Showing 21001 words to 24000 words out of 33406 words

Chapter 8 - ABU NAKA Book 3 end Writing by SODANGI.txt

02 Dec 2024

2170

“To a qara yi maka addu’a baka faxi damuwar da ta same kan ba don mu san irin wacce zamu qara akan wacce dama muke yi”.
Bai vata lokaci ba ya yi mata cikakken bayani.
“Ba za ka haihu ba Mus’abu?”
Abu ta yi tambayar. Nan take kuma ta soma kuka, wani irin kuka mai tsanani tamkar wacce aka yiwa wani abu mai tsanani.
Kanshi a sunkuye qafafuwanshi a harxe yanda dama yake zaune tun farko bai motsa ba. A haka yake jin kukan da Abu ke yi, yake kuma sauraron kalaman da Innarshi ke furtawa.
“Abin da na gudarwa Saddiqa kenan, ga shi kuma shine ya sameta”.
“A’a Gwaggo, A’a, Gwaggo kar ki shiga wannan maganar don ni na warke”.
Abu ta daka mata tsawa ta ce, “Ke tafi can shashasha, wani warkewa za ki yi shi bai warke ba, ina ce shi yake sa miki? To ta ina za ki samu lafiya?”
“Gaskiya ni bana so, Abu bana so, ke ba za ki sasanta magana ta zama mai sauqi ba za ki qara lalatata?”
“Ke matsa can wawuya, wannan maganar taku ai dama a lalace take, a ina kika tava ganin zama ya yi dai-dai tsakanin mai lafiya da mara lafiya? Sokuwa kawai, wai ke ga mai son miji ko? Zai kuwa kai ki ya baro, rashin haihuwa wasa ne? An ce miki in kece ba za ki haihun ba zai yarda ne wata zai je ya kawo in ba ki yi haquri ba ki kasa zama, shi kam ai shi ya jawa kanshi, tun yaushe ne ake baqin cikin wannan shaye-shaye da Mus’abu ke yi? Tun bai isa komai ba”.
Ta bar maganar ta kama kuka sosai.
Cikin nutsuwa Gwaggo ta ce, “In kun gama hutun sai ka tafi ka barta a gida”.
Saddiqa ta yi maza ta ce, “A’a, Gwaggo zan bishi ba yaji na yi ba, ba kuma qarar mijina na kawo muku ba, baqonta muka zo yanda muka zo tare kuma haka zamu tafi tare, ina sonshi”. Ta soma kuka.
Mus’ab ya buxe baki an hankali ya ce mata, “Inna ni zan fita”.
Ta ce mishi, “To”.
Abu ta miqe ta bi bayanshi suka tafi suka bar Saddiqa tana ta faman kuka.
A hankali cikin yanayin rarrashi ta ce mata, “Da kin yarda kin zauna a gida har kafin a ga yanda lamarin zai kasance”.
Ta ce, “A’a, zan bishi, zan je in zauna da shi, bai yi min komai ba, ban ga kuma abin da sauran surukaye suke wa matansu ba wanda shi bai yi min ba. Da nice nake cikin yanayin da na ga Kubrah jiya da kin ce an qwace mishi ni, in muka tafi kuma ni ba zan ma sake…..”
Gwaggo Habiba ta katseta ta hanyar tambayarta, “Kina cikin hankalinki kuwa Saddiqa ko wani abu ne ya same ki?”
“Ki yi haquri Gwaggo ba abin da ya same ni, bana jin daxi ne kawai na yanda ake tafiyar da al’amarin Yaya Mus’ab a gidan nan, sai yaushe za a fara tausayin shi? Duk wani wanda zai yi baqin cikin al’amarin ai tayashi yake yi ba finshi ya yi ba”.
Ta soma ba ta labarin halin da Mus’ab ya shigo lokacin da likita ya ba shi labarin abin da yake ciki, da yanda aka yi ta shawo kanshi har ya samu nutsuwar da yake tare da ita. Har ta gama Gwaggo ba ta sake ce mata komai ba, iyaka dai zuciyarta ta kai matuqar da ba za a iya kwatantawa ba.
“To sai kuma mu zo gabanku Gwaggo shi da kanshi ne ya faxi al’amarinshi sai a turashi a gaba da maganganu masu zafi, Abu tana yi ku kuna yi? Kenan babu mai tausayinshi?”
Gwaggo ta fita ta bar mata xakin ta nufi kicin ta kama aikin abincinta, ita ma Saddiqa ta yi shiri ta fita ta bar gidan.
Mus’ab yana zaune kan tabarma xakin Abu yana cin gasasshiyar masara suna hirarsu lokacin da Saddiqa ta yi sallama ta shiga gidan.
Abu ta yi mata sannu da zuwa kamar ba yanzun nan suka rabu ba.
“Me za ki ci a kawo miki?”
Ta ce, “Masara”.
Ta ce, “Ai kuwa iyakarta kenan, sai dai mijinki ya sn miki. Kai ka san mata masarar ka raba biyu ka ba ta rabi”.
Mus’ab ya kalli Abu ya ce, “To ke ki yi shiru mana ki barta ta yi maganar da bakinta”.
Saddiqa ta yi shiru ba ta yi magana ba. Abu ta lura basa magana da juna da ita kaxai suke yi. Ta yi dariya ta ce, “Au ni fushi da juna kuke yi ne?”
Mus’ab ya ce, “Take yi dai, ni ina fushi ne?”
Saddiqa ta yi maza ta ce, “Waye ma ya fika? Ba ga shi don ka yi fushi wai kana so nima ka bani haushi ba ka je ka aske qasumbarka? To na rantse kanka za ka qarawa haushi, don ba zan sake yin magana da kai ba sai randa ta koma daidai yanda take kafin ka asketa”.
Abu ta qyalqyale da dariya ta ce, “Ai kuwa dai taka ta sameka, kai kuwa me yasa ka yi wannan aski tunda ka san ba a so?”
Ya yi tsaki ya ce, “Abin haushi ne da ita Abu, daga zuwanmu garin nan har ta fara sava alqawuran da ta yi min”. Ya kwashe bayani tas ya yi mata.
Abu ta ce, “Eh to, ba ta kyauta ba, amma kai ma fitana ne da kai, don haka an yi dai-dai dukanku kun yiwa juna shi kenan magana ta qare sai ku sasanta a shirya kawai a kori gaba”.
Ya kalli Saddiqa ya ce, “To kin ji Aisha, Abu ta ce mu shirya”. Ta yi kamar ba ta ji shi ba.
Kwanansu uku da zuwa Misau kullum a gidan Gwaggo Habiba Saddiqa take kwana, tun da ta je gidan Abun ma sau xaya ba ta sake fita ba, kowane lokaci tana manne da Gwaggonta, in tana kicin suna tare, in ma xakin ne haka, ko sallah za suyi ga sallayarta ga tata.
Zuciyar Gwaggo ta yi matuqar jin daxi ganin yanda Saddiqa take matuqar son mijinta, take xai-xai da shi a duk lokacin da ya shigo gidan. Sai dai abin da ya dameta guda xaya ne, maganar da Mus’ab da bakinshi ya gaya musu cewar likita ya tabbatar mishi da cewar da wuya qwarai ya haihu.
To haka za su zauna shi da Saddiqa ba za su haihu ba? Tana yiwa kanta tambayar take yin maza ta kawar da ita ta hanyar mayar da al’amuran gaba xaya ga Ubangiji, don tsananin abin ya wuce duk wani kwatance.
Ranar asabar da yamma bayan sallar la’asar Mus’ab ya shigo falon Innarshi suna tare ita da Saddiqa, cikin nutsuwa ya ce mata, “Inna sanda zamu zo garin nan Aisha ta yi min alqawarin da da muka zo ta qi cikawa”.
Cikin kulawa Gwaggo Habiba ta tambaye shi, “Wanne irin alqawari ne wannan?”
A hankali ya ce mata, “Na gaya mata in mun zo zamu sauka a can gidana ne, daga can ne za ta rinqa zuwa duk inda za ta, amma in dare ya yi za ta koma can ta kwana ta ce to”.
Saddiqa ta yi maza ta ce, “Ba haka bane”.
Gwaggo Habiba ta yi maza ta kalle ta, “Za ki qaryata mijinki ne a gabana?”
Ta yi maza ta yi shiru saboda ganin yanda Gwaggon ta xaure mata fuska.
“Bana son iya shege”.
Ta juya wurin Mus’ab ta ce, “In ka tashi tafiya ka kirata ku tafi, in kuma yanzu kake son tafiyar ma sai ku je”.
Hankalinshi a kwance ya ce, “Na fi so mu tafi yanzu saboda su Bilkisu sun yi min waya wai mazansu za su zo gaisheni na ce to a sameni a gidana”.
Da sauri Gwaggo Habiba ta ce mishi, “Qwarai kuwa su sameka a gidanka, ke Saddiqa xebo mishi girkin da nake yi ki riqe mishi”.
Ta yi maza ta ce, “To Gwaggo”. Ta je ta dawo tana cewa, “To amma Gwaggo ai mun ce zamu Bauchi gobe da sassafe”.
Gwaggo Habiba ta ce, “Eh, in hali ya yi na ki fito da sassafen sai ki fito, in kuma bai yi ba sai ki haqura sanda mijinki ya samu zarafi sai yasa a kaimu”. Ta ce, “To”.
A mota suna tafiya Saddiqa tana gaya mishi kar ka ga ka haxani da Gwaggona ta tilastani binka ka yi zaton ko in munje wani abin arziki zamu qulla ba kulaka zan yi ba”.
Ya ce, “Babu komai Aisha in dai zan samu in tava jikinki ai magana ta qare”.
Washe gari da safe Saddiqa da kanta ta yiwa Gwaggonta waya, “Gwaggo ku yi haquri ba zan samu fitowa daga gidan ba yau su Anti Hamida za su zo wuni. Na ce ko ita ma Kubrah za a yiwa mijinta magana don ta zo tunda ‘yan’uwa za su haxu”.
Gwaggo Habiba ta ce, “To, sai a gwada”.
Baqunta mai daxi su Saddiqa suka yi da kuma tafiye-tafiye masu yawa, har wurin su Ishak da sauran ‘yan’uwa da abokan arziki.
Sati huxu suka yi kafin suka yi shiri suka koma gida da xinbin tsarabar da suka yi ta rarrabawa maqwabta da abokan mu’amala na cikin gari.
Bayan dawowar su Saddiqa gida sun ci gaba da zamansu lafiya a sannu da fahimtar juna dake tsakaninsu.
Mus’ab ya fita hanyar duk wata masha’a, ya mai da hankali kan istigfari, neman gafarar abin da aka aikata a baya da qoqarin gyara na gaba.
A yanzu matsalarshi babba ita ce rashin lafiyarshi, zuciyarshi ta qi yarda ta ji daxin zaman da zai yi da Saddiqa, ita ba haihuwa shi babu, bayan kuma lalurar tashi ce shi ya jawowa kanshi ita.
In shi Gwaggo Habiba ta samu yaxuwar zuriyarta ta wurin wasu ‘ya’yan, to ita Innarshi fa, Saddiqa kaxai ta bari a duniya. Wannan shine abin da ya fi komai damun shi.
Auren nasu ya cika shekaru biyu, yau ma suna gaban likita, zuwa yanzu kuwa an yiwa Mus’ab canjin magani har sau biyu saboda wasu lalurorin nashi da aka sake ganowa.
Sauraron shigowar likitan suke yi don jin sakamakon sabbin gwaje-gwajen da aka yi musu.
Ta xaga ido ta kalle shi cikin sanyin jiki, a hankali ta buxe baki ta ce mishi, “Gabana sai faxuwa yake yi”.
Ya yi murmushi ya ce, “A kan me Aisha?”
Kafin ta ba shi amsa Dr. Usman ya turo qofa ya zo ya zauna a kan kujerar shi, gaba xaya suka mai da hankali wajen sauraron abin da zai gaya musu.
“Ina ganin mun xan samu ci gaba tunda ita Hajiya ba a sameta da wata matsala ba, don haka za ta rinqa shan magani ne kawai na hana haihuwa da qwayoyin cuta.
To kaima kuma mun gano inda asalin matsalarka take, kamar yanda na riga na tava gaya maka ne, ita wannan cutar ta kan yi riqar da take daskarewa har ta toshewa qwai hanyar shiga mahaifar mace, to abin da ya faru da kai kenan, shi yasa magungunan da muke ta amfani dasu basu wani yi aiki na a zo a gani ba”.
“To yanzu babu wani abin yi kenan?”
Ya yiwa likita tambayar. Ya yin da Saddiqa ta yi kasake tana sauraro.
“Eh, akwai abin yi, shine tiyata a buxe wurin a kankare ita jijiyar a cire ciwon daga cikinta, sai kuma ka ci gaba da shan magani zuwa wani lokaci da zamu ga abin da zai faru”.
Saddiqa ta yi shiru in ban da tunanin inda jijiyar take babu abin da take yi.
Sun dawo gida Saddiqa tana zaune tana kuka.
“Ni ban yarda da aiki ba, kaima ka san yinshi hatsari ne, shi yasa ma ka qi tambayar likitan hatsarin shi. Ai ba murxarka ciwon yake yi ba balle ko ka ce yana damun ka”.
Mus’ab ya kalle ta ya xan yi murmushin qarfin hali.
“Hatsari Aisha? Har ya wuce na ina zaune ana cewa in abin ya gagara sai a san yanda za ayi? Me ake nufi? Haka zan zauna duk sanda na je gida sai anyi min kalamai na barazana?”
Ta xan yi shiru kafin ta ce mishi, “Ba dai Gwaggo ce ta yi maka maganar ba Abu ce, ita kuma baka iya nuna mata ka ji haushi balle ta sani, ko ranar da aka yi hakan kuma a kaina fushinka ya qare, ka ce wai na ji daxin abin da ta faxa xin bayan ni ban tava tayar da maganar likita ba a gabansu kai ne”.
Ya yi shiru fuskarshi a xaure alamar ranshi ya sosu, ita ma ta ja bakinta ta yi shiru, dama ta ga abin zai yi nisa ta miqe ta nufi wurinta ta ci gaba da harkokinta.
In har Mus’ab yana da wata matsala a yanzu da ta addabe shi, ta takurawa zuciyarshi, to ba ta wuce matsalar rashin haihuwarshi ba, duk da bai tava ganin wata damuwa a wurin matarshi ba, to amma kuma ya yarda da maganar da Abu ke yawan gaya mishi cewar quruciya da kunya ke hanata nunawa, nan gaba in abin ya yi nisa ba za ta jure ba.
“Hajiya lafiyarta yanzu qalau, mahaifarta kuma a shirye take in aka sa mata qwai za ta xauka”.
Wannan shine kalamin da likita ya yi musu a zuwa asibitin da suka yi na qarshe. Ya waiwaya ya kalli Saddiqa dake ta faman sharar bacci a bayanshi, bacci ne mai nauyi da alama kuma bacci ne na gajiya.
Ya kawar da kanshi daga gareta, cikin wani tunanin wanda daga baya ya ga ba zai fissheshi ba. Ya miqe ya shiga banxaki ya yi wanka tare da alwala ya fito ya fara gabatar da nafilfili.
Washe gari da safe suna tare wurin karyawa, suna kuma hirarsu cikin nutsuwa. Ya sake shigo mata da maganar da ta riga ta ce mishi ba ta son ji.
“Aisha bai fa kamata a ce muna cikin matsala sai mu kawar da ita mu yiwa kanmu qaryar bamu da ita ba. Kin yarda da maganar aikin nan da kike yi sai in ga kamar nine baki damu dani ba”.
Ta yi maza ta xago ido ta kalle shi.
Ya ce, “Eh mana, yanzu ke ba za ki fata da sha’awar ki ganki xauke da cikina a jikinki ba?”
Da sauri ta ce, “Ina yi mana Yaya”.
Ya ce, “To in kina yo don me ba za ki qarfafa min zuciyata ba sai ki rinqa nuna ke baki da matsala, amma kuma kullum kina aiken a kawo miki jariri ki rena? Kullum fa sai kin tura an kawo miki xan da Zainab ta haifa”.
“Ba ina qin aikin bane hatsarinshi ya yi yawa, sai na ce to mu tuntuvi iyayenmu don mu ji abin da za su ce kai kuma ka qi”.
A hankali ya ce mata, “Ina tsoro ne kar su ce basu yarda ba, in suka yi haka kinga ba zan tafi babu izininsu ba, in kuma aka yi sa’a suka amince nan kuma hankulansu za su tashi suyi ta fargaba suna zullumin yaushe za a yi, in anyi kuma me zai faru? Shi yasa na fi so sai anyi sai mu gaya musu tunda lokacin babu sauran zullumi ko fargaba”.
Da irin waxannan kalaman Mus’ab ya rinjayi Saddiqa ta amince da maganar aikin nashi.
Nan da nan ya tasata a gaba suka koma gaban likita don ya sanya ranar da za a yi aikin, inda ya xibar musu kwanaki ashirin da xaya a dalilin akwai magungunan da ake buqatar Mus’ab xin ya yi amfani dasu kafin lokacin.
Duk da Saddiqa a kan ta amince ake yin shirin jikinta a sanyaye yake qwarai.
“Zo ki ji, kawo kunnenki nan ki ji abin da zan gaya miki”.
Ya soma yi mata maganar a kunnen nata cikin yanayin raxa. Ta xago ido cikin murmushi tana kallon shi saboda maganganunshi. Bai rama mata murmushin ba, maimakon haka magana ya soma yi mata cikin nutsuwa yana mai kallon idanuwanta.
“Sanda Innata take raye haka take yi min in na yi mata wani xan abin da ya faranta mata rai, sai ta jawoni kusa da ita ta raxa min wani abu mai daxi a kunnena. Zan tafi tiyatar nan Aisha zuciyata cike da fata da buri na ayi nasara in samu ki haifar min ko da ‘ya mace guda xaya ne da zan yi mata takwara da ita”.
Saddiqa ta qara matsawa kusa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login