Showing 15001 words to 18000 words out of 19791 words
Chapter 6 - Sanadin Boko Book 4 end complete by Halima Abdullahi k Mashi .txt
har abinci ya kamata ace
duk wata kana sai musu ko buhu dai-dai ne." Ya ce, "Zan
soma daga wannan watan Insha Allah, kai yau naji dadi
ashe haka mutum ke samun farin ciki in ya faranta ma
Iyayenshi?" Na ce, "Sosai ma kuwa.Ya ce, "Na gode
Allah da ya bani mace ta gari, yanzun fada min bayan su
ko akwai wadanda ya dace in sai ma kayan Sallar?" Na
ce, "Su Lamido da duk kanne da yayin Babanka, ka sai
musu kowa wanda ya dace da shi zasu ji dadi."ya ce,
"To gobe zamu koma kasuwa kenan." Haka ya kaini gida
yana ta shi min albarka, sannan ya tafi gidan Fadima ya
kwana.
Washegari mun shiga kasuwa harda list din mutanen don
kada a manta, lallai kudi sun mutu a ranar, alheri sai
bawa ya dage, amma in kayi dadi ka ke ji, shi kuma
wanda ka wa yana jin dadi. Ya ce, "To wanene zai kai
musu?" Na ce, "Ka samu Hashim ka ware rana kayi ta
kai musu." Da suka dawo kuwa Hashim sai labarin yanda
Iyayen suka yi ta murna da godiya ya ce Abbanshi, Sarki
kenan, har gori ya mishi ya ce, "Hashim kalubalenka, sai
ayi koyi da Hamma." Na yi murmushi, na san kowa zai
yaba don kaya ne na alfarma da takalma da hula.
Hashim ya ce, "Allah ya nufe ni nima." Ranar ma godiya
yayi ta min, su Lamido ma suna ta shi masa albarka,
wanda ma baya nan in ya dawo gida ya gani sai ya kira
waya yana sa albarka. Allah kasa mu dace amin.
Saura sati biyu Sallah Abubakar ya ce min yana son ni
da shi mu tafi Umara, don haka ma in tashi muje inyi
fasfot. Na ce, "A'a da Fadi ya dace kuje." Ya ce, "Ba
zata iya zuwa ba." Na ce, "Ina tsoron abin da zai ja min
bakin jini cikin zuri'arku, amma ka je ka shawarci
Daada." Ya ce, "Shi kenan" Ko da ya samu Daada da
batun sai ta ce mishi ya bari mun je aikin Hajji
dukkanmu, kada ya zama abin tsegumi ace ya kai bare,
amma Hajji kafin lokacin ta haihu. Ya dawo ya ce min
bakinku yazo daya da Daada. Na ce, "Ka gani ko? In kaje
ka samu a addu'a." Ya ce, "Wannab ba sai kin roka ba.
Ni dai na so inje da ke ne saboda mu dan shakata." Na
ce, "Wata rana zamu shakata. Koda yanzun ma ai mun
sha iska." Ya yi 'yar dariya.da xai tafi ya bar ma kowa
komai, na ce xan je kaduna da salla, ya ce a'a in bari ya
dawo ma je tare na ce to.su Ummina sun xo min da salla
har da Yaya Umar, nayi murna sosai kwanansu 2 suka
tafi da Shadad, na ce su bar min Ummi in xamu xo sai
mu xo da ita. Bayan sallah da kwana 3 xaya dawo,nasan
kuma gidana xaya sauka, domin yana fada min irin yadda
yayi missing dina,ko na ce muka yi missing din juna.Tun
safe na soma shirya masa girki kala-kala da abin sha, jus
nayi mas kusan kala 3 n akuma hada nawa hadin mai
kyau nayi ta sha tun safe.misalin 3 ina tsaye gaban
madubi nayi adona ckn 1 daga ckn atamfofin daya siya
min,sam banji shigowarsa ba,sai dai ji nayi an rungeme
ni ta baya kamshin turarensa yasa na gane mijina ne.da
sauri na juyo muka makale juna cikn murna, ya sumbaci
lebunana, sannan ya ce bari mu isa gidan Fadi, sai in
dawo. In na xauna ba xan iya tafiya ba.xamu wuce ne da
Hashim daya dauko ni naga ba xan iya wucewa ban
ganki ba,na ce to in ka san ba xa ka dawo ba to ka wuce
da abinci.Cikin marairaita nayi maganar,ya shafi
kumatuna. kada ki damu d only yanxun xan dawo naji
gidan na kamshi na ce to "Da sauri ya shige mota suka
tafi.kafin ya dawo na kara gyara gidan, na canza kaya
doguwar rigar leshi nasa mai kalar sky blue, su hudu
suka shigo duk da Hashim.na jera musu abinci da na sha,
in adaga daki ina jiyo su suna santi.Hashim ya ce,
Hamma gaskiya xan kullo ma Hafsat kawance da Shatu,
ina son taxo ta koyi kalolin girkin nan, Dayan ya ce na
riga ka a xuci ka riga ni a baki, shi ko dayn ba shi da
mata, cewa yayi xaya kawo budurwanchi ta yi hadda.shi
kuma Abubakar sai murna da cika baki. fadi ya ke
"Matata yar baiwa ce, duk abubuwanta cikin ilimi ne da
daraja girkin Hafsat daban ce.Amma fa ba xa ku takura
min mata ba, da Ummi taxo tana kwashe kayan bayan
sun gama,Hashim ya ce ko dai xan tsaya nan ne Hamma
ka tsaya min a bani wannan in kiwatat?Abubakar ya ce
"Katon banxa wa xai baka?suka sa daria.Misalin karfe
tara saura muna ta shirin kwanciya, Fadi ta kira shi ya
daga ta ce"sweet hrt ba nan ka ke ba?ya ce "In ji wa?ta
ce Eh!! mana yi lassafi.Ni dai wlhy kada ma ka ce xaka
kwana can, don ba xan yafe ba.Duk ina jin su, kuma ba
gidanta xai sauka ba, saboda randa xai dawo gidana ya
tafi.Na ce to koma can din , ya ce ba xan koma ba, tana
xaton ban san me nake yi ba?ya share ta muka ci
soyayyarmu, dama mun yi rashin juna.Wata juma'a
misalin 3 muna cikin bacci wayarsa ta soma kuka, ni ce
na farka na daga.Sweet hrt na gnai a jiki na daga, Muryar
Goggo Jami naji tace, "Ina Hamma din?N ace "yana
bacci "Ta ce to tashe shi Fadi bata da lfy shi bacci ma
yake?a raina nace kada yayi? Namatsa kusa dashi na
shafa fuskarshi, ya rike hannuna zuwa kirjinshi, nayi
masa rada cikin kunne.
Mr Cool ka tashi yau twins zasu fito, Fadi zata haihu."
Firgigit! Ya mike ya zura jallabiyya ya dauki key din
mota.
Na ce yanzun zaka fita?" Ka bari a kira Sallah."
Ya ce ba komai kada ki damu, na ce to Allah ya raba su
lafiya." Ya ce "Ameen the only."
Takwas na safe na kira shi, ya ce har yanzu dai shiru, na
ce gani nan.
Na isa gurin na samu 'yan gidan su, sai su Rukayya. Shi
kuma can na hange shi tare da su Hashim da Usman
kaninshi.
Na gaida su Goggo Jamin, sannan na nufi gurinshi.
Rukayya harda cewa 'yan biyun nan suna ba mamansu
wahala, Allah yasa kada zuwan wasu yasa abin ya sake
rikicewa.
Wata da ban san ko wacece ba, ta ce ai mun rike Allah,
kuma sai ta sauka lafiya da izininshi.
Ban da lokacinsu bare amsarsu, don nasan dani suke,
gurin mijina ma ni na nufa.
na dube shi har yanzu ko? Na yi maganar ne cikin nuna
tausayawa da tausasa murya.
Ya ce, wallahi, na matso na kama hannunshi na dama na
matsa kadan. Ka da ka damu samu ruwa a tofa mata
addu'a, In shaa Allah zata sauka lafiya.
Goran Ruwa ya kawo na karanta mata, YA HAYYU YA
KAYYUM, YA ZULJALALU WAL IKRAM, BIRAHMATIKA
ASTAGISU, sau bakwai na ce ya bata tasha.
Da kanshi ya kaimata tasha, ya fito, ko minti ashirin ba a
yi ba Nurse ta fito da murna tana fadawa su Goggo Jami
ta sauka.
Kawai sai naji mutum ya rungume ni a bainar jama'a
yana fadin "Alhamdulillah." Usman ya ce "Aunty na Allah
ya amshi Addu'armu, sai dai kuma me? Maimakon biyu
sai aka fito mana da yarinya katuwa mai kyau.
Sai kace mamanta tayi kaki, aka amsa da murna ana
cewa ina dayan? Wannan ce Hassana kenan.Nurse ta ce
ai daya ce, ita kenan aka haifa. Yanzun haka mai jegon
ana gyara mata jiki.
Gaba daya sai naga jikinsu yayai sanyi, har shi kanshi
angon karnin. Usman ya ce amma 'yan asibitin nan sun
cika shegiyar karya, shine suka ce biyu?
Doctor ya fito, su Hashim suka bishi suna tambayarshi,
"dama daya ne? Ya eh ai dama daya ce duk scanning
dinta bai taba nuna biyu ba, wa ya ce biyu ne?
Abubakar ya ce "ita ce" likita yayi tsaki ya ce "haka
wasu matan suke yi ban san amfanin hakan ba, alhalin
sun san cewa akwai ranar irin wannan da za a kure su.
Ya dafa kafadar Abubakar "kada ka damu, ka yiwa 'yarka
addu'a Allah yasa mai albarka ce."
Duka suka ce "Ameen" Masu habaici da rawar kai kowa
dai baki tsuu, shiru kake ji. Kullum nake zuwa gidan mai
jego har ana jibi suna.
Ranar da ya kawo mata zannuwan fitar suna ta ce basu
yi mata ba, ranar ce ya amayar mata da takaicinshi a
gaban 'yan koran nata.
Ya ce "ki bini a sannu, banza makaryaciya, zan
maganinki, kuma in na dawo baki dauki kayan nan ba sun
zama ba rabonki ba.
Ki sani ko bari kika yi zan so shi, bare dan mutum. To
meye ribar karyar da kika yi kika sa muma muka yi?
Mutuncin ki ya zube a gurina da sauran mutane. Sannan
baki isa ki juya ni ba, kinfi kowa sanina.
Zata yi magana ta rike kugu, ya ce yi min shiru, in kin
furta wata magana zan bata maki yanzun nan.
Ta yi tsit, ya fice. Nan ta shiga kuka suna bata hakuri,
Rukayya tana cewa sai ta fadawa Dada da Abba.
Yarinya taci suna Nana Fiddausi, in da ni kuma na
shiryawa Abubakar kalolin girki kusan bakwai da kayan
drinks.
Suka yi walima, Ummi da kanwata Ummi sune yan taya
aiki.
Bayan suna da sati daya muka je Kaduna don maida
Ummi tare da dauko Shadad daga gurin babanshi.
Har da Umminsu ta mana rakiya don sun kulla kawance
da Umminmu,saboda xaman mota sai kafafuna suka
kumbura,sannan nayi ta shar amai,duk Abubakr ya rude
hankalinsa ya tashi.kafin kace haka na kwana
shrkaf.muna isa kaduna asibitin Garkuwa ya wuce dani,
da gudu-gudu aka kawo gadon tura mara lafiya aka yi
ciki dani,likitan yana duba ni yana mishi tambayoyi,tana
da ciki ne?ya ce kai bana xatao, sai dai ko in yanxun.
likitan ya maida allurar da yayi niyar yi min ya aje,yasa
aka tura ni xuwa dakin scanning, kusan min 30 aka fito
dani yaxo ya dauko ruwa aka yi wasu allurai a ciki,
sannan aka dora ni ,ana da nan bacci yayi gaba
dani,likitan ya kalle shi"matarka tana da ciki kusan
wata 5 ko ma fi,sai in ta farka nayi mata wasu
tambayoyi tukunna. Abubakr ya tsura mishi ido,kace
tana da ciki wata 5? likitan ya ce kila ma ya fi.
Abubakar dai yayi shiru,amma ba don ya yarda ba, ya
kira Umar ya fada masa kusan minti 30 suka iso dasu
Baabah.Sannan ban tashi ba, ya ce don Allah yaya
umar ya kai su Ummi gida don suna ta kuka,kujera
Abubakr yaja ya xauna ya rike min hannu su Baabah
sai waje suka fita don kunyar yanda ya tasa ni gaba
kamr xai cinye ni.ya kira su Hashim ya fada mishi su
Daada ma ya sanar da su,kusan wa daya na farka.Da
sauri ya tashi yasa hannunshi a kuskata, yana cewa
"Sannu Hafsat sannu.Na ce yauwa Na yunkura xan
tashi ya kama ni na xauna ya xauna gefen gado. Ina ne
ke miki ciwo yanxun?nace "Ba ko ina yunwa nike ji,
bakina ya cika da miyau,na ce xan xubar "ya miko min
wata yar tasa sannan yace bari in kira likitan.Da sauri
ya fita ya ce ma su Baabah na farka, suk shigo suna
min sannu, na amsa na ce ni babu gurin da ke min
ciwo,yunwa kawai nake ji (dama cin abinci a gurina tun
dana samu cikin nan kmr gara)suka shigo da likitan aka
ce su fita Abubakar kuwa xama yayi kusa dani likitan
ya ce "Madam cikinki wata nawa ne?Da sauri na kalli
Abubakar sannan na sunkuyar da kai.Ya ce "Fada min
mana "Na ce na zaton cewa xai kai shidaa."Abubakrya
dago idona ina da yaro dan wata shida a gurinki, ina me
ban sani ba?likitan yayi daria,'kila tana son ta baka
mamaki ne ko?na ce"Ina son in ci abincin. Da sauri
likitan ya ce me xa ki ci?na ce "Tea xan sha.Nan da
nan yayi waya a kawo min tea.Abubakr kuwa cikin
rigata ya xura hannu yana shafa cikina yana min
magana a kunne."d only me yasa kika rufe min?na ce
To kana fama da mara lfy sai nima in kwanta mu taru
mu daga maka hnkl?Ni ba xan iya ba, bana son in
ganka ckn damuwa,shi yasa na daure. ya ce "Allah yi
miki albarka, dama nasan kece mai son kwanciyar
hankalina. bayanna huta ya sallame mu muka nufi gida
sai yau naga gidan da aka sai masu Baba a nan dai
Abuja Road din ne amma can kasa gurin sabon guri ne
kuma gida mai kyau flat.
.. Abubakar kam da ya fita sai ya je ya kama masauki,
sai dare ya dawo. Ya ce na zo muje, bansan ko ina
bane na cewa su Baba ina zuwa.
Sai kurum ya kaini masauki, wai nan zamu kwana, na
ce "Haba Mr Cool, ka maida ni gida mana su Baba zasu
ga rashin kunyata."
Ya ce, "Bazan iya barinki ba, bakiji Likita ya ce na kula
dake sosai ba?" Sai waya nayi wa su Baba na ce munje
gidan wani abokinsa can zamu kwana.
Suka ce to, kwanan mu uku, kullum da safe zai kawo ni
amma da dare zai zo ya tafi dani.
Wata sabuwar soyayya da tarairaya Abubakar ya soma
yi min, da zamu koma gida jirgi muka bi.
Muna isa ya fara yadawa ina da ciki, dama Likita yace
in mun dawo na soma yin awo.
Shine ya kaini asibitin ya yankar min kati, a dakin
scanning Likita ya ce "Madam kin san cewa 'yan biyu
ne?" Na zaro ido "'yam biyu?" Ya ce "kwarai kuma kin
gansu duk maza"
Na ce ba a fi sati daya ba da akayi min scanning a
Kaduna ba a fada min haka ba."
Ya ce to yanzun dai gashi nan" na ce to don Allah ka
taimake ni kada ka rubuta a cikin sakamakon"
Ya ce "don me?" Na ce "Don haka ta faru ga kishiyata,
a karshe sai ta haifi mace guda daya."............
Zaharaddeen Shomar
whatsapp 08168575100
Sabadin BOKO 4-07
Posted by ANaM Dorayi on 05:21 AM, 29-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Ya ce to shike nan, ya rubuta komai lafiya amma bai
rubuta mace ko namiji ba, bare ya saka 'yan biyu.haka
naci gaba da samun kula, yanzun da asiri ya tonu sai
cikin ya fito yayi rum.
Da da ba a sani ba kuwa lakwam, har cikina ya kai wata
takwas ban taba yi masa batun kayan haihuwa ba.
Shi ne da kashi ya ce "wai the only baza mu sayo kayan
haihuwa ba? Na ce to, sannan muka je ni da shi da
Ummi.
Wata safiya na tashi da matsanancin ciwon ciki da mara,
gashi ya je Lagos amma ranar zai dawo.
Da ya kira duk da koakrin da na ke na nuna masa bani da
wata matsala sai da ya gane.
Ya kira Dada ya ce a zo a duba ni lafiya? Ummi ce ta zo
har ta tafi ban bari ta fahimci wani abu ba, tunda ciwon
yana yi ne yana lafawa.
Kafin dare na jigata, lokacin da ya shigo fayata ta fashe
haka suka kwashe ni zuwa asibiti.
Da Lamido na fadan me ya sa naki fadin banda lafiya,
sai su Gwogwal suka ce ai kunya ce.
Lallai ni yar mutunci ce, ni ba fulani ba amma ina da
kunya. A raina na ce kunya ai ta dan sunna ce bata
Fulani ba.
Don haka duk Musulmi mai Imani zai zama yana da
kunya.
Da kaina na haihu, dana kato zuwa can kuma sai
sabuwar nakuda, sai kuma ga wani dan.
'Yan biyu masu kama da juna, sannan duk wanda ya
kalle su yasan 'ya'yan Abubakar ne.
Tunda Nurse ta kawo na farko Abubakar ya ke ta murna
da su Hashim, sai ta ce zaka bani goron albishir ina
zuwa.
Da tazo da dayan sai suka kama murna, kafin ka ce
haka, dangi sun cika asibitin harda su Rukayya.
Ni dai na ga lele, Fadi ko leke don ko da ta sami labrin
ina da ciki bata zo ba.
Lamido har asibiti ya zo, kwanana daya aka sallamoni
zuwa gida. Tun a ranar Lamido yasa aka kada Sa aka
yanka, nima yan uwana washe gari suka zo tare da su
Rahma.
Abubakar tamkar ya goya ni don kauna. Ranar suna
kuwa fadar shagalin da akayi bata baki ne.
Kyauta dai mun samu Masha Allahu, nayi kyau mai zane
fulawa ta yarfa min nayi kyau har na gaji.
Mun sha hotuna, Abubakar kuwa da abokansa tare akayi
suna dasu.
Na cii gaba da shayar da yarana kuma ana basu madarar
M.S.A, suka yi tubarkallah.
Mijina kullum kara son mu yake. Fadi kuwa na sama
kanta damuwa, kullum ita kenan fada da miji ko a gaban
waye sai tayi ta karta masa rashin mutunci.
Yanzun ma sun raba jiha da Rukayya, dangin mijina
tamkar su cinye ni don so.
Tunda na gama service na samu aiki a gidan TV na Yola,
amma Abubakar ya ce sai yara sunyi kwari.
Ban ja musu ba, watansu shida na soma zuwa aiki na,
bayan ya mallaka mana mota ni da Fadi kowa da tashi.
Bani da matsalar rainon yarana don rubibinsu ake yi.
Account na bude ina zuba albashi na. Domin akwai burin
da naci dasu, tunda ba abindana nema na rasa.
Daidai da katin waya sai Abubakar ya zuba min dubu
biyar dubu goma, nayi kyau da ka ganni kaga matar so.
Gyaran jiki kuwa da sabbin girki ba a magana. Shi kanshi
mijina duk wanda ya kalle shi yasan matarsa tana son
shi.
Kusan in mutun yana cikin kwanciyar hankali daka kalle
shi zaka gane, musamman namiji.
In kaga namiji a hargitse a rame ton ba halittarsa kenan
ba to kila bai dace da mata ba.
Duk ranar da babu aiki na kan ce ya kawo min Nana
Fiddausi, ina son yarinyar don ina son mace.
Fadi bata son ya kawo mata 'yarta gurina. Amma
bayanda zata yi, tunda baza ta iya hana shi daukar
'yarshi ya fita da ita ba. Sannu a hankali rayuwa tana
tafiya kwanukan mu suna karewa, lamurra suna
canzawa.
A hankali na rika dora mijina kan hanyar taimako dukda
cewa yana yi dama.
Lokacin da ya gina sabongida Lamido yace ya saka ni a
ciki saboda ya yarda ni na zama daya daga cikin
zuri'arsu.
Na cancanci in sakata in wala a zuri'arsu, komai sabo ya
saka min, gado dan italiya, kujeru na alfarma, kayan kicin
na gani na fada.
Itama ya sa aka mata fenti ya canza mata kayan
daki.Nayi walima ta alfarma har su Rahma sai da suka
zo, gidan ya tsaru harda gurin wasan yarana.
A ranar farko da zamu kwana a gidan yana zaune yana
waya a bakin gadon dakinsa na alfarma.
Na shigo sanye da kayan bacci, da hannunshi ya nuna
min cinyarshi in zauna, ya ce "Alhamdulillahi, gida ya
dace dake."
Na ce yanzu saura ka gina dakin Allah (Masallacin
Juma'ar) ungwar nan ka sabunta shi. Sannan ka gina
wanda za a dinga kamsus-salawati, a wannan layin da
muka dawo.
Ya ce "an gama gimbiya, yanzun sai ki zabi wanda za a
ba kwangilar ginin."
Na ce duk wanda ranka ya kwanta dashi. Mai amana."
Ya ce "To zan duba." Hakan ce kuwa ta faru nan da nan
aka soma gini.
Taimako marasa lafiya, gajiyayyu da marayu duk na
kwadaita masa yasan zakinsu. Yana mutunta iyayena
tare da taimaka masu.
**********
Shekarar yarana daya da wata biyu, naji ban gane kaina
ba. Hankalina ya tashi matuka. Ranar Abubakar yana
gidan Fadima, na mashi text cewa zanje asibiti, ya ce
Hassan ne ko Hussaini ba lafiya?
Na ce "Ni ce" ya ce sai ga kiran shi, ya ce meke
damunki the only? Sai kawai na saka kuka na kashe
wayar.Minti ashirin sai gashi ya zo. Kayan bacci ne ma
a jikinsa, me aiki na ya samu tana kara goge kicin.
Ya ce "ina take?" Ta ce ina ciki sai gashi na tasa
'ya'yan idanuwana jajir, ya ce wai lafiya? Na soma
sabon