Showing 42001 words to 45000 words out of 122268 words

Chapter 15 - MATAR MAKAHO DOCUMENT BOOK COMPLETE by Rukayya Ibrahim Lawal.txt

Koh riga baisa ba ya rufe kofar, ya nufi inda yake kyautata zaton agun ta musu shimfid'a




Ina kwance Ina kallonsa harya matso inda nake kwance hannu yasa ya tattaba shimfid'ar sai Kuma ya fara laluben Kan shinfid'ar bayan ya xauna.


Jin ya tabata yasashe Hawa Kan shinfidar kwanciya yayi a Gefen pillow n da ta d'aura kanta akai


"Bakaji pillow da na aje maka bane"


Naji Mana Amma a naki nakeson kwanciya


"Kaga ka rabu Dani jikina ciwo yake mini"


Hannu kawai naji yasa a bayana Yana mammatsa mini baya,naso hanasa amma Jin yanda message in ke kauda tsamin da bayana yake mini yasa nayi Shuru


Yana ta mamatse Mata baya da kafa duka har yaji tayi bacci, gyara Mata kwanciya yayi,daga kefuwarda tayi shima ya kwanta a Gefen ta bacci ya d'aukesa.


Misalin karfe biyu na dare ya farka Jin iska na kad'awa ga kamshin kasa na tashi bude ido yayi sosai, ya mike zaune hannu yasa ya taba Sumayya Aiko tana kwance Koh juyawa Bata sake ba tun gyarata da yayi, Sumayya!! Sumayya!!




"Ummmm menene"nace cikin magagin bacci don harga Allah yau dai baccin gajiya nake




Ana iska ga hadari,ki tashi mu shiga d'aki


"Da wani idon kaga hadarin ni wallahih ka barni nayi bacci",na fada Ina gyara kwanciya


Sumayya ruwane fa da gaske


Shuru na Masa abina na koma bacci


Jin Taki tashi yasa ya mike key ya d'auka ya bude d'akin, d'aukarta yayi a hannu a hankali yake tafiya Yana lalube harya shiga da ita d'akin,Kan gado ya haura ya kwantar da ita,Jin an Soma yayafi da sauri ya fitoh a d'akin shimfid'ar su ya tattara ya Kai d'aki randar robansu ya zubar da ruwan ya hada da bokataye ya jejjera a bakin baranda,daidai lokacin aka fara ruwa sosai Kamar me .


Alwala yayi ya shiga d'akin sallaya ya d'auka ya shimfid'a wa yayi ya Tada kabbara,lafilfilu yake har kusan karfe uku na dare kafun ya kwanta shima a gefenta




*Washe gari*
Kamar kullum yaukam da safe kudi na basa yasai Mana manya manyan gongomin Madara da bornviter na sai suga Rabin kwano Lipton kwali d'aya na had'a da cornflakes,dashi muka karya ya fita




Al'ameen kam yasan baida abinda zaiyi haka ya fita yaje ya zauna a bakin titi ya rasa mafita Allah ya gani Yana iyya bakin kokarinsa wajen niman abinda zai rufawa kansa asiri,Amma abin yaki yasan kome na Allah ne Kuma Bai manta dashi ba a hakan ma yana kara godewa Allah tunda Sumayya nada rufin asiri da ace Bata sana'a a war yanzun da kayan abincin ta ya fara karewa baisan yanda zaiyi ba.




***********
Khadija ce ta shigo bayan sallan azahar lokacin Ina kanwa matan da suka zo make-up, Assalamu alaikum


"Waalaikumu salam" dukan mu muka amsa Mata


"Ah ah khadin Goggo idonki kenan"?nace Ina kallonta sanye take da atamfar dana Bata riga da zani sai gyle da takalmi harda jaka sai laida Mai tambarin asibiti a hannunta sosai tayi kyau fuskarta tayi fayau alamu dai batajin dadi,abinka da farin fata


Wallahih Aunty na fitoh asibitine nace bara dai nashigo yau Goggo takece mini kun shigo da dare Ina bacci.


"Eh wallahih mun shigo da yayanki nace abarki kawai kar a tasheki"


Allah sarki,tace tana gaida matan dake zazaune suna jiran na Gama wa Wanda
nakema make-up


"Khadija ki shiga d'aki Mana akwai NEPA ki jona kittle akwai kayan shayi asaman freezer"


Aunty bazan iyya shaba bakina ba dadi Sam shiyasa koh abincin dare ban iyya ciba Haka karyawa ma.


Ah ah khadija dadai kin daure kinsha shayin Daya fi Amma ace bakinki ba Dadi saiki kicin abinci,ai ko magani in ba abinci baya aiki,D'aya daga cikin customers nawa ta fad'a


"Gaskiya ne khadija,ki shiga in kinsha saiki kwanta ki huta"


Toh Aunty tace tana shiga d'akin, kittle in ta d'auko ta zuba ruwa ta jona,shayi ta hada kad'an ta iyya Sha ta balle maganin Tasha kwanciya taye lokaci D'aya bacci ya d'auke ta




Sai kusan 4:30 na Kamala wa sauran kwalliyansu Daman Amarya tun 3 na yamma na Gama Mata saboda bud'an Kai,


Gaskiya yau na damki rabona mutane kusan goma nama makeup heavy make-up
Simple make-up
Light make-up
Duk yau ba Wanda banyi ba sosai na samu kudi 50k yau na damka nan ma banyi na dinner ba kenan.


Misalin karfe biyar khadija ta mike zata wuce gida Aunty nikam Zan wuce sai gobe


"Toh khadija Allah ya Kara lafiya ga wannan ki D'an samu abinda kike bukata ki Saya dashi" nace Ina Mika Mata 10k


Aunty ki barshi kawai d'awainiyar tayi yawa jiyama fa Goggo tace mini kun kawo Mana 5k naje asibiti danaje in ma,Ina saurayin da nace Miki yazo guna?


"Eh na tuna har kikace bazaki fita ba"na Bata Amsa


Ashe Dr ne Ina zuwa na gansa shine ya sayo mini magani kyauta,


"Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari"


Ameen Aunty


"Wancan yayan kine ya baki wannan Kuma nawane,ki karba khadija kid'an Saya Abubuwan da baki dasu"


Gaskiya Aunty nagode Allah ya saka da alkhari,tasa hannu ta karbi kudin


"Ameen khadija"


Yauwa aunty nace Koh Zaki aje mini tunda Naga azumi ya kusa Inna tashi zuwa kasuwa saina karba naje na sai kaya,samun na samu dinki da wure?


"Ah ah khadija insha Allah, Allah zai Bud'a Mana har yayanki ya sai Miki kayan Sallah, wannan dai ki sai Abubuwan bukata irinsu kananan Kaya da mayuka Turare pad omo sabulu ke dai irin Abubuwan bukatar Yan Mata haka"


Toh shikinan Aunty Daman bani da kananan Kaya sai na saya pant biyu Brz sai vest shima biyu Amma na gwanjo Zan Saya aunty sauran chanjen, Ina materials da ake yayi yanzun ana yankawa a dinka dogayen riguna dasu?


"Eh khadija"na gane su


Yauwa yadi d'aya dari uku su Zan Saya kala biyar na dinka


"Gaskiya khadija kinye tunani Mai kyau kema saiki samu na chanjawa kwana biyu"


Toh Aunty Zan tafi nagode Allah ya Karo customers


"Ameen khadija yanzun ma wasu na zuwa da dare maganar dinner aike alkhari ce tunda sanadin ki nake samun kudin"


Ah ah Aunty Allah ne ya tsaga da rabonki , shiyasa kike ci


"Hakane Kam khadija" nace Ina shiga kitchen da sauri nake na d'aura Mana abincin da zamuci


Bayan fitar khadija girki na Gama na juye Mana a kula,sai goshin mangari ba yayan Khadija ya dawo


Sumayya sannu da gida?


"Yauwa sannu yayan Khadija sai yanzun"


Eh wallahih ya aiki?


"Lafiya klau" nace Ina kallon sa ganin Kamar a cikin damuwa yake


D'azun Bashir wani makwancin mu ke tambaya ta Wai MATAR sace taji labarin Wai kina lalle ke kikama Asma'u na aure shine Wai yake tambaya ta zata samu lalle gobe,make-up jibi da Rana?
nace ya bari saina tambaye ki inyaso in mun hadu a masallaci anjima na fad'a Masa amsar ki.


"Lallen me za'a ma MATAR tasa"?


Suna ne haihuwa tayi jibi suna


"Gaskiya nifa bazanje home service ba,in mutum nason lalle Koh kwalliya yazo ya same ni a gidana"


Amfa Sumayya haihuwa ne ya za'a yi mace maijego tazo lalle gidanki?


"Wallahih yayan Khadija ni raini ne banaso a rayuwa na kar mutun yaga kaje Masa lalle ya Raina ka"


Kai Sumayya ba wani raini ai sana'a ce ta kaiki ba maula ba,ki daure kije ki Mata kinji?


"Shikenan Allah ya kaimu goben Amma bansan gidansu ba da yamma ta tura yaro yazo ya kaini"


Sumayya har yamma?ya tambaye ta


"Eh man saina Gama aikina,Koh so kake na tafi da safene,jibine fa sunan"


Toh shikenan Allah ya kaimu yace Yana mikewa ,ruwa ya ibo a boket ya shiga bandaki


Muna idar da sallan mangariba Koh abinci bamu ciba Yan make-up na dinner suka zo su biyar ne dukansu harda Amarya heavy make-up suke so,Dole tasa na hakura dacin nawa zuba Masa nayi na d'auko Masa ruwa a freezer na jira Masa,a d'aki na fitoh waje,don ni bana saka baki a dakina Sam kowa ya zauna a waje kawai


Sai da yaye isha'i kafun ya shigo gidan, gaisawa sukaye da customers nawa,don na fahimci yanzun mutane na ganin kirmansa tunda kofarsa suka shigo


"Abincin ka na d'aki yayan Khadija"nace Masa ganin ya nufi d'akin kar yaje ya zubar da abincin tunda a kasa na jira.


Toh yace Mata Yana shiga d'akin


Make-up na Amarya na fara, Gamawa ta biyani akazo aka d'auketa saura hudun ma duk na Gama musu kafun 9:00,kudin da suka bani 25k Inna hada Dana d'azun kusan dubu saba'in na samu kenan Alhamdulillah yau kawai na tashi da kudi dubu sittin da biyar in aka cire 10k Dana bawa khadija


Wani tunanine ya fado mini akan kudin, murmushi kawai nayi na nufi d'akin
Ina bude labulin idona ya sauka Akan plate inda nasama yayan Khadija abinci nakai dubana garesa da mamaki ganinsa a..............








*My Real and special Fan'S*


*Princess* 🏡️
*Maryam najibu* 🏡️
*Mummy*🏡️
*Shamsiyya Gombe* 🏡️
*Ummu na'eem*🏡️
*Faeexetion* 🏡️
*Zainab*🏡️
*Bebi* 🏡️
*Maman khairat*🏡️
*Oum Abdullahi*🏡️
*UMSAD INCENSE* 🏡️
*Ummul husnah*🏡️


*Duk Naga comments naku Allah ya bar kauna Nima Ina yinku* 🏡️🏡️




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*


πŸ€ *Na tsunguno(habil)*
πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )
πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,
πŸ€ *Na d'aki(halud Al'oud)*

*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*


Contact them vie
πŸͺ€08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ
free book 🀧


πŸ€ *Wannan shafin sadaukarwa ne gareki haj j Aisha Ahmad Allah yabar kauna* πŸ€


Page3️⃣4️⃣&3️⃣5️⃣
Al'ameen ne, Sumayya ta gani zaune ya zuba tagumi Koh abincin Bai d'and'ana ba.


Cikin mamaki ta karaso cikin dakin"yayan Khadija lafiya kuwa"? tace tana matsowa kusa dashi


Firgigit ya dawo hayyacinsa, Sumayya har kun Gama kwalliyar?


"Eh mun gama,Naga bakaci abincin kaba Allah dai yasa lfy Koh" ta Kara tambayar sa.


Lafiya Sumayya jiranki nake in kuka Gama saimuci"ya Bata Amsa


Da mamaki sumayya ke kallonsa"banace kaci ba"?


Sumayya na kasaci ne, kece Kika nema Kika dafa Taya zanyi na rigaki ci bayan ke kina ta faman aiki.


"Karka Kara fad'amin irin wannan magana daga yau"


Don me?ya tambaye ta


"Saboda duk abinda na baka ni gani nake kamar kaika bani mukeci banason Kara Jin irin maganar nan,Ina zaune itdakai ne badon kome ba sai don Allah,rufin asirin ka nawa ne nawa nakane"ta fada tana kallonsa


Shikenan Sumayya nagode,


"Bana bukatar godiyan ka ka gode Allah"tace tana matsowa kusa da abincin budewa tayi tasa shukali"Bismillah muci"tace tana iba


Toh yace Yana laluben nasa shukalin


Abinci sukaci Amma cikinsu Babu Mai magana kowa Yana cin abinci ne,bare Hajiya sumy


Suna Gama cin abincin Al'ameen ne ya tattara Kwanukan yafita dasu waje


Sumayya Kam wanka ta shiga,tana fita tayi Alwala,kayan bacci tasa ta kwanta


Al'ameen Jin ta kwanta yasa shima fita wajen ruwa ya Iba yayi wanka.kamar yanda yazamo musu Al'ada wankan dare kafun su kwanta,Yana fitowa ban d'akin kofar shashen su ya rufe,ya shigo d'akin,rufewa yayi a hankali yake takawa Yana laluben gadon harya iso, Hawa gadon yayi ya kwanta a hankali,


Sumayya Kam mamakine ya kamata ganin sa a hakan Sannan yahau gadon ma Bai Saba Mata yanda yake Mata ba, watoh son mannuwa kusa da ita.


A hankali ta mirgina kusa dashi hannu tasa ta Kama NASA hannun"yayan Khadija"


Cikin sanyin halinsan nan ya amsa mata, na'am.


"Menene yake damunka ne Wai" ?


Ba kome Sumayya me Kika gani?ya tambaye ta Yana Mai dagota ya d'aurata a jikinsa gabaki d'aya




"Ba kome, yauwa nace kanada National ID card ne"?


Sai dai voters card bani da National ID card


"Ok shima zaiyi Daman inason na bude account a bank ne kasan banzo da details nawa ba"


Toh shikenan Allah ya kaimu goben saina baki


"Zaka rakani bank in? Koh naje da kaina"ta fada tana gyara kwanciyar ta akansa


Duk yanda Kika gani goben ne Zaki bank in Koh yaushe?


"Sai na Gama lallen da akayi booking innan"


Toh shikenan Allah ya kaimu saina rakaki,in khadija taji sauki Kuma sai kuje tare kinsan me?ya tambaye Sumayya


"Ah ah"


Khadija na son zuwa bank Kamar me haka lokacin kudin covid 19 ta dameni Wai sai naje mun bude account muma,mun cika Koh zamu samu kudi,Amma da mukaje bank hanani Shiga sukayi security Wai ba'a bara a banki,Kuma su tsaya su saurare mu sunki Haka suka kuramu waje.


Sosai naji maganar ta tabamin rai"aiko Insha Allah da ita zani taga bank,Amma kaima fa Dole zamuje tare tunda account Kai za'a budewa ba niba.


Toh Allah ya nuna Mana yace Yana zura hannunsa a cikin rigan bacci dake jikinta


Jin hannunsa a riganta unexpected yasa ta zabura sai Kuma ta koma ta kwanta a hankali ta lumshe ido Jin abinda yake Mata da hannunsa a cikin riga"kasan me"?


Ah ah ya Bata Amsa


"Nikam Ina ga Zan Saida laptop Ina da waya"


Akan me Zaki saidasu toh?


"Saboda Banga amfanin suba inba kallo ba me nake dasu shiyasa Zan sayar"tace. Tana taimaka Masa ganin Yana kokarin zare rigar Tata


Umm umm Sumayya waike bazaki ringa d'aukar kwalliya kina sawa a media ba Koh Allah zaisa asamu location naki Kinga ai sai afi saninki sosai a Jala


"Kasan ba kowa keson asa hotonsa a social media ba shiyasa ban fara posted ba,Nima nayi wannan tunanin"


Eh ai tambayan su zakinayi Zaki d'aura hotonsu kiyi Tallah Amma fa Yan Mata banda matan aure, insun Amince shikinan,tunda wasu da yawa in sunyi kwalliyar ma post suke.


"Gaskiya ne Amma waya fad'a maka ana d'aura kwalliya a online?
Kuma ya akayi kasan ana Post"?Sumayya ta tambaye sa tana kakkama Masa gashin kai Jin wani magic dake bin jikinta a sanadin abinda yake Mata


Uhmmm ai inaji ana Hira koma ni lokacin da na makance ma waya tayi araha a hannun kowa ba,Kamar yanzun


Washhhh toh,uhmm tace tana zillewa daga kansa ta sauka a gefe.


Jin ta zame yasa ya bita shima, tana kwanciya ya kwanta akanta rumfa ya Mata da kirjinsa,ya had'a fuskarsa da Tata fuskar yayi Yana tsintsinar bakinta,dake kamshi


"Wayyo ka sauka nauye"tace tana mutsu mutsu tana damke damtsen hannunsa


Shagwaba Koh bafa nauyina na d'aura miki ba


"Nidai ka sauka,kawai tsoro nakeji"


Tsoron me?ko ni dodone?ya tambaye ta Yana Mai Kara matsota garesa


"Ka sauka"


Naki,yace Yana Kara Danna kansa akanta


"Nifa bacci nakeji kaji muye bacci"


Nikam banajin bacci


"Nikam ai inaji Koh"?


Sai kiye ai na hanaki ne?


"Amma ai ka tokareni"


Shuru ya Mata yaki kulata sai bidirinsa yake a kanta jifa jifa tana taimaka Masa


Jin abin NASA ya fara yawa yasa ta fashe Masa da kuka


A tsorace ya mike a kanta sauka yayi gefe cikin tsoro,yake tambayar ta,ke Sumayya menene,Yana tattabata yaji Koh lfy


Saura kad'an dariya ya kubucewa Sumayya Jin yanda duk ya tsorata dagajin kukanta kawai,ta rasa ma wani irin namiji ne Mai shegen tsoro haka


"Toh ba Kaine ba nace maka inajin bacci sai matseni kake"ta fada da muryar kuka tana kallonsa tana Masa gwalo ganin yanda sai zazzare ido yake kamar kace kittt ya ruga


Shine abinda ya saki kuka?


"Eh Mana"


Toh Yi hakuri kwanta toh.


Dariyace ta subuce mata Jin abinda yace Yana kwanciya a gefenta baima mannu kusa da itaba




Cikin mamaki ya Tashi zaune Jin tana dariya, Sumayya Anya lfy kuwa daga kuka saiki koma dariya?


Shuru tayi gudun karya harbo jirginta"babu kawai ji nayi kamar jakulkule ake mini a ciki"


Shuru yayi baice kome ba illah rufe ido da yayi Yana nazarin Rayuwa yau Wai shine da Mata,Ashe haka zama da mace yakeda Dadi duk halinda kake ciki muddin ka samu mace na gari ka Gama samun Jin dadi,duk halinda namiji zai shiga mundin dare yayi zata ga tayi kokarin kauda damuwar tasa Koh Bata cireba,zatayi iyya bakin kokarin ta taga ta d'auke Masa hankali


Jin yanda Sumayya keta motse yasa shi kiranta, Sumayya!!


"Na'am"ta amsa tana gyara kwanciya


Bakiyi bacci ba?


"Umm banyi ba"


Saboda me?


"Haka kawai"


Jin Amsar da ta basa yasa a hankali ya matso gareta,lumshe ido tayi Jin yanda tsikar jikinta ke tashi,Jin gashin kirjinsa na goguwa da bayan ta


Hannu yasa a hankali ya Kama waist inta d'an zabura tayi kad'an,yasa hannu ya maidata,watoh kukan shugwaba Koh?


"Bawani shugwaba,Kuma ni ba shagwabebbiya bace atoh"


Shugwabebbiyace Mana ai duk lukutaye akwai shagwaba


"Waye lukutar"?ta tambaye sa tana juyowa suka fuskanci juna


Daga Sumayya har Al'ameen wani yanayi sukaji a tare da junan su sosai kusancin su yayi yawa akwance da suken nan


Kece Mana, lukuta kiga nan naki fa Kato,yace Yana Kama Mata bombs,
Hannu tasa ta buge Masa hannu"ai naka yafi nawa girma"


Zare ido yayi Kamar tana ganinsa,ai Dana shiga uku ai,sai wando Mai shape za'ana dinka min.


Hhhhh Sumayya ta Kama dariya "Wai wando Mai shape waya ganka kana tafiya kana murgud'asu a cikin jallabiya"ta karasa maganar da kamo hannunsa dake Kan kirjinta don wallahih kirjin zafi yake Mata


Shi Karan kansa Al'ameen abin sai da ya basa dariya,Amma yakiye, murmushi kawai yayi,Jin ta Kama Masa hannu kafarsa ya daura Mata akan kafa.


Kokarin mikewa ta fara har lokacin hannunsa na rike a nata Wai don karya taba Mata inda bataso


Jin tana kokarin tashi yasa sa tambayar ta,Ina Zaki Kuma dare fa yayi.


"Rigata nake nema"


Kiye me dashi?


"Me ake da riga"


Sawa, ya Bata Amsa


"Nima sawan zanyi"


Nikam gaskiya banso kawai mu k'wanta haka.


"Jikinka Koh nawa?wato mu k'wanta haka ka karasani ba"


Sorry zafi yake mikine?


"Eh Mana duk ka mammasa mini jiki"


Amma ai kinji Dadi


"Banjiba"ta basa amsa tana mikewa zaune


Ai da sauri yasa hannu ya rike Tata hannun,yana kwance Bai tashi ba,kiyi hakuri mu k'wanta haka ba abinda Zan sake Miki.


"Ai kasan bakyau kwana ba Kaya"


Menene a jikinki Koh tsirara kike yanzun?


"Rigan fa"


Ai nace bazan miki kome ba yace Yana jawota jikinsa matseta yayi a hankali ya jawo blanket inda ke Kan kadon ya rufe jikinsu.


***********


Washe gari Kamar kullum bayan Al'ameen ya dawo sallan asuba, sunnah TV Sumayya ta kunna musu daga ita harshi in suna kwance suna sauraron wa'azi.


Sai wajen 7:3pm Sumayya ta mike shara tayi yayan Khadija ya Mata wanke wanke, ruwan zafi ta jona abuta,Yana tafasa ta juye a boker tasawa yayan Khadija nasa, ta shiga ban dakin


tana fita yayan Khadija ma wanka ya Shiga.


Vayan sun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login