Showing 18001 words to 21000 words out of 98640 words

Chapter 7 - A RUBUCE TA KE PART 2 COMPLETED huguma 2023 .txt

da buqata, batason takura,to amma batason tayi wani abu na rashin girmamawa a gareshi gaban yaransa,dole ta ajjiye qaramar hular da take qoqarin sanyawa sassalkar sumarta daketa sheqi saboda yadda tayi oiling dinta da mai,tana tura baki da shagwababbiyar fuskarta ta isa qofar ta bude masa,sai taja ta tsaya daga bakin qofar,kamar wadda aka zo gayawa saqo take jira a gama gaya mata a fita ta kulle qofarta.


Tun daga kwanyarsa har zuwa tafin qafarsa wani abu ya tsarga masa,yadda batasaka brassiere ba amma hakan bai hana na shanunta tsaiwa kyam suna nuna kansu ba,lafiyayyun cinyoyinta sun fita sosai ta cikin tsingilalliyar rigar,yadda ta turo bakinta gaba kuma ya qarasa kunnashi,soft pink lips dinta daketa sheqin lip gloss,sai yaji kamar ya jata cikin jikinsa ya kama bakin ya tsotse,amma yusra na kafadarsa,tilas ya daure,ya qarasa gefan gadon ya zauna ya dora yarinyar saman cinyarsa


"Sannu da zuwa" shuru ya ratsa maimakon ya amsa mata,ya tsareta da ido yana jin yadda kallonta kawai yake saukar masa da kasala


"Banda na shigo na nemeki bakisan ma na dawo ba kenan?"


"To me zanzo nayi maka?,bayan maganar matarka kawai kake ji" ta fadi haka cikin ranta,amma a fili saita sake tura baki gaba tana yamutsa girarta hadi da sarqafe yatsunta waje daya tana ballaqasu


"Zonan" ya fada a tausashe yana nuna mata kujerar madubin dake gabansa,ta kalli wajen sannan ta kalleshi,ko yaushe girma da kimarsa ke sakata ta kasa masa musu ko wasu dabi'u da basu kamata ba,ta sauke hannuwanta ta dawo inda ya nuna matan ta zauna,wannan karon idanunta cikin nasa tanason jin abinda zai gaya mata kuma.


Rage kaifin nasa idanun yayi kadan daga kanta sannan ya magantu


"Ya akayi gidan ya zamana yau duk a hargitse,infact ma yau girkinki ne amma baki fito kwata kwata ba,ko yanzun ma antynki ce cikin kitchen din" wani haushi ya kamata,aiki?.....a nan tafi kauri kenan, idanunta ta lumshe kadan tana daukesu daga kansa,abinda ya sake fusgarsa da wani madaukakin shauqi zuwa gareta,duk da ba tayi bane don ta burgeshi ko kuma da wata manufa


"Gida a hargitse?,ina cewa mummyn mimi tana cikin gidan,amfanin zaman mutum biyu kenan,idan dayan ya gaza ko ya gajiya sai dayan ya tallafa masa.......girki kuma ni na daina girki,na bar mata komai da komai harda kwanana" mamakin widad din sosai ya kamshi,yadda tayi maganar ya tabbatar da gamewar hankali a jikinta,don tana maganar ne with seriousness in her sound,baibi takan maganarta ta farko ba,maganarta ta qarshe tafi fusgar hankalinsa tare da tabashi,don abune da bayajin ko sama da qasa zata hadu zai amince da hakan


"Kin daina girki?,meye dalili?,da kuma izinin wa kika dauki wannan matakin?" Sake tura bakinta gaba tayi sosai tana hade fuska,ta kuma kaucewa dubansa


"Saboda gidan da mijin duka nata ne,so komai da yake cikin gidan yafi cancanta ya zama nata" sai yanzu ya sake gano inda ta dosa,can qasan ransa murmushi ya kubce masa,kishi take da gaske.....ta kuma ji haushin abinda yayi mata kenan fiye da yadda ma shi ya zata,amma bayason ta dore da haka don haka ya miqe yana dora yusra a kafadarsa


"Ki shirya komai kamar yadda kika saba,banason dawo da zance,abinda ya wuce ya wuce" sai ya taka yana ficewa a dakin.


Sam maganarsa bata bawa zuciyarta sassauci ba,saima tunzurata da yayi,bazai iya daukan mataki ba kenan kwata kwata?,indai haka ne itama bataga dalilin da zai sanyata saukowa ba,don haka yana fita sallar magariba ta sakawa dakinta key tayi sallarta ta jirayi isha'i ta bada ita sannan ta haye gado ta nutse cikin duvet hankali kwance.


Sai daya dawo daga masallaci sannan ya zarce dakinta don ya samu ruwan nan nata me wani irin dumi da qamshi don yayi wanka,ruwan da ita kadai tasan yadda take hada masa shi,don koshi ya hada da kansa baya jin dadinsa kamar haka.


A nutse ya tsaya yana knocking a bakin qofar,tana jinsa ta share,saita saka earpiece ma a kunnenta,don haka batasan adadin awannin ko mintunan da ya dauka yana bugun ba.


Sosai ransa ya quntata,don yadda yayi tsaye yana bugun har mimi taji ta fito ya tabbatar tana jinsa,ya kirayi sunanta kusan biyar shuru,dole ya juya dakinsa dakin kuma hafsat,tana zaune a qasa ta tara kayan qazantar yusra tana waresu,ya wuce gaban cupboard dinsa yana rage kayan jikinsa.


Binsa tayi da kallo ta tabe baki,ita da zasu tabbata a haka sai tafi kowa farinciki,duk bugun akan kunnenta akayishi,tana sane tayi bakam


"Ba kwananta bane?,ya na ganka a nan dakin?" Ta jefa masa tambayar da tasan amsarta.


"Na sani,hadamin ruwa zanyi wanka" ya fada muryarsa da wani irin laushi daya bata mata rai,komai na yarinyar tabashi yakeyi,saka masa damuwa yakeyi,duk qoqarinta na kau da hankalinsa amma baya wani tasiri yadda take da buqata,ita sau nawa suna irin wannan sabanin,amma ko a fuska bata taba gani yayi laushi irin haka ba,komai dadewar da zasuyi,sai yanzu akan qaramar yarinya kwana uku kacal amma duka ya canza?.


Da tunani iri daban daban ya shiga wankan,sam ruwan baiyi masa ba,hasalima ya cika zafi da yawa,yaja tsaki ya saki famfo akai,sai kuma yaso salance masa,ya sake jan wani tsakin yana komawa cikin bathtub din ransa duka a jagule.


Koda sukazo cin abinci ma yasa mimi ta bubbuga mata,duk da yadda hafsat ke faman hada rai tana ganin ya girkinta ne batayi ba ita ta zauna tayi kuma saboda gata wai a kirata taci,itama mimin haka ta qaraci bugunta ta haqura ta dawo jiki a sanyaye


"Bata bude ba" sai ya shafa kanta


"Inajin tayi bacci" a yadda yake jinsa koda lafiyayyen girki hafsat din tayi abincin bazai masa dadi a baki ba,bare tafashi kadan hafsat din wadda ta cuccure waje daya,kamar gidan da aka yiwa gorin man girki,bayan komai a wadace yake a store dinsu,zuciyar tata ce dai haka.


Da qyar yayi loma hudu ya ture abincin,ya maida hankalinsa ga news da ake haskowa a channel din al_hadath,duk da a badini fiye da rabin hankalinsa yana kan qofar dakinta,duk bayan mintuna biyu saiya kalli qofar dakin,amma ko motsinta daga ciki baiji ba bare ya sanya ran zata bude ta fito.


Har yaran sukayi bacci hafsat ta debesu takai daki ta dawo tayi masa sallama yana zaune a wajen,sanda sha daya na dare ta buga sai ya tashi yana sake gwada bugun,a lokacin tuni tayi bacci,bugunsa ne ya tasheta,ta sauko a hankali ta wuce toilet abinta,tayi fitsari ta sake alwala ta dawo ta kuma kwanciyarta.


Wannan karon yaji motsinta shigarta bandaki zuwa fitarta,hakan ya nuna masa tana jinsa,bata kuma da niyyar bude masa,ya koma da baya ransa yana baci,ya juya yana nufar dakinsa.


Dadi ya kama hafsat dake labe,saita koma bakin gado ta zauna tana kada qafa a hankali,itakam gaba ta kaita,dole yau ya kwana dakinta,sannu a hankali dai gida yana shirin dawowa hannunta sai yadda ta juyashi, murmushin nasara da farinciki ya kubce mata.
[5/8, 2:56 PM] Sweet sis: *H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*


*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02




Page 09




Yana zaune saman kujera sanye da uniform din nan nasa dake qara masa kyau da kuma kwarjini,ko boots din qafarsa baikai ga cirewa ba,hafsat na tsaye daga gefansa,hannayenta goye a qirjinta,fushi ne kwance saman fuskarta.


Idanunshi a kanta,wani abu daya kasa tantance meye yana tsinkulin zuciyarsa,mabanbantan abubuwa guda biyu daketa faman gogayya da juna,har ta iso ta zauna gefan kujerar dake daura dashi tana masa sannu da zuwa.


"Me ya hadaki da hafsat.....har kikayi mata rashin kunya?" Maganar tazo mata a bazata,mamaki ya kamata,ta dubi hafsat din suka hada ido,sai hafsat din ta aike mata da saqon harara,ta daure ta shanye sanann tace


"Ni bansan yaushe nayi mata rashin kunya ba"


"Kina nufin bakisan maganar kayan da kika kwashe ba?" Ta tambayeta kamar wata diyar cikinta,sai abbas din ya daga mata hannu


"Ya isa.....me yasa kika kwashe kaya da aka dawo dasu daga laundry?" Cak ta tsaya ta zuba masa idanu,mamaki yana kasheta,duk yadda taso hana taruwar qwalla a idanunta amma ta gaza,saita gyada kai tana hadiye wani abu mai tauri daya tsaya mata,cikin rawar murya ta fara masa bayani


"Baba mai gadi ne ya kawo su,tana.bacci yace a kwashe maka kada yara su tattaka,don ma debe shine nayi laifi?,ina cewa kusan kaso uku cikin hudu na kayanka suna dakinta a wajenta,na taba magana?" Sosai ta taba zuciyarsa yadda hawaye ke sauka saman fuskarta,tana kuma maganar muryarta tana rawa cikin sautin kuka,yanason yace ta tashi taje,tayi dai dai amma kuma kamar ana ingiza zuciyarsa,kamar kuma ana hura masa bacin rai haka yakeji.


"Tashi kije ki debosu!" Yadan fada a kausashe,idanunta ta sanya cikin nasa mamaki yana sake daskarar da ita,totally uncle abbas din canzawa yakeyi cikin kwanakin,ba yau ya fara ba amma na yau yafi qona mata rai da tsaya mata a rai,ba yau ya fara ba,cikin kwanakin ko meye hafsat din tayi gaskiya yake bata,yana kuma qoqarin goyuwa da bayanta,sai ta miqe tsam cikin matsanancin bacin rai,ta dauke idanunta daga kansa ta maida ga hafsat,sai taga tuni yanayin fuskarta ya sauya zuwa madaukakin farinciki.


Janye idanunta tayi daga kan fuskokinsu gaba daya,ta kuma juya da sauri ta nufi dakinta, abbas ya rakata da idanu yana jin kamar ya bita amma kuma wata zuciyar na gaya masa yayi dai dai,sai yaci gaba da kallon qofar da kuma tsammanin fitowarta.


Cikin bacin rai ta fara tattara dukka wani abu da tasan nashi ne cikin daki,bata bar komai ba koda kuwa agogo ne,tana hade kayan hawaye na fita a idanunta,ta tsani rashin gaskiya,ta tsani a bata rashin gaskiya a rayuwar ta,ta tsani batayi abu ba ace tayi,tana jin kamar ta mutu idan akayi mata haka.


Debo kayan ta fara yi hannu bibbiyu,ba ruwa ta da wadanda suke zubewa ta riqosu zuwa falon,tana zuwa batayi wata wata ba ta watsar dasu a wajen ta juya da sauri taci gaba da debo sauran tana zubarwa a wajen,ran hafsat ya sosu sosai,wanne irin raini ne wannan?,ta tsammaci zaice wani abu,sai taga bai ko motsa ba yana kallonta ne kawai,yana karantar zallar fushin dake fuskarta,wanda bai taba ganin irinsa ba a tattare da ita ba


"Wai baka ganin abinda yarinyar nan takeyi?,kaga fa yadda take watso mana kaya?" Maganartata yayi da gama kwaso kayan,ta juya abinta da nufin komawa dakinta


"Widad" ya kirata a tausashe,bata ko waiwayo ba bare ta saurareshi,don kuka takeyi sosai ta wuce daki abinta.


Cikin qarfin ikon Allah ya miqe da wani irin zafin nama,zuciyarsa yaji kamar zata fashe da kukan da widad din keyi,ya tuna meye a jikinta,ta yaya zai barta tana irin wannan kukan?,sai ya nufi dakin da wani irin sauri wanda yasa hafsat ta zaci zuwa zaiyi yayi maganinta,ya dauki mataki akan abinda tayin yanzu,don haka ta saki wata qaramar dariya cikin nishadi da jin dadi,ta tako cikin rashin damuwa ta fara tsince kayan tana dibansu zuwa dakinta,sai a sanann ta lura da mimi dake sharar qwalla


"Ubanki kike a wajen?,wato an saka uwarki kuka shine kikazo kika rabe a nan kina naki kukan,zaki tashi ki wuce ciki ko sai nayi ball dake?" Ba shiri yarinyar ta zame ta wuce daki tana tura baki gaba hadi da ci gaba da goge qwalla.


Rub da ciki takeso tayi kukanta yadda takeso ko zata rage zugi da radadin da zuciyarta ke mata,amma tudun da takeji a cikinta ya hana,dole sai saman pillow ta dora fuskarta tana sakin kuka sosai.


Jiki a matuqar sanyaye ya qarasa shigowa dakin,sai ya kasa qarasowa ya tsaya daga bakin qofa yana kallonta,shi kansa baisan me yake damunsa ba,baisan me yasa yake wasu abubuwan ba,duk da abinda yakeyi din bata taba nuna damuwarta ba,koda ta nuna mintuna kadan take sakin fuskarta kamar ba'a yi ba,sai ayau data nuna fushinta har haka.


A nutse ya qaraso ya zauna gefanta,tunda ya buda mata qofar daki tana jinsa amma bata nuna tasan da shigowarsa bama,hannu yasa a tausashe ya zare pillow din ya maye gurbinsa da tattausan tafin hannunsa,sai tayi saurin kawar da fuskarta daga wajen kamar ya dora mata wuta,yasan halin kayarsa,ta iya rigima a duk sanda taso ko aka tabota,don haka yayi amfani da dukka qarfinsa ya azata saman jikinsa.


Dukka qarfinta ta sanya ta zame a jikinsa,bai gaji ba ya sake maidota yana kiran sunanta tare da qoqarin son su hada idanu amma taqi bashi wannan damar.


Kin zama tayi bare ta saurareshi ba,haka ya gaji da son yin magana da ita ya haqura ya fice yana sauke ajiyar zuciya,ransa gaba daya a jagule babu dadi.


Da kanta ta lallashi kanta,saidai a ranar ta yiwa kanta hukunci qauracewa abbas din da dukka abinda ya shafi hafsat dama cikin gidan,ba zata iya gani ba bazata iya jura ba,duk jarumtar ta abun ya taba ranta,tana iya bakin qoqarin bashi farinciki da son ganin walwala da nutsuwarsa.....gefe guda yana bawa hafsat go ahead tayi duk abinda yake shine dai dai,yana kuma mara mata baya,ta yaya ita tata zuciyar zata samu nutsuwar bashi nutsuwa?.


Washegari ranar girkinta ne,tun safe tana kwance a dakinta wanda tun dare ta saka muqulli ta rufe abinta,tana da abubuwan ciye ciye da yawa a dakinta da bata rabo dasu,don a lokacin abbas da ya shafe babin fita da iyalinsa zuwa wasu guraren shaqatawa a baya,a yanzu widad din ta dawo masa da wannan dabi'a tasa,ko rana daya hafsat din bata taba yunqurin binsu ba,sai mugun haushi da takaicin da take fama dashi,har zuwa sanda zasu dawo cikin gidan,takan ce ita tafi qarfin zuwa nan wajen.


Zamu iya cewa borin kunya ne takeyi,don tun sand yake marmarin kaita take watsa masa qasa a ido,take nuna tafi qaunar ya bata abinda za'a kashe a wajen ta adana,har abun ya fita a kansa,ko ssnda ta haifi su mimi yana son kaisu amma bai samu wannan qwarin gwiwa daga wajenta ba,don haka sai a jima bai fita da yaran ba sai sanda ya samu hutu mai tsaho,gaba daya ita din opposition na rayuwarsa ne totally,bata kuma taba sawa a ranta ta sauya wani tsari yanayi hali ko dabi'a tata saboda shi ba,saboda a samu dai daito da zama me dorewa.


Tana jin motsinsu daga parlor din amma bata ko motsa ba bare tayi yunqurin fitowa,ciye ciyen da tayi a daki ya dauketa fes,don dama bata iya cin abinci me yawa,yana zaune dining area amma hankalinsa yana kan qofar dakinta,jiya da abun ya kwana dashi ya tashi,duk kuwa da yadda hafsat din keta qoqarin mantar dashi da wasu salo da sam baibi jikinta ba bare ya dace da ita,don ba dabi'arta bane.


Ya kammala shan tea din da babu qamshin komai a ciki saina Lipton da milo,ya ajjiye cup din ya miqe yana sauka daga wajen,hafsat din na zaune tana kallonsa batace komai ba,tanason ganin ya za'a qare,ya isa qofar dakin nata ya tsaya a nutse ya fara knocking yana amsa wayar data shigo masa a lokacin.


Taso ta shareshi taqi bude qofar,saboda Wani mugun zafinsa da takeji har cikin ranta,amma sai taga hakan bai kamata ba,tunda tasan a lokacin kowa yana parlor,ta kuma tabbatar hafsat din tana ganin komai da zai faru,don haka ba'a son ranta ba ta miqe a hankali tana gyara zaman yaloluwar rigar jikinta ta zura bedroom slippers dinta ta nufi qofar.


Tana bude masa ta saki qofar ta koma,yabi bayanta da kallo tsigar jikinsa tana zubawa,ko kadan baya gajiya da ita,baya qosawa da ita,kwanaki biyun da basu tare mugun yunwar ta yakeyi,yaci gaba da kallonta yana dan hangen cikinta daya turo kadan,wanda sai ka saka ido da tsananin kula zaka iya ganinsa.


Guri ta samu ta zauna ta gaidashi ba tare data kalli fuskarsa ba,yanata qoqarin su hada ido amma taqi


"Ya jikin naki?"


"Lafiyata qalau" ta amsa masa a shashance,ya sake duban fuskarta sosai yadda taketa basarwa,sai ya ajjiye mata kudin cefane yayi mata sallama ya fice.


Dashi da kudin gaba daya tabi da kallo, zuciyarta ta tsinke kuka yaso qwace mata amma ta danne,ta kalli agogo sannan ta miqe ta shiga bandaki ta watsa ruwa,ta fito taa shirya cikin dinkin doguwar ruga bubu gown ta yane kanta da madaidaicin mayafi ba tare data daura dankwali ba,fuskarta tayi kyau,ta sake wani fresh da haske mai daukan idanu,inda ya ajjiye kudin cefanen ta isa ta dauki kudin,sannan ta qarasa inda wayarta take ita dauketa tare da daukan wasu abubuwan masu amfani sannan ta fito falon.


Babu kowa,sai ta zarce kitchen,ta dan samu abinda zataci wanda bazai mata wahalar narkewa ba,don yanzun matsalar da take fama da ita kenan.


Ta gama ta dauraye cup din ta maidashi inda ta dauko tana kallon yadda kitchen din ya hargitse,kamar ba kwanaki biyu baya ya koma hannun hafsat

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login