Showing 15001 words to 18000 words out of 33406 words
Chapter 6 - ABU NAKA Book 3 end Writing by SODANGI.txt
suka hau gadonta tare suka kwanta, shima kuma ya yi haquri ya kawar da kai daga gareta, don ya fi son shiryawarsu maimakon kara tsoratata. Sai da aka kira sallar asuba ya miqe zai yi alwala ya mai da wutar gidan.
Har wajen qarfe taran safiya ba ta sake ganin ya shigo wurinta ba, ba ta ga yana shirin tafiya aiki ba. Kalmomin Abu suka faxo mata, kullum ki gaishe shi, kullum ki yi mishi abinci mai daxi, kullum ki gyara mishi shimfixa.
Don haka ta miqe ta nufi wurin nashi da nufin zuwa ta gaishe shi. A hankali ta tura qofar xakinshi tare da yin sallama, saboda ganin ba ta ganshi a falon ba.
Ya amsa yana daga kwance a gadonshi, ta kai gwiwowinta qasa a yanayin girmamawa ta ce mishi, “Ina kwana Yaya?” Ya amsa “Lafiya lau Aisha, ya ya gidan ya kwana?”
Ta ce mishi, “Lafiya, me kake so ayi maka na abin karyawa?”
A hankali ya ce mata, “Huta kawai Aisha”.
Ta xan kalle shi ta ce, “Ba ka da lafiya ne?”
Ya zuba mata ido yana kallon ta tare da tambayar ta, “Me kika gani?”
Cikin nutsuwa ta ce, “Na ganka a kwance bayan yau xin akwai aiki, kuma na ce me kake so in yi maka ka ce in huta”.
Bai kawar da kanshi daga gare ta ba ya ce mata, “Bana cikin yanayin da zan ji daxin zuwa aikin yau, saboda na xan takura, in kuma abin da nake so za ki yi min ki zo kusa dani mana ki rage min damuwa ta”.
Ta xan yi shiru kanta a sunkuye, a hankali sai ya ce mata, “Sai na ji kamar Abu ta yi ta yi miki magana a kan kar ki yi wasa da auren ki, na xauka ni da ke zamu yiwa nasihohin da ta yi mana biyayya Aisha”.
Ba ta kalle shi ba balle ta yi mishi wata magana, sai dai hawayenta da suka soma zuba. Ya shure abin rufar nashi ya zo ya kama hannunta ya shigar da ita xakin.
“Zo muje ki gaya min abin da ke saki yawan kuka. Nisa da gida da kika yi? Kina son ganin Gwaggonki ko?”
Ta yi maza ta gyaxa kai nuna alamar, “Eh”.
Yasa hannu ya share mata hawayen.
“Ai na sani, na san kina ganin Gwaggonki nima kuma ba zan hanaki ko in qi kai ki wurinta ki ganta ba, illa iyaka dai kawai zan bari sai kin kwantar da hankalinki mun zauna lafiya tukunna, ko yau xin nan kika yarda muka fara zama lafiya, to ni kuma a shirye nake mu daidaita lokacin da zan kai ki ga Gwaggon naki”.
Da irin waxannan kalaman na dabara ne da yawan nuna na fiki daxewa a duniya Mus’ab ya samu ya shawo kanta cikin ruwan sanyi, ta yarda ta miqa mishi al’amarinta ya samu ya yi yanda yake so da ita, ta kuma jurewa hakan.
Wunin ran nan ko qofar gidanshi bai buxe ba sai da ya yi nufin tafiya sallar juma’a, ana idarwa kuma ya dawo gida. Haka washe gari asabar da kuma lahadi yana gida yana hutawarshi.
“To Yaya yaushe zamu je wajen Gwaggo?”
Sai ya yi maza ya soma lissafi.
“To bari ko kwana talatin da tafiya Abu ta yi don kar a ganmu yanzu ayi zaton ko babu lafiya”.
Ta ce mishi, “To”.
Kwanaki talatin xin suna cika ya xauke ta ya nufi qasar Italy in da ya je ya yi hutun aikinshi na kusan watanni biyu, tafiyarshi ta farko tun bayan dawowarshi daga can inda yaje ya sadu da aminai, abokai da kuma tsofaffin malamanshi da aminanshi.
A lokacin da suka dawo gida kuwa tunanin Saddiqa da tattalinta bai wuce na me za ta yi ko ya ya za ta yi ta kyautatawa mijinta ba.
Watanni biyar sun cika bayan kawo Saddiqa da Abu ta yi har lokacin bai ce ga ranar zuwa gida ba, tamkar ya mance alqawarin da ya yiwa Abu na ba zai bari ta rinqa jin marmarinshi ba ta ganshi ba.
Ita ma Saddiqa mafi yawancin lokaci ta kan tuna Gwaggon nata ne, ta ce kai Yaya yaushe ne za ka samu lokacin da zamu je gida ne? Ina fa marmarin ganin Gwaggona”.
Ya yi tsaki ya ce, “Ai ayyuka ne bari dai mu gani daga nan zuwa qarshen watan nan. In ta ce to. To sai kuma wani jiqon in ta sake tunawa. Daga shi har ita sun zama tamkar basu ba, ko Liman da Mus’ab xin ya tasata a gaba ya kaita gaishe shi mamakin ganinta ya yi, ya cewa, Mus’ab xin yi qoqari ka kai wa iyayenku ita su ganta don su sanya maka albarka. Ya ce, “To malam”.
Suna zaune a falonshi suna hira, sun gama karyawa Mus’ab ya kalle ta ya ce, “Ki gama aikinki da wuri ki shirya in anyi sallar magariba zamu je mu ga Dr. Usman”.
To kawai ta ce saboda ya yi maganar ya fi a qirga, yau xin dai ya zartar da hukuncin tafiyar ne kawai.
Da daddare Mus’ab da Saddiqa suna zaune gaban likita, Mus’ab ya gama yi mishi bayanin abin da ke tafe dasu. Gwaje-gwaje sosai ya yi musu, ya kuma umarcesu dasu kawo mishi wasu abubuwa na jikinsu.
Bayan sunyi hakan ne ya xibar musu kwanaki uku ya ce su dawo don su ji sakamakon gwajin nasu.
Sun dawo suna zaune gaban likitan wanda yake kallon takardun dake gabanshi cikin nazari kafin ya xan xago ya kalli Saddiqa ya ce mata, “Ko za ki xan jiramu a waje?”
Mus’ab ya harzuqa da jin maganar tashi ya ce, “Matata ce fa, me za ka gaya min da ba za a faxa a gabanta ba?”
Saddiqa ta miqe tsaye ta ce, “Babu komai Yay bari in je in jiraka a mota, in ka gama kawai sai ka sameni a can mu tafi”.
Ya bita da kallo har sai da ta fita ta ja musu qofar kafin ya dawo da kallon shi wurin likita.
“Me kake so ka gaya min likita wanda yasa ka korar min mata?”
Likita ya ya kalle shi cikin nutsuwa ya ce, “Ba korarta na yi ba, bana yi maka sha’awar tashin hankali ne da ita, na san a yanda ka renita ta zama haka ba za ka so komai tsakaninka da ita ba illa zaman lafiya da kwanciyar hankali”.
Gaban Mus’ab ya yi mummunan faxuwa, cikin sanyin jiki ya tambaye shi “Me ya faru likita?” Ya tsare shi da ido yana kallon shi tare da sauraron abin da zai gaya mishi.
“Barasa da sigari sun riga sun yiwa kayan cikinka lahani, haka nan ka daxe kana xauke da ciwon sanyi da ake samu wurin matan da basu tsaya wuri xaya ba, saboda baka kula ka xauki matakin da ya dace a kanta ba har ta yi maka illa, ka kuma san ita wannan cutar tana cikin cututtukan dake hana maza haihuwa, don tana toshe jijiyar dake fitar da qwai zuwa mahaifar mace.
To ga kuma wancan matsalar da na ce maka barasa da sigari sunyi maka, ban da wannan ita ma matarka mun same ta da ciwon, sai dai bai riga ya yi mata qarfi sosai ba, na kuma san zai yiwu a wurin ka ta samu”.
Mus’ab ya ji tamkar a sama yake saboda tashin hankali, gaba xaya kunnuwanshi suka daina jin komai in ban da kalaman da likita ya furta mishi sune kawai suke ta nanata kansu.
“Ka yi haquri Mus’ab kar ka xauki abin da tsanani sosai, akwai magungunan da zamu baka in ba suyi ba mu canza wasu, kai dai kar ka bari matarka ta san abin da kake ciki ba wani tabbas ne dasu ba. Kar ka kalli wannan xawainiyar da ka yi a kanta ka mai da ita matar zamani ta bijire maka ba komai bane, musamman ma da yake abin ya shafi haihuwa.
Don haka in ta matsa tana so ta san abin da ake ciki ni zan iya ba da result xin da zai nuna matsalar a wurinta yake, don dai ka samu zaman lafiya a gidanka. A nan asibiti kuma ba za ta samu mai gaya mata komai ba”.
Mus’ab ya miqe tsaye tare da faxin “Na gode likita”. Ya fita ba tare da ya saurari rakiyar da likitan yake yi mishi ba.
Saddiqa tana zaune a qasa gaban Mus’ab, kuka take yi. Ya buxe ido a hankali cikin nutsuwa ya ce mata, “Yanzu nan baki yarda da abin da na gaya miki ba cewar ni lafiyata qalau bani da wata damuwa ba”.
“Ya ya zan yi in yarda bayan ba haka na saba ganinka ba, ni idan na yi maka laifi ne baka son gaya min to ka yafe min”.
Ya miqe zaune a kan kujerar ya ce,”Haba Aisha, ni kuwa a rayuwata me za ki yi min ya vata min rai?”
“To mene ne? Tun daga ranar da muka je asibiti gaba xaya ka canza ka sauya, ka zama wani irin, in bani na yi maka laifi ba waye?”
“To bari mu yi sallah kin ji ana kira, jeki ki yi alwala ki yi taki sallar kafin in dawo daga masallaci”.
Bai jira amsarta ba ya miqe ya fita, bai dawo gidan ba ko da aka yi sallar ya yi zamanshi a waje yana hira tare da jama’ar unguwa.
Saddiqa tana kwance a xakinta saboda ta dena zuwa xakin Mus’ab, shi da kanshi ne kuma ya nuna mata bai son zuwan nata, don haka ta yi qoqari ta kame kanta.
Me ya samu Yaya Mus’ab? Ta yiwa kanta tambayar. Tsawon lokaci tana tunani wani abu ne ya same shi bai son gaya mata, ko kuwa dai haka kawai yake fito mata da waxannan halayen da ba ta tava sanin yana dasu ba.
Ta yankewa kanta shawarar zuwa ta same shi ko barci yake yi ta tashe shi in yaso su yita ta qare, ta gaji da kauce-kaucen da yake yi mata.
Ta jawo zaninta ta xaura kan rigar baccin dake jikinta ta nufi xakin nashi, tun daga falonshi ta soma shaqo warin sigari, gabanta ya faxi, kar dai Yaya Mus’ab ke shan sigari a wannan tsohon daren?
Ta kutsa ta shiga cikin xakin nashi ba tare da ta yi mishi sallama ba, yana zaune a bakin gadonshi da karan sigarinshi a hannu, gefe guda kuma kwalbar barasarshi ce ‘whisky’.
Saddiqa ta zube gabanshi cikin kuka mai tsanani, nan take ya sureta da sauri ya yi waje da ita ya nufi falonta ya shimfixeta a kan doguwar kujerarta.
“Ba na ce ki dena zuwa wurina ba ki gaya min ba?”
Ta ba tanka mishi ba kukanta kawai take yi, ba ta dena ba har ya bar wurin ta ya koma nashi, saboda zai yi shirin sallar asuba.
Kafin ya dawo har ta gama yin shirinta, yana shigowa ya kalle ta cikin nutsuwa ya tambaye ta, “Wannan jakar fa?”
Ba ta kalle shi ba ta ce mishi “Gida zan tafi”.
“Gida ina?”
Ya yi tambayar cikin wani irin yanayi.
Ta ce, “Misau”.
“Na yi miki wani abu ne?”
Ta ce, “A’a”.
“Ban miki komai ba amma kike so ki tafi ki barni, don kin ganni a cikin damuwa kina so ki qara min ita?”
Ba ta kalle shi ba ta ce, “Ai ban santa ba balle ka ce ita ce za ta koreni”.
“Ko baki santa ba ai kin san ina da ita”.
Ta yi maza ta ce, “Kai kaxai ta shafa bana kuma so in jita”.
Ta miqa hannu ta soma jan jakarta za ta fita ya yi maza ya kamo ta ya riqe.
“Kar ki tafi ki barni Aisha, in kin barni da wa kike so in zauna?”
Ta ce, “Da halayenka”.
Ya qi sakinta.
“Me na yi miki Aisha kike nema ki qara min damuwa bayan wacce nake ciki, ban son ganinki cikin tashin hankali ne yasa ban gaya miki ita ba, Aisha ba wai ina voye miki ita bane, ki yi haquri ban gaya miki ita bane saboda ni na jawo komai sai nake ganin ya kamata ne ni kaxai in yi ta damuwar ba in watsa ta zama damuwar kowa da kowa ba.
Duk da hakan kuma ban samu kwanciyar hankali ba saboda na riga na cuci kaina na kuma cuce ki ta hanyar sanya miki cutar da baki san hawa ba baki san sauka ba, ko Innata bana jin za ta yafe min abin da na yi mata, tunda dai ke ce ‘yarta guda xaya da ta bari a duniya”.
“Kai Yaya Mus’ab wacce irin magana kake yi haka?”
“Na cuci rayuwata Aisha, na cuci rayuwata, na cuci rayuwata”.
Saddiqa ta soma kuka sosai saboda kalaman nashi. A hankali cikin nutsuwa ta gama sauraron bayanin da yake yi mata.
“Shine dalilin da yasa ka koma shaye-shayenka ka sha barasa ka sha sigari? Wato duuk ma abin da zai faru ya faru? Wacce irin rayuwa ce wannan? Yanzu ko abinci me daxi ne aka ce ya cutar da lafiyarka ba za ka fita hanyarshi ba balle savo?
Ka yi savo an jarrabeka sai kuma ka ce to tuban da ka yi ma ka fasa? Wataqila har neman matan ma ka koma”.
Ya yi maza ya ce, “A’a, Aisha ai ba zan yi miki qarya ba, ban tava kowa ba, ai kema na haqura dake balle wasu can qazamai. Ki ji tausayina kar ki tafi ki barni ki yi min alqawari kuma za ki taimakeni ki rufa min asiri a kan abin da nake ciki, ki yafe min ciwon da na sanya miki”.
Ba ta kalle shi ba ta ce mishi, “Ni ba kai ka sanya min ciwo ba rayuwata ta san qaddara tana kuma shirye da karvar ta a kowanne lokaci, kuma cikin godiyar Ubangiji”.
Tausayin Mus’ab ya kama ta, ta saki jaka ta shiga kicin don shirya mishi abin karyawa. Sai lokacin ne ta lura da irin ramar da ya yi, lokacin ne kuma ta tuna rabon da ta ganshi ya zauna yana karyawa ko yiwa kanshi wani abin da ya dace.
“Kin barni ina ci ni kaxai ko baki huce bane?”
A hankali ta ce mishi, “Ni bana fushi da kai, ina dai Azumi ne kawai, anjima dai ina so mu koma wurin likitan”.
Da sauri ya kalle ta ya ce, “Me zai mana Aisha? Ya ce ba zan haihuwa ba”.
Ta ce, “To sai kuma a zauna da cuta? Haihuwa ma ai ba shine mai ba da ita ba, ba kuma a wurinshi muke neman ta ba. Ciwon da ya ce muna da shi shine zamu koma wurin shi ya bamu magani”.
Ya ce mata, “To Aisha”.
Mus’ab da Saddiqa suna zaune gaban likita.
“Ta san komai likita na riga na yi mata bayani na gaskiya, yanzu abin yi kawai za ka gaya mana”.
Likita ya gyara zama ya ce, “To magani ne za a baku kai da ita ka san na gaya maka cewar ita cutar cuta ce mai wuyar war…….”
Saddiqa ta katse shi da cewa, “Likita bamu magani kar ka yi bayani, ai ka riga ka yi mishi ya ji ya kuma yarda”.
Ya kalle ta ya ce, “Haka ne, to babu damuwa”.
Ya miqe yaje ya haxo magungunan ya kawo ya shiga yi musu bayani.
“Wannan za ta rinqa sha ne da safe da daddare na tsawon watanni huxu, kar ta yi fashi. Wannan kuma na cusawa ne za ta rinqa sanya shi a gabanta sati-sati har na tsawon sati shida. In ta gama sai ta dawo mu sake yin wani gwajin don mu san halin da take ciki”.
Ya ce, “To”. Ya kwashe su ya miqawa Saddiqa ta zuba a jakarta. Ya sake juyawa wurin likita yana jin bayaninshi.
“Za ka sha magani da safe da daddare tsawon shekara guda kafin mu sake yi maka gwaji don mu ga yanda qarfin ciwon yake”.
Ya ce, “To”.
“Ga wannan na wata guda ne, a haka za ka rinqa karvarshi wata-wata don ba zai yiwu cewa ka je ka ajiye a gida ba”.
Ya sake cewa, “To”.
Ya sake kwashe su ya sake miqa mata, ita ma ta sake xiba ta sake zubawa a jakarta, suka dawo gida.
Saddiqa tana kwance jikin Mus’ab cikin yanayin kwalliyar da ya fi son ganinta a ciki, ga qamshinta a tare da ita.
“Ban qi