Showing 9001 words to 12000 words out of 33406 words
Chapter 4 - ABU NAKA Book 3 end Writing by SODANGI.txt
ji tana bacci sai ya ji ta amsa, zuciyarshi ta yi mishi daxi jin ita ma ba ta yi bacci ba.
“So nake na sha sigari”.
Da sauri ta miqe ta zauna a firgice qwarai ta tambaye shi.
“Sigari fa ka ce?”
“Eh, na kasa bacci ne, bana zaton zan iya bacci in ba shi na sha ba”.
“To bari in je xakina kawai”.
“Kina nufin saboda zan sha sigari sai ki nunawa Abu abin da muke ciki ba za ki rufa min asiri a gabanta ba, in ta san mun zauna lafiya ai daxi za ta ji, kin sani sarai saboda ke ta dawo garin nan”.
“Saboda ni?”
Ya ce, “Eh mana, saboda ke”.
Ya faxi hakan daidai lokacin da ya miqa hannu ya xauko ta daga inda take ya kifata a kan qirjinshi, ya kuma zagayeta da hannayenshi duka biyu ta yanda ba za ta zame ta sauka ba.
“Haka Inna take yi miki sanda kike damunta da rikicinki Aisha”.
Tsawon lokaci yana yi mata kalamai masu daxi kafin ya soma tsotson bakinta cikin nutsuwa, babu alamar za ta bijire mishi kan abin da yake yin.
Suna cikin wannan halin suka jiwo kiran sallar asuba daga masallacinsu, don haka suka tashi suka yi shirin yin sallah. Suna idarwa Mus’ab ya shiga xakinshi ya kwanta don ya samu ya xan yi bacci kafin ya fita ofis.
Ita kam Saddiqa kicin ta nufa ta kama aikinta, kafin qarfe takwas tuni har ta gama aikinta ta shirya komai ta yi wanka ta yi kwalliyar ta, ta nufi wurin Mus’ab cikin qamshinta mai daxi don tashin sa daga baccin da yake yi.
Saddiqa da Abu suna falonta suna hira bayan sun gama karyawa, Mus’ab ya shigo yana qamshi, ofis zai fita, bai zauna ba ya ce, “Abu bari in je ofis in dawo sai mu gaisa sosai na riga na makara”.
Ta ce, “To, a dawo lafiya, Ubangiji ya kiyaye”.
Ya ce, “Amin”.
Saddiqa ta vata rai ta ce, “Ba ka karya ba za ka fita?”
“Na makara ne fa”.
Ta xaure fuska sosai ta ce, “Ko kuma kana da wani wurin karyawar ba?”
Ya yi murmushi. Abu kuwa ta galla mata harara tare da jan tsaki. A hankali ya ce, “Ban kunun gyaxar kofi xaya”.
Ta zuba ta miqa mishi ya karva ya shanye, ya yi musu sallama ya tafi.
Mus’ab ya isa ofis ko zama bai yi ba qawayen Jennifer suka tare shi da labarin rashin lafiyar ta da kwanciyar ta a asibiti, sai dai wai ta qi faxin wanda ya yi mata abin. Ya nuna musu jimaminshi kan abin da ya faru, ya kuma ce musu zai dubo ta da zarar ya rage ayukan dake gabanshi.
Suna barin ofis xin ya koma kan ayukanshi, har zuwa lokacin da Sarah ta iso.
Tana zaune a gabanshi ta fiddo kwalin sigarinta daga jakarta ta kunna ta miqa mishi, ya ce, “A’a, Sarah sha kawai”.
Ta zuba mishi ido fuskarta a yatsine.
“Ba ka da lafiya ne?”
Ya ce, “A’a, lafiyata qalau ina dai son rage yawan abin da nake sha ne, matata ba ta son warin taba, kinga yau ma tun a wurin wanka da na sha biyu sai xazu da na sake sha, ina ganin kuma ba zan sake sha ba sai na kusa tashi daga ofis kafin in je gida”.
Ta kalle shi ta tave baki ta ce, “Yana da kyau”.
Tasa hannu cikin jakarta ta zaro wani kati ta miqa mishi ya karva ya duba cikin nazari, kafin ya xago kanshi ya kalle tana murmushi.
“Barthday xin Diana ne ai ka santa, ban yi inviting xin kowa ba in ban da kai, ina fata ba za ka yi min irin na jiya ba na yi ta zaman jiranka baka zo ba”.
A hankali ya ajiye katin hefen tebur xin dake gabanshi ya haxa hannayenshi wuri xaya ya zuba mata ido cikin nutsuwa, ya ce mata, “Ki yi haquri Sarah, gaskiya idan na sake yi miki alqawari ban cika ba ranki zai fi haka vaci, kin san matata yarinya ce qarama ba zai yiwu in rinqa raba dare a waje ba ina barinta ita a gida”.
Ta zuba mishi ido tana kallonshi tare da qoqarin voye vacin ranta.
“Amma kai ne ka ce min don ka yi aure ba wai yana nufin mun rabu bane”.
Ya ce, “Eh, amma ba ina nufin zan ci gaba da irin waxannan abubuwan bane, amma ai ba zamu daina gaisawa ba”.
Ta miqe tsaye ta suri jakarta ta ce, “To sai anjima mijin jinjira”.
Ta fita ta barshi yana kallon qofar da ta buga mishi, tsawon lokaci yana kallon qofar kafin ya miqa hannu ya xauki kan wayar dake gabanshi. Gidanshi ya kira, ya jiwo muryar Saddiqa tana amsa sallamar da ya yi.
A hankali ya kira sunanta.
“Aisha baki ga kamar in dawo gida in same ki yanzu zai fiye mana komai daidaituwa ba?”
Ta gane abin da yake nufi, cikin nutsuwa ta ce mishi, “Eh, to amma sai ka yi min rantsuwar tun zuwan ka ofis yau baka tava wata mace da hannunka ba?”
Ya mai da kan wayar ya ajiye a mazauninta, cikin ranshi yana tunanin irin karvar da ya yiwa Sarah lokacin da ta zo.
Wayar ta yi qara yasa hannu ya xauka cikin mamakin yanda nan da nan daga ajiyewarshi ta bugo.
“Ya ya dai Aisha, in zo xin ne?”
“Ai baka amsa min ba, abin da kake son ci za ka gaya min in shirya maka”.
“Komai kika yi zan ci amma gani nan ma zuwa gidan mu yi maganar gani ga ki. Kin canza shimfixar xakin nan?”
Ta yi kamar ba za ta amsa ba, a hankali ta ce mishi, “Eh”.
“To ki yi min kwalliya irin wacce za ta sani in xan ji sanyi”.
Ta ce, “To sai ka zo”.
Mus’ab yana zaune a gida da daddare suna hira bayan sun gama cin abincin da Saddiqa ta yi musu shi da Abu, ya yin da ita kuma take ta kaiwa da kawowa tsakanin wurinta da kicin, bayan ta sha kwalliya sai sheqi take yi.
“Ni me Saddiqa ke yi ne ta dame mu da zarya?”
Mus’ab ya yi murmushi ya ce, “Abu kenan, gidanta ne fa ki ce kar ta yi zarya?”
Sai da ta gama kawo musu tsiren da ta yi musu na naman rago suka xan yi hira, sai ta miqe ta ce, “Ni zani in kwanta Abu sai da safe”.
Abu ta bita da kallo ta ce, “Ki ce kawai kin gaji da zaman mijinki a nan kina so ku tafi, to ku je sai da safe, tashi ka bita”.
“A’a, Abu ba abin da take nufi ba kenan, baki ga sammakon da ta yi ta toya miki waina da funkaso ba kina ta santinshi”.
Ta gyaxa kai ta ce, “Na gani, gobe ma kuma shi nake so in sake ci”.
Ya ce, “A to, in ba ta kwanta da wuri ba ai sai ta kasa tashi”.
Ta ce, “Haka ne, to ku je sai da safe”.
Kayan baccin da ta samu a kan gadon ta xauka ta sanya saboda tana so ta xan yi mishi abin da zai ji daxi ko da babu yawa.
Ba ta daxe da kwanciyar ba ya shigo, wutar xakin ya kunna hasken ya bayyana, ta yi maza ta ja abin rufa ta rufe jikinta, zuciyarshi ta yi mishi daxi saboda ganin ta bi umarnin da ya yi mata.
Ya canza wutar zuwa mara haske kafin ya isa gadon. Ta yi maza ta kawar da fuskarta gefe saboda ganin yanayin da ya zo gadon a ciki. Ya miqa hannu a hankali ya juyo da ita gareshi.
“Daina juyawa mijinki baya Aisha babu kyau, dakata ki gani, tsaya ki ji abin da zan gaya miki”.
Hankalinta a tashe saboda gane abin da yake son yi da ta yi.
“Ni mu bari sai Abu ta tafi”.
Ta faxi hakan cikin murya mai rawa.
“Ai babu ruwanmu da Abu, Aisha muna wurinmu ne tana nata, ba ta zo gidanmu don ta takura mana ba, ta zo ne don ta tabbatar da zaman lafiyarmu, in ta kama zamu iya zama da ita gida xaya muna sha’aninmu tana nata. Saurareni kawai ki ji”.
Ta kama kuka tana faxin, “Ba ta so”. Sai dai hakan bai sa ya saurara ko ya haqura da abin da yake nufin ba.
Kar dai na wahalar da ita? Ya faxi saboda ganin yanda jikinta ke vari.
“Aisha”.
Ba ta yi magana ba, ba ta kuma bar kukan da take yi ba.
Miqewa ya yi ya shiga banxaki ya zuba ruwan zafi ya zo ya xauke ta ya je ya tsoma a ciki, ya yi mata abin da yake ganin ya dace ya yi mata, sannan ya yi mata wankan sabulu, ya kuma ba ta umarnin ta yi wankan ibada, ya fito ya canza musu shimfixar gadon.
A hankali ta hau kai ta kwanta saboda tsabtace shi da ya yi, a haka suka kwana da Saddiqa, in ban da ajiyar zuciya babu abin da take yi. Ba ta samu rintsawa ba sai bayan da suka yi sallar asuba.
Ganin haka yasa shi gyara mata rufa ya fito ya shiga kicin xinta wai zai toyawa Abu wainar da ta ce yau ma in so samu ne ita za ta ci.
Ba a je ko ina da fara tuyan nashi ba ya kama tari babu qaqqautawa, ita ma Abu ta fito daga wurinta tana faxin “Kai wannan tuya yau dai kam ya yi gardama, ya ya aka yi? Ta jiya ai qamshinta kake ji gwanin daxi ba irin wannan qaurin ba”.
Suna haxa ido da Mus’ab ta ja ta tsaya ta yi turus.
“Au! Haba, yau kai ne mai tuyan ina matar gidan?”
Ya kalle ta ya ce, “Na karveta ne ta xan huta, ko za ki taimakeni ne kema ki karveni?”
Ta ce, “A’a, a na me tunda ka karve ta ai ka iya ne, gara kawai ka qarasa”.
Ta juya tana cewa, “In ban da saunanci mene ne haka? Mace tana can a kwance shememe miji yana kicin yana fama da aikin abinci, sai ya gama ya tasota ta zo ta ci ko?”
Mus’ab ya ce, “A’a, Abu yau dai don Aisha nake yiwa shi yasa kika kira abin saunanci, amma ni kam tun yaushe nake karvarki girgi kina zaune in yi tankaxe, in yi talge, in kaxa miya a gidanki, ai na yi shi ya fi sau nawa?”
Ta ce, “To ai shi kenan ka tsayar da wannan qaurin da yake yi don hayaqinshi yana sirqeni ya sani tari”.
Shi da kanshi ya san qaurin ba mai daxi bane irin na jiya, ga shi kuma duk sun qone, mafi yawancinsu ma sun gutsittsire basu da wani sha’awa, ya kuma san Abu da halinta babu yanda za a yi ta ci abincin da bai mata kyau a ido ba, ko xanxano a baki, don haka ne ya yiwa kanshi qiyamun lailai ya tattara ya ajiye tuyar ya shiga shirya musu wani abin karyawar na daban. Nan da nan ya gama.
Yana tsabtace wurin sai ga Abun ta sake dawowa.
“Ni in ce ko dai ba kukan yarinyar nan na ji jiya da daddare ba?”
Bai kalleta ba ya tambaye ta, “Wacce yarinyar?”
Ta ce, “Saddiqa”.
Idonshi yana kan aikinshi ya ce mata, “Ita ce Abu”.
Ta xan yi shiru kamar ba za ta yi magana ba, sai kuma ta sake tambayar shi, “In ce ko dai lafiya?”
Ya ce, “Lafiya qalau, mafarki ta yi wai damatsirin gidanki sun cijeta”.
Shaqiyancin da ta ji ya shigar cikin maganar ya sata wucewa ta tafi ta ba shi wuri tare da faxin “To madallah”.
Ya gama shiryawa Abu abin karyawar da ya shirya matan a gabanta, ta zuba mishi ido tana kallo, ya xaga ya kalle ta saboda shirun da ya ji ta yi.
Kallon da take yiwa abin karyawar yasa shi murmushi.
“To baki yi min addu’a irin wacce na ji kina yiwa Saddiqa ba jiya da ta kawo miki abin karyawa ba”.
Fuskarta a xaure ta ce mishi, “Addu’ar me zan yi maka bayan ka hana yarinya ta zo ta yi min abin da zan iya ci, wannan duk ai ba abincina bane”.
“Ba hanata na yi ba Abu”.
“To me ka yi?”
Ya xan yi shiru kafin ya ce, “Jiya ne ranar aikinta yau kuma nawa”.
Ta yi tsaki ta ce, “Ai sai ka yi ta yi, jeka ni ka xumami miyar wainar da na ga yarinyar nan tana shiryawa da daddare ka xebo ka haxo min da wainar da ka toya in tsinci wacce zan iya tsomawa cikin miyar in ci ko don sha’awarta”.
Ya ce, “To Abu yanzu kuwa”.
Yana gama kawo mata abin da take so ya yi maza ya nufi wurinshi, bai saurari maganar da take yi na “To ya ya za ku watse ku barni ni kaxai in karya?”
Yana tura qofar xakin ya ga ta buxe ido, a hankali ya matsa kusa da ita.
“Sannu Aisha, bari in kira Dr. Usman ya zo ya xan taimaka miki don tun xazu na ji jikinki da xumi”.
Ta xan kalle shi na xan wani lokaci ta kawar da kai, ya yin da zuciyarta ke raya mata Yaya Mus’ab wane iri ne? Abin kunya ba ya ba shi kunya. Ya kira likita ya ce mishi me?
Sanin da ta yi matuqar tana wurin zai kira likitan ya sata miqewa cikin qarfin hali ta nufi wurinta, in ban da haka da ita kam yau ba ta yarda ta haxa ido da kowa ba.
Tana tafiya yana binta a baya.
“Aisha! Aisha tsaya mana ki saurare ni”.
Ba ta kula shi ba balle ta saurari wata magana.
Abu ta na zaune a falo tana jan carbinta bayan ta idar da sallar walaha, ta kammala addu’o’inta. Saddiqa ta wuceta ta shiga xakinta ta hau gado ta kwanta.
Da sauri Abu ta bi bayan ta.
“Lafiya dai ko Saddiqa? Ko baki ji daxi bane?”
Ta yi tambayar daidai ta xora hannu a kanta.
Ba ta yi magana ba ta soma kuka.
“A’a, mene ne na kuka kuma Saddiqa? In ba a da lafiya saia yi kuka?”
Tana maganar tana nazarinta. Nan da nan ta gano kan al’amarin.
“Uh-uhum! Mus’ab ne ya vata miki rai?”
Ta yi tambayar tare da zama a bakin gadon.
Saddiqa tana jin ta ambaci sunanshi ta kawar da kanta daga kallonta ta juya kallon bango tare da tsananta kukan da take yi.
“Yi haquri, yi haquri, yi haquri shatuwallena, yi haquri ‘yar Gwaggonta ba qwararki ya yi ba, bai kuma zalunce ki ba girma ne ya ja miki, in aka girma ai haquri ake yi, sai kuma a nutsu.
Shi kam ma ai ya yi haquri dake, yau kwananku nawa yana zuba miki ido, Mus’abu ai mai haquri ne. yi haquri kin ji. Ubangiji ya yi miki albarka, ya zaunar miki da aurenki lafiya, ya baki zuriya xayyiba su faranta miki rai kema kamaar yanda kika farantawa iyayenki. Bari ki gani in tashi yanzu zan yi miki maganin ciwon da jikinki ke yi”.
Ta tashi tana shirin abin da za ta yi Mus’ab ya shigo.
“Abu likita ya zo duba Aisha”.
Abu ta galla mishi harara.
“Kai kar ka damu mutane ka ji, duk wahalar da ka gana mata ba ta isheka ba sai ka kira wani likita ya sossoke mata jiki da allura, to babu inda za ta”.
Ta ja tsaki tana harkar gabanta tana mita.
“Shi yasa ko qwari baku da shi, to duk kashi a soke”.
Mus’ab ya yi kamar bai ji kunyar kalaman nata ba, don shi kam yana son sirrin mu’amala tsakaninshi da iyalinshi. Cikin qarfin hali ya ce, “Abu da kun bari an duba ta jikin nata babu lafiya”.
“Ai ba rashin lafiya take yi ba wahalar da ka ba ta ne ya xumama