana cikin halin buƙatarki akusa dashi,kitaimakemu"
"kabeer na fahimci bakasan darajar auren dake kainaba,shiyasa kakemin zancen wani ƙato"
"salma nifa na aurekine dan najeeb, ina tsoron wani ya aureki,lokacin da najeeb ya waiwayeki kuma yarasa ki,shiyasa namasa adashin gata dake wanda yaune ranar daze kwasa,salma komai namiki namikine dan son da najeeb yake miki,inde akan aurena dakene yasa kikace bazakije gurinshi ba,salma nasakeki saki uku "kabeer ya furta yana kuka.
Arazane salma take kallonshi bakinta na rawa tace.
"what do you mean Kabeer,ashe duk soyayyar daka nunamin ƙaryace?kayine dan abokinka,kabeer banmaka laifin komaiba kasakeni,saki irin na wulaƙanci me naimaka kaida abokinka dakukeso kuga kun jefa rayuwata cikin ƙunci?"
"salma akan najeeb zan iya yin komai,ina nufin komai"ya faɗi cikin ɗaga murya.
hannunta yaja tasake kwacewa tana kuka.
Cikin tsawa kabeer yace.
"Salma fitar najeeb dazu daga gidan nan,sunyi karo da tirela,inda ta wurgoshi shida motarshi ƙasan gadar Abuja junction,inda wata tirelar tasakeyin tafiyar yaji dashi da motar tashi,ankaishi asibitin garden city,likitoci sunyi iyayinsu,najeeb yayi numfashi amman yaƙi yi,salma likitocin sun shaidamin awa ɗayace taragewa najeeb a duniya matuƙar baakai masa abinda yakeso kusa dashiba,ze mutu,kece wacce najeeb yakeso batare dayasan yana yi ba,saura minti goma shabiyar yarage najeeb yabar duniya,nasan zakiyi alfahari da cewa najeeb yaceto rayuwarki daga gidan yari,shi kuma kinyi sanadin turashi lahira"ya ƙarasa maganar yana kuka.
Da wani mahaukacin gudu salma tafice daga falon,binta yayi abaya,motar dayazo acikinta taje tashige,ƙafa ba takalmi,kai ba ɗankwali,sanye da wando three quater da riga armless.
kamin kabeer ya ƙaraso taja motar tafice daga gidan da mahaukacin gudu.
Ta nufi Asibitin garden city dake kaduna,inda aka kwantar da najeeb.
Koda kabeer ya iso yaga tafice wata motar yaje yashiga shima ya fice da gudu,sede shi ba Asibitin yanufa ba gidan iyayen salma yanufa.
Tofa🙆🏻
muje zuwa,akwai bidiri.
surbajo for life.
.*👩🏻💼Y'AR BAUTAR K'ASA*
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*duk meson ayi adding wata number agroup pls yaba wata admin din baniba,ni sim card dina yacika da numbers,masu bina naturo yar bautar ƙasa ta pc kuyi haƙuri ku tambaya a group bana turawa ta pc,ku kuma masu shi don Allah in antambaya kubayar ni uzuri yamin yawa,pls*
*24*
Tana isa asibitin,tayi parking,bata tsaya kulle motar ba ta ruga da gudu zuwa cikin asibitin kamar mahaukaciya,dama gata akwai gashi.
Wata nurse ta tare tana tambayarta najeeb,ayko ba musu takaita ƙofar ɗakin dayake ciki.
Tura ƙofar tayi da gudu tashige cikin ɗakin,da sauri likitocin suka waigo suna kallonta,itako ko kallonsu batayi.
Ƙarasawa tayi jikin gadon najeeb ɗin tana kallon yadda aka naɗe jikinshi da bendeji sabida raunukan dayaji,ga karaya da yayi a ƙafarsa,duk wanda yaga najeeb awannan yanayin se ya tausaya masa bare salma masoyiyarsa,
Kuka take kamar wata zararriya,hannunshi ta kamo tana kiran sunan shi cikin kuka,amman shuru bemasan tanayiba.
Naurar jikinshi ce tafara ƙara alamar lokacin da aka ɗiba yayi,gaba ɗaya likitocin sun rude,
Faɗi suke,"we lost him"
A gigice salma take kallonsu,dubanta takai fuskar najeeb,da sauri takifa fuskarta akan fuskarshi,ta haɗa bakinta danashi tashiga hura mishi iskar bakinta daƙe shiga cikin huhunshi.
Yitake iya ƙarfina tana gunjin kuka.
Tarin da najeeb yafarayine ya maido da hankalin salma dana likitocin,da sauri suka janye salma suka samasa oxygen a bakin.
Da kyar yake zuƙar numfashin,salma se kuka takeyi gwanin ban tausayi,likitocin se alokacin suka fahimci ciwon so ne yskama najeeb me tsanani.
shiko kabeer yana isa gidan su salma shima ko ƙofa be rufeba ya ruga kofar gidan inda babanta ke zaune shida wasu dattawa suna hira.
Da gudu kabeer yazube agabanshi yana haki yana kuka yace.
"Baba don Allah karka tambayeni dalili,nasaki salma saki uku,batare dana ɗora mata iddah ba,a iya zamana da ita,najeeb yasamu labarin ni salma take aure,yabar gidana afusace sanadin hakan yayi taho mu kara da tireloli har guda biyu,yanzu haka yana asibiti,cikin halin mutuwa ko rayuwa,baba in har ka amince masoyine ze ita ceto masoyinsa daga gidan yari,baba ka aurawa najeeb salma,idan har ka amince da natsuwa da tarbiyyar najeeb baba ka aura masa salma,in babu salma arayuwar najeeb baba mutuwa zeyi,katausayamin nida aminina ka aura auren salma da najeeb yanzu"kabeer ya fadi cikin kuka.
"Jamaa salati goma ga Annabi"cewar baban salma.
"S,A,W"Sauran mutanen suka amsa,
Hannu yasa a aljihunsa yaciro kudi dubu biyar yamiƙawa kabeer,kabeer hannu na rawa ya karɓa,
"ni malam hadi ina nemawa ɗana najeeb auren salma agurinka"
Bakin kabeer har rawa yake yace.
"Ni kabeer naba ɗanka najeeb auran salma abisa sharudda kamar haka"
Nan aka lissafo hakkonkin aure,baban salma yace.
"na amsa masa"
kamin wani lokaci me tsayi angama ɗaurin auren najeeb da salma,kabeer rasa bakin godiya yayi da gudu yamiƙe yanufi motarshi da sauri baban salma da sahabi suka bishi yaja suka nufi asibitin.
Koda suka shiga ɗakin salma ce zaune kan kujera ta kifa kanta akan goshin najeeb hannunta riƙe da hannunshi,gashin kanta ya zubo yarufe fuskokin nasu,
Kabeer ganinsu ahaka seji yayi wasu hawaye na farinciki sun kama shi,yau yayiwa najeeb abinda ze godemasa,yayiwa najeeb abinda har ya mutu baze manta dashiba,yayiwa najeeb abinda ze dauwama cikin farin ciki,wato aura masa salma.
Har suka shigo salma batasan sun shigoba hankalinta nakan najeeb,tana tunanin yaushene ze farka.
Mahaifin salma da sahabi seda suka koka ganin halin da najeeb yake ciki adalilin salma.
jansu waje kabeer yayi,suka zauna,wayarshi ya dauko yakoma gefe yakira mahaifin najeeb.
Bayan sungaisa,kabeer yakwashe komai yasanar da mahaifin najeeb ɗin tun farkon haɗuwar najeeb da salma har zuwa yanzu da aka ɗaura musu aure.
sosai hankalin mahaifinshi yatashi,anyi saa yana ƙasar,dan haka yashaidawa kabeer nan da awa biyu ze iso.
Suna nan zaune jugum jugum,har awa biyun ta cika,mahaifin najeeb ne yashigo Asibitin da gudunshi.
Da sauri kabeer yatarbeshi,yakaishi ɗakin da najeeb ɗin yake,sede har lokacin gashin salma yarufe fuskar najeeb baa gani yayin da itama tata baa gani,
Kabeer ne ya ƙarasa kusa da kunnen salma yace mata ta tashi ga mahaifin najeeb.
Hannunshi ta saki amman se taji shi yayi sauri yariƙe nata,da sauri ta ɗago kanta tana duban fuskarshi,
ba salma kowa seda yayi mamakin ganin idanun najeeb a buɗe yana kallon salma hawaye nazuba ta gefen idonshi.
Da sauri mahaifinsa yamatsa kusa dashi yana masa sannu.
Binsu kawai yake da ido amman ba baki.
likitocinne suka zo suka korasu waje,sannan aka canjawa najeeb ɗaki zuwa wani na musamman wanda babu me shiga sede me jinyarsa wato salma.
Guri suka samu suka keɓe aka sake maimaitawa mahaifinshi komai,ga mamakinsu be ji haushin aurawa njeeb salma ba,sema godiya daya dunga yiwa mahaifin salma harda hawayensa.
Muje zuwa.
Surbajo for life.
*👩🏻💼Y'AR BAUTAR K'ASA*
Zahra Muhammad Mahmud
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
*PLS MESON BOOK DINA YATAMBAYA A GROUP,NI BANA TURAWA PC,SABIDA NAYI ME WUYAR TUNDA NATURO GROUP,ADDING NUMBERS KUBA WASU ADMINS DIN KOWANNE GROUP DINA AKWAI ADMIN KUBASU,NI WLH UZURI YAMIN YAWA,KU KUMA ADMINS IN ANBAKU KUSA KA,AMMAN ADMIN DIN SURBAJO HAUSA NOVELS(MY SCRET)KARKIYI ADDIN DIN KOWA ACIKIN SA,AMMAN SAURAN AYI,PLS🙏*
*25*
Waya Alhaji hassan yayi yasanar da hajiya kaltum halin da ake ciki,harda auren da aka ɗaurawa najeeb din.
A wayar harda kuka tayi na tausayin najeeb din,tana kashe wayar tamiƙe afusace tana kai kawo.
"najeeb kayi kuskure daka faɗa tarkon son wata ƴa mace baniba,wlh inde sunana kaltum,sena hanaka jin daɗin auran da kayi dani kake magana"sune kalaman sa hajiya kaltum ke furtawa cikin fushi.
Salma kowa yaganta se yaɗauka tare suke ciwon,dan itama bakinta ya kulle tadena magana sede ido,babu yadda baayi daita ba akan taje gida tabar kabeer yakula dashi amman fafur taƙi amincewa,dan ko ma ta miƙe zata yi wani abun sede tayi da dabara dan hannun najeeb riƙe yake da hannunta kowannen motsinta akan idonshine,sede inyayi bacci ne take da lokaci.
Hajiya kaltum tazo dubashi,yayinda taga salm seda numfashinta yakusa tafiya,sabida ganin ƙirar da Allah yay mata,take taji kishi da tsanarta sun baibaye zuciyarta,inda ta ayyana ko tawacce hanya seta rabasu.
Wasa wasa seda najeeb yayi wata uku a Asibiti sannan yafara magana,amman be fiye yiba yafison yayi shuru.
Idan kabeer yazo dubashi rufe idonshi yakeyi sabida ji yake kamar zuciyarshi zata fito inya kalleshi,yatuno yanzu fa kullum seya kwanta da salma seyaji kamar yakasheshi.
kabeer yasan najeeb na kishi dashine shiyasa be masa magana,dan haka be damuba illah dariya ma da abun yabashi.
Mahaifin najeeb ganin yasamu sauƙine yasa yakoma kano,yasa aka,ginawa najeeb plat me kyau da tsari acikin gidanshi,abisa jagorancin umarnin da hajiya kaltum tabashi,sabida da awaje ze gina masa,se tsautsayi yasa yafaɗa mata,ayko ta shiga ta fita.ba abinda baa zuba acikiba na more rayuwa,sannan dakanshi yaje kasuwa yasa aka haɗa lefe nagani na faɗa,dazeje duba najeeb din yakai gidansu salma da kuɗi milyan daya amatsayin dukiyar auren salma.
Yau aka sallami najeeb a asibiti,babu mecewa yayi ciwo,yawarke garas.se ƙafarshi dayake ɗan ɗingisawa
Tun da daɗewa yake so yasamu wanda ze tambaya meyasa salma take kwana agurinshi,amman yarasa wanda ze tambaya.
Tun safe kabeer yazo awata mota marcedez venz 4matic,fara,me baƙin glass anyiwa motar decoratin da kayan decorating,dasu balam