Showing 1 words to 3000 words out of 33406 words

Chapter 1 - ABU NAKA Book 3 end Writing by SODANGI.txt

02 Dec 2024

2160


ABU NAKA…


3






















HAFSAT C. SODANGI
Haqqin Mallaka (m)
Naquin mallakar littafin na Hafsat C. Sudan ne (Mrs. Yunus Abdullahi Davai)








Shekarar Bugu:
2006




An sake Bugawa A:
2015







Alura
An xan yi gyara a cikinshi kaxan saboda wasu dalilai, sai dai yana nan a kan tsarinshi na farko.
Na gode.
11/8/2006

TA`ZIYYA
Ubangiji ya ji qan HAJIYA AISHATU BALARABE (JAZAN). Marubuciyar litattafan ABOKIN HIRA da rahamarsa. Ubangiji ya kyautata makwancinta, in tamu ta zo kuma yasa mu cika da imani.
Amin.








ABU NAKA…-3
A
garin Misau gidan Gwaggo Habiba ranar Laraba da hantsi, Abu tana zaune kan kujera ‘yar tsugune a tsakar gida, ya yin da Gwaggo Habiba take zaune gabanta kan tabarma tana kuma goga mata goronta bayan ta gama gyara mata farcenta da ta yanke mata.
“Ni kuwa Inna sai nake ganin kamar bakya jin daxi saboda rashin walwalarki ta yi yawa, tun bayan kai Saddiqa gidan mijinta da kika yi har yanzu baki dawo cikin sukuninki ba. Sannan a zaman yanke miki farcen nan da na yi sai na fahimci jikinki yana vari tamkar wani abu ya tsorataki”.
Abu ta kalli ‘yan yatsun nata da aka ce suna vari kafin ta yi maza ta xauke qafarta daga kusa da ita, ranta a vace ta soma magana cikin faxa.
“Kin ga fa shi yasa jiya da shekaran jiya duk ban zo gidan nan ba, saboda yawan tasani a gaba da kike yi kina tuhumata zuwan Malam kan wai ya ganni ko bani da lafiya ne jiya, shi yasa yau ya zo kuma tun ban gama hutuwa ba za ki fara. To jikina ba zai yi vari ba ni ba tsohuwa ba ce?”
Gwaggo Habiba ta yi murmushi ta ce, “Haba Inna yaushe kika yi tsufan da jiki zai rinqa rawa haka?”
Ta xan kawar da fuskarta gefe ta ci gaba da yin bayani a nutse.
“Ni dai a zuciyata na san akwai xayan biyu in ma dai kina voye min halin da kika baro Saddiqa da mijinta a ciki, ko kuma ke xin baki da lafiya baki yarda kin gaya min ba, amma ki yi haquri”.
Abu ta zovara baki ta ce, “A’a, mene ne na vacin rai kuma daga magana, ko don an mai dani kububuwa don faxa?”
Suka ci gaba da wata hirar. Zuwa can Gwaggo Habiba ta ce, “Ni dai Inna yawan mafarkin Saddiqa da nake yi yana damuna”.
Gaban Abu ya yanke ya faxi, mafarkinta na daren jiya ya faxo mata. A firgice qwarai ta tambaye ta kema kina mafarkin ne?
Gwaggo Habiba ta xaga ido ta kalli Abu cikin nazari da lura, a hankali ta buxa baki ta ce mata, “Dama kina mafarkinta ne Inna baki tava gaya min ba? Kema ashe hankalinki bai kwanta da yanayin da kika barotan a ciki ba”.
Ta soma kuka, kuka kuma mai tsanani.
Abu ta yi hanzarin abka mata da faxa don ta kawo qarshen kukan nata.
“Sai na daina zuwa gidanku tunda haka kuke ke da mijinki, kun tasa Mus’abu a gaba bakwa mishi fatan alheri kullum burinku…..”
Ba ta kai ga qarshe ba ta tsaya saboda jin maganar da Gwaggo Habiba ke faxa.
“Zan tafi can garin in gano halin da Saddiqa ke ciki, zan je in gani da kaina in bai yi min ba zan xauko ta. Saddiqa marainiya ce ba ta da kowa sai ni, nice uwarta nice kuma ubanta. Yaya Gixe ne ya cuce mu ni da ita, shine ya xauke ta ya baiwa mutumin da ya fi mu sanin ba zai riqeta ba, baqin ciki kawai zai cusa mata. To ba zan barshi ba, dama tunda na ga ina munanan mafarkai a kan ta na san…….”
Abu ta katse ta da cewa, “Babu wani mafarki kina dai son zuwa wurin xanki ne kawai, in kuma kika fito ma kika ce za ki je ganin Mus’abu wa zai hana ki”.
Gwaggo Habiba ta zuba mata ido cikin kaxuwa wasu sababbin hawaye suka zubo mata masu zafi saboda takaicin kalaman na Abu, sai dai babu yanda za ta yi.
Cikin nutsuwa ta ce, “Haba Inna, ni kuwa me zai sa ki gaya min haka? Kin sani sarai in ban da Saddiqa tana wurin nan babu abin da zai sa qafata ta taka gidan nan”.
Abu ta ce, “Oh’oh! Ni za ki kawowa wayo, in so kike a dubo miki Saddiqa ba wurinshi za ki ba, ba kya tunanin in je in gano miki in zo miki da wani sabon labarin”.
Ta miqe tana jan zanin ruhuwarta tana tafiya, fita gidan take nufin yi tana kuma qarasa zancenta, “Ba fa hanaki zuwa gidan nashi nake nufin yi ba, ai ba a raba xa da uwa”.
Takaici ya kama Gwaggo Habiba, can cikin maqogwaronta har wani xaci take ji saboda vacin rai, sai dai babu halin ta tanka.
“In kin je ki gai da Mus’abun”.
Ta faxi daidai tana fita.
Da daddare Gwaggo Habiba tana tare da mijinta Malam Abdallahi a gefen tabarmar da yake zaune yana cin abincin shi, yana kuma sauraron bayanin da take mishi na yanda suka yi da Abu.
Sai da ya ji ta yi shiru sai ya yi murmushi ya ce, “To ai sai ki haqura ki tura ta xin tunda ta ga za ta iya wannan wahalalliyar tafiyar”.
Gwaggo Habiba ta kalle shi cikin nutsuwa ta ce, “To amma Malam wane bayani Inna za ta zo da shi in dai a kan wannan yaron ne? Ka santa sarai halinshi na zahiri ma in za a faxa ranta vaci yake yi, ko yanzu ma kuma na fi zaton akwai abin da take tsoron kar a je a gani wanda yasa take faxanz uwan da na ce zan yi balle a ce ita ta zo ta faxa da kanta”.
Ya ce, “Eh, duk da hakan cikin biyu ne za ki zavi xaya, ko ita xin ta tafi ne ko kuma a haqura gaba xaya tunda ga irin kalaman da take furtawa”.
Gwaggo ta ce, “Ni kam gara in dangana in yi ta yi mata addu’a Ubangiji ya kuvutar min da ita daga dukkan sharri”.
Ya ce, “Eh, hakan ma yana da kyau”.

AJAKUTA
Mus’ab yana tsaye a falon cikin tashin hankali da fargabar rashin ganin Saddiqa a cikin gidan.
“Ke Zainab”.
Ya sake qwala mata kira da sake fitowa da gudu hawaye suna zuba a idonta
“Kin leqa nan maqwabta zuwa wajen su Abida ba ta nan?”
Ba ta iya amsawa ba saboda yanayin da ta ga Mus’ab a ciki, in ban da rawa babu abin da jikinta ke yi, ga shi kuma kusan awa xaya da rabi ne tunda suka nemi Saddiqa a gidan basu ganta ba cikin gida da cikin Ajakuta babu ita babu dalilinta.
“Kika ce kinga tana waya?”
Ta gyaxa kai nuna alamar eh, haka ne.
“Me kika ji tana faxa?”
Ya sake wata tambayar.
“Ban ji tana magana ba sauraro kawai na ji tana yi”.
Gabanshi ya sake faxuwa da ya gane wayarshi da Sarah ta saurara.
Anya Saddiqa tana garin nan ma kuwa?
Kai tsaye tambayar ta fito mishi daga cikin zuciyarshi. Kar dai gudu ta yi za ta koma Misau?
Bai jira jin amsar da zuciyar tashi za ta ba shi ba ya yi waje da gudu ya nufi cikin motarshi, sai da ya tabbatar ya xaure kanshi tamau da belt xin dake jikin motar sannan ya shiga tayar da ita, cikin zuciyarshi kuwa addu’o’I yake ta karantowa iri-iri na neman tsari da taimako wurin Ubangiji.
Mus’ab yana tafiya cikin matsanancin gudun da ba zai kwatantu ba, duk da kashedin da zuciyarshi ke yi mishi saboda yanda iska ke kaxa motar duk da mota ce mai nauyi.
Wayarshi ta yi qara a karo na uku, ya yi kamar ya sake yin buris da ita sai kuma ya yi tunanin to ko dai wani cikin masu taya shi neman ta ya ganta? Ya yi maza ya miqa hannu ya xauki wayar ya karata jikin kunnenshi.
“Hello!”
“Mutanen nan fa sun qi yarda su karvi cikiyar da muka kai musu, wai sai bayan awa ashirin da huxu da vacewar ta tukunna”.
Muryar Sani ce ta yi mishi wannan bayanin. Bai tanka ba ya mai da wayar mazauninta ya ci gaba da tuqinshi, cikin zuciyarshi kuwa mamakin hukumar ‘yan sanda yake yi wai basa karvar labarin vacewar mutumin da ya shekara goma sha takwas sai bayan awa ashirin da huxu da vacewar tashi. Ko mene ne dalilinsu na yin hakan? Oho!
Ya kwatanta yawan awa ashirin da huxu abin da za su iya yiwa Saddiqa sun isheta ta je har Misau ta zauna ta huta, ta ma kwana tana baiwa Gwaggonta labarin Mus’ab da abubuwan da ta gani a tare da shi.
In har Saddiqa ta samu nasarar isa gaban Gwaggo anya auren shi da ita zai xore? Tambayar da ta zo cikin ranshi kenan.
Tafiya mai tsanani ta awowi uku da mintoci arba’in kafin ya iso wata mararraba ta motocin da suka fito daga kudu suka nufi arewa, a nan ya yi parking cikin surquqin bishiyoyin da suka lulluve wurin, ya fito daga cikin motarshi riqe da kwalin sigarinshi a hannu da fankon ashana, cikin zuciyarshi yana tunanin a irin tafiyar da ya yi in dai Saddiqa motar haya za ta shiga kuma direban mai hankali ne, to ya wuto shi a baya, yana lissafi tare da raba awowi da mintocin tsakanin abin da ta yi kafin isarta tasha da shigar ta mota, da sallamar direba, har kawo isowarsu wannan mararrabar da ya ja ya tsaya.
To in kuma vuya ta yi a cikin garin fa?
Wata zuciyar ta aiko mishi da wata tambayar. Wurin wa? Ya sake tambayar kanshi. Nan da nan ya kori wannan tunanin.
A sanin da ya yiwa Saddiqa gida kawai za ta dosa ba za ta tsaya neman mavoya cikin mutanen da ba ta sani ba.
Da wannan tunanin ya isa wurin ‘yan sandan dake lura da wajen waxanda suka tsare hanya suna ta faman karvar naira ashirin wurin qananan motoci, hamsin ko xari wurin manya, gwargwadon dai irin lodin da ka zo da shi.
Barka da aiki Yallavai”.
Mus’ab ne yake isar da gaisuwarshi wajen xan sandan dake zaune kan wata mota a gindin wata bishiya mai yawan ganye da inuwa, wanda shi ke shugabantar wannan Road Block xin.
“Yauwa barka dai”.
Ya amsawa Mus’ab gaisuwar tashi bayan ya gamsu da kallon da ya yi mishi.
“In ce ko lafiya?”
Ya tambaye shi.
Mus’ab ya sanya hannu cikin aljihunshi ya zaro hoton Saddiqa da ya saka a ciki daidai yana cewa, “Lafiyar ba ta da yawa yallavai”.
Ya miqa mishi hoton yana cewa, “Matata ce ta baro gida ina kyautata zaton za ta biyo ta hanyar nan in har ba ta riga ta wuce ba, taimako nake so ka yi min na in tsaya tare daku”.
Ya yi mishi bayanin abin da yake so suyi mishi.
Xan sandan ya zubawa hoton ido ba tare da ya ce komai ba, tamkar dai wani nazari yake yi. Bai barshi ya kai qarshen tunanin nashi ba ya zaro bandir xin xari biyar-biyar ya jefa kan kujerar motar yana cewa, “Wannan a baiwa yara su sha kunun zaqi”.
“Ai ba sai ka yi wannan wahalar ba don za ayi maka xan wannan taimakon, su mata waxansu irin mutane ne, al’amarinsu har mamaki yake bani, ga shi dai duk wahalar da muke yi a rayuwarmu mafi yawancinta a kansu muke yi, amma basa gani balle su yaba mana, sun fi so kowane lokaci su rinqa tayar mana da hankali. Ni wani lokacin idan abin takaicinsu ya ishe ni sai in ji tamkar a raba mana wurin zama a ce ga garin mata ga na maza, su yi harkarsu muma muyi namu kowa ya yi harkar gabanshi ba ruwan wani da wani ko kuwa?”
Mus’ab ya yi murmushi daidai lokacin da ya gama fitar da hayaqin sigarinshi daga bakinshi, ya ce, “To amma yallavai da anyi hakan anya duniyar za ta yi mana daxi kuwa? Ai ina ganin da bamu yi jarumtakar da muke yin ba ma”.
Yallavai ya yi tsaki mai qarfi ya ce, “Ai kuma tsiyar kenan”.
Ya diro daga kan motar ya nufi cikin motarshi kamar zai ajiye sandar hannunshi, nan kuwa yana nufin sanin abin da Mus’ab ya ajiye mishi ne. yasa hannu ya xauka ya adanasu kafin ya fito, ya kalli Mus’ab cikin yanayin murmushi ya ce, “Amma wannan kunun zaqin ba zai yi musu yawa ba kuwa?’
“A’a, haba Yallavai wannan wuni da kuke yi a rana”.
“To an gode, bari in haura can wajan nasu don in ga irin aikin da suke yi”.
“To Yallavai”.
Mus’ab ya yi godiya, ya koma inda ya voye motarshi a surquqi ya zauna yana hangen abin da su Yallavai suke yi a inda yake voye.
“Park well!”
Tun Yallavai bai qarasa isa ba ya shiga ba da umarni, nan da nan motoci suka yi ta yin parking a gefen hanya.
Qananan ‘yan sanda suka shiga sosai leqa motoci, har duba but saboda umarnin Yallavai. Shi kuma hankalinshi yana wajen fasinjojin motocin ko zai dace da ganin yarinyar da hotonta ke sunne cikin aljihun wandonshi.
Ta kowanne vangare motoci sunyi dogon layi, ga matsanancin bincike cikin zafin rana Yallavai sai xigar gumi yake yi amma babu alamar zai gaji.
Mus’ab yana zaune cikin motarshi cikin fargaba da zaquwa daxewar lokaci ne ya dame shi, anya basu riga sun wuce ba ma kuwa? Ya tambayi kanshi.
Yawan harbawar da zuciyarshi ke yi ya hana shi ci gaba da zaman cikin motar, ya fito ya nufi bakin hanyar shima.
“Yallavai na ce anya basu riga sun wuce ba kuwa?”
Ya yi tambayar a yanayi na damuwa. Ya zubawa agogonshi ido tare da nazarin daxewar da suka yi a wurin suna cajin motocin.
Ya xago ya kalli Mus’ab ya ce, “Ina ganin har yanzu ba zamu fidda rai ba, ai ka san ba daga gida kai tsaye za ta kamo hanya ba, sai ta je tasha tukunna. Don haka ka qara haquri a wurinka don ba zamu so tsayuwarka a cikin mu ba”.
Mus’ab ya sake kunna sigarinshi ya sanya a baki, kafin ya sake gangarawa wurin zaman shi. A daidai wannan lokacin wata mota ta iso wajen peogout qirar station wagoan, ta bi bayan sauran motocin dake tsaitsaye.
Yallavai ya nufe ta da sauri zuciyarshi tana dakan uku-uku, anya ba ita ba ce wancan? Zuciyarshi ke tambayar shi.
Cikin hikima ya qara kallon hoton don ya qara tabbatarwa. Ita ce. Zuciyar tashi ta qara tabbatarwa. Yasa hannu ya buxe qofar motar.
“Fito nan”.
Ya nuna ta da sandar dake hannunshi.
Mutumin dake jikin qofar motar wanda sai ya fita kafin ta samu damar fitowa, wanda tun shigar shi motar hankalinshi yake kanta, iyaka dai bai ga fuskar yi mata magana ba, don haka ya mai da nutsuwarshi kan mujallarshi yana sauraron zuwan lokacin da zai dace da yi mata maganar.
Ya xago kanshi ya kalle shi ya ce, “Ta fito ta yi maka me?”
Gaba xaya jama’ar motar suka zubowa Yallavai ido.
“Common fito nan”.
Ya ba da umarni mai zafi don tuna musu ko shi waye?
Mutumin dake varin nashi ya fito ya tsaya gabanshi suna kallon juna.
“Wai kai waye da kake ja da hukuma? Ka kuwa san matsayin wannan abin da kake yi?”
“Ban sani ba Yallavai sai ka gaya min”.
Ya yi mishi bayani a yanayi na gatse.
Yallavai ya rabu da shi ya mai da hankali wajen baiwa Saddiqa umarnin fitowa”.
Mai mujallar ya kalle shi ya ce, “Haka kawai za ta fito ba tare da ka yi mana bayanin dalilin fitowar tata ba? Me yasa baka ce kowa ya fito ba sai ita wannan yarinyar?”
“Ita wannan da kake gani ta gudo ne daga gidan mijintaa, shi yasa zan fito da ita don in mayarwa mijinta da ita”.
Jin wannan bayani na Yallavai yasa wurin ya kaure gaba xaya fasinjojin cikin motar, waxanda mafi yawancinsu maza ne suka firfito suka kewaye Yallavai, daga masu gyaran zanzaro sai masu naxe hannun riga tare da faxin, “Wannan ai shine zance, ka tsare mu cikin jeji ka fitar da tsaleliyar budurwa a cikinmu ka ce wai za ka mayarwa mijinta da ita. To a wane matsayi, waliyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login