Showing 1 words to 3000 words out of 16222 words
Chapter 1 - RUHIN FANSA By Maryam Majidadi part 2 -1-1.txt
ο»Ώππππππππ
*RUHIN FANSA*
ππππππππ
Na
*Maryam ismail Majidadi*
Part 2 ,part 2 ,part 2
*ππ°AINUWA πΌRITER'SβπΌ*
*π¦SSOCIATIONπ€π»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*ππ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
Bismillahir rahmanur rahim
Page 1-5 part two (2)
Aiban yana fita da Najma kai tsaye hospital dinshi ya wuce da ita,fadin tsantsar tashin hankalin da yake ciki ma b'ata lokaci ne,gaba d'aya ya rasa me yakeyi masa dadi a rayuwa ya rasa gane shin sama yake ko k'asa,miyan bakinsa ya k'are bayajin zai iya furta ko da kalma d'aya karanto duk wata addu'ar da tazo bakinsa yakeyi,ga kukan Nani da yakeji har cikin ranshi dan shikan baya san kukan mace balle babbar mata irin Nani.ko daidaita parking beyi ba ya fito da sauri tare da daukar Najma yayi ciki da sauri Nani na biye dashi kai tsaye Emergency ya wuce da ita,nurses ne suka bisa baya tare da abokinsa Dr Auwal,d'aya daga cikinsu ne ta rike Nani tace"kiyi hakuri malama bazaki iya shiga ba"janye k'ofar tayi tare da rufewa,wani kukanne ya Kuma kwacewa Nani ta zauna a chair bakin wurin ta rasa abun yi,addu'arta kawai Najma ta samu lafiya,dan idan ta rasa tasan tabbas bazata kumayin rayuwa mai dadi ba.
Duk'ufa Dr Aiban da Dr Auwal sukayi akan Najma amma ba wani labari,dafe kai Aiban yayi yace"innalillahi wa'inna ilaihir raju'un"dafasa Dr Auwal yayi yace"kayi hakuri abokina,ae munyo sa'a da allurai bata gama cika kwanankinta ba kaga akwai yiwuwar bata gama shiga jikinta ba,insha Allah zamu gwada wata hanyar yanzu"cikin sauri Aiban yace"Dr Naman,bara n Kira shi yanzu"Dr Naman zaune yake a k'asar India,shine farkon malamin Aiban lokacin da yake k'asar India yin karatun likitanci,babban likita ne da akeji dashi a k'asar,yana matuk'ar son Aiban saboda maida hankalinshi da kuma kwazo a wurin karatu.bugu d'aya ya dauka tare da fara magana cikin harshen turanci yace"Dr Aiban ya aeki da k'ok'ari?".shima cikin harshen turanci ya ansa da "Alhmddlh sir,dama na kiraka ne akan wata matsala"natsuwa Dr Naman yayi kamar Aiban na a gabanshi yace"ina jinka ".sosai Aiban yayi masa bayanin abunda ke faruwa da Najma .jinjina kai Dr Naman yayi sannan yace"kada ka damu komai zaiyi daidai,ae anci sa'a da allurar bata gama bin jikinta ba,zan fad'a maka alluran da zakayi mata zai tsaida gubar alluran ne,ya zama dole ka taho da ita nan da zuwa gobe kada ka yarda a wuce goben,sai ka kula da fuskar nata ,nasan kasan me zakayi"godiya yayiwa Dr Naman sannan sukayi sallama,cikin sauri ya fita neman alluran balle wahala takeyi yasha wahala sosai sannan ya samota lokacin da yazo Dr Auwal harya gama gyaran fuskar Najma ya rufeta da bandeji ruf baka ganin komai sai farin abu.cikin ikon Allah sukayi mata alluran,sannan ya fita nema masu yarda za'ayi suyi tafiya ba tare da b'ata lokaci ba.
A hankali Ahaad ya soma bud'e rinannun idanuwansa wanda suka sauya kala zuwa ja,bin mutanan dake wurin yayi da kallo,sannu kawai su Mummy suke jera masa amma ya kasa ansawa koda mutun d'aya a cikinsu,dafe kansa yayi da yake barazanar tarwatsewa,lumshe ido yayi da k'yar Mama ta lallab'ashi yasha magani sannan ya koma barci,"daga ina kike ke Kuma"Mummy ta jefawa Fadila tambaya.turo baki Fadila tayi tace"Wai Mummy ni kamar wata k'aramar yarinya zaki sakani gaba da tambayar ina naje"share maganar Mummy tayi kawai tace"Wai baki San meya faru da y'ar uwarki bane?"yatsina fuska Fadila tayi da nuna alamun k'osawa da magana tace"naji waye a garin nan da Wanda ma baya cikinsa zaice be sani ba,an tab'a yarinya mai tashe da dukiya daji da kyau,ae ko ina ya dauka an watsa mata acid an Kuma kasheta an sace gawar,ni zanje ciki na huta".bata jira cewar Mummy ba tayi ciki abunta tana kunshe dariyar muguntar da takeyi.
Aiban kam be koma gida ba sai wurin 11 sai da ya tabbatar ya had'a komai na tafiya,Kuma be wani sha wahala ba kasancewar da marar lafiya za'a bar k'asar,da shi da Nani da Dr Auwal ya tsara tafiyan,yana shigowa Hajiya Sadiya ta jefo masa tambayar da yasa y'an cikinsa juyawa"ina fatan bakai ka dauke Najma ba?,bazan tab'a yarda wata alak'a ta kullu tsakaninka da wannan shed'aniyar ba"Hajiya ta Kuma maimaita tambayan,a tsarinshi baya yiwa Hajiya k'arya komai yana k'ok'arin fad'a mata Amma wannan karon saiya tsinci kanshi da fadin "ko kusa Ummana,ni tun da mukaje da Shuhada d'azu gidan to ban sake komawa ba ae,Allah ya tsare gaba ae naji abunda ya faru"tab'e baki Hajiya tayi tare da wucewa d'akinta bata bashi amsa ba.shafa kanshi yayi ya mike tare da nufar part din shi a hanya ya had'u da Muslin ,kallon Muslin yayi fuskarsa dauke da damuwa ,"wai lafiya kuwa?,me yake damunka ne?"Aiban ya tambayi Muslim,had'iye yawu Muslim yayi yace"bari bro ina cikin tashin hankali,shi wancan uban zuciyar yayi saki cikin fushi,gashi yanzu Kuma yazo ya damu da acid din da aka zubawa yarinyar abun d'aga hankalin shine ko gawarta ba'a gani ba,Kuma babu wanda yasan Wanda yayi mata haka,ga Shuhada can na rasa ya zanyi da ita,ni kaina inajin babu dad'i dan inajin Najma tamkar yarda nakejin su Islam a raina"."Allah sarki sai hakuri kayi k'ok'arin shawo kan Ahaad insha Allah zan kula da Shuhada ita Kuma Kuma Najma Allah ya bayyana mana ita,nima dauriya kawai nakeyi.yana tura k'ofar d'akinshi ya hango Shuhada zaune ta had'a kai da gwaiwa sai rafsar kuka takeyi,da sauri ya k'arasa ciki yace"haba haba mana my sweet sis,meye abun kukan Kuma?,ina Ahaad din ya saki matar da aka daura masa a gabanki ?meye Kuma na kuka irin haka?"Aiban ya fad'a,cikin muryar kuka tace"haba Yaya ni yanzu bata wannan nakeyi ba,kaji zalincin da aka aekatawa Najma amma kai kamar baka wani damu ba,nu ina Santa har'a Raina ina jinta kamar ya yarda nake jinku ,duk yarda akayi wannan bak'in zslincin nasan makirci ne"."ya isa haka bana sonji,kiyi hakuri kiyi mata addu'a insha Allah komai zaiyi daidai bana son kuka irin haka"da irin wannan kalaman Aiban ya kwantarwa da Shuhada hankali har ya samu ta daina kuka Kuma ta tafi ta kwanta.
Tunda asubar fari Aiban yayi sallama k'ofar d'akin Hajiya,ansawa tayi tana fadin"shigo mana Muhammad aena tashi",shiga yayi samunta yayi zaune a bakin bed tana sanye da hijab da alamaun sallah ta gama,duk'awa yayi har k'asa yace"Hajiya ina kwana?,an tashi lafiya?".cikin sakin fuska da tsananin soyayyar d'an nata tace"lafiya qlau Muhammad,lafiya na ganka da sassafen nan?".sun kuyar da kai yayi cikin jinjina maganan da yakeson yi mata can k'asan mak'oshi yace"Hajiya zan tafi wani aeki India yanzu da safen nan"."Muhammad yanzu kuwa ,tafiya har India ba shiryawa tafiya"."Hajiya tun jiya nasan da tafiyar to ganin ban dawo da wuri ba shiyasa ban sanar maki ba,aekin na gaggawa ne,kuma munyi magana da Abba a masallaci yanzu ,zanyi kusan sati biyu a can"jinjina kai Hajiya tayi tace"to shikenan ae da yake sha'anin aekin ceton rai ne,Allah ya bada sa'a ya kuma tsare"da Ameen kawai yake ansawa sannan ya taso ya fito domin shiryawa.zuwa k'arfe takwas ya gama shiri har breakfast yayi dan Hajiya tsareshi tayi,sallama yayi da mutan gidan sannan ya fita,adaidaita yahau ta k'arasa dashi asibitin,kai tsaye Emergency ya wuce ya samu Najma tana nan yarda ya barta sai dai an shiryata shi kawai ake jira su wuce airport,shafa kan Najma yayi cike da matuk'ar tausayi yayi magana a hankali yace"Allah ya baki lafiya Khadija,Allah Kuma yasa fitarki k'asarnan ya zama warakar dukkanin wani abu dake damunki,Allah yasa ki samu sabuwar rayuwa ki mance da burikan daukar fansa dake ranki dan ba'a gyara b'arna da b'arna".guntun hawayen dake idonsa ya goge aka tura gadon da take aka sakata a motar asibiti sannan suka dauki hanyar airport,lokacin da suka isa kusan jirginsu na haramar tashi dan haka basu wani b'ata lokaci ba suka shiga cikin mintoci jirgin nasu ya lula cikin sararin samaniya suka doshi k'asar India.
Tunda ya tashi ya soma had'a kayanshi a akwati ,duk wani abunda yake buk'ata sai da ya had'ashi sannan ya dauki wayarsa daketa faman ruri murya can ciki yace"ya akayi ne?",lumshe ido Muslim yayi yace"haba Sulaiman yanzu bazaka d'aga tafiyar nan ba?,ka duba jikinka ko kwari babu Kuma bamu k'arasa abunda ya kawo mu ba"."kaga malan idan zaka je ka shirya in Kuma baka zuwa ni yanzu zan Kama hanya"be jira ansar Muslim ba ya kashe wayarshi,akwatinshi ya janyo daidai na matafiya ya fito yakoyi sa'a duk suna dining suna break ,ciki ciki ya gaishesu sai kuma yayi shiru daga duken da yake,Mummy tasan y'an mishkilancin suna saman kai idan za'a shekara a haka bazai ce komai ba shiyasa tace masa"Ahaad tafiya zakayi ne?"kai kawai ya iya d'aga mata alamar eh,"haba ka zauna ka idasa warkewa mana"girgiza mata kai yayi alamar a'a ya mik'e tare da d'aga masu hannu yasa kai ya fice,yaransa suka karb'i kayan dake hannunsa ,sannan suka jera motocinsu suka fice a hanya suka d'auki Muslim dan haka suka dau hanyar Niger Delta".
Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan k'arshe.
Kamar kullun majidadi ta dawo,ina fatan yarda muka fara lafiya Allah yasa mu gama lafiya,sannan Kuma inji ruwan comments kamar yarda aka saba mu farantawa juna rai.
Stylish star
Jorderh majidadi
Page 6-10
ππππππππ
*RUHIN FANSA*
ππππππππ
Na
*Maryam ismail Majidadi*
Part 2 ,part 2 ,part 2
*ππ°AINUWA πΌRITER'SβπΌ*
*π¦SSOCIATIONπ€π»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*ππ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
Ga mai neman bayani akan sabon book dina*DIKKO AHMAD* mai fita gobe ya tuntubi 07033636337
Birnin India
Jirginsu ya sauka a garin Mumbai ,juye juye yakeyi yaga ta ina zai hango Umti motar asibiti ta k'araso lokacin da ake fitowa da bed din da Najma take kwance tamkar gawa,can ya hango Dr Naman da Umti,murmushi Umti ta sakar masa sannan sukayo inda yake,rungumeta yayi tare da sakin ajiyar zuciya cikin muryar dake son sakin kuka yace"Umti kinga yarda suka mayarmun da ita ko?"bubbuga bayansa tayi tace"ni dai Aiban dina jarumi ne,dan Allah ya daure komai zaiyi daidai insha Allah"(Umti itace Aunty Maryam k'anwar Aunty Sadiya ,Kuma mahaifiya ga Shuhada da Muslim).risinawa yayi tare da gaishe da Dr Naman shima murmushi yayi sanann ya rungumo Aiban zuwa jikinshi,Umti gaisawa sukayi da Nani ta Kuma jajanta mata,tun a nan Nani ta gazgata tsananin kirkin Aunty Maryam,mota suka shiga tare dabin bayan motar asibitin ,kai tsaye asibitin Dr Naman aka kaita Wanda suke had'in gwaine da Aunty Maryam,d'aki na musamman aka kai Najma cikinsa duk injina da na'urori na gwaje gwaje.office din Umti aka kai Nani ,sannan su Kuma suka duk'ufa akan Najma da take k'afa d'aya duniya d'aya lahira,sosai manya manyan likitoci suka duk'ufa a kanta dan ceto ranta,ajiyar zuciya Umti ta sauke tace"Alhmdllh,nasara ta farko da muka samu shine allurar ko kad'an bata tab'a cikin dake jikinta ba"gyad'a kai kawai Aiban yayi yace "Umti what about her?",dafa kafad'arsa wani baturen Dr yayi yace "soon komai zaiyi daidai"wannan maganar da sukeyi duk a harshen turanci ne.wata allura Dr Naman yayi mata suka tsaya jiran tsammani tare da mak'ala mata wata na'u'ra mai danjoji,addu'a Aiban ya somayi yana a matuk'ar tsorace dan wannan ne lokaci na k'arshe in bata farka ba sai dai ayi hak'uri da ita.ganin danjar jikin na'u'rar zata kawo yayi saurin rintse idonsa ya rike Umti sosai yana karanto duk addu'ar da tazo ransa dan nesan wacce kala ce zata kawo ba,dit dit haka na'u'rar ke k'ara tare da halba tsanwar danja,"Alhmdllh ya Allah,Alhmdllh"abunda Umti ta fad'a kenan,godews Allah Aiban yaci gaba dayi cikin tsananin farin ciki da jin dad'i,ganin Najma ta farfad'o har k'afarta na motsawa.sosai Drs din sukaji dadin nasarar da suka samu,kula ta musamman suka bata sannan aka saka Nurses kula da ita office din Dr Naman sukaje hannu ya bawa Aiban yace"congratulations,na tayaka murnar dawowar y'ar uwarka,insha Allah nan da kwana biyu za'a iya bud'e mata fuska Kuma allurar barcin da aka mata zata saketa,sanann Kuma sai muga wacce hanya zamu b'ullowa fuskar tata"godiya sosai Aiban yayi sanann yayi transfer din kudin da ake buk'ata na aekin yau dan yacewa Umti baya son komai a kyauta ayi mashi kamar kowa.Nani da taji labarin tashin Najma saida ta taka rawar murna,taita zubawa Drs din godiya ,ansha daga da ita sannan aka jata zuwa gida.
Tun daga waje Nani ke kallon gidan dukda ba yau bane rana ta farko da ta fara fita waje ba da Kuma zuwa gidaje irin wa'annan,amma ta jinjina kyawu da tsari na gidan,babban gida ne sosai komai a tsare yake kwanin ban sha'awa ko ina ga filawoyi suna kad'awa.tunda suka shiga takebin wani makeken pic da kallo a parlon na wani Dattijo mai tsananin kyau,amma sam ta rasa ina ta tab'a ganin wannan fuskar sai kawai ta share ta wuce d'akin da masu aekin suka nuna mata,wanka ta shiga lokacin da ta fito har an jera mata abinci a madaidaicin table na d'akinta dan haka taci ta kwanta danta d'an huta.
Har k'asa Aiban ya d'uka tare da gaishe da Abba,cikin sakin fuska Abba ya ansa yace"watanni da yawa malan Muhammad,sai yau har nayi cigiya na gaji"sunkuyar da kai Aiban yayi yace"Abba ayyukane keyin yawa"."to Allah ya taimaka,naji abunda ya faru Allah ya bata lafiya ya kuma tsare gaba,jibi zanje na dubata insha Allah"Abba ya fad'a,godiya sosai Aiban yayi masa sannan ya wuce d'akinsa ya shirya ya koma asibitin,haka Aiban yaketa d'awainiya da Najma ba dare babu rana ko yaushe yana hanyar asibiti da Kuma kashe mata kud'ad'e.
3days later
A hankali Dr Naman yake warware bandage din dake rufe da fuskarta,yayinda take zaune ko hadiye miyau ta kasayi sai fargaba da tsoro,Aiban kam kasa shigowa d'akin yayi,zaro ido Umti tayi tare dayin baya tasa hannu ta rufe bakinta,a hankali Najma ta d'aga idanuwanta Wanda suka zama kalar ja,ta kalli mirror din dake gefenta k'arami,zaro ido tayi tasa hannu a hankali ta shafi gefen hagun fuskarta,wata irin razana tayi ta fasa wata irin razananniyar k'ara ta zube k'asa akan gwaiwowinta,ta fitar da sautin kuka mecin rai.
Wani irin zabura Ahaad yayi amma ya kasa furta komai,zuciyarsa sai ambaton sunan Najma takeyi amma saboda tsabar mishkilanci ya kasa furta koda kalma d'aya.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un"shine kawai abunda Najma ke maimaitawa tana sake hararo yarda taga fuskarta gaba d'aya rabin fuskarta ya toye ya jagule ya lalace ta tashi daga Najmarta kyakyawar budurwa,hawayene suka soma zarya a kuncinta,daga Window Aiban yana hangen komai beyi aune ba saijin siraran hawaye nabin fuskarshi yaji.
Stylish star
Jorderh majidadi
ππππππππ
*RUHIN FANSA*
ππππππππ
Na
*Maryam ismail Majidadi*
Part 2 ,part 2 ,part 2
*ππ°AINUWA πΌRITER'SβπΌ*
*π¦SSOCIATIONπ€π»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*ππ»
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
Page 11-15
Shigowar Daddy mijin Aunty Maryam yasa Najma saurin mik'ewa wani irin bugawa k'irjinta yayi da k'arfi ta tsare mutumin da ido,shima ba k'aramar fad'uwa gabansa yayi ba,kallon yadda aka b'ata fuskar yarinyar yakeyi,k'arasowa yayi inda take yace"kefa musulma ce,kiyi hak'uri ki rungumi kaddararki ki zauna kinji ko"ji tayi wani irin nauyin mutumin takeji da ganin girmansa dan haka babu musu ta zauna,tare da sunkuyar da kanta k'asa.d'agowa yayi yace"Dr yanzu meye abunyi game da fuskar nata?"nisawa Dr Naman yayi ya kalli y'an uwan Drs y'an uwansa dake wurin Dr Ishani ne yace"fuskan ya b'aci da yawa bama da wata mafita daya wuce a canza mata fuska"wani irin razana Najma tayi ta d'ago tace"yanzu hazan dawo da kamanni na na asali ba?"gyad'a mata kai yayi alamar eh, innalillahi wa'inna ilaihir raju'un shine abunda take maimaita hawaye na Kuma wanke mata fuska,da sauri Aiban ya shigo d'akin ya Kama hannuwanta yana girgizata ganin tana neman fita hayyacinta sai da yaga tad'an dawo daidai yace"ki kalleni"d'ago idanuwanta tayi ta zuba mashi su,goge mata hawayen fuskarta yayi yace"ki daina wannan kukan,ur d must strongest women I have ever seen,so karki bani kunya,wannan ma wani matakin nasaran ne,ki bari ayi maki aekin nan,cikin kwanaki kad'an zaki warke,ina so kiyi karatu sosai ki dogara da kanki ki haife abunda ke cikin ki,sannan kiyi k'ok'arin had'a kan Family dinki,ki sani ba'a rama cuta da cuta"shiru tayi can tace"to kayimun alk'awari zaka barni na cika mafarkina ina so in zama soja"girgiza kai yayi tare da shafa gefen fuskarta yace"ga iyayena su zama shaida bazan tab'a hanaki cikar burin ki ba".murmushi ta saki tana zancen zuci."to Alhmdllh hakan yayi kyau,ni Kuma na dauki nauyin karatunta da aekin canjin fuskar da za'ayi mata"Daddy ya fad'a.har k'asa Najma ta d'uko tana zubawa Daddy godiya,hannuwa yasa ya d'ago kafadunta yace"kada ki damu,abunda nake so dai karki bani kunya,ki mai da komai ba komai ba kiyi rayuwa kamar kowa,ki dauka mun zama iyayenki karkiyi fargaba a kanmu"har cikin ransa yakejin kaunar yarinyar kallo d'aya da Daddy yayi mata yaji ta gama zama wani b'are na jikinsa,kallon Dr Naman yayi yace"a fara shirya kayan aekin".gyad'a Kai Dr yayi yace"to wanne suna za'a saka mata a rasid'in da takardunta?".kafin kowa yayi magana Najma tace"yarda Kama ya canza dole komai ya canza,ka samun SHUZNA BASHIR"ta fad'a tana sunkuyar da kanta k'asa.shafa kanta Daddy yayi yace "na gode kwarai da kara Shuzna,kinga yanzu y'an matana biyu Shuzna da Shuhada"dariya Umti tayi tace "baban y'an biyu kenan.
Duk yarda Nani taso ganin fuskar Najma hanata sukayi sunsan ba k'aramin tashin hankali zata shiga ba,dan haka sai dai suka ce mata za'a canza saboda wani b'are ya toye sosai,Nani tasha kuka marar misaltuwa amma haka dai ta hak'ura ta zubawa sarautar Allah ido.
After 3 days
Sanye aka fito da ita da kayan aeki a jikinta fuskarta lullub'e da bandeji,kwance take a bed tamkar gawa ,turata akayi zuwa d'akin da za'a kwance fuskar,kowa addu'arsa Allah yasa anyi aekin a sa'a.Aiban ne ya fara warware mata fuskar sannan ta mik'e zaune amma idanuwanta a rufe tana tsoron ganin yadda ta koma,Daddy,Umti Nani duka suna wurin,"Alhmdllh ,Masha Allah "abunda duk suka fad'a kenan,sab'anin Nani da taketa faman wangale baki tana dariyar farin ciki ga hawaye na zubo mata na dadi, mirror Aiban ya dauko ya kara mata a gaban fuskarta ,a hankali ta soma bud'e idonta wanda yalwataccen gashi