Showing 96001 words to 99000 words out of 114936 words
Chapter 33 - Cuta Ta Dau Cuta Complete Hausa Novel By Billyn Abdull .txt
Doctor Giɗaɗo bai shigo asibitin ba. Zuciyarsa taso ɗan shiga ruɗani, amma sai wani sashe ya gargaɗesa akan ba hakan bane.
Kwanakin Hajiya Kainaat biyu a asibitin aka sallamesu. Sai dai har yanzu babu Doctor Giɗaɗo babu labarinsa. Tun Dafeeq na ɗaukar al'amarin wasa har lissafinsa ya fara canjawa. Gashi bai san ainahin gidan su Doctor Giɗaɗo ɗin ba, sai gidansa kawai ya sani, yaje ya samu kuma a rufe wai sunyi tafiya masu gidan. Yata bin Nurses na asibitin su sanar masa ko Dr Giɗaɗon nada wani gidan bayan wannan sun ƙi, da ga ƙarshe wani ke sanar masa Doctor Giɗaɗo fa ainahinsa baɗan Adanawa bane, kuma zaune yake shi kaɗai babu matarsa. Hasalima ba ɗan Nigeria bane. Ɗan Cameroon ne. Neman faɗi Dafeeq yayi, amma ya daure ransa da ƙyar suka bar asibitin zuwa gida a napep.
Sun iso kowa da abinda yake tattaunawa a ransa, sai kuma mi, suka sami ƙofar gida danƙare da kayayyakinsu duk an fiddosu waje. Sai mai gadin makwabta ne ke sanar musu ai aikin wanda suka sayi gidan ne. Sannan kuma wani yazo ya bada saƙo a bama Dafeeq. Baibi takan saƙon ba hankalinsa ya karkata ga Kainaat dake tambayar ina sauran motocinta biyu. Da mamaki maigadin ya bata amsa da ai ƴar uwar nan tata da wanda ya bada wannan saƙon a bama mijinta ne suka ɗaukesu suka wuce. Neman yanke jiki ta faɗi tayi dan tasan dai Nadwa ce kowa ya sani matsayin ƴar uwarta, nan ma sai da Dafeeq ya riƙeta. Ganin mutane sun fara taruwa Dafeeq ya lallaɓata akan tazo suje gidan da ya zauna da Khadijah dan shi ya kasa fahimtar komai. Bata da zaɓin daya wuce binsa, dan wlhy jitake kamar kanta zai fashe...
Sosai gidan yay kura, dan ba zama ake ba. Shi kansa yayi kusan wata biyu ma bai zo ba. Da dai yakan zagayo ya ɗauki kayan Khadijah yana shin shina wani lokacin harda hawaye. Sai dai wannan abin daya tasa gaba akan dukiyar nan ta Kainaat ta ɗauke hankalinsa kwana biyu. Kuka sosai Kainaat keyi na tashin hankali. Babu abinda ke juya mata a rai da ƙwaƙwalwa kamar batun wai Abaan ɗinta yayi aure sati ɗaya kenan daya wuce.
Yanda take kukan ne ya sake hasala Dafeeq, a kausashe ya ce, “Wai minene kuma?!”. Cikin suɓutar baki tana ƙara fashewa da wani sabon kukan ta ce, “Yayi aure fa, kana ji wai ni Nadwa ke faɗama Abaan yayi aure”.
Wani harara ya wulla mata zuciyarsa na tafarfasa. Sai dai yay dauriyar yimata banza ya ɗauke kansa kawai. Sai ma warware babbar envelope ɗin da maigadin nan ya bashi yake. Wayace a ciki, wayar da shi da kansa ya bama Doctor Giɗaɗo akan suna waya. Baima san sanda yay saurin shiga wayar ba, kamar an saita da video ya fara cin karo. Nadwa da Doctor Giɗaɗo da Mom suka bayyana. Wani shegen zabura da ya maido hankalin Kainaat kansa yayi. Ƙoƙarin miƙewa yake ya fita Kainaat ta warce wayar ta danna play.
“K miye haka?!!”.
Ya faɗa cikin daka tsawa. Ko kallonsa batayi ba ta maida hankali akan videon. Dan abu na farko da mutanen uku suka fara shine dariya a tare. Kafin Doctor Giɗaɗo ya ɗaga hannu ya ce, “Hy Dafeeq mijin Kainaat. Oh Hajiya Kainaat.” sai kuma suka kwashe da dariya. Sai da sukai mai isarsu sannan ya cigaba da faɗin, “Nasan zakuyi mamaki, matuƙar mamaki. Amma karku damu. Dafeeq kai tsuntsune mai wayo. Sannan ALLAH ya baka kwanya sosai. Sai dai matsalarka ɗaya ce baka da ilimi. Ƙarancin iliminka yasa ko kayi lissafi yake wargajewa batare daka farga ba. Zan fayyace farkon alaƙarmu saboda ko ita Hajjajun taka zata gani dan saƙon ya isheta. Hajiya Kainaat kamar yanda kika sani nasan Nadwa da mamarta ne a dalilinki kamar yanda na sanki a dalilin Alhaji Abaan. Mun ƙulla alaƙa mai ƙarfi tsakanina da Nadwa da jimawa lokacin kina tare da Abaan, sai dai mun rabu daga baya sakamakon wasu matsaloli. Tunda muka rabu bamu sake ganin juna ba sai randa aka kawoki asibiti, a dalilin gano kina da shigar ciki na nema number Alhaji Abaan domin na sanar masa. Sai dai yanda ya karɓi batun cikin naki yaban mamaki. Ina tsaka da taraddadi sai ga Nadwa. A wajenta nake jin ai kun rabu, yaron daya kawoki shine mijinki yanzu. Nasha mamaki, amma sai wani zancenta ya shafe min mamakin nawa. Ta nema mu ƙulla dil, in har na taimaka mata muka mallaki dukiyarki to lallai ko zata auran. Humm naji daɗi kamar zan mutu, dan ina son babyn nan”. Ya wani shafa ƙirjin Nadwa yana dariya da kashe ido duk da kuwa mahaifiyarta na wajen ko'a jikinsa balle ita. Cike da shaƙiyanci ya cigaba da faɗin, “Mun sami nasarar hakan, bayan ta amshe takardu da komai naki cikin siyasa sai kuma ga mijinki, shima yazo min da barazana, wai yaji duk abinda muka tattauna da Nadwa a office dan haka in ban bashi haɗin kai ba zai yimin miye-miye so soki burutsunsa na ƙuruciya dai da rashin ilimi. Niko na zarmashi ya shiga, nama nuna masa tsaronsa nake ji. Shine ya bani duk wani point dazan iya cimma gaci. Ada munyi niyyar barinki da motocinki da gidan da kuke ciki, sai muka fahimci ai ke da shi CUTA CE TA ƊAU CUTA. kawai mukazo suma mukai packaging nasu. A yanzu dai ki sanar masa ya daina wahal da kansa. Dan ni da matata Nadwa da Mom namu bama ma ƙasar, har abada kuma bazaku sake ganinmu ba byeeee”. Ya wani warwatsa yatsu kamar ɗan daudu.
Dariya Mom da Nadwa suka sanya. Sai kuma can suka tsagaita. Mom ta fara magana, “Humm Kainaat Kainaat. Nasan zaki shiga mamaki, sai dai ki sani ba abun mamaki bane dan kece kika jama kanki. Kina da son zuciya, yanda na riƙeki a rayuwa ban taɓa tunanin zaki saka mana da mugun hali ba. Ke kin samu dukiya tsakaninmu dake sai dai kiɗan tsakura mana ko. Ƙyauta 500k bata taɓa haɗamu ba duk wahalar da mukai miki a rayuwa. Har ƙasar waje na kaiki karatu saboda ƴata, amma da kika samu mijin nunama Sa'a sai kika maidamu wawaye ni da ita. Sai abinda kikai ɗan niyyar sammana. To dama binki muke sannu a hankali har zuwa gaɓar data dace. Gashi mun kai, karma ki wahalar da kanki a neman mu. Yanzu haka mun sayar da kaf kaddaririnki har company ɗin, mun tsallake ƙasa, saboda lawyer ɗin da duk wani mai motsin kirki a companyn dama mune muka haɗaki da su. Ki taya ƙawarki murna sunyi aure da Doctor kuma, nima zan sami wani mai jini a jikan nai wuff da shi kamar yanda kikayi da wannan yaron Dafeeq yake ko mima oho muku. Dama ita bariki alalan gero ce, wanda bai iyaba saita kwaɓe masa. Tun barowarki gidan Alhaji Abaan muke fakon dukiyar nan, sai zuwan yaron nan ya sauƙaƙa mana aiki. Muna masa godiya, ga ladan aiki nan mun bar masa ya rage zafi 500k ne babu yawa.” itama tai mata wani salo tana kashe ido ɗaya.........✍️
*_WAI KINA SHIRIN WUCEWA NE BAKI KARANTA BA😨._*
*_TO MAZA DAWO BAYA KI DUBA. IN BA HAKA BA ZA'AYI BABU KE NE_*
*_INA KUKE MASOYAN ZAFAFA BIYAR DAMA WANDA BAZU TAƁA SIYA BA SAI DAI SU KARANTA A HANYA_*.
*_MAZA KU MARMATSO KU MALLAKI NAKU DAN GAB JIRGIN YAKE DA BARIN ƘASA. MA'ANA GAB ZAFAFAN SUKE DA FARA SAKAR MUKU ZAFAFAN LITTATAFAN SU NA SABUWAR SHEKARAR 2024_*
*_KAR KUYI MAMAKI IDAN NACE MUKU TAFIYAR FA TA BANBANTA DA BAYA. SABODA SALON NA DABANNE, NA KUMA MUSAMMAN NE_*.
*_TSUTSAR NAMA....!!_*
_(Bilyn Abdull)_
*_AMEENATU_*
_(Mamu gee)_
*_KWANKWASON JIMINA...._*
_(Mss xoxo)_
*_GUDUN ƘADDARA_*
_(Safiyya Huguma)_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na talatin ta takwas_
*_NACE KIN MALLAKI NAKI👋??._*
*_NAKI NAKE NUFI KIN MALLAKA KUWA👋🏻👋??_*
*_TIKITIN SHIGA JIRGIN TAWAGAR ZAFAFAN LITTATAFAN NAN NA ZAFAFA BIYAR NAKE MAGANA SISTER KIN MALLAKA👋👋👋🤔??_*
*_KIN SAN KUWA A WANNAN SHEKARAR TA 2024 TA DABBANCE. IDAN NACE DABAN INA NUFIN DABAN A CIKIN DABAN_*
*_A 2024 ZAFAFA BIYAR ƊIN NAN NAKU SUN SAKE ZUWA MUKU DA WASU SABON SALO NA MUSAMMAN DA ƘAYATARWA AKAN FARASHI KAI SAUƘI DA RAHUSA. DAN HAKA INA GAYA MIKI ƳAR UWA KADA KI BARI AYI TAFIYAR NAN BABU KE_*
_Littatafan sune kamar haka 👇🏻_.
*_KWANKWASON JIMINA....._*
_(NA MSS XOXO)_
*_GUDUN ƘADDARA_*
_( NA SAFIYYA HUGUMA)_
*_TSUSTAR NAMA....._*
_(NA BILYN ABDULL)_
*_AMEENATU_*
_(NA MAMU GEE)_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
_________
........Murmushi Nadwa tayi, sai kuma ta gyara kwanciya a jikin Doctor Giɗaɗo tana faɗin, “Ni dai shawara zan baki kamar yanda na saba. Kainaat ki nema iyayenki ki koma garesu, dan in dai Abaan ne ya miki nisa, kamar yanda yaƙi yarda da tayin aurena da naketa jelan masa, kema wlhy sai dai ki rasa dan ya miki nisa. Nisa irin na tsakanin samaniya da ƙasa. Shiyyasa nake ta fargar dake. A yanzu haka yana tare da ƙyaƙyƙyawar matarsa a gidansa cikin aminci da kwanciyar hankali. Dan haka ki riƙe shuga boy ɗinki yafi miki. Nasan zakiyita tunanin mune kuwa. Humm mune ɗin dai, a tunaninki bazan taɓa jin kishi a raina ba ne. Kefa ba ƴar kowan kowa bace. Mune mika ɗauke ki muka suturtaki da sutura ta ƙawa, muka kaiki ƙasar waje kikai ilimin da ya fiddoki har irinsu Abaan ɗin suka kalleki. Saboda mu ahalinsa suka yarda ya aureki ma. A tunaninki banda zuciyar da zanji a raina ni ya kamata na samu wannan bake ba. Nice fa keda komai ɗin, amma sai kika koma komai a kaina. Shiyyasa nai alƙawarin sai kin gama tattara mana mu kuma muji daɗin, dan na lura sam ke ba ƴar halak bace ba baki san halacci ba. Akwai fa lokacin da har gwadaki nai nace ki aramin 10mil zan fara Business amma matar nan kika nuna min baki da shi, ashe ƙarya kikeyi sai daga baya na gane hakan. Hummm kar dai na cikaki da surutu maybe idan kin haihu zan zo suna, ko in matar Abaan ta haihu nazo miki barka, a gaida angon jego Dafeeq byeeeee!🖖”.
Ba Kainaat ba hatta shi uban gayyar jikinsa kakkarwa yake yi. Jin hajijiya na neman yadda shi ya wani zube a kujera. Dai-dai nan Kainaat ta fita gabansa. A bazata ta ɗaukesa da wani kalar wawan mari irin na bazatan nan. Domin kuwa bai tsammani zuwansa ba sai saukarsa yaji. A gigice ya ɗago, ta kuma sake ɗaukesa da wani haggu da dama. Rikicewa yay har kunnensa na masa wani dommmm.
Nuna shi tai cikin fashewa da kuka ta ce, “Matsiyaci ɗan mage baka daɗin goyo. Azzalumi tsinanne, ashe da kai ma aka shirya komai” ta sake kai masa wani dukan. Gam ya riƙe hannunta yana huci, yanda nata jikin ke tsuma haka nashi keyi. Cikin rufewar idanu ya shiga kaimata duka tako ina. Ƙarfin mace da namiji ba ɗaya ba koda ace ta girmesa. Amma duk da haka tayi ƙoƙari itama ba kamar Khadijah ba. Dan duk abinda taci karo da shi wawusowa take tana ƙwala masa. Cikin ƙanƙanin lokaci sukaima kansu jina-jina. Sai da maƙwafta suka shigo aka rabasu anata mamakin yaushe ma suka zo gidan tunda ansan yanzu Dafeeq ɗin yayima gidan ƙaura. Tuni kuma an garzaya an sanarma Baba Hakimi abinda ke faruwa.
Yanda suka jigata juna da raunika yasa dole suka nufi asibiti da su. Baba Hakimi kuma ya hana a sallamesu a ranar dan yamma tayi sosai sai washe gari. Da farko daya tambayesu abinda ya haɗasu shiru sukayi, sai dai bafade ya musu tsawa sannan Kainaat ta shiga zayyane komai tana kuka. Dan a ganinta mafitar da zata rabu da Dafeeq ɗin ce ma tazo mata. Sai dai me, maimakon samun yanda take ai nasiha Baba Hakimi ya musu. Batare daya kawo komai a ransa ba ya ce, “Kai Dafeeq in ma Khadijah ce ka kwantar da hankalinka. Dan yanzu haka tana gidan mijinta tai aurenta. Garama ka riƙe matarka ku zauna lafiya ku kuma ɗauki abinda ya faru matsayin ƙaddara. Dan kai da ita ɗin duk CUTA TA ƊAU CUTA ce kawai”.
Tashin hankali kenan. Dan yanda Dafeeq ya miƙe zambar yana ɗura ashariya sai ma ka ɗauka ya haukace. Fadawa zasu saka a masa duka Baba Hakimi ya hana. Sai dai ya saka an fiddashi a fadar. Aiko a ɗimauce ya nufi gida ya fara haɗa kayansa sai Kano. Wannan al'amari ya sake haukatar da Kainaat, dan duk wanda ya ganta a ranar sai ta bashi tausayi. Kamar ba Kainaat ɗin nan ƴar gayu ƴar ƙwalisa mai ji da kuɗaɗe a gidan sanyi ba. Ta harmutse, ta hargitse, ta gama fita a hayyacinta abun ba'a magana....
A haukace Dafeeq ya iso Kano, sai dai kuma ya samu amsar da yaji inama bai zo ba. Dan ta tabbata dai Khadijah tayi aure. Yanda ake zuzuta masa labarin ta auri wani babban mutum mai kuɗi a Abuja ya nema saka zuciyarsa bugawa. Sai ga Dafeeq da kwanciya ciwo rejiff. Mamansa taso wannan karon ma taje tayi tujara a gidan su Khadijah baban Dafeeq ɗin ya taka mata birki da tuna mata gargaɗin d.p.o, dole ta haƙura ta cigaba da tsine-tsinenta a cikin gida kawai.
Washe gari sai ga Kainaat itama ta iso Kanon kamar sabuwar kamu a hauka. Ta tada musu hankali akan sai fa Dafeeq ya saketa. Babansa yace idan har ya saketa sai ya saki mamarsa shima ya kuma tsine masa. Ai sune dai-dai da juna dan haka su cigaba da kasancewa a tare. Dan kuwa a haukar Kainaat ta kwancema iyayen Dafeeq ɗin komai ne wai dan su sakashi ya saketa. Sai kuma ta ɗaure kanta da kanta. Da farko itama Maman Dafeeq ta ce ya saketa jin kuɗi dai babu su. Sai dai furucin mijinta ya gigitata. Sai kuma cikin da Ƙainaat ke ɗauke da shi ya sake saka jikinta yin sanyi, dan duk duniya kuma babu abinda take buƙatar gani a yanzu sama da jinin Dafeeq ɗin. Wannan shine sanadin zaman Kainaat da Dafeeq a Kano dan su duka biyun ciwo ya kwantar dasu. Ita laulayi shi jiyyar zuciyar rasa Khadijah. Akwai randa harda su aman jini, sai da aka garzaya da shi asibiti. Kusan satinsa uku sannan aka sallamosu. Itama jikin Kainaat ya rikice, nanma suka garzaya asibiti, sai ake sanar musu ai cikinta a bayan mahaifa yake, dole sai sun lura da bata kulawa har lokacin haihuwa a ciresa ta hanyar cs dan yana cikin ƙoshin lafiya. Ina kainaat ta birkice musu akan sai dai fa a cire ciki, dan wata ƙawarta data samu irin hakan cire mata akayi tun yana wata uku. Anta tafka bala'i Dafeeq da Mamarsa sukace bazasu yarda ba, daga ƙarshe dai sai da aka dangane da police station, acan ne aka musu iyaka. Babu yanda zatayi dole ta haƙura dan bata da gurin zuwa yanzu, saboda satinta ɗaya da zuwa Baba Hakimi ya lodo kayansu a mota da ƴan rakiya aka kawo Kano. Acewarsa ya amshi gidansa Dafeeq ya cigaba da zama a gidansu. Dole fa aka share musu ɗakin ajiye-ajiye na gidan suke zaune anan. Idan fatara ta ishesu a zari wannan a siyar, a cire wancan a siyar, wataran ma Maman Dafeeq ɗin ke sata ta sayar basu sani ba. Dama dai kayan Ƙainaat ne masu daraja a ciki. Ga faɗa kullum kamar kaji. Yanzu basa jin nauyin ɗaga hannuwa su shararama juna mari. Saboda yana marinta itama take ware hannu ta sauke masa. Sai in zasu harƙume dambe ne Babansa ya tsawatar tare da tuna musu lalurar dake jikin Kainaat ɗin....
__________★
Yau ta kasance weekend, dan haka tun kusan sha biyu Abaan da Khadijah suka fita domin ɗan hutama ransu. Tunda aka kawota bayan asibiti babu inda ta taɓa zuwa sai yau. Yawo yayi da ita sosai wajaje daban-daban da suka nema juye kan Khadijah ta sake tabbatar da ganin Abuja yafi jinta ma. Dan wani wajen ma idan suka shiga ita mantawa take Nigeria ce fa. Bata wani ɓoyewa taita santi abunta da nuna al'ajabinta. Shiko Abaan na mata dariya da tsokanarta wai baƙauya. Sunsha hotuna, dan duk inda akeje cewa take suyi hoto dan ta nuna ma su Ni'ima. Tun yana tayata shikam harya gaji ya