Showing 3001 words to 6000 words out of 6282 words

Chapter 2 - MATAR HARIJI Part 1 Free PAGE 1-10.txt

NIl   

07 Apr 2025

2458

zuwa babu bata lkc suka daga zuwa South Africa zuciyarsa cike da kewar parents dinsa da yar fulaninsa Hauwa da kewarta take neman zame masa jiki a wannan lkcn haka ya wanzu cikin wata irin rayuwa daya kasa gane wacce iri ce kullum zasuyi waya sau biyu da Mubaraka ya tambayeta lfyrta data yarsa Fadwah amma ya kasa daina kewar qasarsa ta gado musamman Rugar Sambajo.



____________Kwananta uku bata dauki tallan nono ba ko dandali ta daina fita duk a qoqarinta na karsu hadu da Madi dan burni yace zai sanya mata bindara tunda taji Indo qawarta da akayi Mata aure tana cewa bindira lubebiyace idan ta shiga bata iya fita saidai ta yayyaga mutum kuma idan ta tashi dane yake tunkudota waje.

Shiyasa take masifar tsoron bindira ita har kuka takeyi da tumami idan akace zaa kaita asa mata bindira, tana tafi tana yan waqoqinta taci uwar dammara abinka tayi kwalliya ta rambada kanta kile harda digon india a goshinta da kumatunta tasa kayansu na fulani shudaye tana tafe tana waqar “lula lulaye aluliya zani bikin andi aluliya" batasan binta akeyi ba saida tazo jikin wata bishiya kawai taji an dumbular mata nono an kwasa da gudu.



Aikuwa ta dora hannunta akan nononta tana ihu tana burgima tana hwadin “shikenan na mitu na lalashe dan innini na sun tabamin wayyoh Goggo wayyohhhh Baffa wlh bazan yarda ba saina taba nonon uwarsa nima" wasu yanmata ne guda uku sukazo wuccewa suka ganta a kwance duk tayi birgima tayi tumu² suka tsaya suna kallonta tare da tafa hannu sukace “Hamdi imboni Jiddoh meye hakadin?"

Miqewa tayi zaune tana karkade qasar data shiga cikin dogo baqin gashinta da ya mulku da manshanu tace “Qur'ani saina mulmulawa uwar Wanda ya dumbularmin Inninina Fura a gatonta"🤣🤣



Dariya suka kwashe da ita Lantana ta kalli Jummai tace “kiji doluwa to yau aka fara dumbular inninin naki naga cewa akayi har Kado kike bawa yakesha shiyasa sukayi girma sukayi ruguza ruguza haka"

Zabura tayi tace “kutmar dumadu naci hagu naci dama naci tattabatsinin kantalin baqoramar inyaniyar marurun tsohon gwailon uban wanda ya hwadi haka" kafin suyi wani aune ta hade kansu guri guda ta kama jibgarsu hagu da dama tana wani tsalle tana naushi ta ko Ina.



Suna ganin haka kowa yaci na kare ta kuwa rufa musu baya a guje fadi take.

Yau har bayan tsoho da tsohuwa suna doki doki sai nabi ƴa naci uwar galken ubanta Kaɗon dako mgn bata dameshi ba ina ya iya wannan iskancin shi banda sumba da qaquba babu abinda ya iya kuma qur'ani saina hwaɗí muhi bashi kawo lantarki gidanku"

Yanda suka rinqa gudun a daji abin abin dariya kuma sai qara rungume qirjinta takeyi wai kada a qara dumbular mata nono😁





Jitayi an riƙeta ta baya taja ta tsaya tana huci tare da waiwayowa zatayi bala'i sai tayi ƙasa luuuu saboda ganin yayanta lawan tasan ta kaɗe har rassanta rirriƙeshi tayi tana kuka tana cewa.

"Alqur'an bani na tsokalesu ba sune kawai ina kukana da burgimar tuba sukazo suka tambayeni meye yasani kuka nace adumbili akayimin shine sukace wai ai dama ance ina bawa Kaɗo nono na wannan na jikina bana shanuwa ba yanasha kuma aradun Allah ƙarya sukeyi barima na fito maka dashi ka gani"



Hannu ya dora aka yace “honi lawwali ni zaki nunawa dan qaniyarki yar ja'ira tashi muje wuro kiyi bayani" yanayin gaba ta miqe da sauri ta nade zanenta ta kuma kwasa da gudu ta nufi gdan yana kiranta yana komai amma bata tsayaba saida ta isa gdan ta shige dakin kishiyar Goggonta tana mazari Inna Jummah ta miqe da sauri tace.

“Wanne niya meye hakadin ubanwa kika taokano" sake qanqameta tayi tana kuka tana girgiza kai yana zuwa ya cake yace “zakici qaniyarki yar kusun uwa"



Yana fita ta zube a tsakar dakin tana mayar da numfashi tace “wlh sai nayi qulla ciki akan wanda yayimin adumbuli" tafa hannu jummah tayi tace “gide shiyasa nice da baffanki yayi miki aure"

Saurin rufe Mata baki tayi tace qur'ani baniso ance idan akayi wai...Wai...." Saurin daga mata hannu tayi tace “aradu ya isa kuma dole baffanki ya aurar dake shekara sha hudu qawayenki harda yayansu ke kinanan kina bambadanci a gari"



Miqewa tayi tace “ai saiki aurar dani din yo aradun Allah guduwa zanyi kamar yanda Ladin Moddibo ta gudu nima na rinqa shigowa daga maraya Ina taunar danqo Ina tafiya qwasqwas.

Binta tayi da kallo har ta fice daga dakin ta nufi dakinsu ta kwanta tare dajan mayani ta lullube jikinta dashi yau goggonta da kanta ta fita tallan nono, zuciyarta ce ta tafi tunanin Lameer ta dallawa kanta mari tare da jan tsaki tace “aikin banza ma ko meye gamina dashi.
___________Lkc yanata tafiyarwa Lameer ya kasa sukuni kullum da tunanin Hauwah yake kwana yake tashi idan ya kwanta bashida mafarki sai nata wannan mafarki shine yake dauke masa kewar abubuwa da yawa saboda idan yayishi yakan yini cikin walwala da farin ciki.

Watansu biyu suka gama abinda sukaje yi suka fara haramar tahowa gida shidai farin ciki gurinsa baa cewa komai ya rasa meye yakeji game da Hauwah amma yafi alaqanta abin da soyayya to kuma shi wanne irin so yakeyi mata ya zaiyi ma ya tunkari iyayenta yace yana son yarsu?



Ya fahimci sudin irin fulanin nan ne masu tsauri sosai a dan shiga cikinsu din da yakeyi ya fahimci sun tsani Bahaushe musamman ta fanni auratayya zaiyi walaha kaji mutanen rugar Sambajo sun aurar a waje ko sun auro.

“To wai nima da nake wannan lissafin ta Yaya zan auri mace sama da daya bayan dayar ma bana iya sauke nauyinta dake kaina dari bisa dari?"

Ya tambayi kansa yana shafa qasumbarsa tare da lumshe idonsa ya hadiye wani yawu me ciwo shikam yanason Hauwah matsayin Mata to amma ya zaiyi ya riqeta ya sauke mata dukkan haqqoqinta sannan ya zaiyi da Hajiyarsa data tsani ko mgnr kishiya taji wani yayi balleshi da dama kamar ta tsaneshi cikin yayanta ya lura har tafison Mubaraka akansa saboda indai abi ya shafi Mubaraka to yanzu zata rufe ido taci mutuncin sa, "Ni wai ya zanyi ne?" ya fada yana dafe qirjinsa da yakeyi masa zafi saboda ba yau ya fara wannan tunanin ba.

Ya jima yana saqawa da warwarewa domin samun mafita amma ya kasa jin Hauwah yakeyi a duk wata kusurwa ta jikinsa.



Ji yakeyi dama ace zai sameta batare da yasha wahala ba shikam koma meye zai faru saidai ya faru Hauwah itace muradinsa a yanzu baya fatan ya rasata a rayuwarsa jima yakeyi kamar idan ya rasa Jiddah bazai rayu ba.



____________Abubuwa da dama sun faru a cikin watanni biyun ciki harda tsayar da ranar aurenta da Madi wannan abu ba qaramin dagula lissafin Jiddoh yayi ba ta tashi hankalin kowa akan cewa itafa bazata aure Madi ba dan iskane har cewa yayi suzo su zagaya duhun dawa ya gwada mata bindira.

Duk yanda tayi tunanin abin zaizo Mata da sauqi ta kasa samun wannan gatan hakan yasa kullum cikin kuka take da damuwa ko zaman gidan ta daina duk da sun hanata fita amma suna fita tallan nono zata haure dangar karar da suka kewaye gidansu da ita ta shiga cikin duhun daji.



Sau tari sai baffanta yaje gindin magwaron data mayar gurin zamanta ya korota sannan take tafiya hatta abinci ta dainaci saidai idan taji yunwa Tasha madarar shanu ta kwanta sukam iyayen ko a jikinsu hidimarsu kawai sukeyi.

Ana haka ta fara rashin lfy sosai kamar bazatayi ba nanfa hankalin baffanta ya tashi sosai ya shiga damuwa dan baiyi tunanin qiyayyar da takewa dakai har ta kwanta jinya ba.



Yaso ya canza raayi amma yayarsa Yadammu tazo har gida ta rinqa sababin bala'i wai ai iskokine da Jiddoh dama haukanta ba irin na masu hankali bane wauta tsokana da rashin kunya duk ta tattara kuma a gurin uwarta ta kwashe komai.

Shiga gdan yayi yana fadin “Hari! Hari!! Ke Hari dake nake wannan ja'irar yar taki bazata jamin abin fadaba maza fito Yadammu tace yau Boka bawa yake hawa bori fito da Jiddoh muje yau duk uban aljanin dake kanta saiya sauka kuma aure tsakaninta da Madile babu fashi saidai idan bana raye"



Dukkan matan gdan fitowa sukayi suka fara sallalami suna fadin “oya maigida Moddibo Dalha ma yana maganin iskoki basai kaje gurin Boka Bawa ba"

Daquwa ya watsa musu yace “kunfini ko kunfi Yadammu sanin abinda ya dashe ne to aradun Allah duk Wanda shi qara buda baki sai ta koma gdan tsohonta almuran banza almuran wofi ai dama nasan kune kuke daurewa Jiddoh gindi takeyin abinda taga dama nan har gda akazo aka yimin gorin nabarta ta gandame ta zama uwar mata a gda tunda rugannan take babu yar data tabayin shakara sha hudu a gdan iyayenta sai ita kunsani yarinya tun tanada shekara tara ake dauranta aure a rugannan amma ita saboda bakin jininta da mugun halinta gatanan daqyar ta samu Madilen ma ya tsaya yo banda sharrin iskoki inane zatashe batasonshi har tani jinya yo kwarankwatsa saidai tayi bunga"



Shiga daki goggonta tayi tana tashinta amma fir taqi tashi saida sukakai ruwa rana sannan da taga Baffa ya dauko kokara zai sabeta yasata tashi ta fice da gudu tayi bayan gdan gudu takeyi sosai bata tsayaba saida tayi nisa da rugarsu ta shiga wata fadama ta samu gindin bishiyar kashu ta zauna tana haki dafe da qirjinta saida tayi me isarta sannan ta hade kanta da gwiwa taci gaba da rera kukanta zuciyarta na tuno mata da Kado tana tuna rana ta farko da suka fara haduwa dashi.
_________Goggonta ta dora Mata tallan nono su Idin Tasha suka shanye Mata harda sanyata ta siyo musu sukari ta zuba musu suka tashi zasu tafi tace su bata kudinta suka kama zaginta harda dungure mata kai Mati ya zare Wuqa yace zai yankata idan bata tafiba babu arziqi ta tashi ta dauki qorenta ta nufi hanyar rugarsu tana tafi tana waiwaye batayi auneba kawai taji ta bugi mutum tayi baya da sauri jikinta na rawa ta dago ta kalleshi kyakkyawan Saurayi me cikar zati dago kakkaura wankan tarwada sanye da kayan turawa injita da fada.

Shima kallonta yakeyi cikin hasala yace “ke wacce irin yarinya ce kina tafe kamar makauniya kalla yanda kika batamin jiki da nono...."



Daga hannunta tayi tana ajiyar zuciya da niyyar bashi haƙuri bata iya buɗe bakinta ba saboda kukan da yaci ƙarfinta kawai sai ta kama ƙafarsa ta fashe da kuka.

Jikinsa ne yayi sanyi tunaninsa mgnr daya fada mata ce tasata kuka shima durƙushewa yayi ya sanya hannunsa ya ɗago fuskarta ya zuba mata kyawawan manyan idanunsa ƙirjinsa na bugawa da sauri da sauri yace "meye dalilin kukan?"

Cikin in...ina tace "su... su Idi da Mati suka shanyemin nono har sukashe ni siyo masu sukari da ciniki na kuma suka hanani kuɗin kuma sukashe idan nace sune sai sun kasheni kullum sai sunsa Goggona ta bugeni idan kuma na hanasu su shunamin karnukansu suyita yimin haushi kwanaki wani har cizona yayi" ta zauna sosai ta bude masa gurin saman santala santalan sangalalin qafarta farare tas da suka cika da suma kwantacciya lufluf dashi ya sauke idonsa a gurin da karen ya cijeta gurin har yayi rami sai ruwa yake zubarwa...........



Rintse idonsa yayi da sauri yace “subhanallahi meye yasa bakije an wanke miki gurin ba?" Shiru tayi tana sharar hawaye kafin ya miqe yace “zo na wanke miki nasa miki magani" batayi jayayya dashi ba ta miqe tabishi yasa ta zauna a gefen motarsa shikuma ya dauko hydrogen da corton ya fara wanke Mata tana kuka tana ciccije leɓe yanayi Mata sannu lkc zuwa lkc yana ɗagowa yana kallon kyakkyawar fuskarta data jiqe sharƙaf da hawaye yanajin wani tausayinta yana kwarara a sassan jikinsa.

Koda ya gama yayi mata plasting ɗin zama yayi ya zuba mata ido yana kallon kyakkyawar halittar bafulanar yanajin wani shauqi na taso masa, a hankali cikin dashewar murya yace



"Ya sunanki?" haɗiye kukanta tayi tace "Jiddoh Arɗo Jibir" iska ya furzar ya miƙe yace "ok gobe kizonan idan kin ɗauko nonon ki kawo min zan siya zan taho da likita yayi miki allura kinsan cizo kare dafine dashi ƙafarki zata iya ruɓewa idan baayi miki allura ba, na nawane nonon dasu Idin suka shanye miki"

Shiru tayi kamar bazatayi mgn ba ta fara haɗe kayanta bayan ta gama ta miƙe zata tafi ya riƙe hijjab dinta fuskarsa murtuk ya zaro dubu biyu ya bata yace "ki ajiyemin canji na gobe zan karba kada Goggo ta dakarmin ke" ƙememe taƙi karɓar kudin wai dukanta zaayi nononta na jaka huɗu da rabi ne.





Kama gefen kallabinta yayi ya ɗaure mata dubu daya ya bata ɗaya a hannunta yace "kice da goggo wani ne ya siyi nono babu canji shine yace gobe kibashi na rabin jakar"

Dariya tayi tace "aradun Allah kaɗo kanada wayo sosai zaka tai dani burni na ƙaro wayo?"

dariya ta bashi ya shiga motarsa ya kunna tana tsaye har yayi kwana zai tafi ta bude baki tace "Kaɗo" juyowa yayi ya tsaya wai kaɗo sai kuma yayi murmushi ya daga mata hannu itama ta daga masa hannu ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo yana ajiyar zuciya a hankali yace "Hauwa'u kulu Maijiddah.

Figar motar yayi a guje ya fice daga lungun tundaga wannan lkc ya kasance kullum shine yake siye nononta idan ta dauko idan kuma zaiyi tafiya bazaizo ba to yakan bawa manajan gdan gonarsa kudin ya rinƙa bata kullum hakanne ya wanzar da shaƙuwa me ƙarfi tsakaninsu.
___________Tananan zaune a wannan guri har duhun magaruba ya fara sawo kai ta miƙe a hankali ta fara fita daga saƙaƙiyar har ta fito titi sosai ta fara tafiya cikin rashin kuzari har ta isa rugarsu takuwa yi saa Allah bai haɗata da ƴan dumbule ba don ta lura nononta da Allah ya wadatata dasu suna mugun jan hankalin maza duk da cewa kullum cikin taresu takeyi da hannunta kasancewar ba bra suke sanyawa ba haka suke yawo da abunsu a tsaye cako cako wannan dalilin yasa kullum take taresu saboda kunya takeji taga sunyi cokal cokal dinnan.



Isarta gda kenan taga gilmawar wata baqar LAND GRUSSER ta bayan bukkokinsu a guje hakanan taji gabanta ya fadi tanason ganin waye a ciki amma babu dama da alamun na cikin ma a fusace yake.

Ƙwafa tayi ta shiga gdan nasu taja tayi turus ganin ƴan gidan nasu gabaɗaya tun daga kan baffansu har zuwa kakansu mahaifin baffansu kowa yayi cirko cirko suntada gemu da alamun wani abune mara daɗi ya hwaru batasan hawa ba balle sauka taji an fincikota tsakiyar filin da mutane sama da talatin sukayiwa da'ira wanda ko gutsuttsurata akayi ƙila wani bazai samu ba anyi cilli da ita an hau bugunta ta ko'ina suna haki kamar waɗanda aka sanyasu dole.



Itakuwa baiwar Allah Jiddoh sai ihu takeyi tana roƙonsu su bar dukanta zata mutu amma babu wanda yaji tausayinta ya ƙyaleta ita kuwa goggo tashi tayi tabar gurin saboda tanayin mgn kanta zaa dawo ace tayi rashin kunya.

Basu bar jibgar Jiddoh ba saida sukaga ta daina numfashi sannan kowa ya koma gefe yayi duru duru suna kallon kallo wannan yana faɗin kaine ka daketa a makasa wannsn yana faɗin aa kaine, baffane ya ƙuta yace "yo ba gwara a kashetan ba a huta da wannan abin kunyar da ta janyo mamu, wai ni Arɗo Jibo nine Kaɗo ya iya tarar cikin idona yace yanason irin mutum daga gareni wannan wanne irin tozarci ne Jiddoh tajamin a duniya"...............

Kuka sosai Baffa yakeyi yana kwaso kwashewar albarkar duniya yana jibgawa Jiddoh dake kwance a qasa magashiyan rai a hannun Allah.

Goggo dake bayan danga tana hangen halin da ƴqr tata take ciki ta share hawaye ta koma ta zauna tana tunanin ko meye yasa baffa yake tsangwamar ɗiyar tata tilo wadda duk cikin ƴaƴansa babu meyi masa biyayya kamarta.



Allah ya sani har ranta itama bataji zata iya bawa kaɗo auren ɗaya ɗayar ɗiyar tata ba amma wannan dukan yayi yawa dole ne tasan abinyi saboda ta lura rayuwar Jiddoh ake nema a rugar tasu, da wanne zataji da auren dolen da ake shirin yi mata da ɗan shaye shaye ko kuwa da mangarin da akeyi mata ko kuwa da mugayen alkaba'ain da akeyi mata?

Bata koma cikin gdanba saida kowa ya fashe sannan ta shiga ta tarar da jummai akan Jiddoh tanayi mata surkullensu na fulani tana shafa mata ruwa a fuskarta.

Miƙa tayi tare da jan zuciya suka miƙar da ita zaune ta zauna tana bude idonta daya kumbura saboda bugu tana kallonsu gwaggo da Inna Jumme tana matsar kwallah ta buɗe bakinta daqyar tace.

"Meye nayiwa Su Moddibo da Arɗo suke buguna wlh bansan komai da nayi musu ba wayyoh bayana Gwaggo wayyoh ƙuguna zani mutu wayyoh kaico...." tana mgnr ne cikin zubar hawaye kamata sukayi suka shiga da ita bukkarsu Inna Jumme ta ɗora sanwar ruwan zafi ta dawo ta zauna kusa da ita tace.

"Kema Jiddoh bakyaji kinsani cewa a wannan rugar tamu bamu bawa kaɗo aure meye yakaiki soyayya da kaɗo kaɗon ma maƙiyi irin jinin sarkin noma Mudansir na alƙalawa kinsan har abada babu jituwa tsakaninmu da irin sarkin noma nikam saidai hande jiddoh wai har kika turoshi shikuma ya ɗauko tsayi kamar daren mutuwa yazo wai yana neman izinin aurenki"

Kallonsu takeyi da rashin fahimta tace "ni bani bace ɓatan burtali yayi ya shigo jejinmu amma ni ban saneshi ba aradun Allah..."







Buge mata baki tayi tace "kusun uwarki ya kawoshi bakece kika faɗi mashi sunanki Hauwa ba yar gidar Arɗo jibo ko kuwa ƙarya yayi miki to nidai shawari zan baki in kinƙi kisha wahala garama ki nemai inda kuke haɗuwa ki hwaɗi masa yabi tsawanyarsa daban kibi taki saboda mudai ko mazan rugarmu sun qare bamu daukan subarjo kamarki mu bawa kaɗo kaɗon ma jinin Sarkin noma"

Miƙewa Inna jumme tayi taje ta juye ruwan zafin ta surka tazo ta kamata ta kaita makewayi ta rinƙa gasa mata jiki ita kuma tana kuka tana ciccijewa tana rufe ƙirjinta a cewarta da tsirarar nono gara ta gindi.🙈
__________Shigar dare Lameer yayi cikin garin saboda yana tafiya yana hutawa kasantuwar irin suyar da zuciyarsa takeyi masa tunda yake a rayuwarsa bai taba ganin wulaƙanci irin wanda yau ya fuskanta a rugar sambajo ba.

Ikon Allah ne kawai ya kawoshi gdan yana shiga baibi takan komai ba ya

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login