Showing 3001 words to 6000 words out of 17050 words
ba,,to idan barci kake ka farka ka tuna wane ne kai ".
Murmushin takaici yayi tareda fadin " Ko zakisaka kaina gabas ki yanka mama baxan fasa fada ba me martaba bai yanke hukunci ckn adalci ba saboda bai hada da niba,kuma mgnr yarima sameer Wannan rayuwarsa daban tawa daban,saboda haka nima a yanzu zanje na rufe kaina a kuskuku har zuwa lkcn da mai martaba ya dibawa muwadda,,yakarasa yana kokarin fita,,A fusace me babban daki ta fuzgoshi idonta har yasauya saboda bacin rai,,ckn masifa da takaici tace "Yarima yusufu kana ckn hayyacinka kuwa???,,kasani Wannan shine mafi girman kaskanci da zakayiwa kanka a masarautar nan, wace ce kuyanga muwadda da zaka damu saboda an rufeta,to inaso kasani indai ka aikata abinda kafada wlh saina wulakanta kuyanga muwadda a garinnan,sai na maidata abin kyama a wajen kowa idan kayi musu jeka ka aikata.
Murmushin takaici yayi tareda matsowa daf da ita yace " Narantse da Allah mama abinnan da kika lissafo indai ya tabbata akan kuyanga muwadda to tabbas zai tabbata akan danki yusufu,don zan koma kaskantacce mara yanci ko kadan,,A fusace ta fuzgosa ckn matsanancin Bacin rai tace "Me kake nufi???.
Babu abinda nake nufi face abinda nafada ynz,yana gama fadin haka yafice daga dakin a fusace.
Sharaf ta zube akan kujera ckn matsanancin bacin rai,kallonta takai kan fulani wadda tasaki baki da hanci tana kallon ikon Allah,ckn bacin rai me babban daki tace " Tabbas fulani yazama dole nadauki tsatstsauran mataki mafi muni akan kuyanga muwadda".
Girgiza kai fulani tayi tareda fadin "Karkiyi haka me babban daki, wlh abinda yarima yusufi yafada har zuciyarshi ne,saboda haka ko wani Abu zaki aikata kibari daga baya amma ba ynz ba,,shawarar da zanbaki ynz kije gurin me martaba ki rokeshi a fito da kuyanga muwadda ko dan rayuwar danki.
Ajiyar zuciya me babban daki tayi tace " Anya kuwa fulani me martaba zai fito da kuyanga muwadda???kinsan halinsa idan ya yanke hukunci kaifi daya ne.
Hakane amma kije ynz ki jarraba.
Mikewa tayi ckn sanyin jiki tace "To bari naje,,Tana gab da fita sukayi karo da mufeedah zata shigo,,ckn iyayi mufeeda tace " Yawwa mama gurinki fa nazo,Wai yaushe yarima na zai dawo ne??Wlh na kagu yadawo kimasa mgn ta.
Ckn kosawa da mgnr mufeeda tace "Nan da kwana takwas",,,Wani mugun tsalle mufeeda tayi ckn matsanancin farin ciki tayi hugging me babban daki tareda fadin " Wayyo dadi yarima na zai dawo".
Ckn takaici me babban daki ta yakiceta daga jikinta tafita don abinda ke damunta ma ya isheta.
Mufeeda ko kulawa batayi ba ckn murna tadinga kissima gata a faffadan kirjin yarima anyi aurensu suna soyewa,A fili tace "Gimbiya jalila kinkusa wulakanta".
Yarima yusufu yana fita kurkuku ya nufa ,yana zuwa yacewa ma'aikatan wajen su bude yashiga su rufeshi,ckn mamaki da tsoron abinda zai biyo baya sukace " Ranka ya dade a rufeka fa kace??".
A fusace yace "Ehh ko bazaku bude bane??.
Russuna sukai tareda cewa " Allah ya huci ran yarima ai mana aikin gafara",,daya daga cknsu ne yadauko mukulli ya bude katuwar kofar kurkukun,,cire alkyabba yarima yusufu yayi yabasu sannan yashiga wajen".
Sudai gabadaya a tsorace suke,don tashin hankali ne aga yarima a kurkuku, amma ba yanda suka iya tunda umarnin yariman ne.
Saboda tsabar kuka idanun muwadda har sun kankance sosai,gawani yaji da suke mata,sun kunbura sunyi suntum tareda matsanancin ja,hakama fuskarta gabadaya tayi jajir musamman kan hancinta,tunanin mahaifiyarta kawai takeyi musamman da lokacin tafiyarta gida yayi,tasan ynz iyarta nasan tana jiran sallamarta,kuma ta tabbata bataci komai ba,,kukan zuciya takeyi sosai don na filin ma yadaina fitowa ynz.
Ubaida ce ta lallabo tazo wajen me gadin kurkukun da muwadda take,tsoho ne mutumin sosai,ckn girmamawa ta gaisheshi tareda fadin "Don Allah baba kaimin taimako naga kuyanga muwadda ko na dakika 5 ne.
Zaro ido tsohon yayi ckn mamaki yace " Ki turamin asiri yarinya,idan ba so kike nima a rufeni ba".
Ajiyar zuciya ubaida tayi don tasan Gaskiya tsohon yafada,ckn sanyin murya tace "To dan girman Allah baba kaimin wani taimako zanbaka takadda ka kaimata",,Shiru yayi nawani dan lkc kafin yace " to yisauro ki kawo",,ckn farin ciki ta ruga da gudu tabar wajen ,bata jimaba sai gata tadawo, takardar tabashi tareda yimasa gdy sosai sannan ta tafi ckn tausayin aminiyarta da mahaifiyarta.
Muwadda na zaune ta hada kai da gwuiwa tana kukan zuci,cinnakai sai buga mata cizo sukeyi amma bata kulaba don basu ne a gabanta ba,,har tsohon yabude kofar batasaniba,,tsayawa yayi akanta ckn tausayi yace "kuyanga muwadda",, dasauri tadago rinannun idanunta ta kalleshi,,takaddar yamika mata tareda fadin " inji kawarki tace abaki",,karba tayi shikuma yafita tareda datsawa kofar katon mukullinta,,bude takaddar tayi don ganin abinda ke ciki,,dan guntun rubutu ne kamar haka: *" Kiyi hakuri kawata Allah yana sane da ke kuma zai saka miki ,watarana sai labari,don Allah ki nutsu ki kwantar da hankalinki kibar kuka,nayi miki alkawarin daga yau har zuwa ranar da zaki fito zan dinga kwana a gdnku wajen iya, zan kula da iya fiye da tunaninki saboda haka ki kwantar da hankalinki don Allah!!*",,kuka ne ya kubce mata data gama karantawa,ckn kuka tace "Tabbas kinwuce kawa ubaida kinxama yar uwa,,Allah nagode maka daka kawomin dauki,sosai taki sanyi a ranta don dama mafi yawan damuwarta akan kula da iya ne.
Me babban daki tana zuwa kofar shiga dakin me martaba bayin da ke biye da ita suka tsaya a kofa,tana shiga ta taddashi da amarya,haushi taji sosai amma ba yanda ta iya haka ta karasa ciki,taso dai ace shi kadai tasam*Y͟A͟N͟C͟I͟N͟ B͟A͟Y͟I͟*
{Historical fiction}
➰
*STΩRΨ ШRITTΣΠ βΨ*✍🏻
*SURAYYERH B.ABDUL*
___________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
___________________________________
Dz book completely goes to *HASSAN 90k& HUSSEIN 80k*
*Special gift to my besty*
*UMAMATU UMAR ADAM*
*PAGE 4*
Sallama amarya taiwa me martaba ta fita bayan sun gaisa da me babban daki,, sbd tasan idan daya daga cknsu tazo wajen me martaba kuma ba ranar girkinta ba mgn zasuyi .
Zama tayi kusa da me martaba tareda fadin "Barka da hutawa ranka ya dade".
Amsawa yayi da kai saboda Apple dake bakinsa,,ckn kissa tace " Me martaba Ashe dana yakusan dawowa amma ba labari nafara shirin tarbarsa???,,,murmushi yayi sosai da yakular da me babban daki kamar ta makeshi saboda takaici,,ckn annashuwa yace "Auuu dannaki bai fada miki ba??? ai kunfi kusa ke da shi tunda gashi ma harya fada miki yanzu,,haushi ne yakara kamata ganin da tayi dagayin zancen yarima sameer me martaba sai wani washe baki yakeyi,,basarwa tayi tace " Me martaba nazo neman wata alfarma ne a wajenka",,juyowa yayi ya fuskanceta sosai tareda fadin "Inajinki",, Ajiyar zcy tayi tace ", Don Allah me martaba ina neman Alfarmar a fito da kuyanga muwadda daga kurkuku saboda..... Keeeee halima kinsan Abinda kike fada kuwa????,,Me martaba ya fada a tsawace sai da gabanta ya fadi,,,lkc guda annurin fuskarsa ya gushe,ckn fushi yaci gaba" Anya kuwa ba shaye² kika faraba halima???Don nasan bazaki manta wane ni ba da kuma dokata a kasarnan,,narantse miki da Allah babu wani mahaluki da zaiyi laifi nayanke hukunci akansa wani dalili yasa nafito dashi karyane!!! Ai Wannan tozarci ne da wulakanci ace sarki kamata yayi magana biyu,,saboda haka indai kinsan Wannan banzar maganar ne ya kawoshi fitarmin daga daki!!!! Yakarasa tareda nuna mata kofa a fusace,,,Kuka tafarayi ckn kissa da makirci tace "Haba me martaba,,yarima yusufa yanacan fa kurkuku yasa an kulleshi saboda ita ,a cewarshi wai ai tare sukai laifin kuma yace bazai taba fitowa ba har sai kwanakin da aka dibar mata yayi,,Haba me martaba ka dubafa kamar yarima yusufu danka ya kwana a kurkuku ai.......To saime????badai shi yazaba ba???To bari kiji wlh ko shekara na dibarwa kuyanga muwadda yace shima zaiyi babu dalilin da zaisa na fito da ita saboda shi,,ke waima natambayeki mene ne hadin ta dashi???? Ai wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa har abada.
Ni bansan wata alaka da ke tsakanin su ba,,kuma ma mene zai hadasu kuwa???Tausayi kawai tabashi,,ynz me martaba haka zai zauna a kurkuku cinnakai da komai na cutarwa a ciki???
Daga kafada me martaba yayi yace " Shi yaso hakan ai,,kinga ni zanshiga daga ciki,,yakarasa da mikewa yabar parlourn,, kwafa tayi ckn bacin rai tana fadin ",Inda wancen shegen ne me girman kai ai da zaka fito da ita saboda shi,,kai tsaye kurkuku ta nufa fuskar nan a hade kuyanginta na biye da ita.
Tana zuwa masu gadin wajen suka zube suna kwasar gaisuwa,batareda ta amsa ba takalli babban cknsu cikin raini da nuna isa da gadara tace " Budemin kofa",,mikewa yayi jiki na rawa ya budemata,,dagawa kuyanginta hannu tayi alamun su dakata ita kuma ta shige,,,a xaune ta sameshi yanacin abincin da ake bawa yan prison din,,dasauri ta karasa hankali a tashe ta dauke kwanon abincin ckn tsananin bacin rai da jin haushi tace "Meye haka wai kakeyi yusufu????Ko ka haukace ne???Wane dan iskanne yakawo maka Wannan wulakantaccen abincin kaci??Kawar da kanshi yayi batareda yace mata komaiba,,haushi ne yakara kamata a tsawace tace " Baka jina ne zakamin banza ina maka mgn???",,Dakyar yabude baki yace "To mama me kikeso nace miki???,,Tambayar ka nayi wane dan iskanne yakawo maka Wannan wulakantaccen abincin????,,Murmushi yayi yace " Mama wulakantacce fa kikace???Karki manta abincin da mutane sukeci ne fa kuma ai nima mutum ne kamar su sannan....Dalla rufemin baki sakarai kawai!!!Wai ni anya kuwa ba sauyo min kai akaiba da na haifeka,,yaro kwata² kamar ba jinin sarauta ba,, to wlh kafin na sabamaka ka taso mutafi daga wajennnan akan wata banza mara gata,,ckn kosawa da mgnr ta yace mamaaaa haba Don Allah wai yaza'ai muyita mgn daya???Nace miki babu inda zanje sai satin ya cika Don Allah kiyi hkr ki banni,,,Ckn takaici take kallonshi tamkar ta makeshi sbd takaici,,rasa abinyi tayi kawai sai tayi kwafa tafice a fusace,,binta yayi da kallo a fili yace "Kiyi hkr mama wlh zan iya komai akan muwadda!!! *{Tofaaa}*
Ita kuwa tana fitowa ta kalli ma'aikatan gdn a tsawace tace " Uban waye a cknku yakaiwa yarima wancen dan iskan abincin????,,,Ckn tsoro babban su yace "Wlh ranki ya dade da kanshi yaje dakin girki ya ebo,,wani mugun takaici ne yasake rufeta ganin danta na cknta yarima da Wannan aikin tozarcin,,,A fusace tabar wajen tamkar zata tashi sama.
Iya na zaune ta zubawa kofa ido tana jiran sallamar tilon yarta amma shiru gashi har lkcn dawowarta yawuce kuma tasan muwadda batada tsaye² ko ina burinta tazo gd,,,sallamar ubaida ce ta dawo da ita daga duniyar tunaninta,,gabanta ne yafadi sosai,, dasauri tace " Don Allah ubaida kar kicemin wani Abu Mara dadi yasamu muwadda na bazan juraba wlh",,,Hadiye miyau ubaida tayi ckn tsananin tausayinsu,,kakalo murmushi tayi tace "Kayyyy iyarmu babu komai fa,,zama tayi gefen iya tana fadin muwadda tana lpy gimbiya jalila ce tasata wani dan aiki amma anjima zata dawo,,mikewa tayi tace " Iya nasan yanzu kina bukatar ki kewaya bari na taimaka miki,,ba musu iya tamike ta dafa ubaida takaita bayi,,,rufe ido tayi ta gama abinda zata yi sannan takamota suka dawo daki,,,kwanan da ke gefenta tadauko tace "Iyaa ga abinci kici natawo miki dashi daga gd,,budewa tayi taga shinkafa da miya hadda nama,,murmushi tayi tace " Bakya gajiya da dawainiya ubaida,sannu Allah yai miki albarka,,amma abincin sai muwadda tadawo zamuci,,dasauri ubaida tace "A'a iya ai shiyasa ma ta turoni saboda tace hankalinta bazai taba kwanciya ba tabarki ckn yunwa kici kawai ki rage mata,,shiru iya tayi kamar me tunanin wani Abu,zuwacan kuma sai tafaraci,,ruwa ubaida ta ebo mata tasha sannan ta shimfida mata dadduma ta rada sallar magriba a zaune Don lkcnta yayi kuma dama tadauro alwala.
Bayan iya tagama azhkar ta juyo ta kalli ubaida data idar da tata sallar ynz,,ckn damuwa tace " Anya kuwa ubaida bakina boyemin wani Abu bane??? Muwadda fa bata taba kaiwa hakaba,, dn Allah ki fadamin idan wani Abu ne yafaru, takarashe kamar zatayi kuka,,,riko hannunta ubaida tayi ckn taushin murya da lallashi tace "Wlh dgsk nake miki muwadda tana lpy sai dai tana kurkuku,,ckn matsanancin tashin hnkl iya taja da baya tareda dafa kirji murya n rawa tace kurkuku!!!!!!u.*'Y͟A͟N͟C͟I͟N͟ B͟A͟Y͟I͟*
{Historical fiction}
➰
*STΩRΨ ШRITTΣΠ βΨ*✍🏻
*SURAYYERH B.ABDUL*
Dz book completely goes to *HASSAN 90k & HUSSEIN 80k*
```Special gift to my besty ```
*UMAMATU UMAR ADAM*
___________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
___________________________________
*PAGE 5*
Duk yanda ubaida taso ganin iya ta kwantar da hankalinta abin ya faskara,,don rudewa iya tayi sosai tadinga kuka tana surutai tuni wani zazzafan zazzabi ya rufeta jikinta yahau rawa,,da gudu ubaida taje gida tadauko wani maganin zazzabi tabata,bata jimaba bacci ya dauke ta.
Tagumi ubaida yazuba ckn tsananin tausayin rayuwarsu muwadda,a fili ta furta Allah ya kawo karshen Wannan kuncin rayuwar taku.
Iya fa tariki ce sosai baji ba gani,,babu yanda ubaida bataiba amma inaaa ko abinci iya taki ci sai aikin kuka da kiran muwadda na,,dole ta kyaleta,sai da akayi kwana biyu taga yunwa tana Neman hallakata sannan taci shima kuma kadan.
A bangaren muwadda ma zancen daya ne,,ta rame sosai saboda tunanin mahaifiyarta da rashin sanin halin da take ciki,, tasan dole iya zata shiga mummunan yanayi,,taci kuka tamkar ranta xai fita,,bacci kam sai dai barawo,,sosai kiyayyar masarautar zinsari ta karu a ranta.
Babu yanda me babban daki bataiba akan taga yarima yusufu yafito daga kurkuku amma kekam yaki,,dole ta kyaleshi tana aiko masa da abinci amma shima yaki ci,,sosai take takaicin halin yarima yusufu,,a cewarta bata taba ganin shashashan yarima kamar sa ba.
Yau satin muwadda daya a kurkuku kuma yau ne za'a fitar da ita daga kurkuku,,hakanan kuma yau ne ake shirye shiryen dawowar yarima sameer daga south Africa gobe,,,a Daren ranar duk satar bacci haka yaga muwadda ya kyale har garin Allah ya waye.
Tana zaune ta hada kai da gwuiwa tana sana'ar tata taji an bude kofar,,dasauri tadago kanta taga wani bafade yana bude kofar kurkukun,,mikewa tayi tamkar wadda aka tsikara tayo wajen kofa,,ckn tausayawa yace mata jeki an sallameki gobe sai a kiyaye,,ko karasa jin abin da yake fada bataiba tafice da gudu burinta kawai taganta a gida ko ganin gabanta batayi da kyau bata Ankara ba taji tayi karo da mutum,,dagowa tayi idonta yasauka akan gimbiya jalila,,dasauri muwadda ta zube jiki na rawa tafara bawa gimbiya jalila hakuri,,wata kuyanga ce tadaga hannu zata zabgawa muwadda mari gimbiya jalila ta daga mata hannu,,kallon wulakanci da kaskanci take jifan muwadda dashi,,kamar wadda akaiwa dole tace "Tashi ki wuce",,, ba muwadda kadaiba hatta sauran kuyangin sai da suka cika da matsanancin mamaki,,godiya muwadda tadingayi har saida gimbiya jalila tawuce sannan taci gaba da gudunta tafice daga masarautar.
Gimbiya jalila kuwa abinda yasa ta kyale muwadda saboda tana farin cikin Prince din ta zai dawo gobe shiyasa zuciyarta take kyall.
Kamar kullum yau ma ubaida na zaune tana lallashin iya sai ga muwadda tafado gdn da wani matsanancin gudu kamar wacce aka jefota kai tsaye ta nufi iya ta rungumeta tareda sakin wani irin matsanancin kuka,,itama iya tuni ta fashe da kuka,ido ubaida tasa musu ckn tausayi bata hanasu ba tasan ko tabasu hakuri a banza,,sai da sukayi mai isarsu sannan muwadda tazame jikinta tareda kallon iya ckn bakin ciki tace " Iyata kiyi hakuri don Allah da kuskuren da na aikata aka rufe ni,duk kokarina na ganin na kaurace masa sai da abinda nake tsoro yafaru,,iyata kalli fa yanda kika rame ai da bakisa damuwa a ranki ba tunda zan fito.
Murmushin takaici iya tayi tareda girgiza kai tace "Muwadda na kenan,, taya kike tunanin hankali na zai kwanta???Kalli fa yanda kikai wata iriyar rama sai haske kema.
Hawayen da ya zubo mata tashare tareda fadin " wlh iya ta bazan daina fada ba natsani masarautar zinari,,bantaba ganin azzalumai masu son kansu kamar su ba,,dasauri ubaida tace "muwadda tun ranar da aka rufeki fa yarima yusufu ma yarufe kansa yace ai tare kukai laifin,babu yanda me babban daki batai dashi ba yafito yaki hala ma yafito ynz bansaniba.
Mamaki sosai muwadda da iya sukayi,,tabe baki muwadda tayi tareda mikewa tana fadin " Wannan kuma bangaren su ne bai shafe ni ba,,fita tayi daga dakin tanufi bandaki,,a ranta tana kara girmama matsayin ubaida a gunta don daga gani tana kula da mahaifiyarta tunda ko ynz da taxo akwai abinci me kyau a gaban iya duk da bata ci ba,,sai bayan maghriba sannan muwadda taraka ubaida hanya ta tafi gida bayan inna tagama shimata albarka,,ko a hanya haka muwadda tadinga yiwa ubaida godiya har saida tace "Idan kika cigaba damin godiya zanga kamar baki dauke ni yar iya ba nima" Sannan muwadda ta baryimata gdy.
Yau gabadaya masarautar zinari ta kacame da hidimar tarbar yarima yusufu,,zuwa ynz labari yabaza ko ina a garin,,mutanen gidan farin ciki tamkar bakinsu zai yage,yayinda wasu dayawa suke yake.
Su muwadda suna bangaren girki don ita dama aikinta kenan a bangaren gimbiya jalila kuma,, girkuna akayi sosai kala kala,,suna ckn yi saiga me babban daki,, zubewa sukayi sukahau gaisheta tana wani yamutsa fuska kamar taga kashi,,ckn gadara tace "idan wani tsautsayi yasa kukai kuskure a girkin dana wlh saina baku mamaki saboda haka ruwanku ne ku kula,,karasawa tayi tana bude kulolin abincin tana gani,,fakar idonsu tayi ta shammace su ta zuba magani a miyar tumatir din da akai masa don tasan yana sonta sosai kuma sai yaci,,daukar kular miyar tayi tana jijjigawa tareda fadin " Kun tabbata miyar nan dai tayi ko??"
Dasauri suka amsa mata da eh ranki ya Dade,Ajiye kular miyar tayi tana wani irin murmushin mugunta da samun nasarar babu wanda yaganta a cknsu gashi tayi abinta ckn kankanin lokaci,a ranta tace "Zakasan bakada wayau yarima sameer,,ficewa tayi daga kitchen din bayinta dake kofar ckn din suma suka bita.
Gimbiya jalila taci kwalliya sosai tamkar wadda zataje gasar kyau,,wani murmushi ne na musamman kwance a fuskarta,,kai tsaye fitowa tayi daga part dinta don zasuje tarbo yarima sameer ynz, kuyanginta na biye da ita,a fada suka hadu da me babban daki da yarima yusufu da gimbiya jidda da gimbiya farida tareda mufeeda daketa rawar kai tana zumudi,,fitowa sukayi aka bude musu motoci suka nufi airport tareda masu rakiyarsu anata busa algaitu da sarewa.
Shi kanshi me martaba farin cikin sa yagaza boyuwa,hakama amarya(mahaifiyar sameer),,sosai me babban daki take jin haushi kamar ta shake su saboda takaici.
Basu jima da zuwa ba jirginsu yarima sameer ya sauka,,baza ido gimbiya jalila tayi tana hangen Prince dinta,,can ta hangoshi yana