Showing 3001 words to 6000 words out of 33406 words
Chapter 2 - ABU NAKA Book 3 end Writing by SODANGI.txt
ko wakili?”
Hargowa ta jawo hankalin sauran jama’a suma suka firfito, masu isowa ma kowa ya zo sai ya yi parking ya fito don ganin abin da ke faruwa, duk wanda ya iso sai ya buqaci sanin me ke faruwa? Tun ana bayani na gaskiya har aka koma qara gishiri a kai.
Mus’ab ya iso wurin don ya kasa fahimtar abin da ke faruwa, cincirindon jama’a yasa ko motar ba a gani daga nesa, da qyar ya kutsa kai ya smau ya isa wurin da abin ke faruwa.
Yallavai wanda tuni ya gundura da lamarin ya shiga fargaba saboda cincirindon mutanen dake kewaye da shi waxanda suka zamo mishi barazana, don ya san kes suke jira su afka mishi, don sun riga sun tunzura.
Yana ganin isowar Mus’ab ya yi maza ya ce, “Yauwa ga ma mijinta nan ya zo da kanshi”.
Gaba xaya wuri ya kaure da hayaniya, “Haxin baki ne da shi suka haxa baki”. Wasu har suna cewa, “Za ma ku sani, mu nan da kuke gani ba za a kawo mana wannan iya shegen ba”.
Yallavai ya yi maza ya ciro hoton dake aljihunshi zai nuna musu don ya samu ya wanke kanshi daga zargin da jama’a ke mishi.
Wani mara kunya a ciki ya yi maza ya fige hoton ya raba shi biyu ya jefa shi a baki ya tauna ya haxiye yana cewa, “Hoto kuma har wata shaida ce”.
Mus’ab ya yi shiru yana kallo cikin nazarin al’amarin, kafin ya zaro karan sigarinshi ya sanya a baki ya kunna yana zuqa a hankali yana kallon Saddiqa dake amsa tambayoyin mai mujallar.
“Kin san wannan da ya ce wai shi mijinki ne?”
Ta girgiza kai nuna alamar ba ta san shi ba, ta kuma qara da cewa, “A’a”.
“Za ki iya tunawa kin tava ganin shi ko da sau xaya ne a rayuwarki?”
Ta tave baki ta ce, “A’a”.
Mus’ab ya gama sauraron ta zuciyarshi cike da mamaki, bai ce mata komai ba sigarinshi kawai yake sha cikin nutsuwa. Ya miqa hannu ya jawo Saddiqa daga cikin motar ba tare da wani ya lura da lokacin da ya yi hakan ba, sai kawai ganinta aka yi a tsaye yana riqe da ita ya mayar da qofar motar ya rufe.
“Ba fa za ka je ko ina da yarinyar nan ba”.
In ji mai mujallah.
“Kai waye da za ka hanani yin hakan?”
Mus’ab ya buqaci sani. Yasa hannu a cikin aljihun gaban rigarshi ya zaro kati (conplimentry card) xinshi ya miqawa Mus’ab ya karva ya gani.
Lauya ne mai zaman kanshi, ya saki katin ya faxi a qasa sannan ya yi mishi lalataccen kallo tare da tambayarshi “To sai me?”
Kallon da tambayar suka tunzura shi ya ce, “Sai ka san ba za ka ko ina da ita ba tunda ko matarka ce sai ina tana son zama da kai, don haka ni zan tafi da ita in kaita gaban iyayenta, in kana sonta sai ka bita can ka same ta ku sasanta, amma baka tsare mu a jeji ka cireta a cikin mota ba bayan mun san mugaye sun yi yawa”.
“Kana da wata shaida ne Yallavai da za ta nuna ita xin iyalinka ce?”
Wani daga cikin fasinjojin ne ya yi tambayar.
Mus’ab ya kalle shi a nutse cikin kwanciyar hankali ya ce mishi, “Babu”.
“To tunda shi da kanshi ya ce babu shiga mota mu tafi kin ji, ya tsai damu yana vata mana lokaci”.
Mai mujallah ne yake wannan bayanin.
“Wasu mutanen basu da hankali, mace ba ta son su sai suje su baiwa iyayenta kuxi su aura musu ita a kan dole”.
Saddiqa ta yunqura za ta shiga motar Mus’ab yasa hannu ya kama hannunta ya riqe.
“Da kin sallame su sun tafi kar ki yi ta vata musu lokaci”.
Ya zuba mata ido yana kallon cikin idonta.
Ita kuma ta fara kuka tana faxin “Ka sake ni, ka sakar min hannuna ban sanka ba”.
Ta shiga kici-kici da qoqarin qwatar kanta daga gare shi.
“Malam in ma matarka ce ba ta sonka”.
Mai mujallah yasa baki, ya kuma yi nufin taimakon Saddiqa ta qwaci kanta wurin Mus’ab.
Mus’ab ya yi maza ya saki hannun Saddiqa dake hannunshi, cikin zafin nama ya taqarqare ya danqarawa mutumin naushi mai qarfi a muqamuqi, abin da ya yi sanadin faxawarshi kan mutanen dake tsaitsaye bayanshi suka tare shi daga kaiwa qasa. Ya taso fuskarshi cike da mamaki.
“Ni ka buga? Za ka yi dana sani, za ka gane ku…..”
Kafin ya qarasa faxin abin da yake so ya faxan Mus’ab ya yunqura ya sake kirva mishi wani wawan naushi. Wuri ya kaure da hargowa, jama’a suka kasu kashi biyu dake qoqarin shiga tsakanin daben dake shirin aukuwa tsakanin Mus’ab da mai mujallah saboda tasowar da ya yi zai rama dukan da ya yi mishin.
Haquri suke bayarwa a sasanta al’amarin cikin ruwan sanyi ba tare da anyi tashin hankali ba.
Mus’ab yana riqe da karan sigarinshi da yake qoqarin kunnawa yana kuma sauraron maganganun da kowa yake yi, ya yin da hankalinshi da nutsuwarshi suke kan duk wani yunquri na Saddiqa.
Wani dattijo ya iso wurin yana faxin, “Haba Yallavai ya ya kuna wuri kai da yaranka amma kuma rikici yake nema ya tashi a gabanku kana kallo?”
Yallavai ya yi mishi bayani kan yanda Mus’ab ya zo wurin ya nemi taimakon shi da duk abin da ya faru, don haka shi a ganin shi yanzu tunda abin ya zama haka, to sai a xunguma ayi can gaba inda za a samu hukumar ‘yan sanda a awurin.
Mus’ab ya ce, “Shi daga inda yake tsaye ba zai qara taku xaya zuwa gaba ba tunda ya riga ya ga abin da ya fito nema, sai dai ko a xunguma a koma gari na baya tunda shima ya wuto ofishin ‘yan sandan a can”.
“Dubi nan yaro”.
In ji dattijon. Mus’ab ya mai da kallon shi gare shi da girmamawa.
“Gaya min gaskiya ka ga tsayawa nan ta yi yawa, inda muka dosa nan ba nan kusa bane arewa fa zamu. Me ke tsakaninka da wannan yarinyar?”
Mus’ab ya kalle shi cikin girmamawa ya ce, “Baba qanwata ce, kakanninmu xaya, mahaifinta wan mahaifiyata ne a wurinshi na girma, shine kuma ya bani ita matata ce”.
“Kai ku tafi ku barshi da matarshi kowa ya shiga mota ya nufi inda za shi”.
In ji dattijon. Mutanen da tsayuwar ta riga ta gundiresu suka nufi motocinsu suna tsaki tare da faxin “MATA! Hum sai a barsu kawai”.
Mai mujallah kuwa tsayawa ya yi ya ce, “To ai ita yarinyar ba ta gaskata maganar ba balle mu yarda da gaskiyarshi”.
Dattijo ya kalli Saddiqa ya ce, “Yarinya ba ki yi kama da mutuniyar banza ba, abin da ya faxa gaskiya ne ko akwai gyara a ciki?”
Ta ce, “Gaskiya ne”.
Ya kalli mai mujallah ya ce, “To kai ka ji”.
Nan da nan jama’a suka watse aka bar Saddiqa da Mus’ab suna tsaye cirko-cirko, hatta Yallavai ya koma wurin sauran ‘yan sanda sun koma kan aikinsu.
Mus’ab ya kalli Saddiqa cikin murmushi ya ce, “To ya ya kenan? Waxanda kika sani sun tafi sun barki da wanda baki sani ba, ya ya kenan? Za mu tafi gida ne ko kuwa?”
Ta yi kamar ba ta ji ba, ta soma kuka. Ya kamo hannunta ya jata zuwa inda motarshi take, ya buxe ya sanya ta a cikin wurin mai zaman banza ya rufe, sannan ya juya ya koma nashi wurin ya shiga ya zauna.
Sai da ya kunna sigarinshi ya sanya a baki kafin ya juya kan motar ta nufi inda ya fito, bayan ya yi sallama da su yallavai.
Sun fara tafiya ko wani nisa basu yi ba Saddiqa ta soma kwara amai, nan take ya tuna kalaman Innarshi.
“Saddiqa da kake gani warin sigari ma sa ta amai yake yi balle a ce ta ji warin barasa a jikin mijinta”.
Ya yi maza ya wurgar da sigarin tare da sauke gilasan motar saboda samun tsarkakakkiyar iska.
“Ki yi haquri Aisha na mance bakya son hayaqin sigari”.
Ba ta yi magana ba in ban da kukan da take yi, duk da tsayuwar da ya yi don ta gyara jikinta ta kuma xan huta.
Mus’ab ya biyo Saddiqa xakinta da shigarsu gidan.
“Ina kika samu kuxin motar da kika biyasu?”
Ta yi shiru ta qi yin magana.
“Ni dai na san tun zuwanki wurina ban tava baki kwabo ba, da abokaina suka zo ganinki suka baki kuxi ma na karve, saboda dama ni zuciyata ba ta kwanta dake ba, na daxe ina ganin kamar za ki iya aikata abin da kika aikatan, shine kika gudu ashe ba kuskure na yi ba.
Wato ke kina nufin za ki iya yin dalilin da mahaifiyata za ta qara yin fushi dani? Kina nufin bayan duk abin da kika sani na tsakanina da ita za ki iya yin dalilin da zai fi haka rashin daxi?
In bakya sona ai ba zan tilasta ki zama dani ba, ni wani irin mutum ne da yake girmama abin da yake son shi. Ko da kika ga na bi hanyoyin da na bi wajen karvar auren ki na lura da quruciyar dake gareki ne, sai kuma na ga ni za a gwada min qarfi, amma in bakya sona ai zan iya yin haquri ba zan so kaina a kanki, zan mutunta al’amarinki in bi son zuciyarki tare da adalci a kai.
Amma ai babu wulaqanci ko tozartarwa a tsakanina dake, ki tashi daga nan ki je ki shiga cikin qartin maza ki nufi Misau ki je ki cewa iyayenmu me?”
Cikin matsanancin vacin rai yake jero kalaman nashi, don haka bai ko saurari kukan da take yi ba.
“Waye ya baki kuxin mota?”
Ta yi shiru.
“Ko shi wannan mutumin ne ya biya miki?”
Ta yi maza ta ce, “Eh”.
Ya zuba mata ido shi ba abin ya xauke ta da mari ba. Ya yi qarfin halin sake tambayar ta.
“A ina kika san shi?”
Ba tare da ta kalle shi ba ta ce, “Tare da shi muka zo daga Misau”.
“Ke da shi da Abu?”
Ta ce, “Eh”.
“Zancen banza kenan”.
Ya miqa hannu ya kamata, ya ce, “Ai duk inda mavoyar kuxin naki suke sai na gansu yau, tunda na ganeki”.
Ya soma cire kayan jikinta yana watsarwa, ita kuma tana kici-kicin hana shi da qoqarin rufe abin da take ganin shi ta fi qin ya gani. Ba tare da ya saurari kukan ta ba.
Lilita ya tarar xaure kan siket xin ta, ya zubawa likitar ido cikin sanyin jiki. Wannan ai lilitar Inna ce dake zuba cinikin kayan miyanta a ciki. Wato Inna ce ta baki kuxin da za ki gudu daga nan ki koma gida ke kaxai? Wai me na yi? Gaskiya ba zan bar maganar nan ba.
Ya miqa hannu ya ciro lilitar don ya cire kuxin dake ciki, har da qullin magani a xaure.
“TAFXIJAM! Har da magani ta baki ki rinqa saka min?”
Ya zuba mata ido yana kallon ta.
“To bari Kawu Gixe zan kai wa in yi mishi bayanin komai don ya ga irin abin da aka shirya min”.
Jin ya ce, “Zai kai wa Kawu Gixe maganar yasa Saddiqa buxe baki ta ce mishi, “Ba Gwaggona ta bani magani ba Abu ce ta bani”.
Ya ce, “A’a, babu ruwan Abu, ita za ta yarda a qwareni ne? Kuma in ma ita ta bakin na yarda ni gara min magani da a baki kuxin motar da za ki gudu ki bar gidana ba tare da izini ba, ko wannan xan fitan da kika yi kin san iyakacin mutanen da kika tayarwa da hankali? Ba gara a tara miki magunguna ba, za ki ba masu mota magani ne su xauke ki a motar haya?”
“Is any one at home?”
Wannan kalmar da Mus’ab ya jiwo ita ta katse shi, a lokaci guda kuma ta jefa shi cikin fargaba da faxuwar gaba mai tsanani saboda fahimtar muryar da ta yi maganar.
Jennifer ce, to me ya kawo ta? Ya fito falon da nufin fita waje inda take, sai kawai ya ganta cikin falon zaune kan kujera riqe da karan sigarinta a hannu tana zuqa, ga kuma kwalbar giyarta a gabanta.
Mamaki ya kama shi, ya ce, “Ya ya haka Jennifer? Ya ya za ki shigowa matata wuri ba tare da kin jira ta baki izinin yin hakan ba?”
Ta kalle shi a lalace kafin ta tambaye shi cewa, “Ina ne wurin nata?”
“Kar mu yi haka dake Jennifer, kashe sigarin muje can wurina sai in ji abin da ya kawo ki, mai nan xin ba ta son warin sigari”.
Ta yi dariya ta ce, “Ba zama da kai ta zo yi ba kenan, any way wannan ku ya shafa, ina fata ba kirana ka yi don ka gaya min abin da matarka take so da wanda ba ta so ba?”
“Ni na kiraki?”
Ya yi tambayar a yanayin dake bayyanar da rashin jin daxin shi, don bai son fitina da ita a lokacin.
“In baka kirani ba me zai kawo ni?”
Ta ja tsaki tare da tofar da yawu tuf! Nuna alamar tir bai isa ba. Hakan da ta yi ya qara fusata shi.
Ya ce, “To na ji na kira ki kin zo, na ji kuma bana son ganinki don haka tashi ki fita”.
Ta ce, “Ai kuma baka isa ba tunda ka kirani sai na huta, sai na shanye barasata”.
Ya yi maza ya ce, “Ba a nan ba”.
Ba ta saurare shi ba ta jawo ledar da kwalbar ke ciki za ta buxe.
“Ba a nan ba Jennifer, kar ki neme ni da magana”.
Ya yi maza ya nufo ta don ganin ba ta fasa ba, nufin shi ya hana ta yin abin da za ta yin ta hanyar fitar da ita daga falon, ta yi zumbur ta miqe, yana isowa gareta ta yi maza ta wanke mishi fuska da wani irin lafiyayyen mari mai qarfi tau!
Ya ja ya tsaya ya zuba mata ido yana kallon ta zuciyarshi cike da mamaki.
“Marina kika yi Jennifer?”
Ta ce, “An mara, kai da kake marin mutane fa?”
Ya ce, “Ai kuwa kin sayawa kanki wahala, don kuwa zan tabbatar da wannan hannun naki ya daxe baki more shi ba”.
Yana rufe baki ya cafke hannun da ta yi marin da shi, yana cafkewa ta soma kururuwa saboda wahala.
“Ka yi haquri Mus’ab”.
Ya ce, “Haba, ai gara kar ki ba da haquri Jennifer, ai kin daxe kina burin marina na kuma daxe ina yi miki kashedin hakan, don haka tunda baki ji ba nima bari in yi abin da na yi alqawari”.
“Na tuba Mus’ab”.
“A’a, ai gara kar ki tuba, in kika yi haka ai baki zama cikakkiyar ‘yar iska ba”.
Saddiqa ta gaji da leqen abin da ke faruwa ta koma gadonta ta hau ta zauna cikin rawar jiki da tsananin tsorata da abin da ke shirin faruwa da hannun Jennifer.
Ban da duk wani mugun halinshi da Gwaggo ta sani bai da tausayi ko na anini. Ta faxi hakan cikin zuciyarta.
A waje Mus’ab ya tari mai tasi ya jefa Jennifer a ciki ya miqawa mai tasin jakarta a hannunshi, ya ce, “Ku tafi ta gaya maka inda za ka kaita, in kun je ka xebi ladan aikin ka a ciki”.
Ya juya ya koma cikin gidanshi inda ya bar Saddiqa.
“Kukan me kike yi Aisha?”
Ya miqa hannu zai tava ta, ta yi maza ta maqure a jikin bango.
“Kar ka tava ni”.
Ta yi mishi kashedi.
“Bana son ganinka kusa dani tsoro kake bani, duk abin da Gwaggo ta gaya min game da kai haka abin yake, sa’a ma ka ci ba ta san rashin tausayinka ba da ta qara tsanarka.
Na sha jin tana cewa, halinka guda xaya da ta sani shine kai xin