Showing 177001 words to 177664 words out of 177664 words
Chapter 60 - Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete by Garkuwa .txt
a zatonshi wani mugun abune ya farmata, jin kalamanta da ganin abinda takeyi ne yasashi bud'e labulen ƙarasowa cikin falon yayi tare da duban Zaleeha dake kuka harda shiɗewa still knife ɗin na hannnunta da alama ƙiris take jira ta cakawa kanta.
Cikin tsananin takaici haɗi da ɓacin rai da tsantsar tashin hankali da bak'in ciki ya bud'e bakinshi cikin tsananin cushewar sauti muryarsa cike da amon ɓacin rai yace.
"Kin nunamin ban isa dake ba, kin nunamin cewa baki ɗaukeni matsayin uba agareki ba, haƙiƙa kin nunamin cewa ke bakizama ƴa ta gari mai biyayya ba, shikenan zan barki keda mahaifiyarki kuyi duk abun da kukeso, zama daku sam bashida amfani awajena saboda haka yau zan tafi zanyi nesa daku, Zaleeha yau zanbar miki gidan idan yaso kiyi duk wani abun da kikeso, duniyace ae ta isheki riga harma da zanin ɗaurawa, zan tafi inyi nesa daku tun kafin ku kasheni da bak'in ciki." Yana kaiwa nan azance nasa ya juya yanufi ƙofar fita daga ɗakin.
Cikin tashin hankali da fargaba Ahmad da Maryam suka zube aƙasa tare da kamo ƙafan Baban nasu cikin matsanancin kuka suka shiga basa haƙuri.
Rumtse ido Baba Malam yayi har cikin ransa yanajin wani matsanancin ɓacin rai, saidai suyi haƙuri amma tabbas tafiya zaiyi zaiyi nesa dasu domin bazai iya jurar haɗiye baƙinciki da ɓacin ran da Zaleeha da kuma Mama ke ƙunsa masa ba.
Hawayene ke zuba a idanun Mamy yayinda zuciyarta tayi wani irin mummunan karyewa tabbas idan Baba Malam yatafi itama bazata zauna ba, saboda dama danshi kawai take zaune agidan.
idan babushi kuwa me zata zauna tayi agidan.
A kid'ime Maryam ta dawo kusa da Zaleeha cikin muryar kuka tace.
"Dan Allah Zaleeha kice kin amince kada kice a a, Baba fa tafiya zaiyi Zaleeha, kiji tausayinmu! Zaleeha kiji tausayinmu!! dan Allah kada ki bari bak'in cikinki yasa mahaifinmu yayi nesa damu." cikin matsanancin kuka Maryam takare maganan.
Kai Zaleeha ta girgiza cikin bushewar zuciya tace.
"Wallahi Bazan auresu ba, natsanesu dukansu biyu ba wanda nakeso, wlh xan kashe kaina matuƙar aka matsamin kan aurensu."
Cikin ƙaraji tace.
"Natsanesu Bana sonshi!"
Wani irin gigitaccen ihu tasa tare da sanya knife ta yanka wuya..............!
Alhamdulillah...
Mu had'u a kashi na biyu, dan jin yadda wasan zai kaya. K'ak'a-tsara-k'ak'a?." Shin Dalla me zai aikatawa Zaleeha? 1 towai ina Baba malam zai tafi? 2 Ya cire hannunshi cikin auren ne? 3 wa zai auri Zaleeha!? 4 Anya kuwa Saifuddeen zai iya ratsa budurcin budurwa?. 5 Wacece Amina me nufinta kan Saifuddeen? 6 Shin Asma'u zata hak'ura da wannan zazzafan matashi mai suran laraban kuwa? 7 Ummi dai tace dolefa a fasa wannan auren na Zaleeha da kekyawan d'anta! 8 Me nufin Ishaq akan Bilkeesu? 9 Me gskyar zuciyar bilkeesu akan Zaleeha? 10 Shin Saifuddeen kuwa zai iya yin sex kamar ko wanne lafiyayyan namiji? 11 ina Habu zaisa akai kayan da akace na Zaleeha ne? 12 Me Raveel zai iya yi a rayuwar Zaleeha?. 13. Me nufin Mama me zata aikata? 14 Ya Aminu da Ya Habu me zasu aikatawa Zaleeha shalelen Ya Ahmad in sunji tasa Baba malam Kuka? 15 Amsoshin tambayoyin nan duk suna cikin littafin Nakasa ba kasawa bace part two kada ku sake a barku a baya, dan yanzu muka shiga cikin ainihin gundarin labarin. Zazzafar soyayya mai kashe jiki da ratsa zuk'ata, al'ajabi, tausayi, mamaki, dariya, Shauk'i mai girgiza zuk'atan makaranta duk abubuwan suna cikin part two. Saifuddeen zaiyi abunda babu jarumin da ya tabayi cikin jaruman books na, zai shayar daku mmki zai saku Shauk'i mai tunzuro k'uruciyar amarci...!
*BY*
*GARKUWAR FULANI*