Showing 102001 words to 105000 words out of 114936 words
Chapter 35 - Cuta Ta Dau Cuta Complete Hausa Novel By Billyn Abdull .txt
da tsana ita da Dafeeq ɗin taja tsaki ta shige mota. Ko kallansu Abaan bai sake yi ba ya birga motar sukai gaba. Har sukaje gidan kawun babu wanda ya sake magana. Kusan awarsu ɗaya a can suka sake dawowa gida. Ƙofar gidan da suka bar su Dafeeq suka samu cike tamm da mutane, Abaan yayi niyyar wucewarsa sai dai kuma ya tsaya jin mike faruwa?.
Wata mata ce ke sanar musu ai Dafeeq da matarsa ne wani mai napep ya buge yay tafiyarsa. Yay musu horn yay musu amma suna tsaye a tsakiyar titi kamar gunkina shiko yabi takansu dan barikinsu ba ɓoyayya bace a anguwar. Kullum ne sai sunci uban dabe har titi, a garin dabben nasu ne ma suka makema uwar Dafeeq ɗin ido yanzu haka ido ɗaya ne da ita ɗayan ya tsiyaye. Ubansa kuwa tuni ya gudu garinsu yay aurensa. Har Kainaat ɗin nada ciki haka suke zuba dambe, yanzu ma data haihu kuma basu daina ba, a kullum faɗan nasu bai wuce kan abinci sai kace karnuka. Dan shi dai Dafeeq ɗin baya aikin komai balle sana'a sai zaman gulma a majalisar abokai, yanzu haka suma sun gaji sun korosa. Ita kuma Matar tasa wahala tasa tana bin gidajen mutane tana wankau ana bata sauran abinci da kuɗin da basu taka kara sun karya ba. Shi kuma da son zuciya idan ya gani yace zai ƙwace hakan ke haɗasu faɗa kullum a tsakkiyar anguwa. Yau kuma ance wai shi tsohuwar matarsa ya gani, ita kuma tsohon mijinta sun zama mata da miji suma shine sukai sumar tsaye har mai napep ɗin yazo yay awan gaba da su. To yanzu dai gasu can anyi cikin gida da su......
Noor ce taja tsaki saboda gajiya da surutun matar, cikin hasala tace, “Please Hamma mutafi Mamy na jiranmu muka zauna jin wannan shirmen banzar”. Numfashi ya ɗan sauke kawai yana ƙoƙarin tada motar Khadijah ta ɗaura hannunta a saman nashi. Kallonta yay kamar yanda take kallonsa itama. A hankali ta sakar masa murmushi mai sanyi. Shima murmushin ya sakar mata, sai kuma ya girgiza kansa kaɗan ya ce, “Ya akayi Baɗɗo am”.
“Hamma mu taimaka musu, Aunty Noor kiyi haƙuri kinji. Babu abinda yafi rama sharri da alkairi nasara a rayuwa. Mu musulmai ne, masu tarbiyyar koyarwar MANZON ALLAH (S.A.W). Ya mana dukkan ni'ima ta rayuwa badan munfi saura daraja da kima ba, sai dan kawai haka yaso. Wannan wata damace UBANGIJI ya bamu, idan mukai amfani da ita mune da riba har abada”.
Kusan a tare Abaan da Noor suka saki ajiyar zuciya. Wata irin ƙaunar Khadijah na sake ratsasu....
Da ƙyar suka sami ganin su Dafeeq da aka zagaye anama fifita. Ga mahaifiyarsa da alamu suka nuna bata gani da ƙyau nata kuka a gefe. Haka yarinyarsu sai tsanyara kuka take itama da rauni a goshinta. Hannu Khadijah tasa ta ɗauke ta, duk da kuwa yarinyar duƙu-duƙu take da datti har wani tsami-tsamin dauɗa take da zarni. A zabure Dafeeq da Kainaat suka tashi kamar basu ne kwance magashiyan anama firfita ba suna nishi da ƙyar.
“Da gaske ku ma'aurata ne a yanzu?”. Cewar Kainaat cikin rawar murya da zubar hawaye. Kafin Abaan da Khadijah suyi magana Noor ta amshe a gadarance.
“Yess su ɗin ma'aurane. Masoyan juna na bugawa a sararin samaniya bama bango ko dutse ko jarida ba. Gasu ma har ALLAH ya azurtamu da samu rabo, nan da watanni uku in sha ALLAHU ɗanmu ko ƴarmu sun shaƙi iskar duniya. Ya kukaga haɗin dan ALLAH”. Ta ƙare zancen da ƙyalkyalewa da wata shegiyar dariya har sai da Abaan ya harareta. Kuka Dafeeq da Kainaat suka fashe da shi a lokaci guda tamkar wasu ƙananun yara. Yayinda Mahaifiyar Dafeeq ke tayasu. Cikin kuka tana faɗin, “Yanzu duk ƙoƙarina na kar Khadijah kiga Dafeeq dai ko ya ganki haƙata bata cimma ruwa ba kenan. Oh ni oh ni duniya haka zakimin. Yau ga Khadijah gaban ɗana tamkar matar shugaban ƙasa. Ga ɗana a ƙasƙance gabanta kamar almajirin gidanta. Dafeeq ka cuci kanka ka cucemu daka kwaso mana wannan KARA DA KIYASHIN da bakin iyaye ke ɗawainiya da rayuwarta. Gamunan ta goga mana ƙashin tsiyarta matsiyaciya kawai tsinanniya mai yawo da tsinuwar iyaye aka....”
“Ashaa mama haka bai ƙyautu ba. Ai daga ɗanki har matarsa duk ɗaya suke a gareki. Hakan garesu kuma rubutaccen al'amarine da babu hannun da ya isa ya goshesa a cikinsu. Haka ALLAH ya tsara, batare da mun taɓa sanin juna ba amma ya auri mace ya saka na aura, na saka nima ya aura. Wannan wani hukuncine da ga UBANGIJI......”
“CUTA TA ƊAU CUTA... ALKAIRI YA ƊAU ALKAIRI ba Hamma”. Noor ta katsesa tana wani balla musu harara. Aiko atake jama'ar da suka cika tsakar gidan duk da ana korarsu sun ƙi fita suka shiga faɗin, “Wannan haka yake.dan babu wanda bai san soyayyar da Khadijah ta gwadama Dafeeq ba. Amma yaci amanarta shi da uwarsa. To gashi nan ya rabu da ita saboda abin duniya ya auro dai-dai da shi mai fama da bakin iyaye. Dan tuni a surutun Dafeeq da mahaifiyarsa sun fayyacema mutane wacece Kainaat. Kullum cikin mata gori ake a anguwa. Tana son zuwa ga iyayenta bata da ko kuɗin motar barin Kano. Data fara tarawa kuma Dafeeq ke sacewa. Haka zasu ci uban dambe su jigata juna ta haƙura. Hakan kuma bai hana ta sake tarawa ya sace su.
Jin al'amarin nasu dai babu daɗin ji Abaan ya basu kuɗi. A take Khadijah ma ta basu daga jakarta sukace suje asibiti suka fito suka barsu dan Mamy nata kiransu lokaci zai ƙure musu gashi jirgi zasu bi. Haka dai suka dawo gida jiki a sanyaye. Yayinda suka bar Dafeeq da Kainaat da mahaifiyarsa na rusar kuka. Da ga ƙarshe faɗa ya nema hargitsewa tsakaninsu akan kuɗin. Dafeeq na son nuna musu ƙarfa-ƙarfa daga uwarsa har Kainaat ɗin sukace bai isa ba kowa yaje yaji da kansa. Dan haka maimakon asibiti ma camix suka je aka duddubasu kowa ya matse kuɗinsa. Burin kainaat gobe asubar fari ta nufi Niger neman iyayenta ta nema gafararsu ko hakan zai sa ta samu sassauci kamar yanda mutane keta bata shawara. Maybe hakan zaisa ta samu Dafeeq ya saketa ta dawo ta auri Abaan. Shiko Dafeeq nasa hangen ya haɗe kudi ya fara kasuwanci ko shima ALLAH zai azurtashi Khadijah ta dawo garesa.......
✍️
_Niko nace Hummm hauka maganinka ALLAH. Ai an baro shiri tun rani Kainaat da Dafeeq 🥱🥱😆🧑🦯._
*_NACE KIN MALLAKI NAKI👋??._*
*_NAKI NAKE NUFI KIN MALLAKA KUWA👋🏻👋??_*
*_TIKITIN SHIGA JIRGIN TAWAGAR ZAFAFAN LITTATAFAN NAN NA ZAFAFA BIYAR NAKE MAGANA SISTER KIN MALLAKA👋👋👋🤔??_*
*_KIN SAN KUWA A WANNAN SHEKARAR TA 2024 TA DABBANCE. IDAN NACE DABAN INA NUFIN DABAN A CIKIN DABAN_*
*_A 2024 ZAFAFA BIYAR ƊIN NAN NAKU SUN SAKE ZUWA MUKU DA WASU SABON SALO NA MUSAMMAN DA ƘAYATARWA AKAN FARASHI KAI SAUƘI DA RAHUSA. DAN HAKA INA GAYA MIKI ƳAR UWA KADA KI BARI AYI TAFIYAR NAN BABU KE_*
_Littatafan sune kamar haka 👇🏻_.
*_KWANKWASON JIMINA....._*
_(NA MSS XOXO)_
*_GUDUN ƘADDARA_*
_( NA SAFIYYA HUGUMA)_
*_TSUSTAR NAMA....._*
_(NA BILYN ABDULL)_
*_AMEENATU_*
_(NA MAMU GEE)_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏_*i
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na arba'in_
*ZAFAFA BIYAR FAMILY*🫂🫂🫂🫂🫂
🔥 *me kike jira ne da har yanzu baki shige ahalin zafafa ba*
*_ZAFAFA BIYAR_*❤🔥🔥❤🔥🔥❤🔥🔥
❤🔥 *_SABUWAR SHEKARA_*
❤🔥 *_SABON TSARI_*
❤🔥 *_SABBIN LABARAI_*
❤🔥 *_TSUMAMMIYAR SOYAYYA_*
❤🔥 *_CAKWAKIYA_*
❤🔥 *_LABARAI NE MASU RATSA ZUKATA DAKE TAFE DA WANI IRIN SALO_*
❤🔥 *_SALON DAKE DAUKE DA ZALLAR GOGEWA DA QWAREWA WAJEN SARRAFA ALQALUMA_*
❤🔥 *LABARANSU NA MUSAMMAN NE DAKE DAUKE DA WANI IRIN SALO ME RATSA JIKI_*
*_KWANTAR DA ZUCIYA_*
*_CIRE DAMUWA DA SABUNTA SOYAYYAR MASOYA_*
*QAWATATTU KUMA TSARARRUN LABARAN 2024 DIN SUNE KAMAR HAKA*
*KWANKWASON JIMINA* _ME WUYAR TABAWA_ (miss xoxo)
*TSUTSAR NAMA* _ITAMA NAMA CE_ (Billynabdul)
*AMEENATU* (Mamuhghee)
*GUDUN K'ADDARA* _GUZURIN TARAS DA ITA_ (Huguma)
*_KOWANNE LABARI NA DAUKE DA SUNA ME HARSHEN DAMO,KAMAR YADDA GUNDARIN LABARIN KE DAUKE DA SALON DA ALQALUMAN ZAFAFA BIYAR NE KADAI ZAI WARWARE MUKU SHI_*
*_Biya naki ta wadannan lambobin domin ki zamo cikin ZAFAFA FAMILY HOUSE_*
*TSARIN SHINE KAMAR HAKA*
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*THANKS FOR CHOOSING US*🫂🫂🫂🫂
_______________________
........*_YEARS LATER_*. Shekaru sun ja, rayuwa ta canja. Tuni jiya ta sauya daga yau zuwa goben wasu. Al'amarin tamkar mafarki ko labari suma sun zama iyaye. Wannan Abaan ɗin da kowa ya sani a matsayin matashi yanzu sunan dattijo yake amsawa. Hakama Khadijah ɗin nan ta zama babbar mace uwa mai ƴaƴa har huɗu jinin Abaan. Ɗiyarsu ta farko suna kiranta Mimi, wadda taci sunan mahaifiyar Abaan ne. Sai na biyu Muhammad. Na uku Abubakar Sadiq. Sai auta Umar Fharooq. Dukansu kamanni suke da Abaan, babu wanda ya ɗako Khadijah a kamanni sai dai jini shi baya ƙarya, duk wanda ya gansu dai yasan itace mahaifiyarsu.
Ƙarfe biyar da wasu mintuna zuƙeƙiyar mota ta shigo ƙaton harabar gidan. Driver na kammala parking a gaggauce ya fito domin buɗe mata. Hamshaƙiyar mace da hutu ya nuna kansa a jikinta ce ta fito cikin yanayin gajiya. Tana sanye cikin shiga ta alfarma. Dan wani lass ne mai masifar ƙyau da ɗaukar idanu a jikin nata. Sai farar riga ta likitoci ƙal dake tabbatar da ita ɗin wacece. Sannu direban ya shiga jera mata ganin yanda take ta faman yamutsa fuska alamar a gajiye take. Ta sakar masa murmushin nan nata mai sanyi batare da tace komai ba. Kafin ta raɓashi ta wuce zuwa cikin gidan. Tarkacenta dake a mota shima ya tattaro ya biyota.
A kusan tare ƙyawawan samarin yaran dake a falon kowa na harkar gabansa suka ɗago. Sai kuma duk suka miƙe suka nufota kowa na faɗin oyoyo Ammie. Hannayen ta ta buɗe musu duk suka shige abinsu. Jikin nata suka bari kowa na jera mata sannu da nuna tausayawa. Itako na faman musu murmushi. Babban da zai iya kaiwa shekara goma sha biyar ne ya kama hannunta har tsakkiyar falon ya zaunar. Sai kuma ya duƙa gabanta yana mai kama ƙafarta ya zare takalmanta ya na danna mata ƙafafun da sukai ɗan fushi. Da sauri autanta da zai iya kai shekara goma shi kuma ya iso gabanta da ruwa yana faɗin, “Ammie tun ɗazu na fito miki da shi a freight ya huce dan kar kisha mai sanyi kiyi mura.”
Fuskarta da murmushi ta furta, “Oh my AUTA ALLAH yay muku albarka. Yanda kuke ji dani ALLAH ya baku mata da zasu ji daku kuma da ƴaƴa”..
A tare suka amsa da Amin cikin ɗoki harda na tsakkiyar da zai iya kai shekaru sha uku. Shi kuma kayanta dake hannun driver ya amso.
“Daddy fa?”.
Ta faɗa tana kallon babban. Sauran ƴan uwansa ya kalla sai kuma ya kwashe da dariya. Harararsa Khadijah tayi da faɗin, “Miye abin dariyar?”.
AUTA ne ya matsar da bakinsa saitin kunnenta. Cikin raɗa ya ce, “Ammie ya ɓuya a sama ne. Wai idan kin dawo muce bai dawo ba. Kuma ya kashe phones nashi sai kin ruɗe sosai zai sakko. Ammafa kar kice ni na faɗa”.
Murmushi Khadijah tayi mai sanyi tana girgiza kanta. Sai kuma ta miƙe tana kallonsu da kulawa. “Shike nan bari naje na watsa ruwa. A haɗamin shayi kar a saka suga. Ina Mimi?”.
Shiru yaran sukai saboda tambayar ƙarshe. Sai kuma babban ya ja numfashi muryarsa da alamun ɓacin rai ya ce, “Ammie ta fita. Kuma da alama wannan shegen yaron ne yay kiranta. Ta ƙofar baya ta fita batare da tasan na ganta ba. Naso binta sai nai tunanin kar Daddy ya ji”.
Shiru Khadijah tai tana kallon yaron nata. Sai dai gaba ɗaya fara'ar dake saman fuskarta ta gushe. Wani kalar bugawa zuciyarta keyi da sauri-sauri. Dan al'amarin yarinyar tata ya fara caja mata ƙwaƙwalwa. Ɗakinta ta nufa, sai kuma ta fasa ta nufi upstairs. Da kallo samarin yaran nata duk suka bita fuskokinsu cike da damuwa. Dan sun san al'amarin yayar tasu shine abu mafi zama damuwa ga mahaifiyar tasu a kwanakin nan...
Tun kam ta ƙarasa hawo steps ɗin ƙamshinta ya gama cika masa hancinsa. A hankali ya ɗago daga abinda yake ya zuba ma hanyar fararen idanunsa dake cikin glasses fari tass da alama na ƙara gani ne. Saurin ture laptop ɗin saman cinyarsa yay yana mai riƙota ganin yanda take tafiya kamar zata faɗi. Muryarsa na rawa alamar ruɗewa ya ce, “Boddo am mike faruwa? Yau ma daga asibitin ne? Ko kuwa n.....”
Da sauri ta girgiza masa kai hawayen da take ta son riƙewa na gangaro mata. Sai kuma ta faɗa jikinsa tana mai ƙanƙamesa da sakin kuka mai ƙarfi. Sake rikicewa Abaan yayi. Dan babban abinda ya tsana a rayuwarsa shine ganin matar tasa cikin ɓacin rai ko damuwa. Yana ƙaunar baiwar ALLAHr nan. Ƙauna irin wadda baisan yaya zai misaltata ba ga mai saurarensa. Domin ta gama masa komai. Ta riƙesa amana. Ta ƙautata ma mahaifiyarsa a lokacin da take jiyya har ALLAH yay mata rasuwa. Ta haifa masa yara har guda huɗu. Ta tsaya tayi karatu kamar yanda yay fata ta zama babbar likita saboda shi yana son hakan. Ta bama yaransa tarbiyyar da suka zama abin sha'awa a wajen duk wanda ya sanshi dama wanda bai sanshi ba. Tayi hakuri da abubuwa masu yawa domin shi.....
“Hamma har abada bazan daina nadama ba. Bazan daina takaicin kaina ba akan bijirema iyayena. Duk da sun yafe min kafin su bar duniya hakan bai hana tarihi neman maimaita kansa ba. Ashe da gaske ne duk abinda ka aikata ga iyayenka kaima sai ƴaƴanka sun aikata gareka....”
“Haba Boddo am miyasa kike irin wannan maganar ne. Abinda ya faru ya riga ya wuce ai. Baba da bakinsa ya sake maimaita ya yafe miki a randa zai bar duniya. Hakama Mama bata gushe ba sai da ta sake nanata yafiya a gareki tare da sanya miki albarka ke da zuri'armu. Miyasa zaki faɗi haka?”.
“Dolene na faɗa Hamma. Domin kuwa Mimi data kasance ya ɗaya mace tilo a garemu. Ta kuma farko da muka fara gani a duniya ta fara ɗakko irin wacan hanyar da nabi da har yau ban daina nadamar binta ba. Na ɓoye maka ne da tunanin zan iya control ɗinta. Sai dai ba hakan bane. Sati uku kenan Sadiq ya sanar min duk sanda driver ya kaisu school ya ajiye sai ta koma ta fita. Hankalina yay masifar tashi da jin zancensa. Amma sai bance da shi komai ba washe gari na kaisu school ɗin da kaina. Bayan na ajiyesu sai na samu wani waje na ɓuya. Ban rufa mintinan biyar ba sai gata ta fito. Da ƙyar na iya riƙe kaina saboda hajijiya data nema ɗibata ganin wani saurayi da bai wuce shekara ashirin ba ta nufa. A mota ya ɗauke ta suka bar makarantar, hakan yasa na bisu da sauri ta yanda bazasu gane ba har zuwa wani sabon garden da Fharooq keta maka nacin muje ɗin nan. Na ɗanji nutsuwa ganin ba wani wajen ashsha suka nufa ba. Haka na ɓata lokaci a wajen har awa kusan uku suna tare kafin ya ɗauketa su koma. Makarantar ya sake maidata ta shiga shi kuma ya tafi. Ranar nayi kuka, na kira Ni'ima na sanar mata ita da aunty Noor. Shine suka bani shawarar kar nai mata magana kaima haka na cigaba da bibiyarya na sati guda. Haka nabi shawarar tasu har sati ɗayan kullum ina zuwa school ɗin nasu batare da ta sani ba kaima haka. Kuma kullum sai sun fitan sai dai garden ɗin nan dai yake kaita suje suyi zaman awa uku ya maidata. Ranar da sati ya cika Aunty Noor taje ta ritsasu a garden ɗin. Tun a can ta faffalesu da maruka su duka ita da yaron sannan ta ɗaukesu zuwa gidanta. Nasiha tai musu sosai bayan ta tambayi yaron ya sanar mata yana lavel 100 ne a jami'a baima cika wata hudu da farawa ba. Bayan ta musu nasiha da faɗa sosai muka cigaba da bibiyarsu. Sai naga ya daina zuwa ɗaukarta akaf satin can daya gabata. Ganin haka yasa na saki jiki nabar bibiyarsu saboda ayyuka sun min yawa ma a asibiti a satin nan gaba ɗaya. Hamma ashe yaran nan basuji faɗa da nasihar Aunty Noor ba. Yanzu na shigo gida shine yaran nan ke sanar min tana ganin ka hawo sama ta fita ta kofar baya. Muhammad ya kuma tabbatar min yaron nan ne yay kiranta. Hamma duka shekarar Mimi nawa ne? Hamma wlhy ji nake kamar zuciyata zata fashe.....”