Showing 54001 words to 57000 words out of 58555 words
kafin ta ce " ranka shi dade , akwai wata bishiya bayan masarautar nan , ita kadai ce a wajen , ina son a cire ta "
cike da rudu kowa ya ke maimaita abun da ta fada
har sai kanshi Diya sai da ya ce " ranki shi dade , bishiya kuma ? wace irin bishiya ? "
wani dan karamin murmushi ta saki ta na fadin " Bishiya dai , na san da wuya ku san da ita saboda cen bayan masarautar ta ke da ga yamma , babu komai a wajen sai wannan bishiyar , ina son a cire "
har Diya ya bude zai yi magana Malik ya daga mishi hannu ya na fadin " ku yi abun da ta ce "
cikin rudu Diya ya ce " amma ranka shi dade , me ye laifin bishiyar , a .... "
cikin nitsuwa Malik ya katse shi da cewa " ku yi abun da ta ce , yanzun nan "
gyada mishi kai Diya ya yi a hankali kafin ya bawa wasu dogarai umarni a kan su je su cire bishiyar da ke bayan masarautar da ga yamma , ba musu wasu dogarai har guda shidda su ka fice fadar dan cika umarnin Malik
su na fita Inaya ta saki wani kyawatencen murmushi ta sunkuyar da kai ta na fadin " na gode ranka shi dade "
gyada mata kai kawai Malik ya yi da allamun na miskilancin da izzar a sama su ke a yanzu
" zan iya tafiya ? " ta fada cikin sanyin murya
yanzu ma gyada mata kai ya yi ba tare da ya ce komai ba ya na kallon ta
wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ta yi mishi kiss cikin iska har da kashe ido guda
wani dan zaro idanu ya yi ya na kallon ta nan take kawai ya ji duk sigar jikinsa ta tashi ,
( π€£π€£π€£π€£ Ku taimaka kar ta kashe min Malik lokacin shi bai yi ba ππ )
sarai ta lura da ta tabo mishi abun , amma kamar ba ta yi komai ba ta juya ta fice fadar
ta na fita Diya ya sunkuyo wajen Malik ya na fadin " Malik , ni fa ban ga dalilin cire bishiyar nan ba , yo ni ko zaman ta ban san da shi sai yanzu da ta yi maganar "
kassa kassa Malik ya ce mishi " ni kai na ban san da zaman bishiyar , amma tun da ta ce a cire ta , ita ta san dalilin ta na yi hakan "
" okay " Diya ya fada a takaice kafin ya koma ya gyara tsayuwarshi , da ga haka su ka ci gaba da aikin su
βͺINAYA
a hankali ta turo kofar dakin da MALIKAT AL'UMU ke ciki ta na sallama
a tare Rouksar da Tesnim su ka juya su na amsa mata sallamar ta , Tesnim na ganin ta ta saki wani kyawatencen murmushi ta na fadin " baby ! "
da murmushi a face din ta Inaya ta karaso wajen Tesnim ta rungume ta , ta na fadin " barka da safiya Aunty Tesnim "
murmushi mai dan sauti Tesnim ta yi ta na fadin " barka baby , hope ki na lafiya ? "
" Fine " Inaya ta fada ta na raba jikinta sa na Tesnim
a hankali Rouksar da ke zaune baya ta mike ta na fadin " Tes , ni zan tafi "
da sauri Inaya ta ce mata " ina kuma za ki je ? ko dan na zo ne za ki tafiya ? "
wata yar karamar dariya Tesnim ta yi ta na fadin " no baby ba haka ba ne , gida za ta koma dama ta zo ta yi min bankwana ne "
dan tabe baki Inaya ta yi kafin ta tako gaban Rouksar ta ce "hmm kin gama aikin ki shi ne za ki tafi ko ? "
wani dan karamin tsaki Rouksar ta yi kafin ta juya ta kalli Tesnim ta ce " Tes , sai mun yi waya " ta fada ta na kokarin takawa
da sauri Inaya ta riko hannunta , ta medo ta baya da karfi ta na fadin " babu inda za ki je "
[26/10 Γ 07:14] MEERAH:
β€βE X I L E D P R I N C Eββ€
( LOVE MEETS POWER ) ππ₯
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : MEERAH βπ
γBOOK ________3 πβγ
______________________βββββββ___________________
ο½ P A G E β¦β¦β¦17 πΉπο½
a tare Tesnim da Rouksar su ka zaro idanu su na kallon Inaya
a hankali Tesnim ta karaso geffen Inaya ta na fadin " baby , lafiya ki ka tsayar da ita ? me ya faru ? "
da sauri Rouksar ta ce " Tes , ni fa ban san abun da na yi wa yarinyar nan ba , tun lokacin da na shigo masarautar nan duk ta dauki tsanar duniyar nan ta daura min kawai dan na ce ta rabu da Malik , ni da farko ban san abun da ke tsakanin su ba shi ya sa na yi mata wannan kashedin saboda ina son shi , amma kin gani yanzu na bar zancen , asali ma Daular Ottoman zan koma "
a hankali Tesnim ta kai hannu saman shoulder din Inaya ta na wani dan karamin murmushi ta ce " baby , na san kishi ki ke yi , kar ki damu kanki , Malik ba shi da wata mata a duniya bayan ke , please ki sake mata ku yi bankwana , may be shi ne last time za ku ga juna "
wani cool murmushi Inaya ta saki kafin ta ce " ba za ta bar wajen nan ba sai ta cire abun da ta yi wa momy , idan kuma ta dauka da wassa na ke bismillah ga hanya nan " ta kai karshen ta na nuna mata hanyar fita
cikin bacin rai Rouksar ta ce mata " ba ki da hankali wlh " ta kai karshen ta na fara takawa
da sauri Tesnim ta bi bayan ta ta na fadin " Rouksar , please ki ts....... "
ba ta kai karshen maganar ta ba ta ga Rouksar ta tsaya cak ta na sakin wata yar karamar kara ta dafe saitin zuciyar ta
" Rouksar , lafiya ? " Tesnim ta fada ta na nufar Rouksar
da sauri Inaya ta riko hannun ta , ta na fadin " Ki tsaya kar ki taba ta " ta kai karshen ta na janyo ta da karfi ta yo baya har sai da ta fadi kassa
a rude Tesnim ta mike ta na kallon Inaya ta ce " baby , lafiyar ki kuwa ? " ta kai karshen ta na fara takawa za ta nufar Rouksar da ta Zube a kassa ta na murkuso
da sauri Inaya ta riko ta da duk hannayanta biyu ta na fadin " Aunty Tesnim , kar ki taba ta , don Allah wlh za ta cutar da ke , asirin da ta yi wa momy ne na kare "
cak Tesnim ta tsaya ta na kallon Inaya irin kallon nan na rudu kafin ta juya ta kali Rouksar
a hankali Rouksar ta mike sai faman hakki ta ke yi , murya a disashe ta ce " me ki ka yi wa bishiyar nan ? " ta fada ta na kallon Inaya idanun ta cike da ruwa har wani lumshe su ta ke kamar mai jin barci
cikin ko in kula Inaya ta ce mata " na sa a cire ta , kuma na san yanzu haka sun kusa Kamalawa "
Dum Rouksar ta ji zuciyar ta ta buga wata yar karamar kara ta saki ta na fadin " No , me ya sa za ki yi haka , ba ki san abun da ki ka aikata yanzu , na tabbatar miki abun da zai biyo bayana ba za ki iya yaki da shi ba "
ba ta gama rufe bakin ta ba Tesnim ta daga murya ta na fadin " ya isa haka , wai maganar me ku ke yi haka ? na kassa ganewa "
Har Rouksar ta bude baki za ta yi magana kawai ta ga Ruhin MALIKAT AL'UMU ya shigo dakin ya nufi MALIKAT AL'UMU zai koma jikin ta
a dubu dari Rouksar ta yi kokarin kamo shi ta na sakin wata yar karamar kara
amma ina ko taku biyu ba ta yi ba ya shiga jikin MALIKAT AL'UMU
wani irin dogon nunfashi MALIKAT AL'UMU ta ja kafin ta ware idanun ta a dubu dari ta mike zaune ta na nunfashi da karfi
a dubu dari Inaya da Tesnim su ka nufe ta su na fadin " momy , momy "
a rude MALIKAT AL'UMU ta ke kallon wajen ta na fadin " Baby , Tesnim , me mu ke yi a wajen nan kuma ? "
har Tesnim ta bude baki za ta yi magana su ka jiyo Muryar Rouksar ta na fadin " why , why za ki yi haka , ba ki san abun da ki aikata yanzu ba , wlh abun da zai biyo baya ya fi karfin ku baki daya "
a rude su ke kallon Rouksar ta Zube a kassa , nan take idanun ta su ka sauya su ka koma na maciji , har skin din ta ta koma ta maciji
a razane Tesnim da Inaya su ka saki kara su ka fada jikin MALIKAT AL'UMU su na sakin kara , MALIKAT AL'UMU kuma ta na faman karanto addu'ar tsari
su na a haka kawai su ka ga Rouksar ta koma wani dankareren maciji
wata irin razananiyar kara ce Tesnim ta saki ta na kara shigewa jikin MALIKAT AL'UMU ta na karanto kalmar shahada
karar da ta saki ne ya sa Guards din da ke tsaye bakin kofar su ka shigo
su na ganin macijin Rouksar su ka tsaya cak su na karanto kalmar shahada , nan take su ka fiddo gun su ka fara harbin shi
amma ina ko a jikin shi , nan take ya sa wutsiyar shi ya buge guards din nan su ka yi cikin bango su ka fadi
su na faduwa Inaya ta raba jikin ta da na MALIKAT AL'UMU
da sauri Tesnim ta riko hannun ta ta na fadin " kar ki tafi za ta cutar da ke "
da karfi Inaya ta kwace hannun ta , ta fara takawa ta nufi macijin nan lips din ta na motsi allamun ta karanto wani abu
ta na karasowa dab da macijin nan idanun ta su ka koma bakin kirin ko digon fari babu , a hankali gown din jikin ta da Alkyabar ta su ka koma baki kirin , har wani bakin hayaki ke tashi da ga saman su , veil din ta ya warware da kan shi ya fado kassa , gashin ta ya fara yin sama , bakinshi ya kara cizawa har wani kwarri ya yi kamar an nadde shi
Tesnim na ganin haka ta fadi sumamiya a wajen dan abun ya fi karfin ta , MALIKAT AL'UMU kuma bayan kalmar shahada ba abun da ke fitowa da ga bakinta , zancen guards kuma a bar ma maganar su dan tun bugewar ban da maciji ya yi musu , su ka sume a wajen
a hankali Inaya ta daga hannu sama , kamar da ga sama wata katuwar sword baki kirin mai mugun tsawo ta fito cikin hannunta da ta daga sama
move guda ta yi da hannunta ta raba macijin nan gida biyu da takobin hannunta
nan take wata bakar guguwa ta tashi ta mamaye sa-san macijin nan kafin ta bace bat tare da macijin kamar ba a taba yi ba
ya na bacewa ko Malik da Diya su ka turo kofar dakin su ka shigo kamar an koro su , lokacin da guards din nan su ka shigo dakin guda cikin su ya juya da sauri dan ya je ya fadawa Malik abun da ke faruwa
cak Malik da Diya su ka tsaya su na kallon Inaya tsaye da wannan sword a hannun ta ga idanun ta sun koma bakin kirin ba karamar razana Diya ya yi ba har ya fara karanto kalmar shahada
a hankali Malik ya daga kafa ya karaso cikin dakin , kafin ya yi taku biyu wannan sword din hannun ta ta bace bat , kaya jikin ta su ka koma kamar da farko , a hankali ta fara lumshe idanunta , ta fara yin kassa allamun sumewa za ta yi
da sauri Malik ya tako ya riko kugun ta ya janyo ta jikin shi , ya daura hannunshi saman kumatunta ya fara bubugawa a hankali ya na cewa " Cutie , Cutie ! "
wani irin dogon nunfashi Inaya ta ja , a razane ta ware idanun ta ta na sakin kara
da sauri ya rungume ta jikin shi ya na fadin " calm down ba abun da ya faru "
ta na jin Muryar shi ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya
a hankali ya dago ta da ga jikin shi ya talabo face din ta da hannayanshi ya ce " shikenan ? "
a hankali ta gyada mishi kai ta na sakin wani dan karamin murmushi
lips din shi ya kai saman forehead din ta ya manna mata kiss kafin ya raba ta geffen ta ya nufi MALIKAT AL'UMU ya riko hannayan ta ya ce " momy , ki na lafiya ? "
a rude MALIKAT AL'UMU ke fadin " Nawfel , mafarki na ke yi amma ko ? "
cikin sigar rarrashi ya ce mata " calm down momy , ba abun da ya faru , ki kontar da hankalin ki "
da sauri ta katse shi da cewa " Nawfel ta ya za ka ce na kontar da hankalina , yarinyar da ta girma gaban idona ta koma maciji , ni , ni , ni ban ma san yadda zan kwatanta maka , wacece yarinyar nan da ka kawo matsayin matar , wlh mutum ba ce aljana ce " ta fada da allamun ta fita cikin hayacin ta
a hankali Malik ya juya ya kalli Inaya da ke tsaye kamar an dassa ta a wajen
wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juyo ya kalli MALIKAT AL'UMU ya ce " momy , ba abun da ya faru , ki kontar da hankalin ki please "
a hankali MALIKAT AL'UMU ta sauke ajiyar zuciya ta na lumshe idanun ta , ya na jin ta sauke ajiyar zuciya ya juya ya kalli Tesnim da ke konce a wajen
hannu ya kai hannu wajen yar drawer da ke bakin gadon , ya dauki bottle din ruwa guda , ya bude ya zuba kadan a hannunshi ya yarfawa Tesnim
wata razananiyar kara ta saki ta na dawo cikin hayacinta kafin ta mike da sauri ta fada jikin MALIKAT AL'UMU ta na sakin kuka kamar mahaukaciya
a hankali ya daura hannun shi saman face din Tesnim ya na fadin " Tesnim , ki kontar da hankalin ki please "
slowly ta ware idanun ta , ba su sauka ko ina ba sai cikin na Inaya
wata yar karamar kara ta saki ta na lumshe idanunta da karfi ta kara kankame MALIKAT AL'UMU
cikin sanyin murya Malik ya ce mata " Tesnim , ki kontar da hankalin ki ki fada min abun da ya faru "
ba tare da ta bude idanun ta ba ta shiga ba shi labarin abun da ya faru tun shigowar Inaya dakin har zuwa lokacin da ta suma
a hankali Malik ya juya ya kalli Inaya ta ce " minene a cikin bishiyar da ki ka ce a cire ? "
cikin ko in kula Inaya ta ce mishi " a ciki ne ta boye ruhin momy , da ba a cire ta ba momy ba za ta tashi ba , kuma ita ce ta saka poison cikin fruits din da ka sha , shi ya sa su ka kasa samo mishi antidote saboda na tsafi ne , ni tun da na sauke ido saman yarinyar nan na ji ba ta konta min ba " ta kai karshen ta na turo dan bakin nan nata
kare mata kallo da kyau Malik ya yi kafin ya juya ya kalli Diya da ya yi mutuwar tsaye bakin kofa
da sauri Diya ya girgiza mishi kai allamun bai sani ba
tun kafin Malik ya juyo MALIKAT AL'UMU ta ce mishi " Nawfel , wacece yarinyar nan ? aljana ce ba mutum ba "
cikin nitsuwa Malik ya mike ya juya ya kalli Diya ya ce " ka sa a shirya min jet yanzu zuwa US "
gyada mishi kai Diya ya yi kafin ya juya ya bar dakin
ya na fita Malik ya juya ya kalli MALIKAT AL'UMU ya ce " Momy , matata ba aljana ba ce mutum ce , dama jira na ke ji tashi , tun da yanzu kin tashi ba zan kwana cikin garin Saudiya ba , i'm tired , na gaji , kullum neman kashe ni a ke yi , har wanda ke jini na bai kyale ni ba ba na tunanin wani zai iya kyale ni saboda wannan banzan Mulkin , na hakura da kujerar Malik , ba zan iya jure wani abu ya samu familyna a dalili na , su je su yi abun da su ke so da kujerar ni dai ba zan sake hawan ta ba "
wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta mika mishi hannu
ba musu ya daura hannun shi saman nata ya dawo ya zauna
a hankali ta matso da bakin ta