Showing 6001 words to 8600 words out of 8600 words

Chapter 3 - AUREN YARINTA By Khadija s dogarai (lipton girl) .txt

ja wai wanan wanini ya ki kirana cikin daren nan
Dago fuskan shi yayi ganin haskin da ki cikin dakin shi yasan gari ya jima da waye wa
Dauka yayi yah ni
Banji abunda yace masa ba yace ya bashi 2mnt ga shinan saukowa
Sauka yayi kan gadon shi yana nishi guda guda.
Har zai shiga toilet ya watsa ruwa kuma sai ya fasa don baya son ya karya alkaware yace nan da 2mnt zai sauko kuma yasan idan ya tsaya wanka zai jima sosai haka ya fita dakin shi Tun a sama ya hango su sunkai su 15 waton abokan shi suna zauni kan kujera ko wanin su reki da cup in jus Nafisa kuwa sai murmushi taki ye masu
Kallon ta yayi "I hope bata lalata masu abun sha ba"
Abokinan da ya hango shi sama ya meki tsaye yana bugun na kusa da shi duba ango guda guda suka fara tashi sun ka saki baki suna kallon shi har ya karaso kusa da su kallon su yaki ye
"What happen meyasa kuki ye man wanan kallon kamar kun ga dodo"


Nafisa kuwa ba abunda taki ye sai dariya.
Kallo daya yayi mata ta saida dariyan ta.
Dukan su suka saka dariya. Aminu kuwa har kasa ya kai yana dariya..




Kallon shi yayi
"Meye abun dariya a ciki pls saje up"


Tashi yayi.
"Tell me what wrong with my face....!


Jan shi yayi har gurin dinner area gurin da aka laka mirrow ya kai shi ya nuna masa.
Wani ihu ya buga dukan su sai da suka razana dukan su sukaye shiru
Nafisa kuwa bata san lokacin da ta saki dariya ba
Karasawa yayi kusa da ita
"How dare you???
Murmushi tayi "Yaya Aziz kaga yanda kayi kyau kuwa kaga nayi maka gira na shafa maka eye shadow ji yanda bakin ga yayi kyau da na shafa maka jan baki ga blush so beautiful da mace kaki da kayi kyau sosai.. Shiyasa aki cewa soyaya dadi ae wanan duk cikin soyaya ni"
Bai san lokacin da ya daga hanu ya wanka mata mare ba sai da ta kai kasa
Aminu ya yo kan shi


"Aziz kana da hankali kuwa? Matar ka zaka mara"
"Enought Aminu bana son jin kome let me fresh up"
Haurawa yayi sama Nafisa kuwa ga kunya ga zafin mare da Aziz yayi mata kuka taki ye sosai dukan su sun tausaya mata tashi tayi ta dauko Hijab inta ta fita daga gida.......




*Tofa ko ina Nafisa zata ji muje zuwa*๐Ÿšถ๐Ÿปโ€โ™€





































Auren Yarinta
Writing by
*lipton girl*๐Ÿฅค
[12/17, 3:13 PM] ๐Ÿ’™lipton girl๐Ÿ’™: *AUREN YARINTA*
๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน


*Daga Alkalamen*โœ๐Ÿป
*Khadija s dogarai (lipton girl)*๐Ÿฅค




*A short story*๐Ÿน





*~โœ๐Ÿฝโœ๐ŸฝGOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONโœ๐Ÿฝโœ๐Ÿฝ~*








*~We are bearer's of so golden pen๐Ÿ–Š~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden penโœ,behold our words.~*


*~A product of our pen๐Ÿ–Š,savour our words, for it will cause you no pain.~*


*Addu'a Idan Ya Sauka A wani masauki a Halin Tafiya ko waninta.*


ุฃูŽุนููˆุฐู ุจููƒูŽู„ูู…ูŽุงุชู ุงู„ู„ูŽู‘ู‡ู ุงู„ุชูŽู‘ุงู…ูŽู‘ุงุชู ู…ูู†ู’ ุดูŽุฑูู‘ ู…ูŽุง ุฎูŽู„ูŽู‚ูŽ.
A'oothu bikalimatil-lahit-tammati min sharri ma khalaq.


Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abin da Ya halitta.






*Dedication*
๐Ÿ‘‡๐Ÿป


*HK nayi missing in ki over*๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜




๐ŸŒคPage 12&13.... ๐Ÿน








ยฐยฐยฐยฐYa kusan awa daya yana bathroom, da kyar ya samu ya goge kwalliyan da tayi masa, ranshi ba karamin bace yayi ba, shi yasa auren yarinta ko hauka baiyi ba, yarinya zata mai dani mahaukaci wanda bai san abunda yake nufi ba, bazan dauki wannan iskan ci nata ba zan gyara mata zama.


Kaya ya saka ya sauka inda ya tarar da abokan shi suna zaune suna jiran sa sai firan su suki ye.


Guri ya samu ya zauna, Muktar ya kamayi masa dariya.
"Mijin Yarinya har an fito".
Watsa masa harara yayi.
"Sorry".
Cigaba da hira sukayi.
Daga bisani suka koma gidajen su.




Muktar ne ya tsaya suna magana da shi.


"Amm... Aziz abunda kayi sam bai kamata ba. Kasan me idan ni ni matata tayi man haka ba zan yi mata yanda kayi mata ba imagine, marin ta fa kayi kuma a gaban friends dinka idan kai baka ga mutuncin ta ba taya mu zamu ga nata??
"Pls bana son surutun banza kayi tafiyar ka".
Murmushin takaici yayi.
"Ni Babban abokin ka ne dole na gaya maka gaskiya meyasa ba zaka karbi destiny din ka ba she is your wife kama ta yayi ka bata kulla wa ka nuna mata soyaya i know she is too young but kai ya kamata ka koya mata wasu abubuwa pls try to understand me kaga yanzu bata nan and baka ma tambayi ina taje ba baka ganta ba kasan ta fita gidan nan kuwa tana kuka only God know inda taje pls ka kwantar da hankalin ka. Ka fahimci abunda nake nufi ka zauna ka ba matar ka kulawa ka daina banzan tunanin da kake yi na barka lafiya"
Tafiyan shi yayi Ya shiga mota bai tsaya ko ina ba ya tarar da mom din shi zaune tayi zugum.
Karasawa yayi kusa da ita ya zauna a kasa.
"Mummy lafiya? Ya naga kamar kina cikin damuwa meke damun ki pls tell me kin san bana son abunda ya taba ki"
Murmushin karfin Hali tayi.
"Allah yayi maka Albarka son ina son kayi aure ni".
Zaro ido yayi "Aure kuma mummy meyasa kika yi wannan tunanin ni fa bani da wace naki so i am alone so taya zanyi aure"??


"Nayi maka kamen mata".


Juyowa yayi don ko ba'a gaya masa ba ya san gwaggon shi ce tashi yayi ya karasa kusa da ita har kasa ya kai ya gaidata.
"Sannu da zuwa Gwaggo yaushe kika karaso?".


Fuskanta dauke da murmushi.
"Yauwa.. Banjima da iso wa ba".


Hanunta ya rike ya kai ta kan kujera ta zauna.
Gyaran murya yayi.
"Nayi maka kamen mata waton yar uwarka Suhaila ".
Kallon mamaki yake yi.
"Gwaggo Suhaila fa kika ce".
"Eh kuwa. Ina fatan bazaka bijire ma magana ta ba".
Mummyn shi kuwa kokarin magana take yi ta dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu.
A kasalance yake magana.
"Amma Gwaggo naga ai Suhaila yarinya ce ba zata wuce 14years ba kuma kike ce wa na aure ta?".
"Sosai kuwa to meye in yarinya ce Mace ce fa ko shekara 10 ana iya yi mata aure kuma lafiya lau ta haihu bale 14".
Yaji kunyar maganar da tayi.


"Tau gwaggo ba damuwa amalma ni ban shirya ma auren yanzu ba saboda akwai abubuwa da yawa da akeyi kafin akawo Amarya".


"Na riga da nayi magana da Daddy din ka kuma ya yarda kawai za'a kawo maka Amarya".


"Tau gwago Allah ya bamu zaman lafiya. Ki huta lafiya".
Ya tashi ya shiga dakin shi.
Mummynsa kuwa bata ji dadi ba don taga ana yi ma dan nata auren dole.


*****


Nafisa kuwa bata tsaya ko ina ba sai gidan su Aziz tun a bakin kofa ta kara bude muryar ta.
Falo ta tarar da Dad din Aziz yana ganin ta hankalin shi ya tashi.
"Nafisa lafiya meya same ki? Meyasa kike kuka?".
Karasawa tayi kusa da shi tana kuka tana shesheka.
Kwallawa mom Aziz kira yayi.
"Hajiya salamatu kina ina maza kiyi sauri ki karaso".
"Ina zuwa Alhaji".
Ajiye kayan da ta dauko tayi da sauri ta karasa falon.
Ganin Nafisa na kuka abun ya bata mamaki.
"Nafisa meya same ki haka? ".
"Nima dai tun dazu nake tambayar ta bata ce man kome ba ki tambaye ta ki jiya ko zata gaya maki".


Jawo hanunta tayi ta zauna da ita kan kujera ruwan da ke gefenta ta bata ta sha tana sha tana saukar da numfashi.


"Gaya man diyata meya same ki?".

"Nafisa meya same fuskan ki haka kamar kwanciyar mari...."!!


Fadan Daddyn sa.


Mom kuwa abun ya bata mamaki.
"Ki gaya mana kinga hankali mu ya tashi sosai pls gaya man".


Cikin muryar kuka tace.
"Yaya Aziz ne"




Tare suka ce.
"Aziz meyasa yayi maki haka?".


"Uhmm...Amm. Mari na yayi kuma a gaban Abokan shi".


Alj. Sanusi ya zauna kan kujera dafe kan shi yayi.


Hajiya salamatu kuwa ta rasa wa za tayi lallashin sa ka Nafisa kuma ga Alj.


"Alhj. Dan Allah kada ka tayar da hankalin ka kasan kana da hawan jini kamata yayi mu kira Aziz din yayi mana bayani da kan shi saboda ba zamu yanke hukunci ba akan abunda bamu sani ba na san Aziz ba zai mare ta ba bata re da tayi masa wani babban abu ba"


Wani irin kallo yayi mata.
"Salamatu me kike nufi da hakan? Yanzu fisibililahi don tayi masa wani abu sai ya dauki hannu ya mare ta duka-duka kwana nawa da auren da har zai fara dukan ta ban aura masa ita ba don ya mai data jaka ba Aziz ya bata min rai yau matuka muddun zai rinka taba Nafisa zai rinka fuskantar fushi na!".


"Kayi hakuri Alhj. Ka kira shi ya zo".
"Ba zan kira shi ba. Idan ke zaki iya sai ki kira shi".


Tashi tayi ta dauko wayan ta kiran shi tayi amma bai daga ba...




Shikuwa wayan shi tana kusa da shi amma bai ji lokacin da tayi ringing ba maganar Muktar kawai ya tuna da ita kawar da zancen yayi.
"Dole naje na nemo ta ko bana so domin in dad ya san bata nan nasan rai na zai bace. To ina zan nemo ta? Bari naje gidan su na san can taji"


Wayan shi ya dauka ya fara hanya wayan shi ni tayi kara ganin mom in shi gaban shi ya fadi.
Ko dai Nafisa tana can?


Daukan waya yayi ya kara a kunnen sa.
Tun bai yi magana ba tace masa.
"ka same ni a gida yanzu duk abunda ka ki ye ka ajiye shi ka zo".
Ta kashe waya.
Gaban shi yana faduwa uku uku ya shiga motar shi ya nufi hanyar gidan su....






*lipton girl*๐Ÿ’™
[12/17, 3:13 PM] ๐Ÿ’™lipton girl๐Ÿ’™: *AUREN YARINTA*
๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน๐Ÿน


*Daga Alkalamen*โœ๐Ÿป
*Khadija s dogarai (lipton girl)*๐Ÿฅค




*A short story*๐Ÿน




*~We are bearer's of so golden pen๐Ÿ–Š~*


*~we write assidiously perceive no pain~.*


*~So magical,Our creative golden penโœ,behold our words.~*


*~A product of our pen๐Ÿ–Š,savour our words, for it will cause you no pain.~*




Addu'a Idan Ya Sauka A wani masauki a Halin Tafiya ko waninta.


ุฃูŽุนููˆุฐู ุจููƒูŽู„ูู…ูŽุงุชู ุงู„ู„ูŽู‘ู‡ู ุงู„ุชูŽู‘ุงู…ูŽู‘ุงุชู ู…ูู†ู’ ุดูŽุฑูู‘ ู…ูŽุง ุฎูŽู„ูŽู‚ูŽ.
A'oothu bikalimatil-lahit-tammati min sharri ma khalaq.


Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abin da Ya halitta.


*Dedication*
๐Ÿ‘‡๐Ÿป


*HK nayi missing in ki over*๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜




๐ŸŒคPage 14&15.. ..๐Ÿน










ยฐยฐยฐยฐยฐยฐยฐGabanshi yana duka uku uku ya shiga motar shi ya nufi hanyar gidan su.


Yana zuwa yayi horn mai gadi ya wangale mishi gate,guri ya samu yayi parking ya fito a bude ya bar motar ya shiga cikin gidan a falo ya same su, ganin Nafisa yayi mom din shi sai lallashin ta take yi.
Guri ya samu ya zauna.
"Barka da wuni Dad".
"In ban wuni ba zaka ganni?".
Dagowa yayi ya kalli Dad din shi ko ba'ayi masa bayani ba ya san ranshi a bace yake.


"Allah ya huci zuciyar ka".


"Aziz bana son iskanci yanzu fisibilillahi haka kawai zaka dauki hannu ka mare diyar mutane!".
"Haba Alhj. Meyasa bazaka tambaye shi ba sai ka hau shi da fada, ehmm!".


"Hajiya wannan wane irin magani har sai an tambaye shi. Ai tunda ki ka ga ya mare ta to a cikin hankalin sa yayi amma tunda kince haka kayi mana bayani meyasa ka mare ta?".


Sunkuyar da kan shi yayi kasa yana sosa kan shi kamar wanda yayi karya.


"Uhmm.. Amm. Dad.. Daman.... "


Nuna shi yayi.
"kin gani daman nagaya maki ba abunda zai ji haka kawai don jin dadi ya mare ta".


"A'a Dad laifi tayi min".


"Don tayi maka laifi sai ka daga hannu ka mare ta? Shekara na nawa da Mamar ka ka taba ganin ko a mafarki na daga hannu na da sunan in buge ta??".
Girgiza masa kai yayi.
"To meyasa baza kayi hakuri ba. kasan da cewa dukan mace ba kyau ko?".


"Ayi hakuri Dad ba z'a sake ba".


"Alhj. Ni na so ka bariyayi bayani meyasa ya mare ta don da na san ba karamin abu bane".
"Bisimillah zaki iya tambayar shi".


"Son ka gaya min meya faru?".




"Amm... Mom ina bacci tayi min kwalliya yanda kin ka san aljani kuma ta san da cewa abokaina sun zo ta kyale ni suka tayi min dariya abun ya bata min rai shiyasa na mare ta".




"Ka gani ko wannan wane irin iskanci ne?".


Fadan Dad din shi.
"Shikenan don tayi maka kwalliya sai ka mare ta kuma a gaban abokan ka? Wai meke damun ka ne baka san soyayya ba, yarinya ce fa dole sai kayi hakuri da ita".


Dagowa yayi ya kalle ta ya saka mata wata harara murguda masa baki tayi ta cigaba da wasa da hanunta.


"Amma dad....".


"Yi min shiru bana son jin shirmen ka. Maza ka dauki matar ka ku bani waje!".
"Allah ya baka hakuri insha Allah zan kiyaye".
"Nafisa ki tashi ki bishi kinji kiyi hakuri".


Mikewa tayi tsaye tayi masu sai anjima suka nufa gurin motar shi.
Dad ya biyo bayan shi.
Shiga yayi ya rufe mota ita kuwa tayi tsaye.
Har zai tada mota yaga bata shiga ba.
Horn yayi mata alaman ta shigo su wuce, amma tayi kamar bata ji sa ba.
Ganin Dad din shi yayi ya daure fuska ba don ranshi ya so ba ya fito daga motar bude mata kofa yayi.
Ita kuwa ta shiga tana jin dadi. Da karfi ya rufe mota sai da ta razana. Zagayo wa yayi ya tada mota fuuuu......








******




Muktar kuwa tunda ya shiga dakin sa babu abunda yake tunawa sai abunda Nafisa tayi ma Aziz shima haka za'aye mai?


Kawar da zancen yayi ya san suhaila bazata yi yarinta irin ta Nafisa ba.
Ko ya za'ayi auren a ranshi ya nasa ba zai yi ma Suhaila yanda Aziz keyi ma Nafisa ba.




***
Tunda suka fara hanya ba wanda yace ma wani kala sai wasa take yi da Hannunta.
Shikuwa ranshi a bace don ta rame shi ta saka shi cikin kunya kuma tazo ta kawo karan shi??





~lipton girl~๐Ÿ’™

1
2
3

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login