💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page1 ......." Katanfarin company ne da tsayawa fadar iyakarsa bata lokacin ne domin mutun bai Isa ya fadi adadin girmansa ba , hatta shi Karan kanshi mamallakin company bazai ce ga iya adadin girmansa ba adalilin kullum sake siyan wasu bangaren yake yana hadewa da company . "mutane kimanin million biyu da wani abu ne ke aiki a karkashin wannan maikatar daake sarrafa karafuna sanye da kayan aiki ." mamallakin wannan company ya mallaki companies masu yawa sai dai akwai guda daya wanda ya kasance hadin gwiwa ne tun mahaifinsa na raye suke kula dashi tare da ya'yan 'yanuwa ."haka ma bayan babu ran mahaifinsa bai wuftar da al'amarin wannan company ba ya cigaba da kula dashi saboda yana matukar qaunar company a cikin zuciyarsa dan ba qaramin wahala mahaifinsa ya sha akansa ba kafin ya samu daukaka da kar'buwa a duniya gabadaya ba ." A.G.C"wato Abdullahi group's company,company ne daya amsa sunansa, company né da suke da duk wani nau'in kayan sakawa ajiki ,kama daga na sarakuna ,manya attajirai ,shuwagabanin na duniya , kayanmu na gargajiya har ma dana turawa wato suit da kowani irin design's na tsarkoki ,daga ko wacce kasa ka bukaci kayansu zaka samu cikin sauki sannan kuma suna zana duk irin design's din kaya da tsarkokin da kake so har ma da zanen kanfanunnuka ,zanen hotuna kai duk wani nau'in na zane suna da kwararun masu zanawa wuyarta ka zaba desing's zasu yi maka ." daya daga cikin maaikatan gurin ya dago yana kallon shugaban da aka d'aurawa halakin kula da ma'aikatar karafuna wanda isowarsa kenan "barka yallabai "barka dai malam mashkur fatan komai dai yana tafiya kamar yadda aka tsara ? dan sam bana son a samu wata matsala sannan bana son a samu sa'banin akan karafen can ka tabbatar an cigaba da samun irin wadan can, sannan wadan can kayan Ina son akawo su da wuri dan mai gida zai .... "bai kai ga karasa maganarsa ba sautin qarar jet din mai gidansa ya katseshi hakan yasa a hankali manager malik ya d'aga idanunshi dake manne da bakin glass zuwa sararin samaniyya cikin sauri yace "shikenan kaje ka cigaba da kula da duk masu aiki ga mai gida nan ya iso ." ADAM TARIQ ABDULLAH kenan, shugaban kafanunnunka ATA companies ...... matashin dan kasuwan da yafi kowani dan kasuwan bahaushe kudi a Duniya kallo daya zaka masa ka fahimci matakin shekarunsa, bazaka kirashi da yaro ba haka zalika bazaka kirashi da dattijo ba shi din matashi ne me kimanin shekaru talatin da bakwai a duniya fuskar shi babu yabo babu fallasa kasancewar haka yanayinsa yake, kullum haka zaka ganshi fuskar nan tashi a hade tamkar hadari sai dai na wannan lokacin ya zarta na sauran lokutan baya wanda hakan ya faru ne akan abinda ke dawainiyya da rayuwarsa." .Adam Tariq abdullahi wanda ake kira da (mr ATA) a duk fadin duniya kyakkyawa ne ajin farko mai tsantsar kamala da kamewa tattare da haiba sai dai sam bai da faraa komai cikin zafin rai da zuciya yake aiwatar wa , " rayuwarsa rayuwa ce dake da bambamci data sauran mutane , shi din mutun ne miskili mara saukin Kai dan idan kayi Kuskuren shiga track dinsa zaka gane baka da wayo dan ya iya duk wani nau'i na tozarci da rashin mutunci tare da disga mutun sabanin mahaifinsa da mahaifiyarsa da sauran yanuwnasa da suka kasance masu tsanani saukin kai tausayin mutane tare da tallafawa bayi mabukata ,fari ne sol dan babu digo tabo ko daya ajikinsa hatta bakin kwayar idanunshi gauraye yake da fari ,dogo ne sosai mai matsakaicin jiki , da kyakkyawar fuska da idanuwa , fatar jikinsa na ya'yan masu kudi sai sheiki yake daga samansa har kasansa babu makusa sannan babu alamun babu a tattare dashi yana da matakin karatu na Phd akan kasuwanci kuma har lokacin yana kan karatu bai ajiye ba ,shine ya tattara gabadaya kyawun mahaifiyarsa hajiya zulaiheart da mahaifinsa marigayi barrister Kuma shararen dan kasuwa Alhaji Tariq Abdullah ." "duk wani ma'aikacin dake aiki agurin tsayawa yayi cak ya kasa cigaba da aikinsa kamar yadda aka umarcesa saboda kwadayin ganin wannan kyakkyawar fuska har sanda jirginsa mai saukar ungulu ya sauka idanunsu na kanshi , sai da jirgin yayi kamar minti biyu da tsayawa sannan a hankali kofar jirgin ya bude Inda ya matso a hankali shi bai fito daga cikin jirgin ba haka zalika shi bai zauna sosai ba yana kada kafarsa daya cikin nuna Isa da izzar shi din wani ne .a zahirin ake iya ganin gangar jikinsa wanda hakan yasa kayan dake sanye dashi suka bayyana, Suit ne wando da riga ruwan madara yayinda yar cikinsa ya sakance baki kafafunsa sanye da black shoe's haka idanunshi na manne da farin glass yana qarewa haraban gurin kallo tare da kallon ma'aikatan dake aiki ." a natse ya fito hannunsa daya na cikin aljihun wandonsa yana taku daya bayan daya cikin Isa da izza yayinda escort dinsa ke gefen hagu da damansa kowannensu sanye da suit iri daya da makaman tsaronsa wato bindigu ."daya daga cikin escort dinsa na rike da wata karamar brief case kalar suit din jikin Mr ATA ." manager malik ya karaso da sauri cike da ladabi ya tsaya a gabansa "ranka shi dade mr ATA barka da zuwa? shiru ne ya biyo baya na kamar second biyar sannan a hankali ya motsa labbansa da kyar "barka m . malik ya kokari ?." alhamdulillah sir " m.malik ya fada yana mika masa hannu Mr ATA ya mika masa dayan hannunsa dake waje yayinda har lokacin dayan hannunsa ke cikin aljihun wandonsa " gaskiya naji dadin yadda na iske kamfani kowa na kan aiki Wanda nasan duk cikin kokarinka ne dan ga dukkanin alamun aiki na tafiya yadda ya kamata ya karasa maganar yana zare hannunsa cikin na malik ya tsotsa bayan keyarsa sannan ya cigaba da magana yana tafiya a natse "kana yin yadda ya dace daman ba daidai bane tsuntsu ya cinye tsaba batare da yayi aiki ba "ai yallabai dole ayi aiki yadda ya kamata dan kai din na dabam ne sannan bakayi abinda tsuntsun zai cinye tsaba batare da yayi mata aiki ba "ka ajiye wannan maganar na gama daita yanzu, ma cigaba daga baya " m.malik ya gyada masa Kai alamun yaji cike da ladabi yace "sir mu karasa zuwa office mana ? runtse idanunshi yayi kawai batare da yayi kokarin aikata hakan ba ." bayan kamar mintuna talatin ya numfasa "Petir da sinadarin gas tsawon shekara bakwai kenan nayi Ina nema a wani yakin a cikin apapa ban samu ba sai gashi kwatsam na sameshi bayan na kashe billiyoyin kudade , sai dai ka taki sa'a dan Kai na zaba a matsayin wanda zai kular min da gurin ..." duk wannan maganar da yake har lokacin bai zauna ba tafiya yake ahankali a haraban ma'aikatar "Kai amman gaskiya naji matukar dadi ranka shi dade sai dai da za'a barni anan na cigaba da kula da bangaren karafai zai fi min , dan ba lallai ka samu Wanda zai kular maka da gurin nan yadda ya kamata ba ." "karka damu m. malik already y ma nazo da wanda zai cigaba da kulawa da nan din ,adaidai karshen wannan maganar tasa ya samu guri ya zauna akan wata hadaddiyar kujera mai runfa zagaye da kujeru na alfarma dama Kuma duk sanda bai ra'ayin shiga office dinsa ba idan yazo anan yake zama ya d'aura hannunsa daya akan table , Shima m. malik ya samu guri ya zauna yana fuskantar me gidansa da sauraronsa "na zabeka ne saboda baka da wasa akan aikinka gashi kana da rikon amana da mazantakan kula da komai fatana ka cigaba a yadda na sanka ." Ya Kai hannunsa na hagu bangaren hagunsa , nan take escort dinsa me rike da brief case ya daura brief case din hannunsa akan table ya bude ya ciro wasu manyan freme mai dauke da zane day day har guda goma Kuma duk abu daya ne zane acikinsu . Mr ATA ya dauka ya tsurawa zanen lumtsamtsun Idanunsa masu fitar da zaiban haske tsabar hasken dake cikinsu, second biyar ya dauka yana kallon zanen sannan ya numfasa ya ajiye akan tablet din gabansa yana cigaba da kallo "ko ka samota m. malik ? ko samun labarin wanda ya santa ? "Ina har yanzu dai tukun nan yallabai amman Ina iyakar kokarina kuma zan cigaba wai shin wa...."babu ruwanka da wannan hurumin m.malik dan ....." qarar daya daga cikin wayoyinsa ne ya katse shi yayi shiru batare daya ci gaba da magana ba yana jiran a miko masa wayar escort din dake rike da wayoyinsa ne ya miko masa "my sweetheart " .ya fada tare da rusunawa mr ATA . da sauri mr ATA ya amshi wayar a hannunsa ya manna a kunnenshi ya mike tsaye cikin tsananin tashin hankali da girmamawa ya fara tafiya yana magana a natse "inna lillahi dan girman Allah sweetheart ki qara hakuri dani , ki Kara bani lokaci zan yi qokari ,okay I know nasan kin yi hakuri dani amman Ina da tabbacin wata rana zakiyi farinciki sosai, ina kan neman matar da zan aura ni dai ki tayani da addua murmushin gefen baki ne ya bayyana akan fuskarsa adalilin uzurin da tayi masa nan take ya samun natsuwar zuciya ya cigaba da abinda yake ." ******* LAGOS Da misalin karfe biyar na yammacin ranar laraba "Yammata ne su hud'u zaune a cikin wata hadaddiyar mota kirar land cruiser prador ,mutun biyu zaune a gidan bayan ,yayinda biyu ke zaune a gaba akan titi masha dake surelere , humaira dake kusa da mubina ta Ciro wayarta iPhone 12 Pro max acikin jakarta ta soma d'aukarsu snap tana ta'ba kafad'ar mubina dake driving dan ta shigo cikinsu ,mubina tayi murmushi ta dan shigar da fuskarta tare da d'aga yatsunta biyu kana ta maida hankalinta kan tuki ." tafiyar mintuna ce ta kawosu Apapa gra suka tsaya a gaban wani makeken get da aka rubuta ABDULLAHI ESTATE tare da yin hon ,daya daga cikin masu gadin estate din ya leko adaidai lokacin da mubina tayi kasa da glass din motar ganin yaran estate din ne ya koma da sauri ya bude .mubina ta danna hancin motarta ta shiga Katafaren estate din nansu mai d'auke da gidaje fiye da ashirin sama da kasa sai dai acikin gidajen akwai guda daya wanda ya bambamta dana saura wato gidan hjy zulaiheart ." yanayin gidanta ya bambamta dana saura ne sakamakon marigayin mijinta yafi sauran yanuwansa tarin dukiya kuma ko bayan mutuwarsa yaranta sun cigaba da qawata mata gidanta kullum cikin gyara yake da canza kayan ado na zamani , 'yan aiki ma sun bambamta dana saura ,yan aiki guda goma sha biyar ne ke zariyar kula da kowoni bangare na gidanta ,sannan kowannensu sanye da fararen kaya masu ratsin baki . babu mutun ko daya na cikin ahlin estate din dake tsaye akan kafafunsa domin yin aiki sai dai dan aiwatar da ibada , kowa acikin gidan dan gata ne hatta bakin dake zuwa gidan jin kansu suke tamkar ya'yan wasu saboda mutuntaka na mutanen gida, tsarin gidan hjy zulaiheart kuwa kace a gidan turawa ne kowani bangare shirye yaki da kayan alatun na more rayuwar duniya ,haka ma kofar da zata shigar da mutun bangaren hjy zulaiheart tsare yake da securities guda biyu masu duba jikin mutane koda zaa shigo da wani abun cutarwa . mubina ta dauki hanyar inda aka tanada domin paka motocin bangaren gidan hjy zulai nan take sauran yanuwanta kuma kawayenta suka hada baki gurin cewa "ya haka kuma ?"Sai data dan marairace fuska sannan tace "dan allah mun dan shiga muga su marsi kwana biyu bamuga juna ba daga nan ma sai mu tsaya muyi sallar magrib da ishai sai kowace ta kama gabanta dake duk suna shiri da juna yasa babu wacce tayi mata mutsu har tayi parking tare suka firfito daga cikin motar suka nufi hanyar gidan hjy zulaiheart ,babu wacce ta jira ayi checking din jikinta ko mata iso shiga ciki kasancewar nan din ma gida ne a wurinsu tunda bangaren danuwan mahaifansu ne . sallamarsu maryam da nana hauwa'u suka ji suka mike cike da farinciki suka rungume juna suna wa juna barka da zuwa sannan suka zube akan royal chair's suna tambayar hajiya zulaiheart "mami tana ciki tana amsa waya maryam ta basu amsa zamansu ko cikakken minti biyar basu yi ba sai ga mutun uku cikin masu aikin gidan kowacce sanye da farin kaya da ratsin baki hannunsu rike da tire , tiren na farko lemu da ruwa ne ,sauran biyu din kuwa duk kayan motsa baki danginsu snacks da dambu naman rago , suka gaishesu cike da girma mawa ,suna gama ajiyewa baki abin motsa baki suka Kara gaba suka koma bakin aikinsu .." "Daga ina haka dan naga alamun kamar fita kukayi ? "eh ! fita mukai muje birthday din wata abokiyarmu da muka qare karatu tare ne , dawowar mu kenan nace mu shigo kwana biyu bamu ga juna ba inji cewar mubina "ai kuwa mun gode muma kuna ranmu ,wallahi kullum sai nayi maganarku inji cewar maryam , nuzla taí saurin cewa "babu wani maganrmu da Kikeyi ga baki ga hanci amman zuwa ya gagreku kullum kuna gida kunshe kuna faman posting a social media ." "wannan kuma da sister kike ba dani ba nana hauwa'u ta fada tana murmushi tana kallon maryam , maryam ta kai mata duka ta kauce da sauri tana sake murmushi tana cewa "ai sister daana daura kashi to wallahi data daura nata nifa idan tanayin wani abu har takaici take bani ahankali suke hirar yaushe gamo duk da suna cikin wuri daya amman sukan dauki lokaci basu hadu ba kowa yana nashi wuri ." Suna cikin hira idanun mubina ya sauka akan tangamemen hoton mr ATA dake manne da bangon falon yana sanye cikin suit bakake fuskar nan tashi kmr Koda yaushe babu faraa amman hakan bai hana kyawunsa fitowa ba ." ta d'auki sama da mintuna talatin tana kallonsa Yayinda sauran yan'uwanta suka cigaba da hirarsu, murmushi ne ya subuce akan fuskar mubina wanda bata san sanda tayisa ba , nana hauwa'u ta Kai hannu ta dafa kafadanta tana cewa "ya'akayi mubina kika tsare mana yaya da Ido ko dai ko dai ? a matukar firgice wacce aka kira da mubina ta waigo ta sauke idanunta akan nana hauwa'u tana sakar mata murmushi tare da sauke ajiyar zuciya "wallahi kamar kin sani yar'uwata tunda na taso babu abinda nake so kamar ya adam "inna lillahi kice dai saboda kiga hotonsa yasa kika matsa lallai sai mun fara shigowa nan?inji cewar diyana "kuyi hakuri wallahi yana cikin dalilin saboda na kwana biyu bangansa ba ko wulgarwasa fa ina jin ma kamar baya kasar ko ...."? wannan furucin da tayi yasa gbdy yan'uwanta suka maida hankalinsu kanta cike da tausayawa , nana hauwa'u ta dinga kallonta cike da matsanacin mamaki dan tasan mubina da tsatsanin kunya uwa Uba aji dan ta sha ganin yadda takewa samari wulakanci, samari ma yayan masu arziki amman bata da lokacinsu "wallahi nana hauwa'u da gaske Ina son ya adam so Kuma me tsanani da Ina da tabbacin zai aureni da zan ajiye komai na furta masa Ina son shi saboda son da nake masa bana wasa bane, maryam dake zaune kusa da nana hauwa'u tayi murnushi kana tace "zai soki mana amman sai kinyi kmr kina kiyi gsky ,dan wallahi kallon fuskar shi ma abar tsoro ce kullum fuska a hade ga babu mgn mai dadi komai daga nonsense,rubbish, stupid girl ,crazy girl ,Ke ni gbdy tsoro yake bani bana ko iya kallonsa. suka kwashe da wata mahaukaciyar dariya suna cewa "shegiyar matsoraciya ,shine dan iskanci kike bata kwarin gwaiwa taje yaci ubanta ? "suka sake kwashe da wata dariyar " Nan hirarsu ta koma ta mr ATA wasu na bawa mubina goyon baya ta fada masa zai amince tunda bai tsaida matar aure ba ,yayinda wasu na nuna mata illar hakan amman ita mubina ko uffan bata furta ba illa dai tana ji Kuma tana sauraronsu daya bayan daya, a natse maryam ta tsurawa mubina Ido "mubina idan kin tabbatar kina son shi shawarata ki cire tsoro dan nasan shi kike ji , ki furta masa in sha allahu zai amince Kuma zai soki tunda duk kin hada abubuwan da zaki sace zuciyar kowani nmj "Kai yar'uwata kina gani zai Soni kuwa ?why not ya Adam zai amince da sauri ma a wannan zamanin namiji ya samu macen dake sonsa kmr yadda kike son ya AD ai babu jiran da zai tsaya yi ,kefa sauraniya ce acikinmu karki ji komai na baki goyon baya dari bisa dari ki ........" Kiran hjy zulaiheart ne ya katse maryam ta mike da sauri ta nufi d'akin mami ta barsu suna cigaba da tautaunawa byn wasu mintuna hjy zulai ta fito tana sakar musu murnushin jin dadi tana aiyana Ina ma Adam dinta zai daure ya zabi mata a cikinsu kamar yadda sauran yanuwasa sukayi gasu nan masha Allah dan kusan auren zumunci ake yi a family din amman dai zata gwada yi masa magana taga ko za'a yi sa'a ya amince ,suka hada baki suka gaisheta a mutunce ta amsa tana tambayarsu lafiyar iyayensu , anan suka qarasa yini suna Hira daga wannan hirar zuwa wata hira sai dare suka kama gabansu ." ****** Bayan wata daya aka wayi gari akaga gawar mubina agdan qanwar mahafiyarta zainba an kasheta ta hanyar tsoka mata wuka a daidai saitin zuciyarta Kuma aka bar wukar ajikinta ba'a cire ba hankalin family's din abdullahi ya tashi matuka mahaifiyarta kuwa kuka da sambatu take tana cewa daga ziyara shikenan an kashe min 'ya daga ziyara fa ,daga ziyara fa!! haka ta dinga furtawa har abun yaso zame mata kmr ta zautu saboda ita kadai gareta mace sauran ya'yanta duk maza ne ,sauran yanuwanta sunyi kuka kamar zasu bita lahira maryam kamkame da hannun mubina tana wani irin kuka me ban tausayi saboda akwai sabo me tsanani a tsakaninsu "waye yayi mana haka ?waye ya kashe mana yar'uwa ?an kasheta batare da burinta ya cika na auren ya AD ba sai lokacin mutanen gidan suka San da batun soyayyar da mubina ke yiwa AD batare da bata lokaci ba jamian tsoro suka shiga lamarin suka shiga d'aukar gawarta hoto yayinda daya daga cikin police Ke rike da farar takarda yana rubuce rubuce akan gawar byn sun gama sannan aka cire wukar aka soma kokarin shiryata zuwa makwancinta Inda har lokacin jini bai daina tsiyayya ba." Mr ATA na gidansa dake banana estate yana kallon zanensa dan wani lokacin idan yana son hutawa can yake zuwa yayi kwana biyu idan ya gaji ya dawo gida wurin mahaifiyarsa dan bazai iya yin nisa daita ba , Kiran sweetheart dinsa ya samesa inda cikin kuka take sheida masa halin daake ciki a zaune yake amman bai san sanda ya mike tsaye rike da zanensa gam yana furta kalmar innalillahi "yaushe kenan ? ya furta cikin tashin hankali " okay ganin nan zuwa nan da wasu yan mintuna bai tsaya katse Kiran ba ya mike ya leko zuwa falonsa na uku Inda ya bawa masu tsaronsa umarnin fita yana gama fadar haka ya koma ya shirya dan daman yyi wanka cikin kankanin lokaci ya fito ya karasa Inda motarsa yake aka bude masa gidan baya ya shiga ya zauna zuciayrsa na tsinkewa hankalinsa na sake tashe sai dai ba'a iya hango bacin ransa a fili sai dai daga ciki yake iya bayyanashi ai kuwa da yana nunawa da duk ahlinsa sai sun fahimci yadda yaji mutuwar mubina .Kyawawan idanunshi wadan da suka wadatu da gashin idanu ya zubawa gawarta dake kwance a parlour dan har an fito daita domin tafiya daita makwancinta .duk da kasancewarsa mutumin da baya sakewa da 'yanuwansa amman yaji zafin mutuwar mubina sannan ya tausayawa iyayenta kasa furta komai yayi duk da maganar yake son yi amman maganar taki fitowa hankalinsa sai sake tashi yake yana mamakin yadda aka kashe mubina yana wannan tunanin aka fito da gawar mubina da jini duk ya bata likkafani aka nufi gidanta na gaskiya ." Bayan an dawo daga kaita duk yan'uwa suka yi tsuru tsuru kowa ka gani yana cikin tsananin tashin hankali me tsananin ,Sosai mr ATA yaji mutuwar yar'uwarsa duk da ba wani sabo ne a tsakaninsu ba, batun tana son shi kuwa sai lokacin yaji abun ya mugun tsaya masa rai duk da yasan babu digon sonta a zuciyarsa kawai dai tausayi ne da jimami , yan'uwa sun jajantawa juna "yarinyar da bata da hayaniya yaushe take fad'a bare a samu abokin gabarta da har zai yi sanadin mutuwarta ,bata shiga harkar mutane kullum cikin faraa take inji cewar hjy zulaiheart kowa mamakin da yake yi kenan a tsakaninsu .muryar mr ATA a sanyaye ya dube police officer din dake tsaye kusa da mahaifiyarta yana mata tambayoyi "kuyi iya bincike da zakuyi Ina son a gano wanda yayiwa mubina kissan gilla dan sam bazan barshi ba koda kuwa danuwana ne ," ya karasa maganar cikin tsananin fushi "karka damu ranka shi dade tabbas zamuji da komai bai ce komai ba ya k'arasa kusa da mahaifin mubina dake rike da wukar da'a aka kashe masa tilon diyarsa ya dafa kafad'arsa sannan ya karbi wukar daga hannunsa yana kallon wukar mai dauke da kan sarauniyya ya dinga kallon wukar da akayi kisan sabuwa ce fil da alamun ma akan mubina aka fara amfani dashi ya furzar da numfashi kana ya soma mgn "karka damu uncle jay dake haka yake kiransa inshallahu za'a gano ko waye yake da saka hannu gurin kashe mubina ka kwantar da hankalinka muddin Ina raye sai nasa an gano wannan mashekin ."ya karasa maganar jijiyo kansa na mikewa, hawaye ya zubo a idanun mahaifin mubina ya daura hannunsa daya akan hannun Mr ATA dake kafadarsa "na gode ADTA dake shima hk yake kiransa Allah ya jikan mahai ...."kasa karasawa yayi saboda kukan daya ci karfinsa dan sai lokacin ya samu damar zubar da hawaye mr ATA ya rungumeshi ajikinsa tsam yana rarashinsa ." bincike sosai akayi akan mutuwar mubina sai dai har wannan lokacin da ta cika wata biyar da mutuwa ba'a samu nasarar gano hannun wanda yayi kisan ba a karshe mahaifinta yace abar case din ya barwa Allah komai amman mr ATA yace sam a cigaba da bincike da kyar uncle jay ya shawo Kansa ya hakura , maryam ta dade tana Jin mutuwar mubina a zuciyarta dan ko runtsawa bata yi duk sanda ta tuna maganarsu na karshe kafin akasheta sai ta rushe da kuka Mai tsanani "ki tayani da addua marsi ina Kara Jin qaunar ya ad a cikin zuciyarta gashi bani da yadda zanyi ya fahimceni tsoronsa ya hanani fuskantarshi da maganar amman zanyi qoqarin fad'a masa acikin satin nan Allah yasa idan na furta masa ya amince ya aurenni ,ni ko baya sona zan zauna dashi haka bare ma wuyarta mu kasance miji da mata tuni zan mantar dashi wani kiyyaya Allah sarki rayuwa kenan mubina Allah yayi Miki rahma .." ******* Bayan shekara daya Yana zaune akan gadon hjy Zulaihat sanye cikin kananan kaya wondo da riga ash colour idanunshi sanye da farin glass yana fama tura sakonni ta shigo dakin ta nufi inda beside dinta yake "sweetheart! ya kira sunan da yake kiranta dashi sabani Kowa dake kiranta da mami "Yaakayi my love ta amsa tare da kallonsa "ko zan samu black tea ?yayi mgnr yana cigaba da aiki "me zai hana shalelena bari nasa maryam ta kawo maka nayi baki ne . "No abarshi kawai sweetheart idan itace zata kawo min yaran da babu abinda suka iya sai shirmen banza da wofi .tayi shiru shima yayi shiru ,shi dai bai san dalili ba amman baya son maryam a kusa dashi Kullum qara jin tsanarta yake wanda da zaa tsaresa da bindiga bazai ce ga dalili ba, shi dai hk kawai yake jin baya sonta a duk cikin family's dinsa na bangaren uwa da uba ." ta juya ta bude beside tana duba abinda ya shigo daita "yauwa ko zaki bawa auta ta kawo min idan tana nan "still bai dago ya kalli inda take ba ?dagowa tayi a natse tana sauke numfashi sannan ta d'an matso kusa dashi ta daura hannunta akan sumar kanshi tana lumshe ido kana tace" ai duk abu daya ne da auta da maryam dukkaninsu shirmen banza da wofi suka iya zai fi kyau ka kawo wacce bazata dinga maka shirmen banza da wofi ba ta dinga maka abinda kake so " . "ta fad'a tana dauke hannunta akan sumar kanshi ."ya dan dago a hankali ya kalleta suka hada ido yaga yadda fuskarta ya canza sosai alamun bata ji dadin abinda ya fada ba, ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa yace "am very very sorry ma "shikenan yanzu auta zata kawo maka ta dauki abinda ya shigo daita ta fice daga dakin ". Byn minti goma auta ta shigo a hankali tmkr kazar da Kwai ya fashewa aciki bakinta dauke da sallama hannunsa kawai ya mika mata tana mika masa cup din tea ta fice da sauri ta bar dakin, yana cikin aiki ya samu kira daga danuwansa hisham ya dauki wayar "hello hisham ! "Okay just give me ten minutes I will meet you there ya fad'a yana kokarin kashe system dinsa byn ya kashe ya dauki system dinsa ya rungume a qirjinsa ya nufi kofar fita ." yana qoqarin fita maryam na qoqarin shigowa dakin hannunta rike da akwatin sarkokin hjy Zulai da wayarta on exepecting taji tayi karo da gangar jikin mutun nan take system dinsa yayi tsalle daga qirjinsa yayi kasa ...,"da wani irin mugun sauri tayi watse da kayan hannunta har ma da wayarta tayi kasa ta tarô system din da hannuwanta duka tun bai kai kasa ba ta shiga uku ,shi kuwa ATA tsaye yayi batare da wata alamun damuwa a tattare dashi ba yana dubanta sai dai kallo daya zaka masa ka fahimci ransa ya baci da abinda tayi ,shi bama system din yafi damunsa ba kamar haduwar da jikinsu yayi ." jikinta na rawa ta miko masa system tana cewa "am ... am very sorry kayi hakuri dan allah ban ....."ai batasan sanda tayi shiru ba sakamakon wani kwallo da yayi daita da system din nasa gbdy kamar ball sai gata a waje bisa gwiwowinta ta dunkule guri daya , bata bi ta kanta ba ta maida hankalinta ga system dinsa ,nan ta hango system ya wargaje a kasa kallo daya tayiwa system din ya fahimci ya tashi aiki nan fa hankalinta ya sake tashi "stupid girl kawai ." ya furta da karfi yana qarasa fitowa daga cikin dakin sosai ya daga kafarsa daya zai daki gefen cikinta yaji sautin muryar hjy Zulai "karka soma adam ". Numfashi ya sauke yana waigowa zuwa inda take tsaye ranta a matukar bace tace "me yayi zafi adam zaka kashe yar mutane ne ?laifin me tayi maka ?tayi masa tmbyr ajere ransa a matukar bace yace "ask this nonsense girl ." ya fad'a yana nuna maryam da dan yatsansa hjy zulai ta qaraso tana kokarin daga maryam "me kikayi masa yake kokarin kasheki "? ranta a matukar bace ta soma magana, ahankali ta zayyanewa hjy zulai komai tana sheshekan kuka tmkr ranta zai fita .."naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana dubansa " shine zaka mata irin wannan hukunci ko da gangan tayi bai dace ba bare babu daya "ya kada kai zai wuce "adam ! ta tsaidashi ta hanyar kira sunansa Ya juyo a matukar fusace yana dubanta " daga yau kar na kara ganin ka ta'ba lafiyar jikinta bama ita ba kowani yaro a gidan nan ban amince ba ban lamunta ba kaji na fada maka........" iska ya shaka ta cikin bakinsa daman kuma duk sanda ransa ya baci baya fesar da iska a fili sai dai acikinsa juyawa yayi ya kama gabansa ."hjy Zulai ta kamo maryam suka shiga cikin dakinta tana bata hakuri "ki dinga kula kinji maryam wannan yayan naki hakurinsa mai yawa ne ta zaunar da maryam akan gado itama ta zauna tare da daura kan maryam akan ciyarta ta daura hannunta akan sumar kanta tana shafawa" ki tayani da yi masa addua allah ya yaye masa wannan nukufurcin da zafin rai da yake fama dashi ".Allah kiyaye na rasa wanda zan wa addua sai mutumin daya tsaneni kamar ya kasheni ta fad'a acikin ranta mami tace ,"zaki tayani yi masa addua maryam ?."cikin muryar kuka ta gyada mata kai kawai ba dan zatai ba "Yauwa na gode Kwarai diyata allah yayi miki albarka ." Da daddare ATA na zaune akan makeken gadonsa yana operating din wayarsa hjy zulai ta shigo bakinta dauke da sallama lumshe lumtsatsun idanunsa yayi saboda ganinta duk halin damuwar da yake ciki da zarar ya ga mahaifiyarsa yake jin sanyi aranshi "fatan kina Lfy sweetheart "?ya tambayeta yana riko yatsun hannunta daya cikin nashi "alhamdulillah ta fada fuskata babu yabo babu fallasa ."ga coffe ta mika masa sannan ta zauna kusa dashi ya saki yatsun hannunta ya karbi cup din coffee ya kai bakinsa "me zakayi breakfast dashi da safe ? yayi shiru yana tunani can yace "komai sweetheart dina zata ci nima zanci ." Adam!!! ta kira sunansa har sau uku ya sake rike hannunta gam cikin nashi yana kurban coffe yana lumshe ido har dimple dinsa na lotsawa ," ina son nayi wata magana mai mahimanci da kai,nan take ya bar abinda yake ya tattara dukkanin natsuwarsa zuwa gareta "abinda kayi dazu sam banji dadi ba dan allah na roki arziki ba dan ni ba karka sake maimaitawa ."tai shiru tana jiran taji me zai ce "ya lumshe mata idanunshi "naji amman itama ki mata mgn ta daina shiga hanyata "wannan kuskure aka samu domin kuwa maryam na qoqarin gani bata shiga harkarka ba ". "kai ba ita ba kowa acikin family's din nan yana takatsntsan ba yara ba ,ba manya ba sai kace wani azara ilu "yayi murmushin ciki wanda ita kadai take iya fahimtar haka ,"wallahi ka canza kai gaka nan kullum cikin bakin rai da miskilanci yanzu kai ko shaawa rayuwar gidan nan bakayi kowa na son kowa kalli su hisham dasu tariq sweetie nah kenan ya dauko mai sunanshi tsab ,kai hatta muhd bello da ba dan gidan nan ba yana jan yaran gidan nan ajiki amman kai kowa tsoronka yake ji Kmr wani dodo wallahi ka dinga son mutane dan mutane rahma ne." "to ni nace bana son wani ne acikinsu ?ya fad'a a shagwabe yana daura kanshi saman cinyarta " girgiza kai kawai tayi tana daura hannunta a sumar kanshi tana shafawa tana kallon kyakkyawar fuskarsa mai cike da haiba ga kwantaccen gashin fuskarsa dake mugu mugun qara masa kyau sosai ya kwanta luf luf saboda gyaran da yake sha . "ni sweetheart kin kasa ganewa ne nifa raini ne banason su kuma yan renin sense ne kinga gara na dinga kama kaina "yyi mgnr Kmr bashi yayi mgnr ba ,girgiza kai ta sake yi kana ta cigaba da mgn "sai abu na gaba "ya batun aure ko har yanzu baka samu true love din ba ? ."Yes of course ban samu ba sweetheart ,"yanzu kai baka tausayawa wannan mamartaka da shekarunta yaja ? " "Adam at any time zan iya amsa kiran allah ko sai bayan mutuwata zakayi aure ? tayi mgnr tamkar zatai kuka nan fa hankalinsa yayi mugun tashi ya mike zaune tare da riko hannuwanta gabadaya cikin nashi yana kallonta cike da matsanancin soyayyarta gbdy yanayinsa ya sauya kamar zai yi kuka dan baya qaunar abinda zai nisan tashi da mahaifiyarsa bare rabuwa ta har abada ,muryarsa a kasalance ya soma mgn "haba sweetheart me yasa zaki fadi haka ?" Me yasa bazan fadi haka ba ?ai gaskiya na fad'a kaki kayi aure kai dai kullum aiki kawai kasa gaba baka ma duba lamarina bare ka tausaya min Adam , bana son na koma ga allah banga aurenka da ya'yan ka ba ta qarasa mgnr cikin raunanniyar murya wannan karon kam hawaye ne taf acikin kwayar idanunta "karki min hk sweetheart Kinsan illar zubar da hawayenki akaina, kuma Kinsan babu abinda na tsana kamar na ganki cikin damuwa "idan har da gaske baka son ganina cikin damuwa to ka dan duba ko a cikin yammatan estate din nan ai bazaka rasa masu sonka da aure ba sai ka zabi biyu ko daya acikinsu ". Ya ware mata lumtsatsun idanuwanshi sosai yana mamakin jin abinda tace "har mata biyu sweetheart ina zan kai su ? "bansani ba ta fad'a tana zabga masa harara sannan ta cigaba da mgn "wallahi shine burina ka auri mata biyu kuma duk arana daya saboda kasancewarka namiji kwaya daya tilo da allah ya mallamin "girgiza kai kawai yayi yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa batare da yayi yunkurin sake cewa wani abu ba ya sake jin sautin muryarta "zakayi abinda nace ko nasa araina sai bayan na mutu zakayi aure ?" ya shafa goshinsa yana cewa "okay zanyi kokarin yin haka sweetheart." Ya fadi hk ne dan ya kawo karshen mgnrsu ."ko kai fa yaron albarka allah ya zaba maka mata na gari , runtse idanuwanshi yayi sosai tare da yin shiru yaki cewa komai dan har kanshi ya fara ciwo ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page2 ....Da misalin karfe goma na safiyar ranar asabar mr ATA ya sauko daga saman dakinsa jikinsa sanye da bakin riga da wondo baki yayinda kafafunsa ke sanye cikin wasu hadaddun silifas masu matukar kyau suma black kana gani kasan masu tsada ne haka idanunshi suna makale da farin glass wanda ya zame masa tamkar na gado, ko bacci wani lokacin dashi yake sai idan Mahaifiyarsa ta shigo ta gansa dashi ta cire masa ,yayi kyau sosai acikin shigar kasancewarsa fari ."ya qaraso ya dauki jarida daily trust da'aka ajiye masa ya samu wuri ya zauna akan doguwar kujera mai zaman mutun uku ya daura kafarsa daya a kan daya ya shiga duba jarida " yana zaune nana da maryam suka fito suna magana akan inda mai decoration zatai decorate din birthday din maryam dana hanan diyar Aunty zabiba kanwar mr ATA da zaa gabatar a ranar ." suna gama qarasowa parlour'n suka gansa zaune Kmr an dasashi a gurin ."suka bishi da kallo suna jin faduwar gaba babu yadda zaka ga mr ATA gabanka bai fadi ba ko kai waye kuwa saboda tsananin tsare gida , ya gansu amman yayi tamkar bai san da wasu halitta tsaye a wurin ba ,nan take kowacce ta shiga taitayinta jiki a sanyaye suka hada baki wurin gaishesa "good morning ya adam" ? sai daya dauki second goma batare daya amsa ba har sun cire rai da zai amsa suka jiyo sautin muryarsa daga can kasan makoshi "morning ! ya amsa batare daya dago ya dubesu ba ." Naunayen ajiyar zuciya maryam ta sauke dan tasan darajar sister taci yasa har ya amsa gaisuwar dan da ita kadai ta gaisheshi bazai ta'ba amsawa ba Kai tsaye hanyar kitchen suka nufa domin bawa masu aiki umarnin abinda zasuyi na birthday duk da sauran abubuwa masu wuya tun jiya a kammala ,duk abinda suke hankalin maryam na kan mr ATA bini bini ta kallesa taja tsaki acikin ranta dan hakan nan kwanaki take jin matsanancin tsanarsa a ranta dan tasha alwashin tunda bai qaunarta itama bazata qaunacesa ba mai qaunarsa ma baso ." Sai dai duk da wannan tsanar da tayi masa ta kasa dauke kwayar danunta akanshi har sanda ya mike ya isa dining table ya dauki cup din coffee dinsa baki mai shegen kyau da gani daga wata kasar yazo dashi , a natse ya sake dawowa mazauninsa ya zauna fuskar nan tashi a hade tamkar wanda ake masa wahayi da bacin rai." "tunda aka haifeta ta bude idanunta akansa bata ta'ba ganin dariyarsa ba ,kuma haka kowa yake fad'a acikin family's ,komai zaayi na dariya sai dai ya bata rai yaja tsaki tare da cewa nonsense ko rubbish ga shegen miskilanci wani lokaci halinsa na dan burgeta Irin mijin da take so kenan mai matukar kamewa da sanin ciwon kai, dan gsky ita dai nmj mai yawon surutu ko shiga abinda bai shafesa ba yawon fara'a matsala ne agurinta bata so sai dai nashi yayi yawa ko dan murmushin nan ba yayi matukar kaga fuskarsa a d'an sake to yana tare da mami ne shima wani lokacin bata gane kansa kome zatayi bazai sakar mata fuska ba ." byn ya sha kad'an ya ajiye cup ya cigaba da abinda yake har sanda hjy Zulaihat ta fito itama ta shiga kitchen yana nan zaune ya tsurawa jarida idanunshi , al'ameen daya daga cikin securities na bakin get ya shigo bakinsa dauke da sallama sannan cike da girmamawa hannunsa rike da white lailon da box blue and white ,mr ATA ya amsa sallamar aciki yana mai d'ago kansa ahankali ya zubawa al'ameen lumtsatsun idanunshi "Alameen ya qaraso gabansa kad'an ya rusuna "barka da safiya yalla'bai "mr ATA ya gyada masa kai kawai batare daya amsa ba . " amm ga sako wai inji Ana's" mr ATA ya d'an kankace lumtsatsun idanushi yana bukatar qarin bayani daga bakin al'ameen,alameen yayi sauri yace "sakon hjy maryam ne ita yace abawa "shiru mr ATA yayi yana kallonsa da sakon hannunsa kamar bazai ce komai ba sai kuma ya nuna masa kan table din dake gabansa yana jan tsaki a fili al'ameen ya ajiye ya juya ya fice da sauri ya kama gabansa." Maryam dake kitchen wacce daman idanunta da hankalinta yana parlour ta shiga tashin hankali mara misaltuwa, da sauri ta qarasa inda nana take tsaye "sister na shiga uku nah" ta fada tana riko hannun nana cikin nata "me kuma ya faru allah ya rabamu da shiga uku sister ?"kalli can ki gani sister ta nuna mata parlour'n "me ya faru ? "sakon Ana's ne daman ya turo min text message zai zo ya kawo min gift gsky al'ameen bai kyauta min ba maimakon ya kirani ya bani a hannuna tana magana idanunta na cikowa da ruwan hawaye hjy zulaiheart ta juyo a natse ta dubesu "ku kuma lafiya kuka tsaya kuka hade kai wa ya mutu ? a matukar firgice suka juyo suna dubanta maryam na 'kokarin dauke hawayenta a d'an rikice suka girgiza mata kai alamun "babu kowa " to meke faruwa daku ?babu komai suka sake hada baki "to allah yasa babu komai din amman ni dai na fahimce da komai tsayawa sukai suka qasa cigaba da aiki ." shi kuwa Mr ATA naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske yana shan yaji kamar yadda ya saba sosai ya tsurawa box din dake dauke da sunan maryam da kallamar happy birthday yana lissafa abubuwa dayawa acikin ransa "wai gashi inji Ana's sakon hjy maryam "ya maimaita abinda al'ameen ya fad'a , kafin daga baya ya kwabe baki tare da kai hannu ya bude box din ,da wani hadadden freme idanunshi ya soma cin karo mai matukar kyau da d'aukar hankali an rubuta sunanta da larabci da kuma hausa ." "shiru yayi yana jin wani iri a gabadaya ilahirin jikinsa na tsantsar bakinciki ,a hankali ya dinga kallon abubuwan dake cikin box din mug, pray mate ,Casbaha alqurani da wani qaramin greating card na sokon taya murnar birthday sai kuma qaramin yellow takarda mai dauke da kalaman soyayya "ya dauka yana tabe baki kamar yaga wani mugun abu ya soma karantawa ." hjy Zulaihat ta fito daga kitchen tare da masu aiki mutun biyu zuwa dining maryam da auta suka biyo bayanta jikinsu duk a sanyaye dan basu san abinda zai faru ba "na shiga ukuna sister ki taimakeni karanta sakon fa yake " maryam ta sake fadan hk cikin tsananin tsoro "to sai me idan ya karanta ? " wallahi kin cika abun ban haushi kamarki dan an aiko miki da sako zai zama abun tashin hankali? Ke yarinya ce karki manta master's gareki kuma dole zakiyi aure "ni sister rabani da wani master's na yarda kowa ya karanta sakon amman ban dashi "bangane banda shi ba ? shi waye naki da zakice ban dashi ? tayi mata tmbyr tana kallonta "haba sister ya kike yi kamar baki san abinda nake nufi ba kema kinsan ba haka nake ba ni ba matsoraciya bace amman wallahi shi mugun tsoronsa nake ji ,sannan kinsan halinsa da disgi ." "Dana san halinsa fa ? shi zai auremu?Ko kuwa munyita zama haka kenan bazamuyi aure ba ?"Kinga idan zaki cire tsoro ki cire dan ni wallahi ina samun miji aurena zanyi na barki bazan zauna ba aiki ba aure ba dole zanyi daya ta qarasa mgnr tana jan tsaki maryam tace "banza kamar kema ba tsoronsa kike ba "ina jin tsoronsa amman ban kai ki ba dan dani anas da abbas suke mutuwar só da son aure da tunin ina gidan daya daga cikinsu "ta fad'a tare da qarasawa wurin Hjy Zulai ta rabe a gefenta." daga can inda hjy zulai take tsaye ta hangosa ya baje kayan sannan yayi zurfin cikin karata yellow takarda "Lafiya adam !? ta furta tana cigaba da dubansa ,a tsanake ya mike tsaye fuskarsa a yatsine ya nufo wurinta yana cewa "wani haukan shirme nake karantawa ".maryam tayi wuf ta koma kitchen da sauri tana daura hannuwnta duka bisa kanta itama auta tayi nesa da hjy zulaihat "haukan shirme kuma adam ? hjy Zulaihat ta maimaita abinda ya fad'a "yes sweetheart wannan bashi da maraba da haukan shirme ,wai nmj né zai zauna yana wannan haukan abun kunya kawai "yayi maganar yana yatsuna face dinsa kamar yaga wani mummunar abu "wannan ai iskanci ne ba soyayya ba ya sake mgn yana jan dogon tsaki ." hjy Zulaihat tayi shiru tana duban mr ATA cikin tsananin tausayawa kanta dashi kanshi ,"bata san ranar da zai canza wannan mummunar halin nasa ba ,bata san ranar da zai bude baki yace ga matar da yake so ya aura ba ko fad'awa soyayya "duba ki gani sweetheart ya mika mata letter yana sake jan tsaki kamar wanda akayiwa dole sai ya karanta." Jiki a matukar sanyaye mami ta karbi letter daga hannunsa tana dubawa gabadaya bata ga inda zantuttukan dake rubuce sukai kama da haukan soyayya ba ,illa ma maganar soyayyar mai sanyaya zuciya da kwantar da hankalin abokin rayuwa , byn ta gama karantawa ta kalli nana hauwa'u fuskarta dauke da tmby, kai ta gyada mata "mami sakon maryam ne "wani mugun kallo ya wurga mata wanda ya hargitsa hantar cikinta da mugun sauri ta bace masa da gani ." sai lokacin Hjy Zulaiheart ta fahimce abinda yasa taga hankalinsu a tashe a kitchen ,numfashi ta fesar tana kallon bayansa dan tuni ya juya ya koma inda kayan suke tare da rike kugunsa ,qarara ake iya ganin bacin ransa bancin alqur'ani dake cikin kayan daya banka masu wuta gabadaya ya kona dan takaici ." wannan shine soyayya ta gsky da gsky yaji sautin muryar mahaifiyarsa tana magana tana tahowa zuwa in da yake "duk abinda ka gani anan kyautatawa ce ta soyayya tare da nuna kulawa "okay yanzu ta haka ne zai nuna emotiona dinsa ?kai gsky dai wasu mazan jakai ne, ya fad'a yana jan tsaki tare da nufar hanyar step har yayi taku biyu yaji mahaifiyarsa ta kira sunansa "adam !." cak ya tsaya tare da juyowa ya tsura mata kwayar idanunshi da suke cike da bakinciki" zaka iya kin yarda da wannan kalaman amman at least kayi respect din emotion din wani ,karka wulakanta soyayyar wani domin bakasan yadda taka soyayyar zata kasance ba ,idan kai baka raayin soyayya karka ji haushin masuyin soyayya domin soyayya maganar Allah ce ."shiru yayi lokaci daya emotion din mafarkinsa ya shiga kai kawo a gabadaya ilahirin jikinsa ,mafarkin ma ya daukesa da mahimanci fiyye da komai arayuwarsa wannan tunanin yasa ya bude bakinsa da kyar "alright sweetheart amman yana da kyau idan har soyayyar gskiya ce ya turo magabatansa "ya fadi haka ne saboda ya gaji da ganin fuskar maryam din acikin gidan dan bai san dalilin dayasa ta tare masu a gida ba ,a natse ya juya ya cigaba da taka step fuskar yarinyar mafarkinsa na yawo acikin kwayar idanunshi yayinda mami tabi shi da kallon tausayi tana girgiza kai ." Sallamar abida né yasa mami ta dauke idanunta daga kallon hanyar da mr ATA ya bi ta maida bakin kofa tsaye take hannunta rike da hannun yesmin sanye cikin doguwar riga yar saudiya mai tsansi sosai cike da sakin fuska mami ta amsa sallamarta tana mata sannu da zuwa "yauwa mami fatan kin tashi lfy ?" ta fada tana zama cikin daya daga cikin kujerun falon .mami ta qaraso ta zauna kusa daita tana kamo hannun yesmin a lokacin mrym da nana hauwa'u sun gama tattara kayan ." a mutunce suka gaishe da aunty abida sannan suka bar wurin zuwa dakinsu nana hauwa'u na cewa "ai kin dai ji abinda ya Adam yace ?me yace sister ? ban gane me yace ba yanzu ke bakiji yace idan soyayyar gaskiya anas yake miki ba ya turo magabantasa ba ?"oh ! abinda ya fad'a kenan ai gabadaya rudewar da nayi bai sa naji komai ba?ta numfasa sannan ta cigaba da magana "wannan ai ba matsalarsa bace idan naga dama na zauna har karshen rayuwata babu aure bai shafesa ba ,yadda bai son ana shiga lamarin rayuwarsa bai dace shima yana shiga rayuwar mutun ba ". oh! ai bansan wuyanki ya isa yanka haka ba amman zo muje ki fad'a masa kar ya sake shiga rayuwarki" nana hauwa'u ta riko tsintsiyar hannunta ta nufi step din da zai kai mutun samansa ,nan take maryam ta zaro idanuwa waje "haba sister kar muyi haka dake mana wannan ai maganarmu ce " a'a babu wani maganarmu ce Ke dai muje kinga daga yau zai kiyaye ,maryam ta fixge hannunta da karfi sauran kadan kwalin hannunta ya subuce "haba sister ! haba sister Ko gskiya? shegiyar masoraciya kawai iskancinki baya qarewa akan kowa sai akanmu yake qarewa dasu anas."maryam ta kwashe da dariya "ai kema Kinsan oga nada ogansa, ina ni ina tarar aradu da fad'in kai ai sai ya tarwatsani , barni na tsira da raina da lafiyata kar ya rage min sadaki suna tafiya suna magana kuma duk akan mr ATA ne ." shiru aunty abida tana zaune har kusan mintuna shabiyar sannan ta dubi mami da kyau "wai ina ATA ne nasan yau asabar yana gida dan duk kwanakin nan bana ganin shigarsa da fitarsa ?"kullum sai yesmin ta tmbyeni shi shiyasa ma yau nace bari na kawota ta gaishesa tunda weekend ce ta fad'a tana murmushi ,mami ta gyara zamanta tana kallon fuskar yesmin "Adam yana nan galau yanzu nan ma ya hau sama ,kwana biyu da bakya ganin shigarsa da fitarsa yanayin aiki ne kwanakin nan duk bai dawo wa gida da wuri haka zalika da wuri yake fita amman yau kam yana gida bana tunanin ma zai fita dan ma ya dauko rigima ai da kin samesa a kasa . "Rigima kuma mami kamar wani qaramin yaro ?ta fad'a tana murmushin farinciki". "wallahi fa nan mami ta zayyane mata abinda ya faru, dariya aunty abida tayi sosai "lallai kam rigima amman ai wani lokacin akan gsky yake abubuwansa ni wallahi yana matukar burgeni yadda yake gudanar da rayuwarsa babu ruwansa da kowa sannan baya daukar raini kamar su abban yesmin koda yaushe hakoransu a bude Kmr masu tallar close up ." "ikon allah banda abunki abida me zaayi da miskilili? ai gara masu farar nan akan masu nunkufurci da miskilanci sun dan jima suna hira sannan ta mike "to mami ni zan wuce daman abinda ya shigo dani kenan sai anjima . "shikenan abida na gode sosai da kulawa amman ki bar yesmin ki aiko mata da sabbin kayanta zuwa anjima zaa kawo hanan domin gabatar da birthday dinta "aunty abida tai murmushi "to ai shikenan mami zan aiko mata da...." shiru tayi sakamakon jiyo sautin muryarsa yana saukowa daga matattakala cike da izza da shan kamshi hannunwansa duka zube cikin aljihunsa wandonsa, yayinda iPod Ke manne da kunnensa yana amsa waya yesmin na ganinsa ta kwasa da gudu tana kiran sunansa "uncle AD! Hannunwansa duka yayi saurin zare wa daga cikin aljihun wondonsa ya dauketa yayi sama daita na second biyu sannan ya riketa a gefen jikinsa yana shafa fuskarta sai dai ko kadan babu alamun annuri akan a fuskarsa." qarasa saukowa yayi ya wuce aunty abida da mami ya daurata akan wani dogon stood mai tsawo yana cigaba da wayarsa murmushi abida tayi najin dadi domin duk cikin jikiokin gidan baya daukar kowa sai yesmin kuma ta fahimci yana matukar qaunar yarinyar sosai hakan yasa itama take mugun qaunarsa fiyye da qaunar burinsu akansa." a hankali ta qarasa inda yake tsaye "AD ..! ta kira sunansa " baki ga abinda nake yi bane ?ya fad'a a matukar hassale yana wasa da gashin yesmin."Taja bakinta tai shiru na second biyu sannan ta sake yunkurin sake yi masa magana ganin bakinsa bai motsi " uhm daman zan wuce ne ma nace mu gai..." bata kai ga qarasa abinda zata fad'a ba cak taga ya dauki yesmin ya sabata a kafad'arsa ya haura samansa a hankali ta juyo tana duban bayansa Yadda yake tafiya ma kawai duniya ne gabadayansa shi din mafarkin kowace mace dake numfashi a duniya ne shiyasa duk runtsi duk wuya sai burinsu ya cika akansa ." Yesmin ta sakar wa mamanta murmushi tare dago mata hannu tana mata bye bye "abida Kiyi hakuri dan allah nasan Kinsan halin danuwanki ba tun yau ba "no mami ki daina bani hakuri ai idan da sabo na saba da halinsa ya zanyi da halin danuwana ?ni gabadaya abubuwansa basa damuna burgeni ma yake ."Masha allah haka ake so duk wani mutumin kirki ya kasance allah ya qara mana hakuri da zaman lafiya da junanmu "Ameen ta amsa ta juya ta fice daga part din hjy zulai ." "Adam na bani matukar kunya mami ta fad'a a matukar fusace adaidai lokacin da mrym da nana hauwa'u suka dawo parlour'n sosai suna tmbyr ta "kunya kuma mami ?eh mana ku duba kuga yadda abida ta damu da shi amman shi bashi da abun wulakantawa kamarta ,ni na lura ma duk yafi tsanar ta akan kowa acikin family's din nan amman dan iskanci ya iya dauke mata diya ya wuce daita sama ." ta fad'a cike da takaici. "ta nan bangaren ya Adam fa yana da gaskiya itama banda abunta taya tana matar aure zata dinga wani shishige masa ".?"Uhm auta ai ita ba da wata manufa take yin haka ba tana yi saboda yanuwantaka ne "kai mami kefa bakya fahimta ,wallahi munafuci ce da bakinciki ne taf acikin zuciyar wannan matar da kike kallo amman kin kasa ganewa yanzu da kin qare mata kallo murmushin yake tayi, waya san abinda ke zuciyarta "babu komai sai alkhairi ku dinga yiwa mutane fatan alkhairi ". ******* Bayan kamar awa biyu da wasu mintuna ya fito sanye cikin wasu kananan kaya riga Orenge da white jeans kana ganin shigar kasan fita zai yi ,lokacin parlour'n Hjy Zulai ya soma cika da kawayen su maryam da yan'uwa sai dai parlour'n babu wani hayaniya a hankali suke komai sanin boss na gida da zarar zasu daga murya, sai maryam ta tsaidasu suna ganinsa kowannensu ya shiga hankalinsa tamkar basa da numfashi ." yaja tsaki yana janye jikinsa dan kar jikinsa ya ta'ba na wata acikinsu ,ya nufi kofar fita nana hauwa'u da mrym suka hada ido tare da dagawa juna gira alamun jin dadi "nuzla tayi tsalle" yeeee ya Adam ya fita zamu sakata mu wala "tayi mgnr tmkr wata qaramar yarinya "ke dai bari nuzla wallahi tun dazu a firgice muke nida maryam ,wallahi gbdy bama cikin natsuwar mu tun dazu addua nake acikin zuciyata allah ya kawo dalilin da zaisa ya fita ya bar gidan gbdy ko ma sakata mu wala sai gashi allah ya amsa adduata, gashi ma ya fito ya ganmu dayawa bai ce komai ba wallahi baqaramin dadi naji ba inji cewar nana hauwa'u ." Maryam tai juyi cikin doguwar rigar dake sanye ajikinta sannan ta tsaida kananun danunta akan nana hauwa'u "sister wannan yayan naki mai sufar zaki akwai shi da mugun iyayin tsiya sai dai fa yayi kyau sosai exactly irin mijin da nake muradin aure kenan amman samun irinsu da matukar wahala , Ina ma zan samu yadda yayi kyau din nan ace Ana's ne da yau mu dauki hotuna masu yawa mu daura a social media nasan da ba qaramin comments da like's zan samu ba." tunda ta fara magana ya dawo bata sani ba yana tsaye a bakin kofa sai faman zuba take "burin kowace mace a duniya ta samu miji kamarsa amman samun irinsu da wahala amman babu komai mayi hidima wa Allah mu samu a aljanna idan muna da rabo " "Kun san wani abu dake bani driya dashi ? duk sukai shiru babu wacce tayi tari "abu kadan zai hade fuska ya kalli mutun ya disga mutun da kalmar nonsense , crazy girl " ta fad'a tana karairaya cak ta tsaya tana duban wadan da ke tsaye a gabanta ga mamakinta taga dukkaninsu babu wanda yayi dry Kmr yadda suka saba a duk sanda wani yayi irin maganarsa ." a hankali ta juya bayanta cike da tsananin faduwar gaba aiko idanunta suka sauka akanshi yana mata wani irin kallo mai dauke da yawon tsanar da yayi mata ,da sauri ta zaro idanuwa waje tana kallonsa kmr a mafarki, ta lumshe idanunta na second daya ta bude taga dai tabbas shi din ne tsaye agabanta ,ta dan juya bayanta tana kallonsu Kmr zatai kuka." Gbdy jikinta ya kama rawa a hankali ta sakê juyowa ta fuskancesa ta hade hannuwanta duka wuri daya tare da yin kasa har ta kai kasa muryarta na rawa "am very very so.." sorry " . shiru yayi yana qare mata kallo tsab sanye take ckin doguwar rigar wanda hannunta daya long sleeve ne dayan kuma hamless gabday an canza mata kamani ta hanyar yi mata make up ga gashin kai tayi fix ya sauko har gadon bayanta abinda yafi tsana kenan daga mace too much of kwaliya da qarin gashi da farce ita kuma duk ta kware wurin yinsu "ita fa a ganinta tayi kyau da wannan shigar da kwaliyar da tai ?ya tmbayi kansa yana jan tsaki dan a idanunshi muni tayi masa barin ma rashin tsawon da Allah yayi mata ,shi kam yayi imani banci farin fatan da allah yayi mata da babu shegen nmj da zata dauki hankalinsa har ma ya tsaya bata lokacinsa wajen haukan shirme akanta ". "kusan second goma ya dauka yana kallonta yana hukuntata da idanunshi kafin daga baya ya bude bakinsa Kmr baya son yin mgn " maid your business duk abinda zaki yi karki sake kuskure ambaton sunana cikin shirmenki me nace ? ya fad'a yana zaro mata ido "Kar...kar !! na sake ambaton sunanka kayi hakuri wannan ma kusku.....you're very stupid dake da kuskuren , daman kin saba this is not your first time koni sa,an wasanki ne ? da sauri ta girgiza masa kai ya gyara tsayuwarsa " ki dinga abu kamar wata mental sam sam baki da natsuwa crazy girl kawai ki godewa allah akwai abinda zanyi mai mahimanci dana tsaya naci ubanki guntuwar banza kawai ." ya fad'a yana sa kai ya hau sama ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya aranta tace "oh my god you save me for the first time ,byn kmr second biyar ya sauko ya fice gbdy daga gidan . Bayan fitarsa cikin bacin rai tace "ko kun tayani jin abinda ya fad'a? suka kwashe da wata mahaukaciyar dariya "wai kece mental crazy girl mara natsuwa a karshe wai guntuwar banza wallahi ni duk shi yafi bani dariya wai guntuwar banza cewar nuzla ta fad'a tana tafa hannu tana dariya "see me see trouble shi fa idan ba zagi ba babu abinda ya iya arayuwarsa dan wulakanci ma har da zagin halittar Allah cewar diyana "kunga karku qara mata bakinciki byn kunsan yau ranar farinciki ne gareta nana hauwa'u tayi mgnr tana mikar da maryam tsaye dan tunda ta durkushe kasa bata iya ta mike ba tsabar tsoro ." Byn ta mike tsaye bisa kafafunta ta kallesu daya byn daya tana maka masu harara mai kunshe da bakinciki "gsky gbdy baku kyauta min ba, kuka barni ina ta faman zuba aka rasa wanda zai min alamar nayi shiru acikinku daman burinku yaci min mutunci kuyi dariya ko? Kema idan zakiyi magana next time ki dinga kallon kofar shigowa ba baya zaki bawa kofa ba in case inji cewar nuzla ,asra tace "au ke nan yanzu haushi kika ji da ba ki godewa allah ba kamar yadda yace dan da yanzu ba wannan labarin kike ba "na so oooo I thank god for saving me." Bayan wani lokaci gidan mami ya cika da ya'yanta da jikokinta da wasu daga cikin jama'ar estate din parlour'n ya hargitse da hayaniyar mutane anci an sha anyi rawa hanan ta yanka cake haka ma maryam tare da daukar hotuna da vedios mutun biyu ne kawai acikin yammatan family's da basa cikin hotunan marigayiya mubina da sultana wacce Ke matakin karshe a jamiar cairo ." su maryam abun nema ya samu domin kuwa duk hotuna da sukai babu bata lokaci take daurawa a social media "nuzla ta samu wuri ta zauna shiru idanunta na cikowa da ruwan hawaye sakamakon tuno marigayiya mubina ,maryam ce ta lura da yanayinta ya sauya dan haka ta qaraso gareta ta zauna akan hannun kujerar da take zaune tana tmbyrta "Lafiya nuzla kika zauna shiru haka ?numfashi ta sauke tana furta sunan "mubina...!" tun kafin ta rufe baki sai hawaye sharrr sharr!! sun zubo Kan kuncinta dan haka ta kasa qarasa maganarta , maryam ta tsuke baki tana riko hannunta cikin nata " nuzla ki daina kuka haka addua ya kamata kiyi mata alokacin da kika tunota ,wallahi koni sai data fado min arai kuma nasan gabadayanmu babu wanda bai tunata ba domin mubina ta shiga ranmu fiyye da komai ta fad'a tana goge mata hawaye "ki bar kuka haka kada sauran su fahimta kisa hankalinsu ya tashi ,wanda ya mutu babu abinda yafi bukata kamar addua kuma muna mata babu ranar da zatazo ta wuce banyiwa mubina addua ba allah ya jaddada rahma gareta ta fad'a tana mikar da nuzla tsaye suka shigo cikin sauran yan'uwa nuzla kam baa qarasa gudanar da birthday party daita ba ta wuce ." ****** Byn wata shida Sanye yake cikin kananun kaya jeans da riga t shirt tsadaddu product din American yana tsaye a haraban katanfarin estate dinsu tare da hisham hannuwansa duka zube cikin aljihun wandonsa , kallo daya zaka masa ka fahimci ransa a 'bace yake dan fuskar nan tashi babu alamun rahma sakamakon abinda ke dawainiyya da rayuwarsa , uwa Uba sweetheart dinsa dake sake hargitsa masa lissafi da batun auren data bijiro masa da yarinyar daya tsani gani a rayuwarsa dan idan yana qaunar mutuwarsa to yana qaunar yarinyar ."Suna nan tsaye hisham nayi masa magana akan sakonnin daya samu akan kasuwancinsu amman shi sam hankalinsa da natsuwar basa garesa , yana nazarin yadda rayuwa ke tangaliliya dashi da Inda zai ajiye akalar rayuwarsa, da rayuwar da mahaifiyarsa da yan'uwansa suke son yayi a yanzu ." a hankali hisham ya matsa kadan daga gefensa domin amsa kira dan yasan halinsa baya son qarar waya , ringing din wayar hisham daya fara ne ya dawo dashi haiyacinsa ya fesar da iska mai zafi daga bakinsa tare da kai Kyawawan idanunshi saitin gidansu ,maryam da muhd bello babban amininsa ya gani suna 'kokarin fitowa daga cikin gidansu wani irin mugun haushi ya kamashi zuciyarsa ta dinga zafi da tuttukin bakinciki bangaren maryam ganin in da yake tsaye suka nufa yasa bugawar da qirjinta yake ya qaru fiyye da kaida ." Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page3 ......da wani irin sauri mr ATA yayi saurin d'auke kwayar idanunshi akansu yana juya baya tare da jin wani zafi mai tattare da bakin ciki, gabadaya ya rasa me Ke masa dadi arayuwarsa a halin yanzu babu fuskar daya tsani gani kamar fuskarta ."daga Inda maryam take bata sake yunkurin qara taku daya ba ta cigaba da tsayuwa a waje daya qirjinta na bugawa da matsanancin karfin gaske sbd tsananin tsoronsa ."wannan dalili yasa dole shima muhd bello ya tsaya anan suka qarasa maganarsu ta juya da sauri ta koma ciki ranta duk babu dadi kallonta nana hauwa'u tayi tace " ba dai har kin dawo ba ? ta fad'a haka ne sanin da tayi duk lokacin da suka ke'be da ya muhd bello suna daukar lokaci suna tautaunawa dan jininsu ya had'u sosai dashi ." maryam bata ce mata uffan ba tsabar bakinciki dake kunshe acikin zuciyarta nana hauwa'u ta cigaba da magana tana dubanta a tsanake "halan ya adam na waje ne naga kin shigo fuskarki wani iri ? ta'be lip's dinta tayi tana cewa " ai kema kinsani idan ba ganinsa ba me zai sa fuskata tayi haka ta sauke naunayen ajiyar zuciya " sister na rasa dalilin wannan tsana da ya adam yayi min ,wannan abu na matukar ci min rai ina jin kamar na tattara na bar gidan nan na huta da ganin irin kallon tsanar da yake min kamar ni kadai ce acikin gidan nan ? " tsana kamar ya kashe ni." "haba haba !! sister dan me zaki fadi haka?" ai ba ke kadai yakewa haka ba , ki daukeni misali ma kawai ya isa ki kwantar da hankalinki , ba ke kadai ya adam yakewa haka ba shifa tsanarsa kowa yake wa "maryam ta sake tabe lip's dinta "kowa yake wa amman wallahi nawa yafi na kowa nifa ko kallona baya qaunar yayi na rasa me na tsare masa arayuwa kamar fa ya kasheni haka nake gani acikin kwayar idanunshi nana hauwa'u tai murmushi kawai "kisan ma abinda ya qara kona min rai ne ?nana hauwa ta girgiza mata kai "alamun a'a " wai yana hangomu nida ya muhd bello mutumin nan ya juya mana baya da sauri kamar yaga wani mugun abu ,wallahi bakiji yadda na muzanta ba gabadaya kasa cigaba da tafiya nayi " nana hauwa'u ta kamota zuwa Kan kujerar da take zaune ta zaunar daita tana murmushi a hankali ta shiga kwantar mata da hankali tana kawo mata misalai iri iri dan bata son abinda zai sa maryam ta bar gidan dan ko babu komai abubuwanta na social media na sakata nishadi shiru kawai maryam tayi tana sauraronta ." muhd bello ya k'araso Inda Mr ATA yake tsaye ya Kai hannunsa d'aya ya dafa kafad'arsa ya juyo dashi a hankali ya tsura masa idanunshi fuskarsa kwance da murnushi yace "why ATA ? "me yasa kake quntatawa rayuwarka ?"me maryam ta rasa ? "me yasa bazaka bi zabin mahaifiyarka da yan'uwanka ba ? ya lumshe lumtsatsun idanunshi yana furzar da iska me zafi daga bakinsa "kasan komai akaina m.b tun daga farkon rayuwata har zuwa yanzu da nake tsaye a gabanka babu abinda baka sani ba ..." Na sani ATA ! ya fad'a yana sake matsoshi sosai " Amman at least ka duba lamarin mahaifiyarka da yan'uwanka sun dauki tsawon lokaci da baka dama amman shiru babu wani bayani amman yanzu tunda suna sonka da maryam ka amince masu ka sota ." shiru mr ATA yayi yana masa wani irin kallon up and down "ka amince masu ka sota " kwalkwa luwarsa ta maimaita masa abinda ya fad'a yanzu kafin a hankali ya kai hannunsa daidai saitin zuciyarsa da yaji bugawarsa yana qaruwa sakamakon furucin muhd bello ,bai an kara ba yaji sautin muryar muhd bello ya cigaba da magana " itama maryam din bata san da maganar ba a yanayin yadda mami ke maganar zaka fahimci hukuncinta ne ta yanke akanka kuma ina da tabbacin ko tasani bazata ki ba, biyyawa kawai zatayi ta aureka koda ranta bai so "shawarata ka amince da aurenta yarinyar nan tana da natsuwa da hankali sosai bazata baka matsala ba ,sannan tana da ilimi tana da kirki daidai nata uwa Uba jininku daya daita abinda yayi ka shi yayita, shi abinda kake gani acikin rayuwarka ba lallai ya zamo gaskiya ba dan ba kowani mafar......" "Stop! "Mb don't don't !! talk anything rubbish okay ya fada a fusace yana sake fuskantarshi sosai ya rungume duka hannuwansa a faffadan qirjinsa ido cikin Ido suke kallon juna tmkr ranar suka fara ganin juna zuciyar mr ATA na wani irin tuttukin bakinciki da zafi muryarsa a zafafe ya cigaba da magana "ko kai ne Allah da zaka fad'a min haka ?" well I don't care about all what you said dan nasan da Allah na dogara ba da kai ba kuma nayi Imani bazai wuftar da lamarina ba zai cika min burina." "Na sani Allah ba zai wuftar da lamarinka ba amman dole sai kabi umarnin mahaifiyarka tukun allah zai duba lamarinka domin Allah ( swa) yace waqada rabuka alla tahbudu ila iyahu wabil walidaini ihsan sannan manzon allah (saw )sai daya ambaci abi uwa har sau uku kafin uba kaga tunda har kasan allah keyin komai to ya kamata kasa aranka kamar anyi wannan auren an gama da izinin Allah har ma na fara tsinkayo sautin muryoyinku cikin farinciki kai har ma ka durka mata ciki yan shida tana takawa da kyar kana rike da jakarta kana mata sannu ya karasa maganar cike da zolaya yana murnushin mugunta tare da dukan kafad'arsa wanda hakan yasa mr ATA sake d'aure fuskarsa sosai yana zabga masa katuwar harara ." suna cikin wannan halin hisham dake tsaye gefensu yana waya ya gama ya tura wayarsa cikin aljihunsa ya qaraso yana mikawa muhd bello hannu shima ya mika masa nasa hannun yana cewa tun dazu nake allah allah ka gama wayar kazo mu taru mu taya mami yakin karshe "akan wa kenan ?"akan wannan stupid din d'an nata mana mai shegen taurin kai kamar dutse "nan ya shiga zayyane masa halin da'ake ciki hisham ya gyada kai yana cewa "gsky mami ta yanke hukunci mai kyau sai dai muce allah ya tayaka rikon amanar maryam , dan allah friend ka amince karka zubawa mami kasa a idanunta bugu da kari aure shine cikar kimar mutun duk inda zaka shiga matsawar baka da aure wallahi kimar ka raguwa take , nima nan da kagani kokarin shawo kan nuzla nake kaga idan allah ya taimakeni ta amince kawai sai a hada bikinmu tare." Mr ATA yaja dogon tsaki ya zabga masa harara Kmr kwayar idanunshi zasuyo waje "naga alamar kai ma baka da hankali kamar wannan "ya fada tare da juya yana kiran all you of are very stupid ." Ahankali mr ATA yake daga kafafunsa batare da ya sake yin wata magana ba dan idan yace zai cigaba da magana sai dai d'ura masu zagi , yana tafiya yana sake jin bacin rai duk wanda ya gansa yasan yana cikin damuwa ,dan haka masu kula da lafiyarsa duk suka shiga hankalinsu kowa na taka tsantsa ,da sauri escort dinsa suka biyosa cikin kamewa da taka tsantsan kiyaye aikinsu , dan duk lokacin da ransa yake a bace yafi dakatar da mutun daga aiki ." muhd bello ya biyosa suka jero tare zuwa Inda akayi parking din motocinsa escort suna kokarin bude musu murfin mota yayinda hisham ya juya ya nufi gidansu ."mr ATA na qoqrin shiga mota Kira ya shigo wayarsa ya tsaya cak hade da tura hannunsa cikin aljihunsa ya ciro wayar yana dubawa sunan aunty shahida ya gani yana yawo akan screen din wayar ya furzar da iska me zafi sannan ya danna koren maddanin ya manna wayar a kunnensa yayi shiru yana sauraronta " can bangaren aunty shahida ta fara magana saboda tasan ba magana zai yi ba "kana Ina yanzu ? shiru ya cigaba da yi yana ciza lips dinsa na kasa sai data sake maimatawa sannan ya bude bakinsa da kyar "Ina shirin barin gida yanzu "to karka kuskura ka bar gida batare da kabawa mami hakuri ba "naji zan dawo anjima da daddare dan tayi fushi sosai yanzu yayi maganar yana runtse idanunshi zuciyarsa na suya "no kaje yanzu saboda nasan ranta yayi mugun 'baci shiyasa kaji nace haka Kuma bana son tayi fushi da kai adam kasan mami na matukar hakuri damu most especially kai tana hakuri da kawaici akan komai, wannan ma ka kaita makura ne "to ni yaya kuke son nayi da rayuwata ne ? "hakuri sannan kabi umarninta ta fada atakaice "shikenan haka ni rayuwata zata qare cikin kunci Kunki ku tsaya ku fahimceni ? "Wani fahimtarka Kuma zamu tsaya yi tunda an baka lokaci Kaki kayi komai akai ?"fatanmu kayiwa mahaifiyarmu biyayya ka rike mana amanar maryam karka cutar daita sannan na tabbatar maka zakaji dadin maryam dan .."Kinga shahida karki dameni da wani amana ko zan ji dadinta kar in cutar daita "yayi saurin katseta ta hanyar fadar haka " kanku kawai kuke dubawa baka duba halin da zan shiga akan auren nan haka kawai zaku cutar dani akan wani auren baza "shahida kai tsaye ko adam ? "ta tambayesa numfashi ya sauke bai ce komai ba " kiran sunana yau babu ladabi ba komai ba ?"share wannan maganar raina ne ya baci zan zo office din na sameki idan na gama da sweetheart mu tautauna wasu abubuwa daya shafeni ," "karka sake Adam kazo min da wani tsari ko rashin kunya dan ba zan tsaya naji raayinka ba sannan kasani bazan dauki raini ba ,dan iskanci tun yaushe ake fama da kai ? shekara biyar kenan ana fama da kai ka fito da mata Kaki kullum ka zaunar da mutane kana masu karyar baka samu tru love ba ,haka kawai kanata batawa kanka lokaci abanza,tukun nama kana wannna iskanci na ji da kai da fadin rai yaushe zaka samu tru love ."?" kai wace shegiyar ce ma zata dauki wannan wulakanci da ji da Kan da kake fama dashi ? ai daman karshenka kenan ayi maka auren dole kaje can ka karata kowa ya huta dan .."bai tsaya Jin abinda zata sake cewa ba ya sauke naunayen ajiyar zuciyar yay disconnecting din Kiran Yana adduar samu sausauci daga gurin mahaifiyarsa ." ya maida wayar aljihunsa ya koma cikin gidansu a Inda ya bar sweetheart dinsa anan ya isketa zaune gefenta maryam ce ke matsa mata kafafu suna hira cike da tsantsar biyyaya kyakkyawar datjijuwa me tsananin kyau da nagarta da sanin ya kamata da son zaman lafiya da lumana ta d'ago a natse idanunta sanye da farin glass wanda da gani na Kara lafiyar idanu ne ta zuba masa Ido tana mai tsananin qaunar d'anta ."kamshin dadd'adan turarensa (Reed ) mai sanyi da sanyaya zuciya tare da Kashi jiki da sace zuciyar duk wanda sautsayi yasa ya shaka yasa maryam ta fahimci ya sake dawowa falon ,a hankali ta bar abinda take ta dago idanunta dan tabbatarwa kanta shi din ne ko kuwa , ai ganinsa tsaye kikam kamar wani jami'in tsaro ba dan kasuwa ba yasa nan take qirjinta ya shiga dokawar daya Saba a duk sanda zata d'aura idanunta akanshi sannan ta dinga kokuwa da numfashinta kenan har sanda zai bar gurin ." Ahankali idanunsu ya tsarke cikin juna wani irin kallon banza me hade da harara ya sakar mata babu shiri ta zare hannunta daga kafafun Mami ta mike tayi dakinsu ,Koda ta shiga dakin ma kasa samun natsuwar zuciya tayi ta rasa dalilin da yasa take tsatsanin Jin tsoronsa haka da Jin faduwar gaba akansa sannan ta rasa dalilin dayasa ya tsaneta haka koda bai fada mata ba tasan baya qaunarta dan tana ganin tsanarta acikin kwayar idanunshi ." bayi ta bud'e ta shiga qirjinta na dokawa ta kulle kanta dan ganinta shine Inda yafi mata saukin zama ta rarrashi zuciyarta shiru tana tunanin ta nesanta kanta dashi zai samammata kwancinyar hankali, sai dai ina hakan ma ba mai yuwa bane domin mami bazata yarda ba wani sabon tashin hankali ya caki zuciyarta nan take faduwar da gabanta ke yi ya qaru ya wuce misali hattar cikinta sai kadawa take tayi Imani a lokacin da tana da ciki tsab zai fice ya barta ." cike da ladabi da biyayya ya dan saki rashin kadan ya k'araso ya durkusa a gaban mahaifiyarsa kmr zai mata sujjada "Sweetheart! ya kira sunanta bata amsa ba ta cigaba da kallonsa "kiyiwa Allah kiyi hakuri ki bar maganar nan a tsakankanimu karki bayyanata bare kowa ya sani ita kanta yarinyar idan ta sani sannan taji rashin amincewata zataji babu dadi a ranta ," shiru hjy zulaiheart tayi taki cewa uffun har sanda ya dasa Aya " Allah ya huci zuciayrki hjy sweetheart dan nasan zuciyarki na tattare da fushina amman kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi " yana gama fadar haka yaja bakinsa ya sake yin shiru yana sauke numfashi ,hjy zulaiheart ta kafeshi da idanunta sosai ta cigaba da kallonsa taso ya fadi fiyye da abinda ya fad'a idan ma da hali yace "ya amince da umarninta amman sai sa'banin haka yake furtawa ,ya tsaya a iya hakuri kawai da kin amincewa ."ta rasa wace irin zuciya ga Adam sam idan ya kafe akan abu ya kafe kenan is very hard ya canza ra'ayinsa wannan halin kawai tafi tsana a rayuwarsa tun yana yaro tayi iyakar kokarinta akan wannan hali abun ya cutura sai dai akan wannan lamarin ta rantse ko zai rasa ransa sai ta canzasa Kuma sai yayi abinda take bukata .. ya d'auki tsawon minti goma yana durkushe yana bawa mahaifiyarsa hakuri wanda ita ba hakuri tafi bukata daga tillon dan nata ba amincewarsa tafi bukata ,naunayen ajiyar zuciya ta sauke da karfi sannan tace "shikenan komai ya wuce na yafe maka amman ka San da sanin bazan taba janye maganata ba tunda na baka lokaci mai tsawo ka kawo min wacce kake so Kaki kullum da dramar da kake bullowa daita ayi mgn kace tru love kake jira ,dan haka bazan zuba maka Ido ba kayita zama babu iyali ba "Kai yanzu sbd Allah baka jin kunya ?duk sa'aninka sunyi aure har da yayansu abun sha'awa ? amman Kai baka wannan kasar baka wancan kasar , Neman kudi kawai kasa a gaba to meye amfanin kudin da Babu magada ? Kai da mahaifinka bai haifeka ba ka gaji tarin dukiyar daya bari ?yayi shiru yana riko tafukan hannuwanta cikin nashi dan bashi da amsar bata " ni dai gaskiya na gaji da zaman ka haka babu iyali Ina bukatar ganin ya'yanka idan Kuma kafi bukatar sai na mutu kayi auren shikenan sai na hakura na daina maka maganar amman fa kasani muddin nayi shiru yana nufi babu ni babu kai har abada ko mutuwa nayi zan bar wasiha kar abarka ka ta'ba ga....." "Dan Allah Dan girman Allah kiyi hakuri Sweetheart ki daina ambato mutuwar Nan ki rufa min asiri idan kika mutu duniyar fa bazata min dadi ba , kece duniyata, ke kike sakani farinciki idan nayi cikakken awa daya banji muryarki ba Ina rasa gane kaina inaga baki duniyar ...?"kiyi hakuri inshallahu zaki ga aurena nida auta kmr yadda kika ga na saura yanuwanmu amman ki dan bani lokaci zan kawo miki wacce nake so nan kusa ,sai byn da yayi maganar ya fahimci maganarsa ta fito ne ba a yadda ya dace ta fito ba dan ta Ina zai fara ...? "Wannan lokacin ya Kure Maka Adam har abada Babu wani sauran lokaci da zan sake baka kaje ka fara shirin aurenka da maryam kawai , tana gama fadar haka ta kawar da fuskarta gefe dan idan ba haka tayi ba zuciyarta zatayi sanyi akan tillon danta har ta fasa aiwatar da nufinta akanshi tsam ya Mike ya soma kokarin barin falon zuciyarsa na tafarfasa da tuttukin bakinciki dan yasan tunda ta kafe ta nace Babu wani sausauci baya ga amincewa kudirinta ." Kai tsaye mota ya shiga muhd bello na ganin haka Shima ya shiga bangaren daya shiga ya zauna suka bar gidan har suka hau kan titi nasiha m b ke masa me kwantar da hankalinli da ratsa zuciya sai dai ko Daya Adam bai jin zai iya saduda da auren maryam gabadaya ya maida idanunshi yana kallon motocin dake gudu akan titi yayinda kwakwaluwarsa ke tunanin neman mafuta dan dole yasan abun yi kafin ayi masa auren dole da yarinyar nan " "Adam ......"! M.b ya kira sunansa ko gezau bai yi ba bare ya nuna alamun mutun na kusa dashi bai tsaya jiran jin amsarsa sa ko akasin hk ba ya cigaba da magana "ka kasa fahimtata amman kayi hakuri kasanyawa zuciyarka sallama ,na fahimci yadda kake ji amman me kake son nayi daya wuce na tayaka yiwa mahaifiyarka biyayya ? yayi maganar kmr zai yi kuka dan ya tsani yaga damuwar amininnasa ya dafe kanshi da hannunsa daya yana dukar da kanshi tausayinsa ya kama Adam ya furzar da iska me zafi daga bakinsa sannan ya soma magana . "MB nima ka kasa fahimtata ne amman Ina da ra'ayina akan mace da nake son na ajiye agidna , muddin na auri Maryam ya zama dole na qara aure abinda bazan so faruwarsa kenan ba bama haka ba ni bani da ra'ayin ajiye mace sama da daya a gidana ."to meye dan ka ajiye sama da daya ? ka Kara mana tunda kana da abinda zaka iya rike mata ko sama da goma ne ba biyu ba ." tsaki Mr ATA yaja a lokacin da direbansa ya karya kwana yana cigaba da tukinsa ,motar tayi shiru can ya sake motsa bakinsa "mb kasan komai akaina sai dai abinda bakasani ba ni bana son auren farar mace, nafi son mace chocolate colour ita ba fara ba ita ba baqa ba sannan mara kiba wace matakin karatunta iya diploma ne sannan doguwa daidai kafad'ana ba guntuwar mace ba "Kai yanzu me zakayi da doguwa har kafad'arka sbd Allah? " yar daidai fara kmr maryam ai ta isheka rayuwa sannan a matsayinka me zaka yi da mai iya karatun diploma ga mai digree har biyu " "Zanci master's ne ? yayi masa tambayar a matukar fusace "yariyar nan babu abinda ta iya common ruwan zafi sai an daura mata ga balain son social media ,Kai ni duk bama wannan ba na tsani farar mace arayuwata ni dai chocolate itace type dina kasan Allah dana yi rayuwa da farar mace sol irin yarinyar nan gara na mutu ban yi aure ba saboda na tsaneta "subhanallah ATA ka daina fadar haka dan allah , dukkaninsu halittar Allah ne , da baki da fari duk Allah ne ya haliccesu ya tabe baki kawai yana furzar da hucin numfashi mai zafi haka suka cigaba da tafiya m.b na nusarsheshi ." Maryam yan'uwa ne da adam, da mahaifin maryam da mahaifiyar adam uwa daya uba daya maryam ce babbar diya agurin iyayenta sai kanwarta Faiza ,islaha manir , Abusufyan , Salman sai auta izzatu wacce suke kira da izza suna zaune a Abuja yayinda adam suka kasance su biyar agurin mahaifiyarsu aunty shahida itace babba Kuma ma'aikaciyar likitanci ce a babban asibitn gwanaty dake jahar lagos a ikeja ,sai aunty khadeja wacce ta kasance maaikaciyar zenith ,sai adam wanda ya kasance dan boko Kuma rikakken dan kasuwar da duniya ke ji dashi,sai aunty zabiba wacce ta kasance lactura ce a lagos state university, sai auta nana hauwa'u wacce tuni itama ta gama karatunta a London tare da maryam akan harkar compurte science , a london akwai tsananin shakuwa atsakanin nana hauwa'u da maryam Hakan yasa sanda suka kare karatu maryam ta kasa zama tare da iyayenta ta dawo suka cigaba da rayuwa gabadaya dangin mahaifiyarsu da mahaifinsa babu baki duk wanda kagani fari ne sol babu mixed ." Direban mr ATA bai tsaya akoina ba sai a haraban asibinti da aunty shahida ke aiki yana parking ya fito da sauri ya Bude masa murfin mota mr ATA ya yunkura da kyar ya fito yana gyara zaman rigarsa "friend ka bani minti ashiri yanzu zan dawo "na baka awa daya ma har ya juya m.b yace " , dan Allah friend karkayi wata ja inja da aunty kawai kace mata ka amince wani banzar kallo mr ATA ya juyo ya banka masa sannan ya juya cigaba da tafiya ." m.b yayi murnushi dan daman yasan sai ya samu tsaraban wannan kallon daga gurinsa kai tsaye office dinta ya nufa cikin takun nan nasa mutane sai kallonsa suke saboda hotunansa sun qarade koina na matsayinsa na dan kasuwar da duniya Ke ji dashi wasu kuwa tsananin kamaninsa da yaruwarasa yasa suka dinga kawo masa gaisuwa wasu ya amsa Wasu ya share barin ma idan ya fahimci yanmata ne , ya tsaya a bakin office dinta yayi knowking ta bashi izini ya shiga yana taku da kyar yana furzar da iska ." ta dago da sauri ta kallesa tana nuna masa gurin zama Dan tasan Halinsa ba karamin aikinsa bane zuciya tasa ya juya ya kama gabansa "zauna na Dan karasa abinda nake zama yayi ya daura kafarsa Daya akan Daya Yana ciza gefen lips dinsa daya zame masa jiki .byn kmr minti biyu ta tsaida abinda take ta sake dagowa ta zuba masa idanunta "Ina sauraronka wani taimako zan maka ?"kisa a fasa auren nan kawai shine babban taimako da zakiyi min ". "me yasa kake kin auren marym? shin kana da wacce kake so ne data fi Maryam komai ?ya gyada mata Kai alamun "eh ! Yana lumshe idanunsa "a Ina take Kuma su waye iyayenta ?wani mataki iyayenta suke dashi a kasar nan ko ....."? Ki tsaya iya haka ma ya isa dan ban San komai daya shafeta ba sbd ban San komai nata ba , Ina take a ina zan ganta duk bansani ba ina dai kan nemanta sai ki tayani da addua Allah yasa na ganta nan kusa kuyi min auren soyayya idan ma soyayyar zanyi kenan ." "aunty shahida na San idan na fada miki komai zaki fahimceni sbd akwai fahimta a tsakankanimu shiyasa kika ji Ina maganata Kai tsaye dake , a zahirin gsky matar da nake so na aura ni kaina na dade Ina nemanta sai dai har yanzu ban ganta ba ......"nifa ban gane nufinka ba Adam , " I mean matar da nake so ban San Inda take ba ya sake maimaita mata abinda yace "Amman dai ku bani lokaci zan cigaba da nemanta idan na ganta zan kawo muku ita ya karasa maganar tare da fito da pendat din sarka dake makale da wuyansa wanda ke hade da hoton zannen yarinyar ya nuna mata ." Shiru tayi tana kallonsa da kallon zanen yarinyar kyakkyawa ce chocolate colour " kinganta aunty ita ce rayuwata , ni dai kaina na zanata akanta na koyi Zane , ta miki kyau ko ?yayi mata tmyr yana sakar mata tsadaddaden murmushinsa wanda ba ko yaushe yake yi ba "subhanallah Adam kana hauka ne ko me ?" Taya zaka kamu da soyayyar macen da baka San Inda take ba hasalima baka taba ganinta ba ....?"Haka ne aunty Amman ta shiga zuciyata ta samu kyakkyawa mazauni acikinta shekara goma sha biyar kenan nake nemanta aunty babu Inda ban nemi yarinyar nan ba acikin garin Nan har ma da kasashe da garuruwan da nake zuwa Amman ban sameta ba ,Kai ko me kama daita Bangani ba "shine Kuma Dan hauka ka cigaba da Sonta? "ya lumshe idanunshi tare da cewa "ya zanyi haka tawa qaddarar ta kasance itama ba wai ina sonta bane amman muddin zanyi aure ita zan aura". "ka manta wannan shirmen dan har abada bazaka ganta ba dan dayawa mafarki ba gsky bane "wallahi aunty jikina na bani tana Nan a duniyar Nan shiyasa kika ga bana son na karbi auren yarinyar Nan mrym gbdy aunty shahida ta dauke maganarsa a matsayin shirme ta cigaba da kallonsa kmr wani sauna ,Taya zai ce yayi mafarki da mace Kuma Yana Saka ran tana Nan acikin duniya Kuma zai aureta sai Kuma tayi tunanin ko aljanu sun shafesa ne a take agurin tace "Adam ka sausarareni da kyau mafarki baya zama gsky ..."no aunty wannan zai zama gsky yayi mgr a fusace .... " jikinta yayi mugun mugun sanyi ta ajiye nata damuwar ta fara lallabashi dan taga alamun idan ta cigaba da mgn komai zai iya faruwa dan ya zurfafa soyayyar yarinyar sosai ya mike tsaye "ki taimakeni ki fahimtar da sweetheart ku tayani da adduar samota "aikuwa zan fada mata, a ranta tace babu adduar da zamu tayaka tunda mun san abinda muke yi har ya bar office din bata dauke idanunta akansa ba ...." Washegari aunty shahida ta shirya ta samu hjy zulai "ta Koro mata duk halin da adam yake ciki" mu tashi da addua mami saboda Adam yayi nesa cikin wata duniya ,hjy zulai ta gyada Kai cike da matsanacin fargaban tace "Allah kyauta inshallahu zan tashi tsaye da addua da Kuma sadaka lallai da alamun aljana ta auresa idan ba haka ba ga lafiyyayar yarinya me zai Yi da wata a mafarki "shine abinda nayita kokarin na fahimtar dashi yaki yarinyar Nan tunda ta taso bata da matsala ke din mahaifiyarta ce zamu shiga gidansa a duk sanda ranmu yaso, Kuma zamuyi abinda muka ga dama tunda ta muce ita ." "Allah yasa ya gane alkhairi ake binsa dashi "Ameen aunty shahida ta fada tare yiwa mami sallama har wannan lokacin Babu Wanda ya sanarwa Maryam batun aurenta da adam ana jiran sai ya amince sannan a tunkareta da batun cikin saa da jajicewar mahaifiyarsa da yayarsa mr ATA ya amince a wanni yammaci sun dade a dakin suna tautaunawa ya numfasa idanunshi a runtse ya cigaba da magana "Amman fa duk sanda na samu yarinyar da nake nema zan Kara da daita "ai wannan ba wata damuwa bane inji cewar aunty shahida ta fadi haka ne sbd tasan da wahala ya samu yarinyar mafarkinsa ita kuwa mami shiru tayi tana kallonsa a karshe ta girgiza Kai tana masa addua acikin ranta ." aunty shahida ta fito daga dakin mami tare da Mr ATA dake faman cika Yana batsewa da cicci magani bai tsaya ba ya nufi kofar fita aunty shahida tace "adam Dan Allah bari na fito ku saukeni a gurin aiki Bai ce mata uffan ba ya wuce sannan ta Kalli Inda maryam dake zaune tare da nana hauwa'u suna kallo da wayar maryam tace "Maza Maryam dauko mayafinki kizo muje kiyi min rakiya zuwa asibiti Nan take ta mike daman a shiryenta take mayafi kawai ta dauka suka fito tare , Kai tsaye Inda motar mr ATA yake suka nufa limoxin ta bude gidan baya ta shiga maryam ma tayi kokarin bude dayan bangare ,aunty shahida tayi saurin cewa "zauna a tsakiya kusa da adam maryam taji maganar wani iri ta dan saci kallon aunty shahida tana mamakin jin furucinta" zauna a tsakiya kusa da adam to me hakan yake nufi?Tana son tai tmby babu hali dan haka jikin a sanyaye ta bude ta shiga ta zauna nesa dashi kamar wata tsuntsuwa ta kame Kanta tana jin mummunar faduwar gaba from no where " . Direban mr ATA ya ta-da motar suka soma kokarin fitowa daga cikin gidansu "Ina muka nufa ma kika ce ? ita Kuma wannan ina zaki daita nifa bana son kwashe kwashe a motata? asibiti ta bashi amsa duk da tasan yaji abinda tace , bai sake cewa komai ba har suka iso asibiti ,yaki fitowa Yana jiran aunty shahida ta karasa fitowa dan maryam tuni ta fito "adam muje akwai sakon da zan baka yayi shiru yana maimata maganarta yaji Kmr yace ta bawa mrym ta kawo masa Amman Kuma baya son abinda zai hadashi da yarinyar "a hankali ya fito ransa a bace Kai tsaye office dinta suka nufa aunty shahida ta bude office dinta dukkaninsu suka shiga Yayinda mr ATA ya tsaya daga bakin kofa yana jiran ta bashi sakon da tace aunty shahida tace "bismilla mana ranka shi dade mr ATA shigo ka zauna ga guri nan yayi mata wani irin kallo yana bukatar qarin bayani akan abinda ta keyi "ta gyada masa kai "shigo mana ." da kyar mr ATA ya shigo office din ya zauna yana hura hanci sannan itama maryam ta samu guri ta zauna tana satar kallon fuskarsa kwata kwata babu digon annuri ," " Maryam tashi ki bude fridge ki dauko masa ruwa dan nasan bai fiyye shan lemo ba ,ta mike a hankali ta karasa ta dauko masa ta ajiye a gabansa ta koma ta zauna gabanta na faduwa "ka bani minti goma kawai zan duba wani fayal ne yanzu zan gama sannan ta soma aiki tsaki yaja a ransa dan dai tana da matsayin aunty shi ce if not bai ga dalilin da zai yita batawa kanshi lokaci ba akaron banza ba ."baka sha ruwan ba ?ta dago ta tambayesa cike da kulawa "no need !ya bata amsa ataikaice byn kmr minti biyu ta mike ta fita tace "kanina ina zuwa "zuciya ta sake kawo masa wuya sakamakon barinsa da zatai yi shi da wannan guntuwar yarinyar mai siffar aljanu yaja tsaki yana dafe goshinsa da hannunsa ." Zamansu daga ita sai shi acikin office din baqaramin tashin hankali maryam ta shiga ba ,gbdy duk ta rude sai zufa take fitarwa da zarar tayi kamar zata dago ta kalleshi sai ta kasa dan gbdy ta nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zata buga allah allah take Aunty shahida ta shigo domin bazata iya cigaba da irin wannan zaman ba ,minti biyar kawai Aunty shahida tayi da fita amman ganin take Kmr awa biyar tayi da barin office din ,shi kuwa mr ATA banda tsaki babu abinda yake yana qarawa domin ya fara gajiya da zamansa tare da abinda yafi tsana arayuwarsa ." Aunty shahida na fita ko cikakken minti goma batai yi ba sai ga nuzla ta shigo office din bakinta dauke da sunan Aunty shahida,turus tayi sakamakon ganin maryam zaune gefe guda kuma mr ATA ne zaune kallon tsoro tayi masa ta dauke kanta tana gaishesa bai amsa mata ba kamar sauran lukuta ta qarasa ta dafa maryam "marsi ina Aunty shahida ."? "ta dan fita amman tace bazata jima ba ki jirata , "okay da ido tayi mata tmby me ya Adam yake yi ? itama da kwayar idanunta ta bata amsa da bata sani ba dan babu damar ayi magana mai sauti kasamcewar sun san baya son hayaniyar komai saurin ciro wayarta tayi ta maida silet ." sadiya wacce ta kasance me koyon aiki ce a asibiti ta shigo bakinta dauke da sallama "Assalamu alai...... kasa karasa sallamar tayi sakamakon gani mr ATA zaune idanunshi na kallon screen din wayarsa sanye cikin kanan kaya ,gbdy ta rikice akansa madadin ta karasa ta ajiye file din dake hannunta ta kasa ko daga dan yatsan kafarta garin kallonsa ma har file din hannunta ya subuce daga hannunta ya fadi kasa da sauri ta tsugunna ta dauka jikinta na rawa ta karasa ta ajiye fayal din akan table ,tana faman kallonsa sai lokacin ta lura da maryam dake zaune tana kallon yatsun hannunta yayinda nuzla ke tsaye a gefenta "sannuku da hutawa ta furta a hankali ." maryam ta dago tana murnushi tace "yauwa ya kokari ? alhamdulillah sadear ta bata amsa tana kallon nuzla sannan ta fita tana waiwayen Mr ATA tana yaba kyawunsa acikin ranta shi kuwa Mr ATA ko ajikinsa dan iskar ma data debota bai gani ba idan da sabo ya rigada ya saba da irin kallon da suke masa haka ma kallon da mrym da nuzla Ke masa bai sa ya dago daga duban wayarsa da yake ba . Nurse sadiya na fita daga office suka ci Karo da husaina itama maakaciya ce "ke lafiyarki kika fito a hargitse Kmr wacce aka koro ?"uhm ke dai bari husseina wani matashi na gani a office din doctor shahida mutumin yayi min kyau matuka ya dauki hankalina wallahi irin mijin da nake nema kenan mijin duniya Mijin novel ya hadu sosai da gani yana da kudi yana da tarin ilimin boko da Arabic uwa Uba kyau "ke sadear raba kanki da wahala, kina diyar talaka dake naci ma da kyar kuke samu kullum Kuna yawo a gidan haya , yayanki ma da kyar yake daukar dawiniyarki Amman kin kashe kanki da mugun buri , ki roki Allah idan yaga dama zai Baki ki Daina zafafa burin akan auren me kudi ." sadear ta Dan turo mata karamin Bakinta tana yatsina fuskar ,jikin Sadia yayi sanyi sosai husaina taja tsaki ta wuce ta barta Nan tsaye tana maganar a fili ." Wayar hannunsa da yake ta faman daddanawa ce ta dauki qara ya manna a kunnensa tare da zamowa kad'an daga Kan kujerar da yake zaune yana lumshe idanunshi "na barota a gida ne ,okay suna bukatar new design's da kaya ?shikenan ki bawa kwararrun wadan da suka iya domin bana son a samu matsalar komai aikinsu dan last time sunyi complain okay may be tomorrow yana magana yana lumshe idanuwa yana lasar lip's dinsa na kasa ." uzla,maryam duk suka zuba masa idanunsu suna kallonsa kowacce da abinda zuciyarta take saqawa jikinsa ya bashi kallonsa suke dan haka ya tsaida lumtsatsun idanunshi akansu yana masu wani irin kaskantacce kallo sannan ya dauke kansa ya cigaba da waya a daidai lokacin da husseina da sadiya suka shigo tare ita kanta husseina ta jinjinawa kyawunsa dan sai da tabawa idanunta abinci suka dauki abinda ya shigo dasu suka juya ." Ya sake tsaida idanunshi akansu ganin still shi din suke kallo har lokacin Kmr basu san shi ba wani irin taikaci ya kamashi dan baya son yawon kallo arayuwarsa wani abu ya hadiye mai daci a makoshinsa kafin ahankali yaja tsaki yana cigaba da kallonsu yayinda su kuwa a matukar firgice suke kallonsa cikin tsananin tsoro da firgici sam basuyi tsamanin zai sake kamasu suna kallonsa ba irin kallon da yake masu yasa suka sake shiga rudani dan basu san abinda zai biyo bayan kallon da yake masu ba sannan basu abinda zasu fad'a dan kare kansu ba nuzla ta kalli maryam itama ta kalleta gabadaya jikinsu ya kama rawa nuzla tayi saurin durkushewa kasa bisa gwiwowinta dan tasan na lahira zai fisu jin dadi idan bata hanzarta bashi hakuri ba dan taga maryam bata da alamar bada hakuri "ka..! kayi hakuri ya Adam magana yake son yi amma ina jin isa acikin ransa yasa ya gagara furta komai illa kafarsa daya daya shiga jijigawa yana takaici ." ganin har kusan minti talatin aunty shahida bata dawo ba yasa mr ATA ya Mike a fusace ya tura hannunsa daya cikin aljihunsa ya bar office din dan jikinsa ya fara bashi so take ta hadasu da Maryam ta fayyace mata komai a gabansa,yana fita nuzla ta nufi kofa cikin sand'a itama mrym ta biyo bayanta, nuzla na gama bude kofar turus sukai yi sakamakon ganin sadiya da husseina tsaye rungume da file suna kallon byn mrs ATA suna magana can kasa kasa sakamakon mutanen dake kai kawo " ai wannan ba bakon fuska bane sadiya matashin dan kasuwan nan ne da duniya Ke ji dashi sannan kani ne ga sister shahida yana zuwa lokaci zuwa lokaci ke baki ga kamarsu ba "?lallai kam sai yanzu na ganesa ko dan na rikice ne amman yafi kyau a fili km suna matukar kama sosai da Sister shahida sai dai har ya fita kyau ,wallahi husseina mutumin nan ya shiga raina sosai ban ta'ba ganin halittar daya dauki hankalina ba kamarsa komai nashi irin mafarkina "uhm uhm sadiya na sha gaya miki ki daina irin wannan hange ki tsaya matsayinki kin kasa fahimtata ."kisani babu abinda allah bayayi bansan dalili ba gani daya nayi masa amman na kamu da matsanancin soyayyarsa " wallahi wannan yafi karfinki Ke ko yaronsa yafi karfinki bareshi idan zaki dawo haiyacinki ki dawo taja hannunta sukai wuce sadiya na juya bayanta ." Naunayen ajiyar zuciya nuzla da maryam suka sauke atare suna dafe qirji "marsi wallahi ba qaramin tsorata nayi ba ,koni kusan nafiki tsorata wallahi kadan ya rage ban saki fitsari ajiki ba qaramin saa muka ci ba da yau mun sha maruka suka kwashe da dariya "kinga bari na wuce bazan iya jiran Aunty shahida ba daman nazo karban test din hjyrmu ne nace nazo mu gaisa kinga wucewata sai mun hadu a gida ta zame hannunta dake cikin na maryam ta wuce tana daga mata hannu , maryam ta koma cikin office zaman jiran Aunty shahida ." Bai Dade da wucewa ba doctor shahida ta dawo ta ga wayam bashi Babu alamunsa "sarkin zuciya halan ya gaji ya wuce "eh Maryam ta fada muryarta a sanyaye "okay ta shiga tattara kayayyankinta muje kou daman akwai maganar dana so muyi mu uku Amman zanzo gobe inshallahu idan na tashi daga aiki muyi a gida "magana kuma aunty.?"ta tmbyeta a tsaro ce . "Eh! " wacce magana ce haka Kuma har da ya adam zaayi ?aunty shahida tace ",magana ce me mahimmam ci , dan girman Allah aunty shahida wallahi bana son duk abinda zai hadani dashi nifa tsoro yake bani culmdown my sister ki cire wannan tsoro ba wani Abu bane face alkhairi shiru mrym tayi tana nazarin maganar aunty da tunanin wacce magana ce wannan da har sai anyita da ya Adam Kuma tace alkhairi ne ...? suna fitowa haraban asibinti suga direbansa na jiransu "a ruwa Ina mai gidanka ? sai daya rusuna mata sannan yace "ya kira anzo an daukesa da wata motar aunty shahida ta girgiza Kai ta shiga mota ita da maryam inda take fad'a mata zuwan nuzla "Ayya kanwata ai kuwa na gode sosai itama kuwa ina son ganinta nan hankalin maryam ya dan kwanta jin har da nuzla sai dai har sanda a ruwa ya sauke aunty shahida a kofar gidanta zuciyar mrym bata bar Saka da warwara ba Allah Allah take gobe tayi taji ko meye .." washegari da misalin karfe goma na safe sakon mutuwar sadiya ne ya riski doctor shahida, tayi matukar firgita da Jin wannan mummunar labari saboda cewar da akayi yankar rago akayi mata ta zabura ta mike daga zaunen da take jikinta na rawa ......." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH Arewabooks username Ayshabagudo bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page4 "Wani irin gumi ke tsatsafowa ajikin aunty shahida yayinda zuciyarta ta dinga bugawa da karfi fiyye da kaida ,nan take ta mike tsaye ta shiga zariya a office ta kasa zaune ta kasa tsaye tana sake jin wani sabon tashin hankali tana cikin wannan halin sai ga doctor sa'a ta shigo a rud'e ta tsaya suna kallon juna yanayin doctor shahida ya tabbatar mata taji abinda ya shigo daita office din dan duk ta fita haiyacinta ,a matukar tsorace aunty shahida take kallonta qirjinta na dokawa "nasan kinji abinda ya shigo dani ? wai an yiwa sadear yankan rago a gidansu." har lokacin fargaba da tashin hankali bai bar gangar jikin aunty shahida ba ,da kyar ta iya motsa labbanta "yanzu doctor zinnira ta kirani take fad'a min wannan mummunar tashin hankali alamarin nan ya d'aure min Kai matuka , hakika mutuwar sadear ya gigitani jiya fa iwar haka muna tare daita har tana cewa zatayi magana mai mahimmanci dani yau idan mun had'u ko me zata fada min ? ta k'arasa maganar idanunta na ciccikowa da ruwan hawaye "gbdy mutuwar mubina ce ta dawo min , Allah sarki rayuwa , Allah ya jikansu ya tona asirin duk wanda yayi sanadiyyar barinsu duniya , "duniyar nan ma guda nawa take da zaka kashe dan'uwanka ?cewar doctor sa'a "ya kamata muje gidansu yanzu ko ? "Eh ! wannan gaskiya ne ya kamata muje " da sauri aunty shahida ta tattara abubuwanta dan bata Jin zata dawo asibiti daga can gidan hajiya zata wuce doctor sa'a ta nufi kofar fita itama aunty shahida ta biyo bayanta da s auri ta rufa mata baya suka jera tana kokarin neman number doctor zinnira suje tare ." "Kai tsaye gidansu sadear dake ijora olopa suka nufa a kofar gidan suka iske 'yansanda suna tambayar aminu yayan sadear yadda abun ya kasance "to ni dai bazan qarar da komai ba , kawai dai na tashi da asuba na shiga d'akinta Inda take kwana tare da yarana guda biyu domin suyi sallah kawai naga gawarta cikin jini amman babban yarona sadi yace yaga bayan matar Kuma ya ganeta duk da jikinta lullube yake da bakin kaya ba'a iya ganin komai nata ".ya qarasa maganar Idanunshi na sauya kala." yauwa haka muke so yanzu Ina yaron yake ? police officer ya tambayi aminu yana gyara tsayuwarsa " kan aminu na kasa hawaye na tsiyaya daga idanunshi cikin rawar murya yace "yana ciki gida " girgiza Kai aunty shahida tayi cike da tausayawa masa ,." a tsanake suka gaisa sannan gbdy suka had'a baki da doctor sa'a da dr zinnira sukai masa gaisuwa "aminu ya qarin hakurinmu Allah ya jikan sadear Allah yayi mata rahma halinta na gari ya bita "Ameen ya Allah , na gode Allah ya bada lada "Allah ya tona asiri duk wanda keda sa hannu a kisan sadear ya sake amsawa da" amen na gode Kwarai da gaske yana kukan an cucesa an rabashi da yar'uwarsa tilo , a lisafinsa yanzu tayi awa hud'u a kabarinta shiru yayi yana juya girman alamrin zuciyarsa na zafin da bai san ranar dainawa ba ." "Nan su aunty shahida suka barsu tsaye suka shiga cikin gidan suka nufi bangaren yayan sadear Inda suka tadda tsirarun mutane zaune a cikin d'akin ana karba gaisuwa ,a natse suka gaisa da mutane tare da yi musu gaisuwa suka zauna Inda ake ta jimamin mutuwar kowa na fad'ar albarkacin bakinsa ,wasu na cewa ai hadiza ce ta kasheta tunda daman ta furta cewar itace zataga bayanta a bayyanan nasi ,yayinda wasu na cewa ba lallai bane ya kasance itace ta kasheta ." Suna zaune police officers suka shigo tare da aminu da yaronsa sadi dan kimani shekaru goma shabiyu yana musu bayanin wacce ya gani ." 'yansanda na sauraron yaron daki daki gefe guda kuma suna dudduba gidan a karshe suka tsaya a kofar d'akinsu hadiza tare da tambayar wacce ake zargi da aikata kisan ." batare da 'bata lokaci ba akayi sallama a bakin kofar d'akinsu, hadiza kam tunda taji sallama police cikinta ya duri ruwa ta soma juya Kai zuciyarta na tsinkewa dan tunda akayi mutuwar take cikin tsoro da matsanacin firgici mara iyaka gabadaya komai nata ya tsaya cak ."mahaifiyarta ce ta amsa sallamar tana fitowa daga cikin d'akin "muna son ganin hadiza ko tana ciki ?"."eh ! tana ciki ta fad'a muryarta na d'an rawa "hadiza ki fito ana son ganinki da kyar hadiza ta fito kamar wacce kwai ya fashewa aciki ta tsaya a bakin kofar d'akinsu , kana kallonta zaka fahimci a tsorace take , sai da suka mata duban tsanake sannan daya daga cikin police din yace "kece hadiza ko ? ta gyada masa Kai alamun "eh! gabanta na faduwa da sauri da sauri suka ce "muje akwai wasu tambayoyi da zamu miki a office dinmu ." "akan wani laifi kenan? mahaifiyarta tayi karfin halin tambayarsu". idan muje office dinmu kwaji akan wani laifi ne " suka tasa keyarta gaba mahaifiyarta ta biyosu da sauri tana cewa "bazan bari ku tafi min da yarinya ba ku zubar mata da mutunci ba ." jin maganar mahaifiyarta yasa hadiza ta tsaya cak taki cigaba da tafiya police suka ce "muje ko!" "shiru tayi jikinta na rawa taki motsawa daga Inda take aiko daya daga cikin yar sanda mace ta rike tsintsiyar hannunta "zaki da girma da arziki ko kuwa mu tafi dake ta karfin tsiya ? "cike da tashin hankali hadiza ta fixge hannunta daga hannun yarsanda tare da marairaice fuska kamar zatayi kuka "ni bazani koina ba har sai na san dalilin da yasa zaku tafi dani office dinku ". zata sake magana suka daura bakin bindiga keyarta "idan kika sake furta wata Kalma zamu sakar miki wuta mu tasheki aiki," oya muje "tsimi tsimi hadiza ta soma tafiya mutane gidan na kallonta cikin tsananin farinciki dan daman taadabi kowa acikin gidan kowa tsoronta yake ." "wani mummunar tashin hankali ya shigi mahaifiyar hadiza da hadizan karon kanta, ana k'okarin turata cikin motar 'yansanda su aunty shahida suka fito suka kama gabansu zuciyoyinsu cike da tsoro da fargaba ,direban aunty shahida ya sauketa a kofar gidansu sannan ta bashi umarnin ya kai doctor sa'a da zinnira ya dawo, suka yi sallama da abokan aikinta da zumar sai sun had'u gobe , Jiki a sanyaye aunty shahida ta shiga cikin tangamemen falon mahaifiyarta parlour'n shiru babu alamun akwai wani bil adama acikinsa hatta 'yan aikin gidan bata ji motsinsu ba ." Ta samu guri ta zauna jagwab akan d'aya daga cikin kujerun Parlour'n tana sauke ajiyar zuciya har lokacin wani iri take ji ajikinta , shiru parlour'n baka Jin motsin komai sai na AC dake aiki a falon . ko cikakken minti biyar batayi ba ta fara Jin motsin mutane , ta d'ago a hankali masu aiki ta gani cikin shigarsu ta kullum dukkaninsu rike da farantin silver suka rusuna tare da had'a baki "barka da zuwa hajiya "barka sannuku ya aiki ?" "alhamdulillah ! suka amsa tare da ajiye tire suna tambayar abinda za'a kawo mata " me za'a kawo miki hjy akwai rice and stew akwai tuwon shekafa akwai dabmu shimkafa akwai ......? "duk babu wanda zanci aciki ta fada tana runtse idanunta dan kanta wani irin sarawa yake kmr ana buga mata guduma ,tana nan zaune hajiya zulaiheart ta shigo cikin shigar alfarma doguwar rigar lace har kasa wanda kimanin kudinsa ya Kai 500k ta zauna akan kujera mai zaman mutun d'aya tayi shiru tana duban fuskar babbar diyarta "lafiya shahida duk na ganki haka ?a hankali ta bud'e idanunta ta saukesu akan hajiya zulaiheart "wallahi mami wata mutuwa akayi mana agurin aiki mai shiga jiki ko ince an kashe yarinyar ......" "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun oh ni zulai me mutane suka d'auki rayukan mutane ne yanzu kashe mutun bai musu wahala ?"wallahi mami sai ma Kinga yayan yarinyar abun tausayi marayu ne babu uwa babu uba sai Allah abun daya fi d'aga min hankali yankar rago akawa yarinyar abun tausayi sam babu Imani a zukatan wasu mutane taya zan iya kashe mutun da hannuna ?ta karasa maganar hawaye na zubo mata."uhm duniya kenan Allah dai ya tona asiri ko suwaye suke bin ya'yan mutane har gida suna kashesu to Kalli mutuwar mubina kigani abu kamar wasa har an kusan shekara biyu amman har yanzu babu labarin wanda yayi kisan." Allah dai ya kyauta sam kasar nan babu tsaro shiyasa nasa aka qara tsaro mai karfi a gidan nan." "hajiya ai ita sadear ana zargin makwafciyarsu ce tabi dare ta kasheta yanzu haka maganar da nake miki tana hannu jami'an tsaro zasu fara bincike akanta "alhamdulillah ai gara kam ita kuwa me yayi zafi haka ko akan me zata kasheta ?mutumin duniya hjy ai ba'a iya mutumin duniya sai Allah daya haliccesa, Allah dai ya sawaka kawai zamuce ." "Ameen inji cewar hjy "wai Ina maryam da auta suka shige ne ? sunje gidan zabiba amman dai nasan zuwa la'asar idan anci sa'a babu traffic zaki gansu sun dawo " Anya kuwa zan jira har wannan lokacin ? bari kawai nazo na wuce gida ." "kin kuwa fada ma maryam batun wannan sarkin zuciya ?"wallahi a'a jiya dai nayi kokarin had'asu gbdy a office dina sai Kuma hakan bai yiwu ba ga yau ma ,Ina ganin sai dai weekend zanzo dan gbdy jina nake wani iri, wallahi mutuwar nan ta shigeni yarinya mai kirki da biyyaya da sanin ya kamata sam sadear bata da matsala a rayuwarta sannan bata da abokin fada kowa nata ne agurin aiki ga wasa da dariya ga ..."kira ne ya shigo wayar aunty shahida wanda yayi sanadiyyar katse mata magana ta d'auka tana duba screen din wayar direbanta ne mlm garba dan haka ta mike ta d'auki jakarta tayi wa hjy zulaiheart sallama ko a gidanta ma kasa tabuka komai tayi babbar yarinyarta madina duk ta damu sai faman tambayarta take ta fada abinda ke damunta bata ,boye mata komai ba ta fada mata mutuwar , mutuwar tsaye madina tayi dafe da qirji dan tasan sadear sosai tana janta ajiki idan taje gurin mamanta ,addua tayi mata hawaye na zubawa aunty shahida lokacin da take tuna moment dinsu da yarinya babu abinda yafi daga mata hankali kamar maganar da tace zasuyi a yau din gashi ta mutu batare da san ko akan me zata mata magana ba kwarai taso tasan ko akan meye , Allah sarki rayuwa kenan ta dade zaune tana jimamin mutuwar sadear kafin daga baya ta mike ta shiga dakinta ta kwanta zuciya da gangar jikinta na mata ciwo .." Har yansanda suka karasa office dinsu kuka hadiza take , aka nufi d'akin bincike daita aka nuna mata gurin zama sannan bayan kamar awa daya wasu qararrun 'yan sanda suka shigo nan suka fara Aiko mata da tambayoyi d'aya daga cikinsu tace "ko zamu iya sanin dalilin da yasa kika kashe makwafciyarki sadear ? hadiza taji tambayar tamkar saukar aradu take idanun sukayo waje tare da dafe qirjinta "wallahi bani na kasheta ba nima tashi nayi naji labarin mutuwarta ,"karki wahalar da hukuma zai fiyye miki sauki ki fito ki fada mana gskiya kunyi fad'a da sadear ko ba haka ? cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya tattare da tsoro ta gyada Kai alamun "Eh!"can km ta girgiza musu Kai alamun "a'a! police ta gyada Kai sannan ta cigaba "kenan kina nufin babu wata matsala ko fada wacce tasa kukayi sa'insa daita ? nan ma ta gyada Kai alamun babu cikin kankanin lokaci ta fita haiyacinta saboda tambayoyin da suka dinga mata tana kare kanta a karshe daya daga cikin police mace tace ' kinyi furucin zaki kasheta Kuma kinyi nasara ko ba haka ba ?ta girgiza kanta alamun a'a juyin duniya akayi da hadiza amman ta tsaya akan ba itace ta kashe sadear ba suka barta tare da turata wani d'aki tana shiga taji an rufeta da duka cikin kankanin lokaci kamanin hadiza ya sauya tayi laushi sosai tana ihu tana Komai aka shiga daita wani daki aka garkame . tayi kuka sosai idan ka ganta sai ta baka tausayi gabadaya ta tabbatarwa kanta tata takare Ina ma batayi fad'a da sadear ba ,a she da me kararen kwana tayi fada ? wayyo Allah ni hadiza kaicona me ya kaini fada da gawa ....?yau dai ga Inda karshen wahalana ya kawoni ni hadiza nayi nadama ,nayi danasani ban bar yara ba ,ban bar manya ba ,ban bar matan aure ba, ban bar tsofafi ba , ga dai karshena ban san me gobe zata haifar ba ta karasa maganar tana matso ruwan hawaye mai zafi daga idanunta ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH Arewabooks username Ayshabagudo bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page5 " da misalin karfe tara na daren ranar Juma'a mr ATA ya fito daga bathroom jikinsa sanye da rigar wanka iya gwiwarsa yayinda hannunsa d'aya ke rike da white towel yana goge kanshi zuwa wuyansa ,ahankali ya qarasa gaban mirrow ya tsaya yana kallon kyakkyawar fuskarsa yana qoqarin zare rigar jikinsa ."shiru yayi yana kallon faffad'an qirjinsa dake kwance da laulausan suma tamkar na jariri sabuwar haihuwa ga Kan nipple's dinsa a tsaye makale da qirjinsa sai sheki suke, babu lafiyayyar macen da zata gansa a haka bataji sha'awarta ta motsa ba saboda kyawun cikar halittar da allah yayi masa ." kusan minti goma ya dauka tsaye yana qarewa kansa kallo kafin daga bisani ya juya a natse ya koma bathroom ." ko cikakken second uku bai yi ba ya fito ya d'auki kwalbar bodyspry ya feshe ilahirin jikinsa ya saka white singlet boxer's sannan ya shirya cikin wasu hadaddun kananan kaya t shirt fari sol da dogon wando baki , ya kai hannu inda tsadadden Turarensa (Reed ) yake ya d'auka ya feshe kayan jikinsa , ta koina a sansar jikinsa kamshi yake tashi mai sanyi da tada tsumin shaawa." ya ajiye kwalbar turaren a mazauninsa yasa hannun ya kwashe wayoyin business dinsa guda biyu ya juya ya fito daga cikin dakin tare da janyo kofa ." a natse yake saukowa daga Kan matattakala bene hannunsa daya soke cikin aljihun wondonsa kai tsaye yana gama saukowa ya qarasa dining area ya zauna akan d'aya daga cikin kujerun dining yana sauke numfashi kana ya ajiye wayoyinsa akan table ."ahankali sanyin ac dake aiki a parlour'n ya dinga ratsa sansar jikinsa ,lumshe lumtsatsun idanunshi yayi yana ciza gefen lip's dinsa , cikin haka mami ta fito daga kitchen ta soma hidimar zuba masa abinci ,dan shi baya son masu aiki na shiga huruminsa saboda Allah yayi shi mai tsananin tsabta da kyakyami , shiyasa ba koina yake cin abinci ba, ko fuskar abinci ya kalla yaga yayi wani iri to komai za'a yi bazai ci ba shiyasa duk sanda zai ci wani abu mahaifiyarsa ce kadai ke masa hidima abinci wannan halin kuwa ya samo ne daga gurin kankansa alhaji abdallah dan shima ba abincin kowa yake ci ba sai wanda yayi masa ." bayan ta zuba masa jollof din shikafa yar waje wacce taji pepper chicken ta hada masa coffee dinsa na gado ta ajiye masa a gabansa sannan ta koma ta zauna a kujerar dake fuskantarsa tana dubansa a tsanake tace "kasan wani abu my love ? ta tambayesa idanunta na kanshi ya d'an girgiza mata kansa batare da yace komai ba sai ma lumshe lumtsatsun idanunshi da yayi yana jiran yaji me zatace .Allah Allah !!nake kayi aure na huta da yi maka hidima "shiru yayi bai yi magana ba yana jiran yaji spoon din abinci bakinsa amman yaji shiru har tsawon second goma sai ma maganar aure da yaji ta cigaba dayi masa wanda hakan Ke mugun bata masa rai tare da dagula masa lissafi dan a halin yanzu idan akwai abinda yafi tsana bai wuce maganar auren da take bukatar yayi ba gashi burinta ba abu bane dake cikin lissafinsa ." shiru yay har wata second biyar tazo ta wuce bai ga alamun tana da niyyar bashi abinci ba dan haka ya bud'e lumtsatsun idanuwanshi a hankali ya tsura mata yana kallonta fuskarsa a shagwabe kamar koda yaushe idan yana gabanta "kana wani kallona da wad'an nan idanuwan naka masu firgita mutane ai gsky na fad'a ina bukatar na huta da maka hidima ." muryarsa a kasalance ta fito tamkar mai koyon magana "haba my sweetheart ki daina fadar haka mana yanzu baki jin tsoron wani yaji kina cewa kin gaji dani ?ni bance na gaji da kai ba karka canza min magana hidima nace ta fad'a tana hararasa wanda da gani na soyayya ce." ya sauke naunayen ajiyar zuciya still kwayar idanunshi na kanta sai daya numfasa sannan ya sake motsa lip's dinsa "sweetheart ! ya kira sunanta a shagwabe ta kalleshi kawai tana jiran taji abinda zai ce " ai ko na yi aure bazan daina cin abinci daga hannunki ba domin dashi na saba ." "Ina bazan yarda da wannan tsarin ba dan bazan shiga hurumi da ba nawa ba ,wannan hurumin matarka ce yana da kyau idan mutun yayi aure ya samarwa matarsa farinciki , hurumin mahaifiya dabam haka zalika na mata da dabam , dan haka kasa wannan a ranka da zarar kayi aure babu Kai babu cin abinci daga hannuna ." ta karasa maganar tana murmushin jin dadi jin bai ki maganar data fad'a ba ga dukkanin alamun dai yayi amanna da zabinta dan haka ta dauki spoon ta soma bashi abinci a baki tana kallonsa cike da tsantsar kulawa "kinsan wani abu sweetheart ? ta tsura masa Ido kawai batare data ce Komai ba dan ta lura yana cikin farinciki shima ita yake kallo cike da matsanacin soyayyarta , anan duniya bashi da kamarta ita kadai yake kallo yaji duk tarin damuwarsa ta Kau." "wallahi idan Ina cin abinda kika sarrafa wani farinciki nake tsintar kaina ciki , nifa ganin nake ko Allah ya qaddaro nayi aure to kece zaki dinga girka min abinci , dan abincin my sweetheart babu sauki akwai dadin dandano dan zai iya sa mutun ya cire kansa ya bayar kyauta ."ta sake yin murnushin jin dadi tana zabga masa harara "Kai ko Allah naki wayon." ahankali yake cin abinci suna hira cike da so da qauna dake tsakanin uwa da d'a suna cikin haka auta ta shigo bakinta d'auke da sallama ta zauna a kusa da mami tana Kiran "washhhhhh Allah nah na gaji sannan ta maida hankalinta gurin mr ATA "Ina yini yaya ? "Lafiya ! ya fad'a atakaice yana sake tamke fuska sosai , ta maida hankalinta kan wayarta tana chart "wai ke auta idan kina gida baki da wani aiki ne sai rike waya baki istergram baki facebook baki what's app ? Ko karfe daya na dare na hau online sai na ganki ."yayi maganar a can kasan makoshi sam bazakace shi yay maganar ba tsabar miskilanci ." "wallahi kamar kasani son ita da maryam sam basa gajiya da rike waya da daukar hotuna kamar masu aljanu , wad'an nan duk randa aka daina amfani da waya a kasar nan ban san yadda zasu dawo ba " wallahi kuwa mami akwai matsala nana hauwa'u ta fada tana cewa "shekaranjiya fa muna zaune wayar maryam ta d'auke wuta kamar almara kinsan a daren sai da taje aka gyara mata, ai wallahi garani sau dubu akan maryam tunda ta sako sunan maryam ya d'auke wuta dip kamar anyi ruwa an dauke ya maida hankalinsa kacokan a kan wayarsa dake qara ya d'auka ya manna a kunne yana maganar million kudade da zasu fita da wadan da zasu shigo ." "babu gara auta dake daita duk d'aya ne ,ku dai rage son duniya dan gidan wasu zaku ba kowani namiji ke son irin wannan rayuwar ba , sannan lokacinku kuke ci bamu San sanda mutuwa zata zo ba , suna cikin mgn maryam ta shigo da sallama sanye da riga da wando na bacci ash colour masu yanayi dana sanye sai dai su anyisu ne dan bacci , nan gabanta ya fadi saboda ganin mr ATA ta tsura masa Ido tana kallon yadda yake motsa lips dinsa gashi dai magana yake sai dai sam bazakace magana yake ba tsabar jin kai da Isa da miskilanci yana ji da kanshi kamar yadda yanuwansa suke ji dashi a family ,shine babban alfaharinsu bata taba jin ance ya aikata aikin asha ba ya kame Kansa ya rike mutuncinsa kowa yana sonsa ta kowani bangare ko ita zata so ta samu miji kamarsa sosai tayi nesa a kallonsa .." "yauwa gara da kika zo zauna kiji wa'azi dan kin fini quanar social media kinganta mami Kashi ne kawai maryam bazata d'aura a media ba kinsan d'azu da safe da maryam ta rasa abun d'aurawa kwayar tsintsiya shara ta d'auko tayi hoto dashi ."Mami ta zaro Ido waje tana mamaki sannan ta murmusa ita kanta nana hauwa'u dariyar take kmr a lokacin abun ya faru "shi kam mr ATA tsayawa yayi cak yana cigaba da wayarsa kuma yana sauraron nana hauwa "a she da mahaukaciya ake k'okarin son hadashi aure ?ai duk yadda zai yakice wannan auren zai yi bazai yi rayuwa da mental ba ." "Kai auta banason sharri fa Maryam din ce ke yin wannan shirmen ",wallahi gata nan da ranta ba karya nayi mata ba bari ma na shiga na nuna miki maryam wacce ta dawo haiyacinta adalilin katuwar hararar da mr ATA ya bamka mata tayi wuf ta fixge wayar a hannun nana hauwa'u tana harararta "Kai sister bama yar haka dake fa "nana hauwa'u tayi murmushi "wai gskiya zan nuna ma mami tasan Inda kika Kai a son social media."maryam ta zauna idanunta na kan nana hauwa'u amman kacokan hankalinta na kan mr ATA tana mamakin wannan tsana da yayi mata sam baya qaunar ya ganta a wuri aunty shahida ce ta fado mata arai ko maganar me zatai mata jiya akanshi ? sosai kwakwaluwarta ta shiga thinking ." yana gama wayar d'ayar wayarsa ta d'auki qara ya d'aga wayar dake ringing yana dubawa sannan ya manna a kunne "okay Ahmed shikenan ayi musu guri na mussaman ,su Kuma wad'an can kwantaina's din inshallahu zuwa monday zan shigo sai na saka hannu ya karasa maganar yana lumshe idanunshi yana k'okarin sauke wayar Kai tsaye idanunshi ya sauka akan maryam , ya d'auke kanshi tsawon minti biyu ya sake d'agowa adalilin wani Kiran daya shigo ,cikin natsuwa zai d'auka karaf idanunsu ya tsarke cikin juna idanunta kyam akanshi kamar wata mayya "ke........"kallon uban me kike wa mutane haka na canza miki ne ko yau kika fara ganina ? ya fad'a a matukar tsawace bata San sanda ta sunkuyar da kanta kasa ba jikinta na d'aukar rawa can muryarta ta fito a hankali"ka..kayi hakuri dan Allah it's mistake "you're very stupid with that mistake ya sake magana a fusace yana furzar da iska mai zafi ."yadda ya kura mata Ido ya tabbatar mata da kallon tsana da kyama yake mata acikin ransa." "me ya kai ki kallonsa alhalin kinsan halinsa? "why why !!maryam me yasa zaki kallesa ? nan take taí blemimg kanta dan haka ta sake dukar da kanta kasa sosai ganin bai dauke idanunshi akanta ba dan tana jin yadda suke yawo a gabadaya ilahirin jikinta ta soma kokarin mikewa tsaye dan barin gurin mami ta tsaidaita tana zabga masa harara ya maida idanunshi kan nana hauwa da tsawar daya bugawa maryam yasa ta dawo da hankalinta Kansa , da idanunsa yayi mata alamar ta bar gurin tsam ta mike ta soma k'okarin bawa kafarta iska tun bai sauke zuciya akanta ba ta shiga uku " kema koma ki zauna babu inda zasu "Kai ba fa na son takura karka takura min yara da bakin rai da miskilanci , idan babu hali zo ka tattara ka wuce gidanka mu sakata mu wala Ina dalili wannan maseefa? "Idan dai kana guri shikenan yara basu da natsuwa da kwancinyar hankali ? wani irin daci rai mai mugun tsanani ya rufesa amman idan ba wanda yasan shi sosai ba ba zai gane ba muryarsa a kasalance yace "haba sweetheart wai mai yasa kike min haka ne ki dinga min fad'a a gaban wad'an nan premure din ? anyi maka fadan ai Kai ne premature din basu ba , kai ma ka daina hantarar yaran mutane, babu gaira babu dalili kasawa yarinyar mutane karan tsana "ni ne kuma pre mature ? yayi maganar zuciyarsa na tuttukin bakinciki tare da banka masu harara ai babu shiri suka nufi hanyar d'akinsu da sauri ." "eh mana meye marabunka da premature ? shekararka day day har talatin da takwas a duniya zaka da tara koma nace arbain amman har yanzu ka kasa ajiye iyali akarka shinka shiyasa kullum gaka nan baka san menene rayuwar muamula da mutane ba sai ta kasuwanci , da kayi aure ne zaka gane meye bambamci rayuwar muamula da mutane amman yanzu Kai da dan shekara shabiyar duk abu daya ne tunda bazaka qarar da abinda wanda yayi aure zai qarar ba." shiru kawai yayi yana kallon mami maganarta taso bashi dariya amman ya maze ya cigaba da kallonta ."Ka daina yiwa yarinyar nan maryam haka banaso wallahi bana Jin dadi ,"ai shiyasa nake ganin hadani daita babbar matsala ne dan ban san ta ina zan fara rayuwa da ..."ba wannan labarin na tmbyeka ba ka daina nuna mata wannan tsanar shine abinda nafi bukata ta katseshi ta hanyar fadar haka "ok to kice ta daina kallona haka bana son yawon kallo wallahi yana hassalani ita Kuma ta iya kallo kmr renon kauye " kai da wani idon ka kalleta da kasan tana kallonka ?ya dan kashe mata idonaa daya yana ciza gefen lips dinsa na kasa ." girgiza Kai mami tayi "Kai ko Allah yasa ka gane wallahi maryam zata sha aiki ,"sosai kuwa my sweetheart shiyasa naga gara abar hadin nan kar ta hadu da ciwon hawan jini da.."baka isa ba wannan auren fa ko mutuwa zakayi sai an daura shi kai wallahi idan kasa wasa ma mata biyu zan maka arana daya tayi mgnr tana danne dariyar ta ". nan take ya canza fuska sosai kallo daya zaka masa ka fahimci ransa ya gama baci "duk ranar da aka d'aura aurenka da maryam mussaman zan tasata gaba nayi ta bata hakurin zama da Kai dan Kai mai katoton hakuri irinta ce zata iya zama da Kai ." ya runtse idanuwanshi saboda bakincikin hadashi da maryam datake yi "bama ni zaki bawa hakuri ba nida za'a wa auren dole sai wata banza can ? ya karasa maganar a shagwabe kamar wani karamin yaro murmushi mami tayi sannan ta mike tsaye "kaga tafiyata tunda ka korar min yarana Kai ma ka zauna Kai kadai bazan zauna ba byn ta wuce ya mike daga kan kujera yana ciza gefen baki ya kwashe wayoyinsa ya nufi hanyar waje ." Ahankali yake tafiya cikin hasken daya haskaka haraban gidan ga securities na kai kawo acikin haraban gidan motsin mutun yaji a bayansa ya juyo a hankali kanin mahaifinsa alhj idres ya gani cikin farar jallabiyya hannunsa rike da jaridarsa ta gado a hannunsa dan sau dari zaka gansa to dole kagansa daita da alamun gurin shakatawa zashi dan gurin an kawatashi idan ka shiga Sam bazaka bambamce dare ne ko rana ba.dole mr ATA yaja ya tsaya domin rashin tsayuwarsa zai iya janyo masa tashin hankali dashi kasancewarsa shi din mutun ne mai zafi zuciya da son fad'a sannan baya daukar raini sai dai duk da wannan hali nasa yana dan shakkun mr ATA dan yadda yake saukewa mutane ruwan bala'i na babu gaira babu dalili baya masa haka." "baba qarami brka da dare ?" dake haka suke kiransa dashi haka zalika akwai baba babba wanda shi Ke bin mahaifin mr ATA " sannu Adam dan albarka barka ya fama da business da jama'a? "alhamdulillahi mun godewa allah " to Allah ya taimaka "Ameen ya fad'a ataikaice yana cigaba da tafiya "amm Adam ya batun sakon dan har yanzu ..? "na tura maka sakonka tun safe "to to shikenan Allah yayi wa rayuwa albarka Allah ya jikan mahaifinka ai kana kokarin ka kula da business dinka sannan ka kula da AGC ya fad'a yana qarasowa daf dashi suka jera tare yana masa magana kasa kasa "yauwa Adam daman akwai maganar da nake son muyi da Kai idan babu abinda zakayi yanzu muje gurin shakatawa muyi mgn ?" Yayi shiru na second biyar sannan ya motsa labbansa da kyar "babu abinda zanyi daman na fito na dan sha iska ne amman babu damuwa muje suka nufi gurin shakatawa suka shiga suka zauna a lokaci daya baba qarami ya numfasa kana ya kira sunan mr ATA "Adam bakaga zuwa yanzu ya dace ka ajiye iyali ba ?Mr ATA yayi shiru kawai yana kallonsa daman kuma yayi tunanin maganar aure zai masa , baba qarami ya gyara zamansa sannan ya cigaba da mgn ",ga yara nan acikin dangi me zai hana ka zaba a daura maka aure ?"still shiru mr ATA yayi kawai yana jinsa saboda bai san me zai ce masa ba ." can part din mami kuwa duk Maryam ta damu kanta akan abinda mr ATA yayi mata hawaye ne Shane shabe kwance a fuskarta ta rasa dalilin da yasa mr ATA ya tsaneta ita har a zuciyarta bata Kinsa ganin yadda yake nuna mata tsana ne wani lokacin take jin haushinsa amman tunda abun ya wuce duk yadda take tunani bazata cigaba da d'aukar wulakanci ba gara tasan abun yi zata tattara ta koma gidan iyayenta ta huta." ta dauko akwatinta ta soma hada kayanta ",wai meye haka Maryam ? "ke matsalata dake kenan komai damuwa menene abinda zai sa ki damu kanki byn ba tun yau kika San halinsa ba har da zaki damu kanki ?tayi saurin tarar numfashin nana hauwa'u "Haba sister koma menene bai kamata ba Kiri Kiri fa yake nuna min tsana kmr ba jininsa ba ni dai gaskiya na gaji Ina ganin lokacin yayi da zan tattara na koma Abuja "karki yi haka sister mami bazataji dadi ba ki rabu dashi shi da ba mazauni ba gobe ma tafiya zata iya kama sa" wallahi idan kika wuce nima bazan ji dadi ba sister mun Saba sosai idan kika tafi kika barni zan shiga wani hali "to ke me yasa baya Miki haka sai ni? ",waya ce miki? ba gashi tare ya koro mu ba nima da nake jininsa ya hada dani ,Allah ba ke kadai yakewa haka ba kowa ne sai dai idan bata hadoku ba ina ma tafiya ta kamashi ya tattara da wahalarsa ya wuce ya barmu mu shakata "da kyar nana hauwa'u ta rarrasheta ta fasa tafiya amman da tace gobe gobe zata wuce ." Mr ATA da kawunsa sun dauki lokaci suna tautaunawa sai dai bai sanar dashi hukunci mami akansa ba har sukayi sallama da sharadin nan kusa zai kawo masa matar da zai aura yana shiga d'akin ya ajiye wayoyinsa akan wani karamin stood ya cire kayan jikinsa ya saura daga shi sai farar vest da boxce suma ya ciresu yana shafa qirjinsa zuwa kasan mararsa har ya shiga bathroom ya sakarwa Kansa ruwa byn wasu mintuna ya fito yana goge jikinsa da towel byn ya gama ya tsaya gaban morrow ya d'auki turare ya feshe ilahirin jikinsa wannan wanka na kaida ne duk daren duniya kafin ya kwanta sai yayi tare da pest haka turare shiyasa idan ya tashi bacci zaka dauka yayi wanka ne dan tsab zaka gansa ,ya sauya wasu kayan zuwa na bacci farare sol masu taushi ya zauna a bakin gado ya d'auki remut ya qara karfin ac sannan ya ajiye ya d'auki na tv ya danna tashar aljazeera ya dawo ya zauna rigingine tare da lumshe idanunshi hoton princess dinsa ne yashiga yawo acikin idanunshi , bai san a wani duniyar take ba ."a hankali ya janyo bargo ya shiga ya lullu'be rabin jikinsa ya canza wutar d'akin zuwa dum light idanunshi na kan tv ko cikakken minti ashirin bai yi ba bacci mai nauyi ya daukeshi cike da mafarkin sarauniyar zuciyarsa , kmr Koda yaushe idan ya kwanta dole sai yayi tunaninta, yadda tunaninta ya zamemasa dole haka mafarkinta ya zame masa abincin ruhinsa kafin ya kwanta . yana kwance sai gata ta hau kan gadon cikin kayan bacci wanda shi da babu duk d'aya dan a fili ake ganin tsayayyayun nipples dinta ta yaye bargon daya lulluba ta tsura masa Ido a hankali ya bud'e lumtsatsun idanunshi akanta yana kallon fuskarta bai tsaya iya nan ba yayi kasa da idanuwansa sai kan nipples dinta dake tsaye cak ,wani irin yanayi ya tsinci kanshi me wuyar misaltuwa , runtse idanuwanshi yayi da suka sauya alokaci daya yana control din kanshi kafin ya bud'e idanunshi yaji tafin hannunta a fuskarshi zuwa chest dinsa tana shafawa tana lumshe masa Ido , yarinya ce karama da bata wuce shekara shabakwai zuwa shatakwas ba a yanzu sai dai Allah yayi mata baiwa da ba kowace mace yayiwa ba , qirjinta a cike suke bammmm da dukiyar Fulani ga shape wanda ya bayyana figure either dinta ga dara daran idanu masu dauke da wadatattun gashi Ido da gira , jin saukar hannunta a girjinsa tana murza kan nipples dinsa yasa gbdy ya susuce bai tsaya wata wata ba ya fixgota zuwa jikinsa ya rungumeta tsam yana sauke wani wahalallen numfashi da ajiyar zuciya yana shinshina wuyanta zuwa qirjinta "Ina sonki my princess kullum da tunaninki nake kwana nake tashi a ina zan ganki .?" Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 6. shiru tayi tana kallonsa tana sakar masa murmushinta wanda ke bayyana ainihin sahihin kyawunta da wushiryarta " am serious my princess Ina sonki da yawa ki fad'a min Inda zan ganki ? ya fad'a yana busa mata iskar bakinsa mai dumi tare da had'e fuskarsu guri d'aya suna shakar numfashin juna "kice min wani abu mana zuciyata na kwad'ayin Jin sautin muryarki Ina sonki dayawa Ina muradinki Ina qauarki Ina sha'awarki princess". shigewa jikinsa tayi sosai kmr zata raba jikinsa gida biyu suna shakar numfashin juna suna nan makale da juna sai ga saukar ruwan sama "it's raining princess lamme go inside you in this rain I really need you." nan take ya shiga romancing dinta cikin zafin nama yana kissing din wuyanta kafin daga bisani ya birkitota ta dawo kasansa ya koma samanta yana kallonta itama shi take kallo bakinsa ya Kai cikin kunnenta yana tsotsa yana zira harshensa ciki wani irin yanayi ." mika tayi ta sake shigewa jikinsa ,ta lumshe masa nata sumammun idanun tana sake shigewa jikinsa "sonki ya hau min kaina da yawa habibaty you're the best princess in this world ya zare rigar jikinta yayi filinging dashi ta saura babu komai ya had'eta da jikinsa tare had'e bakinmu guri d'aya har yayi nasarar cafko laulausan harshenta nan ya shiga tsotsa nishi yake fitarwa da iyakacin karfinsa kmr wanda yaci yaji sannan ya zare bakinsa yayi zaman dirshsn a gabanta ya kamo hannunta ya d'aura akan jijiyarsa bata d'auke hannunta ba haka zalika bata d'auke idanunta akanshi ba sautin muryarsa ya doki kunnenta "ki shafamin ta lumshe masa idanunta ya sake damke hannunta da joystick dinsa sosai "a hankali ta dinga shafa joystick dinsa tana laulaya kan tana had'owa da dick dinsa matsota yayi sosai ya sauke bakinsa akan nipples dinta yana tsotsa yana lasar wuyanta ita Kuma tana cigaba da shafa joystick dinsa dake sake mikewa tana fitar da ruwa ,hanyarsa yake k'okarin nema ta takure jikinta guri daya "a hankali ta Kai bakinta daidai saitin kunnensa ta soma rad'a masa magana cikin sanyayyiyar muryarta mai tsananin dadi da tsuma zuciya "banason abinda kake min ganika naxo yi kawai ba dan kayi wani dani ba ,da kyar ya cire bakinsa akan nipples dinta yana furta "wowww my princess sautin murya mai dadi amman karki ganni kawai ki kasance dani na har abada shine abinda nafi bukata yayi maganar yana sauke ajiyar zuciya ya sake rungumeta tsam tsam ajikinsa ya matseta har ta bud'e baki zatayi magana ya sake had'e bakinsu ya lullubesu da bargo tsawon lokaci suna tare a cikin bargo babu kaya ajikinsu yana romancing dinta sai juyata yake yadda yake so yana tambayarta sunanta ." "ki fada min sunanki my princess Ina son sani da Inda kike ki taimakeni ki fad'a min yana mgn yana kokarin shigarta sam taki yarda ya cigaba da kokarin shigarta yana cewa "plz my princess kiji tausayina yau kibani kanki Ina muradinki sake hade ka'fafunta tayi,ya sake manneta yana kokarin bude leg's dinta cikin kuka tace "ni ka sakeni ba dai zaka auri wata ka barni ba shine ni kake son na mallaka maka kaina ? cikin tashin hankali yace "no no it's not like that my princess Ina sonki kuma zan aureki babu wata mace da zan aura sai ke ,ke kadai ce mace agurina sauran matan duniya tamkar maza nake ganinsu babu macen da zan samu natsuwa daita sai ke Ina sonki Ina sha'awarki ki taimakeni ki barni nayi ya k'arasa mgn yana hade bakinsu ya kamo lip's dinta itama ta cafki nashi. sosai Adam yake juyata yana Kiran my princess ......." qarar wayarsa ce ta farka dashi daga mafarkinsa a firgice ya bud'e idanunshi yana fidda numfashi ya zauna a tsakiyar gadonsa yana kallon jikinsa gbdy ya hada gumi sharkaf tmkr wanda akayiwa wanka jiyayyarsa kuwa ta mike sambal tana haniniya duk ruwan sha'awa ya gama bata masa wando numfashi ya sauke yana dafe goshinsa da hannu daya "ya rabbi har yaushe zan daina ganinta a mafarkina ?ya Allah idan yarinyar nan mutun ce kuma tana raye Allah ka bayyana min ita a duk Inda take na samu natsuwar zuciya , jiki a sanyaye ya mike ya shiga bayi yayi wankar sarki dan ya samu natsuwar zuciya ya d'auro alwala ya fito ya sanya jallabiyya fara sol ya kashe tv sannan ya karasa Inda abun sallarsa yake ya tadda ikama yana sallah qirjinsa na dokawa ... Ya dade yana nafilfili da rokon Allah ya kawo masa sauki ,bai koma bacci ba sai da yayi sallah asuba har karfe goma bai tashi ba shigowar hjy zulaiheart uku duba shi yana bacci na hudu ne ta iskeshi kwance idanunshi biyu amman bai tashi ba ta k'araso ta zauna a bakin gado tana shafa gefen fuskarshi "lafiyarka adam baccinka yayi tsawo yau ko baka jin dadi ne ?motsawa yayi ya daura kanshi akan cinyar mahaifiyarsa zuciyarsa cike da rauni yana fatan haka ya zamo Silar samun sausauci , "sweetheart ..."! ya kira sunanta a raunane "menene adam? " fada min meke damunka ?duk ta rude tana son sani halin da danta yake ciki "zuciya ta na cikin rudani sweetheart soyayya na kikiniya dani ina son yarinyar Nan sosai sai dai ban san Ina zan ganta ba , ta shiga zuciyata zata iya sawa ki rasani "naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana riko tafin hannunsa cikin nata ta rike gam "Allah bazai sa ba sai naga aurenka da ya'yanka " yaushe zan ganta sweetheart kullum sai nayi mafarkinta ?har tsoron runtse idanuna nake saboda dole sai tazo .tausayinsa ya kamata ita dai Allah yasa ba aljana bace ta aure mata da "wata rana zanganta ko Sweetheart ?yayi maganar yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa. "Adam ba dukkanin mafarki ke zama gaskiya ba "Ina ji ajikina gaskiya ne sweetheart Kuma lokacin haduwarmu daita ya kusa tunda har tayi min magana a daren jiya abinda bata taba min ba ,naji sautin muryarta , tana da sauti mai zaki da rikitarwa "shikenan ya Isa ni mahaifiyarka ce zan tayaka da addua idan mutun ce Allah ya bayyanata idan aljana ce Allah nesantata da Kai amman ka kwantar da hankalinka ka aure maryam zata Saka zuciyarka natsuwa zata mantar da kai komai,zakayi alfahari daita "ya runtse idanuwanshi gam yana Jin zafin furucin mahaifiyarsa "Ina jin kunyar auren maryam sweetheart wallahi bansan dalili ba gani nake kmr abun kunya ne na aureta "Babu wani abun kunya yarinya ce mai sauki hali "Kuma bazata damu ko ka aureta sai ka qara da princess dinka ta fad'a tana shafa sumar kanshi "wannan ai ya zama dole shiru tayi tana jinjina girman alamarin ta fad'a masa haka ne ba dan ranta yaso ba domin ita dai maryam ce cikar burinta ,kuma koda zai hadata kishi da wata ya zamanto ita ce gaba da kowa a zuciyarsa naunayen ajiyar zuciya ta sauke muryarta a sanyaye tace "shikenan tashi ka shiga wanka ga break can na jiranka Allah ya jishemu alkhairi "ya mike da kyar rike da kugunsa ya shiga bathroom ita Kuma ta fito zuwa parlour. Karfe daya daidai ya shirya sai dai ya kasa fitowa zuwa falon mahaifiyarsa saboda baya son haduwa da maryam shi Kansa Yana mamakin zazzafan soyayyar da yakewa princess wanda ma'abota so da shauki ne kawai suka San zakinta yana son yarinyar kamar ranshi, soyayyar da yake mata mai tafiyar da ruhi ne Ina ma ya ganta a duniyarsa ta zahiri da shi kadai yasan irin so da tattali da zai mata."sauke numfashi yayi da karfi "anya kuwa zaka iya ?zaka iya nuna mata soyayya a fili ?ban yarda zaka iya nuna mata tarin qaunar da kake mata ba saboda kai din mutun ne mai jin kai zuciyarsa ta fad'a masa haka ya furzar da iska mai zafi yana shafa goshinsa yana girgiza kai ." a natse ya mike ya goya hannuwansa duka a bayansa yana zagaya dakin numfashi kawai yake saukewa ya dan tsotsa keyarsa "Ina da tarin kudi Ina da tarin yan'uwa Ina da fada aji a kasar nan Amman duk na banza tunda duk sun kasa samammin abinda zai bawa zuciyata natsuwa da zaman Lafiya . karfe daya daidai na washegarin ranar ya bar lagos zuwa kasar togo sai dai a can din ma kasa tabuka komai yayi haka ya wuni ya kwana yana tunaninta yana son zuciyarsa ta bar tunaninta amman abun ya cutura duk saukar numfashinsa tafe yake da tunaninta yana son ya samawar kanshi natsuwa amman hakan yaki samuwa yayi shiru kawai yana kallon saman dakin da yake kwance yana tunanin abinda ya kamata yayi babu abinda ya zoma zuciyarsa a wannnan lokacin kamar kwadayin sigari abinda ya dade bai sha ba hassalima baya sha sai yana cikin damuwa irin wannan shiyasa bazaka ta'ba cewa yana sha ba dan bai nuna a skin dinsa ba ." "a hankali ya qarasa inda akwatin kayansa yake har zai bude ya tuna baya yawo dashi dan haka yaja dogon tsaki yana mai dafe goshinsa ya koma da baya da baya ya zauna akan kujera jagwba yana murza goshinsa wayarsa dake gefensa ya soma ringing ya kai hannunsa ya lalubo ya dauka ya d'an bude idanunshi kadan ya duba trucaller ne yasa ya gane ko wacce ke kira direct call ya dan ja saki yaki dauka munubiya ce diyar alhaji madu tsohon shugabansa nigeria school mate dinsa ce tare sukayi karatu a chaina ." ta dade tana son shi Amman shi Sam baya tata gbdy duk hanyar da zata hadasu ya kulleta yanzu ma bai San Ina ta samu wanna number nashi ba ." Byn second biyar wani Kiran ya shigo ganin me Kiran ya dauka yayi shiru har sai da yaji yace " hello sir ! sannan yace "Ahmed ykk ? ya fada a kasalance "okay shikenan zan turo maka zuwa anjima Jin yanayinsa ahmed ya fahimci yana cikin damuwa dan haka ya dinga jansa da hira ,Ahmed yana cikin wad'an da Mr ATA ya taimaki rayuwarsu ya hadu dashi a bakin titi Antoni mota ta bugeshi Mai motar ya gudu ya barshi shine ya taimaki rayuwarsa daga rana ya Maida shi tamkar danuwansa har ya samammansa aiki akarkashinsa saboda ya gama karatu aiki ne ya zama matsala Kuma shine babban a d'akinsu ga kannen da iyaye , agarin nema aikin ya hadu da wannan accident din Mr ATA na qaunar ahmed sosai babu abinda baxai iya masa ba dan jinsa yake tamkar ciki daya suka fito zuciyarsa a cunkushe yake da damuwa amman sai da Ahmed yayi sanadiyyar dawo dashi daidai dan shi mutun ne me abun dariya da barkwanci haka nan ya tsinci Kansa da Jin dadi Kuma yasan Hakan nada nasaba da wayarsa da ahmed ya sauke wayar yana farinciki ." ****** Tun daga ranar da'aka tsare hadiza police basu sake tuntubarta akan komai ba, illa bincike da jami'an tsaro suke babu dare babu rana har suka samo wani abu daya dan danganci fadan hadiza da sadear ,macen police ce ta taso hadiza gaba zuwa d'akin bincike ta zauna cike da tsoro "inspector abbas kunna mata voice dinta taji da kunnenta nan take aka kunna "shegiya karuwa muguwa mai fitsarin kwance Ina dalili da duk saurayin da zanyi sai ya dawo yana sonki da zarar Kinga nayi saurayi shige da fecenki bai karewa har sai kin d'auke masa hankali, abinda zan bari ki gani da idanunki sai kinyi mamaki , wallahi wannan yayan naki sai ya tausaya miki sai yace bai sanki ba, ke kadai kike da kan maza wallahi idan baki shiga hankalinki akan Umar ba zan siyawa yan iskan unguwar nan kayan maye su cire miki abinda yake ciki idanunki , ke wannan yarinyar anyi tsinanniyar me nayi miki ? shegiya mai ruwan Ido muje neman aiki tare dake ke aka d'auka yanzu kuma Umar dake sona kin shiga kin fita kin d'auke masa hankali sadear ki shiga hankalinki dani dan wallahi zan iya kasheki zan kasheki na kashe banza danuwanki zayi kukan rashinki ki shiga hankalinki bani fada kune kuke son maidani mahaukaciya Kinga wannan Umar wallahi muddin kika ce zaki kwace sai dai kije lahira idan baki tsaya matsayaki ba zan kasheki , idan ban kasheki ba kuwa abinda zan miki zaki sha mamaki , idan zakiyi bacci karki saki jiki dan zan iya zuwa na tsoka miki wuka tunda voice ya fara babu sautin muryar sadear yansanda suka zuba mata Ido a zaune dake tana kuka tare da danasani "ko akwai abinda zaki kare kanki dashi ?tabbas muryarta ce Kuma munyi haka daita amman har ga Allah bani na kasheta ba kawai dai na fada mata haka ne dan na bata tsoro "daya daga cikin police yace "a'a hadiza daman haka halinki yake kowa Kuma ya sheidake da son fada , ko kinsan wannan wukar da kika yi kisan daita an ta'ba kashe wata yarinya dashi a gra diyar alhaji jamilu ?nan hadiza ta sake rikicewa ta gigice hawaye na zubo mata , "wallahi ban san komai ba gara ma ki fada gsky dan bawa hukuma saukin bincike abu na karshe ki shirya daukar lawyer da zai kareki nan aka sake tasa keyarta zuwa cikin cell ..yadda take kuka sai ta baka tausayi ." da yammacin ranar asabar zaune maryam take a kusa da aunty shahida da aunty khadeja tana sauraronta aunty shahida ta kalleta a natse tayi murmushi ya naga duk kin firgice ki natsu please "kinsan abinda yasa nake ta son muyi magana dake tun last week ?maryam ta girgiza mata Kai kawai tana tattara dukkanin natsuwarta da hankalinta gareta "mun yanke shawarar za'a had'a aurenku da Adam "take gaban maryam yayi wani irin dokawa ya fad'i ta waro idanunta sosai zuciyarta na tsinkewa cike da matsanacin tsoro take duban duban aunty shahida da aunty khadeja tana jin kamar ba abinda ya fito daga bakinta ba kenan ,maimaitawar da aunty khadeja tayi ya tabbatar mata da lallai gsky taji "wani Adam din Kuma aunty khadeja ? tayi tambayar jikinta na rawa hantar cikinta na kadawa "a'a Adam dai na gidan nan da kika sani dashi za'a had'aku aure tunda yaki fito da mata mu Kuma mun gaji da zamansa haka " aunty shahida aunty khadeja kuyi hakuri ni gaskiya bana sonsa da aure ........" Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page7 ........" Cikin mugun firgici da tashin hankali aunty khadeja da aunty shahida suka yi shiru gabad'aya suna kallonta cike da sansar fargaba da tashin hankali "me zasu fad'awa mami data d'auki soyayyar duniya ta d'aurawa aurensu ? " ita kam Maryam kasa kallon cikin kwayar Idanunsu tayi ta takure jikinta guri daya tayi kasa da kanta idanunta na ciccikowa da ruwan hawaye gbdy ta kasa kwakwaran motsi a zaunen da take , wani iri take ji a gabadaya ilahirin jikinta ,sai lokacin taji wani irin kunyarsu tayi mata diran makiya . ji tayi kamar ta tashi ta bar gurin sai Kuma taga hakan ba daidai bane ,basu cancanci haka daga gareta ba ,zasu d'auka raini ne dan haka ta cigaba da zama zuciyarta na tsalle da bugawa wasu hawaye masu zafi suka samu nasarar zubowa akan kuncinta tasa hannu ta goge wasu na sake zubawa ." Sanyayyaye numfashi aunty shahida ta sauke tana gyara zamanta tare da janyo maryam zuwa jikinta tasa tafin hannunta tana share mata hawaye "kukan ya isa haka tunda baki son shi shikenan zamu san yadda zamu fahimtar da mani amman da zakiyi hakuri kiso AD hakika maryam da kin san kin dace miji na gani na fad'a ba dan AD ya kasance dan'uwana ba ,duk mace zata yi alfahari ya kasance miji agareta kuma uban ya'yanta ki tsaya kiyi tunani maryam karki yanke hukunci cikin tsoro da tashin hankali ". Cikin tsananin kuka da tashin hankali maryam tace "a'a aunty shahida babu wani tunani da zanyi akan ya Adam dan yafi qarfina ta kowani bangare ban Isa na tsaya Inda yake ba bare na kasance mata agaresa ta Ina zan soma rayuwar aure dashi aunty shahida ? "Ta Ina zan fuskanci mutumin da bai qaunar ya bud'e idanunshi ya gani ? "duk duniya idan akwai macen da ya Adam ya tsana to nice "Ina zan kai tsoron da nake masa har nayi rayuwar aure dashi ? uwa uba baya Sona ta yaya kuke tunanin nima zan soshi har naso zaman aure dashi ?" wallahi aunty shahida ni tsoro ma yake bani ban ma san ta ya zan fara rayuwar aure dashi ba , da zarar nagansa bana samun natsuwar zuciya har sai na nisanta kaina dashi to ta yaya kuke tunanin zan iya zaman aure dashi Koda Ina son shi bare bana masa soyayya irin ta aure sai ta yan'uwantaka ?" " ni yanzu tashin hankalina mami wallahi bazan so taji wa......."kuka yaci karfinta ta kasa qarasa maganarta "dan wannan karki damu Ina da tabbacin da zarar kunyi aure shikenan maryam ,bazai nuna miki komai ba sannan zaki daina jin tsoronsa inshallahu zakiyi farinciki a gidansa. "maryam ta zumburo baki "Allah aunty shahida bazan iya ba shine miskilanci shine girman kai , uwa Uba zuciya idan na auri ya Adam bazai barni na rabi Inda yake ba kullum zan tabbata cikin gallazawarsa wa zai ceceni a hannunsa ? ta Kalli aunty khadeja hawaye na gangarowa akan quncinta "yan'uwana ku taimakeni karku bari a had'a auren nan , ban rainaku ba sannan ban ki shawararku ba amman abar wannan maganar yanzu baku ji yadda nake jin zuciyata ba ,ji nake kamar zata fashe tsabar tashin hankalin jin maganarku , Kalli yadda jikina ke rawa aunty khadeja Allah bazan iya ba ta k'arasa maganar tana sake rushewa da wani sabon kuka." Aunty khadeja wacce tayi shiru tana sauraronsu tace " duk na fahimceki Maryam amman yana da kyau mutun yayi dogon nazari akan duk abinda ya kunno kai cikin rayuwarsa zamu baki lokaci kiyi tunani sannan kiyi istahara ..?maganganu masu sanyi da kwantar da hankali aunty khadeja tayi amfani dasu gurin son janyo hankalin maryam duk da a rikice take amman tana fahimtar komai dake fita daga bakinta ,naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana mai kallon aunty khadeja sannan taja gindi zuwa Inda take ta riko hannunta d'aya cikin nata ta damke gam jikinta na sake d'aukar kyarma muryarta a raunane tace "aunty khadeja bazan iya aurensa ba bari ma na fada muku gaskiya akwai wadan da suke sona sosai ku bari ya nemo matarsa a waje zai fi zame mana alkairi ......" duk yadda sukayi daita ta fahimcesu taki sai faman kuka take tana basu hakuri ganin yadda ta rikice sai kuka take tana rokonsu tana juya Kai yasa suka hakura da batun tare da sallamarta da kyar ta mike tsaye tana layi saboda juwar dake dibarta ta bar parlour, a tare aunty shahida da aunty khadeja suka Kalli juna suna sauke ajiyar zuciya " ban ta'ba tunanin maryam zataki amincewa da wannan had'in ba ,na d'auka zata fi kowa farinciki da murna zata kasance matar AD duba ga yadda naga 'yammata na maseefar son shi da son aurensa inji cewar aunty shahida "ai abun ba daga nan take ba aunty abincin wani gubar wani kuma ma ni banga laifinta ba shi kasan AD matsala ne bare a kai ga halin miskilancinsa aunty khadeja ta fad'a tana jan tsaki " bayan wannan miskilanci nashi bashi da wani aibun da zaa ki aurensa gaskiya kawai dan bata son shi ne abar zance zuwa wani lokaci sai mu fahimtar da mami . "Haka ne amman ya kamata ki kirasa ki fad'a masa ba'a son shi ko ya dan rage jijji da kai da mislinci da nuna fad'i da Isan da yake "yanzu kuwa zan sheida masa aunty shahida ta fad'a tana ciro wayarta daga cikin handbag dinta kira d'aya ya katse ya biyo byn Kiranta "kazo yanzu muna parlour'n mami na uku , tana gama fad'ar haka ta katse Kiran tana jan tsaki dan tasan bancin halaiyan da yake nunawa maryam da babu yadda za'a yi takisa ". maryam kuwa tana fita d'akinsu ta shiga ta zube kan gado tana kuka sosai har da shesheka tana jin rashin dadin kin amincewa yan'uwanta da tayi , ko babu komai yaci darajansu agurinta ta amincewa aurensa "mai yasa na ma su aunty shahida haka ?mai yasa bazan so zabin su ba kuma jininsu da suka fi qauna akan komai ?" hakika ban kyauta ba na yiwa yayar mahaifina butulci da yan'uwana sam basu canci haka daga gareni ba "why why maryam why do you do this to them ?tana cikin wannan halin nana hauwa'u ta fito da sauri daga bayi dan sheshekar kukanta ne ya hankaltar daita ganin yadda take kuka kamar wacce aka aikowa da sakon mutuwa yasa ta k'araso da sauri ta hau sama gadon tana mata magana cikin tsananin tashin hankali "menene marsi ? dan wani loakcin da haka take kiranta mrym ta sake fashewa da wani sabon kuka zuciyarta na zafi da qunci banci tsakaninta da nana hauwa'u basa boyewa juna komai tabbas da bazata fad'a mata ba zata boye wannan maganar ta barwa kanta ita kad'ai tunda tasan su aunty shahida ma bazasu fito da maganar ba . sheshekar kukanta ya qara dagawa nana hauwa'u hankali jiki a mace ta kamota ta rungumeta tsam ajikinta itama ta fara hawayen tausayin yar'uwata duk da bata san dalilin kukanta ba a hankali ta soma jin sautin muryarta cikin kuka "na shiga uku nana hauwa'u na kasa yiwa yan'uwana abinda ya kamata na kasa bin umarninsu nasan zasu ji babu dadi a ransu tayi mgnr hawaye na gangaro mata ...." "menene abinda kika kasa sannan su wani yan'uwa kenan ? ta fad'a tana sake rungumota jikinata' kiyi hakuri ki natsu marsi ki fahimtar dani abinda ke faruwa "naunayen ajiyar zuciya ta sauke sannan tayi mata bayani komai cikin muryar kuka tana mai zare jikinta daga nata ta cusa cikin tsakankanin qa'fafunta tana sheshekar kuka tare da kamkame jikinta . Shiru nana hauwa'u tayi a matukar tsorace tana kallonta tana maimaita maganarta kafin daga bisani ta motsa bakinta ta soma magana a zafafe "hakika babu aibu a maganarki sister tunda shima bai sonki kema bai dace ki so shi ba amman wani hanzari ba gudu ba maryam nayi noticing ba ya Adam Kawai ne bakya so kowa ne bakyau qaunar yace yana sonki dan duk wanda ya nuna yana sonki gocewa kike".ta d'ago a hankali ta Kalli nana hauwa'u da take magana "kin tsareni da idanu ai gaskiya na fada aure fa rahma ne yana d'aya daga cikin dokokin Allah da manzonsa cewar aso aure Kuma a girmama shi me yasa ke bakya so ? Kalli yadda abbas da anás suke haukan sonki kmr zasu mutu byn su ma akwai wasu amman kullum wulakanci da tozarci ke shiga tsakaninku ,ki duba lamarina maryam kad'ai ya isheki ishara mutun nawa suka ce suna sona a rayuwa ? ." Shiru maryam tayi tana kallonta hawaye na tsiyayowa daga kwarnin Idanunta "me na rasa ajikina ko a tare dani amman har yanzu shiru babu wanda yace yana sona ko acikin family's bare maganar aure ? bamu da wani lokaci maryam a shekarunmu na talatin a duniya ,idan akace babu lokaci ba komai ake nufi da hakan ba illa mutuwa ake magana domin zata iya zuwawa mutun a kowani lokaci ,ni dai shawarata anan kiyi addua abinda yafi zama alkhairi a tsakaninku da ya Adam Allah ya zaba miki ba kuka ba dan duk yadda zaki ki aurensa idan Allah ya qaddaro mijinki ne dole sai anyi ta qarasa mgnr tare da riko hannuwanta duka cikin nata tana kallonta a sanyaye kana ta cigaba da magana "kina da sa'a marsi arayuwarki da har akayi tunanin a had'aki aure da yaya adam byn akwai tarin yammata acikin danginmu wad'an da nake da tabbacin da sune aka nemi a hadasu dashi da tuni an wuce gurin." " hakika mami ba qaramin qauna take miki ba , ba dan ya Adam yana dan'uwana ba yana da kirki daidai nashi marsi ,nagarta ga kyawawan halaiya da kyakkyawar zuciya illarsa dai rashin son magana da mislinci da km tsanar da yake nuna miki byn wannan bashi da wata aibu da za'a kishi , idan kika auresa zaki zamo matar da babu kamarta acikin matan duniya ,kema kuma haka ne kina da halaiyan da baza'a ta'ba barin kije ki auri wani ki barshi ba ." "hankali nana hauwa'u ta dinga kwantar mata da hankali har kukanta ya tsaya ta qura mata Ido tana sauke ajiyar zuciya "ki saki ranki please idan ba kina son nima na shiga cikin damuwa ba "murmushi maryam ta sakar mata tare da goge hawayenta "yauwa ko ke fa matar yayana inshallahu ta fad'a tana mikewa ta bar d'akin mrym ta kwanta lamo akan katifa tana sauke numfashi sama sama tana tunanin mafuta zata amince ko kuwa zata tsaya akan ra'ayinta ne ?" A parlour hajiya zulaiheart ya samesu zaune sunyi shiru kowannensu da abinda yake sakawa a cikin ransa , yayi sallama a ciki kmr baya so ,suma aciki suka amsa masa kamar yadda yayi dan gbdy haushinsa aunty khadeja take ji dan gaisuwar da yayi masu aciki ma bata amsa ba shima bai damu daya sake gaishesu ba dan ba kasafai yake son gaisuwa ba hasalima yawon gaisuwa na cikin abinda ke motsa zuciyarsa "ya k'araso cikin sanyin jikin nan nasa ya zauna akan kujera mai zaman mutun d'aya ya d'aura kafarsa d'aya akan d'aya ya fuskancesu batare daya yi magana ba ." gyaran murya aunty shahida tayi kana ta soma mgn "burinka ya cika AD domin kuwa maryam taki amincewa da aurenka juyin duniya munyi daita tace bata sonka bata ga abinda zatayi da aurenka ba shikenan sai hankalinka ya kwanta ka zuba ruwa a kasa kasha tunda kai ma alal lalurati zaka aureta ba dan kana sonta ba , amman kasan da sani bazaka cigaba da zama haka ba dole ka fito da mata Kuma cikin wannan lokacin kayi aure dan kwancinyar hankalin mahaifiyarmu .." ban san dalilin da yasa kake kin yarinyar nan ba batare da wani huja ba wallahi sam banji haushinta ba kaso mai sonka haka zalika Kaki mai kinka inji cewar aunty khadeja wacce ta k'arasa maganar cikin tsananin fushi tana jan tsaki a fili wani mugun kallo ya watsa mata mai had'e da harara yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa , ta kawar da kanta gefe tana zuba tagumi ." Shiru kowannensu yayi bayan sun gama zayyane abinda ke ransu shi kuwa yafi minti ashirin yana zaune zuciyarsa na wani irin bugawa batare da yace uffan ba kafin daga baya ya motsa lip's dinsa a hankali "sweetheart tasan da wannan maganar ?ya tambaya yana kafesu da Kyawawan idanunshi masu matukar kyau da bugar da zuciya sai dai a yanzu kallosu kawai zai sa ka fahimci tashin hankali da balain dake cikinsu "bata sani ba amman dole zata sani Kuma a yanzu "A hankali ya dinga girgiza kafarsa d'aya yana cizan lip's dinsa na kasa yana maimata Kalmar da aka fada masa mrym tace " bata sona ? wannan karon a fili ya fad'a yana kallon aunty shahida zuciyarsa na zafi da quna da tuttukin bakinciki mara misaltuwa ,kai tsaye tace "tabbas abinda ta fad'a mana kenan kai daga gani ma tana da wanda take so....."stop aunty shahida karki fad'a min haka mana taya zatace bata Sona?" wacece ita dan ubanta da har zata ce bata son Adam Tariq Abdullah ?"mace mai daraja da zuciya mai kin wanda yake kinta" ta bashi amsa da haka tana zabga masa katuwar harara." murmushin gefen baki yayi wanda yafi kuka ciwo yana girgiza Kai "impossible babu wannan macen a fad'in duniya da zata ce bata son ni Adam wallahi ta raina muku hankali ne sannan tayi balain rainaku ni ko giyar wake ta sha bazata ta'ba fada min haka ba , numfashi ya sauke a maganarsa ta karshe sannan ya mike tsaye ya zuba hannuwansa duka cikin ajihun wandonsa ya soma taku kamar baya son taka kasa yana k'okarin barin parlour'n a matukar fusace har ya Kai bakin kofar fita ya tsaya cak batare da juyo ba "abar maganar nan a tsakankanimu banason sweetheart tasan komai zan san abunyi .." "Da dai ya fiyye maka ka ajiye wannan shegen girman kan naka ka fuskanceta da kanka wata Killa zata yarda "inji cewar aunty shahida " ai ni idan na fuskanceta umarnin kawai zan bata Kuma dolenta tabi umarnina koda kuwa mutuwa zatayi yana gama fad'ar haka ya k'arasa ficewa daga parlour'n bai tsaya jin abinda zata ce ba . girgiza Kai sukayi a tare "kinji ba aunty , kinji abinda yake cewa ko ?"wato shi bazai rusunar da kai ba, Komai ta karfi zai yi byn ita mace yar rarrrashi ce ." Allah dai ya shirya AD yasa ya gane kuma ya wanke masa wannan zuciyar tasa aunty shahida ta fad'a . bedroom din hajiya zulaiheart suka shiga suna qoqarin danne damuwarsu dan karta fahimci komai a hankali suka dinga nuna mata babu wata matsala sunyi mgn da maryam kuma ta amince "masha Allah "Kai alhamdulillah amman naji dadi Allah yayiwa rayuwarsu albarka wannan aure Ina son shi Ina qaunarsa Ina farinciki dashi yanzu sai a sanar da baba babba shi kuma ya nemi sauran yanuwansa aje neman aurenta gurin saidu ko ? "wannan haka ne amman ki dan tsaya tukun kinsan halin 'yan kayanki muna son ya dan saki jiki da mrym din su samu fahimtar juna sai ayi maganar aure hjy zulaiheart ta gyada Kai tana murmushin jin dadi "wannan ma shawara ce mai kyau Allah ya daidata tsakaninsu dan mrym bani da matsalata daita , nan sukayita biyewa hjy zulaiheart dan basa son tasan abinda ke faruwa ta shiga damuwa , domin kuwa muddin tasani akwai gagarumin tashin hankali a gidan ." "Yana shiga d'akinsa zariya ya soma yi daga farkon d'akin zuwa karshe ya kasa zama kamar wanda yayiwa sarki karya can ya tsaya cak yana jan tsaki har lokacin mamakinta yake dan yasan aunty shahida baza ta'ba fad'a masa qarya ba daya qaryatata cikin zafin nama ya soma balballe botiran gaban farar rigar dake sanye ajikinsa ya cire sannan ya zame ash three quarter din da yake sanye dashi ya shiga toilet yana sake jan tsaki ya kunnawa Kansa ruwa yana jan numfashi da rarrashin zuciyarsa tare da son karyata zuciyarsa akan jin haushin maganar yarinyar shiru yayi ruwan na sauka ajikinsa " dole yana bukatar saita kanshi dan ya samu damar tarwatsa zuciyarta cikin ruwan sanyi ban da ma hauka da jakanci irin nata Ina ita Ina shi Adam ai sai dai darajan iyaye ? shi da yake da mace kamar princess yarinyar da ta samu kyakkyawan mazauni a zuciyarsa me zai yi da mai jiki kamar na turkey, abinda batasani ba da abashi mace irinta gara ya kare rayuwarsa babu aure yana cikin toilet ya dinga jin sautin qarar wayarsa bai fito ba sai daya samu natsuwa sannan ya fito d'aure da white towel iya gwiwarsa ya tsaya gaban mirrow yana karewa kanshi kallon tsab sannan ya sauya kaya riga armygreen da wando baki kafafunsa sanye da takalmi fari sol ya zauna shiru akan kujera duk yadda yaso ya cire damuwar rashin son shi da'akace mrym batayi abun ya cutura wani irin zabura yayi ya mike ya kwashi wayoyinsa ya fito zuwa haraban gidan Inda security da escort dinsa ke faman safa da marwa suna ganinsa suka hau kikiniyar bud'e masa bayan mota suna furta" barka da fitowa ranka ya dade ya shiga ya zauna fuskarsa a hade batare daya amsa ba direbansa yayi saurin shiga mazaunin direba "aka bude makeken get din gidan ,motor daya da direba da wasu escort sukayi gaba sannan motar da Mr ATA ke cikin sai daya a bayansu suka bar gidan suna hawa kan titi kira ya shigo wayar direba sai daya nemi izini agurin A Mr ATA sannan ya d'auka mgn daya ya katse kiran Tare da tmbyr mr ATA"ranka ya dade Ina muka nufa ne ? "gdn mb ya fada ataikace yana kallon gefe titi zuciyarsa na zafi ,tafiya mintuna kadan sukayi suka k'araso ikeja gra a kofar gidan suka ja suka faka suka yi saurin firfitowa suka zagaye motar da Mr ATA yake ciki ,daya daga cikinsu ya bude masa murfin mota , masu gadin gidan muhd bello na ganinsa suka fara rawar jikin da kokarin kawo gaisuwa. " Kai tsaye ya shiga gidan batare da neman iso ba waje ya samu a rumfar dake ajiye da kujera na alfarma dake haraban gidan ya zauna ya d'aura kafarsa d'aya akan d'aya wannan ya rigada ya zame masa jiki no matter how ya zauna sai ya d'aura kafa daya a kan d'aya , hannunsa daya ya d'aura a kan table yayinda wayarsa ke manne da kunneshi yana neman layin MB cikin kankanin lokaci ya bayyana a gabansa ."sai da gabansa yayi mugun bugawa hankalinsa ya tashi da ganin yanayin Mr ATA , ya zauna kusa dashi yana kallonsa "Lafiya friend na ganka haka kmr kana cikin damuwa ?" shiru yayi masa zuciyarsa na zafi da tafarfasa kmr zata kama da wuta "please talk to me friend what's wrong with you ?"yin duniya mr ATA yaki magana shiru Shima yayi yana kallonsa zuwa sanda mai aikinsa ta k'araso rike da tire dake d'auke da ruwa da lemuka masu sanyi tun kafin ta k'araso ya amsa a hannunta dan yasan yadda mr ATA ya tsani ganin fuskokin masu aiki ya ajiye akan table ita Kuma ta juya da sauri .ta kasan idanunshi yake kallon yadda take daga ka'fafunta haka nan ya tsinci kanshi da kallon every step of her zuciyarsa na quna ." MB ya tsiyaya masa ruwan ya mika masa "Kar'ba ka sha ka dan ji sanyi ATA ya numfashi ya sauke numfashi kana ya nuna masa kan table "ba ruwa nazo sha ba MB wai har ni wanan stupid monkey din zata ce bata so ......?"yayi maganar yana nuna qirjinsa da d'an yatsansa . a matukar firgice MB yace "who's she ?"wannan monkey revenble person din mana har ni zata ce bata so? " is a lie she just say it "ka natsu plz nifa ban ma fahimceka ba amman duk da haka nasan babu macen da zata ce bata sonka "wannnan yar iskar yarinyar diyar kanin sweetheart dake fama da danyen jiki kmar daga alhalin china aka samota yayi maganar a tsawace yana dukan table din gabansa nan take tire da glass cup suka tarwatse MB bai tsaya bi ta kansu ba ya riko hannuwansa duka cikin nashi dan gbdy zuwa yanzu ya fahimci ko wa yake nufi "calm down ATA ba fushi yakamata kayi ba soyayya haka take kayi hakuri ka natsu musan abunyi tunda kaji kana sonta yanzu shawo kanta bazai yi mana wa......" MB yayi saurin katse maganarsa sakamakon wani mugun kallon da ATA ya watsa masa yana zare hannuwansa dake cikin nashi "nace maka Ina sonta ne ? MB yayi saurin girgiza masa kai alamun a'a "to me yasa kace Ina Sonta ?wai naga kamar ka damu ne" "to bana Sonta kuma har abada bazan sota ba Koda kuwa tazamo mata agareni wallahi bazan sota ba kai bancin darajan sweetheart bazan ta'ba iya aurenta ba, bugu da kari ni mallakin princess ne ba kowace mace ba ,Ina son yarinyar nan MB Ina zaka nemo minta ?na saka 50 billion ga duk wanda ya nemo min ita ka taimakeni abokina ka tayani nemota wallahi muddin na auri yarinyar nan zan cutar da zuciyata sannan zan cutar da yarinyar mutane dan bana son mace irinta bazan yi mata adalci ba bazan iya italic ba ." "Is okay ATA Ina iyakar kokarina wallahi amman zan qara ya kife kanshi akan table kmr wani karamin yaro zuciyarsa na zugi da rad'adin bakinciki "kayi hakuri friend ka sanyaya zuciyarka maryam bazata kika ba sai dai ta furta hakan ne adalilin yadda kake mata amman ni zan sameta muyi magana kune da kune da fahimta nasa zata fahimceni km zata yarda da au.. ."karka yi MB ka barta kawai kar Allah yasa ta amince "no no !! baza'a yi haka ba ai ba saboda ita ba darajan sweetheart zata ci, kasan yadda ta damu kayi aure , hakuri kawai zakayi a shawo kanta " ai bana sonta MB , ta'ba kaji yadda qirjina yake bugawa ,km yana bugawa ne duk akan yarinyar mafarkina tunda na fara mafarkinta ban sake samun natsuwar zuciyata ba burina na ganta na mallaketa " yayi mgnr yana furzar da iska tare da kamo hannun MB ya kai daidai saitin zuciyarsa dake beating very fast . " ban taba jin soyayya ba irin wanda kake wa yarinyar nan " "wallahi ni kaina nakan zauna Ina wannan tunani MB ban taba gajiya da tunaninta ba daidai da second daya soyayyarta bata raguwa sai ma karuwa ya karasa maganar tare da yin shiru qirjinsa na dokawa da matsanacin karfin gaske". maganganu masu sanyi MB ya dinga rarashinsa dashi har zuciyarsa ta dan yi sanyi a karshe yace "ka rage tsanar yarinyar nan ATA saboda baka da hujja tsanarta kabi umarnin mahaifiyarka kawai ku rabu Lafiya ita irin wannan tsanar idan ta juyi zuwa soyayya abun ba'a magana please aboki kabar komai a hannuna zan san abun yi ". shiru ATA yayi kawai yana jinsa amman sam baya jin zai sota a rayuwarsa ko neman soyayyarta tare suka je matsalaci basu dawo ba sai da suka gabatar da sallahar ishai sannan suka dawo MB yayi dashi ya shigo suci abincin dare amman sam ATA yaki sai ma cewa yayi ya gaishe masa da madam da yaransa sadiq da hanif ya shiga mota suka d'auki hanyar gida ."hancin motar da yake ciki na shiga haraban gidan idanun maryam ya sauka akansa hakince a byn mota kanshi na sunkuye da alamun Idanunsa na kallon screen din waya ne , motacinsa na kokarin daidaita tsayuwa ita Kuwa tana zaune a baradan dake zagaye da kofar shiga ainin babban falon gidan akan fararen kujerunsa tare da lawan d'an PA din gwana kano,da kyar da balai ta fito gurinsa har sai da hjy zulaiheart tasa baki tace "taje su rabu lfy wulakanta dan adam bashi da amfani ,Jin motor ya tsaya ya dago idanunshi a hankali karaf ya sauka akansu Aiko ya balain had'e rai har sanda aka bud'e masa murfin mota ya fito yana taku kamar baya son taka kasa ta kasan idanunshi yake kare musu kallon tsaf acikin hasken daya haskaka gurin sai dai idan ba kwakwaran sani kayi masa ba bazaka gane su yake kallo ba .." Gabanta sai luguden bugawa da ganinsa yake sai dai hakan bai sa ta tsaida maganar da ta fara ba "Lawan ka daina zuwa gurina saboda banason abinda zai sa na dinga maka wulakanci, "idan har kina ganin daidai ne abinda kike min ki cigaba mrym , numfashi ta janyo da kyar ta sauke" ni dai lalla'baka nake amman ka gagara ganewa ,"to meye dalilin da bazaki amshi soyayyata ba ? yayi mata tambayar adaidai lokacin da AAT ya k'araso gurin. tayi shiru saboda buguwar zuciyarta daya qaru Shima lawan shiru yayi yana kokarin mikewa domin gaisawa da ATA Amman Ina bai tsaya bin ta kanshi ba tuni ya shige ciki . ya koma ya zauna yana kallonta "Uhm ki bani amsar tambayata Ina jinki me yasa baki Sona me na rasa mrym? yayi mgnr yana kallon jikinsa a ranta tace "many things lawan hatta sunanka bai min ba bare akai ga surar jiki sai data hadiye abinda ya tsaya mata a makoshi kana ta cigaba "Ina son namiji fari sol dogo sannan intelligent abinda zai kara kashe ni ya zamanto yana da tsoron Allah shikenan ya gama da rayuwata zan iya mutuwa akanshi " kasancewar mu bakake yasa ba'a sonmu kenan ? a'a bance bakin mutun bai yi ba amman ni dai a gurina mutun fari sol nake so Irina wallahi ni ko nmj baki zai bani rabin duniya akan sadakina bazan amsa ba na fison kalata dan banason black .."sake baki yayi yana kallonta gbdy yaji ya munzata aguri dan shi baki ne sitik kuma ba wani mai tsawo bane can sai dai baza'a Saka shi cikin sawun gajeru ba tun bai kai ga magana ba ta mike tsaye "to malam lawan ni zan shiga ciki ta nufi hanyar part dinsu bayanta yabi da kallo yana aiyana abubuwa dayawa akanta sai dai baya jin zai iya hakura daita dan yana son farar mace koda kuwa mayya ce . Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 8 "Ahankali take tafiya cikin sand'a tamkar wata 'barauniya yana hankalce daita duk da idanunshi a runtse suke amman bazaka ta'ba gane hakan ba sai wanda yayi masa cikakken sani , da d'an sauri ta nufi hanyar d'akinsu tana sauke numfashi Tare da ajiyar zuciya ,ta cire mayafinta ta wula saman katifa sannan ta samu waje ta zauna tare da rafka tagumi cikin zullumi da rashin sanin madafa zuciyarta a matukar tsorace take duk da tasan ba wani laifi tayi ba amman tasan tsoronta baya rasa nasaba da muguwar kiyayya da tsana mai tsananin da ya adam yayi mata tayi shiru tana sake zurfafa tunaninta sam bata hango ta inda zata iya amincewa aurensa ba gara kowa yaje ya nemo abokin rayuwarsa a waje domin rayuwar aure dashi daidai yake da kamuwa da cuttutuka kala dabam dabam ." "mr ATA ya cigaba da zama a parlour'n yana karkada kafarsa daya har sanda hajiya zulaiheart ta shigo parlour'n fuskarta a sake amman ganin yanayinsa yasa ta d'an shiga damuwa muryarta a raunane ta soma mgn "Adamcy nah har ka dawo ? ya had'e rai sosai tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa tare da gyada mata Kai kawai batare da yayi magana ba "Lafiya naga duk kayi wani iri ?fuskarshi a murtuke ya soma magana cikin tsananin fushi "wa yace waccen yarinyar tayiwa saurayinta masauki akan kujerun zamana ?mami ta numfasa irin nasu na manya kana tace " ban da abunka Adamcy wa zai sa tayi haka ?" ta dai yi haka né dan tayi ra'ayi tô ma menene aciki dan ta zauna da bakonta akan kujerarka kwana nawa ne ma ya saura ?"ni dai babu ruwana da wani kwana nawa ne ya saura ni dai banaso dan ba ra'ayi bane kawai raini ne idan ba haka ba kujerun da nake zama akai shine ya zama na zancenta?yayi maganar yana shan kamshi ." "Kai dai wallahi anyi rigimamme wannan zuciya wannan zuciya !! Allah ya sausauta maka, bakaken magana ya dinga fad'a akan maryam batare da yayi la'akari da matsayinta a gurin mahaifiyarsa ba mami batace komai ba har sanda ya dasa aya sannan ta kira sunansa a tsanake "Adam !bai amsa ba illa ya tsura mata kwayar idanunshi dake cike da bakinciki yana kallonta ta sake kiran sunansa "adam ! "a karo na biyu shiru yayi still yaki amsawa tunda yayi haka tasan bazai amsa ba yasa ta soma magana cikin kaukausan murya "zaka iya yin komai da kake so amman at least kayi respect din emotion din wani idan kai baka son maryam ka girmama masu sonta kuma naji dadi da hakan ya faru domin kasan diyata ba rasa masoya tayi ba yasa zan hadaku aure." wani kallo yayi wa mami yana mai rausayar mata da kwayar idanunshi cikin nata muryarsa can kasa yace "alright sweetheart amman da me zai hana ku bar masa ita ya aureta dan zata fi bukatarsa da duk wani abinda kuke bukata daga gurina "tabbas nasa zata samu, zata samu duk wata kulawa a wajen duk wanda ta aura acikin masoyanta domin kuwa suna mata tru love most especially lawan kalli kaga irin abubuwan daya zo mata dashi ."ta fad'a dan qara masa haushi dan babu abinda ya tsana sama da wannan arayuwarsa ,ai kuwa tayi nasarar takalosa." " He most be a fool da har yake bayyanawa common mace emotiona dinsa ta wannan hanyar , Kinsan allah sweetheart ko mafarkina na hadu daita a zahiri bazan iya mata irin wannan haukan ba ta zabga masa harara alokacin da yake kokarin yunkura wa zai mike ta dakatar dashi "adam !koma ka zauna ya koma ya zauna a kufule yana dubanta "kowani dan adam da yadda yake irin tashi soyayyar idan kai abubuwan bai maka ba watakilla su samarinta ya masu ,dan kyauta yana da matukar kyau ga masoya domin yana qara damkon soyayya dan haka kar na sake jin ka fadi haka ,kai kullum kana yin kuskure amman kai gani kake daidai kake aikatawa ,kowani dan adam yana kuskure amman wannan bana tunanin akwai wani kuskure acikisa sai ma kyautatawa soyayya sam sam bana jin dadin abinda kakeyi ...." "to ku aura mata shi dan allah kunga ni na huta daman ni wallahi bana sonta dan wannan auren babu abinda zai jawo sai damuwa I really has to tell you the truth before everything could mess up ya fad'a a matukar zuciye ."murmushi hjy zulai tayi dan gbdy ta fahimci dan nata haushi yaji koma tace kishi yake yaga maryam da wani ,ta girgiza kai "ai kasan bana magana biyu tunda muka tsaida magana da mahaifinta idan kaga baayi auren nan ba to mutuwa nayi ,idan ba mutuwa nayi ba kuwa na rantse da girman allah adamcy sai ka aureta kai ko yau na mutu a daura maka aure daita zan bar wannan wasiya maryam takace ta har abada haka zalika kaima nata né mutuwa ce kawai zata rabaku sannan kai ma muna jiran naka gift din soyayyar tunda ka kamu idanushi ya ware sosai akanta yana kallonta a rude tare da furta kalmar "what ? " your gift ! ta fad'a tana tsare shi da idanunta "Allah ya tsareni da wannan shirmen hau..."shut up Adamcy ai baka da wannan bakin dan ka rigada ka haukace tunda kake son abinda babu shi a duniya kuma lallai ka tabbatar da ka kawo naka gift din soyayya ranka shi dade a matukar zuciye ya juya ,da sauri sauri ya dinga taka step zuciyarsa kamar ta kama da wuta ta sake saida shi "adamcy nah !wannan karon a fusace ya juyo kamar zai yi kuka yace "what again ? "kaje kayi wanka ga dinner dinka ya kammala "bana bukata ya fad'a a kufule ."this is totally nonsense my love ta furta tana sakar masa murmushi dan tasan bancin itace da abinda zai fad'a kenan a fusace ya sake juyawa yana girgiza kai ." Hjy zulai zaune tana sake duba kayan da lawan ya kawo ta kiran maryam ta fito da sauri tana amsawa cike da girmamawa "maza tattara kayanki ki kai daki shi kuma Lawan din kin fad'a masa an tsaida miki miji dan ya daina wahalar da kanshi ? ta sauke numfashi sannan ta girgiza mata kai alamun" a'a ! "okay kice masa yazo gobe ina son ganinsa ta gyada mata kai kawai ta tattara kayanta ta shige dakinsu cike da zullumi ta bar Hjy zulai cikin zullumin wannan auren da take kokarin hadawa sam sam bata jin maryam domin ita din yarinya ce mai tsananin biyayya da hakuri akan komai adam take ji tasan shi tasan halinsa shine matsalarta tunda yace bai só tô har cikin ranshi bai só né sai ta tashi tsaye da rarrashi da addua ,zata bari adduarta yayi karfi da sadaka , sosai tayi zurfi cikin tunani ." Bayan kamar wasu mintuna ya fito sanye da wasu kayan wondo da riga farare sol kana ganin shigar kasan fita zai yi ,lokacin daya sauko parlour'n babu kowa zuciyarsa nayi masa wani irin zafi kamar zai fito waje ,sai dai ya kasa fita koina Kmr yadda yayi niyya ya bude bayan motarsa ya shiga ya zauna yana sake jin bacin rai mara iyaka yana marmarin shan sigari domin shansa na rage masa bacin rai sai dai tunanin illarta yasa baya son yawo daita domin yana bukatar ya bar shanta na har abada ." mr ATA bai shiga gidan ba sai karfe shabiyu na dare yana daf da wucesu ya haye step yaji sautin muryar mami "adamcy !cak ya tsaya yana ciccin magani "zakazo ne ranka dade koni na taso nazo ?"tayi mgnr cike da tsokana." jin ta fadi haka ya soma qokarin qarasowa inda take su maryam naganin hk duk suka mike suka kama gabansu byn sun masa sannu da zuwa bai amsa masu ba ya cigaba da tsayuwa "zauna ta nuna masa wuri kusa daita "laifin me mahaifiyarka tayi maka da ka dauki fushi mai tsanani daita ? "what ?! "Yes fushi kake daita mana tunda gashi kaki cin girkin data sha wahala ta girka maka da kanta sannan ka tsallake ka bar gidan nan tun 9:00 sai yanzu batare da kai mata sallama da zaka fita ba wanda hakan ba dabiarka bace muddin kana kasar nan duk inda zaka sai ka sanar min sannan ka dawo km kana kallona zaka wuce baka da niyyar ce min komai ya dan kalleta ta kasan idanunshi yana cewa "Wannan yake nufi ina fushi dake ? yayi mgnr a shagwabe Kmr zaiyi kuka ?shine mana idan ba fushi kayi ba fad'a min abinda kayi ?shiru yayi kawai dan bai san me zai ce ba dan fushi fushin yayi dan bai ga dalilin da yasa zata dinga tura masa yarinyar da tasan yafi tsana arayuwarsa wanda shi kansa bai san dalili ba ." maryam ta lallabo ta fito daga dakinsu ta rabe a gefen step "uhm ina sauraronka shiru ne dai ya sake biyowa baya "ina gift din din soyayyar maryam "? ya zaro ido sosai yana kallonta "haba sweetheart wai me yasa kike min haka ne ?"what did I do to you? yayi shiru yana kallonta Kmr zai yi kuka ta sake bude baki zatai magana yayi saurin dakatar daita . "Dan girman allah sweetheart ki daina hadani da yarinyar nan kin ce na aureta naji na amince yanzu kuma zaki sake hadani da wani sabon aiki kina son na mutu ne tun kwanana bai qare ba ?tai mur mushi irin nasu na manya "mafarkinka bai kasheka ba sai mutun a zahiri ne zai kasheka?" " adamcy wallahi ka canza rayuwa ina guje maka hakin mata akanka." yay shiru kawai yana kallonta "yanzu sweetheart fatan da kike min kenan ?me nace maka nace ka canza sai kace zaka canza ko ba shikenan ba ,ni ai kasan bazan ta'ba maka mummunar fata ba amman dan allah ka canza kaji masoyi ta riko hannunsa cikin nata shima ya daura hannunsa akan nata " naji zan canza Kiyi hakuri da duk abubuwan da nake yi wanda bakya jin dadinsa maryam ta kasa kunne sosai ko zataji abinda suke tautaunawa amman babu abinda taji dan can kasa kasa suke mgnr zai mike Hjy Zulai tace "abinci fa ?akoshe nake "me kaci dan nasan baka cin abinci a waje ? Kawai dai bana felling cin komai amman da zan samu tea mai dan kauri zan sha ya fad'a a yatsine ta girgiza masa kai alamun taji tare da kwallawa maryam kira "ya salam! ya furta yana dukar da kanshi kasa dan bai so haka ba sam baya son abinda zai shi kallon fuskarta ".a natse ta qaraso tana cewa "mami gani ." "Dan Allah maryam hadowa wannan sarkin zuciya tea mai kauri "to mami ! ta juya a hankali ta nufi inda kayan tea yake ta hado ta dawo a natse dan tasan halinsa abu kadan Ke hassalashi bare ita data kasance makiyayiyarsa ko batayi kuskure ba zai iya maidashi tashin hankali "mami gashi ,Yauwa maryam sannu da kokari kinji mika masa" tayi Jim tana jin faduwar gaba da tsoron mai tsanani numfashi ta sauke a boye na samun sausauci tunda mami na gurin komai zai zo da sauki bazata bari wani mummunar abu ya same ba ,bazata bari ya tozartata ba no matter how zata tsawatar idan taga zai yi wani abu jiki a sanyaye ta mika masa tana cewa "yaya ga..."Banza yayi tamkar bai ji ba nan kuwa yaji haushi ne yasa bazai karba ba " maza ka karba ka shanye ka miko min cup still kin karba yayi ko kaukauran motsi dainawa ya yi a zaunen da yake ma idan ka kallesa ma zaka dauka baya numfashi ne "ka kar'ba mana "sweetheart bana sha ya fad'a yana fusrzar da iska mai zafi ran mami ya soso tasan yayi haka ne dan maryam ce ta hada "amamn kace zaka sha "yanzu na fasa babu yadda mami bata yi dashi amamn yaki ya karba ya shan akarshe ma ya mike ya mata sallama ya nufi saman dakinsa bata amsa masa ba tabi bayansa da kallo har ya bacewa ganinta gbdy mami ta rasa meke mata dadi shiru tayi tana jin bacin rai har sai datayi datasanin kiran maryam amamn ita tayi haka ne dan su dinga samun kusanci da juna, ganin yadda mami ta shiga damuwa yasa maryam ta zauna inda ya tashi ta fara shan tea tana cewa "mami tunda baya sha bari ni na sha daman cikina empty ne shiru mami tayi tana kallonta ita dai bata fushi akan komai "mami dan allah karki damu kanki akan dan wananan abun da bai ya kawo ba "dole na damu maryam mutun Kmr mai zuciyar dutse ?dan Allah kar wannan abu ya dameki nima da yayi dani ban damu ba wallahi ahankali ta dinga kwantar wa mami hankali ." Cike da natsuwa ya tura kofar dakin ya shiga ahankali ya zauna akan daya daga cikin kujerar cushion dake dakin dafe da goshinsa yana furta oh my goodness god wai me yasa sweetheart bazata bar zuciyata ta huta da wannan yarinyar ba ?me yasa abubuwa suke faruwa dani ne komai ya zama worst a gareni ?daman har yanzu anayin auren dole ne bare shi daya kasance nmj "me yasa bazaa barshi har zuwa lokacin da yayi raayin ba ?shine tambayoyin da ya dingawa zuciyarsa ya dauki wasu mintuna zaune sannan ya fara cire kayan jikinsa ya shiga bathroom ya watsawa jikinsa ruwa ya fito ya sauya kaya zuwa na bacci ya hau gado ya kwanta shiru yana tunanin wannan auren da mahaifiyarsa ke bukatar yayi bai wani jima ba bacci ya daukesa hannuwansa duka a saman qirjinsa ." Washegari "10am ya sauko daga bed dinsa yana mika bakinsa dauke da addua kai tsaye bathroom ya shiga yayi refreshing kansa tukuna sannan ya saka wasu hadaddun kaya wando da Riga suit duk brown colour shiru yayi lokacin dayazo saka takalminsa domin kusan lokuta dayawa adaidai wannan lokacin mami ke shigowa dakin akarshe ita Ke saka masa ya numfasa ya shan iska komai nashi tô mach yayi har glass din dake manne da idanunshi ya kwashe wayoyinsa ya sauko cikin takun isan nan nashi ya soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa tare da jin kai yana neman inda mami take "sweetheart ! ya kira sunanta bai ji ta amsa ba ita kuwa tajishi Sarai tayi masa banza dan haka ya nufi hanyar kitchen dan nan yafi tunanin take idanunshi suka sauka akan hjy zulaiheart cikin shiga na alfarma ." a natse ya shiga kitchen din inda masu tayata aiki suka soma kokarin gaishesa sai dai babu wacce ya amsawa acikinsu wanda daman idan da sabo sun saba da yanayinsa ,ya qarasa ya tsaya bayan mami ya daura kanshi a kafardarta yana mai lumshe lumtsatsun idanunshi "my sweetheart good morning? "Morning! ta fad'a atakaice tana hade rai "Hope you had a great night? bansani ba kamar yayi murmushi amman ya maze yana cewa "sweetheart kamshin girkinki so nice tare da kai hannu zai bude kular gabanta "don't open! shiru yayi tsaye shi bai ajiye murfin ba shi bai rufe ba ya sake kokarin budewa "I said don't open "kullum aikin kenan yabon girki amman ..." bai san sanda ya tamke fuska ba ya katseta da sauri "you're worst sweetheart ! naji muje parlour'n tunda ka hanani magana dan ban san abinda ya shigo da kai kitchen ba sai ka gama batawa mutun rai kazo kana salo" ya sake hade rai sosai tamkar an aiko masa da sakon mutuwa "me nayi km ?"Bansani ba wallahi adamcy idan baka kiyayeni ba to tayi kwafa kawai bai sake cewa komai ba ya juya ya fita daga kitchen din ransa a matukar bace dan yasan akan abinda yayi jiya ne yasa tayi masa haka dining ya qarasa ya dauki cup din tea dinsa da chocolate cake yaci duk da shi din ba mai son zaki bane sosai bai jima ba mami ta shirya masa breakfast "your breakfast is ready "am okay ya fad'a ransa a hade sannan ya mike tsaye tun kafin tace wani abu ya fita zuwa haraban gidan ya nufi motar daya bada umarni yana son shiga Range Rover black color driver yajashi suka fita zuwa babban office dinsa kai tsaye ." ******* Yauma kamar jiya maryam tana zaune akan kujerar mr ATA tare da saurayinta abbas ta tsura masa idanunta tana kallonsa tana kallon yadda yake sauke numfashinsa ,muryarsa cike da kasala ya soma fadin "ina matukar sonki maryam da'ace mutun ya Kan iya shiga zuciyar mutun ya gani hakika da kin shiga tawa kinga irin zallar soyayyar da nake miki amman ni nasan bakya sona maryam kamar yadda nake miki wahalar da kaina kawai nakeyi ." "yaushe na furta maka bana sonka abbas ?Ko na taba furta maka haka ?ta fad'a tana hade hannuwanta wuri daya tana kallonsa" tabbas da zata tsaida mijin aure cikin masu sonta da aure to data tsaida abbas domin kuwa yafi sauran dama dama kuma ya dan kwanta mata arai "yadda tayi shiru tana kallonsa haka shima yayi shiru yana kallonta yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa akanta "me yasa kayi tunanin bana sonka abbas ?ta katse shirun dake tsakaninsu ta hanyar fadar haka ."abbas !ta kira sunansa ya tsura mata ido kawai "kamar yadda kake sona nima ina jin wani abu akan..." "Shiiii !"shima ya katseta "sam ban yarda da abinda zaki fad'a ba maryam zuciyar dake son mutun bata banza dashi dan haka karki fad'a min cewar kina jin wani abu akaina dan bakyasona maryam , ban ma ta'ba ganin soyayyata acikin kwayar idonki ba sau nawa zan kiraki sai kinga dama Kike dauka ?baki ta'ba tunanin ki kirani a duk tsawon lokacin da muka dauka koda kuwa zan shekara ban kiraki ba , duk wata alama ta soyayya da mutun maryam bakya nuna min hakan kawai ya ishi ne hujja amman ni nasan tabbas ina sonki dan allah karki boye min abinda Ke ran..." Wayarsa ta soma ringing wanda sanadiyyar hakan ya katseshi ahankali ya dan zame hannu shi ya ciro ya duba dan zabura yayi ganin mai kiransa maryam ta dago ido tana dubansa ya dauki wayar ,bata ji yace komai ba sai "to gani nan ya riko hannun maryam cikin nashi adaidai lokacin da mr ATA Ke qoqarin qarasowa gurin wanda wannan ne karo na farko da hakan ya faru "ki kulamin da kanki na samu wani kiran gaugawa ne amman zanzo dawo zuwa gobe mu qarasa maganarmu ina sonki mar..."giftawar mr ATA ya katseshi tayi saurin zare hannunta dake cikin nashi jikinta na daukar rawa ,abbas ya dan bi bayan mr ATA da kallo sannan yayi mata sallama ya wuce ya bar zuciyarta cikin tashin hankali." jiki a matukar sanyaye ta shige ciki yana zaune akan kujera kusa da mami sai dai kana kallon fuskarsa kasan yanayinsa babu alamun rahma bata tsaya ba ta nufi hanyar dakinsu mr ATA ya dago lumtsatsun idanunshi da suka canza kala wanda suka nuna tsantsar bacin ran da yake ciki ya zubawa mami sannan ya fara magana a natse sai dai mgnr tattare yake da 'bacin rai byn kmr mintuna goma sai ga maryam tare da nana hauwa'u sun shigo daskarewa tayi agun zuciyarta na rawa ,kamar ta juya saboda rawar da jikinta yake sai Kuma ta sanyawa jikinta jarumta ta cigaba da tsayuwa tana sauraronsu , "wallahi da tasan yana parlour'n har lokacin bai tashi ba bazata dawo ba batare da bata lokaci ba ta fahimci maganae da mami keyi akanta ne ." cikin sanyi jiki ya mike tsaye ya soma taku da kyar fuskarsa har lokacin a murtuke take ya jingina jikinsa da bangon parlour'n yayinda idanunshi ke kallon screen din wayarsa "wa yace ki sake zama min akan kujera da wani gardin banza har kuna taba juna dan ku din tattun yan iska ne ?tayi tsuru tsuru tana kallonsa hantar cikinta na kad'awa da jin kalmar daya jefesu dashi "wannan shine first and last karki yarda ki sake zama min akan kujeru dan ba dan ke na tanadaisu ba koni sa'anki ne ?"tayi saurin girgiza masa Kai kamar ta durkusa ta bashi hakuri dan ya bar zuciyarta ta hutu sai ta daure taki aikata hakan "ban tanadi kujeruna dan wata gardiya da garden banza su zauna suyi iskanci akai ba "adamcy ! no sweetheart bari na fad'a mata taji ko auta tayi min wannan ganganci sai na ballata wallahi bare wannan useless din ya fad'a yana nunata da babban d'an yatsa hannunsa" idan mutun ya sake min ganganci nima zan masa ganganci aikin banza kawai zuba masa ido kawai tayi tana jin wani zallar bacin rai na ratsata yayinda tuni hawaye ya soma bin kuncinta "yanzu irin mutumin daake son tayi rayuwa ta har abada kenan ? mutumin da duk duniya babu abinda ya tsana kamar ita burinsa bai wuce ya wulakantata ya tozartata ba lallai duk yadda zata gujewa wannan hadin zatayi koda kuwa zai zama sanadin rasa rayuwarta ne tun yanzu ma ya kamata tasan abun yi bazata iya ba ,zuciyarta bazata iya daukar wannan wulakancin ba ta bud'e baki da niyyar kare kanta kar mami ta dauka maganarsa gsky ce taga tuni har ya wucewarsa yana jan dogon tsaki ." idanuwanta suka ciko da hawaye cikin rawar murya ta soma "ma..mami wallahi abinda ya fad'a ba gsky ba.."kukan da take ya hanata qarasa maganar nana hauwa'u ta matso kusa daita tare da rike kafadunta "da Allah meye abun kuka bayan kowa ya San halinsa muje please nana hauwa'u ta janyota suka koma cikin d'akinsu tana rarrashinta "Ina ganin lokacin barina gidan nan yayi zan koma Abuja da zama duk sanda yake gidan nan bana samun sukuni"wallahi babu Inda zaki idan yayi miki ki daina nuna kina jin tsoro dan hkn da kike nunawa power kike Qara masa idan yayi miki ki rama duka shekara nawa ya bawa mutune duka fa 9 ne ..?" "naunayen ajiyar zuciya ta sauke "bazan iya daukar shawararki ba sister "manta da wannan maganar yanzu dai ya kuka kare da abbas ?wallahi ya bani tausayi gbdy na kasa fad'a masa gskiya sbd ina dan jin wani abu akansa "kenan kina son shi ? Ta girgiza mata kai alamun a'a "ina jin wani abu akansa baya nufin ina son shi bane "tunda bakya son ya Adam shi me yasa bazaki bashi dama ba ?" shiru tayi taki cewa komai "heeeee maryam kiyiwa kanki karatun ta natsu yanzu maza wahala suke karki ga wai iyayenmu nada arzki irinmu wahalar auruwa muke amman Kya kare a auren ya Adam din tunda baki da wanda kike so tana gama fad'ar haka ta d'auki wayarta ta shiga yanar gizo "kisa akawo mana abinci yunwa nake ji sosai ,abincin na fita ci wannan mai dacin zuciyar ya bata min rai " da idanu Maryam ta bita tana jinjina Kai ta d'auki waya ta kira layin kitchen ta bada umarni . ko cikakken minti biyar ba'a yi ba mutun biyu suka shigo cike da girmamawa suka ajiye tiren abinci da lemun irin wanda suke sha suka juya nana hauwa'u ta bud'e kula ta zuba abinci ta soma cin mrym tana dubanta ."kici abinci mana kin tsaya tunani "jiki a sanyaye mrym ta soma tsukura tana ci tana fargaban sake haduwa da ATA gara tayi ta gudu tun sakon rashin amincewa aurensa ya Isa kunnensa ya sake damarar cin kaniyarta koma asani ne tsanar ya qaru"? Bayan kwana biyu Mr ATA na kwance akan kujera mai zaman mutun uku a parlour'n hjy zulaiheart ta samesa ta zauna a kusa dashi ta soma magana cikin sanyin murya "kana son ginawa kanka rayuwa na gari dole sai kayi hakuri shiyasa kullum nake bukatar naga kayi aure domin ka zama magindaci saboda hakan zai sa ka canza , mata da ya'ya zasu canzaka saboda qaunar dake tsakanin iyaye da yayansu , Adamcy ka canza Sam bana jin dadin yadda kakewa Maryam acikin gidan nan ko babu komai Maryam yar'uwaka ce Kai yanzu kana ganin da wannan zuciyar zaka samu macen da zata iya zama da Kai ?bari kaji Maryam ce kawai zata iya zama da Kai saboda tana da zurfinn hakuri sosai ,zata yi hakuri da halinka da wannan zuciyartaka ko dokin zuciya ka hau nayi Imani zata san yadda zata faranta maka ka sauko , ka tausaya min Adamcy Kai kadai Allah ya bani namiji acikin ya'yana banason na mutu na barka da wannan zuciyar ta k'arasa maganar kmr zatayi kuka yayi saurin ya mike zaune daga kwance da yake ya kamo hannuwanta cikin nashi "kiyi hakuri sweetheart karki min haka karki zubar da hawayenki akan wannan matsalar shikenan komai ya wuce ai farincikinki shine nawa inshallahu zan canza Kuma zanyi duk abinda kike so ya karasa maganar yana zamewa ya d'aura Kansa akan saman cinyarta . Sanyayyayen ajiyar zuciya ta sauke na farinciki ta d'aura hannunta akanshi tana shafa sumar kanshi "Allah yayi maka albarka ,Allah yaye maka damuwarka Allah ya sausauta maka zuciyarka Allah ya baka zuria masu albarka kuma ya nuna min wannan lokacin, nifa a son raina ma mata biyu naso aura maka a rana d'aya, d'aya diyar talaka d'aya diyar shararran hamshakin mai arziki ." yayi murnushin gefen baki wanda ita kadai Ke iya ganin hakan ya lumshe lumtsatsun idanunshi yana cewa "lallai sweetheart kina ji dani "sosai kuwa Adamcy nah ai shiyasa kake min salo saboda kasan Kaine zuciyata "Nima kece zuciyata rayuwata sanyin idaniyata Ina sonki fiyye da komai " a hankali suka dinga hira mai kwantar da hankali daga karshe ta d'auke kanshi ta daura masa akan pillow kujera "thank you my sweetheart "you're welcome my happiness ta fad'a tana mikewa ". Ko cikakken minti ashirin bata yi ba ta had'o masa abincinsa yana ganin dawowarta ya mike yana murmushi "sannu da hidima dani sweetheart ",yanzu kam sauran kwana nawa na huta ta fad'a ta janyo karamin stood gabansa ta ajiye "bismillah kaci ya narke mata fuska "yau daya kaci da kanka ya lumshe mata lumtsatsun idanunshi kana ya soma ci a hankali "kalli cin abinci so nice my dear komai naka dabam ne bai ce komai ba ya cigaba da kai abinci bakinsa tayi gyaran murya ya dan kalleta domin jin abinda zatace tayi shiru dan haka ya d'auke kanshi ya sake Kai abinci bakinsa ."baka ga ya kamata ka fara jan yarinyar nan maryam ajikinka ba"? " ka dinga janta kana kiranta hira ta haka ne zaka...."wani irin tsarkewa yayi ya fara tari babu kaukautawa "sorry !! ta fad'a tana bud'e rabon ruwa .." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Free page *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page9 "Cike da kulawa mami ta tsiyaya masa ruwa a glass cup ta Kai bakinsa "sorry dear kabi ahankali ya kur'bi kad'an yana furzar da numfashi mai zafi ya dafe goshinsa kusan minti goma yana dafe da goshinsa yana jin wani zallar 'bacin rai ,da zai iya daya saka mata kuka a yadda yake jin zuciyarsa dame take son yaji ? mami kuwa zuba masa idanuwanta tayi tana faman jero masa sannu har sai dataga ya dawo daidai sai dai bai iya cigaba da cin abinci ba ya d'an zame jikinsa kad'an akan kujera yayi rigingine ya runtse lumtsatsun idanunshi gam yana jin radadi." muryarta a sanyaye tace "ka qarasa cin abinci "am okay sweetheart ! ya fad'a atakaice batare daya bude idanunshi ba . "Numfasawa tayi ta kira daya daga cikin masu aiki ta tattara kayan abinci sannan ta mike ta shiga bedroom dinta tana tunanin yadda zata bullowa ATA sosai kwakwaluwarta tashiga neman mafuta dan dole tasan abun yi matukar ya nemi ya zuba mata kasa a ido zai ga bacin ranta ." Mr ATA ya cigaba da zama yana kallon tashar CNN ".Kusan awa daya da wasu mintuna yana zaune yana nazarin maganar mami "shine zai kira yarinyar da sunan zance ?"no no !! it can be possible koda zai iya hakan sai dai ba daita ba domin bata kai wannan matsayin ba ."a natse ya mike ya shiga bedroom dinsa yayi taku cikin falon wanda babu motsin komai sai na'urori sanyaya wuri kai tsaye bedroom dinsa ya nufa yana furzar da hucin iska mai zafi daga bakinsa wai kamar shi ne zai kira yarinyar zance wannan lamari na sake bata masa rai da daga masa hankali amman ya tabbatarwa kanshi bazai ta'ba iyawa ba yana da raayin shi sannan ga karfin iko da yake dashi dan haka bai ga abinda zai sa shi kiranta da sunan zance ba koda kuwa zasu shekara dubu ne hakazalika ko auren sukai a haka zata qare rayuwarta batare da samun farinciki ba ." ahankali tamkar mara lafiya ya qarasa bakin gado ya soma cire kayan jikinsa yana mamakin mami "hakika tana qaunar yarinyar dayawa wanda hakan yasa tsanar yarinyar yake sake ninkuwa a zuciyars a hankali ya shiga wanka ya fito ya sanya wasu hadaddun kayan bacci wando da riga farare sol ya feshe ilahirin jikinsa da turaruka masu sanyin kamshi ya kashe wayoyinsa guda biyu ya bar na business dinsa sannan ya kashe tv ya haye gadonsa ya lullu'be rabin jikinsa da bargo mai taushi yana runtse idanuwanshi da princess dinsa ya soma cin karo sanye cikin fararen kaya sol tana sakar masa murmushinta mai rikitarwa ya tsura mata Ido." duk da idanunshi a runtse suke amman shi ganinsu yake abude " ya za'a yi na gaki ? ya furta yana tsareta da lumtsatsun idanunshi sai daya fesar da iska ya sake motsa lip's dinsa "da zanganki da kin fahimci Ina sonki fiyye da komai , me kike so nayi ki yarda Ina sonki ki bayyana min kanki , ina son ki fada min inda zangaki please, zanyi komai akanki ko cewa kikayi na mutu a yanzu zanyi ya Kai hannunsa yana shafa beautiful face dinta ." idanunta na kallonsa ta sauko ta jingina da bangon daki ya mike ya tsaya a gabanta suna fuskantar juna tana kokarin juya masa baya da sauri ya rikota ya matsota sosai kmr zai shige jikinta har dukiyar fulaninta na gogan qirjinsa " ina son ki kasance tare dani ki bari na ganki azahiri Koda sau daya ne ya karasa maganar suna fuskanta juna " idan Ina kallonki sai naga kin fi kowace mace kyau a duniya idanunki , lip's dinki you look so beautiful....." ya ware hannuwansa duka yana k'okarin rungumeta jin ya rungumi iska ya bude idanunshi fesss yana kallon d'akin kamekame da jikinsa, baya felling din kowace mace sai ita ,baya son kowace mace sai ita, da zai mallaketa tabbas da shi kadai yasan irin rikon da zai mata, zai yi mata riko mai karfi ta yadda babu abinda zai rabasu." a hankali ya mike ya sauko ya fito parlour'nsa ya shiga dayan d'akin da kayan zanensa yake ya shiga firfito dasu daya bayan daya ya dawo falo ya zauna ya shimfida black cavenperpa ya soma zanata cikin shigar da tayi masa gizo ,tayi kyau sosai kamar 'indiya "wooow ya furta tare da furta a fili " gbdy gani yayi ta kara kyau sosai ga tsayayyun dukiyar fulaninta masu girma , shiru yayi yana tunanin anya kuwa yarinyar ba aljanna bace Ke neman yi masa wasa da hankali ba ?yana wannan tunanin shaawarta na sake lulluesa ." ahankali joystick dinsa ya mike tsaye har Kan na harbawa murmushin gefen baki yayi yana sake tsura mata Ido" na rantse da Allah ko aljana ce ke idona idonki baki Isa ki hanani kanki ba wallahi sai na ciki ci mai azaba sai na fanshe wahalata ta shekara da shekaru , sannan kowa kika aura a duniyar nan Ina da tabbacin sai ya bar min ke saboda akwai rabona ajikinki , kin sa min sha'awarki a raina fiyye da kowace mace a duniya, ji nake idan bake na aura ba bazan iya aurar kowace mace ba, dan Allah princess ki bari mu hadu ko brest din nan naki na d'an tsotsa please .." " dan girman Allah princess ki bari mu hadu Koda na kwana daya ne mu kwana akan gado daya cikin blanket guda muji dumin juna shiru yayi yana kallon surar jikinta mai daukar hankali ," wallahi princess da kinsan irin son da nake miki da tun tuni kin bayyana min kanki , nasan da zarar mun hadu zaki kamu da matsanacin Sona sannan zaki bani kulawa kamar yadda zan baki a yadda nake jinki idan ban mallakeki ba kin cuceni har abada ,wallahi bana kallon mata a matsayin mata , ki bayyana gareni ki tsotse min baki ,ki tsotse min joystick dina, ki tsotse min nono kinji princess dina yayi kasa da muryarsa sosai kmr zai mata kuka "dan Allah Princess ki bayyana min kanki a zahirin Ina son ganinki yana magana yana shafa fuskarta da gashinta,ya d'auki lokaci yana kallonta yana jin soyayyarta na bin jinin jikinsa hannunsa ya Kai yana cigaba da shafa kwantaccen sumar kanta sannan ya mike ya shafa superglue a bayan cavenperpa din ya manna ajeren zanenta ya dawo ya kwanta akan kujerar kushin dake ajiye a d'akin yana kallonta. a hankali ya yaye rigar jikinsa sama kad'an ya d'aura hannunsa a daidai saman mararsa yana shafawa a hankali yana furzar da iska mai zafi yayinda sha'awarsa ke sake motsawa wani irin yanayi ya dinga ji a sansar jikinsa ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa a haka bacci ya daukeshi cike da mafarkinta, cikin mafarkinsa ya ganta tana gudu sosai tana haki tayi gudu sosai sannan ta tsaya ta dafe gwiwowinta da hannuwanta can sai ga wani hayaki ya llubeta ta koina a jikinta can sai kasa ta dinga budewa ta soma yin kasa tana ihu tana daga hannuwanta sama domin neman d'auki a daidai wannan lokacin wasu mutane su uku mata biyu maza biyu suka k'araso gurin a lokacin da kasa ta rufeta mutun biyu acikin wadan mutane kuka suke sosai suna kokarin taimaka mata ." shi kuwa dayan wanda ya kasance babban mutun Tare da mace suka cigaba da tsayuwa rungume da hannunwa a qirji suna dariyar mugunta "a matukar firgice ya farka yana dafe grjinsa gumi ya rufesa kmr babu ac a d'akin zuciyarsa cike da mamaki mafarkinsa na yau "Anya kuwa mutun ce wannan yarinya ?Anya maganar yan'uwa da abokan arziki bazai tabbata ba kuwa ?ba mutun bace aljana ce yarinyar nan ya furta a fili "da sauri ya girgiza kanshi "Allah bazai sa haka ba inshallahu a mutun zata kasance ,idan km mutunce hakika a duk Inda take tana cikin damuwa da tashin hankali nan take shima ya shiga damuwa da jin tsoro , ranar dai bai iya komawa bacci ba dakinsa ya koma ya dinga juyi cikin tsananin damuwa ." washegari sukusuku ya tashi jikinsa babu kwari kana kallonsa kasan bashi da natsuwar zuciya shirun nasa ya qaru fiyye da sauran lokutan baya, mami duk ta damu da ganin yanayinsa sai dai tambayar duniya yace babu komai ya boye mata saboda muddin taji abinda ke damunsa sai ta fishi shiga damuwa yau kwana biyu kenan bai sake d'aura maryam a cikin kwayar Idanunsa ba bai damu ba dan damuwarsa tafi rashin qaunar data nunawa yan'uwansa tana yi masa ." yana zaune a part dinsa yayi shiru yayinda MB ke zaune a gefensa "ka daina damun kanka da tunani kada wani ciwo ya kamaka kasa mu shiga uku meye ma matsalarka?sai daya furzar da iska yace "ka kasa fahimtata ne kawai amman matsaloli gasu nan takoina kuma ace mutun bazai ji babu dadi ba. "friend abinda zaka dinga dubawa Allah ya baka Lafiya ya baka tarin dukiya bila'adadin wanda Kai kanka baka san adadin kudadenka da gadarorinka ba ,Allah ya baka komai da komai me yakamata kayi sai ka gode masa ?komai mai wucewa ne inji cewar MB "to alhamdulillah na gode masa amman bangaren damuwata ba mai karewa bace. "kaga duk wannan mai sauki ne ni sai nake ganin kamar har da rashin amincewa da aurenka da mrym yasa damuwar tayi maka yawa koma nace yana cikin abinda ke damunka karka ji komai zanji dashi. "Me zai sa damun tunda ba sonta nake yi ba kawai zan auri maryam ne saboda darajan mahaifiyata kuma zata kare rayuwarta a gidana sbd darajanta "Kai yanzu kana ganin zaka aureta?" zan aureta saboda sweetheart "angama zan san abun yi sun dade suna tautaunawa kafin daga baya ya mike ya fito a parlour ya iskesu har hjy zulaiheart yayi mata sallama "har zaka wuce muhammadu bello bazaka tsaya Kaci abinci ba ? a'a mami a koshe nake da zai fice daga falon yace "Maryam muje na dan ganki tace "to ! tare da d'aukar mayafinta ta yafa ta fito a haraban gidan suka tsaya ." "wato maryam kinsan abinda yasa na kiraki ?ta girgiza masa Kai "ba'a kan komai bane sai akan maganarki da ATA me yasa bazaki amince da aurensa ba ?"banason ki rufe min komai idan kin boyewa su aunty nasan ni zaki fada min gasky menene dalili ? Numfashi ta sauke tana lumshe ido"ina jinki ? a natse ta fara mgn cikin raunanniyar murya "abu na farko ya Adam bai sona sannan abinda na fahimta kamar dole akayi masa ya aureni , ni km bazan iya auren mijin da baya sona ba gsky . "da zai fada miki da kanshi zaki yarda ki auresa ?"a'a bazan auresa ba saboda bana son shi shima km baya sona "shiru yayi yana kallonta "ki dai yi tunani ba yabon Kai ba abokina yana da nagarta da za'a auresa ke ya'yan manyan kasar nan fa binsa suke suna rokonsa ya auresu babu wacce ya amincewa zai aura sai ke "gsky sunyi kokari da son aurensa ni Kuma kaga banason shi zaka iya fada masa gara ya zabi daya acikinsu ya aura "bazaki duba darajan mami ba dan itace me son had'in ko shi baya so sbd mami ne ?ya fada cike da Jin haushin furcinta ."gaskiya da wahala duk ta Inda MB ya bullo mata sai ta kawo masa hujja haka ya gaji yayi mata sallama sai dai yasan ko giyar wake ya sha bai Isa ya fadawa ATA cewar mrym bata bashi had'in Kai ba ." washegari ranar mr ATA yayi tafiya zuwa hollond Kan harkokin kasuwancinsa gbdy ya manta wata aba maryam a rayuwarsa harkokin gabansa kawai yake da tunanin princess dinsa ."Kwana biyu da tafiyar ATA maryam ta soma hada kayanta da abubuwa amfaninta ta fad'awa hjy zulaiheart da nana hauwa'u cewar ranar juma'a inda Allah ya kaimu zata Abuja zatayi sati biyu ta dawo "Kinsan sati biyu zakiyi shine baki bari mun tafi tare ba ?inji cewar nana "kiyi hakuri sister nayi kuskure nest time inshallahu iya haka kawai ta fad'a saboda taikaita maganar . Ranar juma'a jirgin karfe goma tabi zuwa Abuja tana sauka ta tarar da kannenta da mahaifiyarta sunzo tarbarta dake sun san da zuwanta daya byn daya ta rungumesu ajikinta suna murnar ganin juna "nayi kewarku sosai "muma mun yi kewarki inji cewar izza ta k'arasa ta rungume mumynta dake tsaye tana sakar mata murmushi "mumy na sa meku lafiya ? Lafiya qalau maryam ya mutanen lagos ?tayi mata tambayar tana shafa bayanta da gani kasan akwai soyayya mai karfi a tsakaninsu, Ta zareta ajikinta ta rike hannunta suka d'auki hanyar gida tun akan hanya mumy ta fara mata magana akan ATA tayi matukar mamaki da Jin tasan komai "eh haka naji sai dai gaskiya ni bana son shi dan bazai yi caring din mace ba shi kenan kullum cikin dacin rai no yayi gaba ya nemi mata nima Allah zai bani nawa mijin ." "karki soma wannan maganar ke Ina ruwanki da dacin ransa tunda yana da kudinsa ,shi fa mai kudi sai a hankali har suka karasa gida mgn daya suke yi Koda mahaifinta ya dawo yayi murna da ganinta nan ya shiga zolayarta "Hjy mrym ko ace maryamu damtso ko amaidashi irin na turawan nan ace mary duk ke kadai gilashina a she babban kamu kikayi alagos ? Kin tashi daga diyata kin zamo surukata matar d'ana da nake ji dashi gskiya naji dadin wannan had'in, kwarya tabi kwayar kenan kinyi sa'a da dace miji na gari .mrym ta zumburo masa baki "Allah dady ka daina cewa hk ni yarkace ba wata suruka ba km ni babu wani dacen miji danayi tsokanarta sukayita yi har dasu izza..." "zamanta a Abuja taji dadinsa tana zaune cikin yan'uwanta cikin kwanciyar hankali da annasuwa babu tsana babu tsamgwama Kuma kullum suna waya da nana hauwa'u da hjy zulaiheart sati daya sati biyu mrym shiru taki komawa lagos tun abun bai damun hjy zulaiheart har ya fara damunta wani tunani tayi tasan halin d'anta Allah yasa ba wani abun yayiwa maryam ba kafin ya tafi hollond yasa tayi musu wayo ta koma gurin iyayenta ". da yammacin ranar asabar hjy zulaiheart ta kirasa yana dauka tasa masa kuka "wallahi muddin baka auri mrym ba babu ni babu Kai Adamcy "subhanallah sweetheart ki kwantar da hankalinki menene ya faru kike kuka da fad'ar haka ? ni dai ka auri maryam shine kawai abinda nake bukata ,Idan km kana son kwancinyar hankalina Kuma tabbas ni ce rayuwa agareka kmr yadda kake fada lallai kayi wani Abu mrym ta dawo gidan nan sannan ka hanzarta aurenta acikin kankanin lokaci na ganta acikin gidan a matsayin surukata ". Sai daya sauke numfashi sannan yace "shikenan naji ki daina kuka zanyi yadda kike so nayi miki wannan alkwari zan aureta sai da yayita rarrrashita sannan ta sake , suna gama waya Kiran MB ya shigo wayarsa byn sun gaisa mgnr minti biyar sukayi sukayi sallama . kullum abu daya ke damunta har yasa gidan ya fita ran mrym kullum sai mahaifiyarta ta dameta da batun ATA cikin zafin rai tace "mumy nifa inada Wanda nake so jira lokacin nake zan bashi dama ya turo" ke ban son zance banza da wofi ni na haifeki ko yar riko ce ke arzikin rikon danayi miki nace ki auri Adam zaki min alfarma ballanata ni na haifeki acikin cikina har nace ga abinda nake so kiyi min gardama to ki d'auke soyayyar wancan ki maye na adam agurin dan dashi za'a yi babu fashi munafukar Allah butulu kawai , shiyasa kika wani tattaro kika dawo nan? " to dan ubanki sai kin koma tana gama fad'ar haka taja tsaki tana zuba fada ." mrym ta fashe da kuka mai tsananin har ana iya jiyo kukanta "zance banza zance wofi ba kuka ba idan idanunki zai fado tsakiyar d'akin nan aure babu fashi sai anyisa saboda haka garama ki daina kuka karki je kisawa kanki bacin rai hawan jini ya kamaki dan ko hawan jini zai kamaki sai na zama surukar adam, wannan aure babu fashi tana magana mrym na sharba kuka kmr wacce aka aikowa da sakon mutuwa ".Iskanci banza har da cewa Ina da Wanda nake so to ni wannnan nake so Kuma shi zaki so wancan kisa masa kiyayya daga yau na gaya miki ki dauko soyayyar wancan ki d'aurawa Adam ki dauko kiyayyar Adam ki d'aurawa wancan shashar banza shashar wofi munafuka kawai mai yiwa kanta bakinciki ta k'arasa maganar tana sake jan tsaki , Yayan zamani Allah ya shirya wannan maganar fa tun asalin iyaye da kankani uwa ko Uba suna da iKon da zai d'auki duk wanda yake so ya bawa yarsa batare da yar taí yi gardama ba dan yanzu zamani ya rigada ya canza nan ta mike ta barta tana surutai da zaginta ." Tana kwance a d'akinta tana kuka faiza ta turo kofar dakin ta shigo ta hau har kan gadon ta rungumeta tana rarrashinta nan kukanta ya qaru "aunty mrym ki daina kuka dan Allah sheshekar kawai take "wai me yake faruwa ne kike kuka haka?, Kin cewa komai tayi tana cigaba da kukanta nan Faiza ta fashe da kuka tana cewa "Dan Allah ki fad'a min ki Daina kuka cikin muryar kuka tace "wallahi bazan auri ya Adam ba sbd banason shi "Amman aunty mrym yakamata ki duba daranja mami tunda tana sonki sosai "wallahi bazan iya ba bazan iya ba tunda ba da ita zanyi rayuwa aure ba ta k'arasa maganar tana sake rushewa da wani sabon kuka ...." Da daddare ta iske mahaifinta akan batun auren "mrym naji duk bayaninki sai dai banji dadi ba Amman Ina son ki rike abinda zan fada miki mrym karkice zaki yiwa yar'uwata haka karki bari wannan abu yayi silar rugujewar zumuncinmu mrym , idan har kika ki wannan auren zakiyi danasanin a rayuwarki dan bazan yafe miki ba a matsayina na mahaufinki bazan so kiyi nadama a rayuwarki ba, duk d'a na halak so yake ya rabu da iyayensa lfiya ki d'aure kiyi ta addua da sannu soyayyarsa zai shiga zuciyarki idan wannan auren alkhairi ne arayuwarki allah ya tabbatar dashi idan ba alkhairi bane mrym Allah ya canza miki da wanda yafi shi zama alkhairi bare Ina ji ajikina wannan auren alkhairi ne ni kaina bazan so Adam yaje ya auri wata ya barki ba, ni kaina na dade Ina wannan mafarkin duk da na gari zai so ya rabu da iyayensa lfiya Ina sonki mrym hk zalika Ina son aurenki da Adam kuka take a tun sanda ya fara magana har ya dasa Aya yana gamawa ya mike ya shige bedroom dinsa ya barta tana kuka ..." ******* Barrister hayat ne zaune a gaban hadiza lawyer da suka dauka domin kareta "Ina son ki fad'a min gaskiya menene gaskiyar abinda case din yake ciki domin mu san yadda zamu kareki "menene gaskiyar halakarki da wadan wukaken da ake tuhumarki da kisan Kai dasu karki boye min komai yadda zan fuskanci shara'a na kareki "barrister zan fada maka gaskiya yadda alamarin nan yake bazan boye maka ba saboda Ina bukatar na fita acikin wannan matsalar tayi shiru tana numfasawa tare da fargaba fadar abinda ke zuciyarta ...." Bayan wasu mintuna ta cigaba da magana "Wallahi barister bani da halaka da wad'an nan wukaken ban san komai akansu ba , yadda ka gansu haka nima na gansu kawai dai na shiga track ne a sanadiyyar furucina. shiru barister hayat yayi yana kallonta tare da nazarinta "ka yarda barister bani na kashesu ba ta sake fad'a tana rushewa da wani kuka mai ta'ba zuciya "mai zai sa na kashesu bani da wani halaka da kisansu gara ma ita sadear mun samu matsalata daita har nayi furucin zan kasheta amman ita wannan yarinyar da naji ana fad'ar sunanta sam ban santa ba hasalima ban ta'ba ganinta a rayuwata ba tayi maganar tana sheshekar kuka. Ganin yadda barister hayat ke kallonta yasa ta shiga furta kalmar "na shiga ukuna ni hadiza na jawowa kaina rashin kwanciyar hankali, ni kaina a daren ranar da sadear zata mutu naga shigowar mutun cikin bakaken kaya an shiga d'akinsu amman sam ban kawowa zuciyata cewar kashe sadear za'ayi ba , Ina da tabbacin da police zasuyi aikinsu yadda ya kamata zasu gano ko waye yake da saka hannu cikin mutuwar wad'an nan mutane guda biyu da'ake tuhumata akansu ta k'arasa maganar cikin tsananin tashin hankali ." kuka take sosai kamar ranta zai fita "naunayen ajiyar zuciya barister hayat ya sauke "tabbas na yarda dake Kuma inshallahu zanyi iya qoqarina naga kinsamu ku'buta duk da mahaifiyar mubina ta tubure lallai sai an kar'bawar diyarta hakinta shi dai mahaifinta alhj jamilu ne yace ya barwa allah amman kiyi addua sosai dan idan mahaifiyar yarinyar ta rinjayi mahaifinta gsky sai dai wata bake ba , bangaren su sadear wannan mai sauki ne da kansu zasu gaji da zuwa kotu kar'ban kwana wata su hakura , amman su alhj jamilu suna da baki a kasar nan suna da fad'a aji akoina dan haka ki dage da addua sosai . "na gode sosai barister da k'okarin, "karki damu Allah ya bamu sa'a inji cewar barister hayat "Ameen ta furta tana kuka sukayi sallama da zumar zai sake waiwayota kafin a zauna kotu ." ****** Zaune mahaifiyar mubina hajiya sha'awanatu take a had'ad'd'en kujera a parlour'nta kallo d'aya zaka mata ka fahimci tana cikin tsananin damuwa domin kuwa idanunta sun kod'e saboda kuka dan tunda jami'an tsaro suka zo musu da bayanin anyi kisan Kai da irin wukar da aka kashe mubina har anyi nasarar kama mashekiyar take cikin damuwa da kuka , duk yadda mijinta alhj jamilu ke k'okarin shawo kanta taki yarda burinta bai wuce a gurfanar daita a yanke mata hukunci daidai da abinda ta aikata ba .a yanzu ma zaune yake a gabanta yana fuskantarta domin son kawowa zuciyata natsuwa "dan Allah ki bar maganar kisan mubina da ma duk wanda yake da saka hannu cikin kasheta mubarwa Allah ,haka Allah yaso bazamuyi rayuwa mai tsawo tare daita ba , yanzu karshe wad'an da basu ji ba basu gani ba sune zasu zo suna cin wahala bana jin wannan yarinyar zata iya shigowa har cikin gidan zainab ta kashe mubina , dan haka ki natsu dan Allah ki samawa zuciyarki salama da hakuri ". "uncle jay ........." da yake haka itama take kiransa kamar yadda ATA ke kiransa " kace na hakura na bar maganar alhalin an kama wacce tayi kisan ?ya gyada mata Kai al'amun haka yake nufi" nifa say Inda karfina ya tsaya, wallalhi sai nayi shari'a daita Koda duk zan qarar da abinda na mallaka , Kai bari ma na takaice maka sai na rakata har zuwa gidan yari sannan ruhina zai samu salama , ai tunda asirinta ya tono bazan yarda ba sai itama an sha jininta kamar yadda tasha jinin di........." Nace kiyi hakuri mu barwa Allah ya katse mata numfashi ta hanyar fad'ar haka " duk wani matakin da zaki d'auka bafa zai dawo mana da diyarmu da muka rasa ba ,ta kwa'be. masa baki da fuska dan sam maganarsa basa shigarta ya mike tsaye yana dubanta "muddin Ina da iko akanki ki bar maganar nan mubarwa Allah Komai yana gama fad'ar haka ya shige bedroom dinsa ya barta tana girgiza Kai hawayen bakinciki rasa tilon diyarta na zubowa akan kuncinta bata Jin zata iya yafewa wannan yarinyar ." ******** "Adam zaune a makaken office dinsa dake cikin kasar hollond zagaye da makeken table wanda ke d'auke da file files dabam dabam sai qaramin frem din hoton mahaifiyarsa da mahaifinsa , sanye yake cikin riga fara sol da wondo baki sai yar saman suit dake sanye a saman farar rigar . ya d'auki wayarsa dake qara tun mintuna ashirin da suka gaba har zuwa lokacin daya d'auka yana dubawa miss call's ne rututu bama zai iya kirgawa ba , wasu yasan number's wasu kuma bai sani ba . ya sauke numfashi sannan ya fara da kiran MB kasancewar shine wanda ya kirasa karshe MB ya d'auka yana cewa " hello friend ykk ? Lafiya alhamdulillah okay ai Ina ganin zan shigo cikin satin nan dan sweetheart ta matsa lallai nazo ayi mgnr aurena da wannan yarinya gashi ni wallahi har yanzu bana Jin son yarinyar Ina jin qinta sosai abinda ke Kona min rai yadda sweetheart ta nace akan lallai sai anyi auren nan kusa . "kasan har cewa tayi bata yafe ba muddin ban aureta ba ."Kai gskiya Ina ganin ya kamata kayi wani Abu tunda kaji abinda tace maganar MB ta doki kunnensa ",amman ni aganina da an bari zuwa wani lokaci sai ayi auren tunda ba neman kai akayi dani ba " waya fada maka ?ai kuwa muna neman kai da kai mun gaji da ganinka haka dan haka karka fara cewar ba yanzu ba domin kuwa zaka samu matsala da mami kawai kabi umarni ka tunkari yarinyar da kanka."nace mata me MB ? yayi masa tambayar yana ciza lips dinsa na kasa , shiru shima MB yayi yana sauke numfashi "ya kake wata mgn haka ?ya sake tambayarsa a kufule "darajan da tsinuwar mami shine abun lura shiru ATA yayi can yace "Anya kuwa zan iya MB gara kawai a d'aura auren zai fiyye min sauki akan na tunkareta da batu na soyayya dan har abada bazan iya ba ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 Book one Last free page *AYSHA A BAGUDO* AREWABOOKS AYSHAABAGUDO WATTPAD @HAUESH bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 10 "ai Kuma shine babban matsalar abokina domin yarinyar itama ta kafe akan bata sonka amman nasan da zaka mata magana da kanka zata iya amincewa kayi k'okarin ka shawo kanta da kanka dan Allah ,ka kwantar da kai ka shawo kanta yarinya nan yar'uwarka ce jininka ce sannan ita din mace ce ,mace Kuma 'yar rarra..." "ban son iskanci MB ya katseshi a matukar tsawace yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa " sbd me zaka fad'a min hk ?" how dare you talk to me like that ? “ shiru mb yayi yana mamakin yadda abokin nashi ke saurin daukar zafi akan abinda bai kai ya kawo ba "to me ma ya fad'a da zai dauki zafi haka ?mr ATA ya mike zumbur daga Kan kujerar da yake zaune tare da tura kujerar baya tamkar ita tayi masa laifi ya soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa "Ita din makiyata ce ita din ba jini bace karka sake fad'a min cewar yaruwata ce ko jinina ce Ka dinga sanin irin maganar da zaka fad'a min taya da girmana da mutuncina zakace na tunkareta common mace daita yarinyar da umarni kawai zan bata kuma dan dolenta tabi ,ta Inda yake shiga bata nan yake fita ba " Shikenan kayi hakuri abun ne yazo hk amman dai ka k'okarta ka....."dan Allah malam ka maida hankalinka jikinka sai wani qoqarin son saka min magana abaki kake wannan ai mgnr banza ce "ka tsaya ka saueareni mana nifa hankalina yana jikina kai dai.... "dan Allah malam kayi min shiru babu wani saurararka da zanyi a yanzu ".yana gama fad'ar hk yay disconnecting din Kiran yana huci ..." "Nonsense girl kawai ai bata Isa ba ,bata ma kai wannan matsayin ba shi da mata ke bi suna kuka suna rokonsa ko gaisawa su dingayi bai kaskantar da kanshi ya amince ba bare har ya ajiye girmansa matsayinsa komai nashi yace yana son mace macen ma irinta ko cikakken minti biyar bai yi da katse kiran ba kiran hjy zulaiheart ya shigo sai da gabansa yayi wani irin mummu nar fad'uwa kusan yanzu duk sanda zai ga kiranta sai hankalinsa ya tashi saboda yasan Kiran baya wuce akan wannan banzar yarinyar bane ." ilai kuwa yana d'auka da maganar ta fara "Adamcy kana son ganin 'bacin raina yayi saurin girgiza mata Kai kmr yana gabanta "wallahi zan cire hannuna acikin lamarinka idan haka kake so "kiyi hakuri sweetheart inshallahu zanyi yadda kike so "kullum abinda kake fad'a kenan ka kasa aiwatarwa dan hk ka shirya shigowa nigeria dan cikin satin nan maryam zata dawo Kuma tana dawowa zaayi mgnr aurenku da baba babba har ta gama maganarta bai sake cewa qala ba ganin tayi shiru shima yayi shiru yaki cewa komai duk da yaso komai yaya ya bata hakuri amman zafin da zuciyarsa keyi ta hanashi aiwatar da hakan har kusan minti goma tana jin yadda numfashinsa Ke sauka da karfi kamar wanda yayi gudun tsare da kyar ya iya fezgo magana "sweetheart akwai abubuwan da nake son na kammala bazan samu damar dawowa nan kusa ba zaku iya yin .." "No babu wani uzuri da zanyi maka kayi duk abinda zakayi ka gama ka shigo cikin satin nan shiru ya sake yi yana sauraronta tana gama fad'ar haka ta katse Kiran bayan wayar ta katse ya bita da kallo zuciyarsa na rawa ."ajiye wayar yayi akan makeken table din dake office din ya buga wani uban tagumi wanda dagani na takaici ne." ya sake had'e fuskar nan tashi sosai wani irin bakinciki yake ji acikin zuciyarsa, ji yayi kamar zuciyarsa zata kama da wuta yana matukar jin bakinciki abinda mahaifiyarsa take bukatar yayi ,shi da yake adduar komai ya watse a manta komai amman ita kullum burinta bai wuce taga faruwar wannan auren ba . banda 'bacin rai mai Kona zuciya babu abinda yake ji mikewa yayi ya shiga zariya a office din yana zagaya koina yana zurfafa tunaninsa kafin ya soma magana shi kadai "ya zanyi ?me zanyi ?taya zan soma rayuwa da yarinyar da kake qoqarin amincewa aurenta ? sosai kwakwaluwarsa ta shiga tunani neman mafuta dan dole yasan abun yi kafin mahaifiyarsa tayi masa wannan auren mr ATA ranar kwana yayi yana tunani ." ****** Bayan kwana biyu maryam ta dawo daga Abuja murna gurin nana hauwa'u hjy zulaiheart da sauran 'yammatan gidan babu magana dan sunyi matukar kewarta sosai hira ce ta yaushe gamo ta barke a tsakaninsu sai yamma suka bar gidan haka ma washegari suka cika gidan har da rukkaya makociyarsu anan grã gidansu yake asalinsu nufawa né suna cikin hira rukkaya ta Kalli maryam sannan ta Kalli diyana da nuzla tace "nafi kowa Jin dadin dawowar marsi bari na baku labari nayi wa marsi saurayi kyakkyawa ajin farko ." maryam ta kalleta tana kwa'be fuska cike da takaicin Jin maganarta yayinda itama rukkaya ta kalleta tana sakar mata murmushin jin dadi . Sai dai a matukar wulakance maryam ta cigaba da kallonta kamar ta rufeta da dukan mutuwa sannan ta fara magana cikin fushi da 'bacin rai "bangane kinyi min saurayi ba ance Miki bani da saurayi ne ko ya ? ke da duk fuskarki ta dame da bille kota Ina an watsa miki shi ba'a ce anyi miki saurayi ba sai ni da fuskata take lafiya lau babu zane ko daya ,Kalli bakinki duk a warwatse kamar lefen sakarya shine zakice kinyi min saurayi , karki qara min irin haka wallahi banaso ai kinfini bukatar saurayi ." Gabad'aya suka kwashe da dariya rukayya kuwa tsayawa tayi tana kallon maryam da mamaki nana hauwa'u kam har da zubewa kasa tare da rike ciki dan dry ."Ina ganin dai baki san aljanu sun shigi marsi ba ko ? ai babu damar ayi mata maganar maza sai hankalinta ya tashi ." nifa ba haka bane Ina da zabi acikin zuciyata Ina da ra'ayin irin mijin da nake son aure ba kowani shasha ba amman dai na barwa zuciya irin mijin da nake so Ke mai bille sai ki rike saurayin dan kinfini bukata ." rukayya ta Kalli nuzla nuzla ta kalleta sannan a matukar fusace rukayya tace "karki qara cewa fuskata anyi min bille "to karya ne ba'a yi miki ba ? "idan bakya so nace miki hk nima ki barni da batun wani saurayi can tun da bance miki nayi ina son ba wadan da nake dasu ma sun Isheni bana neman qari sun dade a d'akin suna hira akarshe duk suka watse suka kama gabansu." ****** Karfe shabiyu daidai jirgin Mr ATA ya sauka a lagos a haraban gidansu tun kafin jirgin ya k'arasa sauka security's dinsa ke zagaye da gurin har sanda ya sauka , a hankali ya mike yana gyara zaman rigarsa Sannan ya fara takowa daga matattakalar bene yana taku da kyar cikin tafiyarsa nan nashi na Koda yaushe wato tafiya cike da alfarma da izza yana d'aga kafafunsa yana shakar iska da kyar tare da hura hanci escort dinsa already sun fito suna nan tsaye suna jiransa duk Inda ka duba acikin haraban gida masu aiki ne ke Kai kawo suna aiwatar da aikinsu." yana qarasa saukowa escort dinsa da security's sukayi masa caaaa har zuwa Inda yake tsaye Inda ya fara taku suna biye dashi har zuwa bakin kofar shiga cikin parlour'n mahaifiyarsa na d'aya , yana isowa gurin yaja ya tsaya d'aya daga cikinsu mai suna muzammil ya bud'e masa kofar ya shiga yabi bayansa shi kad'ai rike da bakar jaka ATA bai tsaya akoina ba sai a babban falon mahaifiyarsa ya shiga ya zauna ya kame akan d'aya daga cikin kujerun falon ya d'aura hannunsa d'aya akan gwiwarsa yana d'an jijigawa yaronsa muzammil ya rankwafo ya ajiye masa jakarsa ya bashi izinin tafiya ya juya da sauri ..." A hankali mami tayi sallama cikin had'ad'd'en falon a zaune ta samesa akan kujera ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi ,da kyar ya bude baki ya amsa sallamarta batare daya bud'e idanunshi ko matsowa ba har sanda ta zauna akan kujerar dake kallonsa tana jin sanyi da farinciki mara misaltuwa da ganin kamilallen danta mai nagarta da haiba illarsa dai rashin ajiye iyali da miskilanci da zafin rai duk wannan farinciki daga ciki take jinsa dan bata bayyana shi ba . a hankali ya bud'e lumtsatsun idanunshi ya mike ya k'araso gabanta ya rusuna har kasa "mun sameku lafiya sweetheart? Wani sanyin dadi Ya ratsata ta kai hannunta kanshi "alhamdulillah ka sauka lafiya ya aiki Ya fama da jama'a ? ta fad'a fuskarta babu yabo babu fallasa "alhamdulillah sweetheart yayi magana yana matukar tausayin Kansa dan yasan tunda ya zo ya dinga cin karo da matsaloli kenan dole sai yayi hakuri dan magana daya ce za'a yita ana mai maitawa ,." A natse ya mike ya koma mazauninsa ya zauna yana neman layin M.B da sauran friend's dinsa kafin kace me hjy zulaiheart tasa an cika masa gabansa da kayan itatuwa dabam dabam sai dai babu wanda ya d'auka yaci illa amsa waya da yake ta bangare damba dabam , nana hauwa'u ta shigo ta gaishesa cike da ladabi "yayanmu Ina yini ka dawo lafiya .?" "Lafiya auta ykk ya fad'a atakaice" lfiya ta bashi amsa da haka sannan ta mike ta koma ciki dan yadda fuskarsa take a murtuke nan komai zai iya faruwa , haka rashida da muna yaran baba qarami sun shigo gaishesa a mutunce , babu yabo babu fallasa ya amsa haka akayita shigowa yi masa sannu da zuwa sai dai ya amsa atakaice ba tare daya bi ta kansu ba maryam ce kawai bata shigo kawo gaisuwa ba har sanda MB ya k'araso sai daya yi sallama a bakin kofar falon aka bashi izini shigowa sannan ya shiga . ATA bai motsa daga Inda yake ba har MB ya shigo ya zauna cike da tausayin abokinsa dan kallo d'aya zaka masa kasan baya tare da walwala da farinciki har wata siririyar rama yayi "ATA..!" ya kira sunansa anatse ATA bai amsa ba illa zuba masa kwayar idanunshi da yayi yana sauraronsa "yana ga duk ka rame ? shiru yayi bai ce uhm ba bare uhm uhm sai dai ga dukkanin alamun hankalinsa na kanshi "dan Allah ka kwantar da hankalinka komai na duniya mai wucewa ne idan kabi komai a sannu da sannu komai zai zama normal ." wani huci numfashi ya saki yana sake tsaida idanunshi da gbdy suke cikin damuwa akan mb sai da yayiwa MB kallon wasu mintuna sannan ya furzar da abinda ya tsaya masa a makoshi mai mugun daci cikin son danne duk wata damuwarsa yace "na rasa yadda zan cire wannan damuwar MB "kallonsa MB yayi yayinda ATA ya Maida idanunshi ya lumshe "Ina zanganta ?ya furta a saman labbansa cikin tsananin damuwa "wa kenan ..?Idanunsa dake lumshe ya d'an bud'esu da kamar bazai yi magana ba sai Kuma ya furta ", princess.." murmushi MB yayi "ka iya fad'ar sunan nan tamkar kai ka fara tsarashi a duniya "zaka ganta inshallahu Ina maka adduar ta zamo mutun ce ba aljana ba , sai abu na gaba ka fara da abinda mami take so "bana jin zan iya MB zan dai ta bin sweetheart a hankali har sanda zan samo yarinyar ko kuma na samo wata dabam amman wannan guntuwar yarinyar bazata zamo mata a gareni ba sun dade suna tautaunawa kafin daga baya sukayi sallama duk Kuma maganar da suke akunne mami sukayita , dan haka ta shaka sosai tun a lokacin ta fara shirya abinda zata masa ." Tunda masu aikin gidan suka san ATA ya sauka kowan nensu ya shiga hankalinsa hatta shigowarsu part din hjy zulaiheart ya taikaita sannan komai cikin sauri suke yi kasancewar sun san shi dan Oya oya ne duk da ba abincinsu yake ci ba sai na mahaifiyarsa kuma bata zauna ba har washegari tana kan yi masa hidimar abincin da zai ci tare da abokansa Amar, shawul, shamsu MB sun baje a falonsa sai kwasar abinci suke Amar yace "friend duk fa matar da ka aura muddin bata iya girki irin na mami ba zaku samu matsala daita ",Sosai kuwa dan ni dai Ina ganin zan kawo fedy gurin mami a sake bata class na mussaman dan wanan girki yayi inji cewar MB " suka sa dariya banda ATA dake rike da waya yana duba mahimmam bayanai masu shigowa . Sai daya rage mahimmam abubuwansa sannan ahankali ya motsa lip's dinsa "gaskiya ne Ina son macen da ta iya girki kuma qala dabam dabam shiyasa kuka ga Ina dojewa auren yarinyar nan dan nasan babu abinda ta iya sai salo da rike waya da shiga social media ,ni Kuma ta Inda za'a samu matsala dani kenan dan bazan yarda da rashin kamun Kai ba. gbdy suka gyda Kai batare da sunce komai ba sai can shawul yace "ai idan princess dinka ka aura ko bata iya girki ba zaka zauna daita haka har karshen rayuwarka ATA ya sauke numfashi kawai batare da yace uffan ba "kayi shiru ko ba haka bane ? Inji cewar MB "ka'ajiye wannan magana bama zata zo a haka ba am very sure ta iya komai ." Shawul yayi sigili yace " mai kmr mrym me zaiyi da wannan princess din taka ya watsa masa wani mugun kallo "ra'ayina kenan princess bana son mace irin wannan yarinyar da ake kokarin lika min yayi mgnr yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa. "Wai Kai wayace maka ana auren mace mara kiba a yanzu Kai gaka ba jiki ba , Kai Kashi ita kashi kuzo Kuna haihuwar kasusuwa Kai da zaka samu mai nama irin Marym chubi daita komai zamzam inji cewar Amar gbdynsu babu Wanda bai dara ba MB kam har da fadowa yayi kasa daga kan kujera dan dariya "ko jini zamu dinga haifa ba kasusuwa ba. nafi sonta akan wannan mai siffar aljanu guntuwa gata nan dai fari ne kawai ya taimaki rayuwarta. nana hauwa'u da mryam dake tsaye a bakin kofar falon hannu nana hauwa'u rike da tiren silver mai d'auke da gasashen kifi anyi raping dinsa ita kuma mryam na rike da tire na harish suka Kalli juna dan sunji abinda suke tautaunawa daga ciki , naunayen ajiyar zuciya nana ta sauke tace "mu shiga sister ta fad'a tana rike tiren hannun maryam dake k'okarin subucewa qirjinta na dokawa tace "a'a sister ke dai ki shiga ke kad'ai bari na tsaya anan har ki fito banason na shiga Ina jin tsoron kar ya disgani agaban abokansa ta k'arasa maganar tare da d'aura tire dake hannunata akan tiren hannun nana hauwa . suna tsaka da hira suka jiyo sallama a bakin kofar falon MB ya bada izinin shigowa tare da komawa mazauninsa ta shiga a natse ta gaishesu cike da ladabi sai dai kallo d'aya zaka mata kasan ranta a 'bace yake ta tsani taji yayanta yace bai son mrym ko aibantata bare yau a gaban abokansa ." Amar ya washe baki yana dubanta kana ya soma mata wasa kasance warsu abokan wasa "a'a gasu cubi hauwa fa ,farar mace alkyalbar mata Ina ganin nida madam zamu lalla'bo muzo ki sammana man da kike shafawa kullum ke da maryam kmr bakwa fita rana, gaku na nan dau kmr yanzu kuka sauko daga sama." tayi masa banza tana jan tsaki a ranta "Ina kika baro mrym dan nasan ke daita 5&6 ne? ta sake sharesa tana kokarin ajiye tiren hannunta wayarta dake rike a hannunta tayi kasa zata fadi madadin ta bar wayar sai tayi k'okarin rikota Aiko tiren gbdy suka sullube a hannunta sukayi kasa tiren kifi ya kife nan take mai ya fara malala gabanta ya buga da karfi nan take jikinta ya kama rawa ta d'ago da sauri ta Kalli Inda ATA yake zaune gabanta na cigaba da fad'uwa ." wani dogon tsaki ATA yaja kana ya soma magana cikin fushi da zafin rai " kunga irin haukan nasu ba koina zaaje da waya kamar wasu yan kauye "haba ATA me yasa zaka dangantata da Kalmar hauka tsautsayi ne ko babu waya a hannunta hakan zata kasance "shawul karka goyi bayan wad'an yaran sam babu abinda suka iya sai hauka komai na mata basu iya ba basu iya girki ba basu iya gyaran daki ba sam basu iya komai na mata ba yan iskan banza kawai sai aikin rike waya da surutun banza da wofi da maza kije ki dauko abinda zaki gyara min guri kafin na soma kwallo dake, sai naci ubanku daya byn daya kafin na koma idan Kuma baki dawo kin gyara ba kika turo min masu aiki sai na canza miki kamanni stupid kawai ." fuuuuu ta fita tana zunburo baki a bakin kofar nana hauwa'u ta samu mrym tsaye duk ilahirin jikinta rawa yake gbdy duk ta Kara firgicewa Ta kalleta tana hawaye bata tsaya yi mata bayani ba ta wuce dan tasan taji komai daya faru." Kai tsaye kitchen Inda hjy zulaiheart take ta shiga ita Kuma maryam ta gudu tayi dakinsu , nana hauwa'u na gama shiga kitchen ta soma zuba balai "wai mami dole ne sai ya Adam ya auri mrym ne ." "Dan girman allah me zai hana abar maganar kowa yaje ya auri wanda yayi masa ? mami ta dubeta a natse "me yasa kika fadi hk hauwa wani abu ne ya faru ?"to gashi can sai faman fad'awa su ya amar yake wai bai sonta guntuwa ce fari ne kawai ya ceceta mene mene ko ance masa itama tana son shi ne ? gsky kiyi masa mgn ya daina nima yanzu kafin na fito sai daya tozartani a gaban abokansa shiyasa wallahi ban so zuwa ba ,wallahi duk matar data auresa ta shiga uku da matsalolinsa wallahi ni dai a fasa had'in nan da marsi tana gama fad'ar haka ta juya fuuuu ta fita mami tayi murmushin takaici kawai tana girgiza Kai ,nana bata so komawa bangarensa ba amman babu yadda ta iya haka ta d'auki abun gyara ta koma kafin yaci ubanta ". ****** Washegari da misalin Karfe biyu daidai Kiran aunty shahida ya shigo wayar mrym tana d'auka tace ki samemu a parlour'n mami na biyu bata tsaya ji abinda zatace ba ta katse Kiran ,shiru tayi tana sauke wayar daga kunnenta jiki a sanyaye ta mike ta d'auki mayafin abayar dake sanye ajikinta tayi rolling din kanta ta fito ta nufi parlour'n gabanta na dukan uku uku. zaune ta iskesu gbdy ya'yan hjy zulaiheart banda nana hauwa'u ATA zaune yana rike da waya yana daddanawa sau dari zaka gansa to da waya ne ko system yana operate "samu guri ki zauna aunty zabiba ta fad'a tana nuna mata kan kujera kasa zama tayi a Inda ta nuna mata . a hankali ta samu guri ta zauna nesa kadan dasu a qasa dan gudun balain ATA ta kasan idanunta take qare masa kallo sanye yake da dogon wando da riga mai gajeren hannu blue da ratsin fari kayan sun yi masa kyau sosai ga gashin Kan nan nasa sai sheki yake wanda da alama yana shafa man gashi ne yasa yake fitar da sheki ko yaushe ." "Adam ga mryam nan "inji cewar aunty shahida "naga tantiriya mara kunya mara mutunci , uhm Ina jinki ki maimaita abinda kika fad'awa aunty a gabana ". sai da gabanta yayi wani irin mugun fad'uwa taji wani abu ya tsarga mata tun daga qirjinta har zuwa kasan mararta take taji marata ta soma murd'awa taji wani abu mai d'umi ya zubo mata wanda bata raba d'ayan biyu na tsananin tsoronsa ne." ta d'ago kanta a hankali taga har lokacin kanshi na sunkuye yana danna wayar hannunsa "ke har kin Isa kice wai bazaki aureni ba ?tayi saurin sunkuyar da kanta kasa tana sake jin digar wani abu mai zafi na diga a pent dinta wanda babu tantana jini ne yazo mata a dalilin tashin hankalin daya risketa ne ya cigaba da magana fuskarsa a d'aure tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa "daraja kika ci bancin haka har duniya ta nade baki Isa ba , km baki Kai matsayin da zaki zamo mata agareni ba ." ta d'an dago kad'an ta saci kallonsa adaidai lokacin daya dago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro ne wani irin mugun kallo yake mata mai firgitarwa "Ina jinki fad'a min abinda kika fad'a masu ?"kaga AD ba dan ka tutsiye yarinyar mutane muka taro anan ba mufi bukatar amincewarta akan komai "no aunty shahida bari ta fad'a taga yadda zanci ubanta ". "nace abar wannan mgn ta wuce ke mrym kin amince zaki auresa ko kuwa har yanzu baki so dan yau shine final decision domin zamu sanar da mami komai ? "muryarta na rawa tace "na ...na amince .." "kin amince da me ya fad'a a tsawace yana zaro mata Idanunshi "na amince zan..zan aureka " you are very stupid ,useless kawai tashi ki 'bace min da ganin kafin na miki dukan mutuwa ,bana sonki kuma bazan aureki ba daman nasan baki Isa ki kalleni ki fad'a min abinda kika fada musu ba , maza tashi ki bar nan bana son kallon wannan banzar fuskartaki ya k'arasa maganar yana jan tsaki tare da runtse idanunshi ." har ta mike zata tashi aunty shahida tace "koma ki zauna tayi saurin girgiza mata Kai tana duban Inda yake zaune tare da jujjuya hannuwanta cike da tsoro "nace ki koma ki zauna a d'ard'ar ta zauna tana kallon kasa a ranta tace "masefaffe banza kar Allah yasa ka aureni nima ai banasonka . muryarsa a kasalance yace "muddin kuna bukatar na cigaba da zama na saurareku sai wannan yarinyar ta bar falon nan " shiru falon yayi babu wanda yace uffan gashi babu wanda ya Isa yayi mgn sai aunty shahida ko khadija da yake bi bata isa ba bare zabiba da kanwa ce ,aunty shahida ta Kalli maryam tace "mrym kin amince zaki auresa ?tayi saurin gyada mata Kai alamun "eh .! "Okay tashi ki wuce abunki ta mike da sauri kmr iska ta bar parlour'n "a gsky Adamcy ban ji dadin abinda kayi ba ,a hankali ake bin komai Kai komai zuciya da zafin rai Allah ya sausauta mk zuciyar nan karta sa wata rana kayi nadama iska ya furzar "yanzu tunda ta amince shikenan sai mu sanar da mami aunty shahida ta fad'a tana kallon kannenta mata "eh hk ne suka hada baki gbdy . "Da izinin wa kenan zaku sanarwa sweetheart .? "Da fari na amince maku zan aureta amman wannan iskancin da tayi yasa na fasa aurenta har abada km komai zai faru sai dai ya faru amman na fasa "haba yayanmu dan Allah kayi hakuri karkayi haka tunda ta amince ka aureta kawai a wuce wajen tsoronka take ji shiyasa kaji ta fadi hk, cewar zabiba "ka taimakemu karka fasa auren nan kodan mami kabi komai a sannu please "ai bai ma Isa ba tunda ta yarda dole ya aureta ka godewa Allah da kasamu salahar mace mai kamewa kmrta ." "bafa zan aureta ba I repeat it I can't marry her ,na aureta na kaita Ina da wannan rashin tarbiyar nata ?"yanzu ku baku ga rashin dacewarmu ba ?A tare suka girgiza masa Kai "mu bamu gani ba sai sam barka .Ya girgiza Kai " matar data Kalli tsabar idanunku tace bata son jininku har abar so ce agurinku ?yayi musu tmbyr a matukar fusace" dukkaninsu kallonsa sukayi yadda jikinsa ke rawa kmr anjonasa masa shocking ."Ku bar ganinta shiru shiru irin wadan nan mutanen abun tsoro ne wallahi gara a bani masefaffiya daita juyin duniya sukayi dashi yace bai sonta km bazai aureta ba "na yarda ku nemo wasu mata ku aura min ko guda hudu ne km a rana daya na amince amman ban da wannan jakar yarinyar mara tarbiya yana gama fad'ar hk ya mike ya kama gabansa kallon junansu sukayi na second goma sannan suka numfasa "yanzu me kuka ga zamuyi ?inji cewar aunty khadeja "mu fad'awa mami kawai tasan komai dan boye boye bashi da wani amfani zan fada amnan mu bari zuwa jibi zan san yadda zan fad'a mata . atare suka mike suka nufi d'akin hjy zulaiheart tana zaune akan kujera tana duba abubuwan da suka kawo mata suka shigo jikinsu a sanyaye tana ganinsu ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi duk suka yiwa kansu mazauni ta kallesu daya byn daya "Allah dai ya taimakeku gbdy yayi muku albarka yadda kuke tsaye akaina da abinda kuke min dukkaninku Kuna min k'okarin gurin yin abubuwa ." "da wanda ya bani million daya da wanda ya bani dubu dari da wanda ya bani dubu hamsim dukkaninku abu d'aya ne agurina Kuma inshallahu ladanku daya ne saboda dukkaninku abu d'aya ne ni dai fatana Allah yayi muku albarka ,kowa yayi abinda zai iya ban da takura kai , Allah ya raya muku zuriarku yadda kuke hidima dani Allah yasa yayanku suyi muku fiyye da haka "Ameen suka had'a baki gurin fad'ar hk. shiru sukayi babu wanda ya sake kokarin fad'a mata halin da'ake ciki ta d'ago daga duban kayan da suka kawo mata, shiru tayi tare da tsura musu Ido"ya na ga kmar bakwa cikin farinciki alhalin ba haka fuskokinku yake ba a d'azu da kuka zo ? naunayen ajiyar zuciya suka sauke "ku fad'a min idan wani abu ne ? shiru sukayi kowannensu najin tsoron mgnr ta fito daga bakinsa "Kun min shiru ku fad'a min mana Kun tasani gaba Kuna kallona da kyar aunty khadeja ta soma bayani "kiyi hakuri aunty shahida zata fada miki komai amman ba yanzu ba ." "akan Adamcy ne ko ?ta tmby tana dubansu a tare suka girgiza mata Kai alamun "eh suka tsinci kansu da bata amsa da haka "yanzu har akwai matsalar da zaku boye min bayan bani da kowa daga Allah sai ku duk abinda ya kunno Kai cikin rayuwarmu tare muke had'uwa muke magance matsalar shine yau zaku barni cikin duhu, shikenan na gode karku fad'a dan ko Kun fada min daga baya bazan gode ba Kuna iya tashi ku kama gabanku ." zubewa sukayi a gabanta kamar zasuyi kuka "kiyi hakuri mami zamu fad'a miki a natse aunty shahida ta zayyane mata komai tun daga ranar da suka fara magana da mrym har zuwa yau din nan "shiru hjy zulaiheart tayi tana sauraron aunty shahida da sauran yaranta mata byn ta gama Jin komai ta numfasa kafin daga bisani tace "shikenan ku barni dashi zan nuna masa ni na haifesa bashi ya haifeni ba daman na dade da sanin baya son farincikina." nan suka cigaba da tautaunawa "Allah mami ki bud'e masa wuta idan yaga kin haukace masa zai yi abinda kike so "ku barni dashi a yau din nan zai amince ko kuma ya canza uwa aunty shahida tace "duk abun bai kai haka ba ki dai bisa a hankali kar komai ya jagule "babu wani binsa da zanyi ahankali ai shi zuma ne sai ancisa da wuta ake samun kansa daman Ina lallabasa ne na d'auka abun nasa na girma da arziki ne a she wulakanci ne tana gama fad'ar haka ta mike ta nufi d'akinta .." tana shiga aunty khadeja ta mike ta d'auki jakarta ta rataya "ni zan wuce baza'a yi wannan dramar Ina gidan nan ba ,itama zabiba ta mike jirani mu wuce tare gbdy suka mike suka fito tare ." ******* A bangare mrym kuwa tana shiga d'akinsu ta fashe da matsanacin kuka nana hauwa'u dake zaune ta zabura ta k'araso Inda take ta rungumeta tsam tana tambayarta sai dai taki bata amsa kuka take sosai zuciyarta na zafi da qunci "me yasa ya Adam bai sona ?me yasa nana hauwa'u fada min aibuna da yasa baya Sona ? tayi mgnr hawaye na tsiyayowa daga cikin idanunta ,nan nana hauwa'u ta fahimci dalilin kukanta "Kiyi hakuri marsi baki da wani aibu illa rashin sa'a irin nasa domin sai ya aureki zai san yayi Sa'ar samu mata mai kyakkyawar zuciya." qaruwa kukan marsi yayi ",yadda bai sona nima bana son shi amman nayiwa kaina alkwarin zan auresa zan rayu dashi muddin rai " wani murmushin farinciki nana hauwa'u ta saki tare da sake rungumeta ajikinta tana Shirin magana qarar wayar yasa tayi shiru sannan suka saki juna a hankali ta k'arasa ta d'auka tana kokarin fita daga d'akin mrym ta shige bayi ta kulle ta jingina bayanta da kofar ta sulale zuwa kasa tare da sakin wani kuka tana toshe bakinta da sauri nana hauwa'u ta fito zuwa haraban gidan Inda ta iske yayyunta mata da mamaki take kallonsu ",ya haka har zaku wuce ?tafiyar dole ce auta dan yau bom zai tashi a gidan nan Kuma tashin babba ne gara mu san Inda dare yayi mana "daman na kiraki ne dan kisan yadda zaki kwantarwa mrym hankali tare da bata kwarin gwaiwa ." "Ga ta can kuwa sai kuka take amman ai ta amince zata auri yaya ? " eh ta amince amnan ai shi uban gayyar yace bai yi inji cewar zabiba "Kai! ta fad'a tare da dafe goshinta "kiyi kokari ta dawo normal inshallahu zuwa jibi zamu shigo idan munji yarda suka kare da mami juya sukayi a tare kowace ta nufi motarta tana tsaye direbobinsu suka jasu sannan ta juya da sauri ta koma ciki. koda ta koma d'akin bata ga mrym ba tana toilet ta kunnawa kanta ruwa tana kokarin daidaita natsuwarta da rarrashin zuciyarta, dole tana bukatar ta rarrashi kanta sannan ta sanyawa zuciyarta hakurin zama dashi ta kowani hali , guri nana hauwa'u ta samu ta zauna abakin gado tana jiran fitowarta ." Rai a matukar bace hjy zulaiheart ta shiga bangaren ATA tana gama shiga ta fara zuba masa fad'a " tur da haihuwarka Adam " ya waigo a matukar firgice yana zaro Idanu lokaci guda yay fillinging da wayar dake rike a hannunsa ya zube kan gwiwowinsa kasan a gabanta cikin tsananin tashin hankali muryarsa a shake yace "sweetheart me nayi ?"dan Allah ki yafe min ,kiyi min afuwa bazan sake ba." hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka haka har mutuwa ta riskeka tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn sai lokacin ya fahimci laifinsa ." ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ." "a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa ..."mami tayi saurin tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka ATA ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..." Mami ta juya a matukar fusace tana cewa "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani ta karasa fita tana magana cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ." ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani kasa ya zame ya zauna akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ." wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ." "ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika idanunta amman ta danne taki barin su zuba tunda take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS AYSHABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 11 " har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya Kawai zan yiwa mahaifiyata na aureki sai dai zakiji jiki sai kinyi da kin sanin kalmarki gareni, zakin san kin ta'boni yana gama fad'ar haka ya d'auke kafarsa tare da shure mata kafa ya nufi cikin part din mahaifiyarsa ransa a dagule . girgiza kai mryam ta shiga yi kafin daga baya ta rarrafa ta shige parlour'nsu ta ra'be a bakin kofar d'akin tana kukan zuci , cikin yanayi na tashin hankali take furta "me na tsare maka ya adam ? "me yasa baka sona ? "me yasa ka tsaneni hk ? haka tayita jerowa kanta tambayoyin da bata da mai bata amsa sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba gbdy Idanunta sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ." kuka take son yi sai dai zafin da zuciyarta ke yi yasa hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice " baka sona amman ya zama dole na jurewa komai muddin ina son rabuwa da iyayena lafiya , bazata manta kalman mahaifinta ba alokacin da zata dawo daga abuja domin sun samu kyakkyawan mazauni acikin kwalkwaluwarta "maryam muddin ni ne wanda nayi sanadiyyar zuwanki duniya Kuma kina son gamawa da duniya lafiya ki auri adam bisa umarnina Kuma ki zauna dashi zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so .." A bakin gado ya iske hjy zulaiheart ta cika tayi bam ,cikin sanyi jikin nan nashi ya k'araso ya zauna a gabanta yana neman gafararta , ko kallon Inda yake bata yi ba daga karshe ma ta kawar da fuskarta gefe al'amun bata son ganinsa ya runtse idanuwanshi sosai yana sauke numfashi ,byn kmr second biyar ya bud'e idanunshi ya fara Kame kame "uhm ammm kiyi hakuri sweetheart , afuwa sweetheart I will not do it again , inshallahu I promise you zan aureta ." "hjy zulaiheart taji dadin jin furucinsa har cikin ranta sai dai ta share tana jan tsaki a fili. "ki yarda sweetheart duk duniya babu wanda zai soki da son farincikinki kmr ni ,kiyi hakuri bazan juri ganin 'bacin ranki ba ya fad'a yana riko hannunta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke batare data fuskancesa ba ,duk da zuciyarta ta d'an yi sanyi dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta hakura . damuwarta daman yayi aure tana son taga aurensa taga ya'yansa kamar yadda taga na sauran yaranta amman duk da haka bazata sakar masa fuska ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa bai da wuya ya d'auki mintuna masu tsawo agabanta bata daga Kai ta kallesa ba sai ma ta mike zata bar masa d'akin , ya mike da sauri jikinsa na kyarma ya tareta dan sosai ya hango damuwa qarara akan fuskarta ya sake kamo hannuwanta duka cikin nashi , ta fizge a fusace tana watsa masa harara "sweetheart kiyi hakuri dan girman Allah wallahi zan aureta trust Adamcy zai aureta tunda yace zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa zan rasa rayuwata....." hannunta d'aya tasa ta zare hannunta daga cikin nashi ta tsura masa idanunta "wallahi ban san Inda ka d'auko halinka ba , sam mahaifinka ba haka yake ba mutumin kirki ne, mahaifinka baya uhm baya uhm bare miskilanci , kullum cikin neman yadda zai kyautata mana daku ya'yansa da 'yan'uwansa yake , a kullum mahaifinku so yake ku zama na gari a rayuwa sannan masu jin kan iyaye da tausayi Allah ya duba bayan mahaifinku cikin kaf ya'yan mahaifinka Kai ne kawai ka fita dabam acikinsu da wasu halaiya Kai ma Kuma wannan halin miskilancin da zafin zuciyar ne illarka tun kafin ya rasu ya fad'a yace bashi ka d'auko ba .bari na fad'a maka gsky wannan halin naka sam ba nashi bane Kai ka san Inda ka samo abunka dan shi ba haka yake yi ba, dan ta mahaifinka duniya bazai tashi ba ,ga rikon addinin ga tsananin zumunci da sanyi hali ." ga lokaci yazo daya kamata ka tattara biyayyar Uba da uwa ka had'a kayi min amman kullum cikin musguna min kake akan zance aure auren da kai ne kaji dadinsa , wallahi duk macen data samu miji irin mai halin mahaifinka ta gama dace a duniya da lahira ni kaina kullum kukan da nake yi kenan mahaifinka ya bauta mana ya sangartani sannan ya bautawa zumunci Allah ya jikansa yasa aljanna ce makomarsa ka canja idan zaka canza tana gama fad'ar haka ta fita ta barshi cike da zafin zuciya." Jiki a sanyaye ya bar d'akin zuwa nashi yana shiga d'akinsa ya shiga zariya kwalkwaluwarsa ta shiga tunani , sai dai Kansa ya toshe ya cunkushe guri d'aya ya kasa tunanin komai ya zauna a bakin gado ya had'e hannunwansa duka a ha'barsa yana tunanin can byn wasu mintuna ya mike ya koma kan bedside ya zauna yayi shiru yana kallon d'akin ,sake mikewa yayi ya d'aura Kashi akan katifa yana Jin quna a ransa. zuciyarsa na dokawa da matsanacin karfin gaske ya tashi ya nufi falonsa ya bud'e fridge ya d'auki kwalin stute superior cranberry me sanyi ya d'auki glass cup ya d'aura drink akan center table ya juya jiki a mace ya koma zuwa d'akinsa ya d'auko kwalin sigari rotimax ya dawo ya koma kan kujera ya zauna ya tsiyaya ruwan lemun ya d'aura kafafuwansa akan table tare da hard'esu guri d'aya ya Kai Karan sigari bakinsa ya kunna ya fara zuka a hankali yana fitar da hayaki "yaushe rabonsa da sha ? sam bazai tuna yaushe rabonsa dasha ba cike da izza itama sigarin yake zuka idan ba an fad'a maka ba bazaka ta'ba sanin shi din mashayin shigari bane koda yake baya sha sai idan ya tsinci Kansa cikin ' bacin rai mai tsanani " . yayi shiru yana zuka sigari yana tunani mahaifinsa yasan da yana raye duk runtsi da hkn bata faru dashi ba , shiyasa yake son mahaifinsa Sosai wasu hawaye masu zafi suka zubo masa wanda rabonsa daya zubar da hawaye har ya manta a tsawon rayuwarsa amman yau ya tuna qalbinsa masoyinsa , ana cewa mutun yafi son mahaifiyarsa akan mahaifinsa shi dai sai dai sonsu yazo d'aya a ransa , yasan soyayyarsu suyi kanka da juna ,mahaifinsa ya soshi har cikin ransa idan yana cikin damuwa sai ya fishi shiga damuwa , haka idan yana cikin farinciki ,daf da zai rasu da zarar ya kyalesa sai ya fashe da kuka alokacin hjy zulaiheart ke tmbyrsa dalilin kuka sai yace "ba kowa nake wa kuka ba sai Adam ,Ina jin tausayin rayuwar Adam bashi da dan'uwa kamar sauran mutane naso sun kasance su biyu ya samu abokin shawara "a she tabbas shi din abun tausayi ne bai ta'ba sani ba sai a tsakanin wannan lokacin da abubuwa suka kwa'be masa yan'uwansa mata sun had'e kai da mahaifiyarsa yasan da yana da dan'uwa nmj zai iya bin bayansa Koda kuwa zaa fi karfinsa ne hawaye ke gangaro masa kamar karamin yaro yana cigaba da busawa cikinsa hayaki ." ranar a zaune ya kwana cikin tsananin tashin hankali Kash da Kashi damuwar auren dole da za'a masa da tunanin Nurul qalbinsa dan da zarar ya runtse idanuwanshi dan bacci sai yaga hoton princess dinsa tana gargadinsa akan auren da zai yi tana gudu tana binsa tana furta kar yayi aure ya barta .tsawon sati guda tunda daya amince da batun auren mryam bai sake zuwa Inda mami take ba yana d'akinsa yaki barin ya had'u da kowa dan gbdy fita ya fita ransa gbdy soyayyar princess ya dawo masa sabo fil ganin tunanin bazai bar kanshi ba yasashi mikewa daga kwance da yake tare da zura takalmi silifas ya fito ya shiga d'akin zanensa ya tsaya a gaban hotonta shiru yana kallonta kmr yayi mata mgn ta amsa fuskarta d'auke da murmushin da shine ya zanata ." Hannu ya kai ya ja hoton a zuciye ya yaga yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa"A ina kike tsawon shekaru ?"a Ina zan ganki ?"kin hanani ganinki,kin hanani sukuni daga yau kin zamo tarihi gareni bazan sake damuwa dake ba ,bazan sake tunaninki ba zan manta dake arayuwata ,zan cire soyayyarki a zuciyata tunda baki da imani baki da tausayi ya fad'a yana wani irin ihu tare da daga hannuwansa duka sama "haaaaaaaa!!! "Hauka yake sosai yana wargaza komai dake cikin d'akin tare da cigaba da yaga hotunan zanenta yana filinging dasu har da system dinsa da tsarkar wuyansa wanda zanen hotonta ne aciki , gbdy ya hargitsa d'akin yana watsi da komai har sanda mahaifiyarsa ta shigo hannunta rike da cup wanda yake d'auke da ruwan coffee, bedroom dinsa ta shiga bata gansa ba dan ita kanta ta kasa jurewa rashinsa na tsawon kwanaki , ganin baya ciki ta fito har zata fita ta jiyo sautinsa a hargitse dan haka ta shigo d'akin ." ta tsay a bayansa ta cigaba da kallonsa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa bai sani ba yayi zurfi cikin tsananin damuwa cikin haka ya sake d'aukar hoton zanen princess yay sama dashi sai akan fuskar hjy zulaiheart ta runtse idanunta da sauri jikinta na rawa kamar ance ya juyo ya ganta tsaye tana kallonsa cikin tsananin tashin hankali sanye da doguwar rigar shadda milk colour mai dogon hannu kyam idanunta a kanshi ta kasa daukewa ." cikin sauri dunkule hannunsa ya naushi iska tare da durkushewa kasa ya soma tattara kayan daya hargitsa yana cewa "so..sorry sweetheart am really sorry cikin in Ina, numfashi ta sauke da ajiyar zuciya sannan ta zauna a bakin gado batare da ta ajiye cup din hannunta ba sai dai har lokacin idanunta na Kansa tana jin ciwo da zafin halin da yake ciki ,kusan minti biyar tana zaune tana kallonsa yana faman tattara d'akin yana mata sannu sannan ta fara magana a tsanake ." kayi hakuri Adamcy karka damu da wannan" ya k'arasa kwashe kayan da yayi waste dasu zuciyarsa na zafi da quna "kana jina Adamcy ita rayuwa babu takurawa idan baka sameta anan ba wata Killa zaka sameta a aljanna ,yakamata ka gane hakan , karka shiga rud'ani idan an fad'a maka gasky illa ka dinga yarda dashi , komai na duniya babu sauki kmr yadda ka d'aukeshi sai an jajirce be a man Adamcy karka lalata rayuwarka akan yarinyar mafarkinka ." "kamar yadda na sha fad'a maka ba kowani mafarki ke zama gaskiya ba , ta mike a hankali ta k'araso gurinsa ta riko hannunsa tayi taku biyu ta zaunar dashi akan kujera kwaya d'aya dake d'akin , madadin ta bashi coffee din hannunta sai ta fita gabanta na dokawa da matsanacin karfi dan nan duniya idan akwai abinda ta tsana to bai wuce damuwar tilon d'anta ba , sam bata son ganinsa cikin damuwa ko wannan auren ma zata yi masa ne dan dole saboda tasan muddin batayi masa ba zai iya kare rayuwarsa haka batare da yayi ba ." ko cikakken minti biyar batayi ba ta dawo da gorar ruwa mai sanyi ta mika masa , babu mutsu ya kar'ba ya kafa a bakinsa bai cire ba sai daya shanye tasssss sannan ajiye yana sauke numfashi taja hannunsa zuwa bedroom dinsa yana biye daita yana zance zuci .ya yarda tabbas mahaifiyarsa na sonshi kuma gsky take fad'a masa akan yarinyar mafarkinsa sai dai ya rasa dalilin da har wannan lokacin ya kasa yarda iya mafarki ne kawai soyayyarsa zata tsaya ..." Tana shiga d'akinsa ta zauna akan gado ya kwanta ya d'aura kanshi akan cinyarta yana mai Jin damuwarsa tana raguwa , a hankali ta Kai hannunta saman sumar kanshi ta fara shafawa tana mai sake jin tsananin son d'anta Ina ma zata ga wannan yarinyar a zahiri da babu abinda zai hana bata mallaka masa ita ta kowani hali ba ." ta dade zaune har bacci yayi awon gaba dashi Sannan ta d'auke kanshi ta maida kan pillow ta lullu'be masa rabin jiki ta sauko ta qara masa karfin ac ta kashe masa wuta ta duka tayi kissing din foring head dinsa tana sake shafa sumarsa sannan ta nufi kofar fita tana rufo masa kofar ." Koda ta koma d'akinta kasa runtsawa tayi tana tsaye akan ka'fafunta tana Kai wa Allah kukanta akan lamarin tilon d'anta sai da tayi sallah asuba sannan ta d'an kwanta Shima bata wani dade ba ta farka ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin doguwar riga ta sanya awarwaro da zobin ziniri ta feshe ilahirin jikinta da turaren humura mai sanyi kamshi hjy zulaiheart kenna Allah yayita da son kwaliyya da son kamshi tun tana matashiyarta har zuwa wannan lokacin da tsufa yazo mata ta fito zuwa babban parlour'nta tare da danna bell din bangaren masu aiki kafin kace me gbdy sun hallara sun zube a gabanta suna gaisheta cike da girmamawa. ta dubesu tare da amsawa cikin tsananin farinciki dan tana da sakewa da masu aikinta bata zalintarsu sannan bata son su zalinceta yadda take jin dadin zama dasu haka suma suke yabonta da yi mata fatan alkhairi a rayuwarta . Fuskarta a sake ta bawa 'yan aikinta umarni abinda take bukata su dafa a ranar wanda zai zamo na sadaka ne kasancewarsa juma'a "yau za'a yi abincin sadakan da aka saba yi amman ina son a qara hannu sannan a had'a da wake da shinkafa Ina son a rabawa yara kanana suka amsa da "to" sannan kowace ta soma k'okarin mikewa "ke tabawa ..." wacce aka kira da tabawa ta tsaya sauran suka kama gabansu dan fara aiwatar da aiki "ki shirya breakfast wa sauran jamar gida idan kin gama ki hanzarta sanar dani ." "shikenan hajiya itama ta fad'a tare da juyawa da sauri ." Hjy zulaiheart tana zaune mrym da nana hauwa'u suka shigo duk suka zauna suka sanyata a tsakiya kowacce hannunta empty babu Komai kamar Koda yaushe sun baro wayoyinsu na gado a d'akinsu d'aya byn daya suka gaisheta ta amsa cike da sakin fuska a fili tace "yau dai babu danne danne waya ko Kuma an gaji da rike wayar ne ? sukayi murmushi nana hauwa'u tace " ai tun wuri nayiwa marsi kashedi muddin yaya adam zata aura ta saukakawa kanta akan shiga yanar gizo "wannan haka ne domin zai iya kawo rashin jituwa a tsakaninsu abinda bazan so faruwarsa ba kenan nafi bukatarta zaman lfy atsakaninsu. ta Kalli bangaren da nana hauwa'u take zaune tace " ya batun shari'a da ake da yarinyar da ake zargi ta kashe mubina ne har yanzu na kasa fahimtar gskyr magana gashi Adamcy nata k'okarin shiga cikin maganar uncle jay ya hana ?"ai gsky gara da uncle jay ya hana wani shari'a za'a yi mami Abar ko waye da Allah kawai mubina dai ta rigada ta mutu bazata dawo ba komai za'ayi ,haka Allah ya qaddaro mata nata mutuwar zata rataya a wuyan wani inshallahu ruhinta na aljanna suka had'a baki gurin cewa" Ameen " " mrym tashi ki shiga ki d'auko min wayata a daki na kira naji yadda ake ciki ta mike tsam ta shiga cikin bedroom din hajiya zulaiheart ta iske wayar akan katifarta ta d'auka tana duba fuskar wayar nan take gabanta yayi wani mummunar fad'uwa sakamakon idanunta daya sauka akan hoton ATA tayi shiru tana kallonsa cikin suit bakake idanunshi manne da farin glass yayinda fuskarsa ke d'auke da murmushin gefen baki wanda bai gama bayyana ba hakan km qara masa kyau yake , ta lumshe idanunta tana Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta ,ada sam bata jinsa aranta amman tun sanda yasa akayi kiranta akan batun soyayyarsa ta soma Jin wani Abu akansa komai nashi mai kyau tamkar shi ya hallici kansa ." jiki a sanyaye ta Kai mata wayar ta amsa tana kokarin neman layin uncle jay byn sun gaisa take tmbyrsa halin da'ake ciki "mgn dai daya ce nace abarwa Allah abar ruhin diyata ya samu salama ". "uncle jay taya zaka fadi haka byn kasan zuciyar sha'awanatu bazataji dadi ba ? "nasani amman yarinyar nan da ake tuhunma ba itace tayi kisan ba , tabbas makashin mutun d'aya ne da wanda ya kashe mubina da wanda ya kashe sadear mutun d'aya ne amman ba wannan yarinyar bace, ita dai ta taka tsawun barawo ne gbdy bincike ya nuna makashin da hannun hagu yayi kisan ita Kuma hadiza hannun dama take amfani dashi sam gbdy babu alamun sheidar hannunta ,yanzu haka an gama duk wani bincike ranar monday kotu zata wanke yarinyar Allah dai ya jikan mubina yasa ta huta "Ameen Hjy zulaiheart ta furta a fili tana mai tausaya masa "ko me suka yiwa wannan makashi da yake musu kisan gilla? "Allah masani "sun dan jima suna waya sannan sukayi sallama . "Maryam ...!" mami ta kira sunanta gbdy ta tattara duk wani attention dinta zuwa gareta tana kallonta "Ina saka rai zuwa karshen satin nan za'a yi mgnr bikinku da Adamcy " gabanta ne ya sake fad'uwa kmr zai fasa qirjinta yayo waje "ya kamata ki sake kwarewa agurin girki da sauran abubuwan da yake da bukata dan haka daga yau kice zaki cigaba da kulawa da komai na bangaren abincinsa kinji ko ". ta gyada mata Kai kawai tare da amsawa da "to !" hawaye na ciccikowa acikin kwarnin idanunta tayi saurin dennewa ta rasa dalilin da take tsananin Jin tsoronsa da tsoro aurensa." " ki samu natsuwar zuciya ki tashi kije yanzu ki tmbayesa abinda yake bukatar ci a hankali ta mike jikinta na rawa kamar mazari ta nufi part dinsa akan hanyarta ta tsaya tana daidaita natsuwarta sannan ta k'arasa kofar shiga falonsa tayi sallama ba'a amsa ba har ta juya taji sautin muryarsa yana cewa ",waye ne ? ta juyo da sauri "ni ...nice ta fad'a da sauri jikinta da bakinta na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta ta rasa dalilin hawayen nata Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika daga shi sai gajeren wando army green iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana surar jikinsa a fili ake iya ganin kwantaccen sumar dake kwance a cinyarsa da qirjinsa haka kan nipples dinsa sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ." A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin haiyacinta a hankali ta d'ago ta kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace "ke lafiyarki tsayuwar me kike yi anan ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka " ya tsuru mata Ido a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai." mami ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata kenan ba "to shikenan maza ki shiga ki dafa masa abinda yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu" hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam yi tafiyarki kinji duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ." ***** Da misalin karfe biyu na rana bayan an sauko daga massalaci hajiya zulaiheart da kanta ta fito zuwa haraban gidan ta fara rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka wake da shimfa acikin takeaway fari tare naira dari biyar biyar sababbin yayinda ATA ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata dan sauranta yaki barin jininsa komai nashi irin nasu ne sanye yake cikin farin yadi voil kafafunsa sanye da takalmi fari haka ma Kansa sanye da hula fari mai ratsin baki yayinda tsintsiyar hannunsa ke d'aure da agogon silver rolex yayi kyau sosai kamar ka sacesa ka gudu sai dai kallo d'aya zaka masa kasan zuciyarsa dakushe take da tsananin damuwa ." tsayawa yayi cak yana cigaba da kallon mahaifiyarsa cikin haka ta juyo nan take suka had'a Ido daita ya sakar mata taadaddaden murmushinsa dake sake bayyanar da ainihin bawar kyawun da Allah yayi masa wanda wannan murmushin babu mai ganinsa sai ita , murmushi ta sakar masa cike da farinciki ganin murmushinsa da ba kowa yake gani ba tana tsananin son kyakkyawan tilon d'anta shi din dabam ne acikin zuciyarta ,uwa Uba nagarta tana masa so mai tafiyar da ruhi shine karfin gwiwarta ." a hankali ya soma takowa zuwa Inda take har ya k'araso gareta ya tsaya kusa daita yana tayata rabawa yaran kudi duk wanda ta bawa takeway sai ya mika masa kudi ,tana raba abinci tana dubansa tana murmushin jin dadi "thank you my beloving prince " you're welcome my queen ya fad'a yana kallonta bayan sun gama tare suka koma ciki suna tautaunawa a falonta sukayi masauki ya zauna yana runtse idanuwanshi."Adamcy nah...." ! ya amsa can kasan makoshi" inshallahu wannan satin zanyiwa su baba babba maganar aurenku ayi a wuce gurin muryarsa a raunane yace "to sweetheart kuyi duk abinda ya dace na sallama miki komai ." "bangane ka sallama min komai ba kana nufin bazaka tabuka komai ba ?"me kike son nayi sweetheart idan akwai abinda kike bukatar nayi ki sanar min zanyi ganin idan ya cigaba da biye mata maganar auren zasuyitayi yasa yay saurin runtse idanuwanshi yana cewa "wayyohhhly sweetheart cikin kwantar da murya tace "ya'akayi Adamcy ? "sweetheart yunwa nake ji cikina har ya fara zafi murmushi tayi "ko kunya baka ji ba kmr wani jinjiri ka dai rage wannan shagwabar ka bar wa yaranka "a'a sweetheart ki barni nayiwa uwata suma idan sunzo ga guri nan kowa yayiwa mamansa "to ai shikenan bari nasa maryam ta samarmaka abinda zakaci "wace mrym kuma dan Allah kiyi min da kanki karki rage min Jin dadi wannan yarinyar babu abinda ta iya Kuma ma nafi son Ina cin abinci daga hannunki ni dai gsky banason abincinta "ya Isa sarkin naci amman dole kaci daga hannun matar da zaka aura wata rana ." "naji amman ayi sauri ayi min please dariya ya bata sosai wai ayi sauri ayi mishi ATA kenan ko yaushe idan yana tare da mahaifiyarsa daukar kanshi yake kamar karamin yaro hjy zulaiheart ta d'auki wayarta ta soma Neman layin maryam sai dai bai shiga ba ta ajiye wayar tana Kiran daya daga cikin masu aiki ." Tana zaune a d'akinsu hjy zulaiheart ta Aiko mai aiki akirata da hanzarinta ta Isa parlour'n tace "kije ki kawowa Adamcy wani Abu yaci yunwa yake ji ta Dan saci kallon Inda yake tana Jin mummunar fad'uwa gaba sannan ta gaishesa sai dai bai Kalli Inda take ba bare ya amsa gaisuwarta ,Kai tsaye kitchen ta nufa sai dai ta rasa me zata dafa masa shap shap yaci ,kawai tayi tunanin daura masa indomi da kwai ta kawo masa a lokacin data fito bata tarar da hjy zulaiheart ba sai aunty khadeja zaune agurin suna magana da ATA ta ajiye akan table din dake gabansa tare da gaishe da aunty khadeja kamshin indomin da yaji ya ziyarci hancinsa ya balain ta'ba zuciyarsa na take ransa ya baci . a hankali ta juya zata wuce dan Sam bata jurar tsayuwa a duk Inda yake muryarsa a kasalance yace"ke meye wannan kika kawo ? ta dawo a hankali ta tsaya tare da cewa "indomi da ......"a fusace ya dan gyara zamansa ya tsaidaita "shine abinda kika iya dafawa? jikinta na rawa ta dubi aunty khadeja dake zaune tana juya masa Kai "nace shine abinda kika iya dafawa ?ta girgiza masa kai jikinta na rawa gbdy a tsorace take a tsaye,shi kuwa kallonta kawai yake da seyx eye's dinsa wanda hakan yasa hantar cikinta cigaba da kadawa lumshe idanunshi yayi tare da yin shiru ya koma ya jingina jikinsa da kujerar da yake zaune ya soma motsa labbansa "wai irin wannan matar ake min sha'awar ajiyewa a gidana ?yayi mgnr a fili yana sake jan tsaki a fili "wacce irin sakariya mata ce wannan khadeja saboda rashin tarbiya indomi fa me zanyi da ita ? "tuni idanunta suka kawo kwalla bakinta na rawa tace " kayi hakuri bari naje na sake dafa maka wani abu bude idanunshi yayi fesss akanta Yana cewa "shut up me yasa baki dafa ba tun farko ? ya karasa maganar yana buga mata wata hadaddiyar tsawa nan take jikinta ya kama rawa da hannu aunty khadeja tayi mata alamar ta wuce kmr jira take tayi gaba da sauri tana haki ." "kayi hakuri adamcy da sannu zata iya komai "har sai yaushe khadeja ? nifa akan wannan matsalar zamu tabbata muna samun matsala daita bazan juri zama da macen da bata iya komai ba?" shekara ashirin da biyar da wani abu amman ace mace bata iya girka komai ba sai yaushe ? "gsky gsky ni dai an ....... " sai Kuma yayi shiru ya kasa cigaba da mgn "yanzu dai kayi hakuri me zaka ci ni sai na shiga na girka maka da kaina a fusace yace "barshi kawai juyin duniya yaki yace bai ci haka ta hakura ta barshi ."tsaki ya dinga ja bai san me ma ya jashi cewar zai ci abinci ba mikewa yayi ya bar gidan gbdy Aunty khadija tabi da kallo gsky akwai kuskure atattare da maryam dan rashin iya girki babban matsala ne a gidan miji ba wai shekara ashirin da biyar da yan kai ba a tunaninta maryam zata kai talatin dan tsirarau da auta babu yawa .." ****** Maryama na zaune da yammacin ranar monday tana wanke kayan Aunty salma da kayan kanwarta sakina wacce ta kasance diya ga Aunty salma duk da lokacin makarantar islamiyya ne amman ita bata samu damar zuwa ba saboda aikin da matar yayan mahaifinta ta sata , wanke take da iyakar karfinta har ya zamo bata iya wankewa da karfinta sakamakon gajiyar data tsarketa domin ta jima batayi irin wannan aikin ba tun karfe biyu lokacin data taso daga makarantar boko gashi har yanzu biyar ta wuce sallace kawai ta tasheta daga tsugunno datayi tana faman dikar wanki ." Sakina ta shigo cikin haraban gidan da sallama babu sukuni a fuskarta dan kallo daya tayi mata ta fahimci haka ganin halin data ganta yasa ta sake shiga cikin damuwa ta matso kusa daita ta tsaya cikin bacin rai " maryama daman wanki kika tsaya shine dalilin da yasa baki zo makaranta ba yau .?" ta fad'a ranta a bace tana kallon cikin falon Aunty salma." da kyar maryama ta kirkiro murmushin dole wanda yafi kuka ciwo dan komai ya wuce a zuciyarta dan bata qaunar sa'insar sakina da mahaifiyarta akanta muryarta a sake tace "kayan makarantar nawa ne basu bushe ba shine nace Aunty salma ta kawo wankinta na wanke da naki dan zaman bazai min dadi ba tunda bazan samu zuwa makaranta ba ta fad'a mata haka cikin zaro wani kaya daga cikin tarin kayan dake ajiye a gefe guda tana qoqarin dannashi cikin ruwan wanki sakina ta fixge cikin fushi tana cewa "wallahi karya ne nafa san halin mama itace ta hadaki da wannan aikin aikin daya yafi karfin ace mutun daya ne zai yi ni ban san me yasa mama take yin haka ba ..." Aunty salma ta fito daga cikin dakinta sakamakon jin maganar diyarta "sakinata har kin dawo sannu da dawowa sakinata ta fad'a tana qarasowa ta dafa kafadarta cike da kulawa da tsantsar soyayya sakina ta zumburo baki "haba mama yanzu abinda kikayi ya dace dan meye zaki lodawa maryama uban wanki haka alhalin kina sane da cewa ko mu duka muka hadu bazai qare acikin kwana biyu ba haba ni wallahi wallahi bana só abinda kikeyi wa yaruwata sautari umma tana sanar dake illar haka karfa ki manta maryama ba baiwa bace a gidan nan ' ya ce kamar kowani d'a acikin gidan nan ko bakya kaunarta ita da mahaifiyarta bai kamata ace kina daukar abubuwan wahala kina sakata ba tunda ko babu komai yaruwata ce ko dan ni ya kamata kina son maryama saboda ina sonta ina qaunarta in har soyayyar da kike min ta gskiya ce ." Aunty salma ta kwabe baki "sannu sarkin yan iyayi ta fad'a a zuciyarta amman a zahiri cewa tayi "meye acikin dan wannan aikin yanzu dan na saka maryama dan wannan aikin zai sa Kiyi zargin bana sonta ne ko wani abu ? tô idan baki sani ba bari na fad'a miki ina mata kwadayin samun lada ne shiyasa nake sakata aiki yanzu Ke kin san irin ladan da zata samu har idan ta gama min ."? "To ni me yasa baki sani ba tunda aikin lada ne in har idan kwadayin lada Kike mata ?" Ki dinga hadawa dani daita gsky ni banaso ." maryama na durkushe hawaye suna son zubo mata daga cikin kwarnin idanunta amman ta dannesu dan kawai bata son sakina ta fuskanci damuwarta dan tasan dole sai ta qarawa yiwa mahaifiyarta bori ita km abinda bata só kenan taga suna samun sabani akanta da mahaifiyarta domin ita kam tarasa gane maanar hakan rashin kunya ce ko gaskiya take fadawa mahaifiyarta da ta kasance damuwa atattare daita da tata mahaifiyar " "shikenan sakina daga yau na daina Kiyi hakuri ina sata ne dan tafiki kuzari yanzu muje kici abinci ai kuwa sakina taki binta "wani irin muje naci abinci ki dai zo mu hadu har dake mu qarasa wanke sauran kayan Aunty salma tabi wanki da maryama ta wanke sama da rabi ta waigo ta dubi sakina "a'a ki bari ta qarasa tunda sauran ka.." A'a wallahi ki tsaya dai mu qarasa tas ita ba mutun bace tun rana take ta faman aiki kamar wata inji." Aunty salma tayi shiru tana duban yarta ta ja tsaki ta nufi hanyar dakinta tana cewa "ai sai dai idan ke zaki iya ni dai babu abinda zanyi taka nas naje na arota wajen uwarta shine dan tsabar iyayi irin naki zaki ce ga zance ga magana da yanzu Ke na saka bazakiyi ba dan yanzu kinga na saka maryama shine zaki zo da shegen iyayi shikenan ki tayata ku qarasa tare ta wuce tana bala'i maryama na tsaye batare da tace uhm ba bare uhm uhm dan bata son tayi laifi dan a yanzu ma tana hankalce da Aunty salma harararta take sakina ta gyara botiki ta cire hijab dinta ta sunkuya ta tura mayafinta da maryama Ke qoqarin turawa cikin ruwan wanki ta fara wankewa da sabulu data tsinta acikin ruwa ." "Why sakina ? mai haka ki barni na qarasa mana bana son naga kina sai sa da mahaifiyarki akaina ki daina babu kyau tunda kinga ni bana yiwa Aunty haka "itama ai abinda take miki babu kyau ko dan ba itace ta haifeki ba kullum sai ta dinga zuwa tana aroki dan taga Aunty shiru shiru bata son magana aikin yau da dabam na gobe dabam ta hanaki zuwa makaranta malam mustaphata sau uku yana shigowa tambyarki nace bakizo ba kina gida bakya jin dadi "ai ba ita kadai Ke sakani aiki ba umma ma ina yi mata "eh kina yiwa umma amman ita tasan daidai dan bazata barki kina aiki har wannan lokacin bakije islamiyya ba kar ma ki hada mama da umma dan ba abu daya bane ." maryama tayi shiru Tare da sunkuyar da kanta kasa tabbas akwai bambamci tana son aikin umma fiyye dana kowa ko babu komai tana qaunar mahaifiyarta kum tana tausayawa rayuwarsu tun kafin mahaifinsu ya bar duniya ta kalli sakina tana son hanata wanki amman tasan bazata yarda ba kawai ta cigaba da kallonta ita yanzu abinda yafi damunta yunwa take ji sosai domin Aunty salma bata bata ko ruwa ba wai sai ta gama sallah ma da kyar tayi ." Sakina ta cire hannunta ta shiga kitchen ta dauko plet din abinci ta fito ta daura mata akan cinyarta "kici !ta tsurawa abincin ido tana kallona batasani ba itama sakina ita take kallo ta matsota da sauri tana son sani abinda yasa tayi shiru bata fara cin abinci ba maryama tayi tsuru itama haka ta kalli abinci ta kalli maryama "ko abinci yayi kadan ne?ta fad'a girgiza kai maryama tayi "ya ma yi min yawa "to me yasa kikayi shiru kina tunani ?" Kai sakina kina son damun kanki akaina ta fad'a tana soma cin abinci jikinta babu kwari ga rawar da yake saboda yunwar da take ji maryama bata bar bangaren su sakina ba sai daf da magariba shima da taimakon sakina ne ." A matukar gajiye ta shigo part dinsu ta zauna akan kujera jikinta tattare da tsananin gajiya Aunty ta qaraso ta tsaya akanta "ya naga duk kinyi wani iri ko kin aikin da yawa ne ? numfashi ta fesar tare da waskewa dan bata son nunawa mahaifiyar ta damuwarta domin duk hakurinta taji irin aikin datayi yau sai taji ciwo aranta dan haka ta dubi mahaifiyarta tace "babu komai ai aikin ma bashi da yawa kuma har munyi mun gama tare da sakina sai lokaci ta saki jikinta ta zauna kusa daita "sannu princess dina shiyasa nake qara jin sonki araina ta fad'a Tare da shafa kanta da yake sunan datake kiranta dashi kenan atare sukayi shiru Aunty na matukar tausaya mata ita da danuwanta habib kasancewar sun taso cikin maraicin uba gashi dangin ubansu ba qaunarsu suke ba idan aka cire mahaifiyar babansu da yayan babansu da matarsa to babu mutun daya da zata cire." Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS AYSHABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 12 Aunty tayi shiru tana duban maryama yanayinta kamar kazar da'aka tsamo cikin ruwa gaba daya alamu sun nuna gajiya a tattare daita amman dan karfin halin irin nata take boye mata damuwarta , hawayen da suka cicciko acikin kwarnin idanunta tayi qoqarin maidawa tana danne damuwarta saboda farinciki diyarta ." ahankali ta dauke kwayar idanunta aKan tilon diyarta zuwa wani bangare dabam tana tunanin rayuwa da abubuwan da sukai ta faruwa daita ta sha wahala arayuwarta shiyasa batason maryama ta sha wahala irin wanda ta sha ,wannan aikin da aunty salma kesata yana matukar ta'ba zuciyarta domin ko ita da tayi sanadiyyar zuwanta duniya bata sakata aiki haka koda tace zatayi ma bata yarda ta bar mata tayi ita kadai sai dai suyi a tare amman bata da yadda zatayi da rayuwata dan bazata iya hanawa ba "tabbas bata da yadda zatayi kuma bata isa ta hanata ba tunda zaman gidan ya zame mata dole dan bata son rasa yaranta kuma bata son ta koma ga danginta ." tayi maganar a kasan ranta . maryama ta kalli mahaifiyarta duk da bata san me ya canza yanayinta ba amman tasan meke yawo acikin kwakwaluwarta ta matsota sosai tana jijiga Aunty wacce tayi nisa cikin tunanin rayuwa "meke damunki Aunty ?firgigib ta dawo haiyacinta tana dubanta duba mai tattare da damuwa tana cewa " babu abinda Ke damuna princess " ta fad'a tana mai jin tausayinta domin dai duk halin da suka tsinci kansu aciki itace sila, itace silar janyowa ya'yanta rayuwar wahala wacce bata kamacesu ba duk wani abu daya faru da ya'yanta itace ta janyo masu adalilin zunzurutun Kaunar data nunawa mahaifinsu ya janyo mata rasa komai domin ta zabi Mahaifinsu ta bar danginta wanda yasa kowa acikin danginta yaji babu dadi akanta." "me yasa kowa ya tsanemu acikin gidan nan ?" bayan mahaifinmu da granny da umma da abba babu mai qaunarmu acikin gidan nan gashi abba ya rasu ya barmu kamar yadda mahaifinmu ya barmu why Aunty ?me yasa basa qaunarmu ? "Me yasa suka tsanemu ko kin yi masu wani laifi ne ?ina son nasan abinda ya kawo wannan kiyayyar ?shiru kawai Aunty tayi tana dubanta dan bata da abinda zata fad'a mata domin kare kanta maryama yarinya ce da bata wuce shekara ashirin a duniya ba but she's smart in ance smart ana nufin mutun wanda ya kasance mai tsananin hankalin da kwakwaluwa tare da kaifin baseera sannan yarinya ce mai fadar gsky komai d'acinta zata fad'a she's very shap akan komai dan wani lokaci har mamaki take bata idan tayi wani abu kanta naja sosai fiyye da yadda take tunanin tasan muddin taji ta zabi mahaifinta ne akan iyayenta yasa dangita suka juya mata baya tabbas zata fad'a mata gskyr data kasa amsa daga ahlinta "Ina danginki suke Aunty ?ta jeho mata tambayar data nemi bugar mata da zuciya tana mai d'aura kanta a saman cinyarta ." tsura mata ido tayi tana kallonta kafin daga bisani tace "suna nan ! "suna nan amman me yasa bakya zuwa inda suke kamar yadda Aunty salma keyi ?"babu komai "ta bata amsa atakaice tana jin wani tuttukin bakinciki acikin ranta mai tattare da damuwa "Aunty karki ce babu komai lallai akwai dalili akwai abinda yasa bakya son zuwa inda suke har yasa bamu sansu ba ,mahaifiya mahaifi yan'uwa duk ba abun wasa bane domin suna da matukar mahimanci arayuwar mutun ." Naunayen ajiyar zuciya aunty ta sauke tana sake tsura mata ido "dan baki san abinda suka aikata gareni bane maryama shiyasa zaki fadi haka ta fad'a hk a zuciyarta " ahlinki suna da matukar mahimanci sannan suna da hakki akanki most especially iyaye yana da kyau a dinga basu hakinsu domin hakan zai samarwa mai yi kwanciyar hankali ,meye acikin duniyar da babu albarka iyaye acikinta ?yadda kike iya hakurin rashin zuwa ga iyayenki bazan iya barinki daidai da second daya batare dana daura kwayar idanuna akanki ba saboda qaunar da nake miki ina sonki aunty fiyye da komai dake cikin duniyar nan dan haka Kiyi qoqarin kije garesu nasan suma zuciyoyinsu na cike da kewarki da qaunarki tunda kika haifeni na girma na kai wannan shekarun ban ta'ba ganin ranar da kika shirya kika ce zakije ga ahlinki ba , kullum muna cikin dangin dady cikin kaskanci da wulakanci ya kamata ko sau daya ne muje domin nima ina son ganinsu ina son ganin danginki zaki je ga ahlinki ? tayi mata tmbyr tana mai tsura mata kyawawan idanunta masu matukar kyau ." Kusan minti goma aunty bata amsa mata ba har sai data sake maimaita abinda ta fad'a sannan tace "to maryama zanyi qoqarin zuwa." ta fadi hakan ne ba dan zata aikata hakan ba sai dan abar maganar ta wuce "da gaske kike Aunty zaki ga ahlinki ? murmushi tayi mata domin bata son damuwarta dan ta fahimci yau din nan tana cikin damuwa ." maryama ta rungumeta tsam tsam ajikinta tana mai jin dadi "naji matukar dadi Aunty ina son ganin ahlinki nasan habib ma zai ji dadi yaushe zamu je ? ta fad'a tana zare jikinta daga na Aunty yayinda idanunta Ke kallonta aunty tai shiru tana dubanta hakan nan ta tsinci kanta cikin farinciki wanda tasan maryama ce sila tana matukar son farincikin yaranta murmushinsu murmushinta ne haka zalika damuwarsu damuwarta ce tana matukar qaunarsu fiyye da komai dake cikin duniyar nan dan sune iyayenta yayyaenta kannenta komai nata daman tasha yin addua ko a can baya Allah ya bata ya'ya masu albarka wadan da zasu maye mata gurbin yan'uwa." "aunty ! Ta kira sunanta cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki a duk sanda tayi mata magana da wannan muryar tana tuno mata da mahaifinta ko habib da ya kasance nmj bai dauko sanyin muryar mahaifinsu ba sai ita "na'am my princess ta amsa tana dubanta tana saurararta "a ina danginki suke zaune ?"tayi mata tmbyr fuskarta na nuna farinciki." "suna zaune acikin garin nan" "cikin garin nan ? maryama ta maimaita abinda mahaifiyarta ta fad'a cike da mamaki Aunty ta gyada mata kai alamun" Eh!wani sabon mamaki ya sake cunkushe zuciyar maryama "suna zaune a gari daya amman duk tsawon wannan shekaru bata taba zuwa dasu inda suke ba bare su sansu gashi ta zauna tana rayuwa cikin kunci da babu tamkar wacce bata da kowa acikin duniyar nan ,numfashi ta janyo da kyar ta fesar a hankali kafin ta bude bakinta da kyar "yaushe zamu je wurinsu ?". "karki damu sarauniyata in sha allahu zamu " cike da farinciki maryama ta kai hannunta ta dauki remut tana mai kunna tv tare da maida hankalinta Kan program din daake yi a tashar galaxy tv tana mai jin farinciki da natsuwar zuciya "Aunty zan so naji ranar da zamu na soma lissafa kwanaki "canza fuska tayi batare datai auni ba kafin daga bisani ta kawar da kanta gefe dan karta fahimci damuwarta dan gbdy ta soma neman natsuwarta ta rasa bazata iya zuwa garesu ba ,haka zalika ya'yanta ma bazasuje ga danginta ba most especially mahaifiyarta ta barsu har abada kamar yadda suka barta zata karasa rayuwarta a haka cikin kunci ." a qalla sun dauki mintuna goma zaune suna duban tv babu wanda ya sake yunkurin cewa komai Kafin ahankali cikin sanyi jiki maryama ta mike daga kwanciyar da tai akan cinyar mahaifiyarta ."Aunty lokacin sallah yayi bari naje nayi sallah gashi ina son na danyi zane kafin na kwanata ga bacci da nake jin yana fixgata tamkar zan fadi ni zan shiga ciki sai da safe dan gabadaya yau ko gurin umma bazan shiga ba idan sakina ta shigo kice mata na shiga bacci dan bazan sake fitowa ba allah ya bamu alkhairi ."tana gama fadar haka ta juya ." har tayi taku biyu Aunty ta dakatar daita ta hanyar kiran sunanta "princess! Ta dan tsaya tare da waigowa "abinci fa ? maryama ta dan yatsina face dinta tana ciza gefen lips dinta sannan ta girgiza mata kai alamun "a'a ! "to amman karatun jarabawa ya kamata kiyi ba zane ba ko gobe baku da exam ne ? muna da shi zanyi karatu sannan na d'an yi zanen sai na kwanta " "kiyi karatu da kyau maryama Kinsan a final year kike, ni da son samuna ne da kin bar zanen nan har sai kin gama karatu " karki ji komai Aunty duk zan iya Kiyi min addua da fatan samun nasara ." Aunty ta sauke numfashi tana cewa "allah ya bada saa yayiwa rayuwarki albarka "Ameen sai da safe " "okay to shikenan allah ya bamu alkhairi "Ameen ! ta sake juyawa tana rausaya tamkar zata karye dan rashin jikin da Allah ya bata , har sai da Aunty taga ta shiga cikin d'akinta sannan ta dauke idanunta daga kallon bayanta ." Tana shiga dakin bayi ta shiga tayi wanka hade da dauro alwala ta fito cikin sanyi jiki tana goge gashin kanta da towel tana goge jiki tana mamakin abinda yasa mahaifiyarta bata son zuwa ga danginta alhalin suna gari daya ,"me yasa haka? " zata so tasan dalilin dayasa bata son zuwa garesu da wannan tunanin ta saka doguwar rigar bacci fara sol har kasa ta qarasa inda take ajiye sallaya ta dauka ta shimfida ta kai hannunta ta dauki zumbulelen hijab dinta ta saka ta kalli gabas a natse ta tada sallah ." byn ta idar ta mike ta cire hijab ta ajiye a gefen gadonta ta zauna akan kujera kwaya daya dake dakin wanda gabansa dan qaramin table ne mai dauke da tarin textbook da fararen takardu na zanenta ta janyo textbok daya daga ciki sannan ta zaro farar takarda kwaya daya ta ajiye a gabanta ta soma karatu tana joting kusan mintuna talatin sannan ta rufe ta maidashi inda yake ta sake zaro wata takarda ta ciro pencil da kayan aikinta ta fara zane wanda ya kasance abinci ruhinta a duk lokacin da zaka ga maryama a natse zaka ganta kuma akan aiki idan bata makaranta boko tana islamiyya idan bata islamiyya tana Kan aikinta na Architect wanda dashi take samu take taimakawa mahaifiyarta batayi karatu akanshi ba kawai baiwa ce daga allah ya bata babu abinda bata iya zanawa tun tana qarama take Zane dashi ta girma ." cikin kankanin lokaci ta fara zana wasu hadaddun mutane sanye da kaya na maaurata guda biyu macen sanye da wedding gwan yayinda nmj kuma ke sanye da suit sunyi matukar kyau kamar a kirasu su amsa tayi shiru tare da tura pencil cikin bakinta tana taunawa tana kallon zanen ahankali ahankali tana lumshe idanunta alamun bacci "bari na bar aikin nan haka tunda ba urgent bane zuwa gobe na qarasa idan na dawo daga school ta tattara ta bude durowar table dinta ta tura ta mike tsaye ta sake daukar hijab ta sanya ta tada sallah ishai tayi addua ga mahaifinta da alummar muslimai ta mike ta nade dadduma ta maida inda yake ta hau gado ta kwanta ko cikakken minti uku batayi ba bacci ya dauketa ." A can falo kuwa Aunty zaune kawai take duk hirar da habib da sakina ke zubawa da idanu kawai take binsu hankalinta na wani waje karfe goma daidai sakina tayi masu sallama ta wuce tana fita Aunty ta mike tsaye tana cewa habib "ka rufe koina ni zan shiga ciki allah ya tashemu lfy ta nufi hanyar dakinta har zata shiga ta hango haske a dakin maryama dan haka ta dawo ahankali ta shiga dakin ." tana kwance ta dungule waje daya a tsakiyar katifa ta cusa kanta cikin jikinta kwanciya mai tattare da damuwa duk wanda kaga yayi irin wannan kwanciya tabbas yana cikin damuwa ko maraici kuma a duk sanda taga tayi irin wannan kwanciyar ba komai take tunawa ba illa kanta take tunawa alokacin baya irin kwanciyarta kenan wanda damuwa ne silar nata kuma tasan damuwar ce ta janyo mata itama ta qarasa shigowa d'akin har inda take kwance ta kai hannu ta gyara mata kwanciya ta janyo abun rufa ta lullube mata jiki ta shafa gefen fuskarta tana sake jin soyayyarta acikin ranta ya'ya sune farinciki iyaye amman ita ta rasa wannan gatan daga nata most especially mahaifiyarta ." "abinda mahaifiyarta tayi mata abu ne da mutun zai iya yafewa amman bazai ta'ba iya mantawa ba kuma abu ne da bazata ta'ba yiwa ya'yanta ba zata so ya'yanta tamkar rayuwarta bazata iya kuntata masu ba bazata iya azabtar dasu ba sannan bazata iya hanasu cikar burinsu ba zata basu farinciki duk abinda suke so zata basu matukar bai sabawa shari'a ba, fatanta dai allah ya raya matasu cikin aminci "ta mike tsam har lokacin idanunta na Kan maryama dake qoqarin sake dunkulewa waje daya ta kashe mata hasken d'akin sannan ta fito tana mai janyo mata kofar dakin ta shiga dakinta " Ahankali ta zauna a bakin gado zuciyarta cike da zullumi har kusan shabiyu na dare tana zaune sai dai zuwa wannan lokaci tayi rigingine tana kallon saman dakin daya byn daya maganar maryama Ke dawo mata "me yasa bakya son zuwa inda danginki suke ?" mahaifi mahaifiya yan'uwa suna da matukar mahimanci arayuwar mutun ahlinki suna da hakki akanki most especially iyaye yana da kyau a dinga basu hakinsu domin hakan zai samarwa mai yi kwanciyar hankali,meye acikin duniyar da babu albarka iyaye acikinta ?nan take taji wasu hawaye masu zafi ya ganganro gefen idanunta." "tabbas gaskiy diyar cikinta ta fad'a mata amamn ai sune sukace babu ita babusu har abada me zataje tayi masu a yanzu da take cikin damuwa da bata da komai tasan ko taje garesu wulakanci ne zai biyo baya gara ta cigaba da zamanta hk babu dangi har karshen rayuwarta ,maryama da habib sun isheta komai , sheshekar kuka take sosai wanda batasan tanayi ba maraici sosai take ji alhalin ita din ba marainiya bace ta daura hannunta daya a saman kanta ko zataji saukin zafin da zuciyarta take mata ." tana cikin wannan halin taji an turo kofar dakinta da sauri ta dago tare dawowa haiyacinta tana mai goge hawayen idanunta da hannuwanta duka habib ne ya shigo wanda sakamakon sheshekan kukanta ya shigo dashi sai daya mata kallon tsanake sannan yace "me ye damuwarki male? dake shi kuma haka yake kiranta dashi ta sake sanyawa jikinta jarumta tana girgiza masa kai " alamun babu komai." "karki fad'a min haka byn kukanki ne ya shigo dani ya fad'a yana kafeta da fararen idanunshi qara maimaita tmbyrta yayi tayi kasa da kanta sakamakon hawayen daya sake cika mata ido domin kwalkwaluwarta ta toshe ta kasa fad'a masa dalili "ya sake matsota sosai male ki fad'a min damuwarki domin bazan bar dakin nan ba muddin baki fad'a min ba domin dai damuwa Ke saka mutun kuka irin wannna kuma tunda nake ban ta'ba ganin kukanki irin haka ba kuka mai fitowa daga kasan zuciya ." Ya kai hannu ya dago habarta yana kallon hawayenta dake zuba yabi hawayen da kallon hankalinsa na sake tashi cikin tsananin tashin hankali yace "wanene ya bata miki ranki haka? ta girgiza masa kai kawai "wai meye haka ne male kina son zuciyata ta kasa sukuni ne ko me ?ta sake girgiza masa kai ya juya a fusace zai bar dakin "bari naje na taso heartbeat.." ta riko hannusa da sauri "karka tashe ta bacci dan baccinta yayi nisa gashi gobe tana da exam's "to ki fad'a min damuwarki kamoshi tayi ta zaunar dashi a gefenta ya zauna yana sauraronta kusan second goma sannan ta zayyane masa komai sai daya numfasa kana ya soma mgn "male duk abinda heartbeat ta fad'a is right and it good dan daman nima ina neman hanyar da zan miki wannan tmbyr domin abu ne daya dade cikin kwakwaluwata har ya Kan hanani kwanciyar hankali Kiyi tunani male gsky heartbeat ta fad'a miki ya kamata kije ga danginki ko mu ki fad'a mana inda suke muje domin muna bukatarsu " Jin haka yasa ta barke da wani sabon kuka "baku san me suka min ba baku san irin wahalar dana sha a hannunsu ba ,na sha wahala kuma duk akan mahaifinku ne bana tunanin zasu qaunaceku shiru yayi yana dubanta cike da mamaki "me dady yayi masu haka ?sannan wani irin wahala kika sha a hannunsu ?yayi mata tmbyr a jere cikin tsananin tashin hankali kafin a hankali ya kai hannu yana goge mata hawaye shiru tayi ita kanta tana son ta basu labarinta amman bata san yadda zata dauki abun ba "tana son mahaifiyarta tana tausaya mata tana gudun bacin ranta ,bata son ganinta cikin damuwa amman a karshe itace abar kyama itace abar wulakantawa, itace mara mutunci a idanunta har tana cewa allah yasa mijinta ya wulakantata Allah ya hanata haihuwa Allah yasa ya saketa mijin da take tsananin so duk akan ta zabeshi a matsayin jikin aurenta ." Kuka sosai take tmkr ranta zai fita tana furta "na yafesu har abada zan zauna na qarasa rayuwata ni kadai "yayinda habib Ke share mata hawaye yana kuka yana bata hakuri domin yasa duk abinda yasata kuka irin haka mai girma ne muryarsa a sanyaye yace "kiyi hakuri male ki daina kuka kukanki na balain daga min hankali na hakura da son jin komai domin jinsa bazai zame min alkhairi ba amman kema kiyi qoqarin ki manta abinda ya rigada ya wuce amman iyaye da yanuwa duk abinda sukayi baa yafesu ."yana gama fadar haka ya juya har ya fita ya rufe mata kofar dakin hawaye ne yake fita dga idanunta "yaya suke son tayi da rayuwarta duk abinda suka fad'a mata tasan gsky ne amamn har yanzu zuciyarta ta saka mantuwa akwai wani abu da yake tsaye acikin zuciyarta ta rufe idanunta ta sake jingina jikinta da pillow daya saka mata a bayanta tana jujjuya maganganun yaranta tana yin filla filla dasu tana son kawar da bukatarsu amman tasan gsky suka fad'a mata bata taba daukar ya'yanta zasu girma da son danginta irin haka ba kasancewar suna cikin dangin mahaifinsu." ***** mrym zaune a d'akin hjy zulaiheart tana shirya mata kayanta da mai gugansu ya kawo tana tsaka da aikin aunty shahida ta shigo bakinta d'auke da sallama ta amsa tana gaisheta fuskarta d'auke da murmushi "aiki kike yi ne haka amaryar ATA tayi mgnr cike da zolaya " sannu da zuwa auntynmu me kika zo mana dashi ta fadi haka dan kawar da maganarta ,cikin dariya aunty shahida ta zauna akan sofa tana cewa "kayan dadi da bazasu fad'u ba maryam tayi murmushi yasu madina kwana biyu shiru kmr anyi ruwa an dauke "ke dai bari madina exam ne ya sakata gaba Amman Ina ganin ma zuwa wani sati zasu kammala ". "okay to Allah Bada sa'a "Ameen ta amsa tana cewa "wata shawara nazo miki dashi a tsakaninki da ATA jin haka yasa ta dan tsaya ta kasa cigaba da abinda take hankalinta gbdy ta tattara shi kan aunty shahida " Ina sauraron shawara daga bakin aunty nah maganin kukana " Marym please ki sanya kunnen baseera akan abinda zan fada miki "ta sake mika mata hankalinta sosai " kin dai san halin wanda zaki aura yana da kyau ki dan rage wasu abubuwa sannan ki koyi wasu abubuwa nasan kin fahimci abinda nake nufi ki zamo mai kwantar da kai da iya girke girke dan bazance girki ba ,daga ke har nana na fuskanci Kuna da matsala ta wannan bangaren dan haka ki dage ki koyi kowani irin girki da tsafta duk Inda zaki kasance acikin gidanki the next thing shine kamshi domin shi din ma'aboci son dadd'adan girki ne da son kamshi ki zamo mai hakuri da lallabashi domin ta haka zaki yi saurin dakusar da duk wani taurin Kansa abubuwan social media Shima ki rage "dan kinsan bazai yarda dashi ba wasu daukar hoto kullum ana d'aurawa a duniya Shima bazai yarda ba ". "shikenan naji aunty inshallahu Kuma duk zan d'auki shawararki ki dai tayani da addua biyyaya zanyi a aurena da ya Adam Allah yasa ya zamemin alkhairi "Ameen byn biyyaya har da soyayya sai kunyi aure zaki fahimci hk "Kai aunty babu wata soyayya " ki rubuta ki ajiye a Inda bazai goge ba ko na mutu sai kin fada "Kai aunty shahida bana tunanin yaya zai soni a yadda yake nunawa ni dai zanyi iya yina kawai "karki tsaya iya yinki kiyi kokari ki canzasa gbdy ta yadda zai manta da mafar.." "wannan Kuma impossible aunty bazata iya ba " suka ji sautin muryarsa acikin dodon kunnensu a tare suka juyo a firgice suka Kalli Inda yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa tamkar balarabe kallon second biyar mrym tayi masa tayi saurin d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana dan bazan dauka ba ." Take kwakwaluwar mrym ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi kenan akwai wacce yake so aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai ." gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba? "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ? ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu zai dinga baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace . "duk son da nake maka zan iya ajjiyeshi gefe na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada ka sake makamancin wannan maganar a gabanta wannan ya zamo Karo na karshe ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax sweetheart insha Allahu an gama ya fice ya barsu "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa " meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida. Da fari baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu saji daga bakinsa tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ." ***** a natse ta fara neman layin qanwarta hjy nuriyya wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa sosai a tsakaninsu tana zaune a kasar london tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam " Kai alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau sosai Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar kafin lokacin domin ayi biki dani ". Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi bukukuwa duk baki samu damar shigowa naija ba "haka ne kam amman inshallahu zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart tace "nuriyya wai kuwa kina jin labarin bilkisu ?dip hjy nuriyya tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace "bana Jin labarinta Kuma bana son na ji labarin Inda take , kuma Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita ba ,sannan bata sonmu ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ? "ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna babu kafa ta ciki "naunayen ajiyar zuciya hjy zulaiheart ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta wallahi zan nemota . "Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka tana rokonmu kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ." "wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen ajiyar zuciya hjy nuriyya tayi sannan tace "shikenan big sister ai abinda kikace shi zamuyi cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa ." Ranar asabar da misalin karfe hud'u na yammaci baba bAbba yazo bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun gaisa hjy zulaiheart ta karanto masa hukumcinta akan ATA cike da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba ,bugu da Qari zaa sake karfafa zumunci a tsakanin inshallahu zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu dan zamu so a daura auren nan kusa". "wannan maganar tayi Kuma naji dadinta sosai dan haka a fara sheidawa baba qarami dan nasan murnarsa sai tafi ta kowa domin duk yafi mu d'auki son ganin Adamcy yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah kadai yasan murnar da zaiyi idan yaji ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da tautaunawa kafin daga bisani sukayi sallama ." Baba qarami na zaune akan kujera me zaman mutun uku sai ga baba Babba wanda ya kasance yaya garesa Kuma Kani ga mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa ya d'an mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin fatan suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha " . suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani irin abu ya caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj saidu ." shiru baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami ya mike Shima yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni ? yayi mgnr a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam dabam ,nan take wasu glas cup suka tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ? "ya'yana yafi dacewa Adam ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa ."me yasa zaka fadi haka idris? "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa yana maxurai abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri . sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu ke rike da wuyan dan'uwansa uwa d'aya Uba d'aya .Wallahi yaya Kai kare ne da bai san ciwon kanshi ba ! "shin ya'yana basu dace dashi bane ka bani answer ?uncle Umar yayi shiru kawai yana kallon hannun uncle idris dake rike da wuyansa batare daya ce uffan ba. "me yasa kazo min da wannan banzar labarin mara dadin ji ?ya k'arasa maganar yana sakar masa wuya yana dubansa yana huci "saboda mu bamu Isa ta hada jini damu ba shiyasa ta za'ba masa acikin dangi ta ?"to me zai faru idan na hana auren ?"zan hana wannan auren ta karfin tsiya yayi mgnr yana d'aga hannunsa sama sannan ya dungule ya naushi bangon falon sai da gurin ya tsage ya tsaya yana huci da kallon wani bangare ." Baba babba ya tsaya abayansa hankalinsa a matukar tashe " maganarka gaskiya yayanmu suka fi dacewa da aurensa sai dai kayi hakuri dan'uwana bana tunanin da wata manufa zulaiheart ta had'a wannan auren ,idan baka manta ba shekara nawa ana fama da yaron nan akan ya fitar da mata yayi aure bana tunanin zata ki had'a zuria da daya daga cikinmu sannan da kasan kana da wannan burin me yasa baka fito dashi ba ? Baba qarami bai ce uffan ba illa numfashi da yake sauke da sauri sauri gumi na karyo masa "dan haka kayi hakuri karka bari wannan matsalar ta zamo Silar da za'a samu matsala ka bar wannan burin bayan anyi wannan auren sai ayi maganar a had'ashi da daya daga cikin yaran". "Kai kare idan ka sake yin min wannan maganar banzar sai na datseka gbdy Komai naka banga ta yadda nawa burin zai zama daga baya ba muddin d'aya daga cikin yarana basu yi nasarar shiga sawun farko ba babu wacce ta Isa ...." "kayi hakuri ka yafe min ban fad'i haka dan quntata maka ba ya fadi hk kasancewarsa me saukin Kai sannan marason tashin hankali yafi son yayi rayuwarsa cikin salama duk maganar da baba babba yake sam baba qarami bai juyo ba ",shi wannan Karen zai wuce sai kaji daga garesa sai dai ya kamata ka sakin ranka dan wata rana ....saurin d'aga masa hannu baba qarami yayi still bai juyo ba sai dai qirjinsa sai faman bugawa yake Uncle Umar ya juya cike da matsanacin firgici da yanayin dan'uwan nasa ." sai lokacin baba qarami ya juyo yabi bayansa da wani irin mugun Kallo Idanunsa a waje har sanda takunsa ya kai uku bai juyo ba haka shima baba qarami bai daina kallonsa ba .a sanyaye fahad dansa yabi bayan baba babba zuciyarsa na rawa dan shi kansa ya koka da abinda mahaifinsa yayi ya raka uncle Umar sai dai bai Kai shi har bakin get ba a tsakiyar hanya ya barshi yana bashi hakuri "karka damu fahad na gode allah yayi maku albarka ya amsa da Ameen ya dawo part dinsu da sauri . falon ya d'auki shiru na tsawon lokaci yana tsaye yana tunanin bayanin daya samu daga bakin dan'uwansa a yanzu wanda yake jinsa tamkar dalma acikin zuciyarsa , "uhmmmm yanzu dai ta nuna mana cewa itace uwar Adam Kuma ita kadai ke da iko akan shi ?sai mugani idan shi din d'an mace ne Baba qarami yay maganar yana jan tsaki a fili tare da watsa katuwar harara da mugun kallo kamar tana gabansa fahad ya d'auki farin glass cup ya tsiyaya masa tattacen ruwan inibi ya mika masa "kasha baba kaji sanyi a ranka yasa hannu ya Kar'ba ya rike shi gam a hannunsa sai dai bai sha ba haka zalika bai ajiye ba." "zan iya kasheki akan wannan haukan da kika yi zulaiheart domin Ina da tanadi da buri akan adam ya karasa maganar yana filinging da cup din hannunsa a fusace Wanda yasa take yaransa maza da mata tare da matarsa suka sake shiga rud'ani cike da matsanacin firgici suna kallonsa gabansu na faduwa ban da Hindu data samu guri ta kame akan kujerar da mahaifinta ya tashi zuciyarta tafi ta kowa zafi da tuttukin bakinciki tare da shiga tashin hankali" Fahad ...." ! ya kira sunan dansa Wanda aka kira da hkn ya d'ago ya kallesa a matukar tsorace batare da yace komai ba "abinda na fada Ina nufi har cikin zuciyata gara ta bar duniya ko ita yarinyar ta bar duniya akan rasa burina yayi maganar yana nuna sa da d'an yatsansa "wannan shine Karo na sau babu adadi da take kawo mana tashin hankali tun dan'uwanmu na raye dan haka Ina son kasheta na huta da ganinta a doron duniya muddin ba daya daga cikin ya'yana adam zai aura ba ." daya bayan daya suka shiga kallon junansu cike da mamakin jin furunci mahaifinsu hatta hindu wannan karon atsorace take kallon mahaifinta ta gigita kwarai da gaske "a kullum kokarina naga na kawar daita a duniya darajan halakar da nake son qullawa adam yasa na barta ya karasa maganar a kausashe .yayi taku daya biyu ya tsaya gaban hindu yana kallonta "kece ya kamata ace kin auri adam ba wannan yarinyar ba kije kiyi rayuwa tamkar sauraniya a gidansa ki taka kowa yadda kike so sannan ki juya duk Wanda kika ga dama wannan hannun nawa babu abinda yasani a halin yanzu kamar ya wahalar da zulaiheart ya gigita ta hanyar azabtuwa mai muni ,ya matso kusa da hindu Sosai suna fuskantar juna "wannan karon fuskarsa da murmushin mugunta akanta "ke hindu ko zakiyi iya karfin halin kashe min zulaiheart? Wani sanyayyayen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta wanda mahaifinta ne kawai ya fahimci manufarsa ganin yadda ahlinta suke kallonta a tsorace yasa tayi saurin waskewa tace "baba me yasa kake mgn fiyye da kaida ?gsky sam sam hakan bai dace ba tayi maganar tana kawar da idanunta gefe al'amun bata ji dadi ba gumin da ya tsatsafowa sauran yanuwanta suka shiga gogewa suna sauke numfashi da ajiyar zuciya atare Jin abinda tace daman km ita kad'ai ke iya fadawa mahaifisu mgn kai tsaye batare da shayi komai ba , a hankali ya juya yana taku cikin tsananin damuwa da tashin hankali suka juya gbdy suna kallon bayansa har ya shige bedroom dinsa yana shirya yadda zai kawar da hjy zulaiheart ko mrym daga doron duniya .." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 13 "Baba qarami na kwance har kusan tsakiyar dare ya kasa runtsawa dan sam bacci yaki zuwan masa sai faman juyi yake akan makeken katifarsa ,yayinda matarsa hjy aljannatu ke d'akinta kwance tana sharar bacci amman shi kuwa baba qarami sai tufka yake yana warwara ya d'an zabura ya mike zaune daga kwanciyar da yay, ya had'e hannunwansa duka waje d'aya "babu tantama hjy zulai tana da manufar had'a wannan auren yasan tayi haka ne dan kar wani acikinsu yaci arzikin d'anta , kunga idan ta had'asu aure da diyar d'anuwanta dole dai arzikinsa yana tare daita , dan da zarar mrym ta haihu dashi komai na adam zai dawo nata gbdy zuwa yanzu dai bai san abinda ya kamata yayi ba ko hanyar da zai bullo masu a maida auren Kan diyarsa ." Sosai kwakwaluwarsa tayi zurfi cikin tunani neman mafuta har bai san sanda hindu ta shigo d'akin ba , ta matso kusa dashi ta tsaya tana jijjiga baba qarami wanda yayi nisa cikin duniyar tunani "baba baba !! " ta kira sunansa har sau biyu ajere sannan yayi firgigib ya dawo haiyacinsa " wai meye haka baba?" me yasa zaka damu kanka akan wannan 'yar qanqanuwar matsalar ?" baba qarami bai iya amsa wa ba sai zuba mata rinannun idanunshi da yayi yana dubanta har lokacin yana maimaita abinda ta fad'a " ai a wajensa wannan ya wuce gagarumin matsala ba qanqanuwa ba ko ita kanta tasan da zaman haka ta dai fad'a ne dan kwantar masa da hankali shi kuwa hankalinsa bazai ta'ba kwanciya ba matukar ba ganinta yayi a matsayin matar adamu ba ." "Dan girman Allah baba ka kwantar da hankalinka mubi komai a hankali idan muka bari suka fahimci wani abu attare damu bazamu iya nasara akansu ba " cikin wani irin murya mai gyaraye da tashin hankali had'e da rud'ani yake furta "bazan iya ba hindatu , bazan iya kwantar da hankalina ba muddin ba ganinki a gidan adamu nayi a matsayin matarsa ba ,maganar aurensa da mrym ta dokeni fiyye da tunaninki ,Allah Allah nake gari ya waye naje ga zulai ayita ta qare domin kece kika fi dacewa da Adam ba wannan yarinyar ba dan wannan tsantsar muguta ne kawai take son nunawa"kai dai baba ka dan boye damuwarka baba" . D'akin ya d'auki shiru tamkar babu wasu halitta acikinsa sai na qara ac dake aiki da kuma saukar numfashinsu haka zalika baka jin motsin komai daga sai na tsuntsaye dake shawagi kasancewar a gra suke hindu ta sauke numfashi tana mai kamo hannunta mahaifinta cikin nata "idan kaje me zaka cewa mami akaina ? " zan so nasan abinda zakace baba idan ma hali kaje tare dani ayi komai akan idanuna shekaru sha biyar kenan , tun inada shekaru sha shida nake dakon soyayyarsa bazan iya jurar rasashi ba, bazan zuba idanu wata ta mallakesa ba "zan fad'a mata komai akan soyayyarki ni ko ta biyu ce kizo bazan damu ba burina ki kasance matsayin mata acikin gidansa , ki zama tmkr sauraniya, ki yi yadda kike so nima nayi yadda nake só da kamfanunuwansa ."" nan take ta had'e fuska tamkar dariya ba muryarta a kausashe ta cigaba da mgn "muddin a ta biyu zanzo nasan bazai ta'ba aurena ba , ya adam fa yana da tsari acikin rayuwarsa shi din ba mutun bane kamar sauran mutane bashi da raayin tara mata "wa yace miki bashi da raayin haka ? zai yi raayi dan uwarsa Allah dai ya kai mu gobe tare zamu wajen uwarsa kafata kafarki ." Baba qarami ya mike tsaye ya goya hannunwansa abaya yana girgiza kai yana duban hindu kafin daga bisani ya matso kusa daita sosai ya soma mgn can kasa kasa kusan mintuna goma yana mata mgn murmushin jin dadi né ya bayyana akan fuskarta " idan bata yarda ni na zama matarsa ba I will killed mrym idan ni ban samesa ba to babu wacce zata mallakesa anan gidan duniya yadda take mgnr zaka fahimci da gaske take kuma har cikin ranta abinda take nufi kenan ganin byn maryam ." Washegari da misalin karfe goma na safiya a kofar shiga bangaren hjy zulaiheart tayi masu kai tsaye a babban falon gidan suka iske mami zaune yayinda d'aya daga cikin masu aikinta ke zaune tana mammatsa mata yatsun kafafunta sallamarsu baba qarami tasa mami dauke idanunta daga Kan tv ta maida kansu tana sakin fuska sai dai kallo d'aya tayi masa ta fahimci akwai damuwa atattare dashi ,aranta tayi addua allah yasa ba wata matsalar bace ta taso , ta amsa sallamarsu tana cewa "sannuku da zuwa !" baba qarami ya samu waje ya zauna akan kujerar dake fuskantarta yayinda hindatu ta zauna a kasa kan kafet a gaban mami ta sunkuyar da kanta kasa tmkr mai neman gafara tare da gaishe da mami cike da ladabi ta amsa tana mami ta maida hankalinta ga baba qarami tana nazarin fuskarsa sannan ta kalli yarinyar dake zaune a gabanta tace "salaha tashi kije Ki bamu guri cikin sauri yarinyar ta mike tare da fadin "tô !" Mami ta sake maida hankalinta sosai garesu sannan ta fara magana a natse "baba qarami fatan dai lafiya dan naga yanayinka ba kamar yadda na saba ganinka ba yace "lafiyar dai da sauki "ta gyara zamanta cikin tsananin damuwa "daman dai na lura da hakan dan ba haka yanayinka yake ba kai din mutun ne mai faram faram duk sanda za'a ga fuskarka cikin murmushi take tô ina jinka fad'a abinda ke tafe da kai ." Naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana sake gyara zama yace "zulai jiya baba babba yazo min da wata magana akan hukuncinki akan Adam" ta gyada kai tana sauke numfashi "haka ne nasan zaka fi kowa jin dadi "tabbas naji dadi sai dai wani hanzari ba gudu ba nima na dade ina son had'asu aure da hindatu "mami tayi shiru tana dubansa da hindu dake zaune tana nazarinta tana son gano wani abu atattare da hindu domin dai ita din macece mai tsananin baseera tare da saurin karantar mutun sai data numfasa sannan tace "ita hindatu tana son shi ne ? "tabbas tana tsananin sonshi na tsawon shekaru tunda tashi da soyayyarsa ta tashi ni ne mutun na farko data fara sheidawa da fari na nuna mata illar rayuwar data jefa kanta na afkawa soyayya da qarancin shekarunta alokacin na tmbyeta meye dalilinta na son shi ? me ya dauki hankalinta akanshi ? tace ba dan yana dukiya da kyau ba ,yau da zai wayi gari bashi da komai bashi da hannu bashi da kafa koda akan titi zasu rayu zatai rayuwa dashi kawai son shi ta keyi dan Allah alokacin shekarunta shashida né kawai wanda ni nake ganin bata san ma me take ba bama tasan meye soyayyar ba yasa take fadin haka ahankali baba qarami ya fayyacewa mami komai akan soyayyar da hindu ke ma ATA babu abinda ya rage numfashi mami tayi ta saukewa tana girgiza kai cikin tausayawa tana kallon hindu data sake dukar da kanta kasa sosai ." "Masha allah naji dadin wannan abu sosai soyayya mai hade da zumunci allah ya bamu ikon sada zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba ". ta sake numfasawa ta cigaba da magana "nima daman tun farko burina kenan adamcy yayi aure biyu" ahankali baba qarami ya kalli inda hindu take wacce mgnr mami yasa ta dan dago kanta mami ta cigaba da magana "zan yi iya kokarina hindu na kawo karshen damuwarki duk da adamcy baya da raayin ajiye mata biyu amman zanyi convincing dinsa domin kawo farinciki arayuwarki da yarda allah ." da sauri hindu ta kalli mahaifinta shima din ita yake kallo domin dai yasan diyarsa da tsananin kishi zata fi bukatar ganin ita kadai ta mallakesa Kmr yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi masa dadi "fatana mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa gogan naka ya yarda ya amince ya hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi mata sallama ." Suna shiga dakin baba qarami hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta tare da karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ." **** Sanye ATA yake cikin farin yadin vol mai shegen haske da tsada a hankali yake taku yana gyara zaman hullarsa baki haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure da agogon rolex yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko zai qare " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana." Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba . "matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka ,sai dai wannan uban wanka da kashi haka kmr yau daurin aurenka, ai ko yau né daurin aurenka sai iyakarka hk kai ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba ." "sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka arayuwarka data kasuwancinka allah ya tsare min kai ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya sharrin mutun da aljani Allah rabaka dashi yace "Ameen !atakaice ya juya a natse yana taku tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau tsawon kwana uku kenan tana son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara shigo masa da maganar , auren mrym ma da yaya ya amince yanzu kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa kawai zai yi ya gudu ya barta dasu ." har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya tsaya cak ya waigo bayansa adaidai lokacin da mami ta sauke numfashi da girasa ya tambayeta ,ta girgiza masa kai kawai tamkr wata marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu komai adamcy nah ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me yasa bazanyi amfani da wannan damar na fad'a masa bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren gbdy gashi goben nan zaa je neman masa auren mrym numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau juma'at "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma gode sosai allah ya baka zuria masu albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin zama ta cigaba da yi tana tunanin mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah dan shine kawai mafuta agareta." Aunty abinda na gama jin bayanin ibrahim taji kafafunta suna barazanar kasa daukarta lokaci daya zuciyarta na barazanar tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye mata ba haka taji ya fito daga bakinsa " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar kaninta ita zai aura "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara " "ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ." "me yasa ?saboda me kar aje neman auren ?" Meye damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta wayarsa ta sake daukar qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda ya fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ." ***** "Maryama kyakkyawar budurwa ce mai kyan gaske doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa ta rankwafa ba sai dai ita din ba fara bace haka zalika baza'a kirata da baka kirin ba chocolate colour ce tsayinta ya fito sosai domin irin matan nan ne masu shape din cocakola tana da siririn hanci da manya idanuwa masu matukar d'aukar hankali dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli cikin kwayar idanunta sai ya kusan suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ." idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda sune suke qara haskaka kyawunta ,ga gaban goshinta kwance suke da suma luf luf !! duk da kanta a daure yake a koda yaushe da d'ankwali amman kallo daya zaka mata ka gano irin matan nan ne masu yalwan gashi sannan tana da kafa mai kyau haka ma yatsun kafafunta zara zara ne lullube da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana magana dan dole ka tsaya ka saurareta kuma dole ka kalleta ." Maryama ta samu tarbiya mai kyau daga gurin mahaifiyarta tayi karatunta na primary har zuwa matakin jami'an acikin jahar lagos kuma duk akarkashin kulawar gwanaty , haka bangaren karatun alqurni baa barta abaya ba domin tun tana primary ta sauke alqurni km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ." kyawun maryama mai tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu nata bata da wani tsayayyen saurayi duk wanda yazo neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa batare da wani dalili ba koma karshe taga ya koma gurin kaulat diyar kanwar babanta Aunty hassana gata da kyau sosai na bugawa a jarida amman mutane na mata kallon mai bakin jini abun yana d'an damunta sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta ya fiyye mata komai mahimanci koda yaushe ka kalli fuskar maryama zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa mutane suke mata kallon mai tsananin girman kai ." Sannu ahankali maryama take tafiya tamkar tana jin tausayin qasa ko macijiya dan babu wani karfi a tattare daita cikin shiga ta Kamala riga da sket dinki zamani da kuma dogon hijab mai hannu har qasa fuskarta manne yake da bakin nikaf kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta da wannan nikaf din zaka ganta sam bata yarda ta fita koina batare dashi ba a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka yayinda kafad'arta Ke makale da jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta sakamakon ranar data kwaso gefe da gefenta qawayenta ne subai'a da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ." Tafiya suke a natse suna hirar yadda jarabawar su ta qarshe ta kasance adaidai jeaction din ummahani street suka rabu da kawarta sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa unguwarsu market street batayi wani doguwar tafiya ba ta qaraso unguwarsu bata tsaya akoina ba sai kofar qaramin get din gidansu wanda kallo daya zaka masa kasan na masu rufin asiri ne dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan da gidan talaka fútik ba daidai misali gidansu ginin da ne kuma ginin kasa ne filasta ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa acikin gidan ." a natse ta shigo haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat wacce ta sha kwaliya cikin atamfar chiganvy gold black touch of milk ,kallo daya tayi masu ita da wanda ta gani tsaye ta dauke idanuwanta zuwa wani bangaren tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye da kaulat din ba bako bane a wajenta tasha ganinsu tare ."duk da bilal baya ganin faukarta amman duk sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi daga inda yake tsaye yabi tafiyar maryama da wani irin kallo komai nata a natse most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da bai ta'ba ganin fuskarta ba." Kaulat na ganin irin kallon da yake mata taja dogon tsaki yayinda maryama bata sake duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai aikin tara masu samari marasa inganci a gida maimakon tai concentrate akan karatunta da kullum yake yin baya sai ta maida hankalinta ga tara samari marasa amfani , tare suka shiga jss one ,sukai jss1 tare, sukai jss 2 tare sukai exam na zuwa jss3 ta barta suka wuce ss 1 ita da sakina itama sakina lokacin da zasu shiga ss2 tayi fail ta wuceta sai dataje ss3 sannan kaulat taje ss1 sakina taje ss2 gashi ita yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito amman ita kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating ya kai sau hudu allah yayi mata jarabawa ta rashin ilimin dan babu abinda tasani daga bokon har islamiyyar zero ce amman ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita da tarasa dalilin dayasa suka tsaneta suka tsani ganin wani tare daita duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai sunyi qoqarin rabasu " "Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai "? "wallahi da tun asali ita na fara gani to da babu abinda zai kawoni wajenki yayi mgnr acikin zuciyarsa amman a zahiri cewa yayi "meye laifi dan kalli halitta mai natsuwa ? ta zaro idanuwata waje tana masa wani irin kallo kafin daga baya cikin d'aga murya cike da maseefa tace "ko zaka koma wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka wallahi da naji dadi sosai "ya sake fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar duniya ta qare, kana fara soyayya daita komai daka mallaka zai qare idan kayi sa'a ma wani mummunar bala'i bai sameka ba tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana ." "Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ." Da sallama maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad ta fad'a tana cire nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai jima bane saboda ranar daake yau tayi zafi da yawa "gsky kam yau an zuba rana ga doguwar tafiyar mun kwaso wallahi a matukar gajiye nake da kyar na qaraso gida , kasan tun daga dopemu da kafa muka shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ." Ya mike tsaye ya qarasa inda d'an qaramin fridge dinsu thermocool yake wanda ya gaji dan murfin ma ya balle idan an bud'e da kyar ake maidashi a rufe ya ciro pure watar mai sanyi ya ajiye akan hannun kujera ya maida murfin fridge din da kyar ya qaraso inda take "heartbeat ga ruwa ki sha "yauwa after dad na gode sosai ya koma Kan kujera daya tashi yana cewa "ya exam din fatan yazo da sauki ?sai data zuke ruwan sannan tace "babu wani sauki amman muna fatan samun nasara daga Allah bata sake cewa komai ba sannan bata zauna ba ta qaraso bayi ta dauro alwala ta fito ta d'auki wani dadduma sallah daga inda suke ajiyewa ta shimfida kusa da mahaifiyarta dake zaune har lokacin tana kaiwa allah kukata akan yaranta most especially maryama wacce ta fita jarabawar karshe ta tada sallah a natse ." Bayan ta idar da sallah ta mike tsaye tana ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah daga yau dai mun huta bata gama rufe bakinta ba taji an bako kofar shigowa falon nasu da karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku gbdy uwa da ya marasa mutunci to wallahi na gaji ki jawa wannan tantariyar yartaki mai suffar manufukai kunne ta shiga hankalinta bata tashi dawowa gidan nan daga yawon karywancinta sai yamma tayi lokacin da manema auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin ya'yanmu to wallahi kinyi kadan bake ba hatta uwar data kawoki duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan kada miya ,ko su sukayi koba dinki? " ko su sukace maza su dinga gudunki ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan aikin banza kawai kyau har kyau amman bashi da amfani , ana fakewa da karatu ana yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...." aunty wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi saurin rike masa hannu tana cewa " qul habib karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka? "amman male bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane ." Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara." "ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya ta fad'a tana dafe kuncinta . "idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?" habib ya bude baki zai sake yin magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba dan haka komai hassana zata fada akanta banason ka sake cewa uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ." aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba yace "allah Aunty ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ." Kuka maryama take sosai a wajen tamkar ranta zai fita aunty ta qaraso wajen da take tsaye tare da dafa maryama me ye kuma na kuka bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta suna cigaba da rera Kuka wanda har umma ta shigo basu saniba" umma ta qarasa shigowa da sauri tare da dafe qirji bilkisu me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka suka ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke da mamanki da kaninka haka kuke kuka ? ." hannunta umma ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba ta biyo bayansu da sauri umma ta zaunar da ita a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty Salma ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai da ta burkice "wai ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa "a'a salma ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna." "uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman Kiyi hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da kika gani kafin a samu nasara sai anyi hakuri in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km sai ki zauna kina bata lokacinki ." " babu ruwanki dole na rarrashi diyata mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib tana gama shigowa taji saurin muryar Aunty "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa." Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki tana dubanta tace "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita tayi shiru tana tunani ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba." "kiyi hakuri aunty akan duk abinda Ke faruwa a gidan nan wani lokacin Allah yana gwada mutane ya gwada imanin bawa kinsan al'imanu yazidu wa yankus imani na raguwa yana qaruwa to Ke aunty a mizanin da kike allah yana son ya gwada imaninki ne Kan wasu abubuwa dake faruwa damu duk duniya bani da abar yabo da koyi da hali mai kyau sama danaki sannan kowa yasan ke din mutuniyar kirkice hatta makiyanki suna fadan hk a bayanki to me yasa abubuwanki sukaki daidaita duk wannan hakuri naki da juriyar amman ba komai bane kawai Allah yana son ya gwada imaninki da jin tsoronsa ne dan duk allah yana sane ya tsara haka hk ." "Mu qara hakuri hakuri ne kawai zai kawo mana sauki kuma Allah yace annan nasara maasabarin duk wani nasara na rayuwa yana tare da hakuri , hakuri da kike dashi yana cikin tsani da zai kai mutun zuwa aljanna, hakuri halin manzon allah ne wal hilmi wal sabri duk kina dashi aunty kina da dauriya kina da juriya kina da tawakkali kina da imani kina da ibada so duk wani abu da kike ganin yana samunki mara kyau ko yana shirin faruwa dake to wallahi jarabawa ce km kina ta cinye jarabawar sai kiga allah ya tsara bazakaji dadi anan duniya ba sai a lahira ,wallahi aunty da ace kana da rabo a duniya baka dashi a lahira wallahi gara ace kana dashi a lahira baka dashi a duniya ." "sai abu daya da nake son ki fad'a mana" ta dago da rinannun idanunta ahankali tana duba kyakkyawar diyarta son kowa kin wanda ya rasa abar tinkaho kuma yar baiwa domin samun irinta sai an tona "aunty idan bazan takuraki ba ina son ki fad'a mana inda danginki suke muna son musani domin na fara tunanin akwai wani mummunar abu daya faru a baya dake ,dan idan babu komai bazai yuwa kana da dangi kuma kuna gari daya amman bakwa ziyar juna"tunda maryama ta fara magana idanun aunty suka sake cika da hawaye basu samu nasarar zuba ba sai data kawo karshen mgnrta "ki fad'a mana mu yaranki ne bazamu taba juya miki baya ba duk runtsi duk wuya muna tare dake koda kuwa kice kika batawa yan'uwanki zamu kasance dake domin kece karfin gwiwarmu ta qarasa mgnr tana riko hannun mahaifiyarta ." Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 14 "Shiru aunty tayi tana jin fad'uwar gaba mai tsanani tafi mintuna ashirin bata ce qala ba habib ya kai hannu ya d'ago ha'barta yana kallon cikin kwayar idanunta dake kwance da ruwan hawaye "male kece karfin gwiwar dake tafiyar da rayuwarmu Kinyi mana komai arayuwar mu ,kin nuna mana tsantsar soyayya ,kin nuna mana daidai da ba daidai ba kin bamu gatan da ba kowa yake samun irinsa ba wato ilimin addini dana boko , kin inganta rayuwarmu mun yaba miki kuma mun jinjinawa qoqarinki garemu da taimakon Allah da taimakon heartbeat gashi har heartbeat ta kammala karatunta kalamai soyayya iri iri dana sanyaya zuciya yake furtawa gareta wanda yake sake tsuma zuciyarta da soyayyarsu "wannan alfarma ce ki fad'a mana ." Duk yadda habib ya d'auki lokaci yana magana sai dai har zuwa wannan lokacin aunty ta Kasa furta komai garesu illa numfashin da take janyowa ahankali tana fitarwa da kyar sun sake d'aukar tsawon awa d'aya a wannan yanayin batare da ta fitar da abinda ke cikin zuciyarta ba ."sosai idanunta suka canza kala kallonta suka cigaba da yi suna jiran ta fara basu labarinta, yadda suke kallonta haka itama take kallonsu zuciyarta cike da wasi wasi tana son magana amman hakan ya faskara tana tsananin son yaranta ba zataso suji abinda zai d'aga masu hankali har da zai yi silar shigarsu damuwa ba haka zalika bazataso suji irin rayuwar da sukai da mahaifinsu kafin aure ba da irin tozarcin da mahaifinsu ya sha a wajen yan'uwanta ba ,ganinta fad'a masu wannan labarin babban kuskure ne zata aikata ko bama haka ba bata tunanin zuciyarsu zata iya d'auka , zuciyarsu ma bazata iya dauka ba , bazasu iya wannan juriyar ba." Ahankali ta lumshe idanunta adaidai lokacin da habib ya d'auke hannunsa daga ha'barta har yau tana jin soyayyar mahaifinsu acikin ranta duk da bai duniya amman kullum ta kalli ya'yan da Allah albarkacesu da samu soyayyarsa na qara hauhawa acikin zuciyarta kuma bata jin Kuskure tayi dan ta auresa ".tana kallonsu suka mike atare suka nufi kofar fita kowannensu da abinda zuciyarsa ke tunani akanta dan daman sun san da matukar wahala mahaifiyarsu ta fad'a masu labarinta kasancewarta mace mai tsananin zurfin ciki da rashin son magana ." bayansu tabi da kallo har suka 'bacewa ganinta bata iya d'auke kwayar idanunta akansu ba byan fitarsu ta gyara zamanta sosai tare da rafka tagumi gabad'aya kuma sai taji babu dadi aranta ji tayi kamar bata kyauta masu ba hakan yasa taji zuciyarta kmr zata kama da wuta ahankali ta mike tsaye cikin sanyin jiki ta isa bakin window falonta ta kai hannunta ta zuge labule tana kallon haraban gidan yaranta ta hango suna tafiya a natse kafad'a da kafad'a wanda kusan kansu d'aya basu tsaya akoina ba sai bakin part din umma "heartbeat ban san me yasa haka ke faruwa damu ba ? bana son ganin kanmu haka ina jin Kmr na kashe kaina na huta da wannan rayuwa ". ya fad'a yana dafe goshinsa cikin tsananin damuwa . "Subhanallah after dad ka daina fadar haka karka sake fad'ar wannan kalmar Allah bazai sa naga wannan ranar ba ,"ka dinga addua a duk lokacin daka tsinci kanka cikin tashin hankali ambaton sunan allah zakayi karka bari zuciyarka tafi karfinka muryarsa cike da tashin hankali "amman me yasa anayi mana abubuwa rashin mutunci aunty ta hanani d'aukar mataki ? "daidai kenan habib ,abinda aunty tayi shine daidai shine abinda kowace uwa ta gari ya dace tayi idan suna yi muma muna yi to meye bambamci a tsakanin mai ilimi da wanda bai dashi ? kowani irin abu zaka gani a gidan nan ka d'aure ka cije ni yanzu damuwata ba matsalar Aunty hassana bace sanin inda dangin mahaifiyarmu suke shine babban damuwata ." Ya riko hannunta cikin nashi yana dubanta "ki ciresu aranki abinda muka fi bukata sune dangin mahaifi , ace yau bamu da dangin mahaifi ko ba acikinsu muke rayuwa ba shine babban tashin hankalinmu "suma dangin mahaifiya suna da mahimanci domin zuciyarsu tafi ta dangin uba tausayi , jikina na bani akwai abinda yasa suka nisanci juna dole ina bukatar nasan haka har lokacin aunty tana kallonsu har sanda maryama ta nufi kofar shiga bangaren umma shi kuma habib ya nufi get din gidan da alamun fita zai yi ta saki labulen tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta koma ta zauna cikin zullumi tana tuno rayuwarta ta baya " Maryama bata iske umma a falo ba dan haka ta samu waje ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun falon ta runtse idanunta tana tunani "anya ba wani mummunar abu mahaifiyata ta shuka ba wanda yasa yan'uwanta suka gujeta ita kuma take jin tsoron komawa garesu ba ?"anya ma yan'uwanta su suka d'aura aurenta da mahaifinmu ? anya ma akwai gasky a zamanta da mahaifinmu ? "wad'an nan tambayoyin tayita jerowa kanta wanda bata da mai bata amsa sai mahaifiyarta ko umma ." shiru ta sake yi tana qoqarin kawar da zarginta akan iyayenta bata san shigowar umma ba sai dai taji an girgizata sannan tayi sauri ta juyo cikin tsoro taga tana kallonta tace "maryama mai kike tunani haka ?na shiga uku ni aseeya kar dai abinda ya faru Kika zauna kina tunani ?" nan da nan ta soma girgiza mata kai alamun "a'a! tana in in nah "amm uhm Allah umma bashi bane ."umma ta girgiza ka fadanta cikin sanyin murya "kin kuwa san lokacin dana dauka ina miki magana baki sani ba ?na jima anan ina kallonki maryama kina tunanin abinda ya faru d'azu still maryama kai ta girgiza mata alamun" a'a! Cike da nuna kulawa umma ta juya ta qarasa kitchen inda fridge yake ta isa ta bud'e ta dauko kwalin hollandia ta rufe fridge ta matsa kad'an inda d'an qaramin tray da glass cup's Ke kansa ta d'auki d'aya ta dawo inda take zaune ta janyo kujera gaban maryama ta zauna tana kallonta ta zuba mata hollandia ta mika mata tare da cewa "gashi ki sha dan nasan har yanzu baki sakawa cikinki komai ba ta kai cup bakinta tana kallon umma kad'an ta sha ta kawar da bakinta alamun ya isheta." "karki sake tunanin abinda ya faru d'azu abinda ya rigada ya faru ya faru karki sakashi aranki yazo ya dameki wani ciwo yaje ya kamaki mu shiga uku dan sai nafi kowa shiga damuwa "Allah umma bashi bane wannan ai idan da sabo na rígada na saba " "Wani kallo umma tabita dashi tare da sanyaya muryarta tace "idan bashi bane maryama sanar dani matsalarki dan bayan mahaifiyarki baki da wanda ya fini ina jinki tmkr ni na haifeki bancin ke kadai uwarki ta haifa da tuni na kwaceki gbdy daga hannunta , wannan soyayyar da nake miki yasa na janyoki jikina sosai karki ji komai sanar dani damuwarki ta fad'a tana kallonta ." sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da yatsun hannunta kusan second goma sannan ta motsa labbanta "daman ba komai bane kawai ina son nasan inda dangin aunty suke, ko sanin labarinta "me yasa bata zuwa wajen yan'uwanta suma kuma me yasa basa zuwa wajenta?" laifin me tayi masu? " me ya faru daita tunda na taso nake ganinta cikin damuwa da raunin zuciya wanda har yasa nima nake jin haka atare dani ."? Wani dogon ajiyar zuciya umma ta sauke cikin fargaba ta tashi zata wuce har ta juya maryama tayi saurin riko hannunta cikin nata "umma ! ta kira sunanta muryarta na rawa cak umma ta tsaya tare da juyowa fuskarta da tausayawa itama maryama mikewa tayi cikin tsananin tashi hanakali ta rusuna kasa ta daura hannuwanta a saman kafafun umma cikin raunin murya ta fara mgn Kmr zatayi kuka "umma nasan Kinsan komai daya faru da iyayena dan allah karki boye min gskyr dana sanki daita " umma ta zare hannuta ta sake juyawa "umma Kodai mu din bata hanyar sunah aka haifemu bane ?" Umma ta juyo da sauri tana dubanta qirjinta na dokawa da karfin gaske "maryama ta gyada mata kai kana ta cigaba da mgn "duk yadda muke da aunty duk shakuwarmu da soyyyar da take nuna mana ta kasa fad'a mana haka kema gashi umma zaki wuce ki barni byn kece kika bukaci kisan damuwata . "Nasan kinsan komai daya faru ki fada min mu san matsayinmu wata killa ma shine dalilin da yasa muke ganin tasko acikin gidan nan dan girman allah umma karki boye min abinda yafi komai mahimmanci arayuwarmu ki fad'a min na rabu da nauyin dake daskare da qirjina ta qarasa mgnr cike da sheshekar kuka ." Girgiza kai umma ta shiga yi ta dawo inda take tsaye ta kamota ta zaunar daita akan kujera tana kallonta cike da tausayawa kusan mintuna ashirin sannna ta numfasa tana cewa "ku din ba shegu bane ku din yan halak ne" naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tana kamo hannu umma cikin nata "kinsan kowani d'an adam da yadda yake kar'bar gaddararsa . wasu mutane basa gane rayuwa duk yadda allah ya rubutawa bawa babu wanda ya isa ya canza maka ita,ita qaddara kuma tana fadawa bawa daidai da yadda allah ya hukunto masa qaddara bata san talaka ba bata san mai kudi ba ,qaddara ce da rabonku ta nisanta mahaifiyarku da yan'uwanta yan'uwanta sun kasa kar'ban qaddarar data fad'a mata amatsayin su na muslimai amman mgn ta gsky ku din yan halak ne sai dai akwai yan'uwanki da'aka samesu bata hanyar aure ba .." nan take jikin maryama ya kama rawa tmkr mazari ta tsaya tana kallonta tana assessing maganarta umma ta damke mata hannu gam cikin nata tana kallonta tana jin yadda jikinta Ke rawa tamkr mazari , maryama tayi imani bancin a zaune take da ta tabbatarwa kanta kafafuwanta bazasu iya d'aukar ba, da zuwa yanzu ta zube kasa."cikin kyarrrma wasu hawaye masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata tana jin wani zafi a qirjinta mara misaltuwa cikin ikon allah allah ya bata ikon furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shi tayita furtawa tana maimaitawa still jikinta da zuciyarta na rawa ." Umma ta kalleta cikin sarewa ta cigaba da magana "wannan qaddara ce maryama km kowani bawa da tashi irin kalar qaddarar bata wuce Kan kowa ba , ki godewa allah da yasa ta hanyar aure aka sameku bilkisu na bani tausayi matuka kullum idan na kalleta sai na zubar mata da hawaye , da gatanta da komai tana rayuwa tmkr bata da kowa ,tana rayuwa cikin kaskanci alhalin bata cancanci haka ba tunda taji an samu wasu babu aure taji komai ya tsaya mata cak hatta shi karan kanshi labarin taji ya fita kanta ." Mahaifiyarki haifaffiyar wannan gari ce anan aka haifeta aka haifi iyayenta ke hatta kakaninta ana aka haifesu sune asalin yan kasa "Idan mutun ya shigo jahar lagos din nan ya tmbyi family's din alhj rafi'u giwa to babu wanda bai san mahaifinta ba ."mahaifinta ko nace dangin mahaifiyarki gbdy masu arziki ne ."mahaifinta alhj rafi'u giwa yana da mata hud'u kinga kenan suna da yan uba a qalla guda talatin sai dai bazan iya kawo miki sunansu ba ina dai jin Aisha , hauwa wacce suke kira da jiddah abakinta gbdy a gidansu bilkisu ce auta a mata sai kannenta biyu maza dake binta daga kanta mahaifiyarta bata sake haihuwar mace ba haka ma sauran bangaren matan sun daina haihuwa wanda hakan yayi sanadiyar da soyayya mai karfi ya shiga tsakaninta da mahaifinta da yan'uwanta gbdy kowa yana sonta kasancewarta auta a mata " gabadaya yan'uwan bilkisu masu kudi suka aura daga wanda yake london sai wanda yake Canadá ko American ,mafi yawa daga cikin yan'uwanta suna wata kasa daga maza har mata idan kuma anan ne zaki iske su cikin VI ita kadai ce ta auri talaka marashi ,dan gbdy asalin mahaifinki talakawa ne idan aka cire abban sadam wanda yake da d'an rufin asiri dan yana da gidan bread da kowa ya dogara dashi amman basu da komai ." "bilkisu ta taso cikin gata da soyayya da kulawar iyaye tun daga tasowarta har zuwa girmanta duk abinda take so shi takeyi ta taso cikin soyayyar iyaye dana yan'uwa kowa yana sonta sannan ta taso da farinjin samari acikin family's dinsu kasancewarta kyakkyawa hasalima kyawun jikinta kika d'auko fuskarki ce ta mahaifinki amman km shi din ma baki dauko farinsa ba dan shi fari ne sol tmkr bature kmr yadda kike ganinsa a hoto ." kowa na sonta da nuna mata soyayya ,acikin masoyanta akwai mubarak dake mutuwar sonta, mubarak cousing dinta ne da ubansa da uwarta uwa daya uba daya kuma shima mahaifinsa mai kudin gaske ne km shi kadai suka haifa ,bilkisu na da shekara shabiyar a duniya alokacin tana ss 1 a secondary school alokacin mahaifiyarta da mahaifin mubarak sukai alkwarin aure a tsakanin yaransu dan mubarak din zai yi tafiya zuwa american qaro karatu , sun bar mgnr atsakaninsu idan ta gama karatunta na secondary sai ayi musu aure ." mahaifinki ussein adam shima asalin haifaffen garin nan ne haka iyayensa sun kasance su takwas ne a wajen iyayensu mata hud'u maza hud'u umar ,fatima ,gali saadatu ,nazifi fadeela Kmr yadda kikasani , hassana da ussein ne auta ." yana da shekara ashirin da takwas a duniya ya fara aiki a gidansu bilkisu ta sanadiyyar abokin abban sadam abdulwahab wanda shi gadi yake a makotansu ." mahaifinki ussein ya kasance direban ne gidansu bilkisu wanda Ke kaita school , idan lokacin tashi yayi ya koma ya d'aukota duk inda zata shike kaita hussein ya kasance mutun ne mai tsananin kirki gashi kyakkyawa aji farko illarsa dai shi din ya kasance talaka ne mai son jin dadi arayuwarsa km yana harka da yammata da shaye shaye sai dai bai ta'ba barin gidansu bilkisu sun san da zaman wannan halin nashi ba a boye yake yi saboda tsira da aikinsa ." Maryama ta runtse idanunta tana jin wani tuttukin bakinciki a zuciyarta. ta d'aura kanta akan cinyar umma ko zata samu sausaucin zugin da zuciyarta take ,dan tun baaje koina ba ta fara datasanin jin labarin iyayenta , mahaifinta manemin mata ne ga shaye shaye a iyan nan ma kad'ai ta raina kanta ta sake yarda su din marasa gata ne ." " tun farkon ganin bilkisu da ussein taji ya burgeta daman shi Allah yayi masa farinjin mata dan atarihinsa bai ta'ba cewa yana son mace ba dan har prouding yake , wannan yasa ya qara samun kusanci daita sosai , duk abinda taci sai ta rage masa idan zai kaita school ta bashi tun abun yana bashi mamaki har yazo ya daina bashi mamaki ya ajiye abun amatsayin ita din mai alkhairi ce , shima kma yana kulawa daita sosai dan hatta murfin mota kafin ta fito ya fito ya bude mata sannan idan sun iske an gama assembly zai tabbatar da ta shiga class akan idanunshi sannan zai juya ya koma gida ,ga iya bada labari, ussein ya iya bada labarin da zai saka mutun nishadi amman fa ga wanda yake da mahimanci a wajensa duk wannan yana cikin abinda yasa bilkisu ta sake sakewa dashi , shiyasa kullum bata da magana sai na fadar kirkinsa a wajen iyayenta wanda har hakan yasa iyayenta suke son batunsa tana sa ayi masa alkhairi na mussaman kullum da irin kyautar da take sa ayi masa ." haka rayuwa tai ta tafiya mubarak na kiranta a waya amman sam bata bashi lokacinta yayinda wata irin shakuwa mai karfin gaske ta shiga tsakanin ussein da bilkisu lokacin da ta kai shekaru sha bakwai ta fahimci ba shakuwa bace kawai a tsakaninsu soyayya ce mai karfi wanda shima zuwa lokacin ya kamu da matsanancin soyayyarta ta yadda ya kasa hakuri sai daya zaunar dani ya fad'a min ciwon dake zuciyarsa yace zai yi qoqarin ya boye nashi domin itama bilkisu ya fahimci irin son da take masa bazai ta'ba barin wannan soyayya ya tabbata a tsananinsu ba domin dai yasan tafi karfinsa tafi karfin aurensa ita din ba sa'ar aurensa bace babu ta yadda zai sameta arayuwarsa ." "Nima na karfafa masa gwiwa ya danne abinda yake ji akan bilkisu na nuna masa bambamci dake tsakaninsu daita samun auren irinsu akwai wahala duk da babu yadda allah baya al'amarinsa shi yayi talaka kum shi yay mai kudi nace yayi addua sai allah ya kawo masa sauki da mafuta , amman alokacin ya sheida min zai ajiye aiki ya nemi wani still dai nice na hana na bashi kwarin gwiwa ya cigaba da aikinsa ya dai rage sakar mata fuska da kusanci daita ." yana cikin wannan halin kwatsam bilkisu ta bayyana masa soyayyata da fari yaki amincewa hakan yasa ta shiga damuwa mai tsanani har rashin lfy ta kwanta batare da iyayena sun san akanshi take ciwon ba wanda ta kai har dakin daaka bashi a gidan take biyosa tana kukan ya amshi soyayyarta "ya zaunar daita ya fad'a mata gsky soyayya atsakaninsu ba abu ne mai yuwu wa ba duba da matsayinta da nashi , kuka take tana nuna masa babu wani bambamci a tsakaninsu dashi duk abu daya ne a wajen Allah da kalamai masu sanyaya zuciya da soyayya tasa ussein ya amince tunda daman shima yana sonta ranar daya amince aranar yan gidansu suka ga ikon allah domin dai bilkisu ta warke daga rashin lfy da take suka fara gudanar da soyayya ." " tun tana boyewa har tazo ta fara bayyanawa zuwa lokacin a family's duk wanda yasan bilkisu yasan ussein idan har kana son kaga kyautar bilkisu ko yalwataccen fararta to kayi mata mgnr ussein family's dinta babu wanda bai san ussein direba ba idan ya dauko ta daga school zasu samu waje su parka su sha soyayyarsu ussein yana da yammata masu son shi amman soyayyar bilkisu tayi karfin da bazai iya cigaba da soyayya dasu ba ,wata irin soyayyar ussein Ke nuna mata mai karfi wanda har ta kai yana iya ta 'bata batare data hanashi ba nasan wannan ne saboda ussein na kawota gidan nan wajen mahaifiyarsa akwai lokacin dana shiga bangaren hajiya bata nan na iske su a dakin tana kwance ajikinsa sanye da kayan makaranta ajikinta suna romance ."hajiya mahaifiyar ussein ba ƙaramin jin daɗin haɗuwar bilkisu da ussein tayi ba ganin yadda yaron nata ya fara natsuwa ba kamar daba ba yanzu duk wani harkar mata ya jinginar da ita, haka zalika shaye shayensa yayi sauki sai wanda ba'a rasa ba." Bayan bilkisu ta kammala karatunta na secondary akace ta fito da miji saboda masoya sunyi mata yawa kowa na sonta da aure km mafi yawansu cikin yanuwa ne sai kawai ta gabatar da ussein amatsayin mijin da zata aura hajiya rahma na gama jin abinda bilkisu ta fad'a ta mike tsaye tana dubanta abun ya mugun girgizata a matukar firgice tace "bilkisu banji abinda kika fad'a da kyau ba ina son ki sake maimaita min ,fad'a min naji da kyau tayi magana a tsawace batare da wata fargaba ba ta sake maimaita abinda ke ranta ai nan take mahaifiyarta da yan'uwanta da suka fito ciki d'aya suka nuna rashin amincewarsu mamakinta ne ya kamasu daman shakuwarsu ba iya nan ta tsaya ba ,har ta kai matakin soyayya juyin duniya akayi daita tace ussein take so har da ikirarin muddin zatayi aure to shi zata aura ,nan fa suka fara raba jaha da mahaifiyarta yan'uwanta kowa zaginta ya shiga yi me zatayi dashi ta rasa wanda zatayi soyayya sai direba common direba zata aura ? ita dai jinsu kawai take amman ita aranta ta kudurta komai zai faru sai dai ya faru amman ita ussein take so km har lokacin mahaifinki na shaye shayensa sai dai ba kowa ke iya fahimtar hk ba km nasan yawon tsaftansa da amfani da turaruka masu kamshi yasa baa ganewa amman mu dake rayuwa a gidan nan mun sani tunda idan yana gida yana shan kayansa a bayan dakin salma lokacin baa gina ba ." Tashin farko mahaifiyarta tasa akayi kiransa cike da matsanancin fargaba da tashin hankali ya nufi part dinta bakinsa dauke da sallama ya shiga falon tana zaune akan kujera na alfarma bata amsa sallamar da yayi ba haka zalika bata dubeshi ba tun kafin ayi masa gurin zama yayiwa kanshi yana mai yi sunkuyar da kanshi a kasa agabanta tmkr mai neman gafara ahankali ya furta" hjy barka da dare ta dago kai daga Kan tv ta maida kanshi tana qare masa kallon tsab tana nazarinsa ko kayan kirki ma babu ajikinsa kana kallonsa kasan mataiyaci ne mai yaci bare ya bawa bilkisu shi kuwa kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewar ba cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake ba tunda ya samu kiran gaugauwa daga hajiya rahma bai sake samun kwanciyar hankali ba har zuwa yanzu da yake durkushe agabanta sai data gama qare masa kallo sannan ta numfasa ta fara magana a kausashe "meke tsakaninka da bilkisu ?da sauri ya girgiza mata kanshi alamun babu komai ." Shiru tayi tana cigaba da kallonsa kafin daga bisani ta cigaba da magana cikin bacin rai "kace babu komai ?da sauri ya girgiza mata kai alamun Eh ! "ni nasan akwai komai amman tunda kai da kanka kace babu komai to ya tsaya a babu komai din domin idan ya zamo akwai komai zaka hadu da mummunar bacin raina zan maka abinda har ka matu bazaka manta dani ba sannan daga wannan lokacin aikinka ya qare acikin gidan nan ya dago da sauri yana kallonta a tsorace "haka nake nufi ko kana bin mu bashi ne da ka wani tsareni da ido .?" ya sake girgiza mata kai alamun a'a ! "to maza ka tashi yanzu yanzu ka tattara komai naka ka bar mana gidan matsiyaci banza kawai ,kaga yarinya qarama shine kake son kayi mata wayo, guda nawa bilkisun take da zata auri me shekarunka ? Idan km kwadayin kudin ubanta kake kayi kad'an kaci . matsayinka bai kai nan ba, ka bari ya'yan manya ya'yan masu arziki irinta su more ba kai matsiyaci ba , matsiyacin ma wanda ko rigar kirki baka dashi tana zuba ruwan bala'i ya zabura ya mike da sauri zai wuce tace " ba estate din nan ba ko a bakin get din estate din nan aka gaya min anganka wallahi wallahi sai nasa an daure min kai ko nasa a 'batar min da kai idan ma ba son abun duniya da son zuciya irin naka ba ina kai ina bilkisu? kai yanzu kaga dacewarku daita ?da sauri ya girgiza kai "a she kasan gsky maza tashi ka bani guri matsiyaci banza kawai ko maza sun qare a duniya mai bilkisu zatayi da kai da sauri ya qarasa barin falon bai tsaya jin sauran karashen zancen ba yana fita daga falon bilkisu ta fito daga d'akinta daman km hayaniyar mahaifiyarta ce ta fito da daita ta tmbyeta ita da wa ye ." "Nida wannan matsiyacin ne dake neman cutar da rayuwarki "ta bata amsa atakaice tana dauke kanta bilkisu tayi shiru tana nazarinta idan har ta fahimceta da ussein take ? da sauri ta nufi kofar fita ta dakatar daita "idan kika sake kika bar falon nan sai na tsine miki albarka cak ta tsaya tana kallon mahaifiyarta " shasha shar banza da bata san ciwon kanta ba duk cikin yanuwanki wani dan iskan kika ga ya kawo miji Kmr wannan tsukakken da ko kayan kirki babu ajikinsa kullum yana yawo cikin kodaddun kaya ,kisani ko zaki mutu bazaki auresa ba na haramta miki aurensa ke intakaice miki baki da miji sai mubarak dan albarka in sha allahu a ranar useein ya tattara ya bar gidan ya dawo dakinsa dake nan byn makaranta faidiyya ." Tun daga ranar lamari ya sake lalacewa domin tunda bilkisu tasan ya bar gidan hankalinta ya tashi ta shiga damuwa sosai ta kauracewa kowa numfashi kawai take acikin gidansu amman rayuwarta da komai nata yana wajen ussein ta kirasa yafi sau babu adadi bai daukar kiranta da kyar da ban hakuri da turo sakonin ya sauko sannan ta dawo daidai, acikin satin tasan yadda tayi suka hadu da ussein maganar gsky ussein na sonta shima bazai iya rayuwa babu ita ba ,sai dai wulakancin da mahaifiyar bilkisu tayi masa da kiransa matsiyaci da tayi shi yafi komai tunzurashi ,domin duk gargadinta a banza ya daukesu babu abinda yasa aransa kamar cima burin sake kwace mata yarinya ta kowani hali sannan bai boye ma mahaifiyarsa komai da irin wulakanci daakayi masa itama kwarin gwiwa ta bashi tunda yarinyar tana son shi a matsiyaninsa talaka kar ya kuskura ya rabu daita ai su suke da mace sune a wahala , ina son nayi mgn alokacin amman babu halin yi a gabanta domin ussein shine auta km soyayyarsa dabam ce acikin yayanta amman dana fad'a masa gsky ya janye kudinrinsa ya rabunmusu da yarinya " "nasan duk wannan ne sbd ni abokiyar hirarsa ce dan duk gidan nan da yan'uwansa mata bai yarda da kowa ba sai ni domin yace ina da sirri wasu abubuwan ma a gabana suka faru ,ussein ya sha kawo min bilkisu bangarena ta yini anan bilkisu na da matukar kirki da son mutane sannan bata da rowa idan zata zo wajena tana kawo min abubuwan amfani ga aiki da take min sam bazakice diyar mai kudi bace bata da son jikinta tana son aiki sosai da son mutane sadam kam ya sha gata a wajenta dan komai ta gani na yara zata siyo ta kawo masa wanda hakan yasa naji ina matukar qaunarta har cikin raina nake jin tausayinta domin tana sakewa ta fada min damuwarta da duk halin da take ciki a gidansu da yawon mgnr aurenta da mubarak da mahaifiyarta ke mata tana nuna mata mubarak yafi ussein sam bata dace da ussein ba ." "ni kaina nazo na gano bata dace da ussein ba a wani zuwa datai na zaunar daita nace ina son nayi magana daita a matsayinta na kanwata da muka fito ciki daya baa matsayin matar da kanin mijina keso ba ta bani hankalinta ni kuma na fara magana bilkisu ko kinsan ussein yana shaye shaye ? ."tace min "eh !tasani km tayi masa mgn yace da zarar ya auret zai daina ,na numfasa nace "ke kin yarda zai daina ?tace min "eh ! Ko kinsan yana da yammata byn ke ?ta sake ce min eh ai ya rabu dasu Ina son na bata shawara ta auri mubarak ta bar ussein amman ina jin tsoro kar taje ta kwashe ta fada masa tunda idanunta sun rufe shi kuma ya fadawa mahaifiyarsa na samu matsala na kama bakina amman duk wanda ya kalli bilkisu km yasan family's dinta gsky yasan basu dace da juna ba ." Soyayya ta sake yin karfi a tsakanin ussein da bilkisu dan babu abinda barinsa gidansu bilkisu ya janyo sai tabarbarewar rayuwar bilkisu dan a tunanina ussein ya fara saduwa da bilkisu batare da aure ba ni kaina alokacin naso ace iyayenta sun barta ta aureshi tunda ita taji kuma tagani amman mutanen nan suka ki saboda kyamar talaka , dan da irin rayuwar da suke gara ace aure sukayi, bazan ta'ba mantawa ba wata rana bilkisu ta sameni tana kuka na tmbyeta bata boye min ba ta fada min ciki gareta nan take na shiga damuwa mai tsanani nace "haba bilkisu me yasa zaki sakewa nmj jiki haka ?bakya jin tausayin iyayenki da yan'uwanki bakya gudun ranar da ussein zai juya miki baya ?ina ta mata fad'a Kmr kanwata ta jini ita km tana kuka tace ."na taimaketa acire mata cikin nace babu ruwana bazan saka hannu a kashe rai ba ,muna cikin wannan halin hjy ta shigo ashe taji duk mgnr mu itama cewa tayi abarshi kar acire taje gida zata samu iyayenta sai ayi mgnr aure kawai abu ya bani mamaki kamar wasu yoroba tunda sune ake irin wannan rayuwar dasu sai kayi ciki zaa yi aure km su yin ciki ba wani aibu bane a wajensu murna ma zaayi da samunsa tun daga nan na fahimci duk abinda ussein yake da saka hannun hjy ciki ." Tô tun daga ranar ban sake saka bilkisu acikin idanuna ba a she byn ta bar wajena ussein ya bata maganin zubar da ciki ta sha koda ta koma gida sai ciwon ciki kwana tayi tana murkususu ciwo har garin allah ya waye ,cikin yaki fita ga ciki yaki daina ciwo iyayenta dai suka gaji suka kira doctor ya dubata byn ya gama dubata ya rubuta mata scan tô a wajen scan ne likita yaga ciki a mahaifarta tunda likita ya soma bayani mahaifiyarta ta rikice ta dimauce ta kasa gane takamaiman abinda yake fada ganin ta rude yace mata wani abu ya gani me kama da gas a mahaifarta amman ta kira wani daga gida yazo nan ta kira Aisha yayar bilkisu hankalinta a tashe tazo ta samu hjy rahma a reception zaune tayi tagumi bilkisu zaune a gefenta cikin tsoro da fargaba scan taso cikin ya fita cikin sauki batare da kowa yasani ba hjy rahma tace Aisha tashiga taji me doctor yake nufi da gas din da ya gani a mahaifar bilkisu ta shiga nan likita ya fad'a mata komai itama tashin hankali tashiga mai tsanani amman sai ta boye ta fito tana cewa uwar ulcer ke damunta nan hankalin mahaifiyarsu ya dan kwanta suka koma gida ." Aisha ta kira bilkisu zuwa gidanta tana qarasowa bata tsaya wata wata ba ta rufeta da duka sai datayi mata mai isarta kamar zata kasheta sannan ta barta byn ta gama dukanta ta kira kaf yan dakinsu ta sheida masu sannan tasa akayi mata wankin ciki aka cire cikin lokacin da hjytr ussein taji babu cikin Kmr ta mutu dan bakinciki har da kuka tayi an cire mata jikanta dan karfin halin irin nata har da tmbyr bilkisu tayi wa ya cire mata jikanta ita km kuruciya ta fad'a mata tun daga lokacin hjy ta tsani Aisha da yan gidansu bilkisu amman km tana son bilkisu ace warta bazata tsaneta ba dan tana son danta." Hajiya rahma ta lura tun da bilkisu ta dawo daga gidan Aisha ta warke sumul babu kwana ciwon ciki ta cigaba da abubuwanta sai dai Aisha ta kira hjy rahma tace kar a sake barin bilkisu fito koina har sanda mubarak zai dawo a daura masu aure abinda bilkisu ta tsani ji kenan dan ta tsani mubarak tsana mai girma bata ma son ana yi mata maganarsa karki ce shima mubarak din mummuna ne dogo ne sosai Kmr ussein sai dai shi baki ne kyakkyawan gaske dan sai dana sa ta nuna min hotonsa a istagram an kafa wa bilkisu takunkunmi rashin fita koina hatta islamiyya ta daina zuwa alokacin sai datayi wata uku babu shiga babu fita kawai tana gida zaune km babu waya a hannunta an kwace da wayar hjy rahma take mgn da mubarak ." Ganin Kmr ta kwantar da kai suna soyayya da mubarak Kmr gske yasa mahaifiyarta ta dauka ta cire komai aranta kuma taji dadin hk kulawa da soyayyarta ya qaru ta zaunar daita tayita nuna mata illar ussein tana qawata mata mubarak zataji dadin rayuwa agidan mubarak alokacin ta tmbayeta ta yarda zata auri mubarak tace eh ta amince wanda ba haka bane acikin ranta wata rana yan'uwanta gbdy suka zo gidan suna zaune a falon mahaifiyarsu yayanta abubakar wanda ya kasance first born a dakinsu yace a barta ta cigaba da rayuwata ta koma islamiyya Kmr kowa dan lokacin saukar alqurninsu ya kusa duk da bata zuwa baa cire sunanta acikin yan walima ba ba dan me ma zaa hanata rayuwa sbd wani matsiyacin banza Aisha da sauran yanuwata mata sukace a'a basu yarda da fitarta koina ba shi km yace abashi dalili gbdy suka kasa sheida masa dalili su dan haka yace dole ta koma islamiyya nasan kuna tunani ko zata hadu da wannan yaron ne yace su barta dashi idan ta isa tayi Kuskuren haduwa da ussein nan take uwar tace "ai bilkisunta ta canza bama zata kunyatata ba yanzu mubarak ne agabanta ." Cikin satin aka dinka mata sabon uniform ta fara zuwa islamiyya Kmr abun arziki sai dai aranar ta samu waya ta kirasa bai shiga ba sai ta kirani nan na tmbyeta kwana biyu da halin da take ciki ,bata boye min komai ba a karshe tace na fadawa ussein ya kunna wayarsa nace mata "to! na qara da yi mata fad'a kar ta sake yarda dashi tace taji nan fa suka sake din kewa da ussein soyayya ta sake karfi har tafi nada da zara ta fito daga gida suke haduwa dashi km ni na tabbatarwa kaina bazasu ga junansu su bar junansu hk ba tunda sun dandani juna dole sai sunyi wani abu duk da shiedar zina tana da wahala "to ! bazan manta ba ranar wata asabar da safe ta fito daga gidansu da nufin zuwa islamiyya kai tsaye dakin ussein ta zarto ashe ana biye daita abaya batasani ba har ta shiga dakinsa tana shiga suka fara abinda suka saba suna cikin wannan halin sai shigowar mutanen gidansu sukaji tana rungume ajikinsa aiko ranar munga tashin hankalin da bamu ta'ba gani ba ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 18 "wato afa akan dai yarinyar nan ce da nazo akanta yar kanin mijina daya mutu ya barmana amatsayin riko to malam kamar yadda kasani banason yarinyar nan na tsani na ganta dan ina ji ajikina akwai nasarori da anan gaba zata iya samu domin soyayyar da mutane suke nuna mata kamar ma aikinka na farko bai ci ba, yanzu haka samari sunfi biyar da suka nuna suna sonta sai dai dadin abun da zarar sun zo lokaci kad'an sai su gudu ." "to ga aikin nan yaci zaki ce kamar aiki bai ci ba , ai haka zasu dinga zuwa suna 'bata mata lokaci suna wucewa batare da tasamu wanda zai aureta ba babu fa wanda zai like mata acikinsu sai matsiyaci da zarar masu arziki sunzo zasu gudu ." "Ai ni ba abinda nake só kenan ba ,ai bana son ko matsiyaci ma yazo wajenta nafi son ta qare rayuwarta a kaskance a bauta da wahala , sai tawa yar saurayin da yake sonta mutun d'aya ne kuma ba wani mai abun kirki bane gashi kace yarinyata zata samu farinjin samari masu kyau da kudi sai gashi sa'banin haka nake gani madadin maryama tayi bakin jini acikin mutane da samari duk banga haka ba ." "kullum farinjinta sake qaruwa yake jamaa suna matukar qaunarta basa son kula ya'yana koina akaje sai dai ace a gaishe da maryama amman banda ya'yana , wani abun bakinciki afa har yaran nawa suma kullum maryama , suna matukar sonta sunki su gane ita din matsalarsu ce, ko wani abu nayi mata sai dai kaji suna min fad'a suna nuna min rashin daidai nan ta tsaya ta sauke numfashi da ajiyar zuciya ,afa yace "to yanzu ki takaita matsalarki me kike son ayi ? Aunty salma ta gyara zama tace "ina son a fara rabata da ya'yana ina son naji sun tsaneta fiyye da yadda nake jin tsanarta acikin raina wannan shine kawai muradina kafin nazo neman wani bukatar ."afa yayi murmushi yace "ai wannan shi yafi komai sauki ki tafi gida kawai zaki ga aiki da cikawa cikin sati biyu masu zuwa , amman ina son ki dawo kafin kwanakin su cika akwai abinda zan baki indai har na baki ki kai amfani dashi magana ta qare amman yanzu zan fara jaraba 'yan abinda bazaa rasa ba ." aunty salma tayi godiya ta ajiye masa kudi ta fice tana faman zuba godiya tana cigaba da zagi da maseefar kiyayyarta da maryama har ta fice daga gidan afa ta dawo gida tana saka da warwara dan ita ko kashe maryama afa zai yi tana só saboda tsanar datai mata yarinya sai kace lu'u lu'u ai muddin tana cikin gidan sai ya'yanta sun rigata samun gidan aure kafin tayi ,idan kuma har zata yi auren zata sa afa yayi mata aikin da zata auri matsiyacin daya fi ubanta talauci ." ***** Bayan kwana biyu da faruwar wannan alamarin maryama tana tafiya cikin kayan islamiyya ta Ardus-salam yayinda hannunta ke rungume alqurani , yammaci ne duk mazan unguwarsu sun dawo daga aiki duk inda ta wulga sai an kalleta da shaawar tafiyarta tmkr bata son taka qasa tana cikin tafiya taji tafiya abayanta bata juya ba dan hakan baya daga cikin d'abiarta , sai ma qara saurin da tayi ta cigaba da tafiyarta saboda tasan kowaye ita yake bi zarginta ma cikin samarin unguwarsu ne dan akwai masu nuna suna sonta acikinsu ." "maryama wannan uban sauri haka da kike zabgawa ko dan gudun kar na biyoki ne ?ta tsaya cak lokacin data fahimci muryar malamin islamiyyarsu ne na Ardus-salam mlm yahuza ta juyo a natse ta dubeshi cikin nikaf dinta tare da girmamawa ta gaishesa ."ya gyara tsayuwarsa yana kallonta , kunyarta ita tafi komai tsoratashi ,duk iya takun saurayi in har ya had'u da mace mai kunya yana samun karaya matuka a zuciyarsa ." yayi dan murmushi irin nasu na ustaz "maryama har kullum zuciyata bata da sukuni jiddan wala khairan ,na kasa mantawa dake ,bani da wani sukuni face na samu amsarki game da bukatata dana kawo miki ."yayi shiru tare da tsayawa yana sauraron yaji me zatace nan take tayi kicin kicin tamkar wacce aka tsare da wuka zaa yankata sai da ta dauki second goma sannan tace "uhm !sai kuma tayi shiru ta qasa qarasa abinda zata fad'a maganar ta makale acikin zuciyarta shi kanshi ganin motsa lip's dinta bai sawa ranshi cewar zatace uffan ba bayan abinda ta furta ba ." ba yau bane farko haka zalika yasan ba yau bane zai zama karshe ya saba tareta a hanya ta kasa ko ambaton sunan shi bama shi kadai ba kusan mutane suna yawon fad'ar haka akanta bata da yawon surutu da saurin sabo da mutun duk wanda ka ganta dashi tana d'ar d'ar alamun tsoro shima dan matsayin da yake dashi na malaminta ne yasa har ta tsaya akan hanya babu wanda ya kai ta tsaya dashi akan hanya ". "Maryama idan na lura da yanayin fuskarki ba soyayyata bace baki amsa ba amman kuma bazan tabbatar akan cewar kin amsa ba ,tunda a kwayar idanunki kawai nake iya karantawa shine kunya ce ta hanaki ki fad'ar abinda Ke cikin zuciyarki maryama ki daure ki sanar dani menenê acikin zuciyarki akaina ko zuciyata zata samu sukuni da natsuwa ?". shirun dai da baya só shi tayi dan bata da abinda zatace masa ,bazata iya wata soyayya ba da'ace ta d'aurawa kanta soyayyar samari da lokacin da suke guduwa suna barinta da ba qaramin tashin hankali zata shiga ba gara ta qarasa rayuwarta haka tunda soyayya ba dole bane arayuwar mutun haka ma aure sunah ne matukar mutun zai iya rike kanshi domin acikin Sahbbai ma akwai wad'an da suka mutu basuyi aure ba dan haka mutun zai iya zamansa haka kuma aure da haihuwa bashi bane karshen duniya a ganinta ko babu shi mutun zai iya rayuwarsa ." "hakika maryama duk cikin unguwar nan kai garin nan ma gbdy har cikin islamiyyarmu banga diya macen da take burgeni kuma zuciyata take dawainiya da tarin soyayyata kamar ki ba ki samar da amsar soyayyata a cikin zuciyarki ko zan samu farinciki da sukuni koda ta wata sigace da zan fahimta ."sosai hankalinta ya kai kololuwar tashi tama qasa tsayuwa bisa kafafunta , kafafunta suka shiga karkarwa ,yana son ya bata dama ta wuce gida saboda halin daya karanta atattare daita amman kuma bai gaji da kallonta ba kuma shi yasani ko zai kwana tsaye atare daita bazai gaji ba , sakina da kanwata ne suka zo zasu giftasu malam yahuza yayi sauri yace "sakina ku tsaya ga maryama tsaye ku wuce gida tare ." Shukura ta kallesa tana jin wani irin tuttukin bakinciki acikin zuciyarta abun yayi matukar bata mamaki maryama tare da mlm yahuza malamin da take matukar só amman tsoro da shakkansa ya hanata fito da soyayyarsa "malam ! kawai tace tayi gaba tana jan tsaki acikin ranta dan tasan muddin tayi a fili ta kad'e har ganyenta dan mlm yahuza babu wasa wajen disfila d'alibai da iya karatu da d'aukar wanka ga tsantsar kyau shiyasa kowani d'alibi ke matukar jin tsoronsa a kaf ardus-salam babu malamin da'ake shakka da só kamarsa da yawa yammata na qaunarsa ."sakina kam jikinta a matukar sanyaye ta wuce batare datayi mgn ba maryama ta bita da idanuwanta wani abu ya soki zuciyarta domin tun safiyar yau ta lura sakina ta canza mata abun ya matukar d'aure mata kai amman tayi mata uzuri da cewa yanayin rayuwa ne ." Mlm yahuza bai sake magana ba sai tunanin kunyar shi da sakina taji dan ganinsa da maryama yasa ta kasa tsayawa dan haka yace "maryama sai gobe idan mun had'u a makaranta amman fa kisani bazan ta'ba daina tsaidake anan ba har sai ranar dana samu na cire kunyar nan kika amince min "Kanta kawai ta gyada masa muryata a matukar sanyaye tace "sai da safe ta juya ta cigaba da tafiya a natse bai bar wajen ba sai da tayi nisa sosai ta 'bacewa ganinsa ." yana juyawa sukai ido biyu da mlm umar mai hausa atare sukai murmushi "wato kai har kullum bazaka daina wahalar da kanka akan maryama ba ko ?"Mlm yahuza ya qarasa inda mlm umar yake ya tsaya yana cewa "ya zanyi umar allah ya jarabeni da soyayyar maryama bazan iya hakura daita ba "kai kuma allah ya jarabi mata dayawa da sonka ba ?"wannan kuma damuwarsu ce ,ai dama haka zaka fad'a duk kuna son maso wani ,kai ma ka tausayawa masu sonka sai allah ya duba lamarinka ". "Allah ma ya sani babu wacce nasan tana sona bare na tausayawa ya fad'a yana wani sham kamshi "Uhm uhm mutumina banda fad'ar son rai duk wanda ka fadawa haka zai d'auka bakasan abinda kakeyi ba ,"kaga umar rabani da wannan zance mu barta matsawar bata sarauniyar mata zaka min ba "karka duba yanayin gidansu maryama amman dai kai kanka kasan tafi karfin aurenka , maryama macece daya kamata wani hamshakin mai kudi yayi wuf daita ." dan murmushi mlm yahuza yayi yace "haka ne amman ai duk mace bata fi karfin auren nmj ba kuma kowani mutun yana da nashi matsayin da zai iya burge mace , kuma ina dashi ina da quality da mace zata soni koda kuwa bani da kosisi bugu da qari ita mace ba kudi take bukata a soyayya da kulawa take so ni nan kuma zan kula da maryama ." "da me zaka kula daita ?karka manta ita din cikakkiyar 'yar boko ce , yarinyar da idan ta fara aiki yanzu sai ta d'auki nauyin ciyar da mutanen gidanku gbdy dan haka banga abinda zai sa ka dinga wahalar da kanka kana 'batawa kanka lokaci akanta ba , kayi hakuri ka rabu daita domin dai babban goro sai magogin karfe ." Mlm yahuza ya dan ji zafin maganar malam umar dan haka ya rage farar fuskashi "wai me kake nufi ? kana nufin dan ita din yar boko ce tana da kyau na bugawa a jarida kana tunanin zata samu aiki nan gaba zai sa ta iya fin karfin halittar ubangiji "? yahuza abinda nake son ka fahimta duk wad'an nan abubuwa da kake gani fifiko ne a tsakaninka da maryama kawai abinda nake so kaji aranka tafi karfinka tafi karfin aurenka ." "kaga dan allah mlm ka barni ka zuba min ido ba wahalar banza nake yi ba ina cikin zuciyarta kunyar da take yawon nunawa akaina ta wadatar dani cewar nayi mata , nan gaba kad'an zata fahimtar dani ."Ka dai bi a sannu kar wata rana kana zaune wani hamshakin mai kudi ya shigo har cikin unguwar nan ya aureta .". "bari kaji babu wani mai kudin da zai aureta domin suma masu kudin sunfi son ya'yan masu kudi yanuwansu , ita maryamar da ba galihu ne daita ba ,ai ba uban da zai shigo cikin wannan rubabbiyar unguwar ya kwashta ai duk wannan kyawun nata akan irinmu zai qare "yana gama fadar haka ya juya dan baya son ya sake 'bata masa rai ." Tafiya kawai maryama take zuciyarta cike da kunci da tunani barkatai ba kuma akan mlm yahuza ba sai sabon sauyin data gani akan fuskar sakina dan na shukura mai sauki ne idan da sabo ta saba ita da yaran aunty hassana haka suke mata amman sakina fa basu saba haka ba suna matukar qaunar junansu tun suna yara su din masoya ne na hakika ." da wannan tunani ta qarasa cikin gidansu kai tsaye ta nufi bangaren su sakina domin tambayarta dalilin sauyawarta ashe wahala ce ta shigo daita tana sallama aunty salma tace " Yauwa maryama d'auki tsintsiyar ki share min d'akuna tas shine amsar sallamar da aunty salma tayi mata kamar tace bazatai ba amman ta kasa ta ajiye alquranin dake hannunta ta d'auko tsintsiya ta fara shara batare da wata damuwa ba ." tana shara aunty salma na zaginta ita da shukura amman sakina na zaune batace komai ba sa'banin da da bata yarda a zageta ko sakata aiki akan idanunta ,tana shara wani gurin da simiti wani gurin babu ga kuma sakina na zaune ta d'ago idanunta a natse ta kalleta taga kurar sharar na zuwa inda take muryata a sanyaye tace "sakinata ina ganin sai kin d'an tashi kinga kurar tana zuwa inda kike ta wani watso mata harara "ai gudun ruwanki nake kallo naga zaki shareni ko kuwa ."? maryama tayi shiru tsaye tana karantarta akwai wulakanci acikin maganarta "ke kika kyaleta aunty sakina amman banda jakanta irin nata tana kallon mutane suna zaune zatace su matsa , banza shasha kawai mai siffar mayu ." inji cewar shukara dake zaune kusa da aunty salma abun bai yiwa aunty salma dadi sosai ba domin kuwa sakina taso ta furta ma maryama haka ba shukura ba ,sakina kam tun maganar farko datai bata qara ba ta tashi cikin bacin rai ta shige daki tana jin wani zazzafan kiyayyar maryama ." Maryama tayi shiru kawai tana bin shukura da kallo "me kuma hakan yake nufi dani ? me na yiwa sakina ni kuwa daga jiya zuwa yau take fushi daita hk ."tayi wa kanta tambayar da bata da mai bata amsa sai sakina ita zagin shukura bai dameta ba kamar sauyawar sakina ta gyada kanta ta cigaba da shara tana tunanin laifin da taiwa sakina har ta qarasa ta wanke hannunta da kafafunta ta d'auki quraninta ta shiga d'aki inda sakina take zaune akan gado tana cika tana batsewa tana ganin maryama ta sake had'e rai Kmr taga mugun abu maryama bata damu ba ta zauna kusa daita ta soma janta da mgn taso tmbyrta laifin da tayi mata amman ganin yadda take barsarwa yasa tayi shiru daga karshe ta wuce zuciyarta cike da matsanancin damuwa ." ******* Da misalin karfe d'aya na ranar laraba wanda yayi daidai da sauran kwana uku jirgin mr ata ya tashi zuwa france amman har lokacin jikinsa sai a hankali daga matsanancin ciwon kai ya dawo masa ciwon gabobin jiki dan ko miyo baya iya had'eyewa sosai mami ta sauko daga saman d'akin mr ata tare da likitansa byn mami ta sallame doctor rafeeq ta dubi maryam da nana hauwa'u tace "yayanku fa yau tsawon kwana biyu bashi da lafiya ku shiga ku gaishesa keda maryama ,jiki sanyaye suka ce" to! suka mike atare suka hau sama ." A natse sukai knocking wanda nana hauwa'u ce tayi mryam na bayanta ara'be kusan second goma suka d'auka tsaye sannan ya basu damar shigowa d,akin ,da sallama suka shiga parlour suka gansa kwance akan doguwar kujerar kushin ya runtse idanuwanshi yana sanye da riga fari sol da gajeren wondo iya gwiwarsa yayinda hannunsa d'aya Ke daidai saitin zuciyarsa ya d'an bud'e idanuwanshi kad'an ganinsu yasa ya maida idanuwanshi ya runtse gam." nana hauwa'u tace "sannu yayanmu ya jikin naka kayi hakuri walllahi bamu san baka da lafiya ba sai yanzu da mami ta sauko take fad'a mana " shiru yayi bai amsa mata ba nan da nan maryam ta shiga hankalinta dan tasan ita kam sai ya had'a mata da tsaki muddin tayi masa sannu suna zaune shiru nana hauwa'u ta d'an ta'ba maryam tana mai mata alamar ta gaishesa wani abu mai d'aci daya tsaya mata a wuya ta had'iye ta bud'e baki muryarta na rawa "yaya sannu "ta fad'a atakaice ilai kuwa tunaninta ya tabbata dan kuwa bai amsa ba sai ma tsakin daya ja yana cewa "auta ya bani abun na sha a fridge da saurinta ta mike ta isa inda qaramin fridge dinsa yake ta bud'e donsimo ta d'auko masa ta had'a masa da ruwa ta ajiye masa akan table din dake gabansa ." "gashi yaya Allah ya baka lafiya ya d'an motsa lip's dinsa alamun ya amsa ya mike zaune da kyar batare daya kalli inda mrym take ba itama bata sake kallon inda yake ba sai ma fuskarta dake kallon wani katon hotonsa dake manne da bangon falon sanye cikin kananan kaya riga da wondo milk colour touch of black ya zura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa idanuwanshi manne da farin glass fuskar nan tashi a had'e Kmr koda yaushe "auta ! Ya kira sunan nana hauwa'u ta amsa da "na'am yaya! "shiga bedroom ki d'auko min wayoyina da sauri ta shiga wayoyin na kan katifarsa ta d'auko tana danna gefen wayar inda nan take wayar ta kawo haske screen ta duba fusakar wayar wata kyakkyawar fuska ta gani kanta babu d'ankwali gashin kanta ya zubo kad'an ya rufe mata gefen idanunta ." ta tsurawa hoton ido sosai nan ta gane zane ne ba asalin hoto ba ahankali take tafiya tana kallon fuskar wayar duk da zane ne ,amman yarinyar tayi matukar yi mata kyau ta kai masa tana cewa "yaya zanen dake kan screen din wayarka yayi min kyau sosai wacece ?"tayi masa tmbyr tana duban mrym da hankalinta baya kansu yana can kallon mr ata , tana kallon kyaun da allah yayi masa ba abinda yafi burgeta dashi kamar sheidar sallarsa daya fito masa a saman goshinsa yayi baki tmkr tawadar Allah ." ahankali zuciyar mr ata ta soma bugawa da karfin gaske yana jin tmkr ta kunno masa emotion's din da yake ta qoqarin dannewa acikin zuciyarsa nan da nan idanunshi suka canza kala cikin tunanin da maryam take taji yana cewa "yarinyar mafarkina ce dana zanata da hannuna, itace cikar burina ce farincikina ina matukar sonta itace mace ta farko da zuciyata take so .." jin haka yasa gaban maryam yayi wani mummunar faduwa sakamakon jin abinda ya fad'a ta juyo ahankali ta tsura masa idanunta duk da ba karon farko kenan ya ta'ba fadar haka agabanta ba amman na yau din yasa taji wani iri a gbdy ilahirin jikinta ta lura baya iya boye fellings dinsa akan zanen ." ina ma zata ga fuskar yarinyar taga dame tafita da har zuciyarsa ta zabeta alhalin ita din ba gsky bace ?tuna zane ce yasa ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya mai had'e da zallar kishi "ina matukar sonta auta amamn na rasata a yanzu haka ina son raba rayuwata da tunaninta da duk abinda ya shafeta yana magana yana kallon screen din wayarsa wanda Ke dauke fuskarta "mun dace da juna ko ?ya tambayi nana hauwa'u yana lumshe tsumammun idanuwanshi dake cike da azaban ciwo ." Nana hauwa'u bata bashi amsa tmyr da yayi mata ba ta kalli maryam dake tsaye tana dubansu idanuwanta cike da kishi ajiyar zuciya ta sauke tace "yaya zamu ce allah ya baka lafiya "na tambayeki baki bani amsa ba ya fad'a a mutukar fusace yana watsa mata harara "me kace ?" shiru kawai yayi tare da tsura mata idanuwanshi itama kallonsa take tasan abinda ya tsana kenan dan hk muryarta na rawa tace "kun..." kun dace sosai kawai dai matsalar ita din ba genuine bace wani dogon tsaki yaja yana cewa "nonsense !"you and this stupid girl should leave this room right now "ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa da sauri ta kamo hannun maryama suka fice daga d'akin ." Bayan fitarsu kwanciya yayi yana cigaba da kallon hoton screen din wayarsa dayawa daga cikin hotunta ya konasu hatta tsarka zanenta dake wuyansa always yayi flushing dinsa ,kadan ne daga cikin zanenta suke cikin d'akinsa sai na kan screen din wayarsa suma nan kusa yana sa rai zai rabu dasu ya huta da tunaninta sosai yake kallonta "muguwa "ya furta a wahalacce "kin addabi rayuwata kin hanani zaman lafiya ke wace irin muguwa ce da zaki damun rayuwata ?ya tambayi kanshi yana mai kawar da kansa daga kallonta yana tunani "anya bazan dinga zagawa cikin anguwane anguwani ba ko allah zai sa na ganta "? wannan ai hauka ne mr ata kake shirin yi ,me yasa bazaka yarda cewar yarinyar nan ba gsky bace Kmr yadda aka Ke fad'a maka ? shiru yayi yana jin wani irin buguwa da zuciyarsa ke yi akanta sosai yake son raba kanshi da tunaninta ." Bangaren maryam kuwa suna taka step tana maseefa "nifa shiyasa bana son zuwa inda yake bashi da aiki sai maseefa da disga mutun sannan wulakancinsa baya qarewa akan kowa sai akaina ko ban shiga tsabgarsa ba sai ya hada dani ni wallahi bana son auren zan dai yi ne kawai dan kun dameni , dan allah ku raba ni da aurensa na huta tunda ba'ayin aure mutun daya ." murmushi nana hauwa'u tayi "na lura kishi kike da zane fa "babu wani kishi sister amman ka auri mutun zuciyarsa na mafarkin wata aljana can wannan ai sai su shafi mutun azo arasa meke damuna "hhhhhhh nana hauwa tayi dariya "yarinya kina da aiki kam dan fasa wannan auren sai dai idan daya daga cikinku ne ya mutu maryam taja tsaki ta d'auki hanyar da zata kai ta d'aki ta shige tayi kwanciyarta dan kar mami tayi amfani da zamanta a parlour tayita aikenta d'akinsa shi kuma ya samun damar ci mata mutunci ." Mr ata na kwance akai knocking kofar falon yana daga kwance ya bawa mai yi knocking din izinin shigowa hisam ne ya shigo cike da kulawa ya qaraso ya zauan yana cewa "a she bakaji dadi ba ? ya amsa da kai kawai "oh my god amman dai ba matsalar nan bace ? "no ! wannan muguwar yarinyar ce " maganar ta daki kunnuwan hisham ya dan tsaya yana kallonsa yana nazarin maganarsa "yes muguwa ce taki barin na ganta a zahiri taki barin zuciyata ta zauna yanzu ko mafarkinta nayi bata min magana , bata min murmushi this love is so hurt wallahi muguwa ce amman har yanzu ina jin sonta hisham na qasa cireta araina ." ya sake kallonsa ya girgiza kai cike da tausaya masa ya mike da kyar ya shiga bayin dake ciki ya zubar da yawu ya dawo ya zauna ya sake kallon hisham yaga shi yake kallo fuskarsa da mamaki ya sake girgiza kai dan gbdy ya fahimci wa yake nufi "gsky wannan yarinyar tana baka wahala " ya langwabar da kanshi gbdy ya koma kalar tausayi "wallahi yau shekara nawa ina faman da soyayyarta amman sam sam yarinyar nan bata tausayina yayi mgnr duk jikinsa ya sake kana kallonsa kasan bashi da lafiya ." "da ba dan baka da lafiya ba ai da mun dan dinga zagawaya cikin unguwani ko zamu ganta ko wanda yasanya nima nayi wannan tunanina hisham amman bazan iya ba ya fad'a yana lumshe ido yana jin wani d'aci a bakinsa wanda ya rasa na meye ,"karka ce haka ata ka bari idan ka samu sauki kaje france ka dawo lafiya sai mu fara nemanta " nace bazan iya ba wannan muguwar yarinyar kona ganta damuwa zata zame min a zuciyata ." Zuciyarsa na zafi yace tashi muje ka d'a zaga gari ko jikinta zai rage nauyin da yake "ya fad'a yana jin tsantsar soayyarta na ratsashi koina ajikinsa ya mike da kyar "ata kayi zauna gida wallahi jikinka babu kwari "karka damu muje kawai tunda kana tare dani bani da wata matsala ahankali suka sauko falon qasa babu kowa a falonta farko da alamun mami tana falonta na uku yaso sheidawa mami amman yasan zata hanashi fita koina dan haka ta kofar baya suka fice dan baya son escourt dinsa su bishi ya zauna shiru a gefen hisham dake tuki yana ciza lip's dinsa "ina muka dosa "?cewar hisham ". muje gra dan ina ji ajikina a irin wuraren nan zamu samu muguwar yarinyar nan "hisham ya kwashe da dariya har da dukan stearing mota shi kuwa gogan ya hade rai a she a fili yayi mgn ba "wai muguwar yarinyar nan wallahi ata baka da dama ,yanzu dai wani gra ne a kusa damu ?mr ata yayi masa banza ya maida kallonsa gefen titi yana kallon mutane da motocin dake kai kawo "duk da kaki kayi mgn bari muje ikeja gra nan ma shiru yayi yaki cewa komai "gskiy ata ka iya bada suna pricess ta tashi da sarauniya ta dawo muguwa"dan allah malam ban son isknaci ka maida hankalinka ga tuki " ya fad'a yana nuna masa gaban mota da hannunsa "naji amman yanzu ace taki sa'a ka ganta a zahiri zaka ganeta "wallahi zan ganeta ". daga haka bai sake yin magana ba shiru motar tayi babu wanda ya sake cewa komai har suka d'auki titin ikeja ." Ahankali Ummah da aunty da maryama suke tafiya a hanyar fitowarsu titin unguwarsu domin su dauki hanya zuwa marcaz duba jikin hafsat diyar aunty fati , maryamah ta hango mlm yahuza ya nufo hnayar da suke da littafi a hannunsa da alamar islamiyya zashi tun daga nesa ya fara raragefen alamun Kamala ya durkusa har kasa ya gaishe da aunty da Ummah tare da cewa "unguwa zaku né ? maryama ta d'an kallesa ta d'an basar dan kar aunty da umma su fahimci akwai wani abu atsakaninsu tace" rakiya zanyiwa aunty tare da umma zuwa bakin titi ." " allah sarki ya sake durkusawa har kasa ya gaidai umma da aunty duk da yasan tahirin rayuwarta amamn bai ta'ba sanya mahaifiyarta acikin kwayar idanunshi ba amman ya gane aunty ce mahaifiyarta dan ko dan yanayin tsawonsu iri daya ne , mlm yahuza yayi murmushi yace "dan allah ku dan jirani minti uku kafin ku isa titi ma na dawo amman dan allah karku tafi a kafa Ummah ta d'an yi murmushi tace "kada ka damu dan allah , kada ka wahalar da kanka ba wani nisa da inda zamu ba mu gode Kwarai da gaske ." " a dai min Afuwa ina zuwa yanzu Ummah tace tô shikenan mlm yahuza yayi murmushi ita dai maryama ta bisa da kallon mamaki dan bata san me yake nufi da kafin suje titi ya qaraso ba ummah ta dubeta cikin mamaki "wannan kuma wanene ? wallahi malamin mu né na makaranta islamiyya ummah tayi shiru domin ta danyi zargin son maryama din yake itama dai marayam taso ta fada mata kasancewar bata boye mata komai amman ganin fadar bashi da wani amfani tunda da zarar ta amincewa mutun ya fara zuwa kwana biyu sai ya gudu batare da laifin komai ba ." suna tafiya suna hira har suka karaso bakin titin gwagulori wanda ya dawo sabon titi a yanzu sakamakon gyaran daaka masa suna tsaye kawai sai ga mota ta nufo inda suke maryama tasha jinin jikinta domin dai tasan bashi da mota amman babu mamaki ko ta abokinsa ce yayi burki agabansu ya fito daga cikin motar "umma ku shigo na kaiku har inda zaku "maryama shiru tayi mamaki ne ya damu zuciyarta tunda take bata ta'ba jin mlm yahuza ya dan burgeta ba sai yau sosai tayi farinciki da abinda yayiwa mahaifiyarta da ummanta ido kawai ta tsura masa ta cikin nikaf dinta tana kallonsa cikin farinciki shi kanshi ya fuskanci hakan ." ya zagaya ya bude masu mota suka shiga kafin ya zagaya bangaren direba ya jefa mata wani kallo mai nuna tsantsar so kawai itama ta tsinci kanta da mayar masa da murmushi suka wuce ita kuma ta koma gida duk da abinda yayi mahaifiyata da ummah a yanzu bata ji ta fara jin mlm yahuza acikin zuciyarta ba amman ta kudirce zata danne zuciyarta ta fara sauraronsa ." Hud'u daidai ta shirya zuwa islamiyya bata tsaya jiran sakina ba ta kama gabanta acikin aji sune na farkon zuwa ita da kawarta subai'a wacce suka qare karatu tare ahankali suke hira fitowar result dinsu kafin malamin da zai daukesu darasin qurani ya shigo sosai taso tayi mata hirar mlm yahuza amman ta kasa har aka cika a ajin mlm abbas ne ya shigo nan da nan suka fara karatu ita dai karatun yau dai tazo makaranta tayisa amman zuciyarta fal da walwala da irin farantawar da mlm yahuza yayi mata dan tana matukar qaunar mahaifiyarta da umma duk wanda yaga girmansu kuma ya mutunta matasu tô lallai zai samu wani babban matsayi acikin zuciyarta most especially mahaifiyarta tana tausayin halin data tsinci kanta ciki yana daya daga cikin abinda yasa ta d'auki komai nata da mahimmanci ." "ta godewa allah ta kuma ta godewa mahaifiyarta da umman tare da abban sadam domin sun tsaya akan ganin sun ingata rayuwarta da karatun boko da Arabic tun alokacin da take secondary babu wanda yasa rai zata cigaba da karatunta zuwa jamia sai gashi kwatsam allah ya taimakesu ita da subai'a sun samu scholarship daf da zaa tashi ta shigowar mlm yahuza makaranta ,taso Kwarai ta gansa tayi masa Godiya ta fito tana duddubawa ko zata gansa amman bata ganshi ba zuciyarta taso ta gansa farincikin da yasa iyayenta take son tayi masa godiya dan tasan dole zai ji dadi acikin ranshi ." Bayan an tashi daga makaranta bai biyota ba kamar yadda ya saba sai dai kafin ta isa gida kanwarsa nafisa tayi saurin isa inda take daman kuma tasanta sai dai ba aji daya suke ba tana gaba daita sosai suka gaisa tare daita suka cikin gidansu inda suka iske aunty salma a tsakar gida tana zaune tana waya ganinta tare da nafisa yasa aunty salma kashe wayar suka gaisheta suka wuceta suka shiga bangarensu maryama." suna shiga ta nuna mata wajen zama "nafisa ki zauna ga waje tayi murmushi ta zauna akan kujera ita kuma ta shiga dakin aunty ta duba inda aunty tasaba ajiyar kudi taci saa ta samu naira dari ta dauka ta fito tana cewa nafisa "ina zuwa ." "nafisa ta mike ta biyota ina zaki bari muje tare maryama tayi dan Jim dan taso ta zauna taje ta siyo mata lamurje ta kawo mata amman bata da choice dole ta barta suka sake fitowa tare kai tsaye bangaren aunty hassana suka shiga tayi sallama ta isketa zaune tare da yaranta babu wanda ya amsa sallamarta bare ya kalli inda take bata damu ba dan ta saba "aunty hassana ina yini akwai lamurje? "Akwai na nawa zaki tsiya "?amm.. na naira dari ne wani dogon tsaki taja "ai nasan bazaki canza zani ba daga na naira darin babu qari kullum ana waje daya baa cigaba ni bani kudin ki shiga ki dauka ki bace min da gani ." Zuciyar nafisa ta cika da mamakin aunty hassana maryama ta mika mata kudin ta shiga ciki ta dauka suka fito ta mikawa nafisa gashi nafisa babu yawa "kai haba ai babu komai ai danasan ma kashe kudinki zakiyi da tun farko na hanaki " karki damu ai ba wani abu bane maryama ta fada tare suka shiga bangaren Ummah duk inda maryama tasa kafarta nan nafisa take ajiyewa ta share wa umma gida ta gyara mata koina tare da nafisa suka fito zasu wuce aunty salma ta kirata cike da isa ta isa inda take "kije kiyi min shara " "Shara !" Maryama ta furta a hankali?eh ko bazakiyi bane kika tsaya kina maimata min abinda na fada ?zanyi ta fada a taikaice tare suka shiga bangaren aunty salma ta fara shara "aunty maryama kawo na share miki da sauri dan akwai abinda ya kawoni "? itama tashi jinin jikinta dan tunda suke da nafisa bata taba zuwa inda take ba sai yau "no ki barni na share nima yanzu zan gama ta zauna akan kujera sakina da shukura suka shigo shukura na ganinta ta washe mata hakora "nafisa yau kece agidanmu ?ta tambayeta murmushi ya sake bayyana akan fuskarta "eh nazo wajen aunty maryama ne "aunty kuma ?ta fada a rude "eh mana aunty ce ai maryama tunda zuciyar babban yayanmu ta kamu da matsanancin sonta dan har wani kirki ya kirkirawa kanshi dan kawai ya aikoni wajenta ta fada batare da wani shakka ba ." shukura batace komai ba ta zauna kusa da nafisa " inata son nazo gidanku amman ban samu damar zuwa ba saboda makaranta nafisa tayi murmushi "ai kuwa sai ki arawa kanki lokacin ki dinga zuwa gidanmu tunda yayana ya kamu da soyayyar maryama nasan naki matsayin sai yafi nawa zance bai yiwa shukura dadi ba dan haka kawai taji bata son wata halaka a tsakanin maryama da mlm yahuza haka kawai take jin rashin jin dadi aranta ." Maryama tana gama shara ta fara kokarin wucewa yayinda nafisa take qoqarin mikewa shukura kuma tana janta da hira "kinga bari na isar da sakon da aka aikoni gobe ma hadu a islamiyya ta tashi tabi bayansa maryama suka jera har cikin falonsu atare suka zauna akan kujera nafisa na cewa "aunty nah "maryama tayi murmushi "kai nafisa da ki daina ce min aunty kullum fa da sunana kike kirana "ai yanzu komai ya canza baki ji yan karin magana ba sunce idan kidi Ya canza dole ma rawa ta canza nafisa ta fada tana dariya "ya karatu yanzu uzukin nawa ?maryama ta sauya magana dan bata son wata maganar soyayya mlm yahuza yayi mata mutunci Kwarai kuma ta yaba masa amman batu na soyayya bata jin zata iya yayana ne yace na fad'a miki zai zo zuwa anjima maryama tayi murmushi amman shine tun dazu baki fad'a ba kika zaunar da kanki "ai ina sane na zauna ina qarewa zabin yayana kallo naga shin haukan da yake akanta ya dace abun mamakin sai naga tafi gaban tunanina ashe da kawai kallonki nake ta fad'a tana dariya "kai nafisa a she haka kike kema?maryama ta fad'a tana murmushi santi nake yi yayana ya iya zabe wallahi maryama nayi matukar farinciki da yaya ya sanar dani Ke yake so kuma har kin amince nan fa yanayin maryama ya sauya daga murmushi da take zuwa mamaki "ita a ina ta amince masa da zai qarar .? "kun dace da yayana sosai ni daman ina tunani wa yahuza zai dauko mana acikin yammatan dake mutuwar sonshi saboda tsananin kyawunsa da kyawun halinsa uwa uba ilimi kema kuma munyi saa a komai kina dashi taso kwarai ta tsaida nafisa akan yayanta amman kuma sai ta kasa har zuwa lokacin data ciro wata karamar takarda ta bata tace gashi inji yaya in baki hanuna da naki ta fad'a tana shirin tashi daga kan kujerar da take zaune itama maryama ta tashi ganin tana alamar fita domin rakiyarta da hannunta ta dakatar da maryama "zauna abunki ba sai na wahalar dake ba ki zauna ki karanta sakon yayana cikin tsigar wasa maryama tace "ban son iskanci nafisa naga alamun raini ya fara shiga tsakaninmu ta bude baki "ni kuma asuwa na raina aunty amman dai Kiyi zamanki wallahi na gode ?" Ta koma ta zauna ganin idan ta biye mata sai su kai dare bata gama iskancin ba ta fice ita kuma ta samu waje ta zauna ta bude takarda da nafisa ta bata ." _Ina son ki takaita kanki da abinda kikasan zai war gaza farinciki dana gani akan fuskarki ina bukatar ganinki cikin farincikin dana ganinki dashi yau my maryama ina son jin muryarki cikin kunnuwana ina son jin hirarki zanzo yau byn sallah ishai_ Ta sake karantawa ta sauke naunayen ajiyar zuciya ita sam bata jin wata soyayyarsa wata killa da a shekaru biyu da suka gabata yazo lokacin tana shekara shatakwas kuma alokacin maza basu zama abun tsoro a wajenta ba da babu mamaki taji tana sonshi har ma ta iya aurensa amman zatayi kokari ko yaya ta fahimtar dashi illa soyayya gareta ." ahankali ta jingina jikinta akan kujera tana jin bakinciki abubuwan da suke faruwa daita allah ya bata kyau ya bata ilimi tana da nagarta amman bata san dalilin da maza suke gutunta bayan sun kawo kansu wajenta ba , tana zaune tana tunanin taji sautin muryar aunty salma"maryama !maryama!!ke dan uwarki wannan wani irin rashin mutunci né kalmarta ta katse mata tunaninta ta dawo haiyacinta tana magana cikin bacin rai "au zama ma kikayi dan iskanci ni nawa mijin bai kwanta ya huta ba yana can neman abinda zaku ci shine ke zaki zauna saboda sakarci banza da tunanin banza daga yarinya tazo tana sakarci da munafurci sai ki nemi waje ki zauna kina tunanin iska dana banza da wofi allah dai yasa komai zai faru abanza né tunda bashi da wani amfani ana da kyau amman ya zama na banza ." "tô ai dole ya zama na banza tunda mugun hali yayi yawa " tarasa me ta tsarewa aunty salma acikin gidan nan zuwa yanzu bata tunanin iya kiyayya ce kawai ta fara tunani har da hassada take mata akan halittar da allah ya bata idan ba haka ba tana mata komai iya bakin gwargwado tayi mata shara tayi mata wanki idan ta kama wanke wanke duk tana yi dan dai a zauna lafiya da kuma kar ayi masu gorin ciyar dasu daake acikin gidan shiyasa sau tari bata son fita tsakar gidansu tafi son tayi zamanta a daki dan da zarar ta fita ko ita ko aunty hassana sai an samu wanda yasata aiki ko ya zageta ko mata gori ." muryarta a sanyaye tace "yanzu ni aunty salma me nayi miki ?akwai abinda kike bukata da banyi miki ba ?ta rike baki au tambayata ma kike yi saboda yanzu kin kawo karfi an balaga an balallage an zama iyayen mata ? " "allah yasa ba ita kadai ta balaga ta zama iyayen mata ba wadan da suka balaga suka zama iyayen mata suna da yawa " suka tsinkayi muryar habib abayansu yana harararta ta juya tana kallonsa "zo ki fitar mana daga daki kafin na miki dukan mutuwa "uwarka da ubanka basu isa ba bare kai qaramin dan iska bazan fita ba idan kana iyawa zo ka fitar dani tattaccen d'an iska ." Jin haka yasa cikin fusata ya nufota gadan gadan maryama ta mike da sauri ta shiga tsakani tana cewa "Uhm uhm after dad babu ruwanka daita "tô wallahi kice mata ta fita ta bar mana dakinmu "au har wani takama kake da dakin aro? "dakin aro ne a aka bawa uwarka byn kai a kusa da dakin kashi aka haifeka idan bakasani ba kasani ga dakin daaka yi cikinka ga masai Shege ma shegen girman tsiya anyi mugun gado a wajen uwa ". Ya daga hannu zai kai mata mari maryama ta rike hannunsa a rikice cikin muryar kuka tace "haba habib ka barta mana ta fadi duk abinda take son fad'a ai bakinta ne tunda mu din ba shegu bane meye abinda zai dameka arziki kuma na allah né "kinga makira banason iskanci da munafurci ki barshi yayi min abinda ya ga dama amman gamawarsa ke da wuya zanci uwarsa da shi kansa dan wallahi duk iskanci da yayi akan uwarsa zan rama dan ita ce daidai ni ba shi qaramin dan tasha ba ,yana yawo suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ". "Dan allah kiyi hakuri karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ". "What!" "Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ." a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ." Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ". "taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake da kowa allah ya taimakesa yazo idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu." ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ." "Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar aunty tana kiran sunanta tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa " "Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu damar kaga na fita murmushi yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ." Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta zuwan dakin aunty duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita ya zauna yana wasa takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ." Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?" "a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ." Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ? "To wallahi yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ." zaro idanuwa sukayi suna sake ja baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan zai sara mata takobi aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi "zaka kasheni ne ? "Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma . aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ". "Me yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ." nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta ,wuyan baba gali yake shirin damka ya jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 16 Ahankali maryama ta mike daga cinyar umma hawaye ne sha'be sha'be akan kuncinta ta tsurawa umma manyan idanunta wad'an da suka canza kala tana kallonta batare da tace uffan ba ,duk yadda taso ta daure ta tsaida hawayenta kasawa tayi hawaye take zubarwa sosai cikin tashin hankali mai tsanani ita kad'ai tasan halin bakinciki data tsinci kanta ciki adalilin jin labarin iyayenta ."labarinsu yayi matukar d'aga mata hankali "a she wahaalarsu da tsanar da'aka yi musu acikin family's ta samo asali ne daga soyayyar iyayensu ? haka nan taji tausayin kansu na sake shigarta . " Koina ajikinta yayi sanyi yayinda falon ya d'auki shiru ,yadda maryama tayi shiru tana zubar da ruwan hawaye tana sake tariyo halin da iyayenta suka tsinci kansu adalilin soyayya haka ma umma bata sake cewa komai ba " ahankali wani irin so da qaunar mahaifiyarta da qaninta habib ya qara shigarta" allah sarki aunty "hakika kinga rayuwa, hakika ahlinki sun d'auki zafi dayawa akanki ." "hukuncinsu yayi tsanani dayawa domin allah Ke had'a soyayya alokacin daya so ba dabarar mutun ba ,ba son ran mutun bane ,domin kuwa idan da dabarar mutun ne ko son ran mutu da mutanen duniya dayawa basu tsinci kansu cikn ta ba ." a qalla sun d'auki minti goma a haka suna kallon juna sannan maryama ta lumshe idanunta da sukai jajur alamun tarin quna da bakinciki ahankali umma ta numfasa "maryama ! ta kira sunanta a natse , ahankali ta motsa lip's dinta alamun ta amsa dan zafin da zuciyarta keyi ya danne fitowar muryarta "ki godewa allah ba kuka ya kamata kiyi ba maryama." "ki godewa allah daya qaddara aure a tsakanin iyayenki da har aka sameku ta hanyar sunanh " "Alhmd!ta furta a can kasan makoshinta tana dafe kanta dake sara da mugun karfi "ya kai ki godewa allah ki sake gode masa ko bai kai ba ? kanta ta gyada mata alamun "eh!. "To ki manta da duk abinda na fad'a miki muje Kiyi sallah kici abinci ki kwanta ki huta " da karfi maryama ta fizgo magana "bazan iya manta komai ba ,a halin yanzu ma ganin komai nake kamar a yanzu ya faru har nayi danasani umma nayi danasani jin wannan mummunar labarin rayuwa irin rayuwar da iyayena sukayi rayuwar kaskanci ne a wajena." "why umma? "me yasa komai yake faruwa damu haka ?ahankali ummah ta shafa kanta zuwa gadon bayanta tare da cewa "kiyi hakuri maryama kowa da kalar irin tasa qaddara a yanzu jajurcewa zaki qara akan wanda kikayi har kika samu cikar burinki na zamowa cikakkiyar mai ilimin lissafi ,kiyi qoqari ki tsaya bisa kafafunki domin tallafawa rayuwar mahaifiyarki daya qaninka domin ina hango tarin nasara da kwanciyar hankali atattare dake , bilkisu na bukatar farinciki ,maryama nasan da sannu zaki zamewa bilkisu sanyin idaniya amman fa sai kin manta komai maryama kin rungumi qaddarar rayuwarku ." "Na yarda da qaddara ummah domin yana daga cikin cikar imani mutun , na yarda da qaddara amman umma aunty tayi kuskure arayuwarta bance laifi bane dan taso mahaifina amatsayin da yake amamn iyaye fa umma ? "manzon sallahu alaihi wa salam yace "ridal lahi fi ridal walidaini , wa sakad'ul lahi fi sakad'il walidai ."yarda allah yana tare da yarda iyaye, haka zalika fushin allah yana tare da fushin iyaye allah ya fifita iyaye akan komai most especially uwa ummah ,babu uwar da taza ji dadin irin rayuwar da aunty tayi ." umma tayi shiru kawai tana sauraronta "misali na kwatantawa aunty irin abinda tayiwa iyayenta ya zataji ? na kawo mata in responsible man nace naji nagani sai shi duk tarbiyar da tayi tsawon shekaru tana bani nasa kafa na rugujeta ya zataji ?" magana ta gaskiya iyeyenta da yan' uwanta sun d'auki zafi dayawa amman aunty ta fisu laifi kuma lallai ya kamata taje ga iyayenta ta roki gafararsu sannan ta koma cikin danginta zuciyarta ta samu salama ." "wallahi yadda nake jin habib araina bazan iya barinsa saboda wani ba bare iyayena da suka kawoni duniya ba ,abun da ciwo ummah ba kamar yadda kuka d'auka bane kema uwa ce ummah , aunty ta kona zuciyar mahaifiyarta dayawa, yanzu na gano duk aunty ce silar shigarmu cikin matsala , iyayenta na can suna fushi daita har yau ta yaya kike tunanin zataji dadi ?"ta yaya kike tunani zan iya bata farinciki byn ga inda zata samu fiyye da nawa ."? maryama ta kalli umma cikin sarewa ta cigaba da magana " umma abun na da matukar ciwo irin ciwon dake cin zuciya da bargo ,ciwo ne da bashi da magani da mafuta har sai ka had'u da mahad'inka , shiyasa a kullum idan na kalli aunty sai naji tamkar tana boye mana wani abu mai mahimanci ga rayuwarta , ashe gsky né hakika bakinta bazai iya furta mana komai akan rayuwarta ba matsawar ita din uwa ta gari ce , dan allah umma Kiyi min rai ki raba zuciyarta da wannnan rayuwar idan kuma baki yi ba ni zanyi ,zan rabata da nauyin dake daskare a qirjinta ." Tana gama fadar haka ta mike a hankali tana share hawayen idanunta da suka gagara tsayawa tana jin wani zafi a qirjinta , bazata cigaba da d'aukar wannna nauyin ba , koda aunty bata amince ta koma ga yan'uwanta ba ,lallai ita zata nemosu a duk inda suke acikin garin nan ."muryarta a sanyaye tace "umma ni zan wuce sai da safe " kai kawai ummah ta gyada mata sannan maryama ta fara tafiya umma tayi shiru tabi bayanta da kallo tana kallon yadda take d'aga zara zaran yatsun kafafunta da kyar tamkar wacce bata da laka ." " A inda ta bar mahaifiyarta anan ta sameta tare da habib suna hira da alamun shi baya cikin damuwa kamar ita." bata tsaya ba byn tayi sallama tace "aunty sai da safe tana gama fadar haka ta wuce ta nufi d'akin baccinta bayanta suka bita da kallo , yanayinta kad'ai ya fahimtar da aunty akwai tarin damuwa atattare daita shiru kawai tayi tana tunani "har yaushe maryama zata yi farinciki arayuwarta ?". A natse aunty ta mike tabi bayan maryama tana jin tsinkewar zuciya haka shima habib akan kujerar da take zama idan zatai zane suka isketa ta dafe kanta tana sheshekar kuka atare suka qaraso suka zauna abakin gado suna fuskantarta shigowarsu yasa ta tsaida kukanta wanda taso tayisa sosai har taji natsuwar zuciyar." dogon numfashi aunty taja tare da cewa "na shiga uku ni bilkisu " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan bata qaunar abinda zai d'agawa yaranta hankali shi kuwa habib hannun maryama ya kamo cikin nashi ya damke da karfi cikin tsananin tashin hankali " heartbeat meke damunki ?." muryarta a raunane tace "babu komai after dad "ya babu komai zaki shigo cikin damuwa , yanzu mun shigo mun ganiki kina kuka amman kice babu komai ki fad'a min idan akwai abinda ke damunki ." shiru tayi tana cigaba da shesheka "ki sani bamu saba boyewa juna komai ba idan kika min haka baki min adalci ba ,ko km damuwar dazu ce ? still dai shiru tayi ,sosai suka d'aga hankalinsu ita kuma taki cewa komai sai faman ajiyar zuciya ta saukewa ." damke hannunta ya sake yi sosai yana rokonta "dan allah heartbeat karki daga mana hankali ki fad'a min kukan me kike yi ?kallonsa kawai tayi tana lumshe idanuwanta ganin yadda hankalinsa yay matukar tashi da yadda ya d'aga hankalinsa ya matukar bata tausayi daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa." "Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki tare da qoqarin kashe kanki abanza ."? "Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa." hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk yadda suka dinga kwantar da kai da murya dan suji damuwarta amman taki fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka fice d'aya bayan d'aya daga dakin da zumar zasu lalla'bata gobe ta fad'a masu dalilin kukan ." tafi mintuna goma byn fitar aunty da habib zaune sannan ta yunkura ta tashi tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta shiga bayi ta d'auro alwala ta fito ta gabatar da sallahr magariba da isha'i tare da shafa'i da wutiri byn ta idar ta koma kan katifa ta zauna tare da jingina bayanta da pillow ta rungume hannuwanta duka a qirjinta ." ahankali ta runtse idanunta tana tariyo komai daya faru dasu tun suna yara "Kenan adalili rasa mahaifi da kaka yasa rikonsu ya dawo hannun abban sadam ."tun tana qarama yar shekara hud'u a duniya ta taso cikin so daga bangaren abban sadam da umma da mahaifiyarta amman daga bangaren aunty hassana da sauran 'yan'uwan mahaifinta kuwa saboda haushin da kiyayyar mahaifiyata yasa suka dinga nuna masu tsana da tsamgwama , sun ci wuyarsu sosai most especially Ita ganin kiyayyar dangin mahaifinsu da irin tsanar da baba gali yayi masu ya bawa aunty salma damar cin kashi akansu da mahaifiyarta ." tun daga lokacin kuruciya har zuwa girmanta abinda yake rage mata zafin gidan shine soyayyar umma bancin ita kowa a gidan baya sonsu amman kuma wani lokaci shi kanshi baba gali ya kan tausaya masu in dai ba fad'a sukai da sakina ba ko yarshi qarama ba , idan tayi mata laifi ta d'an daketa shine zai fito da 'bacin ransa har ya fito da zallar kiyayyarsa ,kuma tun da ta lura son ya'ya ne dashi domin ba ita ba ko uwar data tsugunna ta haifesu baya raga mata akan ya'yansa ." "yayan baba gali uku ne aliyu sakina wacce sa'artace sai mai bi mata salamatu wacce taci sunan hajiya kakarsu ana kiranta da shukura bata fi shekara sha bakwai ba a yanzu ,itama babu yabo babu fallasa suna d'an shiri daita sai dai idan taga uwarta na fushi da zagina bata hanata sai ma dai ta zugata domin itama tana nuna kishinta akainta idan taga umma tana tarairayata ko wani ." Baba gali dinki yake ada rasuwar abban sadam yasa gidan buredi da rikonsu ya koma hannunsa alhamdulillah babu laifi ita din mai qokari ce ta kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah ya bata ." Alokacin baya kullum ta allah sai aunty tayi masu special lesson ita da habib kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta ,duk unguwar da makarantarsu ana maganarsu akan ilimi bokon da suke dashi haka duk gidan ba masu jin turanci kamar ita da habib ko wani abu za'a tambaya ita ko habib ake tambaya mahaifiyarsu ta tsaya masu akan karatunsu shiyasa ma education dinsu yayi very fast kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ". bangaren sakina da sauran yaran gidan matsalar iyayensu ne dan basa maida hankali akan karatun yaransu gashi sam basu da isashen ilimin boko ko Arabic barin ma aunty salma karta ji labari ba arabi ba boko sai uban girman kai ,sau tari idan shukura tazo koyon wani abu a wajenta bata só sai ta nuna ai itama tasani dan me zatazo wajenta akarshe idan tayi mata zero take samu a makaranta shiyasa da yarinyar ta gane ta daina bata idan tace ta kawo kai tsaye take ce mata bataso zero zataci ." hatta alwala ba daidai aunty salma take yi ba kuma sallah ma bata dameta ba ,tun suna yara baba gali Ke mata fad'a akan tarukun sallah din da take yi amman taki ta daina shi kansa daya gaji sai ya rabu daita ya dinga Kwa'bar yaransa da yin sallah sanin in har dan uwarsu ne sai dai kar su yi babu abinda ya dameta dan idan ma koyi zasu yi daita sai dai su koyi taruku sallah." Su kuwa aunty bata yarda tana gama dauro alwala zata tura habib zuwa masalaci ita km ta umarceta taje tayi alwala sannan a kullum dare auty ta kan fito tsakar gidan tare dasu har sakina kasancewar tana qaunarta ta koya masu darasin lissafi , tana daukar lokaci akansu har sai taga sun gane sannan ta bukaci wanda yake da damuwa a bangaren karatunshi ko baka da matsala zatai 'yan tambayoyi ana bata amsa idan bata gamsu da amsar ba ta qara yi masu bayani , bangaren karatun alqurni kafin suyi bacci sai aunty tasa sun karanta izawaka da tabaraka kafin su kwanta da safe kuma sai sunyi murajaa alqurni sannan su shirya su wuce school ko islamiyya ." A ranar batayi isashen bacci ba ga tsananin tunani ga kwadayin son ganin yan'uwan mahaifiyarta gargadin kanta ta shigayi akan fad'awa soyayya da ma ko waye idan kuma soyayyar ta zama dole sai dai tayi a gidan aurenta ga duk wanda ta aura har asuba tayi maryama batai wani yi baccin kirki ba shiyasa kiran sallahr farko acikin kunnenta akayi ta gyara kwanciyar ta koma ta kwanta bacci kad'an tayi ta lalubo wayarta ta duba taga biyar da rabi saura lokacin sallah yayi dan har an tada sallah a matsalacin unguwarsu ." a hankali ta mike zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da adduar tashi daga bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta shiga bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta gabatar da sallah asuba byn ta idar ta d'auko alqurni ta soma karatu cikin suratul baqara anatse ta kai idanunta ga window d'akin taga gari ya fara sha tayi azkar din safe tana nan zaune tana lazimi har shida saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ." Ta mike da kyar bakinta dauke da salati sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar shara ta share d'akin ta fito har falo ta shiga d'akin mahaifiyarta bata ganta ba tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne kullum safiya sai tayi wanki kayanta wani lokacin da nasu ta share d'akin tasss ta fito da sharan zuwa falo ta shiga kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta kamkame jikinta waje daya wani iri take ji a duk gbdy ilahirin jikinta soyayya irin wacce iyayenta sukayi bazata ta'ba yarda ta jefa kanta cikinta ba". Ta godewa allah daya bata kyakkyawar zuciyar da bata da lokacin maza ,bata jin soyayyar ko wani nmj ta ratsa koina ajikinta ,duk wanda yazo da sunan sonta ya dawo ya gudu bata taba jin haushi ko kewarsa bare ta damu kanta akansa ita fa gsky tafi ganin laifin mahaifiyarta akan abinda iyayenta sukai mata kuma taji dadin mutuwar mahaifinta akan rayuwarsa domin daa kalleta ace ita din diyar dan shaye shaye da neman mata ne wallahi gara mutuwarsa akan rayuwarsa, data dangwama tana masa adduar shiruya allah gara ta qare rayuwarta wajen yi masa addua samun rahmar Allah ." Da misalin karfe goma sha d'aya da rabi daidai na safe aunty duk ta damu tun jiya rabon tasa maryama a cikin kwayar idanunta ga dai alamun ta tashi dan har tayi ayyukanta na yau da kullum data saba dan ga parlour nan a gyare tsab sai zuba kamshi yake koina tsab daga ita har habib sun kasa samun kwanciyar hankali bare su karya ,sai ma wata faduwar gaban data ziyarci zuciyarsu ." mikewa aunty tai ta nufi dakinta shima habib ya biyota kusan atare suka shiga dakin har suka shigo maryama batasani ba tana can duniyar tunani tare da rafka uban tagumi da sauke numfashi a hankali ahankali, da sauri suka qarasa gareta dan yadda suka ganta ya matsifar daga masu hankali fiyye da jiya dan har wani doguwar rama tayi atare suka kira sunanta suna tmbyrta "wai maryama menene damuwarki ne ?" "heartbeat banason ganinki cikin damuwa saboda duk duniya babu wanda nake so byn Allah da aunty sai ke karki bari tunani yasa mu rasaki ya fad'a idanuwanshi na kanta "bansan me yasa kike son kashe kanki akan damuwa ba wanda ni a tunani kowace irin damuwa ce zaki iya hadiyeta". aunty ta qarasa maganar tana furzar da iska me zafi daga bakinta a hankali ta mike ta koma kan kujerar aikinta ta dauko farar takardar daya ta ajiye akan table domin samun damar cigaba da aikinta ta zaro pencil har kala uku ta fara zane sai dai zuciyarta rawa take nan da nan idanunta suka cika da ruwan hawaye tarasa dalili daga jiya zuwa yau ta sake rasa sukuni da farincikinta, bata jin shaawar komai babu abinda take so da bukata kamar ta kadaice kanta ." Aunty ta dakatar daita daga abinda take tana dubanta zuciyarta na mata wani irin suya a game da halin da take ganin maryama din ciki wanda bata san silar faruwar haka ba maryama bata dago ta kalleta ba ta cigaba da abinda take gbdy kamaninta ya canza ,ahankali habib ya shiga rarrashinta da nasiha mai kashe jiki gbdy fuskarsa ta canza Kmr zai yi kuka , Ita kam aunty kasa furta komai tayi ta zuba masu idanunta tana jin tarin damuwa ganin hk yasa maryama ta soma magana kamar bata son yi "abinda muka bukaci Auny ta fada mana taki jiya umma ta fada min babu abinda ta boye min sai wanda batasani ba." ta karasa mgnr tana dago kanta Tare da sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta sakin wani sabon kuka lokaci daya shima kwayar idanunshi suka kada suka canza nan take yaji tsanar dangin aunty ya shigesa kasamcewarsa nmj kuma duk nmj dole yayi kishin mahaifinsa nan take ya yanke cewar a zuciyarsa bazai furtawa aunty komai akan yanuwanta ba koda kuwa ita kanta uwar gayya ta amince zata koma garesu amman shi babu shi babu su har abada ." "Tô princes kinji kadan daga cikin tarihin rayuwata kuma ina fatan kin gamsu ?shiru kawai maryama tayi tana kallonta tare gyada mata kai "good my princess kinga rana ya fara ki tashi kici abinci ki kwanta ki dan huta kafin lokacin sallah yayi ta fada tare da mikewa tsaye "yanzu aunty haka rayuwa zata cigaba da tafiya ?tayi maganr cikin raunin murya aunty taja ta tsaya tana dubanta tare da nazarin maganarta "ina nufin haka zamu cigaba da rayuwa batare da kin san matsayinki a wajen iyayenki ba ? "karki damu dan ni har yanzu bana bukatarsu arayuwata ina ganin kuma ku ciresu acikin zuciyarku "ni daman a yanzu dana gama jin komai na ciresu araina dan basu da wani amfani a wajenmu gara mu qarasa rayuwarmu haka batare dasu ba "haba habib me yasa zaka fadi haka shikenan ita aunty haka zata qare rayuwarta ? kai yanzu zaka iya rayuwa babu ita da kake goya mata baya ?"tayi maganr cikin tsananin fushi "kai daya kamata mu taru mu shawo kanta shine zaka ce haka .?" guntun numfashi ya sauke yana cewa "lallai heartbeat kina da aiki mutanen da suka wulaqanta mana mahaifi dan kawai talaka ne shine zamu tashi muje wajensu alhalin bamu da komai muna nan dai a yadda suka san mahaifinmu babu wani cigaba da muka samu gsky ni bazanje inda suke ba kuma har abada "gsky habib ya kamata ka tsaya kayi tunani da kyau abinda ubanka yayi bai kyauta ma iyayen aunty ba, ni nan naji dadin dana girma baya raye wallahi da cigaba da ganin rayuwarsa gara mutuwarsa a wajena ."kallonta habib yayi yadda ta zuba masa idanunta cikin bacin rai tana fidda numfashi da kyar "ni babu wani tunani da zanyi akan wannan matsalar ke ma kuma ki bar magana a iya nan dan banga abinda zai sa naje gurin makiyanmu ba kuma ni banga abinda mahaifinmu yayi ba daya cancanci tozarci irin wanda akayi masa ba tun kafin ya qarasa maganar qirjin aunty yayi wani irin bugawa da karfi duk da bata bukatar iyayenta arayuwarta amman bataji dadin kalmar habib din ba ." "wallahi wallahi habib idan ka sake furta wannna kalmar zan balain baka mamaki "kinga ni tafiyata ya nufi kofar fita yana cewa "allah dai ya baki hakuri amman babu abinda zai kai mu gurin makiyanmu ya qarasa fita ,jikin aunty yayi sanyi ta bude baki zata yi magana sai kuma ta kasa cewa komai "aunty !. maryama ta kira suannata ,a hankali aunty ta motsa lip's dinta "naam !"karki dauki maganar habib da mahimmanci domin shi yaro ne ke uwa ce da muke kallo muke koyi daita kuma kece malamammu dake nuna mana daidai da ba daidai ba ,ki natsu aunty da kyau ke mai ilimi ce allah subuhanahu wata ala yace acikin suratul ahkhaf aya ta arabin da biyar وَوَصَّيْنَا الْإِنْسَانَ بِوَالِدَيْهِ إِحْسَانًا ۖ حَمَلَتْهُ أُمُّهُ كُرْهًا وَوَضَعَتْهُ كُرْهًا ۖ وَحَمْلُهُ وَفِصَالُهُ ثَلَاثُونَ شَهْرًا ۚ حَتَّىٰ إِذَا بَلَغَ أَشُدَّهُ وَبَلَغَ أَرْبَعِينَ سَنَةً قَالَ رَبِّ أَوْزِعْنِي أَنْ أَشْكُرَ نِعْمَتَكَ الَّتِي أَنْعَمْتَ عَلَيَّ وَعَلَىٰ وَالِدَيَّ وَأَنْ أَعْمَلَ صَالِحًا تَرْضَاهُ وَأَصْلِحْ لِي فِي ذُرِّيَّتِي ۖ إِنِّي تُبْتُ إِلَيْكَ وَإِنِّي مِنَ الْمُسْلِمِينَ Allah yana yiwa mutane wasiha ne akan su kyautatawa iyayensu , mahaifiya ta d'auki cikin mutun ,tana mai shan wahala ,kuma ta sauke shi cikin wahala ,da daukar cikin da yaye d'a na tsawon wata talatin har lokacin da karfin mutun zai kai girma yasan ciwon kansa har zuwa karshen ayar ,cikin girmamawa ta cigaba da magana "kiyi min wannnan alfarmar aunty , wallahi dan kinje garesu a halin yanzu ba kasawa bane bugu da qari iyayenki suna da hakki akanki babu ruwan allah da abinda sukai miki ". "maryama mu bar maganar nan ta wuce dan allah sannan ki fito ki karya kar abincinki yayi sanyi tana gama fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin shiru tayi kawai tare da bin kofar dakin da kallo idanunta na kawo ruwan hawayen tana tausayin mahaifiyarta bata san meke damun mahaifiyarta ba akan iyayenta sam sam bata son ana mata maganarsu tamkar wanda akayiwa farra'u amman tasan abinda zatai zata janye jikinta tare da tsananta addua akan lamarin allah ya daidaita da iyayenta da yanuwanta ,yinin ranar a daki ta yini taki fitowa taci komai ." ***** Tun karfe takwas na safe maryam da mami da masu aikinta ke faman kai kawo a kitchen suna qoqarin had'awa mr ATA breakfast sosai mami take lura da yadda maryam take gudanar da aikinta , babu laifi tafi da kokari sosai sannan ta rage son jikin da take dashi wajen girki suna girki suna hira mami ta cigaba da nuna mata wasu abubuwa suna cikin aiki sai ga sallamar hindu ta shigo maryam ta amsa tare da lekawa tace "hindu ce ki shigo muna kitchen muna aiki ne." wani irin kallon tayi mata wanda yasa maryam taji wani iri ajikinta ,hindu ta tsaya bata shiga kitchen din ba kamar yadda maryam tace ta samu waje ta kame akan daya daga cikin kujerun falon ,mami ta dawo inda maryam take tsaye tana kallonta "sannuki maryam gsky kinyi kokari sosai yau kin aikatu da kyau haka ake so, maryam tayi murmushi kawai tana jin dadin yabon da mami tayi mata "na gode sosai ai nan gaba zan kware na zama professional ta bangaren girki bazan ta'ba baki kunya ba ." mami tayi murmushi tace "da alama zaki wanke zuciyar mamnki ta gyada mata kai alamun "eh !" "To ni zan hau sama na dubo adamcy Idan kin kammala komai ki shirya dinnig kije kiyi sauri Kiyi wanka ki shirya ki dawo Kiyi saving din sarkin zuciyar Kiyi komai a natse kin dai san halinsa dan oya oya ne yafi son komai cikin sauri sauri bare yau din nan sai ahankali ."mami dan allah ki zuba masa da kanki mana"idan kunyi aure nice zan dinga zuwa gidanku ina zuba masa ?"dakewa zakiyi maryam ai ya kamata ace kin saba da halinsa "wallahi mani babu mai iya sabawa da halinsa sai ke nifa mugun tsoro yake bani idan na gansa hatta kayan cikina karkarwa suke mami tayi murmushi tana cewa ni na wuce "To mami sai kin fito ta fad'a cikin murmushi mami ta fito zuwa parlour'n." hindu na ganinta ta saki fuskarta sosai tare da gaishe da mami cike da sakin fuska mami ta masa tana tmbyrta mutanen gidansu ta amsa da lafiya lau kowa yake "mami ina ya adam ne ko har yanzu bai tashi ba ?"eh!hindatu ina tunanin bai tashi ba amman yanzu haka ma samansa zani na taso shi dan yace idan ya wuce tara bai tashi ba na tashesa rausayar da kwayar idanunta tayi tana jin wani zazzafan sonshi ." Mami ta nufi saman dakinsa tana mamakin hindu su dai yaran zamani basu da ta ido akan nmj so na mugun rufe masu ido shiyasa har kullum take ganin girma da kimar maryam, a dai barta da son social media dinta amman rawan kai akan maza sam bata dashi dan tasan bancin itace ta hadata da adam to har abada bazata iya bude baki tace tana son shi ba ." Maryam ta kammala komai a natse ta fito a yatsine hindu ke binta da kallo tana shirya dining ,ita kuma tana tunanin yadda zasu buga kishi daita idan tai nasara shigar gidan ya adam dinta dan dole ta fita ta bar mata gidan ta zauan ita kadai ,dan idan bata kaita lahira ba lallai zata raunatata dan irin son da takewa ya adam ba na wasa ba so ne wanda bazata iya sharing dinsa da kowa ba ." Marayam ta sha jinin jikinta da irin kallon wulakancin da hindu Ke mata dan duk lokacin data kallo bangarenta sai taga kamar hararata take wanda ta rasa dalilin faruwar hakan ,sai da maryam ta tabbatar da komai yayi neat babu abinda mr ATA zai gani yayi complain sannan ta wuce ta nufi dakinsu cikin sauri still tana mamakin hindu ." tana shiga dakin bathroom ta shiga ta fara wanka sai dai matsalarta bata iya wanka cikin sauri ba idan ta shiga wanka a qalla tana daukar awa daya a bayi amman kasamcewar zatayi saving din mr ATA yasa ta tsakaita tayi wanka ta fito ta dauki man shafa warta wanda shima shafa man kanshi aiki ne domin tana daukar a qalla mintuna talati bare aje ga make up ta shirya cikin doguwar rigar shadda bazin har kasa bata gama kammala shiri ba taji sautin muryar mami na kiranta da d'an sauri ta fito zuciyarta na rawa kuma har lokacin hindu na zaune a parlour'n tayi shiru tana yi masa kallon tsab komai nashi yayi mata irin wanda take so nmj ne sai kallonsa take yayinda mami ke qoqarin jawa mr ATA kujera baya" Wani abu mai mugun daci ya hadiye tare da zama yana mai runtse idanunshi ganin mami na son bawa maryam umarnin saving din mr ATA hindu tayi sauri ta mike tsaye tana cewa "mami bari nayi saving din yayana ta fad'a tana mai sunkuyar da kanta alamun kunya "amm...! "Sweetheart bari tayi kawai ya fad'a atakaice mami ta kallesa na second biyu dan sam bataji dadin hukuncinsa ba dan tasan da wata manufa hindu ta fadi hk shi kuma gudun karyaci daga hannun maryam ya fadi haka dan tasan shi tasan halinsa baayi masa gwaninta ranta ya baci sai dai danne damuwarta ." Madadin mami ta zauna kusa dashi kamar yadda ta saba sai ta koma kan kujera ta hankince ta nunawa maryam kusa daita"maryam zauna anan kinji yar albarka ta maida hankalinta kan tv mr ATA yaji babu dadin yadda mami taja jikinta amman sanin dan maryam tayi haka yasa ya share ya dauki wayarsa yana duba sakonin dake shigowa yayinda hindu ke zuba masa abinci acikin wani haddaden plet ta matso daf dashi Sannan ta ajiye plet din a gabansa." cike da girmamawa ta kira sunansa"ya adamccccyy...!yadda ta kira sunan cikin slow voice yasa daga maryam har mami suka waigo suna dubanta murmushi ta sakar masu wanda ke nuna tana cikin farinciki sannan ta dauke kanta ta maida kanshi wanda shi gogan har lokacin bai daina abinda yake ba bare ya dago ya kalleta sai faman ciza lips din yake yana kallon screen din waya ." kira ne ya shigo wayarsa ya dauka a natse "ok but I think kasan nan da 1week zan wuce france ya aikin gunka ina fatan akwai nasara ya hade rai sosai haba hisham you should know me by now ka ta'ba ganin inda akayi haka ?kawai dan na tattara hankalina zuwa wani waje kawai su kamawa yiwa mutane barna ,ka kuwa san adadin kudaden da mukayi asara kuwa ?kowa acikinsu kanshi kawai yasani ba cigaba AGC bane agabansu well sai na shigo dai hindu ta marairaice murya sosai tace "ya adamcy ga abincin ka dan ajiye waya kaci abinci ". Banza yayi mata ya cigaba da wayarsa "a lokacin zuwa office muke gashi naji ya sultan yace yau kuna da zama na mussaman "bai kalli inda take ba bare ma ta samu matsayin ya bata amsa hakan kuwa yayi wa maryam dadi sosai ,sauran kadan ta fashe da dariya amman ta danne ,ta kalli mami wacce itama ita take kallo suka sakarwa juna murmushin jin dadi sai daya gama wayarsa ya ajiye sannan ya fara cin abinci babu irin kwarkwasan da batayi masa ba da jansa da magana amman bai ce uhmm ba bare uhmm uhm ba illa ma mikewa da yayi tsaye yana gyara yar saman suit dinsa ya dan qarasa kusa da mami muryarsa a dake yace "ni zan wuce kuma kai tsaye daga nan AGC zani "to Allah ya tsaye sai ka dawo yace" Ameen! "har ya juya ta kirasa "adamcy ! ya dan tsaya yana saurareta "kabi komai a hankali dan Allah karka dauki zafi dayawa ahankali ake bin komai ka tsaya ku fahimci juna da yanunwaka". Kai kawai ya gyada mata ba dan zai yi abinda tace din ba dan yau kusan sai ya tashi rabin mutanen kamfanin kuma daga aiki wanda dayawa yanuwa ne a natse ya juya ya fice yana fita hindu tabi bayansa har tayi taku biyu mami tace "amm...hindu yau yayanku baya cikin moon mai kyau ba kin kuma san halinsa bare idan yana jin miskilancinsa idan kika nemi ki tsaida shi komai zai iya faruwa ko kina son wani abu ya faru ne ?" Hindu ta girgiza mata kai alamun a'a daman ba tsaida shi zanyi ba gida zan wuce "to shikenan sai anjima sai data fice mami ta dawo da kallonta kan maryam "mami me kika karanta akan hindu ni yau gani nayi tana wasu abubuwa kamar son ya adam take mami ta tabe baki "wai son shi take amman shi har yanzu bai sani ba dan dayasani bazai bari tayi saving dinsa ba" maryam ta dan ware kananun idanunta sanna tasa dariya tana cikin dariya sai ga nana hauwa'u "sister yi sauri kizo kije wani sabon rigima da sauri ta qaraso tana cewa "bani na sha matar yayana "wai hindu Ke son ya adam wace hindu kuma ?" Wacce hindu mike dashi a gidan nan data wuce ta gidan baba qarami wallahi har na tausaya mata dan idan ya kirani guntuwa ita km fa me zai kirata ?" gabdaya suka sa dariya har mami "wanna kam gsky ne ina zai kaita ? ga wani cream na organic tasha duk ya canza skin dinta ta dawo farar karfi da yaji ,shi daaka bashi farar mace sol yace bai so ina ga mai shafa cream? ni wallahi da zai karbeta ma ya barni da naji dadi anan ne mami tasa baki "kar na qara jin kin fadi haka ai babu wacce zaki barwa shi da sannu zai koyi sonki dan nasan you are so different daga sauran mata ai shiyasa nace a saka sati uku ayita ta qare burina ki rage media ki janyo hankalinsa cikin kankanin lokaci ku zo juna ." "mami kina ganin komai zanyi ya adam zai soni ?" Mai zai hana maryam zai soki mana aure nawa akayi irin naku km a karshe ya zama soyayya mai karfi ,ni dai ina ji ajikina aurensa zai sa ku rasani da wuri tun lokacina bai yi ba." maryam ta fad'a idanuwanta na kan Mami "ki daina irin wannan tunani babu abinda zai faru sai alkhairi zai soki ki so shi babu abinda zai rabaku sai mutuwa shiru maryam tayi tana jin mami ." Motocinsa na tsayawa a haraban AGC escout dinsa suka firfito daga cikin motocinsu mutun biyu na qoqarin bude masa murfin mota ya bud'e ya fito fuskar nan tashi sam babu annuri yana miqawa na hannun hangunsa wayoyinsa ya nufi cikin kamfanin kallo daya zaka yi masa zaka qara jin tsoronsa fiyye da yadda kake ji ." tunda ya samu information barnar daake yi a kamfanin walwalarsa ta ragu sosai babu inda zaka kalla a fuskarsa kaga rahma ganinsa yasa kowa ya shiga hankalinsa domin a irin wannan ziyarar da yake kawowa yake korar mutun daga aiki yana tafiya ana gaishesa cike da girmamawa yayinda sectary dinsa some na biye dashi abaya hannunta rike da files wanda ake bukatar saka hannunsa duk cikin wad'an da suke gaishesa babu wanda ya masawa daya daga cikin escout dinsa yayi saurin bude masa kofar office dinsa ya shiga a natse yana duba agogon rolex din dake daure a tsintsiyar hannunsa ." ya qarasa mazauninsa ya zauan ransa a matukar bace, cike da girmamawa some tace "good morning sir ?kanshi kawai ya gyada mata batare daya amsa ba "sir ana bukatar saka hnnunka acikin wadan nan file's din ta fad'a muryarta na rawa dan ta tsorata da yanayinsa na yau gabansa ya nuna mata alamun ta ajiye cike da girmamawa ta ajiye tana rusuna masa "ya tsurawa file's din ido kawai yana kallo kafin a hankali ya dauki daya ya rabashi gida biyu a matukar tsorace ta dinga binsa da kallo har ya gama yagasu gabdaya ya watsasu sama suka tarwatse yana hura hanci sannan yace "are you crazy some ? Mmm sudais 💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 17 " are you crazy some "?ya furta a zafafe yana hura hancinsa har zata girgiza masa kanta alamun "a'a ! sai kuma tayi sauri ta gyada masa kanta alamun "Eh! dan ko giya ta sha bata isa tace masa "no ! ba bare tana cikin hankalinta "what's wrong with mr ata I did not do anything wrong ? tayi maganr acikin ranta tana mai sake kama kanta dan karta yi wani kuskuren da zai dakatar daita na wasu satittuka koma ya dakatar daita aiki gabadaya ." " ahankali ya mike tsaye ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa ahankali ahankali !! magana yake son yi amman ko ya bud'e bakinsa maganar bazata fito ba , daga can bakin kofa akayi knowking tare da cewa "may I coming sir ?". shiru yayi yaki cewa komai sannan yaki kallon kofar , some dake tsaye cikin tsananin tsoro da fargaba ta kalli glass din kofar taga prosper ne tsaye hannunsa rike da file mai cover green wani yawu ta hadiye sannan ta saci kallon inda mr ata yake tsaye taga baya kallonta ta sake juyawa tayi wa prosper alama da hannunta ya koma da sauri ya juya ya bar bakin kofar ." Mr ata yasa hannu ya d'auki wani file mai white cover dake ajiye akan makeken table dinsa yana dubawa , lokaci me tsawo ya d'auka yana dubawa yana shawagi acikin makeken office din nasa zuciyarsa na tafarfasa yayinda wata irin zufa ke tsatsafo wa some akan goshinta kamar an watsa mata ruwa .duk lokacin da taga mai gidan nata cikin damuwa itama sai ta tsinci kanta ciki dan kusan duk abinda yaje ya dawo akanta zai qare tunda itace sectary dinsa duk abinda zai shiga ya fita ta sani ." Ya sake kamo gefen lip's dinsa. na qasa yana cizawa hannunsa dake rike da file ta zubawa ido tana tausayawa duk matar datai ganganci aurensa , tana goge zufan goshinta dake ta tsatsafo mata duk da karfin sanyin ac dake ratsa office din ."Cikin kulawa da girmamawa tace "sir !" ko zan iya kiran metting a yanzu ?" "ahankali ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi da suka d'an canza kala alamun tarin 'bacin rai yake ji acikin ransa "sir !ta sake kiransa a karo na biyu ahankali ya motsa lip's dinsa "go !" ya fad'a atakaice batare daya kalleta ba da sauri ta juya ta fice daga cikin office din tana sauke naunayen ajiyar zuciya ." Cikin kankanin lokaci ta dawo ta tsaya a gefe cike da kamewa da girmamawa tace "sir komai ya Kamala kai kawai ake jira." a natse ya goya hannuwansa duka abayansa ya soma daga kafafunsa dake cikin hadadden black canvers tana biye dashi abaya hannunta rike da wata takarda mai bango ja , tafiya kad'an sukai sai ga hisham da yaya Ibrahim tare da wasu manyan maikata guda biyar suka marasa baya suna takawa ahankali har zuwa qasan kamfanin madadin yabi hanyar da zai kai shi comference room sai suka ga ya karya yabi wata doguwar hanya , nan take some tayi gaba da sauri domin ta fahimci inda yake son zuwa kafin ya shiga conference room yayinda sauran suke take masa baya, bai tsaya akoina ba sai abakin wani makeken kofar glas wanda ya kasance anan ake ajiye duk wasu ayyukansu masu mahimanci ya zura duka hannuwansa acikin aljihun wondonsa yana kallon wajen yana bukatar a bude masa ya shiga tare da qarin bayani ." Ahankali ta danna madan nan bude waje suka shiga gabadaya a natse ta shiga yi masa bayani tana nuna masa kayayyakin dake ciki da kuma wanda aka fitar kudinsu basu shigo ba duk abinda take fad'a yana jinta kuma yana fahimtarta , amman ko tari bai yi bai yi ba ." runtse idanuwanshi yayi sosai domin ransa ya gama kololuwar 'baci , daga nan wani bangaren suka nufa inda suka dinga wuce maikata da masu zuwa sarin kaya ,ba qaramin barna akayi masu ba ,yaya Ibrahim "yanzu kuna kallo akayiwa kamfani barna mai girma haka ? ya fad'a yana sake runtse idanushi dan baya ganin komai sai wani irin azababen duhu na 'bacin rai ." Yayi shiru na kusan second goma sannan ya sake motsa lip's dinsa "yanzu har kunnuwanka sun manta abinda dady ya fad'a mana kafin rasuwarsa .?" Ka manta umarninsa akan wannsn kamfani ?" duk wannan maganr da yayi Idanunshi na runtse sannan cikin tsadadden turancinsa yayita " ban manta komai ba adam "ban manta umarnin dady ba amman bani da yadda zanyi ne kai kasan halin sultan da sauran yanuwansa kowa abinda yaga dama zaiyi yanzu dai tunda kazo Komi dawo daidai amman kuma kabi komai a hankali kar asamu damuwar da zata haifar da matsala a tsakaninmu wani irin azaban ciwo yaji yana saukar masa har cikin kahon zuciyarsa yana sukarsa zuciya tazo masa wuya , baya jin zai d'agawa duk wanda yake da saka hannu acikin 'barnar dakayiwa kamfanin kafa ba ,bai sake cewa komai ba ya juya da sauri suka rufa masa baya ." conference room ."d'akin ne da'aka tanada domin tautauna mahiman abubuwa masu matukar mahimanci , dogon table ne zagaye da kujeru bakake na alfarma yayinda jikin bangon d'akin ke manne da hoton mr president na lokacin da gwanar jahar lagos ,sai hotonsa dake tsakiyar hotonsu da certificate dinsa na kasuwancinsa ."mafi yawan mutanen dake zaune aciki room din yan'uwansa ne dake aiki akarkashin kamfanin ,a natse ya shiga d'akin taron ya yana shan kamshi tsit baka jin motsin kowa sai ac dake aiki da kuma na mutane dake fita a hankali , bai kalli inda suke zaune ba ya qarasa kujerarsa wanda ya kasance mallakin mahaifinsa ne ada ya zauna cikin nuna isa." ido sultun ya runtse da karfi saboda bakinciki ganin yadda mr ata yayi wani irin zauna akan kujera na nuna isa da jarumta da kamala duk da cikin yanayi na bacin rai yake amman hakan bai hana ainihin sahihin kyawunsa fitowa ba daman kuma shi haka yake fushi ko damuwa baya hana aga kyawunsa hasalima kyau yake qara masa." wani dogon tsaki sultan yaja wanda bai san a fili yayisa ba sai daya ga gabdaya mutanen dake gurin sun juya suna kallonsa banda uban gayya mr ata wanda ya sake daure fuska alamun babu wasa ,sai dai zuciyarsa banda tafasa babu abinda take ahankali ya runtse tsumammun idanuwanshi domin saisaita kanshi daga aikata abinda ke taso masa ahankali ya motsa lip's dinsa ya soma magan a natse tamkar baya son magana sai dai jin maganar kasan magana ce ta masu hankali ce ." "The journey of thousands miles begings with a step as you all know ,ya numfasa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya cigaba d'an lokacin da muka dauka bamu ziyarci wannan kamfanin ba yasa kowa yayi abinda ya ga dama "hakika anyi mana barna mai girman da bazamu iya bari ba , bayan acikinmu kowa yasan adadin wahalar daaka sha kafin wannan kamfanin ya samu kar'buwa a idanun duniya gabadaya ,but what's more important is that duk wanda yasan yana da hannun acikinku wajen danne kwandala acikin dukiyarmu ya gaugauta dawo dashi a yanzu kafin na dauki mataki akan kowa ye acikinmu dan bazan ragawa kowa ba ,bayanin mr ata yayiwa wasu daga cikin yanuwa dadi most especially mukhtar wanda Ke rike da wayarsa yana daukar vedio tautaunawa da'ake wanda kusan duk lokacin da zaa gudanar taro haka ana yi wani lokaci a daurashi a social media wani lokaci kuma baa daurawa ." "Ina jiranku wad'an da sukayi taadanci da fashiwa kamfani domin su san kansa ba sai na fadesu ba sannan sun san number asusun kawasuwancinmu mintuna shabiyar kacal na bayar a maida kudaden daaka hamdame cikin asusu "malam ka dinga sanin yadda zakayi ma mutum magana yaji dadi (Al kalimatu dayyibat sadaqat)kazo kana wa mutane magana cike da isa da izza wa kaajie anan ? sannan su waye suka yiwa kamfani taadanci da fashi da hamdame kudin kamfani ?"sun san kansu !mr ata yayi mgnr tmkr ba daga bakinsa mgnr ta fito ba ,ya cigaba da sauraron some ." D'akin taron ya sake yin shiru babu wanda ya sake magana hatta yaya Ibrahim bai tofa albarkacin bakinsa ba illa ya zuba tagumi yana ji kuma kallonsa kuma hukuncin adam yayi masa daidai muryarsa a dake mr ata yace " ina jiranku rashin dawo da kudad'an nan fa daidai yake da bari aiki acikin wannan ma'aikatan ya fad'a yana kallon gefensa inda some Ke zaune tana qara masa bayanin wasu a abubuwa" idan haka ake son mutun yasan kuskurensa har gyara da mutane dayawa basu gyara kuskurensu ba sannan dan haka malamanmu suke koyar damu wallahi da babu wanda ze juri zaman islamiyya ba kafi fili ka fad'a mana su waye masu laifi musani ba ka tsaya jin kai da girman kai ba ,dan anan babu wanda ka ajiye , yadda kake iko da wannan kamfanin haka muke..." "Enough ! ya fad'a a matukar fusace yana dukan table "ka shiga hankalinka ,su waye mahamdama macuta yan fashi daya wuce ku " sam gaku nan tamkar. mutane amman baku da bambamci da dabbobi ,sam babu jin tsoron allah acikin zuciyarku , sultan ,fahad , hamid a wani goma sha biyu kawai na baku ku dawo da komai idan ba haka ba..... "me zakayi ?sultan ya katseshi cikin zafin rai "me ka isa kayi ?babu abinda ka isa kayi " "kunsan su dabbobi basu gane yaren biladam sai na dabbobi yan'uwansu dan Allah karku dawo da kudaden nan alokacin da nace "yana gama fadar haka ya mike tsaye ya tura kujerar daya tashi baya ya fice ."nan hayaniya ta kaure kowa na fad'ar albarkacin bakinsa kai tsaye mr ata office dinsa ya koma ." Karfe biyu daidai na rana mami na zaune a parlour tare da yaranta maryam da nana hauwa'u suka jiyo sallamar baba qarami sai da gaban mami yayi wata irin mummunar faduwa ya qarasa shigowa yayi wa kanshi mazaunin nana hauwa'u ta gaishesa haka ma maryam ya amsa fuskarshi babu yabo babu fallasa mami ta kallesu alamun su basu waje ,bayan sun tashi sun wuce mami ta fuskancesa alokacin da shima ita yake kallo "zulai naji shiru akan maganarmu banji kin neme ni ba har gashi an saka ranar auren adamu da wacan yarinyar yana da kyau nasan inda maganarmu ta kwana abun nan zai yuwa ko kuwa ?". mami ta numfasa gabanta na faduwa domin dai ita kam bazata iya sake kuno wa danta wata damuwar ba maryam ma da yaya ya karbeta ?gara kawai ta ari bakin adamcy tace masa a'a tunda tasan ko ta tunkaresa da batun bazai ta'ba amincewa ba cikin shakkakiyar murya tace "nayi masa magana ammm..."sai tayi shiru tana jin nauyin fitowar maganar "amman me ki fada min abinda yace "Uhm daman cewa yayi wai mace daya ta .." shiru tayi ta qasa qarasa maganar ganin wani irin kallon da baba qarami ke mata ido cikin ido furzar da iska yayi ya lashi lebansa na kasa sannan ya hade hannunwansa still idanunshi na kan fuskarta cikin danne fushinsa dan baya son ta gane fushinsa a fili saboda abinda kan iya zuwa yazo bare su suyi zargin da hannunsu ,cikin dakewa yace "yanzu dai kin nuna min bazan iya zuwa neman alfama wajenki kiyi min ba ko ?sam sam ba haka bane kai ma kasan halin adamcy idan kuma zaka iya masa magana da kanka to kayi kamar ma haka zai fi "no ba sai nayi masa kema uwarsa da kika haifesa bai ji maganarki ba maganar ubanwa zai ji ? " iya abinda ya iya fada kenan ya tashi ya kama gabansa ya barta cikin zullumi." Mr ata a matukar gabalaice ya qaraso gida zuciyarsa tamkar zata kama da wuta , sai dai cike da qasaita ya shigo parlour'n Mami babu kowa parlour'n sai qarar tv da motsin masu aiki a kitchen ya zauna akan doguwar kujera ya d'ora kafarsa d'aya akan d'aya yana ciza gefen lips dinsa ,ko cikakken second goma bai yi da shigowa ba sai ga hindu ta shigo dan akan danunta ya shigo tunda mahaifinta ya fad'a mata yadda sukai da Mami ta kasa tsaye ta kasa zaune , zama tayi a kujerar dake fuskartashi ta tsura masa idanunta tana kallonsa tamkar ranar ta fara ganinsa tana qoqarin bude baki tayi masa magana ya mike tsam ya kwashe wayoyinsa ya haye samansa yana jan tsaki dan shi ya tsani yawon kallo , kamar ta dakatar dashi amman ta kasa ta cigaba da zama zuciyarta na mata wani irin bugawa akanshi ." tana nan zaune har mami ta fito sanye cikin doguwar rigar na atamfar super exclusive sabuwar bugu ,mami bata tsufa saboda tsanani tsafta da gyaran jiki fuskarta a sake tace "a'a hindu yaushe kika shigo ?ban wani jima ba mami nazo wajen yaya ne "to ai bai shigo gidan ba tukun . ya shigo yanzu ya hau sama "to shikenan bari naje dakin nasa nazo har ta juya hindu ta kirata sunanta cike da rauni "mami !" Cak mami ta tsaya tare da juyowa ta tsurawa hindu ido "mami da gaske kin yiwa yaya adam maganata yace miki a'a ?"shiru mami tayi shiru ta rasa me zatace mata kafin mami tayi wata magana hindu ta cigaba da mgn cikin rawar murya "dan girman allah mami karki yi min tsakani da ya adam kullum zuciyata tafasa take akan sonshi Ke kad'aice zaki iya taimakawa zuciyata idan ba haka ba zan mutu cikin rawar murya mami tace "mutuwa kuma ?"kanta ta gyada mata tare da cewa "da gaske zan kashe kaina shine fansa akan soyayyar ya adam "na shiga uku ni zulai "mami ta furta acikin zuciyarta "kiyi addua hindu ni kaina zan só adamcy ya auri mata fiyye da biyu amman raayinsa ne auren mace daya macen dayan ma da kyar ya amince amman Kiyi addua nan gaba idan rabo sai ya qara dake da sauri ta runtse idanunta kana ta koma ta jingina bayanta da kujerar da take zaune tana jin wai irin faduwar gaba mai tsanani ahankali take zubar da hawaye ganin da gaske tarasa farincikin rayuwarta "anya kuwa mami nada tausayi da imani ."Anya mami bata da son zuciya ?"Tayi wa kanta tambayar tana jin radadi acikin zuciyarta bazata iya jurar rashinsa ba ,bazata iya ganin da wata a matsayin matarsa ba, yadda bazata zama matarsa a farko ba to babu wacce zata zama "hindu bari naje naga yayanku nazo hindu ta bude idanunta da kyau tana kallon bayan mami dake taku ahankali." Kai tsaye kitchen ta shiga ta bud'e firdge kwalin dynsimo mai sanyi ta ciro ta rufe ta qarasa inda cup's suke ta dauki daya ta daura akan qaramin tray ta fito ta wuce a parlour ta samesa zaune akan kujera yana sanye da singlet da gajeren wondo ta bude kwalin juist din ta tsiyaya a glass cup taja qaramin table din glass din dake tsakiyar dakin ta dora tray ta mika masa cup ya girgiza mata kai tace "na kawo maka ruwan sanyi ?ya sake girgiza mata kai "coffee fa ? still dai kai ya girgiza aranta tace yau dai akwai damuwa ta d'an zauna gefensa "ka daina barin damuwa na hana zuciyarka sukuni "naji sweetheart amman ba wani damuwa bane zazzabi nake ji kawai "sannu bari naje na kawo maka magani ka sha "no need sweetheart thank you "kai har yanzu bakasan ka girma bane meye abun gudu a magani ?ni dai kawai bana só né da zarar na kwanta nayi bacci zanji daidai ,tô karka kwanta yanzu magariba ta kusa ya gyada mata kai yana mai runtse idanuwanshi ta mike tana cewa "me zaka ci dan tuwon shimkafa kayi yau idanunshi ya dan bude kadan "karki damu sweetheart yau bazan ci komai ba amman zuwa anjima I need coffee tasan haka tsarinsa yake wani lokaci sai ya kwana ya yini bai ba ." ***** Tsawon kwana Uku kenan rabon maryama ta shiga harka mahaifiyarta har ma da habibi hakan kuwa ba qaramin taga masu hankali yayi ba gabadaya gidan yayi wani iri saboda rashin walwalar maryama ,ta kuma san duk akan abinda take son tayi ne domin tasan halinta tasan abinda take so da abinda bata só tana da tsananin hakuri amman idan kaga ta kafe akan abu to dole abun zai zama gaskiya ne ko alkhairi ga rayuwar mutun ,ta sani gsky take fad'a mata amman bazata iya abinda take bukata ba bazata ta'ba komawa garesu ba duk runtsi duk wahala zata daure ta cigaba da rayuwarta a yadda take yi , maryama fa ta dauki zafi sosai akan aunty da habibi duk lokacin da ta fito parlour'n tagansu sai ta koma daki ko taje bangaren umma bata dawowa sai dare da zarar tashigo kuma zata shige daki tayi kwanciyarta ko ta dauko kayan zanenta ta fara aiki ." Da misalin karfe tara na daren ranar litini maryama tana zaune akan kujera ta cilla pencil a bakinta tana taunawa a hankali idanunta na kallon celling dakin tana nazarin abinda zata zana taji an turo kofar d'aki ahankali ta kai dubanta ga kallon kofar dakin ,aunty ta gani tsaye ,ta dauke kanta daga kallonta, aunty ta maida murfin kofar ta rufe ta soma takowa zuwa inda maryama take tana ganin haka ta mike tsam ta haye saman gado tayi kwanciyata tare da kamkame jikinta tana jin tausayin kansu na sake ratsa ko ina ajikinta musamman take jin kewar yanuwan mahaifiyarta da bata taba daura kwayar idanunta akansu ba amman tana jin ajikinta zasu samu kulawarsu da soyayya a duk sanda suka had'u kamar kowani dangin uwa tana kallo aunty ta zauna daidai inda fuskarta take dan hk da sauri ta runtse idanunta tana son tayi bacci ." bacci bai samu nasarar d'aukarta ba ta juya dayan bangaren sakamakon kukan da Ke shirin kufce mata dan ita kanta dauriya kawai take akan sabon canjin data kawo a tsakaninsu hakan bai hana aunty ganin abinda take ba ,daidai inda fuskarta ke kallo ta dawo ta zauna tana dubanta hade da kamo hannuta cikin nata "me nayi miki my princess kike qoqarin Kaurace min byn Kinsan bani da kowa bani komai sai ku ? Kafin maryama tayi yunkurin cewa wani abu aunty ta sake jiho mata wata tmbyr "yanzu na cancaci haka a wajenki ,"?"Na lura kina bukatar rayuwata princess "idan kika bari damuwarki ta kasheni shikenan sau ki huta ai .... " a d'an zabure maryama ta mike zaune daga kwance da take suna fuskatar juna da aunty yayinda hawayen idanunta suka shiga xubowa sharrrrrrrrr....." " meye kuma abun kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba. cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?" Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ." "Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali . Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ." ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ." Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ". Mmm sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 15 "Aisha , saber, da mahamud , ta gani tsaye akansu suna huci kamar zakuna cikin matsanamcin tashin hankali mara misaltuwa suna kallonta kamar zasu cinyeta ai babu shiri daga bilkisu har ussein suka mike daga jikin juna hankalinsu yayi mugu mugun tashi ." bilkisu ta tsaya tana kalle kallen inda zata boye acikin d'akin tare da cure hannayenta waje d'aya jikinta na sake d'aukar rawa bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin na ranar ba domin har ga Allah bata ta'ba tunanin zasu bibiyi takunta ba ." Nan da nan idanunta ya kawo ruwan hawaye ba tace komai ba, ta durkusa qasa bisa gwiwo winta dan tasan sai na lahira ya fita jin dadi mahamud ya rike kungunsa yana cigaba da kallonta ,mamakinta kawai yake dawainiya dashi idan aka fad'a masa cewar zata biyo nmj har d'akinsa bazai ta'ba yarda ba, watakilla ma da sai ya wankawa wanda ya fad'a masa hakan mari "dan girman Allah kuyi hakuri ku yafe min ku rufa min asiri kar mumy tasani ta karashe mgnr tana kuka cikin tashin hankali mahamud ya buga mata wata razananniyar tsawa data hargitsa mata lissafi "yi min shiru makira bana son jin komai daga bakinki ." nan take tayi shiru kukanta ya qaru ta kalli inda ussein yake tsaye shima kana kallonsa kasan baya cikin natsuwarsa "mahamud tsayawa kayi kallonta bazaka fara cin ubanta tun anan ba ? Aisha ta fad'a tana mata wani irin kallo shi kuwa wanda aka kira da mahamud tunanin yake idan yace zai ta'bata to babu shakka zata mutu idan kuwa bata mutu ba zata jikata ." "dan girman allah Aunty ai.."ai bata kai ga fad'ar abinda take son fad'a ba taji wani gigitaccen mari hagu da dama akan kuncinta "you are very stupid bilkisu , akanki aka fara soyayya?" kin haukace kin makance akan wannan banzar ,me yasa zaki mance ko ke wacece ? wato soyayya tasa kin manta matsayinki ? cikin muryar kuka tace " a'a Aunty aisha ban mance ba amman kuyi hakuri wallahi bazan sake ba "hayaniyar yan yan'uwanta ya sake d'aga mata hankali shi kuwa ussein sunkuyar da kanshi. kasa yayi yana tunanin ficewa ya bar d'akin dan yasan Allah ne kawai zai kwacesa a hannunsu ." Kai tsaye bilkisu ta nufi bayan kofa ta boye jikinta na wani irin rawa sakamakon jiyo muryar hajiya rahma tana cewa "ina bilkisu take naga kun tsaya jugun jugun ko ta gudu ne ? kafin kace me an samu wanda yazo ya fad'a mana halin da'ake ciki a guje na bazamo na bar hajiya dan bazan iya jiranta ba kasancewar tana fama da lalurar ciwon kafa ." " ina tafiya ina neman layin yan' uwansashi da kyar na samu ta abban sadam yana gama jin bayanina cewa yayi babu ruwansa dan yasan halinsa da tara yammata , babu yadda banyi dashi ba yace bai zuwa koina ya kashe wayarsa jin abinda ya fad'a yasa na kira yayyensa mata ." Ina shiga unguwar naga jamaa sun yi cirko cirko!! ga manya manyan motoci na gidansu bilkisu jere a kofar gidan ,haka ina shiga cikin gidan mutane na gani makil kowa na fadar albarkaci bakinsa ,yayinda muryar mahaifiyarta ya karad'e koina acikin gidan "da gaske ne bilkisu tana cikin wannna ru'babben d'akin ? Aisha ta nuna mata bayan kofar d'akin "tana ciki kuwa ga makira nan a bayan kofa ta fad'a tana zubar da hawayen takaici ." "inna lillahi ! hjy rahma ta furta a fili cikin tsananin tashin hankali "kunji abinda naji kuwa wallahi ji nayi zuciyata kamar ta buga ?hankalin bilkisu ya bar duniyar da muke alokacin dan sai wuri wuri da idanu take shi kansa ussein kana kallonsa kasan nadama ne acikin ransa nadama irin wacce bata da wani rana ." " amman bilkisu bakince min kin rabu dashi ba ?jikinta na rawa ta shiga gyada mata kai alamun Eh! tana bawa mahaifiyarta hakuri da wani irin fushi ta juya inda ussein yake cike da nadama ta shiga zabzabga masa mari ta koina "bana ce maka ka rabu mun da yarinya ba ? ba banace karka sake shiga rayuwarta ba?"Ko kaga yarinyata tayi kalar wacce zaka ce kana so ? ta juya zuwa ga bilkisu " Ke yanzu har wannan qazamin ne abun so a wajenki ? ta fad'a tana sake juyowa ta d'aga hannu zata sake tsinkawa ussein mari nayi saurin rike mata hannu ina bata hakuri "kiyi hakuri hjy sam ussein bai kyauta ba daya bawa yarinyarki damar zuwa inda yake ,ya karbi laifinsa ayi masa afuwa in sha allahu hakan bazai sake faruwa ba Kinsan kowa da irin jarabawarsa dukkanin rayuwa rubutaccen lamari ne daga Allah ,kuma kowani dan Adam yasan da haka ,yanzu tunda abun ya zama haka ku bamu dama sai mu turo ayi maganar aure "." Wani irin kallo gabadayansu suka bini dashi ,hjy rahma tace "Allah ya tsareni na had'a zuria da wannan ta nuna ussein da yatsanta tana hararsa "wallahi bilkisuna tafi karfen aurensa ki kalleta sama da qasa ki kallesa ta ina hadin yayi daidai ? duk nasan da haka hjy amman a wajenta shine daidai bugu da qari rayuwar yarinyar ku zaku duba domin ita diya mace ce zata iya fad'awa kowani hali ." "Ba kowani hali zata fad'a ba ko mutuwa zatai sai dai ta mutu na yarda na rasata gbdy akan na bawa wannan matsiyacin aurenta ta numfasa tare da sa tafin hannunta ta share hawayen idanunta "hjy ki daina furta haka shi soyayya allah ne yake had'awa , kuma babu ruwan soyayya da tsiya ko arziki yarinyar nan tana qaunarsa shima kuma yana sonta dan girman allah ki barsu suyi aurensu kowa ya huta sannna babu wanda yasan matsiyaci ko mai arziki sai Allah sannan babu wanda yasan mai gobe zata haifar ku barsu su aure juna domin samun kwanciyar hankali ." bata kulani ba har na dasa aya ta fuskanci bilkisu yayinda gabadaya yanuwanta kacokan suka maida hankalinsu Kan ussein duk sun qagu suga hukunci mahamud akan ussein kasancewarsa soja , hjy rahma ta matso sosai kusa da bilkisu tana cewa "ba dai ni zaki wulakanta akan namiji ba ? ."babu irin rarrashin da ban miki ba ,babu irin hakurin da ban baki ba ,me kike son dani ? "wallahi zanyi dake bilkisu , yau zaki ga tozarci ganin idanunki tunda kika nemi ki wulakantani akan wani banza can wanda ba kowan kowa bane shi ,ba kowa bane iyayensa a duk fadin garin nan hasalima rayuwarsa a banza take ." "zaki wulakantani akan wani nmj banza da wofi wallahi zanyi dake muddin kika ce shi zaki aura sai na tsine miki na tsinewa auren ,wallahi auren bazai ta'ba yin albarka tana mgn tana zabga mata mari a fuskarta da bayan hannunta , yayinda azaba tasa bilkisu ta shiga karewa dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe kafa mata hakori a damtsen hannunta." "wani irin gigitaccen qara bilkisu ta saki mai ban tausayi tana kuka tana neman d'auki gashi babu wanda ya kwaceta daga hannun mahaifiyarta sai dukanta take tana hadawa da zagi ganin haka yasa ussein ya nufi hjy rahma cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun kad'a sunyi jajur yasa duka hannunsa zai d'agata daga Kan bilkisu ai ganin ya ta'ba mahaifiyarsu gbdy yan'uwanta suka yo Kanshi shi da bilkisu cike da jin haushi suka dinga dukan su kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi ba kawai ceton bilkisu zai yi daga dukanta, ina kuka ina basu hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa shi kad'ai har sanda hjy ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu daku dan wallahil azim bazan ta'ba yarda ba ". "kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ? "nice uwarsa kuma gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ? "ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada "hjy na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ." "neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" . "ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ." Mahamud kuwa qarasawa yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ." bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai sausauci suke neman masa amman mutanen nan suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani ." wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye tare da matsowa inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali," ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi? Eh ! yana da kyau sai dai bani da wannan lokacin 'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa " Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da suka mata nauyi wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ." fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba yana zaman zamansa muguwa azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah matukar ussein..." saurin toshe mata baki nayi ina cewa fatima karki rantse ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..." na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan sulhu ake nema ." Cikin ko in kula hjy rahma tace da wa zakuyi sulhu ?"kema Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar me kukeyi ku taho min dashi da sauri gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da ussein ." Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ". " tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ". Bangaren su bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba" mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ." a matukar gigice bilkisu tabi byn motar da kallo cikin tsananin firgici, keyarta suka tasa sai cikin bangaren hjy rahma ."Suna shiga part din hjy rahma suka turata daki suka daureta da igiya tamau sukasa saber ya dinga dukanta adaure tun tana ihu har tazo ta kasa a yadda ta fad'a min cewa tayi har da barkono mahaifiyarta ta nika tasa mata a gabanta da cikin idanunta wanda yasa tayi suman wuncin gadi ." Bangaren mu rana babu wanda ya samu sukuni acikinmu gali yafi kowa shiga damuwa safa da marwa yake yana cewa "ban ta'ba kawowa araina duk hakurin dana basu ba zasu hakura ba , na dauka maganata zai sa su hakura amman ina kamar sake fusata mahaifiyarta nayi wadan nan mutane sam basu da imani ."wallahi basu da imani gali inji cewar hjy ka kalli irin duka da sukayi yarinyar nan bilkisu ko rikonta suke bai dace suyi mata irin wannan dukan ba ." "wallahi ku sheida bilkisu bazata sha wannan wahalar a banza ba komai zai faru sai useein ya aureta ba dai bakinciki su kenan ba saboda suna takama da kudi ,ni bana da kudi amman ina da Allah alfarma annabi da alqurni sai wannan auren ya tabbata ko ina raye ko byn na mutu mutane sam babu imani aransu bazai hakura da aurenta ba sai dai su mutu fatima zatayi magana ta dakatar daita "banason jin komai daga bakinku sai fatan wannan auren ya tabbata ." abban sadam ya fito daga bayi daman zagayawa yayi yace "har yanzu bazaku hakura da wannan maganar ba ? hjy tace "taya zaa hakura?" da sukutun fa suka wuce min dashi ?naga diyarsu ce tunda sunce basaso tarayyarsu a hakura mana "bazaa hakura ba bilkisu bazata sha wahala akan ussein ya tafi a banza ba ina sonta tunda tana son jinina ta gama min komai ni yanzu ta'bo min abokika Abdul zanyi magana dashi babu irin kiran da baayiwa Abdul ba amman wayar bata shiga ranar hjy bata runtsa ba kwana tayi tana kaiwa allah kukanta ." Washegari ana idar da sallahr asuba tasa aka cigaba da trying dinsa amman shiru baya shiga sai karfe uku na rana ta shiga ya dauka da sallama byn sun gaisa hjy tace "Abdul ko kasamu labarin abinda Ke faruwa da useein ?bansan me yake cewa hjy ba amman naji tace "meye rashin kyautarwasa haramun ne dan soyayya tashiga tsakaninsu ?saboda shi talaka ne yasa basu dace ba to shikenan nan in sha allahu gamu nan zuwa ." Tana gama waya tace muje gidansu bilkisu mu samu mahaifinta nace" a'a ta bari ni da gali da fatima muje da kyar hjy ta yarda ta barmu muje babu ita sai dai fatima tace bata zuwa koina nace saboda me kai tsaye tace min ta tsani bilkisu da yan gidansu sai da saadatu da gali mukaje da taimakon Abdul muka shiga estate dinsu sai dai baa bari mun shiga cikin gidansu ba a bakin get din gidan aka tsaidamu yayanta abubakar muka samu gani muka gaisa dashi babu laifi fuskarsa da dan rahma dan yafi mahaifiyarsa byn mun gaisa gali ya fad'a masa ko mu su waye da dalilin zuwanmu "ayi hakuri ranka ya dade ,hakika danuwanmu bai kyauta maku ba domin ya shiga hurumin da banashi ba soyayya da diya irin taku shima yasan bai dace ba , dan allah kasa baki ranka ya dade abamu ussein tun jiya da suka wuce dashi baa dawo dashi ba ,dan allah a maido mana dashi ." shiru yayi ya kasa cewa komai ganin hk yasa gbdy muka kwantar da murya "ka taimaka kasa a sako mana ussein cikin ko in kula yace kuje zai dawo gida zuwa anjima amman kuja masa kunne ya fita a rayuwar bilkisu "in sha allahu komai yazo karshe cike da farinciki muka juya zuwa gida zaman jiran dawowar ussein ."bini bini sai mu leka waje ko zamu hangosa amman shiru har kusan karfe shadaya na dare har mun fidda rai dashi sai gashi an shigo mana dashi bangaren hjy yana dingisa kafa da kyar ." da sauri muka taresa dan gbdy muna tare har hassana wacce tafi kowa shan kuka hjy kam cikin yanayi na tashin hankali ta isa garesa tana kuka "yanzu haka suka maka ussein ,kawai dan kana soyayya da diyarsu allah ya saka maka ,allah ya bi maka hakinka alfarma annabi muhammadu sai bilkisu ta zama mallakinka "wai meye hk hjy ana kokarin ya rabu da yarinyar mutane ya huta da wahala amman kina sake dagula masa lisaafi . Gali ya fad'a yana kallon ussein " kai ka rabu musu da yarinya idan ba haka ba wallahi komai ya sake faruwa babu ruwanmu ,babu hannu babu kafarmu sai dai ka karata kai kadai dan bazamu iya wahala ba wadan nan mutanen marasa mutunci ne "wannan gsky ne gali babu ruwanmu dan bazamu iya dasu ba inji cewar saadatu ,to ku yanzu laifinsa kuke gani bakwa ganin na yarinyar ?ai yarinyar tafi shi laifi domin ita Ke zuwa inda yake wallahi na tsani yarinyar nan ." "koni wallahi na tsaneta maryama wannan shima mafarin tsanar yanuwan mahaifinki ga mahaifiyarki alokacin ina kallon ussein wani irin numfashi mai zafi ya fesar kana ya samu waje ya zauna da kyar ya daura kanshi akan hannun kujera ya kwantar tare da lumshe idanun shi yana jin duk abinda kowa yake fad'a daya byn daya bayan wasu mintuna ya kuma budewa yana kallon kowa cikin sanyayyar murya yace "in sha allahu na rabu daita har abada dan kwana ne kawai a gaba da na mutu "ka kwantar da hankalinka muddin ina raye baka da mata sai bilkisu ka daina cewa ka rabu daita dan na nasan kana sonta har yanzu ." "haba hjy wai me yasa kike fadar haka Kmr baki tausaya masa ? "yanzu ku yarinyar nan bata baku tausayi ?ita ma ba laifinta bane soyayya ce da qaddara ke tangaliliya da rayuwarta dacen iyaye ne batayi ba shiyasa take shan wahala amman itama abar a tausaya mata ce "gsky mu dai bamu yarda ba kuma ta ina zasu bada aurenta byn kina kallon haukan da suke akanta ? kusa ido kuga ikon allah muna zaune zasu nemo mu da maganarta da izinin allah "babu wanda yace uffan kowa ya mike ya kama gabansa ." **** Bayan wata biyu da faruwar komai mahaifiyarta ta shiga neman taimako akan bilkisu dan kawai ta rabu da ussein , yau akarbo taimako daga wannan malamin gobe akarbo daga wancan malami , akwai inda aka kaita sai data d'auki alqurni ta rantse akan zata rabu da ussein , hankalinta ya tashi matuka taki amsa ta firgita kwarai da lamarin mahaifiyarta ." fito da duka idanunta tayi tana furta tashi uku bataso ba amman mahaifiyarta na kallo mutumin yasa ta dauki alqurni tayi rantsuwa ta rabu da ussein har abada alhalin ita a zuciyarta ba haka bane " babu laifi bilkisu ta zauna lafiya kamar sauran lokutan baya ta cigaba da rayuwarta gudun kar qurani ya cita ,yanuwanta suka dan sake mata kadan haka mahaifiyarta tun tana gudun abinda zai je ya dawo har ta hakura ta sake janyota jikinta kullum da irin nasihar da take mata "bilkisu ki zama mutuniyar kirki ba wai baa sonki bane yasa kika ga anayi miki duk abinda aka miki ana sonki ne yasa ake gudar miki wahala ,auren wannan yaron wahala zai zame miki arayuwarki , bakya ganin sauran yanuwanki ?kowa na cikin jin dadi me yasa sai ke kadai ce zaki zabar wa kanki wahala? " tace "kiyi hakuri mumy ina tsananin son ussein amman zanyi iya kokarin na cire sonshi araina "ko kunyi imole ne ?hjy rahma ta tmbyeta ."tayi shiru tana kallonta" baku ta'ba shan jinin juna ba ?ta girgiza mata kai alamun a'a to ko ya ta'ba kwanciya dake ne ina nufin sex ?shiru tayi kawai ta kasa bata amsa tmbyrta "idan ya ta'ba kwanciya dake ne ki fad'a min nan ma shiru tayi kawai "karki manta Kiyi rantsuwa da alqurni akan zaki rabu dashi ta gyada mata kai "idan baki son mubarak naji na hakura amman ki kawo min wani banda wannan yaron dan banason shi daga nan ta zarce da nasiha na kwantar da hankali tana nuna mata rabuwa da ussein shine alkhairi arayuwarta wanda alokacin mgnrta na shiga ta kunne na hagunta ne yana bin ta dama ." wannan sakewar yasa ta samu damar turawa ussein sako da duk wayar data shigo hannunta byn ta tura text sai ta goge haka haka dai har ta shirya barin gidan da yammacin ranar laraba ta fice daga gidan babu wanda ya sani sai lalubo wa sukayi bata gidan" abun bakinciki tana zuwa gidan nan da hassana ta soma cin karo lokacin ta dawo gida aurenta ya mutu "Ke tsaya ta daka mata tsawa me ya kawoki gidan matsiyata ?tace dan Allah Kiyi hakuri nazo neman ussein ne "ussein din kanin ubanki ne da kikazo nemansa ? yanzu har kin manta irin azabar daaka gana masa akanki ?" "na sani amman Kiyi hakuri ta marairaice mata ta raba ta gefenta zata shigo tace "kina hauka ne ta kara buga mata tsawa wallahi kika shiga gidan nan da kaina zan fito dake na miki dukan mutuwa kuma bazan bari kiga ussein din ba har sai na danganaki da matsiyatan iyayenki masu kiran wasu matsiyata alhalin sune matsiyata , dan masu arziki basa yin abinda sukayi duk yadda akayi arzikin ma daga sama aka samu zaazo a ishe mutune "pata pata tayi mata batare da sanin hjy ba sannan ta korarta ." bangaren hjy rahma taji shiru shiru bilkisu bata fito ba ta nufi dakinta sai dai wayam tagani babu kowa ta duba bayi nan ma still the same nan da nan duk ta rude sai zufa take fitarwa nan fa ta soma kiran yaranta tana tsaye sai ga aisha da mijinta haka ma sajida cikin tashin hankali aka kira abubakar da mahamud har sulaiman har khadija jugun jugun sukai kafin daga bisani suka fito zuwa nemanta har 12 :00 na dare ba labarinta babansu yace kowa ya tafi kawai makwancinsa har zuwa gobe aga abinda allah zai yi ." daga gidan nan bilkisu ta rasa inda zata domin dai tasan idan ta koma gida azaba zata sha duk yadda zata fad'a cewar bata hadu da ussein ba bazasu yarda ba dan haka ta wuce gidan kawarta farida daman su basa tare da mahaifiyarsu , mahaifinsu ne kuma bai cika zaman gida ba kasancewarsa jamin tsaro in takaice miki kwana da kwanaki ana neman bilkisu baa ganta ba yayinda ussein yake gida abunsa idan kinga ya fita to zashi area ne kuma bini bini ya dawo gida ". muna zaune aka zo nemanta basu ganta ba suka wuce intakaice miki kullum sai sun shigo unguwr nan sai dai basa ganinta sai dai su ganshi shi kadai duk inda suka je nemanta bataje ba duk ahalinta sun rude mazan kuwa sun bazu nemanta abu kamar wasa har sati baa ganta ba abubakar ya kai report police station duk hankalinsu ya tashi haka zalika ussein shima bai zauna ba duk inda yasan zataje yaje bai ganta ba kullum wayarsa tana hannunsa km a kunne koda zata nemesa duk ya rude ya rasa inda zai sa kansa ." kowa a gidansu bilkisu kuka yake daga bangaren yan dakinsu har sauran bangarorin dan kansu a hade yake kuma suna qaunar juna ,duk sun rikice sun baza cigiyarta koina kafofin sadarwa amman babu wanda yace ya ganta dan haka suka sa akayi arresting din ussein a tunaninsu ya boyeta sati daya yana tsare ana gana masa azaba har a underground aka saka shi , ranar daya cika sati biyu akabari muka gansa ,koda aka zube magana sune basu da gsky amman kudi yasa aka bamu rashin gsky muka dauka muna bada hakuri akazo dashi unguwar nan sarka hannu da kafa Kmr wani barawo aka bincika gidanmu daki daki lungu lungu baa ganta ba haka dakunan abokansa da dakinsa duk inda aka san yana zuwa sai da akaje dashi amman baa ganta ba aka sake dawo dashi station dokoki aka kafa mana . daya daga cikin police tace tasan koina bilkisu take zata nemeshi dan haka da zarar ta kirasa ya tabbatar sun hadu ya kawota a haka aka bar maganar muka dawo gida wanda tsanar bilkisu ya sake girma a zukanta yan'uwansa hatta gali alokacin ya fadi maganganu marasa dadi akanta wanda shine har yau baya qaunrku da mahaifiyarku amman ita hjy tana sonta dan tayi kuka rashin ganinta da baayi ba ." Kullum hjy tana cikin zullumi da addauar allah ya bayyana bilkisu wallahi hjy tana matukar qaunar bilkisu sam bata ganin laifinta komai zaa fad'a akanta bata gani , cikin ikon allah sai gashi ta nemi useein da number farida ya tmbyrta inda take ta fad'a masa bai bata lokaci ba ya nufi inda take yana isa sai da yayi mata mari masu kyau har biyu cikin tashin hankali yaja hannunta daga can gidan nan ya zarceto daita muna zaune sai gashi ya shigo daita ." hjy duk tafi kowa jin dadi ta rungumeta ajikinta tana kuka mikewa tayi tace muje police station Muna fitowa ta nemi limamin masalacin unguwar nan tai masa bayanin komai shima kuma ya fahimci akwai matsala duba da yawon zuwan da yanuwanta suke muna isa aka kira yan'uwanta ai a haukace suka shigo sabeer yayi kan ussein "kace bakasan inda take ba ? sukayar da kansa yayi dan rasa me zaice ." liman da police suka tsaidasu suna kwantar masu da hankali amman suka kasa aiwatar da hakan suka rufeshi da duka hjy ta shiga tsakaninsu tana karesa tana kiran sai dai ku hada dani allah ya isa bata yafe ba ,ita kuwa bilkisu kuka take sosai tana fad'a masu bashi da laifi hasalima tunda ta bar gida bata hadu dashi ba sai yau cikin fushi aisha tace "ya lalata miki ingantacciyar rayuwar da iyayenmu suka baki ya maidake yar yawo kororo "yayi miki ciki nasa aka cire miki amman duk ba laifi bane ? "ko dan kinga an rufa miki asiri sai lokacin hjy rahma tasan da wannan maganar wanda hakan ya sake tunzurata da kyar dai da nasiha suka amshi diyarsu nasiha sosai liman yayi masu yace su jajurce da addua sannan muka wuce da ussein ." "ai ranar ashe ruwan zafin uwar ta tafasa ta kwarawa bilkisu a gabanta wanda yasa sai data suma a qalla sai da tayi kwana ta yini bata cikin haiyacinta sosai mahaifinta ya nuna bacin ransa akan abinda aka mata ,sai da tayi sati biyu tana jinya sannan ta dawo daidai mahaifinta abun yafi karfinsa addua kawai yake allah yaye mata wannan masifa data daurawa kanta , amman uwar izaya da maseefa kawai tasa gaba ." "yadda ake mata azaba haka zuciyarta take sake tunzura , dan zuciyarta da idanunta sun bushe basa ji kuma basa gani ,ta manta matsayinta babu ruwanta da kowa acikin gidansu ko ince miki ta tsani kowa km har lokacin bata cire ussein aranta ba duk lokacin datayi raayin ganinsa kawai fitowa take taje su hadu ta koma gida randa dare yayi mata kuma ta kwana a wajensa shima dai mutane suna cewa baya jin mgn wanda ni nasan so ne da tausayin bilkisu ke hanashi juya mata baya ." Kwatsam sai ga bilkisu da wani cikin wata biyu cikin na uku ta fahimci ciki gareta alokacin shekararta shakwas cikin ta shatara hankalinsu ya tashi suka zo min da maganar ranar har da kuka nayi dan bakinciki nayi kuka kamar me cikin kuka tace zasu zubar nace a'a ta haifa sai ta bani tunda ni tun haihuwar sadam ban sake samun wani cikin ba shima sadam din da kyar na samesa kuka take tana cewa na taimaketa a zubar da cikin naki yarda ranar tana komawa gida akasa sabeer yayi mata dukan fitar da tayi wanda yayi sanadiyyar fitar cikin alokacin na bawa ussein shawarar ya tura neman aurenta, hakan ta kasance abban sadam da kanin hjy suka je sai akace masu makaranta zatayi ba yanzu zaa aurar daita ba suka dawo suka fadawa ussein ya sameni da mgnr nace kar ya hakura ya sake turawa haka dai byn wani lokaci suka sake zuwa sai mahaifinta yace zai yi mgn da yan'uwansa duk abinda ake ciki zasuji daya samesu suka ce basu yarda ba daman shima bawai yana son aurenta da ussein din bane ." Bayan sun koma akaro na uku ya turasu wajen yan'uwansa nan suka iske wani sabon tashin hankali domin cewa sukayi muddin yana son aurenta a wannan lokacin zai biya duk abinda aka kashe mata tun daga primary har secondary idan sun amince bisimillah ga list nan aka mika masu duk wani abu da suka kashe akanta jiki a sanyaye suka dawo suka miko min a tsorace na gama karantawa domin ko gidan nan da gidan bread muka saka a kasuwa bazai kai kudin da suka rubuta ba abban sadam ya numfasa yace "ki fadawa ussein ya hakura da yarinyar nan mutanen nan basu da mutunci km ko ya auri yarinyar nan wahala zai sha dan tafi karfin aurensa ni kaina na yarda da hakan kawai dai ayi auren ne dan kar suyita saduwa da juna suna ciki shima ussein koda ya samu labari yace ya hakura dan ina yaga million ashirin da biyar ."? Haka dai suka cigaba da rayuwa duk sanda ta fita idan ta koma sai anyi mata duka tare da zagin tana warin maz gbdy kamanita ya canza ta fita haiyacinta tayi firi firi ta zuke ta rame babbar yayarsu a gabdaya gidan wacce uwar gidan rafi'u giwa ta haifa hjy rabi ta samu yanuwan babansu har ma da baban akan abar bilkisu hakan nan kar rabo yaje ya kashe mutane gabadaya yanuwan mahaifinsu suka ki yarda kuka ta saka masu ta zayyane masu abubuwan da basu sani ba akan bilkisu da ussein tunda sukaji ussein har ciki ya ta'ba mata suka zubar da makamansu , suka ce tunda taji ta gani abarta ta auresa tunda basu zasu zauna mata dashi ba shi dai mahaifinta bai uffan ba ." tun daga wannan lokacin da yan'uwanta da suke daki daya da mahaifiyarta suka ji hukuncin daaka yanke akan bilkisu suka shiga gana mata azaba iri iri batare da sanin kowa ba aka dawo rikonta tamkar yar aikin gidansu yadda zakiga yan aikin gidansu na yawo haka ta dawo tana yawo babu shiga mai kyau babu komai amman hakan bai sa qaunar mahaifinku ta ragu acikin zuciyarta ba ." aka saka ranar sati biyu kacal ana sauran sati daurin aure hjy rahma da ya'yanta kaf suka saka bilkisu a tsakiyarsu "duk ranar datasa kafa ta bar gidan zuwa gidan ussein amatsayin matarsa tasan cewar ta fita kenan har abada karta dawo gidan garesu ta nemi wani gidan ,ta nemi wata uwar ta nemi wani uban ,ta nemi wasu yanuwan ,fasa auren daidai yake da bin umarninsu ,amman zuciyar bilkisu bata girgiza ba ta cigaba da shirin aurenta dan Allaha allah take ta bar gidan ta huta acikin satin muka kai dan abinda muka hada na lefe wanda kusan hjy ce tayi komai wallahi in takaice miki maryama wulakanci har da wankan ruwan sanyi akayi mana byn an watsa mana abinda muka mai ." Ranar daurin aure babu mutun daya daya zo daga cikin ahlinta da wanda suke uwa daya uba daya da wadan da suke yan uba haka zalika mahaifinta bai je ba dan hjy rahma tace muddin yaje ita kuma zata bar masa gidansa kannen mahaifinta mutun uku ne suka je alhj saidu ,Alhaji umar ,Alhaji kaberu ana gama daurin aure aka nemesu aka rasa ,bayan an daura auren hjy rahma ta kira bilkisu ta tsinewa aure babu irin mummunar adduar da bayi ba, allah ya hadata da damuwa allah yasa ussein ya gallaza mata ya korota ,kar allah ya bata haihuwa dashi idan km ta haihu allah ya bata ya'yan da zasu dameta, idan basu dameta ba allah yasa suyi ta mutuwa a duk sanda ta haifesu , bilkisu tayita kuka tana jin Kmr ba hjy rahma bace ta haifeta dan lokacin da take fad'a min cewa tayi ita da uwarta har abada ta yafeta sai dai na fada mata baa yafe iyaye komai abinda suka aikata gareka." lokacin da zaa kawo bilkisu gidan mahaifinku babu wanda ya rakota saboda ta auri talaka daga ita sai mahaifinku suka baro gidansu zuwa rubabben dakinsa inji cewar hjy rahma dan wulakancin da sukai mana yasa babu wanda je dauko amarya . babu abinda iyayenta sukai mata na kayan dakin kuma har yau yan'uwanta na jini babu wanda yasan inda take sun dai san tana zaune acikin lagos din nan amman a ina take basu sani ba babu wanda ya ta'ba zuwa ." Kusan bakin hjy rahma yayi tasiri akan bilkisu dan sai datayi shekara uku tare da ussein batare da tasamu ciki ba har aka auro salma bata samu ciki ba ussein bai bawa mara d'a kunya ba dan sosai ya dawo da shaye shayensa lokacin data masa mgn akan alkwarin da yayi mata na dainawa yace" yaushe sukayi haka ?sai byn da salma ta haifi ali sannan kwatsam sai ga ciki bilkisu ta samu har lokacin da tayi haihuwar fari tace abarta a gidan mijinta ni nasan da wani mai arziki ta aura ko bata je ba dole zaazo a dauketa ,babu wanda yazo dan lokacin mahaifinku da kanshi yaje ya sheida masu ta haihu intakaice miki korar kare aka masa wai yazo rokon kudi shiyasa duk lokacin da mahaifinku ya bata mata rai sai dai ni naji mata haushi ita kuma tayi kuka ta hakura dan bata san inda zata dosa ba mutane gidan nan gbdy sun daukenta sha sha wai ta tare a gindin miji to idan tace ma ta gaji ina zata ? yau da'ace tayi saar uwa da tun tuni ta koma gareta domin tana neman taimakonta amman no way domin zamanta a gidan ussein shine gatanta kinga ta rasa gatanta shiyasa a kullum take ganin bata da gatan daya wuce ussein daku yayanta komai yayi mata take hakuri wanda kusan hakan yake cikin dalilin da yasa salma da hassana suke cin kashi akanta ta sha wahala sosai acikin yanuwan ussein bayan an haifi habib rashin Lfy ya kama hjy haka ta dauko hannun bilkisu tasa a tafin hannuna tace na rike mata amanar bilkisu kar na bari tayi kuka idan ussein yasata kuka na tabbatar na wanke mata zuciya sannan ta qara da cewa byn ta mutu bilkisu ta dawo bangarenta ta cigaba da rayuwa acikisa nace ta tara yayanta ta fad'a agabansu hakan kuwa akayi abun bai masu dadi ba amman haka suka yi hakuri kwana uku tsakani tace ga garinku ." Bilkisu tayi kuka kamar zata bita domin a gasky ita akayiwa mutuwa dan kusan nauyinta akan hjy yake itace komai nata bare Ke da kika ci sunan mahaifiyarta komai tasamu kece da bilkisu ne shekarar hajiya daya da rasuwa rashin lafiya ya kama mahaifinki koda aka dubashi ciwon sigari ne ya kamashi har yayi masa illa bilkisu bata gujesa ba itace komai nashi ,ita Ke kaisa asibiti gwanati ga ciwonsa na bukatar kudi amman babu ke babu irin wahalar da batayi ba har wankau tayi dan ta rufawa kanta asiri cikin wannan halin rashin lafiya aka samu cikin habib har aka haifesa mahaifinku bashi da lafiya ranar da habib ya cika shekara daya a duniya Allah ya dauki ran mahaifinku ,yanzu shekaru ashirin da uku kenan rabonta da yan'uwanta da iyayenta kuma har zuwa wannan lokacin babu mutun daya daya nemi inda take to me zai sa ku ku damu da inda suke ? Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 19 A matukar zuciye ya sauke duka hannuwansa yana huci sai dai har lokacin kwayar idanunshi na kan fuskar baban gali yana masa wani irin mugun kallo mai tattare da bakinciki lokaci d'aya kuma yana ta qoqarin danne fushinsa dan baya son 'bacin ran mahaifiyarsa ." baba gali ya sakar masa murmushin mugunta sannan ya kalli aunty hassana da aunty salma "kuga wannan tantirin mara mutuncin yaron wai ni zai kai hannunsa jikinata saboda nace zasu bar gidan nan kamar da kudin ubansa ko da kudin uwarsa aka gina gidan nan da zai wani d'aga hankalinsa dan Allah ku kalli Irin kallon da yake min nasan yana jin kamar ya kasheni ne ."ya qarasa maganar yana dariya ," Murmushin jin dadi aunty hassana tayi itama "ai kuwa bai isa ya kasheka ba sai dai ya kashe uwarsa ko yaje ya kashe wad'an can marasa mutuncin dangin uwarsa ba amman mu nan munfi karfin d'an kutumar uba, shegen gora mai falla fallan kunnawa , an nace mana an zo an haifa mana irin jaraba kuma wallahi sai Kun bar gidan nan matsawar bazaku daina mana rashin mutunci ba ." cike da raunin zuciya habib yace "mahaukatan banza kawai da basu san ciwon kansu ba " "mu kake cewa mahaukata ?eh !lallai yaron nan wuyanka ya isa yanka ,amman ka sani bamu ne mahaukata ba ga mahaukaciya nan a gabanka kana kallo wannan wannan itace mental itace mahaukaciya da ka kiramu dashi aunty hassana ta fad'a tana nuna gefen kanta ." "Hassana !" ya kira sunanta a matukar hassale Aunty hassana tayi saurin zaro idanuwanta waje tana duban d'anuwanta cike da mamakin habib "yes abinda kunnuwanki suka ji na fad'a kenan dan haka ki ma daina mamaki zan ma iya fad'ar abinda yafi haka " mutun takin me zan tsaya yi tunda kin kasa mutunta kanki ?" ta maida hankalinta da idanunta kanshi sosai tana nazarin mgrsa sa sai daya samawar jikinsa natsuwa sannan ya cigaba da zaro magana "Ki kalli aunty tsab ki gani Kinsan dasu wa maganata ta dace ,ku din dai kune mahaukata kuma bazan ta'ba sauya maganata ba." Hawaye ne yake zubowa daga idanun aunty gashi magana take son yi dan ta basu hakuri sannan ta tsawatarwa habib amman ta qasa bud'e bakinta bare ta sarrafa harshenta a wannan lokacin ita kanta taga ya dace ta koma cikin 'yanuwa cikin asalin ta amman kuma idan ta tuna irin rayuwar datayi har ta kawo wannan matsayin sai taga komawar nata bashi da wata amfani me zata cewa alhj rafi'u giwa da mahaifiyarta wacce tafi kowa d'aukar zafi akan kowa wacce ta gindaya mata sharadin cewar ta manta daita ta manta da kowa nata tunda ta zabi auren ussein ?". "gidan nan kowa yasan gidan kakanmu ne wanda ya haifi mahaifinmu yadda kuke taqamar kuna da iko akan gidan nan haka muma ya'yan ussein muke da iko da gidan nan matsawar zamu zauna acikin gidan nan dan dole mahaifiyarmu ta zauna acikinsa ." " Ke ! hassana da kike cewa a dole mu bar gidan nan kisani bamu ya kamata mu bar gidan nan ba ke da ya'yanki yafi dace wa ku bar gidan nan dan da gidan miji mace take taqama ba da gidan uba ba , aunty a gidan mijinta take zaune Ke fa ? da har yanzu Ke da ya'yanki baku san garin ubansu ba bare su san dangin ubansu ,ki fara zuwa ki kai ya'yanki su san dangin ubansu tukun kizo ki kori wad'an da su muhalinsu suke ." Cike da sanyin jiki maryama ta dinga jan gwiwowinta har ta qarasa gabansu aunty hassana jikinta na wani irin rawa Kafin tai kai ga yin mgn taji aunty hassana ta hau surfa mata maseefa "dan ubanki yau dai karki kuskura ki bamu hakuri , shegiya yarinyar munafukar Allah taala kin wani marairaice fuska kamar ta kirki zaki bawa mutane hakurin gulma wallahi yau shine zamanku na karshe acikin gidan nan sai kun bar mana gidanmu ,gara ma tunda wuri Ki san yadda zaki d'auke wnn uwar taki da wannan shegen kannin naki mai falla fallan kunnuwa Kmr na fir'una ku bar mana gidanmu mu huta da jaraba sanda ussein yana raye bai barmu mun huta ba sannan bai tsinana mana komai ba sai ruwan shaye shaye da d'auko mana magana wanda sanadiyyar haka ya kwaso mana wannan munafukar uwar taku gashi ya mutu ya barmu da mugun iri ." "Kuka maryama ta fashe dashi hade da sake durkusawa a wajen batare da tasan abinda zata fada ba, tana mai bakincikin irin kalar rayuwar da mahaifinta yayi a sanda yake raye, gashi ya bar duniyar amma basu huta ba , wannan wace irin rayuwa ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai arziki ne da duk abinda yayi babu mai tuna masu bare har a zagesu dashi ." tsaki baba gali yaja yana cewa " Munafukar banxa sai anyi magana kisa mutane a gaba kina kuka, da ubannaku bai shaye shaye ba zaa fada? daya zauna da mutane lpy zaa ki fada ?kullum yana cikin d'auko mana magana gashi ya mutu ya bar iri an iya tujara iya tujara sauran shaye shaye .." "Allah bazai sa ba ,baba ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi magana maryama tayi saurin dakatar dashi tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku maza ku san ynd zaku yi ku bar mana gidanmu tunda gdn bana ubanku bane," maryama da tarin qunar zuciya da qunar rai take zubar da hawaye tafi karfin minti goma a durkushe sai daga baya ta koma inda tabar aunty ta durkusa kusa daita hawaye na zuba a idanunta Itama aunty hawayene take zubarwa a nata idanun tana jin ciwon abinda habib yake duk da tasan gsky yake fad'a masu amman bata só yana fadar duk abinda yazo bakinsu dan kome zai faru bazasu ta'ba sonta ba har yau tarasa me tayi masu mai zafi a duniya da suka kasa yafe mata sannan suka kasa danne tsanarsu akanta da yaranta ." Habib ya kalli aunty ya kalli maryama itama duk kuka suke maryama kam har da shesheka tana rarrashin aunty " ku sani ku daina wulakantamu na kyale , kusani nadamarku ta kusan zuwa a nan kusa kuma munafurcinku ya kusan qarewa domin bazan sake yarda da iskancinku dan kuwa kun bari d'an zaki ya girma yayi girman da zai iya kasheku d'aya byn d'aya ,gidan nan kuma babu mai korarmu acikinsa sai dai a d'aga sa d'ungurungun dinsa a sakashi a kasuwa a siyar a bawa kowa hakinsa kowa ya kama gabansa" "Ai kuwa baka isa ba wannan gidan ubanmu ne kai har ubanka ya gama iskancinsa ya koma ga Allah cima kwance ne bai da gidan da zaka yi wannan taqamar da kake yi "kai da ba cima kwance bane sannan bakayi iskancin ba ina naka gidan daka gida yake ? "sannan .." "habib dan girman Allah .." saurin d'aga wa maryama hannu yayi ta hanyar dakatar daita " ki barni dasu heartbeat wallahi kowa sai na bashi size dinsa yau idan sunce basu da mutunci zan nuna masu ni d'an zamani ne , ya d'an tsaya yana kallonsu d'aya byn d'aya ,nan take ya hango tsananin tsoronsa da shakkarsa acikin kwayar idanunsu "oya kuna iya wucewa ku bar mu cigaba da rayuwarmu ko sai na fitar daku d'aya byn d'aya?". A yadda suke kallonsa sun fahimci zai iya jansu ya fitar dasu kmr yadda ya fad'a dan haka aunty hassana ta kalli aunty "sai ki daina kukan munafurci tunda burinki ya cika kin haifa mana maseefa amman in sha allahu maseefar akanki zai qare tunda ya fara zama d'an daba tana gama fadar haka ta fice daga d'akin tana zage zage aunty tayi saurin runtse idanunta tana jin zafin kalmar data danganta mata d'a dashi , itama aunty salma tace "shegu a haka zaku qare jiya iya yau babu cigaba ta nufi hanyar fita " da sauri habib yace "Ke ina naki cigaban da kika samu yake ? "Ke da ko sallah bakya yi , qazama mara sallah mai dotti kawai kije ki gyara tsakaninki da ubangijinki zai fiyye miki sauki akan shiga rayuwar wasu ." shi kam baba gali cewa yayi "bilkisu Ina tarbiyar taki ?yau a gaban idanunki d'anki yake nuna min iyakata "to sai me dan na nuna maka iyakarka a gaban idanunta ? "kai da bakaji tsoron gaban idanunmu kake nuna rashin qaunar mahaifiyarta ba kiri kiri kake zaginta agaban idanunmu akwai abinda yafi wannan ciwo ? wallahi idan bakasani ba kasani yanzu abinda kukayi mata a da tayi hakuri ta shanye yanzu ta haifi d'an da zai kwatar mata 'yanci zan goge wannan tarihin idan ka cigaba da tsayuwa zafin jinina zai iya sa na d'auki takobin can na file maka kai dashi ko na raba katon kan nan naka gida hud'u idan yaso nima akasheni salin alin baba gali ya fice batare da ya sake cewa uffan ba." Yana fita habib ya qaraso inda aunty da maryama suke durkushe suna kuka "cike da girmamawa yace "ku daina kuka in sha allahu ku daina kuka acikin gidan nan , kun daina damuwa matsawar ina raye zan tsaya maku , zan kula daku da zarar na gama karatu zan ...."bana son jin komai daga bakinka habib na fahimci kana bukatar na bar muku gidan nan shiyasa ka kirkiro abinda za'a koreni daga cikinsa tana gama fad'ar haka bata tsaya jin abinda zai ce ba ta mike ta shiga d'akinta ta d'auko mayafinta kawai ta fito zata fice ta bar masu gidan ." Atare maryamah da habib suka sha gabanta cikin tsananin tashin hankali "haba aunty ya zaki mana haka ?kiyi hakuri aunty hakika habib bai kyauta ba amman karki tafi ki barmu ."maryama dan'uwanki baya bukatata acikin gidan nan yana bukatar na tafi na bar masa filin gidan nan ya cigaba da rayuwa ta qarasa maganar tana zubar da hawaye ta tabi gefen maryama zata raba ta wuce ." habib ya riko mata hannu "kiyi hakuri aunty ki fad'a min abinda kike bukata nayi miki alkwarin wallahi zanyi kisani idan kika bar gidan nan bashi da wani amfani a wajenmu "yana da amfani mana tunda gashi kayi son ranka kasa an zageni anci mutuncina anci na iyayena ai gara na kama gabana tunda zamana acikinsa babu abinda yake haifa min sai damuwa da bacin rai ". Kuka ya kufce ma maryama ta d'an rufe fuskarta da tafukan hannuwanta saboda tuttukin da zuciyarta Ke yi "kai ma kasan abinda kayi ba daidai bane har ka iya cire hannu zaka doki baba gali wallahi baka kyauta ba tunda kasan halinsu to meye amfani tsayawa kana fad'a yana fad'a "ki fahimci wani abu heartbeat wad'an nan mutane basa qaunarmu ,babu abinda Ke cikin zukatansu sai tsanar mu " tunda mun san halinsu sai mu kiyaye abinda zai kawo sa'bani dasu shima kukan yake yi "suna nuna mana bambamci akan ya'yansu ,suna quntata mana suna da fuskar gazawa garemu musaman akan ya'yansu yanzu laifin me kikayi ma aunty salma ta shigo tana zaginki ?"maryama bata sake cewa komai ba illa ta cigaba da kukanta haka ma aunty batayi magana ba illa qoqarin zare hannunta da take cikin nashi ." "na tuba aunty bazan sake ba ki fad'a min abinda kike so ,nayi miki alkwarin bazan sake ba ya fad'a yana zubar da hawaye itama ta goge hawayen dake zuba akan kuncinta ta cigaba da mgn "daga yau babu ruwanka da kowa acikin gidan nan duk abinda zasuyi ko zasu fad'a akanmu ka kawo ido kasa masu , kai ba zagi ko dukana zasuyi babu ruwanka a rashin yace ba dai duka ba amman a zahiri yace "to aunty an gama ."wallahi abinda kayi yau din nan ba irin tarbiyar daaka bamu bace "in sha allahu bazan sake ba heartbeat ki bata hakuri bazan sake ba kamo hannun aunty maryama tayi suka koma kan kujera mai zaman mutun uku da duk ashon jiki ya batattake suka zaunar daita tare da sakata a tsakiyarsu suna bata hakuri ." Kamar yadda mlm yahuza ya sanarwa nafisa byn sallahr ishai zai zo sai ga yaro yana sallama da maryama lokacin suna zaune a falon aunty ta dubeta amman ita ko ajikinta sakon da yaro ya fad'a aunty tace "maryama bakiji bane ?ta d'an dubeta ta share yaron ya tsaya yana jiran abinda zaace "to sai ki tashi kije "ina kenan aunty?"bakaji ana sallama daita bane "gsky babu inda zata ban san dalilin da yasa da mutun yazo nemanta ba sai ki bata damar fita baki san ko waye ba mazan da duk 'yan iska ne da zarar sun fara zuwa kamar abun arziki da zance aure ya shigo sai su gudu su barta ni gsky babu wanda zai sake zuwa ta fita ." "Maryama tashi Kiyi maza kije ki dawo saboda ki samu ki d'an huta karki dade duk da nasan ba dad'ewar zakiyi ba ,ina dalili da zakace bazata ba kai zaka aureta ?ya marairaice murya "bani zan aureta ba amman at least aunty ki duba lamarin nan kawai suzo suna 'bata mata lokaci da dagula mata lissafi "Babu wani dagula lissafi a haka allah zai kawo mata wanda zai aureta ,ina son kasan wani abu habib duk cikin masu zuwa neman auren maryama babu mijinta acikinsu , duk lokacin da mijin yazo to babu makawa sai anyi domin babu mai aurenta matar wani kai yaro je kace gata nan zuwa yaron ya juya da sauri dan daman amsar da yake jira kenan zata fito ko kuwa bazata fito ba ." maryama ta tashi ta shiga d'aki dan tasan ko waye yazo ta d'auki hijab dinta ta fito "amman dai ni aunty a wajena ba daidai bane ,ni fa kamar mahaifinta ne a matsayina na namiji acikin gidan nan amman me yasa sai a dinga nuna min iyakata acikin gidan nan , na fiku sanin halin mazan wannan zamani babu komai acikinsu sai tsabar yaudara ". Aunty ta kallesa saboda yadda yake maganar tamkar wani babban mutun tace "wai har guda nawa kake habib ?" duka shabakwai gare fa kawai dan allah ya baka jikin girma "ni dai gsky ban yarda ta fita koina ba girgiza kai aunty tayi tana kallon yadda yake kamaninsa yake canzawa a kullum yana komawa na mahaifinsa tun ba yau ba kusan kowa yana fad'in kamanin nasu "gaskiya habib kar ka zama mai hana neman auren ." tsayawa maryama tayi tana kallon fuskar habib daya had'eta tmkr ance masa idan ta fita guduwa zaa yi daita ,ahankali ta kira sunansa "after dad " "Karki wani kirani da wannan sunan dan dani din ina da wannan matsayin da za'a dinga bin umarnina " ta qaraso ta zauna kusa dashi ta riko tafin hannunsa cikin nata tana kallonsa da idanuwanta da suka canza kalla "after dad me kake so dani ?"ta fad'a tana kallon yadda shima ya zuba mata ido yana kallonta ." "Abinda nake so duk wanda yazo karki qara fita koina idan abinda ake miki acikin gidan nan baya damunki ni yana damuna ,sau nawa kina yi saurayi agidan nan a karshe ko ya gudu ko a kwace miki shi acikin gidan nan ?to ai duk ba mijinta acikinsu ne ,no no aunty akwai cutarwa aciki "to nufinka yanzu haka zata zauna babu mai zuwa wajenta ?"allah aunty dasu dinga 'bata mata lokaci gara ta zauna haka idan na girma na qare karatuna zan mata komai zan siya miki gida da mota itama heartbeat zan siya mata zan kai ku aikin haji ,kai har sojoji zan daukar maku escort duk inda zaku su dinga rakaku aunty da maryama basu san sanda murmushin jin dadi ya bayyana akan fuskarsu ba "shikenan after dad bazanje koina ba domin kai din tmkr uba ne a gareni "yauwa heartbeat sai yanzu naji hankalina ya kwanta muyi zamanmu ." aunty ta kallesu ta girgiza kai "wallahi wannan ba rayuwa bace kin wani zauna ya tasaki gaba yana miki zakin baki ,wallahi ki daina biye masa Ke macece dole kina bukatar Kiyi aure shifa nan gaba kad'an zai ce zai yi aurensa dan wannan da son girman tsiya nasan .."no no aunty karki hadamu da heartbeat babu wani aure da zanyi na barta idan dole sai tayi aure ni zan kawo mata miji wanda zai dinga kwantar mata da hankali duk ranar da yayi gangancin ' bata mata rai na zage naci ubansa ". "Lah lah lallai habib abun naka babba ne "allah aunty sai ma ya cika qaidodina sannnan "wannan ai gara kuje kuyi auren kotu ku huta maryama tai murmushi tana jin dadin yadda dan'uwanta ke tsananin qaunarta "babu kotun da zamu amman dole a kular min da heartbeat ko kuwa a tashi mutun aiki "uhm kaga tashina ta mike tsaye " bari naje na bawa baba gali da hassana hakuri na dawo ." "haba aunty ai komai ya rigada ya wuce wani hakuri kuma zaki basu salon su samu damar ci miki mutunci "? A'a sai naje zaman lafiya yafi zaman dan sarki ina zan iya dasu gara dai naje ."Yauwa aunty kije ki basu hakuri wannan ai ba komai bane wata rana sai labari kai ma ya kamata ka bita kabasu hakuri wani irin kallo ya watsa mata yana cewa "allah kiyaye ai ni .."sai kuma yayi shiru sakamakon tuna alkwarin da yayiwa mahaifiyarsu ." "ai babu abinda zai sa naje da habib sai ya qara dagula lissafi sunan wani police a isokoko ni na wuce sai na dawo "to aunty sai kin dawo tasa kai ta fice daga dakin ta barsu suka cigaba da hirarsu mai cike da kulawa da soyayya shi kam mlm yahuza tsawon mintuna nan duk yana tsaye yana jira Fitowar maryama ya duba agogon dake daure da taintsiyar hannunsa yaga lokaci ya tafi daman kuma yaron daya aika ya sheida masa komai dan haka a natse ya juya sai dai ya kudurce aransa zai dawo gobe." Ahankali aunty take tafiya tana tunane tunane abinda zatace idan ta isa gaban baba gali a natse tayi sallama cikin bangaren nasu basu amsa mata sallamar ta ba dan haka taji gabanta ya shiga faduwa kafin ta kai ga yin wata magana taji aunty salma ta hau surfa mata maseefa kamar kullum "me ya kawo bangarenmu "ba komai bane hakuri nazo baku akan abinda habib yayi ,ya gama ci mana mutunci a gabanki shine dan munafurci kika kwaso jiki bayarwa , shegiyar munafuka kin wani marairaice fuska bayan kin gama zuga d'anki yayi mata walima ta uwa da uba zaki wani kwaso jiki to yanzu hakurin me kika zo bamu ?". Numfashi aunty ta sauke ta samu waje ta zauna kusa da baba gali da ko kallon inda take bai yi ba a tun sanda ta shigo "kuyi hakuri gabadayanku in sha allahu nayi maku alkawarin wannan shine karo na farko da karshe da hakan zai faru ...."dakata bana son jin komai daga bakinki dan duk abinda zai fito daga cikinsa karya ne ni dai abinda nake buqata "ki dauki yayanki ku bar mana gidanmu tunda ussein yake raye bai tsina mana komai ba sai tujara gashi nan ya barwa dansa tsaraba har kamar ni wannan yaron zai dinga gasawa magana kuma a gabanki kina kallo yaron da ya kamata kiyita dukansa har sai kin kusan auna shi lahira amman kika zauna dan tsabar son ya'ya kina kallonsa yana surfa mana zagi ta uwa da uba ai wallahi bazai yuwu ba ." Sake durkushewa tayi Kmr zatayi kuka batare da tasan abinda zata sake fad'a ba sai dai ita kanta a halin yanzu tana mai bakincikin hada zuria dasu tsaki aunty salma taja tana cewa "munafukar banza munafukar wofi sai anyi magana ki wani durkushewa mutane "ni dai ba wani tashin hankali nazo dominsa ba nazo ne dan na baku hakuri dan nasan danku bai kyauta ba "ni wannan yaron ba d'a bane domin kuwa d'ana bazai min haka ba hakuri aunty tayita basu da kyar baba gali yace komai ya wuce amman tajawa habib kunne aunty salma dai ce taki hakura ta mike tana masu sallama "sai da safenku allah kuma ya huci zuciyarku babu wanda ya kulata acikinsu har ta fice zaginta aunty salma take cikin tsananin tsana ." Daga bangaren baba gali na aunty hassana ta shiga itama dai tujara tayi mata ta uwa da uba kaf danginta babu wanda ta bari bare iyayenta zuciyarta tayi nauyi kamar an d'aura mata dotse da kyar ta yunkura ta mike ta fito tana tafiya zuciyarta na kokawa. a inda aunty ta fita ta bar yaranta anan ta dawo ta samesu zaune suna hira "har kin dawo aunty ?suka had'a baki murmushi tayi tare da d'aga mata kai alamar" eh! my princess na dawo ". "Yaya kuka qare fatan sun hakura "Eh to sun hakura my princess!ta fad'a zuciyarta cike da raunin kuka dan shi take bukatar yi a halin da take ciki shi kam habib bai ce uffan ba illa ya cigaba da sauraronsu"my princess Kinga dare yayi bamu samu girka komai a gidan nan ba ni yanzu ban san me zamu dan girka muci ba "wallahi aunty amman bari naje wajen Ummah watakilla bazamu rasa abinda zamu ci ba maryama ta fad'a idanun habib yana kanta "ko zaka raka ni ne? ta fad'a tare da miqewa..."Muje ! kawai abinda ya fad'a kenan maryama tayi murmushi "makalema kawai "kima ce bita zai zai ki huta gbdy muje suka jera ." Suna fita suka had'u da yaya sadam ya fito daga side d'in din baba gali zai shiga side din ummah cike da farinciki habib ya qarasa suka gaisa! "A she rabon mu had'u ne yaya yasa heartbeat tace nayi mata rakiya ."ai ko baka fito ba yanzu nake shirin zuwa tambayarka a wajen aunty !Ya mika masa hannu ya kwana biyu ina fata dai komai lafiya? "Lafiya lau habib kawae aiki ne ya boye ni 2days ya karatu ?yace "alhamdulillah.!" maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa ya amsa mata cike da sakin fuska "Lafiya su aunty maryam"ji tayi kunya ya kamata da kirata aunty da yayi ! Ya gida da karatu ?Alhmdllh! ta fad'a cikin jin kunya"kema dazu nake tambayarki wajen Ummah take bani labari mai dadi lallai kin fita zakka acikin matan gidan nan kin tsaya kinyi karatunki yadda ya kamata allah yasa muji sakamakon mai kyau you're the best maryama duk nmj daya sameki a matsayin mata baqaramin dacewa yayi ba Allah yasa sawa karatu albarka dad'i maryama taji sosai dan duk cikin yanuwanta sadam ne kawai sai habib Ke mata fatan alkhairi idan wani abun farinciki ya sameta tace "na gode sosai yaya ." Habib yace "a she dai yaya ka gane shiyasa sai na zaba mata na durje mata miji dan ita din ba kalar kowani nmj bace "kaga yaya karka kulashi mu je ciki mu qara gaisawa "wucewa sadam yayi side d'in Ummah maryama da habib na biye da shi sunata hiran duniya..." Zama sukayi a parlour'n sadam ya fara kiran "Ummah Kina ciki ne? Eh! Ganin nan zuwa dan albarka har ka dawo ne? sadam yace" eh ! gashi na kawo miki maryamarki "ban gane ka kawo min maryama ba maryama da muke yini tare dan gulma zakace ka kawo min ita Bari dai nazo ganin nan fitowa ." Bata wani bata lokaci ba ta fito cikin doguwar riga qaton tray ta aje a gaban sadam na fruits bismillah sannu da zuwa yau har da habib to duk sannuku "Ina yini "Habib yace " lafiya lau habib Ummah ta kalli sadam ta kalli maryama sai taga sun maseefar dacewa ina ma su kasance maaurata suna hirarsu gwanin ban shaaawa habib ya fahimci maryama kunyar sadam take ji sosai dan taki fad'ar abinda ya kawo su gashi shi yunwa yake ji ." Maryama tace after dad ya kamata mu wuce dare nayi "a'a har zaku tafi kenan maryama to ai bakuci komai ba "karki damu Ummah "ban gane karta damu ba kinga nifa banason kunyar nan take wai ma wa Kike jin kunya anan umma ko yaya sadam ,?maryama tayi shiru tana mai sunkuyar da kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta "kinga Ummah nan ya fad'a mata abinda ya kawosu "kai maryama amman shine zaki jashi ku wuce to kuci me idan kun wuce? allah ya kyauta wannan kunyar taki kaga habib bari nazo ta fad'a tana mikewa tsaye ta nufi kitchen ". Bata wani bata lokaci ba ta dawo hannunta d'auke da wani madaidaicin kula cike da abinci sannan da wata leda cike da su cincin wanda tayiwa sadam ta miqa ma maryama tace gashi kai km habib ka rike kula " mungode Ummah !Suka fito maryama nayi masa mitar abinda yayi dariya kawai yayi yana cewa "ina ganin gara kawai ayi yar gida mu huta da samari masu mana patrol "kai dai kasani ni nasani ko gaskiya suna tafiya suna jan juna har suka qaraso falonsu habib ya zauna yana kiran "washhhh allah maryama ta cire hijab dinta ta ajiye akan kujera tace "habib bari na kira aunty kanshi kawai ya gyada mata ." Ahankali ta shiga d'akin sai dai abinda yayi matukar daga mata hankali shine ganin mahaifiyarta kwance rigingine akan katifa hannunta rike da wani hoto tana kallon hoton hawaye na zuba daga idanunta tana tuna irin rayuwar dadin da tayi ada kafin shigowar ussein rayuwarta ,bata haskowa kanta irin rayuwar da take ba sai data hadu da ussein soyayyarta ta gurba tunaninta ." yayinda maryama ke kallon mahaifiyarta da ita kadai ta rage mata a duniya yanzu a natse ta qara taku biyu domin son ganin hoton waye a hannunta take kallo tana kuka wasu mutane tagani guda biyu cikin shiga na alfarma suna cikin koshin lafiya da farinciki ko baa fada mata ba tasan hoton iyayenta take kallo cike da nadama lumshe idanunta tayi "iyaye ba abun wasa bane , aunty iyaye suna da kimar da darajan da bazaa iya mantasu ba ." ahankali taji sautin muryarta tana fita cikin kuka "nayi kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi kewar kowa da kowa ta fad'a tana mai daura hoto a saman qirjinta tana shafawa tana kuka.." Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ." "habib soyayyar iyaye da yanuwa baa wasa dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ". karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ." "idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ." ****** da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito parlour'n mami ,duk jikinsa yayi sanyi har wata katuwar rama yayi daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi kusantowar aurensa da maryam yasashi jin kmr ana fixgar ransa ,shiru ne ya ziyarci parlour'n yana tunane tunane yana jin kamar idan ya tafi france kar ya dawo domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa byn kmr mintina goma mami ta qaraso da kanta ta had'o masa abun kari , chips da soyayyen kwai da ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table gabansa ta ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ." ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse idanunshi shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji kayi magana kaci abinci kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka abinci bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal ka taimakeni kaci wani abu kanshi kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam baya jin cikinsa zai iya amsar komai shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga saukewa ."sweetheart dina me yasa kika manna min wannan auren haka? " sweetheart zaki kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda na tsawon wata guda ne ." "to me zan maka adamcy nah daya wuce haka ? "me kake son nayi idan banyi maka haka ba ? gani nayi kana neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ." wani irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..? "wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart ni bance tana da laifi ba amman ki duba lamarin da kyau tunda nace bana sonta ai sai a hakura kawai kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi kayi tunani zaka iya juya ni ."Wannan aure sai anyi shi muddin ina raye ." ya marairace muryarsa sosai tmkr mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake ? Allah sweetheart ki daina mata kallon haka saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu lalacewar mace daga miji ne ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. " "Sauran kwanaki goma a daura maka aure da maryam a lissafina gobe ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar france fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta gama shirya komai na aure fatan alkhairi da dawo da niyyar angeancewa lafiya and if you do anything stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata daya runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke." "ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan d'aya byn daya suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu mintuna aka cika gaban mr ata da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci illa coffee daya dinga tsiyaya a cup yana kurba ahankali ahankali shima yana sha ne kawai saboda sabon da yayi dashi ." Parlour'n ya dan rage mutane ya saura daga hisham sai ata nuzla da diyana har ma da mrym da nana hauwa'u suka shigo parlour'n bakinsu d'auke da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar ganin masoyi yarsa gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki banda nuzla Kmr koda yaushe da kyar ya amsa masu hisham yana kallon fuskar nuzla yayinda nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani ." ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun yau ba yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma sunji abinda ya fad'a ." ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba? aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."? "Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta "me zata maka ?Kai dai kira min ita kawai yau yarinyar nan zataci ubanta da me tafika da zata ce bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ." Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta kama gabanta ta bar nuzla tsaye cike da fargaba ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har kusan mintuna shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ". "Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana bukatar jin maganarki ko wani abu kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki goma ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune "me yasa yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata magana anan , karki sake kula kowa acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe soyayyarsa acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki .." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 20 jikinta na wani irin rawa ta k'araso ta durkushe a gabansa har bata san sanda ta d'aura hannuwanta duka bisa cinyoyinsa tana kallon cikin kwayar idanunsa da suka rikid'e suka canza kala a wulakance ya zame jikinsa yana mai kawar da fuskarsa gefen hisham dake zaune tmkr mutun mutumi yana kallonsu cike da matsanancin tashin hankali ,shi kuwa mr ata alamun baya son kallon fuskarta ne yasa shi maida idanunshi kan hisham ". "dan allah dan Allah !! yaya adam kayi hakuri ta kai hanuta tana qoqarin juyo da fuskarsa gareta domin su fuskanci juna , zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske take kallonsa haka ma hisham zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da kaida ya soma jin wani sauyi na daban a gabadaya ilahirin jikinsa wanda ke gauraye da tsantsar tashin hankali, shi kuwa mr ata mamakinta yasa gbdy ya qasa magana duk da maganar yake son yi . Kwayar idanunta suka cicciko da ruwan hawaye muryarta a sarke tace "dan Allah yaya kayi hakuri karka bari wannan auren ya kasance domin zuciyata bazata iya d'aukar wannan nauyin ba, wata razananniyar tsawa ya buga mata wanda ya kamata ace ta tsorata ta dawo da hankalinta jikinta amman ina sai ma sake narkewa tayi a wajen zuciyarta babu tsoron komai acikinta , muryarsa a kausashe yace " tashi ki bar nan ki kuma fara shirinki kamar yadda na fad'a miki oya leave ." "dan Allah ka saurareni yaya "ya girgiza mata kai yana cewa " I don't want to listing anything from you just leave now "dan allah yaya adam kayi hakuri ka saurareni akwai maganar da idan na fad'a maka nasan zaka fahimceni "ata dan Allah ka barta ta fad'i abinda ke zuciyarta Hisham yayi maganar yana qarewa jikin nuzla dake rawa tmkr mazari da kallo , yadda take cikin tashin hankali haka shima ya tsinci kanshi cikin tashin hankali mai tsanani har yana jin ma kamar ya cire mata nata damuwar ya qarawa kanshi " Hisham yayi tsuru tsuru yana jira yaji abinda zata fad'a ,yayinda mr ata bai ce uffan ba ya yunkura ya mike tsaye ya kwashi wayoyinsa ya fara taka kafafunsa da kyar zai bar wajen kasancewar bai son yawon magiya bare irin nata dake hargitsa kwakwaluwa nuzla tayi saurin shan gabansa tana fad'in "yaya karka wuce ka bar zuciyata cikin maseefa tayi maganar cike da tausayawa ,bai yi mata magana ba ya cigaba da tafiya yana mata gargadi da hannunsa alamun ta shiga hankalinta , bata daddara ba ta sake shan gabansa dan gbdy zuciyarta ta rigada ta bushe babu abinda take qoqarin aikatawa face ta bayyana masa ciwon dake cikin zuciyarta ." Ya tsaya kawai yana mata wani mugun kallo yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa muryarta cike da rauni da buqatar atausaya mata ta fara magana "bazan iya jure ciwon rabuwa da wanda nake só na auri wanda kake só ba ta karasa mgnr tana rungumeshi ajikita tana kuka a matukar zuciye ya fixgeta daga jikinsa yana sake furzar da iske "are you out of your sense ?ni sa'anki ne da kike shiga gabana? " ko ina wasa dake ne da ina magana kina magana ? ya fad'a yana kawar da fuskarsa akanta domin dai zuciyarsa ta fara tausaya mata tausayawar da bata da wani amfani dan bazai ta'ba iya mata taimakon da take nema daga garesa ba ." Hisham ya rasa meke faruwa atsakaninsu babu abinda zuciyarsa bata kissa masa ba a zaune da yake tmkr an dasashi irin kallon da take ata da rungumar da tayi masa ya fara gasgata zuciyarsa akan abinda bai niyyar yarda dashi ba yaso ya mike ya qarasa zuwa inda suke tsaye yasan ko akan me take masa magiya har da runguma amman hakan nan yaji gara ya cigaba da zama a inda yake zai fiyye masa alkhairi kuma bugu da qari yayi imani ata bazai ta'ba aikata komai ba face abinda yasan zai zamewa rayuwarsa farinciki he really trust him mutun ne shi mai kyakkyawar zuciya akanshi ." Hawaye na gangaro mata bisa kuncinta yayinda magana ya fara fitowa daga bakinta "ina qaunar ka yaya ? bai yi mamakin jin fitowar hakan daga bakinta ba domin ya rigada ya gama karantata tsab "na sani sai akayi yaya ?ya fad'a yana kallonta yana jin kamar ya soma yar yarfa mata maruka ta dawo haiyacinta "dan Allah yaya karka ce min a'a ! a kowani hali zan kasance tare da kai " ta maimaita hkn a fili yafi sau goma tana mai kai hannu ta shafa kasumbar dake kwance a fuskarsa ji yayi kamar ta shafa masa garwashin wuta ,shi fa duk duniya babu macen da yake jin zata ta'ba shi yaji wani abu ajikinsa sai princess ita ma din yanzu ya soma gogeta a zuciyarsa da rayuwarsa ."cikin fita haiyacinta ta riko fuskarsa sosai ta sanya kwayar idanunta dake tsiyaya ruwan hawaye acikin nasa " ban san hka soyayyarka tayi tasiri acikin zuciyata ba sai dana qasa amsar soyayyar kowa ." "Ban san tasirin soyayyarka ta kai mizanin da zan iya rasa rayuwata ba sai da naji zaka min nisa , yaya kaine duniyata ruhina yana tare da kai ako da yaushe , nayi yunkurin bayyana maka soyayyata a tun lokacin da mubina Ke mutuwar sonka amman na gaza aikata hakan ina ganin cewar zan iya cire soyayyarka na cigaba da rayuwata amman still na qasa domin kuwa every each second nake jin sonka na qaruwa a cikin zuciyata , ina ta qoqarin sheida maka halin da zuciyata take ciki kwatsam kuma sai ga batun aurenka da marsi bance ka bar marsi ba amman dan allah ka had'amu ka auremu " rokonki bai kar'bu ba bare wata alfarmar ya kamata ku koyi yadda ake iya control din zuciya "ka taimakeni ban san ya zanyi ba " kar allah yasa ki sani ya fad'a yana jan tsaki ." kuka take sosai tana kallonsa tmkr ranar ta fara ganinsa shi kuwa haushi ne ya turnikesa a wajen zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda yake , a ganinsa ma ta balain rainashi shi zata kalla tace tana so alhalin ga hisham dake mutuwar sonta? "kayi hakuri dan girman Allah nasan zakayi tunanin komai akaina wallahi haka ne , dan na rigada na haukace akanka bazan iya jurar abinda nake ji akanka ba sannan bazan iya amsar soyayyar yaya hisham ba ,dan kona auresa gangar jikina ya aura zuciyata da komai nawa yana gareka da kawai zan iya rayuwa ..." Ta riko hannunsa hawaye na zuba daga idanunta ta soma tafiya dashi taku d'aya biyu yayi ya tsaya cak , itama ta tsaya suna fuskantar hisham naunaye ajiyar zuciya ta sauke tana goge hawayen dake tsiyaya ,ahankali ata ya zare hannunsa dake cikin nata ya yarfar sannna ya zura cikin aljihun wondonsa yana jan tsaki "ya hisham! ta kira sunansa a kid'eme "banyi niyyar fito da sirrin dake zuciyata ba amamn ya zama dole na fad'a maka tunda na fad'awa yaya adam babu komai acikin zuciyata sai..." karki kuskura kiyi wannan ganganci dan kome zaki yi tawa zuciyar bazata amince ba "to kuwa gara ka ksheni da hannunka na huta dan nima bazan iya auren yaya hisham ba , yana sona ni kuma kai nake so.."you're very stupid Kiyi maza ki danna madannin gogewa ki gogeni arayuwarki da zuciyarki dan ni mallakin mafarkina ce " yana gama fad'ar haka ya juya ya haye sama yana taka step yana magana " hisham ka manta da shirmen wannan yarinyar ka soma naka shirin domin wannan auren ko zata mutu sai anyisa useless girl kawai ga inda ake sonku aka damu daku amman ku dinga kai kanku inda bazaa ta'ba sonku ba nonsense " Hisham ya runtse idanuwanshi "kenan hasashensa ya tabbata , zarginsa ya zama gasky kenan akan ata yake shan wulakanci da tsana da wahala a wajenta ? ,"ya kalleta cike da tausayawa yace "daman ata Kike so ?jikinta yayi mugu mugun sanyi ta rasa me zata cewa hisham illa ta runtse idanunta gam tana jin zafi da ciwo mara iyaka a zuciyarta ,ta durkushe qasa tana kuka tana nemawar kanta mafuta dan dole tasan abun yi kafin a had'ata aure da hisham shima ya durkushe gabanta ya dago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata , tai saurin buge masa hannu tana kallonsa cike da tsantsar tsana "ka kyaleni ni wallahi bana sonka tunda burinka kenan na soka , dan girman allah ka rabu dani ka manta dani, ka manta da maganar ka ta'ba sona arayuwarka , ka mantani ta qarasa fad'ar haka tana fidda huci mai zafi ." "Dan allah kiyi hakuri nasan irin ciwo da zafin da Kike ji acikin zuciyarki ciwo ne kwatankwacin wanda nake ji acikin zuciyata nasan zafin ciwo da radadin kana son wani baya sonka ,wallahi na tausaya miki amman me yasa nuzla ?"me yasa sai ata zuciyarki zata kamu da so byn ni ina qaunarki ya kai hannunsa yana share mata hawaye"ata bashi da wannan lokacin wahalar da kanki da zuciyarki kawai zakiyi babu wannan tausayin a zuciyarsa a karshe ya rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta ahankali ahankali babu yadda ta iya dole ta kasance rungume ajikinsa domin tana bukatar wanda zai rarrasheta kuka take sosai tana rungume ajikinsa "ki daina kuka nuzla dan zuciyata bazata iya ganin hawayenki da damuwarki ina matukar sonki da zaki bani dama da sannu zaki daina son ata ki soni ya fad'a yana qara rungumeta gam ajikinsa ahankali ya mike tsaye tare daita ya nufi kofar fita tun kafin mutane su shigo su fahimci halin da suke ciki ." Washegarin da misalin karfe tara na dare ata ya shiga d'akin mami sanye cikin fararen kayan bacci wondo da riga , hannunsa rike da black cup dinsa dake dauke da ruwan coffee ,yayinda dayan hannunsa Ke cikin aljihun wondonsa ya samu mami tsaye a gaban wordrobe dinta tana qoqarin rufewa tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana nawa ya saura ai Allah Allah nike Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya girgiza kai kawai yana ajiye cup din hannunsa akan bedside dinta ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ." "Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a "Eh ina neman wata alfamar a wajenki sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice murya sosai kafin ya soma mgn "dan darajan Allah sweetheart ki qara min lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce hollond yi wasu abubuwa masu mahimanci a yanzu na samu sauyin lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan fine na amince a daura auren ayi komai amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk wanda aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ". "naji amman har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla ko kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji dashi tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar yar mutane da nauyi akanta gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan qara maka ?uhm ko Kmr wata biyu haka yayi "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba, ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari adamcy ,karki damu sweetheart na ranse fa ,shikenan na yarda da kai ta fad'a kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin nuzla murmshi mami tayi tana cewa "adamcy nah mai farinjini ." Zaune mr ata yake agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake jikinsa na fitar da wani kamshi na daga hankali fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun sallama ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar france "Allah kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar ya tafi amman kamar yau ne zai dawo gareta wannan karan mami ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana dauke hawayenta ." ***** Yau tsawon kwana uku kenan mlm yahuza yana zariyar zuwa gidansu maryama amman kamar kullum bai samu ganinta ba yau ma daga massalaci ya wuto kofar gidansu yana neman yaron da zai aika cikin gidansu ko cikakken minti goma bai yi da tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan ya mika masa hannu suka gaisa "ina fatan dai lafiya kwana biyu nan kake zuwa gidan nan ?"Lafiya lau wajen maryama nake zuwa sai dai duk zuwan da nake yi bana samun ganinta ,shine dan naci kake ta zuwa ?to ya zanyi sadam tunda zuciyata ta kamu da matsanancin sonta duk da bani da tabbacin ko tana sona amman nasan tana son fitowa inda nake habib ke hanata fitowa yanzu dai taimaka min ka fito min daita dan nasan muddin habib na cikin gidan bazai barta ta fito ba ,murmushi sadam yayi yana cewa "kai habib hukuma ne wannan yaron bari ina zuwa !ya juya ya koma cikin gidan ya shiga side dinsu maryama ." a parlour ya iskesu gabadaya suna hirar duniya ya zauna yana fuskantar maryama suka gaisa da aunty sannan maryama ta gaishesa haka ma habib ya amsa masu da "lafiya lau cikin sakin fuska ,ya gida da aiki sadam ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana duban maryama "ga malamin ku yahuza can a kofar gida yana jiranki yau tsawon kwana uku kenan ina ganinsa ashe wai saboda ke yake zuwa amman bakya fitowa."wata irin kunya ta kama maryama ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da zara zaran yatsun hannunta". "ai ga d'an albarka dake hanata fita nan , ko shi zai aureta bansani ba ?yaro qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa tana biye masa aunty ta qarashe maganar tana zabgawa habib harara ,habib bai ce komai ba ya tashi ya shige ciki dan matsawar yana zaune a falon bazai iya barin maryama ta fita zuwa koina ba km hakan zai sa yaya sadam yaji babu dadi "ai yahuza mutumin kirki ne kuma ga dukkanin alamun da gaske yake aunty tace "allah yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka amman in sha allahu komai yazo karshe dan nasan yahuza bazai mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza tashi kije maryama karki dade maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu km tasan duk akan mgnr fita ne ,amman babu yadda ta iya yaya sadam da aunty suna da karfin iko arayuwarta ta mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana atsakaninsu ba ." acikin duhu ta sheida murmushinsa ganin hasken hakoransa ta dan saki ranta da kawar da damuwar fuskarta barkanki da fitowa gimbiya maryama "numfashi ta fesar "kai ya kamata a yiwa barka da zuwa da kuma sannu da qoqarin zuwan da kayita yi baka samun ganina da km qoqarin da kayi da iyayena last week na gode sosai " ya dan kyaleta "iyayenmu dai na gyara miki ." maganarsa ta dan mata dadi wannan yasa ta dan sakin fuskarta kad'an "ya kamata mu samu waje mu zauna ko can ne ya dan nuna mata wani dakali dake makoftansu ." tare suka qarasa amman shi yaki zama ya tsura mata ido ya kamata ace kece kika fara zama sannan ni tayi shiru dan tuni ta gane manufarsa ta dan kallesa da idanunta cikin sauri ta kawar da kai ganin kwayar idanunshi na kanta to shikenan na zauna kema ki zauna ta zauna tana gyara zaman hijab dinta sukai shiru na dan tsawon lokaci daga bisani ya dago ya dubeta "Maryama zuciyata duk ta gama tattara komai agareki a yanzu bani da wani shakka ko kwankwanto akanki muradina ne na samu damar da zan kawo kaina ga iyayenki domin a samu tsayayyen magana a tsakaninmu ." Soyayyarki ta jima ajikina maryama nayi dawainiya da soyayyarki tun kafin ki kai wannan lokacin na koyar da zuciyata dabarun da kuma yadda na dauki hakuri dan kawai na samu soyayyarki ban ta'ba gazawa ba , ina sonki maryama da zuciya daya ban qara jin ina sonki ba sai danaji halin da ke da mahaifiyarki da kaninki kuke ciki a gidanku bazan boye miki ba ina jin tausayinku most especially mahaifiyarki domin ta fuskanci abubuwa dayawa akan rayuwa kuma tayi hakuri na tausayawa rayuwar da kuke ciki ki daure ki samar dani acikin zuciyarki mu daga darajan uwa da kuma danuwa mu tallafi rayuwarta data kanin mu dukkan wani muradinki zan bi na tabbatar kina da burin kiyi aiki byn kin qare bautar qasa kamar yadda naji kawayenki suna fad'a,burinki kiyi karatu mai zurfi Kiyi aiki ni nan zan barki Kiyi komai kike só zan barki ya dan saurara yana kallonta hawaye taji akan kuncinta tasan su da mahaifiyarsu abun tausayi né suna cikin tsananin kunci da bazai yuwu a boyesa ba ." ahankali ta dubesa "naji dadin yadda kace zaka tayani kula da mahaifiyata da kuma danuwana mlm yahuza ina matukar son Mahaifiyata ina son na gatatan rayuwarta domin ita kadace dani na yarda da soyayyarka kuma na amince duk lokacin da kake da lokaci kofar neman aurena a bude take domin burin mahaifiyata kenan na tsayar da mijin aure fatana ka rikeni amana tayi shiru saboda kunyarta ta motsa ya sauke ajiyar zuciya a zahiri take fahimtar farincikinsa dan bai boye ba ." Yayi murmushi yana shafa fuskarshi "maryama amanarki agareni bake zaki bani amanarki daga allah daya halicceni ce domin shi na dinga roko ya bani ke amatsayin mata aurena allah ya amsa tunda har kin amince min dan haka shi ya bani wannan amanar dan haka nayi alkawarin bazaki taba ganin sabanin haka daga gareni ba ,ba kuma zakiyi danasani ba , aurena zai zame miki abun alfahari bazan ta'ba gudunki ba bazan ta'ba juya miki baya ba ."Soyayyar sati uku da sukai da mlm yahuza ta fuskanci tsantsar son da yake mata kulawa kuwa har da mahaifiyarta abun mamaki kowa a unguwarsu yasan da soyayyarsu wasu nasa albarka wasu nacewa ba girin girin ba allah yasa a d'aure kar ya gudu ya barta kamar sauran." ****** Cikin wannan lokacin maryama da kawarta subai'a suka je adamawa domin suyi cam for three weeks bayan sunyi sati uku a adamawa alokacin mlm yahuza yayiwa wani mutun magana akayi masu change of location ita da kawarta daga adamawa aka dawo dasu lagos inda zasu fara bautar qasa a Z &A comapany dake kan titin guness bayan ciku cikun da mlm yahuza yayi masu domin shine ya shiga ya fita ya kar'bo masu letter suka kai wa nysc aka kar'besu a kamfanin bayan sun dawo lagos suka fara savieces dinsu wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama ya wanke zuciyar habib yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da otherhaif kuma yake girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna da matukar wahalar samu ." "gashi shi dai ba wani zurfi yayi a boko ba dan karatunsa iya diploma ne amman yana da hanya kuma yasan mutane sosai dan shugaban RRS mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci da abota , fara bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan islamiyya gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ." Ranar wata asabar tana zaune shiru a side dinsu tana tunane tunane akan sakina tana matukar qaunar sakina aranta ta kasa jurewa abubuwan da take mata batare da tasan laifinta ba ,zuciyarta ta bata shawarar taje ta tmbyeta ko wani laifi tayi mata wanda yasa ta canza mata ,nan take ta amince da shawarar zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa mata dan haka ta wuce daki inda tafi tunanin sakina take mintuna sha uku da zamanta amman sakina bata ko kalleta ba ." Ahankali maryama ta tunkarareta da abinda ya shiga a tsakaninsu "haba "yar uwata mai na yi miki ki ke fushi dani tsawon Lokaci ko magana ba kya min mai nayi miki da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina ta tambayeta tana mai kallo cikin idanuwanta maryama ta sauke nata idanun ganin irin kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô Sakina tsawon lokaci naga bakya min magana, in da nayi miki laifi ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni tsaki kawai sakina taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama bata ji dadin abinda tai mata ba "na shiga uku maryama ta fada a ranta me zai sa sakina ta yi min haka kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah ka sanyaya zuciyar sakina akaina idanunta cike da hawaye ta baro side dinsu ." Ranar wata laraba aunty salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar gida aunty salma ta dubi sakina "wai Ke kwana biyu nan mai yake damunki ne sai ki dinga kadaita kanki kina wani shiru idan wani abu aka miki bazaki fad'a ba sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance min zakiyi ba duk da ku ka jawo halin da muke ciki nida yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu ta dan. tsaya ta kasa kunne aranta tace "allah sarki ashe yaruwata laifi akayi mata tayiwa gidan kudin goro kowa bata shiri dashi." aunty salma tace " koma me akayi muku zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku kema kinsan zanyi qoqarin magance muku ita matukar ina numfashi acikin duniyar nan sanar dani menene aka muku da har yake saka ki cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu sun san yadda shukura ke son mlm yahuza amman kiri kiri kuna kallo wannan banzar ta juya abun ya koma kanta gashi har ana batun saka rana aure ." Da alamun aunty salma taji dadin furucin sakina akan maryama domin duk irin kunci da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye keda yaruwarki ? maryama ta fahimci kalmar cikin zolaya tayi maganar ,ai kuwa nan da nan sakina da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun koresu a gidan Kmr yadda kika ce ai da bata yiwa shukura kwacen saurayi ba yanzu gashi nan muna ji mun gani wanda shukura take so dole zata hakura "a'a waya gaya maku ai babu wani maganar wani hakuri ,kuyi hakuri tunda kun fad'a min ku bani kwana uku zaku ga abinda zai faru." hankalin maryama ya tashi kwarai da gaske har yasa daga nan bata sake sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba saboda wani daci da zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam bazata amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu amman yanzu ya zatayi ?ko da yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata mata dashi dan arabasu dan haka zata bari adduarta tayi karfin da bazasu samu nasara akanta ba tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili domin kiyamullaili tana qarawa nauyin mizanin bawa, tana qarawa mutun hasken fuska da samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri tare da biyawa bawa bukata." Duk bayan kwana biyu mlm yahuza yana zuwa wajenta Kmr yadda ta tsara masu dan bata son yawon zance ,tun bayan kwana biyu sunyi da mlm yahuza zai zo sai dai har karfe takwas na dare daya saba zuwa bai zo ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa hakuri ta shirya tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah ta iske shukura tana zance sai dan kasancewar dare bata lura da wa take zance ba sai dai kawai kamshin turarensa yayi mata kama dana mlm yahuza amman ko kadan bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa Daga nan suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta koma side dinsu cikin tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ." Shigowarta kenan daga wani kamfani kai zanenta domin tallatawa ,da baba gali ta soma ci karo "yar gwal idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta ya fadi tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar haka ba km wai yar gwal yana son magana daita tabbas akwai mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa fargaba ." Karfe tara daidai umma ta aiko a kirata ita da aunty nan fa gaban maryama ya cigaba da fad'uwar da yake , tare suka fito da aunty alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan isa bakin side din umma, haka nan ta kalli shukura dake zaune kusa da aunty salma dake cin abinci atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ." shiru ne ya biyo baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty hassana sannan byn an gaisa umma ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?" Maryama tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan wace irin magana ce akwai abinda umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman dai koma menene batasan abinda yasa take mata wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta sake yin shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje idan yazo bata son fita ." "Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai zane yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura yake so ." ba idanuwanta ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta juya idanuwanta kana tashiga tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai tana jin damuwa mai tsanani " "Magana nake maryama kinyi shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa danuwanta hankali." Sai datayi mai isarta sannan ta fito ta shiga falo kai tsaye ta wuce habib dake zaune yana kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta da taimakonsa gareta hakika bazata ta'ba mantawa dashi arayuwarta ba ta dinga girgiza kai shikenan shima ta rasashi ,hawaye suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar habib yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat tayi saurin gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ." Bangaren umma kuwa gyara zama aunty tayi ta kallesu "hakika bakuyi adalci ba saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?". "to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta." "Uhm kawai aunty ta furta a fili sannan a fili tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi komai "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ". "Dakata dakata!! su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu hassadar zata cinyeku ni natashi allah ya bamu alkhairi allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ." Aunty ta shigo parlour'n tana kuka nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance har lokacin tana zubar da hawaye tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a dakin ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun maryama ta damke cikin nata jikinta har ya dauki zafi ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune cikin mawuyacin hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?" "Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai akwai allah wani irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya ya juya maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da hannunsa daya yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku ,allah ya baki miji na gari, idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza ya dawo gareki ya kula dake ." "Maryam tana kuka aunty tana yi tana goge mata hawaye "Kiyi hakuri maryama "kema aunty Kiyi hakuri bana son ki daga hnkln ki akan matsalar nan ,in sha Allah nan kusa Allah zai bani wani "In sha Allah bazai dade ba Allah karka barmu da iyawarmu ka iya mana dukkanin abinda bazamu iya ba har kusan karfe dayan dare suna tare kuma duk mgnr mlm yahuza suke aunty bata so tayi nesa da maryama , tafi son bacci ya zo mata tana tare daita don Allah ki daina damuwa kinji ' yata ki kwanta Kiyi bacci Allah yayi miki albarka yayi wa rayuwarki data ' ya'yan da zaki haifa albarka, In sha Allah bazaki dangwama a hk ba Allah zai saukaka mk na yafe miki duka laifukan da kikayi min wnd na sani da wnd bn sani ba daga hk tayi shiru tana goge hawayen idanun maryama , amma tamkar sake kara mata su ake . Ba sosai damuwa yake tasiri acikin zuciyar maryama ba bare irin wannan damuwar da idan da sabo ta saba amman tabbas wannan damuwar ta doketa sosai dan duk kwanaki bata iya bacci adduar nenan zabin allah kawai takewa kanta zuciyarta chunkushe da bakinciki mara misaltuwa har akayi kiran sallah asuba bata runtsa ba hakan yasa ta mike da kyar ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 21 Duk da ba wani son mlm yahuza take ba amman tunanin rabuwa dashi Kullum yana bibiyar zuciyarta dan duk yadda take qoqarin ta yakicesa daga tunaninta abun ya cutura ba dan komai ba sai dan tsananin kirkinsa da tausayinsa gareta komai na duniya ya fitar mata a rai hatta zaman gidansu ya fita ranta saboda Harare hararen da take sha daga kowace fuskar ta mutan gidan wanda hakan yasa ta kasa samun sukunu ta rasa da me zataji da kwace mata saurayi da suka yi ko kuwa da nemanta da fitina da suke yi ?." Tana kwance shiru akan katifa kamar mai barci alhalin ba baccin take ba. aunty ta leko d'akin tana kiran sunanta "princes baki ta shi bane ? tasan dole ta kasan tashi saboda abinda ya faru dole zai hana zuciyarta sukuni ."ahankali maryama ta yunkura ta mike daga kwanciyar da tayi ta ari murmushi da sukuni ta dasa a ranta tana cewa "aunty na tashi , tayi haka ne dan kada aunty ta gano har yanzu abinda ya faru yana ranta har yasa ta qara mata zancen addu'ar ma data kwana yi cikin dare ya d'an sanyayyar mata da zuciya, kuma har ranta taji ta samun sauki dan har yanzu data mike tana maimaita adduar Allahuma ajirni fi musibatihi wa aklifini khairan minha yafi sau babu adadi dan bata san iyaka adadin data yi ba , aunty ta riko hannunta cikin nata suka fito zuwa parlour ta zaunar da maryama ta lumshe idanunta cikin sanyayyar muryarta tace "aunty ina after dad ?" "Tun safe ya fita zuwa filin kwallo amman nasan yana kan hanya dawowa yanzu numfashi ta sauke da karfi sakamakon tunawa datai yau asabar ce daman kuma ranar asabar da lahadi sune ranakun daya ware domin zuwa filin kwallo , ta mike tsaye a natse ta nufi hanyar kitchen domin had'a kan kayan wanke wanke ta jiyo sautin muryar aunty tana cewa "ina zaki ?" . "zan shiga kitchen na had'a kayan wanke wanke na wanke ne ." tayi maganar cike da raunin zuciya Kmr zatayi kuka , shiru aunty tayi tana kallonta cike da tausayawa kallo d'aya zaka mata ka fahimci bata cikin natsuwarta da kwanciyar hankali tayi wata muguwar rama " ga abinci akan table ki d'auko kizo ki karya kafin ki fara aiki ." ta sauke numfashi sannan ta rausayar da kwayar idanunta bata jin cin komai amman kuma bazata iya cewa aunty bazata ci ba dan tasan bazata ji dadi ba dan damuwarta damuwar aunty ce , idan ta runtsa aunty ta runtsa ,idan ta kwana Jin motsinta to haka itama bazata runtsa ba ,ta dinga kai kawo kenan a tsakanin d'akinta da nata ." Jikinta a matukar sanyaye ta qarasa inda kular abincin yake ta bud'e ,shiru tayi tana kallon abincin , sai data d'auki second goma tana kallon abincin sannan ta kalli aunty fuskarta d'auke da tambaya "ummah ce ta aiko mana dashi , sanyayyen ajiyar zuciya maryama ta sauke sannan ta d'auko Kula tazo ta zauna kusa da aunty ta fara ci a natse , ba wani abincin kirki taci ba ta rufe kular tana qoqarin mikewa tsaye aunty tace "har kin yi me kenan princess ? " ki koma ki qara cin abinci duk fa kwanakin nan ina lura dake ba wani abinci kirki kike ci ba ,ki taimakeni ki manta da abinda ya faru ga gobe can tana d'aga muna hannu kullum cikin miki addua nake , nayi imani allah bazai barki haka ba zai kawo miki wani mafi alkhairi." "Wallahi aunty na koshi ne sannan idan ban hakura ba ya zanyi aunty ? nasan haka Allah yaga dama dani kuma na kar'bi qaddarata ni kawai mlm yahuza nake tausayawa domin duk ranar da zai dawo haiyacinsa sai yayi kukan bakinciki abinda ya faru , tana gama fadar' haka ta shige kitchen ta ajiye kular abincin da taci ta rage ta fara da had'a kan kayan wanke wanke ta wanke sannan ta share d'akunansu ta fito da sharar har tsakar gidansu domin kasancewar weekend ce kuma daman ta saba hakan a duk ranar weekend ." Lokacin data fito duk mutanen gidan suna zaune suna hira ganinta suka hau fad'a fad'ensu da suka saba akanta musamman aunty salma da aunty hassana da yaranta kaulat da Islam dan ita sakina shiru tayi tana sauraronsu haka ma shukura sai dai duk lokacin da suka had'a ido da shukura sai ta zabga mata harara ,sai dai allah da ikonshi sam bata ji komai game da abinda tai mata ba illah iyaka tausayin mlm yahuza dana mahaifiyarta dake ranta ,adadin soyayyar aunty gareshi mai yawa ce, domin shine saurayi na farko da aunty taji ta gamsu dashi ,shine mutumin da rabuwarsu ta ta'ba zuciyarta ,shine wanda har ta tsaya tayi mgn akan ba'a mata adalci ba duk sanda yazo kuwa sakon gaisuwarta zuwa gareshi kad'ai ta kai ashirin, banda yabo da qara mata kwarin gwaiwa da take mata akanshi." Bayan ta gama aikinta taje tayi wanka ta shirya kanta cikin Jallabiya maron touch of white ta d'aure gashin kanta da rebbon kasancewar tana da yalwan gashi mai tsoho sannan tasa mayafin jallabiyar ta daure kanta ,tana zaune kusa da aunty yayinda hanuta Ke rike da reza ta d'aura kafarta d'aya akan cinyarta tana yanke kunbunan kafafunta suna hira da aunty inda take fad'awa mahaifiyarta tana son zata 1829 super market siyan abubuwan bukatanta ,aunty ta amince tace "sai da yamma kenan zaki ?"a'a idan after dad ya dawo yanzu zamu je tare dashi "princess me yasa bakya iya zuwa koina sai tare da habib ne ?" wallahi aunty bana jin dadi tafiya ni kadai ne sai naji Kmr zaa saceni bare irin wurare nan da jama'a suke cika Kinsan ni fa yawon mutane na matukar tsoratani." "ai na sani princess amman dai ya dace ki saba da yin wasu abubuwa Ke kad'ai saboda kinsan wata rana zakiyi aure gashi kinsa habib aranki dayawa karki manta habib nmj ne shi din d'anuwan wasu ne tunda nan gaba aure zaiyi " " babu wacce ta isa ta shiga tsakanina da 'yaruwata , babu wannan matar a nan gidan duniya wannan shine sallama da habib yayi sannan ya shigo parlour'n sosai ya furta sallama ." atare maryama da aunty suka amsa masa maryama ta d'ago kwayar idanunta daga abinda take ta zuba masa tana sakar masa murmushin farinciki yana tsaye sanye da wondo da riga na yan kwallo na kamfanin arsenal kayan sun amshi jikinsa sosai ,suna matukar kama da habib sosai abu d'aya ne ya bambamtasu shine launin fata shi fari ne sol yayinda ita kuma ta kasance chocolate colour ." Aunty tayi murmushi tana dubansa tana sake maimaita maganarta "to ai gsky ne kai d'anuwan wasu ne mana ,dan girma Allah aunty ki daina furta cewa ni din d'anuwan wasu ne , wasu suwa kenan ? "yan'uwan matar da zaka aura mana ta bashi amsa da haka tana kunshe dariyarta "dan girman allah ki daina fad'ar wannan mgnr nifa babu matar data isa ta juyani ,haka zata ganmu ta barmu mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka faro babu wacce ta isa ta raba mu ko shiga tsakaninmu bakiji sunan da nake kiranta dashi ba bugun zuciyata ? bani da kowa sai ke daita , uwa d'aya uba d'aya , jini d'aya ina jinta araina fiyye da komai dake cikin duniyar nan "dan allah kama mana baki zaka cika mutane da dadin baki har ka girma kayi auren muga yanayinka ,amman a yanzu babu abinda zaka fad'a na yarda da kai nawa nawa suka cika baki irin naka a karshe ..." "A'a aunty akwai shakuwa mai karfi atsakanina da habib ai duk wacce tace zata shiga tsakanin mu allah ma bazai barta ba bare bana tunaninta hakan ,shi kansa ma bazai d'auko mana matar da zata rabamu ba , matar da ma ni da kaina zan zaba masa inji cewar maryama ta fad'a tana murmushi "yauwa heartbeat fad'awa male taji da kyau, nima koda wasa bazan kawo irin wannan matar ba ,sai ma wacce heartbeat ta za'ba min Kmr yadda zan za'ba mata miji anan gaba yana fad'ar haka yasa kai zai shiga bayi maryama tace "karka dade zaka rakani 1829 "okay ki shirya kafin na fito ya qarasa shigewa ciki ta mike tsam tana cewa aunty "bari naje na sake shirya na fito ." ta shirya cikin wata doguwar rigar atamfa yellow touch of black atamfar ba wata sabuwa bace dan ta dan kode sai dai fés take agoge sai takalmi flat kasancewar maryama mayar saka flat ce cikin kankanin lokacin habib ya fito yana kiranta yana d'aura agogo a tsintsiyar hannunsa na gama ke nake jira fa "ganin nan fitowa nima na gama hijab kawai zan saka da nikaf ,byn second biyar ta fito suka yiwa aunty sallama "sai mun dawo aunty ." " to sai kun dawo Allah ya tsare min ku habib ka kular min da yarinya na baka amanarta yayi murmushi yana cewa "to ni kuma wa zai kular miki dani ? ."kai wannan yaro wannan yaro akwai manyamce ku dai je Allah ya tsare karku dade suka fice suna fitowa suka hango yaya sadam a haraban gidan hannusa daya rungume a qirjinsa yana waya da murmushi akan fuskarshi suka gaishesa hannu kawai ya d'aga masu suka wucesa ." Basu suka dawo gidan ba sai daf da magariba habib ya wuce massalaci maryama ta cire nikaf dinta tare da hijab ta fad'a bayi domin yin alwala bayan ta idar da sallah suna zaune sai ga dan sako daga umma cewar tazo babu ' bata lokaci ta mike ta nufi side dinta bakinta d'auke sallama ta shiga a natse kamar koda yaushe umma tana zaune a parlour'n gefenta yaya sadam ne zaune ya d'aura kafafuwansa duka a saman table yayi crossing leg's dinsa suka amsa mata sallamar ,cike da girmamawa ta gaishesu sannan ta samu waje ta zauna tana fuskantar ummah " . "yauwa maryama gobe idan Allah ya kaimu zamuyi baki daga cikin gari zasu zo Ina son dan allah gobe da safe kizo ki tayani aikin kaji dazu na aika kizo aka ce kin fita tare da habib har na aka Islam ta siyo min kayan miya ina ganin gobe ma tare daita da sakina zaku tayani aiki ." "To shikenan ummah Allah ya kaimu zuwa karfe goma yayi ko karfe nawa kike bukatar nazo"? tayi mgnr cikin jin kunya ,"eh to zuwa tara ma yayi ,maryama ta d'an jima suna hira da umma yayinda sadam Ke waya."ahankali ta mike tai mata sallama ta dawo side dinsu tana sheidawa mahaifiyarta bukatar ummah dan haka bata tsaya yin wata doguwar hira ba dan lokaci ma ya fara tafiya kai tsaye taje tayi sallah isha'i ta kwanta bacci dan ta samu ta tashi da wuri ." washegari tun bakwai na safe ta tashi ta fara da gyara d'akunan su karfe takwas da rabi ta kammala da aikinta na yau da kullum sannan ta nufi side din ummah ta fara kama mata aiki sakina da Islam na zaune basu da ma alamun saka hannu har sai da yaya sadam ya buga masu tsawa sannan Islam da sakina suka kama mata aikin kajin, saboda ganin aikin da maryama take yayi mata yawa , wanda ita ko ajikinta dan ko ita kad'ai aka bari da aikin zata kammala komai ta tashi ." d'aya bayan d'aya mutanen gidan ke shigowa hatta baba gali sai daya shigo cikin tsananin murna da zuwa bakin da zasuyi wanda ita maryama aranta take raya irin bakin da umma zatayi hakika ko su waye lallai masu matsayine a gun kowa dake cikin gidan tunda take a gidan bata ta'ba ganin hakan daga garesu ba, baya farincikin da suke ciki har da hidmar wanda ke nuna wani mai matsayi ne zai zo ." Sosai ta kasa kunnuwanta tana son ko kad'an taji irin bakin da zasu zo amman bataji komai ba sai dai ummah da aunty hasana da aunty salma suna ta hira akan bakon da alamun sun san wanda zai zo alhji alqasim maude kenan yaushe rabon shi da kasar nan?". "Ke ai kudi sunyi wallahi dan baki ta'ba zuwa gidansa ba wannan yar wayewar da kike ganin kina dashi sai kin nemeta kin rasa inji cewar ummah ,aunty hassana tayi murmushi cike da jin dadi "haka naji abakin babansu sakina ya ta'ba zuwa tare da abban sadam allah ya jikinsa da rahma yace aljannar duniya ne gidansa kamar ba qasan nan yake ba su kansu mutanen unguwar da yayi ginin kallon gidan suke ."aunty salma ta fad'a tana tafa hannuwanta ." Sai yanzu maryama ta gane waye zai zo abokin abban sadam ne wanda sukayi karatu tare tun daga primary har zuwa diploma har suka girma sukayi aure dake shi alhji alqasim maude yayan mahaifiyarsa yana siyasa shi ya samammarsa shcolaship zuwa qasar india ya wuce tare da matarsa wannan ya dan yanke zumuncin abban sadam dashi sannan mutuwa ta qarasa gabadaya sai dai jin rasuwarsa ya mugun d'aga masa hankali sosai ." mutuwarsa ya dawo da zumuncinsu ya d'aure sosai shine ma ya d'auki nauyin karatun yaya sadam har ya qare karatu kuma shine mutumin daya samammar masa aikin da yake yi ahalin yanzu a awaf ,alhj alqasim maude mutun ne mai kirkin gaske da sanin darajan mutune da taimakawa talakawa a yadda ta samu labari duk ya kwashe ya'yan yan'uwa zuwa kasashen duniya wasu na karatu wasu na kasuwanci shine ma ya bud'ewa abban sadam gidan buredi kuma yana taimaka masa a duk sanda yazo qasar " Umma ta mike tsaye rike da wayarta sakamakon qarar data d'auka ta nufi hanyar shiga side dinta dake a tsakar gida suke aiki aunty salma na gani ta tashi tace "sakina Islam ku cire hannunku haka nan ku huta ku barwa yar wahala ta cigaba da aiki tunda dama ita ta saba aikin neman suna da neman gindin zama ,wallahi ba ai kin kyauta salma daman tun dazu nake son dakatar dasu su bar shegiya yar wahala ta cigaba a haka rayuwarta zata ware bauta ,maryama ta kallesu batare data ji zafin maganarsu ba, dan aiki kam matukar na umma ne zatayi shi sai inda karfinta ya qare ,tayi nasu ma da basu da aiki sai nacin zarafinta bare na umma ,ta cigaba da aikinta ta dauki wata roba ta qarasa inda korfot yake ta wanke shikafar dake ciki ta bud'e tukunyar dake kai ta zuba shimkafar cikin ruwan zafi tana cikin aiki shukura ta fito daga side dinsu ta zauna adaidai lokacin umma ta fito ." Aunty hassana da aunty salma har ma da ya'yansu suna hira ummah ta kalli sakina da shukura da islam zaune suna tayasu hira ta kalli maryama dake faman dikar aiki "a'a ya zaku bar maryama da aiki ita kadai Ke shukura sakina islam kusa hannu kuyi tare mana na gayyatoku ne dan kutayani aiki ba dan ku zauna kuyi hira ba ,maryama ta fahimci maganar ba dasu shukura kadai ummah tayi ba har dasu aunt hassana tayi cikin rashin son aiki suka qaraso inda take gyara kaji shukura na kunkuni wanda bazai kai ga kunne ummah ba , maryama tace "kinga shukura idan baza kiyi ba ki koma ki cigaba da zamanki idan ma gbdy bazakuyi ba ku barshi duk zanyi dan kawai an sakaki aiki zaki dinga wa ummah kunkuni ta watso mata harara tare da kallon banza "ke ki kama kanki dan na lura tunda mlm yahuza ya dawo da neman aurensa kaina kike min kallon gani gani nake miki kallon gani gani ko kike min ?" maryama ta fad'a a dan hassale tana hura hanci . "Ban sani ba banza kawai mai bakin jini sai wani 'bare 'bare kike dan kinga mai kudi zai zo , abinda kome zaayi na banza né tunda babu abinda zai haifar sai cigaba da zaman gida da yawon ta zubar wai ana zuwa bautar kasa "Ke ni kike gawa magana "? an gaya miki me zakiyi ?"ai maryama cikin fushi ta zabga mata mari wani qara ta saki tana dafe kuncinta wanda yasa aunty salma da duk wanda suke wajen suka juyo zuwa inda suke ita kanta irin qarar da shukura ta saki sai da gabanta ya fadi ta tabbatar yau ta dibowa kanta ruwan dafa kanta "kutumar uban can me tayi miki kika zabga mata mari haka ?"aunty salma ce akan maryama take neman ba'asi cike da maseefa." Maryama tayi shiru tana datasanin Marin datai mata hakan shi ya fusata aunty salma bata tsaya wata wata ba ta zabgawa maryama nata mari har biyu a kowani kunci "idan dadi né kema kiji ina dalili daga tazo ta tayaki aikin wahala sai mari jakar gidan ubanki ce ? taja hannunta zuwa kofar dakinsu tana share mata ruwan figar kajin data goga mata ." Ummah tace "maryama me ya hadaku har daya kaiki ga marinta ? tayi shiru tana shayen zafin marin dan bazata iya fad'a mata bakaken maganganun data fad'a mata ba kawai ta rufe fuskarta saboda tuttukin bakinciki da zuciyarta Ke mata nan da nan kuka ya kwace mata umma ta qaraso kusa daita "kinsan kema uwarta bazata barki ba me yasa kikasa hannunki ajikin shukura ?sakina kanta ta tausaya mata tana son tayi mgn dan kare maryama da sheidawa ummah cewar ba laifin maryama bane laifin shukura né amman ta kasa ." "kinsan halinta ya kamata ki dinga kiyayye duk abinda zai hadaku daita da yaranta ni wallahi nayi danasani ma sakasu cikin aikina kinga sakina tashi ki bisu kuje kema Islam jeki na gode kema hassana wuce idan bakin sun qaraso kwazo ku gaisa " kukanta ya fiyye mata maganar ummah , bata cewa ummah komai ba tana tsaye akanta ita kuma tana cigaba da kukanta ta share mata hawaye "kiyi hakuri kinji Allah zai saka miki maryama bata ce mata komai ba ta cigaba da aiki datasata domin tana ganin hakan shine zai fiyye mata akan kukan da take ." Karfe tara da minti arba'in da daya daidai bakin suka shigo cikin unguwarsu cikin wata qatotuwa Jeep mutun uku ne a cikin matarshi da kuma shi kanshi alhj alqasim maude sai mai tuka su inda baba gali da yaya sadam suka fito tuni tsayuwar jiransu da sauri baba gali ya qarasa ya bude kofar da alhj alqasim maude yake da murmushi cike da kulawa suka gaisa sosai." Alhj alqasim maude ya rike hannun baba gali yana cewa "Kai amma an jima ba hadu ba, ya jama'a ya iyali.?"baba ya ce,"duk lafiyarsu qalau barkanka da zuwa ya hanya? da irin wannan gaisuwa matarsa Hajiya mustafshir ta fito daga motar suka gaisa da baba gali cikin kulawa, sannan alhji alqasim ya rungume yaya sadam ajikinsa cike da farinciki dan duk sanda ya gansa yana jin farinciki sakamakon kamaninsa da mahaifinsa "sannu dana fatan kana lafiya ya fad'a yana shafa bayan yaya sadam ya dan zame kadan ya gaishesa "barkanku da zuwa dady da fatan baku sha wahala ba ?"babu wata wahala sadam sukai masu jagora zuwa cikin gida ." kai tsaye babban falon ummah wanda aka qawatashi babu laifi anan abban sadam yake saukar bakinshi kujeru set guda zagaye a dakin sai dan teble a tsakiya na glass , parlour ya sha gyara har da turaran wuta kala hudu maryama ta saka a kowace kusarwa na falon ,suka zauna ana qara gaisawa da tambayar mutanen gidan hajiya mustafshira tana dan duba wajen tana murmushi itama tana dan ta'ba hira umma ta fito daga dakinta maryama na zaune gefe daya kuma aunty salma ce da sakina har ma da shukura da islam duk komai an gama shiryashi daidai ta yadda duk wanda ya gani bazai raina ba "maryama ki kawo wa baki abinda muka yi ta yunkura zata tashi islam tayi sauri ta dauka batare da an bata izini ba ta wuce dakin da farantin dake da kayan ." Hakan yasa ta koma ta zauna batace komai ba sai dai ummah tace taje wajen baban yara mai Shgo zai bata sako dan haka ta fasa zaman ta gyara zaman hijab dinta ta fice daga falon roban ruwan faro ne guda shida wanda suka dauki sanyi da kwalbar multina shima guda shida ya saka mata acikin leda baka ta nufo ummah bata shiga dakin da bakin suke ba tana zaune suna hira da aunty data iske zaune kusa daita da jamar gidan tace "yauwa diyar albarka ki kai masu amman kawo mugani islam je dauko wadan can kofunan na glass acikin dakina cikin sauri taje ta dauko ta hada da bakar ledar da maryama ta shigo dashi taje ta kai hakan kuwa yayiwa aunty hassana dadi dan tafi son ace islam ce Ke kai kawo a masaukin bakin." ita kuwa maryama ta rasa me yasa take son shiga dakin har da zalamarta aunty hassana da yayanta biyu kaulat da islam suka shiga suka gaisa sun dan jima aciki sannan suka fito sannnan ummah da aunty suka shiga bayan wasu mintuna aunty ta fito ita kadai zata wuce har maryam ta mike zata bita su koma side dinsu tare , aunty ta dakatar daita " ki tsaya idan ummah ta fito bata ganki ba zata damu ko bama haka ba dole Kinsan zata nemeki ." "to ! kawai ta furta ta koma ta zauna bata shiga dakin ba dan ita a ganinta babu abinda zai kai ta ciki zama gurin bai mata ba dan harare hararen da take samu daga yammanta ta mike ta shiga dakin ummah tayi kwanciyarta duk da tana son ganin bakin amman haka ta hakura tana jin su sakina suna santin bakin fad'ar haduwar hjy mustafshira da irin kayan alfarmar da take sanye dashi ita dai shiru tayi bata damu ba domin ko sun tafi basu ga juna ba ita ba damuwa zatayi ba dan ganinta haduwarsu bazai wani qareta da komai ba ." Kusan karfe uku saura suna hira dasu ummah da baba gali har ma da yaya sadam suka fito domin niyyar tafiya suka tsaya a falo inda jamar gidan suke zaune aunty salma da ya'yanta haka ma aunty hassana domin suyi sallama dasu "amman gsky yaranku basu da hayaniya amman dai duk sun yi karatu ko "? Murmushi baba gali yayi "Kai kasani dole suyi karatu domin sanin amfaninshi ita wannan tuni ta gama secondary kuma ina son rai zata cigaba ya nuna sakina ." alhj alqasim yace "Allah sarki gsky karatu kam yana da matukar mahimanci kayi qoqarin da ka bar yaranka sukayi karatu dan da sun biyoka da rashin son karatu da abun bai yi kyau ba dan wannsn zamanin sai da karatu sukai dariya gbdy sakamakon jin abinda alhj alqasim ya fad'a "ai gsky ne yayanshi yafi sa son karatu sosai allah dai bai yi zai yi karatu mai zurfi bane Allah ya jikansa "Ameen hjy mustafshira ta amsa tare da jamar wajen ." Alhaji alqasim ya nuna shukura "wannan yarinyar ussein ce ko ?"uhm uhm bata ita bace wannan diyata ce ta uku ita ina ganin tana bangarensu baba gali ya bashi amsa da haka ,allah sarki allah ya jikinsa shima yasa suna aljanna Ameen ai kasan ita maryama bata fiyye son shiga cikin mutane ba mussaman idan bakin fuska ne allah ya zuba mata kunya gashi ita har ta qare karatunta na digree yanzu haka ta fara bautar qasa ta kuma yi saukar alquranin mai girma tana da hadda uzu arbain da wani abu akanta ." "kai masha allah a she dai kuna da zakakura acikin dangi ?"sukayi dariya kawai suna yiwa ussein addau "gsky ussein yayi saa arayuwarsa duk wannan rashin jin maganar daya ta'ba amman allah ya albarkacesa da samun yarinya mai kokari haka "? wallahi abun na allah ne yaransa ma duk masu natsuwa sai ma ka gansu, yabon ummah sam bai yi kowannensu dadi ba amman babu yadda zasu yi tunda umma ce kuma sun san adalilin ta suka zo gidan"ai ina qaunar ussein domin shi din mutun ne mai barkwanci da son mutane ai naso na dawo qasar nan na iske shi a raye maryama tana cikin dakin ummah duk tana jin maganar Alhaji alqasim da ummah tana jin matukar qaunar mahaifinta alokacin da bataji tahirinsu da mahaifiyarta ba amman daga baya dataji komai sai ta daina kewar babanta duk da ba wani saninsa tayi ba dan duk lokacin data tunashi sai damuwarta ta ninku acikin zuciyarta ganinta shine ya raba aunty da yanuwata ,bugu da qari yadda kowa yasan mahaifinta baya jin magana." kuka taji ya kwace mata "Ke shukura je ki kira min maryama taí Jim dan tasan tana dakin ummah amman dan bakinciki karta gaisa da bakin yasa ta fice Jim kadan ta dawo tace "aunty tace bata nan ,bata nan kuma ?ummah ta furta a fili tana qoqarin neman layin aunty can bayan Kmr second goma maryama tajiyo muryar ummah na kiran sunanta "maryama maryama !! hakan yasa tai saurin mikewa ta share idanunta da gefen hijab dinta ta fito ko hada idanu ta kasa da bakin saboda tsura mata idanun da matarshi da shi kanshi Alhaji alqasim sukayi ." "Haka diyar ussein ta girma lallai dan mutun sai allah ussein din guda nawa yake har da 'ya haka ?ita dai maryama gaisuwa ce kawai nata domin bata da abun cewa hjy mustafshira ta shafa kanta sannunki kinji ya aiki da fatan yana tafiyar miki yadda ya kamata kyakkyawa dake tubarkalla masha allah shine kika fitowa kizo mu gaisa ko ? Ta dan yi murmushi ta dago kanta tana kallonta amamn still ta kasa cewa komai "me ya sameki kamar kuka naga kinyi bata san hawaye na makale da idanunta ba da sauri tasa gefen hijab dinta tana sharewa hjy mustafshira ta qaraso ta dagata daga tsugunno datayi ta dan rungumeta ajikinta "babu mamakin maganr da mukayi ta mahaifinta ce tasa ta kuka ita kanta ummah ta shiga damuwar ganin hawayenta ,ki daina kuka kinji allah zai kai rahama kabarinsa Kiyi hakuri ki cigaba da yi masa addaua shi kanshi yana can yana alfahari da samu diya kamarki mai riko da addini kai kawai ta daga mata tana qara goge kwallar data taru a idanunta aunty salma da aunty hassana da yaransu kuwa babu abinda suke aikin yi sai harare harare iri iri da bakinciki ." "Ai mahaifiyar ce ta shigo dazu muka gaisa ko ? alhj alqasim ya tambaya yana duban baba gali "Eh itace baba gali yayi saurin fad'ar haka ai tunda ussein ya mutu taki koma wajen danginta bare tayi wani auren ta cigaba da zama anan ai kasan yadda akayi aure danginta saboda rashin son useein din suka sall.." "Eh nasan komai abban sadam duk ya fad'a min alokacin amman dai nayi tunanin komai ya wuce zuwa yanzu Alhj alqasim ya katse maganar ya zura hannu cikin aljihunsa ya zaro kudi bandir daya na yan dubu dubu ya damka ma maryama taki amsa tare da cewa ya barshi sai ummah ce ta karba ." Gabadaya sai daya bisu da kudi yana cewa" in sha allahu zan sake dawowa nan kusa tare da yarana gbdy asan juna kafin mu tattara mu bar qasar yayi gaba yaya sadam ya bishi da baba gali hajiya mustafshira bata saki hannun maryama har bakin mota ita dai bata ce komai ba binta kawai take da alamun tausayinta ne ya game jikinta sai faman hakuri take bata sukai sallama tayi mata godiya sosai suka shiga mota suka tafi ." Ita da yaya sadam da baba gali suka koma gida kai tsaye dakinsu ta nufa da yamma ummah ta shigo ta mika wa aunty kyautar kudin data samu aunty tace "a'a bazan karba ba ummah saboda me balkisu ? Ki rike kawai domin kece mai yin hidima acikin gidan nan bare ma akanmu wannan ai ba wani abu bane amana ce rike a hannuna, ni dai kawai ki rike ." "to ki cire wani abu aciki aunty tasa hannu ta zari dubu daya ummah ta girgiza kai tana cewa allah baki isa ba kin kuwa san ko nawa ne dubu dari ne fa shine zaki cire dubu daya ta raba kudin biyu ta mika mata rabi allah sunyi yawa ummah bazan karba ba nifa ba butulu bace nasan ya kamata ta cire naira dubu biyar tana cewa wallahi iya su sun isa allah yasa albarka rantsuwar datayi yasa ummah bata qara cewa komai ba ta mike ta koma wajenta ." Da yammacin ranar maryama ta shirya zata wuce makaranta islamiyya "aunty ni na wuce makaranta sai kin dawo princess idan kinga malam yahuza ki gaishe min dashi maryama tayi shiru tana kallonta "Eh haka na fad'a har yanzu zuciyata tana qaunarsa dan haka kice masa ina gaishesa "to ! kawai maryam ta fad'a tasa kai ta wuce zuciyarta cunkushe da damuwar abinda baba gali yayi shi kansa alhj alqasim din yasan maganar bata dace ba shiyasa ya katsesa ". ta kusan kai bakin get din Ardus salam ta hango mlm yahuza yana tahowa ta hanya mai fitar da mutun afanla ta cigaba da tafiya a natse adaidai lokaci daya suka iso bakin get ta gaishesa ya amsa fuskarshi babu annuri sosai bata damu ba domin sakon aunty kawai take son isarwa "aunty tace tana gaisheka "na gode kawai yace yayi gaba ya barta tsaye abun yaso ya bata haushi amman tunawa datai baya cikin haiyacinsa yasa bata ji komai ba sai dai ta kasa cigaba da daga kafafuwanta tayi shiru kawai bata san a tsaye take ba ashe ta kasa tafiya ne sai da wata kawarta lauratu tazo wucewa . "Ke kuwa tsayuwar me kike anan kamar mai jiran wani nan ta diririce "Ke na hango ai kin kusan qarasowa shi yasa na tsaya ta dai jita ne kawai amman alamunta basu nuna hakan ba suka shiga makaranta tare koda mlm yahuza ya shigo ajinsu domin kara masu karatu ko inda take baya kallo sabanin da in har yana cikin ajin murmushinsa kadai ya isheta bayan an tashi ta dan tsaya hira da kawayenta koda suka rabu ta nufi hanyar inda suke tsayawa dashi anan ta ganshi shi da shukura ko kunya babu tasan kuma duk sharrin shukura ne dan ta gansu sosai ne hakan bai dameta ba tunda idan kayi da kyau zaka ga da kyau idan ma akasin haka kayi zaka girbi abinda ka shuka ta wucesu cikin fushin zuciya har ta isa gida abun na cinta arai wai yanzu duk abinda mlm yahuza yake fad'a mata akan soyayyarsa ya tashi abanza ya koma kan shukura hakika basu yi mata adalci ba amman ta barwa allah komai ." ******* Zaune mr ata yake acikin masaukinsa yana jiran abokinsa bashir sosai yayi kyau sai dai ace masha allah dan yanayin gyara tattare da kulawar da jikinsa yake samu ya hana shekarunsa bayyyana dan idan ba kaji shekarunsa ba bazaka ta'ba cewa ya kai 40 wani abu ba , zaka dauka shekarunsa basu wuce talatin a duniya ba fatar jikinsa kawai ka kalla kasan kudi suna aiki ba karya haka ma kayan jikinsa tun daga kan wondo rigarsa takalminsa har zuwa agogon dake makale a hannunsa dukansu tsadaddun gaske né ,shine ma ya zana da kansa kaf duniya su uku kawai ke da irinsa shi mb sai bashir abokinsa rolex ne mai shegn kyau ." ya hade rai sosai kana kallonsa kasan yana cikin damuwa mai tsanani maganganun sweetheart dinsa yake tunowa a wayar da sukai daita a wannin data gabata. inda take sake jadda masa alqawarin da yayi mata kafin ya bar qasar , koda yayi qoqarin sake lallabata cewa tayi "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudararka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ta fad'a tana kashe wayarta." zuciyarsa ta sake cika da tashin hankali "ina zai ma iya karya alqawarin da yayi sweetheart dinsa ? ya shiru kawai yana ciza gefen lips dinsa ,ina bazai iya ba bazai iya karyar mata da zuciya ba ita din jigon rayuwarsa ce zai iya yin komai domin yaga ya faranta mata kamar yadda yasan zata iya sadaukar masa da faricinta haka shima a yanzu ma da yaji muryarta tausayinta ya cika zuciyarsa " ahankali ya daga tsumammun idanunshi ya sauke su akan agogon dake daure a hannunsa 11:44 am tsaki yaja "what a heck sannan ya gyara zamansa "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudarar ka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ." "shine kawai abinda yake ta yawo acikin kwa kwaluwarsa "why sweetheart ?me yasa kika kasa fahimtata instead ki barni tunda na nuna bana son auren nan ya allah ka kawo dalilin da zai sa a fasa auren nan na huta tsaki yayi inda fuskar princess keta masa yawo a cikin idanunsa da sauri ya runtse idanunshi dan a halin yanzu baya son ko tunawa daita ahankali akayi knocking din kofar parlour'n yana daga kwance yayi nisa cikin tunani shiru bashiri yana jiran a bashi izinin shiga amman shiru daya daga cikin masu tsaronsa ya dan leko dakin yana ringine amman bai bawa mai yin knocking din izinin shiga ba ." Dan haka ya dawo ya bawa bashir izinin ya shiga dan ya rigada yasan ko waye bashir din a wajensa kuma tun safe ya sheida masu zuwansa,bash ya shigo parlour'n bakinsa dauke da sallama shiru mr ata bai amsa ba ."bashir ya zauna yana fuskantarshi sai dai kusan mintuna goma mr ata bai bude kwayar idanunshi akan bashir ba haka zalika bai ma san da shigowarsa ba ya yunkura ya tashi ya isa inda mr ata yake ya dafa shi a matukar zuciye ya bude idanunshi da niyyar saukewa wanda ya dafa shi maseefa ganin amininsa yasa ya sauke naunayen ajiyar zuciya "kai mutumina meke damunka ne haka duk kayi wani irin ina lura da kai tunda ka sauka a qasar nan kake yawon tunani ?bashir ya fad'a tare da zama a gefensa kallonsa yayi zuciyarsa na zafi "yaushe ka shigo kuma me yasa ka shigo baka nemi izinina ba ?" Ajiyar zuciya bashir ya sauke sannan yace "kai dai anyi dan iska ina tmbyarka kana tmbyta yanzu dai fara bani amsar tmbyata tukun sai na baka taka numfashi ya sauke mai zafi ,kai dai bari kawai ina cikin rudani auren dole zaa min , bashir ya zaro idanuwa "Ata din dana sani zaawa auren dole ? no no it can be possible ya qarasa mgnr yana dan murmushi,kai ma dai ka fadi haka wai kamata zaayiwa auren dole kamar muna in does day nan ya kwashe komai ya fad'a ma bashir har da alqawarin da yayi wa mami , wallahi bana son yarinyar nan kiyayyarta bazata misaltu a zuciyata ba gbdy zuciyata bata bugawa idan na ganta, kaga mutuwa kusa kenan dariya sosai bashir yayi tuni mr ata ya kule kallonsa yayi rai a bace ,kaji min dan iska ina fad'a maka damuwa kana mun dariya to wallahi maza tashi ka bar nan yanzu ." "Sorry my friend hukunci mami ne ya bani dry kai da yanzu bata zatar da wannan hukunci akanka ba haka zaka qare rayuwarka kana yaudarar kanka shin zaka tuna kafin mu rabu da kai last na fad'a maka wannan yarinyar mafarkinka ba mutun bace sannan ka guji ranar da mahaifiyarka zata gaji tayi maka irin wannan auren kace bazatayi ba ?kaso wannan yarinyar marym karkazo hannu kazo kana sonta ta samu dama akanka." " dan Allah bash ka bar wannan maganar ka bar kawo min maganar zan sota ya zaayi na sota ma ?"mr ata ya fad'a cikin tsananin damuwa zan cigaba da rayuwata haka zan bar zuciyata babu kowa cikinta yadda zan cire soyayyar princess a zuciyata bazan bawa kowace mace damar shiga ba sai dai na qare rayuwata haka ,haka dai suka cigaba da tautaunawa bashir na bashi kwarin gwiwar yayiwa mahaifiyarsu biyayya ." Ana sauran kwana hud'u mr ata ya dawo ya kira mami ya sheida mata ai kuwa taji dadi har ta kasa boye murnar ta , ta tattara kan masu aikinta domin su gyara gida da kuma sauya wasu abubuwa dake gidan sakamakon dawowar dan lelenta jirgin karfe hudu daidai na yammaci ranar lahadi zai sauke su tare da babban yaronsa da masu tsaronsa da sukayi tafiyar tare dan haka mami ta hana kowa sakat acikin gidan daga masu aiki har maryama babu wanda ya zauna suna tsaye bisa kafafunsu duk da tun jiya sun yi redy wasu abubuwa da suka san yafi bukata maryam tana wanke hannunta tana qoqarin fitowa daga kitchen sai ga mami abakin kofar kitchen din suka hadu mami ta kalleta da murmushi kwance a fuskarta ." "tun daga parlour nah na biyu nake ji kamshin girki fatan kice kikayi komai da kanki ?Allah mami ki tambayi tabawa duk ni nayi su kawai wanke wanke sukeyi gsky idan duk wannan kamshi daga hannunki ne naji dadi Kwarai da gaske dan tun banga abincin ba miyona ya tsinke muje kawai na fara da jin dandanon girkin kafin adamcy ya qaraso ,ai mami idan kikaci sai kunnenki yayi rawa ,haka né hajiya duk ita tayi gsky babu abinda muka tayata sai wanke kwanuka ,hakika tayi qaqari sosai ." "ai kam yau zan bada maki mai yawa dan tun daga parlour'na nake jiyo kamshi muje suka koma cikin kitchen din tare mami na bude manya kuloli kula farko alkubus da miyar naman rago kula ta biyu shimkafa bastimatic ce da teaw wanda yaji naman kaza sai kula ta uku wanda sakwara ce da miyar egusi wanda yaji ganye ugu da nama da busashen kifi "masha allah mami ta furta a fili "lallai adamcy nah zai ci dadi ,yau kam nasan har da santi zai yi murmushi mrym tayi tana cewa" allah yasa mami allah yasa ya yaba da girkin tayi maganar cikin sanyin murya ,karkiji komai diyata zai yaba ta fada tare da daukar qaramin spoon ta dibi miyar farko ta kai bakinta ". "Woww miyar nan tayi dadi sosai daya bayan daya ta dinga d'an dana miyar tana lumshe idanunta tana santi da yabawa maryam din ,da gaske mami tayi dadi?sosai tayi kawai abu daya ne zan gyara miki shima idan mutun ya kasance mai son cin maggie dayawa a abinci ne bazai ta'ba miki gyara ba "meye shi mami ?ta tmbyeta cikin tsanani damuwa jikinta har rawa yake ,ki natsu ki kwantar da hankalinki ba wani abu bane maggie zaki rage zubawa miya dayawa ,tun daga tafashe kinsa maggie kuma kinga zakiyi amfani da ruwan miya wajen hada miya dan haka baki bukatar zuba maggie dayawa acikin miyarki yanzu kenan maggie yayi yawa ta fada cikin tashin hankali?bawani yawa bane kawai na gyara miki ne dan gaba idan hannunki yana zarcewa a maggie matsala ne." " wannan ne kawai maggie yayi yawa ko duka miyar né ?Ki kwantar da hankalinki kusan duka ne amman karki damu aa mami dole na damu dan wallahi idan yasan ni nayi na shiga uku gara kawai na sake wani ."What ? "mami ta furta tana dubanta babu abinda zaki sake anan haka zai ci har yayi santi ta sauke numfashi tana cewa "amman mami karki ce ni nayi kice kece kikayi dan allah idan yasan ni nayi wallahi karshenta bazai ci ba ,mami ta kalli agogon dake hannunta kinga karki damu muje ki shirya dan jirgin adamcy ya kusan sauka nima bari nayi sauri na shirya kafin a dauko shi yazo yana yiwa mutane naci dan tun jiya yace bazai ci komai ba sai ya dawo ." Mami ta bawa masu aikinta dake tsaye umarnin su fito da kulolin zuwa dinning suna shirya dinning suna hira suka jiyo sallamar hindu gabdaya suka amsa mata kallo daya mami tayi mata ta dauke kanta tana sanye cikin wani irin ado tasha tamkar wacce zata turakar miji cikin ratsatsen lace maron colour touch of green dinki yaji stone ta koina dan hasken fatarta ya sake haskawa sam bataji dadin ganinta ba bata qaunar abinda zai kawowa adamcynta matsala arayuwarsa ta fada mata tayi hakuri dashi ta nuna a fuska duk wata hanya da zata nuna mata ta hakura dashi tayi amman sam kamar bata fahimta ." "Mami fatan kin shirya muje tarbo ya adamcy ,dawa kenan zakuje?hindu tayi shiru tana dubanta ,ai wannan sai dai matarsa ni kam na yafe ,tô shikenan ni bari naje AirPort tarbosa "allah ya tsare sai kin dawo tace ameen mami ta fada haka né dan tasan halin kayanta bata són taje ya disgata cikin mutane amman hindu ba irin mutunen nan masu fahimta bane ."Mami tana kallonta ta juya tana rausaya cike da farinciki kamar wacce akayiwa albishiri da zata mallakinsa taso ta tsaidaita amman ta barta sai da hindu ta fice daga falon sannan mami ta dawo da kallonta ga maryam zan shiga dakina na shirya kema idan kin gama kije ki shirya mrym tace "tô! Sai data tabbatar da komai yayi daidai sannan ta wuce dakinsu inda ta iske nana hauwa'u kwance tana karanta wani hausa novel acikin wayarta mai suna cutar da kai ,har yanzu kina kan karatun nan sister?ina kai ko akwai abinda zan miki né ?bazakiyi shirin tarban ya adam ba gashi har ya kusan sauka koma mace ya sauka ?ta qarasa mgnr tana duba makeken agogon dake manne da bangon dakin ,wannan kuma kece zan tmby dan ni tsakanina dashi sannu da zuwa né ke dai kije yi maryam bata sake cewa komai ta shige bayi Wanka tayi ta fito ta goge jikinta ta zauna akan kujerar mirrow ta d'auko mai ta fara shafawa ahankali haka nan take jin faduwar gaba mai tsanani ,kinyi shiru bazaki shirya ba sai ya shigo mami tazo tana daga miki hankali ta tsaida hannunta akan damtsen hannunta tana kallon nana hauwa'u ta cikin mirrow sai data numfasa sannan ta mike wallahi sister haka nan nake jin mummunar faduwar gaba jikina har rawa yake gabadaya bana cikin natsuwata tunda mami tace zai dawo yau na tsinci kaina cikin damuwa bare gashi na kwabsa kadan a girki mami tace Maggie ya dan só yayi yawa tsorona kar ya tambayi wanda yayi tace nice ta qarasa magana tamkar zata zubar da hawaye ." "gsky kina tare da aiki marsi wai shi yaya dodo ne da Kike jin tsoronsa haka ?numfashi ta fitar da karfi ta mike tana cewa "ban san me yasa wani lokacin kike manta kiyayyarsa gareni ba ,ki daina cewa kiyayya yaya baya kinki halinsa né km kowa yakewa amman kema zuwa yanzu ya kamata ki saba dan da nice dana maidashi man shafawana ,uhm baki san halin wannan yayan naki ba idan yana kin mutun halinsa dabam kiyayyarsa dabam ta fada tana taku har ta qarasa in da Kwabar kayanta yake ta ciro doguwar rigar lace mai shege kyau da tsada sabuwa ce bata taba sakawa ba sai a lokacin bata tsaya yin wata doguwar kwaliya ba ta zauna zaman jiran kiran mami ." Tana zaune ta jiyo hayaniyar shigowar motoci haraban estate din ahankali cikin sanyin jiki ta mike ta isa jikin window dakin ta dage labule ahankali idanunta ya sauka akan motocinsa da motocin ss guda shida inda masu kula da lafiyarsa mutun uku suka fito da sauri mutun daya ya bude masa murfin mota ya fito ya tsaya bisa kafafunsa ." A natse ya soma taku mutane suka sakashi a tsakiya wanda dayawan su yan tarbosa ne yayi matukar kyau sanye cikin riga da wondo na black suit mai tsaida da sheki yayinda sumar kansa Ke kwance luf yana zuba sheki alamun yana samun kulawa haka zalika farinsa ya qara fitowa alamun yana cikin koshin lafiya sai wani ipod dake manne da kunnensa na jin mgn gaba daya mutanen dake tare dashi ya zartasu a komai hasken fata da tsawo cike da Kamala tana tsaye suka gama wuce wa ta lumshe idanunta na second biyar sannan ta bude idanunta ahankali suka sauka akan hindu tsaye fuskarta murtuke cikin bacin rai aranta tace ko me ya bata mata rai ita da tayi kamkamba da shishigin zuwa tarbosa?." "Uhm yanzu haka halin nasa yayi mata nan wani murmushi ya bayyana akan lip's dinta haka nan ta tsinci kanta da jin dadin yanayin dataga hindu ai kin iya shishigi kuma karshen masu irin halinki kenan ajiyar zuciya ta sauke tana sakin labule ta juyo idanunta cikin na nana hauwa'u,"kin gama kallonsa ." "Shi wa ?" "Ya adam !ta bata amsa atakaice,kai haba sister kai haba sister ko gsky Ke na gama karantarki fa kema kin fad'a sawun masu son ya adam kar muyi haka dake sister ."allah ba wasa nake ba kina son shi son ..." nan da nan idanun maryam ya cika da hawaye nana hauwa'u ta zaro ido ke fa matsalata dake kenan saurin kuka kamar wata qaramar yarinya daga na fadi gsky ." "Aa sister wannan ba gsky bace taya zaki fada min haka ?me yasa zan so mutumin da bai sona? nana hauwa'u ta sauko daga saman gado ta dafa kafadanta zaku so juna wuyarta ayi aure muamular miji da mata ya sha bambam da rayuwar waje fatanmu allah yasa ya sauko da wuri ." " sister bazai sauko ba kema Kinsan halinsa yana son mutun ma ya ya qare bare ni da yake jin Kmr ya kasheni ,ni ban san ya zanyi da rayuwata ba gashi kowa son shi yake kalli hindu fa har airport taje tarbosa " kinga matsalata dake kishin maseefa ." "allah ba maganar kishi bane sister da me zan ji da rashin son da bai me ko kuma da yammatan dake sonshi "kyale wannan mahaukaciyar kema Kinsan bazai sota ba dan hk ki saki ranki kisawa ranki kece sauraniya a gidansa in sha allahu kece glashin idanunsa naunayen ajiyar zuciya mrym ta sauke sai lokacin taji natsuwa ajikinta tana damke hannun nana hauwa'u cikin nata "na gode da addua Sister Allah yasa hakan ya kasance ." Gyada kai nana hauwa'u tayi ta zare hannunta ta nufi kofar fita "ni na tafi tarban babban yaya sai kin fito mami na tsaye a tsakiyar parlour'n fuskata dauke da murmushin farincikin dawowar tilon danta yana gama shigowa tsumammun idanunshi ya sauka akanta cikin shiga na alfarma fuskarsa kamar koda yaushe babu annuri amman duk da haka yayi farincikin ganin sweetheart dinsa cikin koshin lafiya atare suka soma daga kafafuwansu domin isowa ga juna suna gama qarasowa yana qoqarin durkusawa mami tayi saurin rike kafafunsa ta rungumeshi ajikinta tana shafa bayansa "sweetheart mun samuku lafiya ?lafiya lau adamcy nah da fatan ka dawo lafiya ? ajiyar zuciya kawai ya sauke ta zaresa ajikinta ta qarasa dashi kan kujera mai zaman mutun uku ta zauna a kusa dashi tana rike da hannunsa rayuwarta né adamcy tana matukar qaunarsa shiyasa yake mata abinda yaga dama ." nana hauwa'u tai masa sannu da zuwa ya amsa da kyar yana zaune mutanen gidan suka dinga shigowa daya byn daya suna masa sannu da zuwa ita kam maryam bata fito ba tana daki ta kwanta rigingine jiran mami ta nemeta mami bata nemita ba har akayi sallah magrib da ishai sai data ga babu alamun mutanensa a falo dashi kansa ata ta fito ta zauna tare da nana hauwa'u da mami aka cigaba da hira daita " Karfe tara daidai mr ata ya sauko cikin blak long sleve da farin wando na shan iska sai kamshi turarensa na Reed ke tashi akoina ajikinsa ya samu waje ya zauna a daya daga cikin kujerun falon yana duban mami dake zaune tana waya nana hauwa'u ta sake gaishesa ya amsa aciki, ganin haka yasa maryam ta bud'e bakinta da kyar cikin in ina "ya..ya sannu da zuwa da fatan ka dawo lafiya ?"banza yayi mata tamkr bai ji abinda ta fada ba nan kuwa yajita sarai sai ma ya dauke idanunshi akan mami ya maida kan wayarsa numfashi ta sauke da karfi ta kama bakinta ." Bayan Kmr mintuna shabiyar ya motsa lip's dinsa da kyar" sweetheart yunwa nake ji cikina har zafi yake murmushi mami tayi allah shiryeka adamcy kullum girma kakeyi amman sai ka dinga abubuwa kamar yaro ya yatsina fuska a gaban uwata nama fi yaron goye ,allah ya shiryeka me zakaci akwai alkubus akwai rice and stew akwai sakwara "rice kawai ya isa okay maryam maza zuba masa ki daura a tray ki kawo masa nan "bana bukatar daga gareta kisa wani yayi min " "Bangane haka ba ? yayi shiru kawai yaki cewa komai duk bakinsa mgnr yake son yi "zaka fara ko daga dawowarka?yaruwarka kuma matar da zaka aura ce kakewa haka ? Allah adamcy ka fita cikin idanuna daga zuwanka zaka fara da bata min rai kuma ya mukayi da kai ?bance ka bar duk wani mugun nufinka a inda ka baro ba ?"yi ...ha ..kuri sweetheart ya fad'a tare da dago kanshi nan take kwayar idanunshi ya shiga cikin na mrym wani mummunar faduwar gaba ya risketa saurin cire nata tayi ilahirin jikinta na daukar rawa "maryam jeki yi abinda na sakaki a tsorace muryarta na rawa tace "to! ta juya ta shige kitchen domin dauko trya Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 22 Saurin mikewa tsaye mr ata yayi ya haura samansa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ransa a dagule yake taka step dan idan akwai yarinyar daya tsana anan duniya to wannan maryam din ce, ji yake kamar ya kasheta ya huta da muguwar tsanar da yayi mata ,mami tabi bayansa da kallo har ya qarasa sauka akan step tana jin zallar bacin rai da bugun zuciya yana shiga d'akin ya cire rigar jikinsa da singlet ya cila kan kujera ya shige bedroom dinsa ." koda maryam ta fito daga kitchen taga wayam babu shi babu alamunsa a inda ta barshi ta kalli nana hauwa'u ta kalli mami fuskarta da alamun tambaya "zuba masa abincin daya buqata ki bishi d'akinsa dashi maryam tai saurin zaro ido waje ,cike da matsanancin tsoro ta shiga girgiza ma mami kai yayinda yanayin bugun da zuciyarta yake ya qaru, yanayin tsoratanta kuwa sai ya baka mamaki idanuwanta ta runtse jin tashin hankalin daya kusantota ." nana hauwa'u ta mike daga inda take zaune ta qaraso inda mrym take tsaye rike da tray mrym bata ankara ba sai jin mutun tayi tsaye kusa daita ta dafa kafad'anta ta bud'e idanuwanta da kyar akan nana hauwa'u "common sister ki sanyawa jikinki natsuwa ki rage wannan tsoron please ".ta fad'a tana riko hannunta ta fara tafiya daita." "Sister bazaki gane bane wallahi ina matukar jin tsoronsa, na sani yanzu dai kiyi abinda mami tace babu abinda zai iya miki keda kike da mami a hannunki ai sai yadda kikayi dashi, da taimakon nana hauwa'u ta had'a komai a tray ta rakata har samansa adaidai bakin kofar shiga parlour'nsa taja ta tsaya tana cewa "ki shiga da kafar dama sannan ki sanyawa jikinki jarumta daga nan ni zan koma "haba sister mu shiga tare mana Kinsan fa bani da wannan jarumtar "rufa min asiri sister kar ya sauke fushinsa akaina gara ke idan yayi anything stupidty zai had'u da mami ni kuwa fa ? komai yayi min yaci lafiya ,kafin mrym tayi wani yunkuri yin magana har nan hauwa'u ta juya ta soma tafiya tana waiwayenta tana karfafa mata gwiwa " Cikin natsuwa ta tura kofar parlour ta shiga bakinta d'auke da sallama taga baya parlour ta had'iye wani yawu daya tsaya mata a makoshi tana qoqarin daidaita numfashinta da natsuwarta ,ahankali ta ajiye tray hannunta akan center table din dake ajiye ta nufi kofar bedroom tayi knocking ahankali saboda tasan baya són hayaniya jin shiru yasa ta sake knocking amman still shiru ". ganin kar abincin yay sanyi ta sake qarawa kanta laifi a wajensa yasa ta murd'a kofar cike da tsananin tsoro da tashin hankali ta shiga idanunta a runtse tare da rufe kofar ta sunkuyar da kanta kasa tana jiran ya balbaleta da ruwan maseefa amman taji shiru .jin shiru yasa ta d'agowa taga baya cikin d'akin wani naunayen ajiyar zuciya ta sauke , kai tsaye kwakwaluwarta ta bata yana cikin d'ayan d'akinsa ." Ahankali ta juya ta fito daga cikin d'akin har tayi taku uku domin isa bakin kofar d'ayan d'akin sai kofar d'akin ya bud'e ya fito daga shi sai gajeren wondon dake sanye ajikinsa a matukar tsorace take kallonsa da kallon murd'add'en jikinsa dake sheki tsabar kulawar da yake samu ."wani wulakantaccen kallo yayi mata mai had'e da harara yasa a tsorace ta d'auke kwayar idanunta akan shi tayi saurin juya masa baya tana neman afuwarsa "am really sorry mami tace na kawo maka abinci .." Tsaki yaja a fili yana kallon bayanta daga inda yake tsaye yana iya hango tashin hankalin da take ciki ya rasa me yasa sweetheart take masa hk ?ya guji cin abinci daga hannun yarinyar amman sai da tasa aka biyosa d'akin dashi kmr dole sai yaci abincin hannu ?"yayiwa kanshi tmby yana mai sake jan wani tsakin ." ta gefenta ya raba ya wuceta ya shige d'ayan bedroom dinsa dan ganinsa tsayawa ma inda take asara né ,kusan mintuna shabiyar ya sake fitowa a tunaninsa ta fita amman abun mamaki tana nan tsaye Kmr wata tsohuwar soja , ya ja tsaki ya zauna akan kujera ya kunna computer dinsa ya shiga yanar gizo fannin kasuwancinsa . ta cigaba da tsayuwa sai dai ta rasa yadda zatayi masa magana yaci abinci sai ta motsa labbanta zata masa magana amman tsoronsa ya hanata ." tana tsaye aka fara kiran wayoyinsa yana amsa kira ,duk abinda yake ko ajikinsa dan babu ruwansa da tsayuwarta ya cigaba da abinda yake tana kallonsa ta kasan idanunta ya kashe computer ya kwashe wayoyinsa ya d'auki rigarsa ya rataya a kafad'ansa ya fito ya barta tsaye ya sauko kasa har lokacin mami na zaune ita kad'ai ." Ya zauna batare da yace komai ba , mrym ba tayi fushi ba dan daman ita ba mai saurin fushi bace , kafin kaga fushinta da wahala sai dai akwai zuciya ,zuciyar ma yana dadewa bai motsa ba amman idan ya motsa babu kyau ,ta d'auki tray data shigo dashi ta fito, a parlour ta iskeshi zaune yana shan kamshi inda kasan wani jinin sarauta yana daddana waya ,har gabansa ta qaraso ta ajiye tray din akan table din dake gabansa ta bud'e masa kular abinci cike da tsoro dan kar tayi laifi ta d'auki ruwan dake kan tray ta juya a natse ta shiga kitchen ta bud'e fridge ta canza masa da wani ruwa mai dan sanyi kad'an tazo ta ajiye masa "ga abincin ! Biyayyarta na matukar burgesa domin shi din mutun ne mai tsananin son ya juya duk wanda yake karkashinsa most especially mace , yanayin tsoronsa da biyayyarta yayi ,matsalar dai baya sonta , mami dake zaune kuwa kallonta kawai take yadda take komai a natse cike da kulawa da tsoro da gudun kartayi laifi amman sam adamcy bai damu da duk abinda take ba hasalima hankalinsa da natsuwarsa basa gareta ." duk yadda mami take són mrym din ta kasance a yanzu tayi babu wani abu d'aya saura ga dukkanin alamun zata kular mata da adamcy yadda ya kamata , daman kuma irin macen data kamacesa kenan mai tsananin biyayya da hakuri da gudun 'bacin ransa saboda yanayinsa ,maryam bata tsaya ba ta nufi d'akinsu inda ta iske nana hauwa'u kwance tana chart, ita kam zama tayi shiru cike da damuwa ita kadai tasan halin damuwar da take ciki duk yadda take son waya a wannan lokacin ya d'an fara fita kanta , dan ko ta d'auki wayarta dan shiga what's app bata 'barkata komai ,hakan friend's dinta zasu yita mata mgn har su gaji su hakura ." Mami ta tashi daga mazauninta ta dawo kusa dashi ta zauna ta riko hannunsa d'aya cikin nata tana dubansa cike da kulawa dan bazata iya fushi dashi ba , kuma tasan muddin ba itace ta tursasa masa ba haka zai kwana da yunwa, kuma ta rigada tasan bai ci komai ba dan muddin yana qasar baya ta'ba cin abincin kowa sai nata"."look at me adamcy ,ya bar abinda yake yi ya kalleta Kmr yadda ta bukata ,look at the time adamcy ta nuna masa makeken agogon dake manne a bangon parlour'n "lokaci na tafiya tunda ka shigo gidan nan ruwa kawai ka sayanwa cikinka "bai kalli agogon data nuna masa ba bare yasan lokacin daya d'auka bai sayanwa cikinsa komai ba sai ma d'auke idanunshi da yayi akanta yana hura hanci ." "Tsawon wata biyu bamu had'u ba sai kuma tayi murmushi ganin yadda ya qara had'e girar sama data qasa kamar wani qaramin yaro , ta d'aura d'ayan hannunta akan hannunsa dake cikin nata "me yasa baza kayi abinda zai faranta ran sweetheart dinka ba ? Ta numfasa irin nasu na manya kana ta cigaba da magana "koda yake ina son wannan fushin naka ban sani ba ko dan yana qara maka kyau ne ?" lumshe tsumammun idanunshi yayi batare da ya juyo ya kalli mami ba yace "nima ina son fushina ina son yadda Allah ya halliceni " murmushi mami ta sake yi "to ai shikenan daman ai mai hali baya gudun halinsa yanzu dai kaci abinci shine abinda nafi buqata "na koshi ".ya fad'a atakaice yana fesar da numfashi . mami ta juyo da fuskasa gareta ta dungure masa kai tana cewa "allah baka isa ba ,duk yadda aka sha wahala akayi girkin nan kace ka koshi ,allah sai kaci idan ba haka zanyi fushi mai tsanani da kai sai da mami ta had'a da marairaicewa sannan ya fara cin abinci daga hannunta " a ranta tace hukuma sai da rarrashi ."mami girkin nan kamar ke kikayi Kmr kuma bake kikayi ba?". "me yasa ka fad'a haka ?yayi shiru yana nazari sannan yace "yayi dadi Kmr naki but ya dan yi maggie kad'an ba kamar abincinki ba dan sam girkinki maggie baya yawa , kamar ta fad'a masa gskyr wacce tayi amman tasan halin yan kayanta sai ya birkice mata yanzu ta rasa gane kanshi dan haka tace" ni nayi kasan yau da gobe sai allah, ni kaina naji maggie ya d'an so yayi yawa amman ai yawan da yayi bazai hana a kasa ci ba ,shiru yayi ya tsura mata tsumammun idanunshi yana dubanta a tsanake bai san me yasa ba sai yake jin Kmr ba gsky sweetheart ta fad'a masa ba ,dan dai yasan wacece sweet heart dinsa a fannin girki babu karya tana da matukar kwarewa tun yana yaro ya sani suna zaune ma take had'a girkinta ta tashi ." bayan ya gama cin abinci mami ta kallesa a natse kafin daga bisani ta kira sunansa "adamcy nah? ya tsura mata tsumammun idanunshi kawai yana kallonta da sauraronta "ya ake ciki da maganarku dasu sultan naji ko a waya baka sake ce min komai akai ba ?ya lumshe tsumammun idanunshi na second biyar sannan ya motsa labbansa yace "magana ta wuce tunda sun dawo da makudan kadaden da suka sace "ikon allah ! account dinka suka saka kud'ad'en ko kuwa account din agc ?" no Ibrahim suka kai wa cheek amman ya fad'a min fahad ne ya kai masa bayan sultan da salim sun qare masa zagi . "Zagi kuma ?! Ya lumshe mata ido kawai alamun "eh ! "Wannan abu gsky bai yi dadi ba Allah sarki ibrahim bawan Allah to shi meye nashi da zasu zagesa ? a cewarsu yayi masu munafurci alhalin ni bashi ya fad'a min ba hasalima bai sani ba a bakina yaji ,"allah sarki bawan allah ,allah dai ya kyauta kawai , Allah km ya shirye su shiri na addinin muslinci , bancin company agc ya tsaya da kyau nasan da zuwa yanzu an rufeshi kullum daga anemi kud'ad'e a rasa sai a nemi kaya arasa kuma duk masu yi suna gindinmu ." "sosai kuwa shiyasa yanzu gbdy zan tattara hankalina zuwa agc kusan ma nan zan fi karfi a sati sau uku zan dinga shiga sauran ranakun kuma zan dinga leka wanda suka samu acikin companies dina , hakan yayi daidai allah yasa mu dace yace "ameen ! ya fad'a tare da d'aukar remut ya canza channel zuwa aljazera. Mami tayi shiru tana kallon tv can ta waigo inda yake zaune idanunshi na kallon tv , kallonta yayi ta gefen ido kafin ya maida idanunshi sosai kanta ya dage mata girasa daya alamun tambaya ,numfasawa tayi sannan ta soma magana "nace bakaga ya kamata ka dinga d'an jan yarinyar nan mrym ajiki ba ? "Janta ajiki kuma kamar wata yarinya qarama ? ya fad'a cike da jin mamaki " ba maganar kamar wata qaramar yarinya bane yana da kyau ka jata ajiki ta yadda zata sake da kai idan ma ta kama ka dinga kiranta hira domin ku samu fahimtar juna ?"Wani fahimtar juna kuma ya saura sweetheart ? yarinyar nan tasan halina tasan abinda nake so da wanda bana só ." "duk da haka dai ya dace ku dinga zan tawa "gsky sweetheart bana jin zan iya, akan na kirata zance gara a fasa auren kawai dan nasan bazan ta'ba iyawa ba ,taya ma zan fara ?"mami tayi murmushi irin nasu na manya tace ,idan baka san ta inda zaka fara ba ai sai ka tmbyi abokanka masu aure sa koya maka ta inda suka fara , idan kuma kana jin kunyarsu ne sai ni na koya maka ko ba shikenan ba tunda dai ni nasan baka jin kunyata ". tunda mami ta fara magana ata ya sanya hannunsa a tsakanin hancinsa da bakinsa kawai yana kallonta "ko na kira maka ita yanzu ?"mrym ! mami ta kwalla ma mrym kira "oh my godness god , haba sweetheart wai me yasa kike min haka ne ?kai ma me yasa bakasan kayi abinda ya dace ba ?"allah sweetheart bazan iya kira kowace mace da sunan zance ba " Allah ko ?! ya dage mata girasa d'aya alamun "Eh! ai kam dole ka kasa iyawa tunda ka zama tuxuru fuskarsa a had'e yace "sweetheart ai itama yarinyar taki tsohuwa ce wallahi , baki ga duk kashin tsufa ya bayyana ajikinta ba ? mami ta dan ware idanunta sosai "akwai wani kashin tsufa ajikin mutun ne ?ta tmbyesa dry na kufce mata ." Wani sanyi dadi yaji aransa yace "sosai ma kuwa akwai ,to kai taya akayi ka gani ? kodai adamcy ya kamu ne yana so yana kaiwa kasuwa ?bai ce mata uffan ba sai dai a zuciyarsa yace " allah ya tsareni ,ata ya kamo hannun mami cikin nashi yana marairaice murya "sweetheart ! ya kirata sunanta tana dariya tace "ina jinka adamcy nah "dan girman allah laifin me nayi miki da kika zabi ki hadani da yarinyar nan aure ?". "taurin kanka ne ya jawo had'a zumunci "amman sweetheart baki ga rashin dacewarmu ba ni dogo ita duwaf ? ban son wulakanci adamcy yarinyar tawa ce duwaf ?ta fad'a tana had'e rai ."ai yar daidai kusa da kafad'ata kamar zata fi dacewa dani akan mace guntuwa ?," idan ta kai maka daidai kafadanka cin tsawon zakayi ?ta fad'a tana kunshe dryata yayi shiru kawai yana zare hannunsa cikin nata."abinda bakasani ba dogo nmj da mace mara tsawo sunfi dacewa , karka damu da rashin tsawon maryam nagartata zaka duba ,Kmr yadda na sha gaya maka mrym ce daidai da halinka sannan zata haifa maka ya'ya na gari zuqa zuqa ." "Sweetheart sai da safe yayi ma mami sallama ya mike tsaye da rigarsa akafad'a dan yasan bazata barsa ya huta da maganar yarinyar ba , kai tsaye ya wuce saman d'akinsa wanka ya fad'a zuciyarsa cike da tsananin mamakin maganar mami "wai ya kiranta zance idan ya kirata yace mata me ?yaja dogon tsaki ,aikuwa muddin sai ya kirata zance sai dai a hakura da auren ,byn wasu mintuna ya fito yana goge sansar jikinsa , byn ya gama ya qarasa inda turarukansa suke ya dauki bodyspare ya feshe ilahirin jikinsa sannan ya saka gajeren wondo iya cinyarsa da riga fara sol ya kwanta yana mai jin tausayin kansa ." "ya rasa me ya tsarewa mahaifiyarsa da take son ta had'ashi aure da wannan guntuwar yarinyar mai siffar wada yarinya sam babu fasali , yasan muddin ya auri maryam rayuwarsa da farincikinsa zasu yi kasa ,kai gbdy komai nashi zai canza kuma yasan har da walwalansa ,ya gyara kwanciyarsa tare da janyo pillow ya d'aura asaman ruwan cikinsa ya rungume tsam tsam yana jin kamar princess ce duk da yana son mantata amman duk sanda zai yi bacci sai yayi tunaninta sannan bacci mai dadi yake d'aukarsa " a yadda yake jin felling din yarinyar yayi imani zai had'u daita sai dai yaushe ne ? a ina ne ? bai sani ba , ahankali ya dinga juyi akan katifar yana jin felling dinta mai tsanani yana sauka a sansar jikinsa ,ji yayi kamar anyi kissing din lip's dinsa ya d'an bude idanunshi yaga wayam babu kowa sai shi kad'ai a d'akin, ya sake maida idanunshi ya runtse sai dai a haka yake jinta kusa dashi kuma yake imaginetion din komai ." sake janyo pillow yayi ya rungume tsam yana jin tamkr itace ajikinsa , ahankali bacci ya d'aukeshi cike da mafarkinta wai gata ta hau saman qirjinsa ta kwanta tana shafa qirjinsa zuwa kan nipples dinsa wani irin d'auke numfashi yayi da karfi dan alokacin da'ace akwai wani a d'akin dan dole ya fahimci yana cikin wani hali .wani irin juyi tayi har rigar dake sanye a jikinta ya zame wanda daman dashi da babu duk daya ganin abinda yafi so ajikinta wato dukiyar fulaninta ya tashi zaune acikin mafarkinsa ya rike hannunta gam cikin nashi yana murzawa "my princess ina kika shiga two day's baki zo min ba ? banje koina ba ina tare da kai ,tayi masa mgn tana kai harshenta qirjinsa ta fara lasa wani irin abubuwa yake ji suna yi masa yawo a gbdy ilahirin jikinsa ." tsigar jikinsa gbdy suka mike yayinda jijiyarsa ta dinga harbawa da sauri sauri rungumota yayi sosai ya sakata a tsakiyar qirjinsa hancinsa ya cusa cikin suman kanta daya zubo har gadon bayanta ahankali ya dinga shakar kamshin jikinta tare da lumshe ido yana jin wani sanyayyen abu a zuciyarsa". "kina sona ?ta gyada masa kai alamun "eh !,to ki taimaka ki bayyana min kanki tun kafin ayi min auren dole ,wani bayyana maka kaina zanyi byn gashi muna tare ?ni da kai muna tsananin son juna ko ka manta tsawon lokacin da muka kulla soyayya a tsakaninmu ?ya gyada mata kai ," alaka soyayyarmu mai karfi ce domin kai din nawa ne na har abada ,sake matsota yayi sosai ya kai hannunsa kan karan hancinta yayi kasa da hannunsa har zuwa kasan marata , yana jin lokacin data sauke numfashi zuciyarta na bugawa da karfi hakan yasa ta shige masa tun daga wuyanta ya fara shafata itama tana shafashi ,kamkameta yayi ajikinsa ya had'e bakinsu waje daya yana wa bakin wani irin tsotsa na fitar hankali ." Bangaren marym itama kwance take tana faman juyi akan katifa dan ta kasa runtsawa tana saka da warwara kwalkwaluwarta na sake nitso cikin kogin tunani ta yadda zatai rayuwar aure da mutun irin mr ata ,mutumin da baza tace ga ranar data ga murmushinsa ba ,hasalima fuskarsa koda yaushe a had'e take tmkr hadari juyi kawai take tana tunanin abubuwa dayawa akan aurenta dashi bai sonta ,gashi tunda akace ita zai aura bata sake samun isashen bacci ba kullum da abubuwan da take facing ,sai ta dinga jin kamar ana farautarta, wani lokacin idan ta runtsa idanunta sai taga mutun akanta ana qoqarin caka mata wuka da zarar ta bud'e idanunta ta kunna wuta sai taga wayam babu ko alamun mutun dan wani lokacin tashi take tayi alwala ta gabatar da sallar nafila. yayinda take nan kwance cikin tsananin tunani da fargaba shi kuma mr ata yana can duniyar mafarkinsa ."ajiyar zuciya ta sauke ta kalli nana hauwa'u dake sharar baccinta hankalinta kwance "allah sarki sister kin huta, kina rayuwarki hankali kwance baki da wata damuwa ,ya allah kasa auren yaya adam arayuwata alkhairi ne ta furta hakan a fili ,ganin har kusan karfe biyu da wasu yan mintuna na dare bata runtsa ba ga gari ya dauki shiru sosai baka jin motsin komai ,taji kamar ta tashi taje tayi alwala ta roki Allah alkhairi daga cikin alkhairun dake cikin dare amman sai taji ta kasa tashi domin alokacin idanunta sun fara mata yaji alamun bacci ahankali bacci barawo ya d'auketa ." cikin bacci mrym taji numfashinta baya sauka yadda ya kamata kamar an danneta ta kai hannunta tana qoqarin cire abinda taji ya danne mata fuska wanda take tunani pillow ne akayi amfani dashi amman sai taji an sake danneta da iyakacin karfi ta yadda ko sautin muryar ta bazaa iya ji ba nan fa ta fara mutsu mutsu da kafafunta tana kokarin kwatar kanta cikin ikon allah ta samu nasarar rike hannun mai shi nan fa suka fara kokuwa mrym na qaqarin ta amshi pillow amman ana sake danne fuskarta ita km sai qoqarin ceton ranta take ." inda tayi wata irin zabura ta fixge pillow ta kwalla wata razananniyar qara wanda yasa gidan gbdy ya dauki sauti kuwar qararta ,nan da nan nana hauwa'u ta farka daga naunayen baccinta tana kiran sunan da take kiranta dashi " sister lafiya tare da qoqarin kunna wutan dakin ? mrym bata amsa mata ba sakamakon inuwar mutun data ga yana qoqarin ficewa daga dakin tayi wata irin sufa sai gata ta rike gefen rigar mai shi adaidai lokacin da nana hauwa'u ta samu nasarar kunna wutar d'akin adaidai lokacin mai shi tasa hannuwanta duka ta ingiza mrym da iyakacin karfinta tayi baya luuuuu sai dai ido cikin ido suke kallon kwayar idanun juna sanye take cikin bakaken kaya tun daga samanta har kasanta babu abinda zaka iya gani ajikinta sai kwayar idanunta ." a kallon da mrym take ma yanayinta ya nuna mata mace ce hannunta daya rike da wuka duk da suna kallon lokacin da tayi fillinging da wukar a tsakiyar daki ta fice da sauri tana haki nana hauwa'u ta sauko a rude ta tare bayan mrym tana rungumeta ajikinta "sister ki bita karki bari ta fice wallahi kasheni take qoqarin yi duk suka rude sai zufa suke fitarwa mrym tace "wallahi kasheni zata yi ta sake fad'a tana qoqarin mikewa domin tabi bayanta ." Mrym na qoqarin mikewa tsaye alokacin mami tare da masu aikin gidan suka shigo cikin dakin cikin tsananin tashin hankali a matukar firgice maryam ke matsu bayanin komai mami tace "Inna lillahi !a garin yaya ? ta yaya ma hakan ta faru ?wallahi mami da gaske yau kwanana ne kawai Ke gaba dana bakunci lahira daman kullum ina jin ana yunkurin kasheni ,wallahi mami nafi tsawon wata biyar ina jin ana farautar rayuwata cikin dare maryam ta fad'a cikin matsanancin tashin hankali "to akan wani dalili kenan ?"wallahi bani sani ba ta fad'a cikin muryar kuka har da shesheka nan da nan nana hauwa'u ta fashe da kuka ta kamkame mrym magana take son yi amman muryarta ta kasa fita tana kallon wukar dake yashe kasa ,sabuwa fil da alamun baa ta'ba amfani daita ba ." "Mami kalli wukar datazo daita nasan wallahi kwana ne kawai agaba yasa ta fara amfani da pillow bancin haka tana daba min wukar nan cikin bacci sai dai na farka najini a lahira, mami ta qarasa inda wukar take ta tsura mata ido muryarta a sanyaye tace auta miko min wukar data yar , ta dauki wukar ta mika wa mami " wannan kamar irin wukar daa aka kashe mubina ko ?gbdy suka sake shiga rudani nana hauwa'u ta matso kusa da mami sosai tana cewa "tabbas mami irin tace nima kallon da nake ma wukar kenan dan lokacin rasuwar mubina nima na ga wukar " . "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun daman acikin estate din nan makashin mubina take ? domin babu tantama acikin estate din nan ne domin babu wanda zai tsallake masu tsaro sama da goma sha biyar banda securities ya shigo esatate din nan lallai acikin estate din nan ake qoqarin kashe mrym nana hauwa'u ta gyada mata kai alamun haka maganarta take .""auta taso min adamcy da mugun sauri ta fice daga dakin zuwa nashi bata tsaya neman izini ko sallama ba ta banka dakin baccinsa yana kwance rungume da pillow "yaya !yaya! cikin bacci yaji ana tabashi hade da kiran sunansa ya bude idanunshi cikin tashin hankali yana cewa "Lafiya ?wai kazo inji mami da sauri ya kalli qaramin agogon dake ajiye akan bedside dinsa karfe uku yanzu ta wuce saukowa yayi da sauri dan yasan koma meye ba lafiya ba da wannan tsohon dare tace a kirasa ." Jallabiyarsa ya dauka ya zira ya fito rike da gefen Jallabiyar dan ya samu damar daga kafafunsa da kyau biyu biyu ya dinga taka step yana gama saukowa ya karya zai shiga parlour'nta na biyu nana hauwa'u tace "tana dakin mu kai tsaye ya wuce bai tsaya jin dalilin ba atare suka shiga dakin cikin tashin hankali mami take masa bayanin abinda ya faru ." shiru kawai yayi yana duban mrym dake wani irin kuka bai yi mamaki jin abinda mami ta fad'a ba sannan babu wacce tazo cikin tunaninsa sai nuzla domin ta tura masa da sakon lallai idan bai amincewa aurenta ba zata ga byn mrym sai dai itama idan ta kasheta a kasheta lokacin daya ga sakon shi ko ajikinsa dan kuwa da allah yasa tayi nasara kasheta data taimaka wa rayuwarsa ita taje da Allah shi kuma ya huta da qaya." kiran mutanen estate din mami tasa nana hauwa'u ta dinga yi suna nan tsaye a daren sai ga jama'ar gidan duk suka rude iyayen mubina sunfi kowa shiga tashin hankali yayinda mrym Ke kuka har lokacin mahaifiyar mubina kam ta yarda domin kuwa me wukar tazo yi dakin maryam kuma exactly irin wukar ce babu tantama ,mami ta qaraso ga mrym dake zubar da hawaye "me yasa zasu kashe min mrym ?ince duk esatate din nan yanuwan juna ne babu bare acikinmu ? "me yasa zaa dauki ran wani ?dan girman allah ku taimaka ku fad'a min cewar duk wannan abun dake faruwa a mafarki ne domin bana tunanin haka daga cikin ahlin nan, bana tunanin wani zai iya aikata min haka kuce min wasa ne ba niyyar kashe min mrym akayi ba ?"mrym ta sake fashewa da sabon kuka tana rungume mami ajikinta gbdy ta tsure ta nemi natsuwarta ta rasa itama mami rungumeta tayi tana shafa bayanta ." "Sweetheart kukan ya isa ki bar kuka ki kwantar da hankali kowaye acikin estate din nan zan fito dashi Ke kuma malama kin cikawa mutane kunne da hayani just keep queit I don't want to hear any sound please ya juya ya kalli wadan da suka hallara a dakin dan ba kowa ya shigo ba, dan wasu na can na bacci bama su san meke faruwa ba na kusa kusa ne suka samu damar shigowa yace "kowa ya tafi ya kwanta zai dauki mataki , ya dauki wukar ya fice . daya byn daya suka dinga fita daga dakin cike da jima min , mrym da nana suka bi mami dakinta kowace ta haye gado sai dai ba da niyyar bacci ba dan mrym kam kuka take sosai babu abinda take gani sai mubina cikin jini shikenan da yanzu wani labarin ake ba wannan ba ,da yanzu tana cikin jini tana wannan imagenation din tana kuka nana hauwa'u kuwa zaman dirshan tayi da mami suna tautaunawa dan bacci kam ya kaurace masu ." Washgari baba babba ya tara manya gidan tun daga kan kannensa har zuwa kan yayyansa na sama dasu dana kasa dasu dake esatate din acikin dakin na musamman da suke ganawa a duk sanda abu makamancin hk ya faru ,ya dade yana bayanin abinda ya faru a daren jiya tare da jan kunne da nasiha mai ratsa zuciya a karshe yace zaa yi bincike duk wanda aka samu da sa hannusa zaa mikasa hannun hukuma dan maganar da nake daku yanzu haka nayi report wajen police har na mika masu wukar domin a fara bincike duk hankulansu a tashe mrym kuwa har wanna lokacin kuka take aunty shahida da khadija kaf yayan mami tun safe suka yiwa gidan diran makiya jama'a kuwa sai zuwa jaje suke yi wa mami haka ma iyayen maryam sun kira yafi sau babu adadi wuni ranar haka mrym tayi shi cikin dakin mami cikin tsananin tashin hankali ." Bayan kwana biyu da faruwar lamarin da misalin Karfe hud'u sauran wasu mintuna mr ata ya shigo estate dinsu drivenshi na tsayawa batare da bata lokaci ba masu kula da lafiyarsa ta hukumar dss suka fito da sauri kafin ma su bude masa ya bude ya fito yana gyara zaman rigar jikinsa kai tsaye masalacin dake cikin esatate din ya nufa domin gabatar da sallah bayan ya idar da sallah ya nufo gidansu nana hauwa'u da da maryama na zaune idar da sallar su kenan sai ga diyana ta shiga hira suke kadan kadan mrym na bawa diyana labarin abinda ya faru daita "amman Kinsan wani abu diyana duk yadda muke da nuzla bangata ba kuma nasan taji abinda ya faru dani har cikin daki aka biyoni zaa kasheni amman ta kasa zuwa tayi min jaje tunanina ni kuwa laifin me nayi mata? wallahi har da kwalla nayi na rashin zuwanta saboda banyi tunanin hk daga gareta ba ." "gsky da mamaki kuma kinga ai ba haka take ba tana da kulawa da mutane most especially idan abu ya sameka na farinciki ko akasinsa amman Kiyi mata uzuri wata killa tana nan hanyar zuwa tunda duka yau kwana biyu ne da faruwar abun ,wannan gsky ne nuzla bata da haka amman baku lura a tsakankanin lokacin nan ta dan canza ba ?inji cewar nana hauwa'u"eh ta canza kam sosai ko Kinsan damuwarta ?ko daya ban sani ba wallahi na dai kula ta canza ko a yanayin jikinta zaki fahimci akwai abinda ke damunta mrym tace " to koma meye allah yafi mu sani Allah ya yayewa kowa damuwarsa Suna zaune mr ata ya shigo gbdy suka masa sannu da dawowa ya amsa Kmr yadda ya saba aciki sannan ya kalli auta yana tmbyr mami "ke auta ina sweetheart. ? "tana ciki ta shiga tayi sallah yana gama ji ya haye sama suka cigaba da hirarsu ." Bai sauko ba sai bayan awa daya sanye da shirt ajikinsa da wondo ficewa yayi bai tsaya akoina ba sai gidansu nuzla ya tmbyi mahaifiyarta ta sheida masa tana dakinta bata jin dadi a natse ya nufi kofar dakinta ya tura kofar ya shiga tare da sallama akan lip's dinsa tana ganinsa ta mike zaune tana ware fararen idanunta akanshi tayi qoqarin ta sakashi cikin nashi idon sanda yake takowa zuwa inda take tana masa duban mamaki dan bata ta'ba expecting zata ganshi har cikin bedroom dinta ba ." sosai ya dauki hankalinta yayi wani fresh yayi qara kyau kaman zane ta koina ya hadu matsalar dai shi din mugun miskili ne sai dai hakan ma qara masa kyau yake ahankali ya janye idanunshi acikin nata ya maida dakin yana qarewa koina kallo "Lafiya yaya adam da wannan zuwan naka na bazata ?" Shiru yayi yana cizan lips dinsa na kasa kafin daga bisani yace "bai kamata kiyi min wannan tmbyr ba domin kuwa Kinsan dalilin zuwana "ya fad'a alokacin daya jingina jikinsa da mirrow dinta yayi crossing leg's dinsa ya rungume hannuwansa duka a saman faffadan qirjinsa yayi da idanunshi ke kallon zara zaran yatsun kafafunsa." da kyar ta mike daga zaunen da take tana cewa "ni ban san abinda ya kawoka ba idan dai ba kazo da niyyar karbar soyayyata bane amman kafin nan me zan kawo maka ?"yayi mata banza zuciyarsa na zafi jin yayi shiru km ta rigada tasan halinsa tayi tunanin ta kawo masa ko ruwa ne har tayi taku biyu taji ya fixgota da karfi yana watsa mata wani kallo da idanunshi dake cike taf da bacin rai gbdy taji ta fara muzanta daga kallon da yake mata taji gwiwarta tayi sanyi ."Idanushi ya tsareta dashi yana kallonta yayinda gabanta ya fara faduwa tana adduar allah yasa ba wani laifi tayi masa ba ." Sai daya gama kallonta sannan ya watsata akan katifa ta sauka da karfi sai da hantar cikinta ya kada still bai dauke idanunshi akanta ba ,nan take ta soma sheshekan kuka sannan ta fara mgn "yaya idan wani laifi nayi maka ya dace ka fad'a min amman wannan kallon naka na hargitsa min lissafi .kallonta ya cigaba da yi bai ce uffan ba har sai data gama ,cikin izza ya motsa labbansa "nasan kin san abinda kikayi sannan kuma kinsa shine dalilin zuwana " cikin mamaki da tsoro take kallonsa ya tsareta fes da idanunshi yana mata kallon banza ." ranshi a bace ya daidaita tsayuwarsa yana cigaba da kallonta kallon dake qara kashe mata jiki da tsoratarwa "hakika kin tabbatar min da abinda kika turo min a kwanaki uku da suka gabata na zakiga byn mrym , kinyi yunkurin kasheta Kmr yadda kika kashe mubina dan tace tana sona ko?"Idanuwa ta zaro gabanta na faduwa a fili tace" na shiga uku tana dafe qirjinta tare da nuna kanta "ni din na kashe mubina sannan nayi yunkurin kashe mrym ?wani kallon banza yake mata yana jin Kmr ta raina masa wayo ne babu abinda yafi tsana sama da karya yafi son duk abinda ya tmbyeka ka fad'a masa gsky ta haka zaka samu sausauci daga garesa "ban kashe mubina ba me yasa zan kasheta ?"wallahi ban aikata komai ba sannan banyi yunkurin kashe mrym ba tabbas na tura maka sakon zanga bayanta amman wallahi ban aikata hakan ba ,amman ina da niyya to waye yasan da wannan shiri nawa da har ya rigani aiwatarwa? "Lafiyayyen mari ya zuba mata yana cewa "ni kike wa wannan tmby ?nan take ta rude ta dafe kuncinta inda marin ya sauka abinda yafi damuna kashe mubina da kikayi me tayi miki nuzla ?kuka ta saka mashi tare da durkushewa kasa "wallahi sharri ake son min dan ban san komai akai ba .wani kallo ya watsa mata sannan ya juya mata baya "nasan tabbas kece kika kashe mubina dan hatta wukar da kika kasheta kinyi kuskuren barinta a yunkurin kashe mrym ." "Da mrym kika kashe wallahi bazai ta'ba damuna ba saboda neman kai nake daita ,ni da zaki kashe min ita amatsayinki na yartaada kafin ta zama mallakina lallai ni kuma da nayi akawarin aureki .nuzla ta sake rudewa ta gigice ta soma jan gwiwowinta ta qaraso inda yake tana kuka "na baki kwanaki goma masu zuwa ki kashe min mrym kafin ta zama mallakina batare da an samu wata hujjar cewar kece kika aikata hakan ba , sannan kada asirinki ya tono ni kuma zan aureki idan kuma kika gagara kasheta har lokacin dana baki ya cika ni kuma nayi miki alkwarin zan damkaki a hannun hukuma a kwatarwa mubina hakinta kin dai sani idan hukuma ta tabbatar da kece kika kasheta karshenki biyu ne, kisa ta hanyar rataya ko kuma zaman gidan yari na har abada muddin rai kenan yana gama fadar haka ya soma qoqarin ficewa daga dakin .." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 23 Ji tayi qasusuwan jikinta suna barazanar kasa riketa , lokaci guda zuciyarta na barazanar tarwatsewa bata san sanda ta kurma ihu da iyakacin karfinta tana d'aura hannuwanta duka bisa kanta mahaifiyarta hajiya salema ta shigo d'akin da sauri tana dubanta cikin tsananin kad'uwa da tashin hankali, zata iya cewa yanayin data ganta ciki bata ta'ba ganinta cikin irin yanayin ba sai yau wanda shine karo na farko da taga wannan yanayin atare daita , yanayi ne mai cike da firgici da tashin hankali." Rawar da jikin nuzla yake ya qaru hjy salema ta matso kusa daita ta soma girgiza nuzla wacce ta koma tamkar mutun mutumi a wajen "nuzla nuzla!! lafiya what's wrong with you ?!me ke faruwa dake ? me adam yayi miki kike kuka haka ko ince laifin me kikayi masa dan nasan ruwa baya tsami banza tunda naganshi nasan akwai abinda kikayi masa ? ta jera mata tmbyoyin a rud'e tana riko hannunta cikin nata. nuzla tayi shiru tana wani irin kuka mai d'aga hankali "ki min magana mana ko hankalina zai kwanta ? ta mike a matukar firgice tana duban hjy salema sai dai bata iya amsa mata tmbyoyinta ba dan bata da amsar da zata bata a halin da take ciki ,dan haka ta cigaba da kallonta da rinannun idanunta dake cike da ruwan hawaye kafin daga baya ta fara kuka wiwi tana safa da marwa acikin d'akin hajiya salema na biye daita cikin tsananin damuwa ." " tabbas idan har hasashe da yarda yaya adam akanta ya tabbata a zuciyarsa to fa tabani ta lalace ta shiga ukunta dan wallahi tasan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a mata .hankalinta ya sake matukar tashi tabbas tayi niyyar aikata hakan amman daga ita sai Allah'n daya halicceta da zuciyarta da kuma yaya adam ne kawai suka sani ,"ba itace tayi kissan ba to waye yayi ?ta furta hkn a qasan ranta tana furta "wayyo allah na shiga uku ni nuzla ta ina zan fara ? waye yake son jifa rayuwata cikin maseefa ? da wani irin sauri ta nufi kofar fita hjy salema ta biyota tana kiran sunanta amman ina bata tsaya ba tunin ta kai kofar fita daga gidan ta biyo bayan ata ." ya d'an yi nisa amman bai kurewa ganinta ba dan tana hango bayansa daga inda take ta kira sunansa da karfi cikin tsananin tashin hankali , shi kuwa ata yana jinta amman yaki waiwayowa ya cigaba da tafiya kmr baya son taqa qasa ."ta qara sauri sosai kamar zata hantsila , kallo d'aya zaka wa nuzla ka fahimci bata cikin haiyacinta da natsuwarta ."adaidai bakin kofar shiga side din mami ta iske shi tare da shan gabansa gif haka nuzla ta zube qasa bisa gwiwowinta agabansa idanunta na qoqarin sake kawo ruwa cikin wani irin murya mai gauraye da tashin hankali hade da rudani take furta "yaya ka taimakeni ka tsaya ka fahimceni karka yanke wannan hukuncin wallahi ban san komai akan lamarin nan ba." ya tsura mata tsumammun idanunshi kafin ahankali ya soma magana cikin izza "taya zan iya yarda da hakan bayan kece da bakinki kika furta hakan kuma kika aikata ? "wallahi wallahi !! idan ka yarda da rantsuwata bani bace sam sam ban aikata abinda kake zargina akai ba hasalima ni yau tsawon kwanaki goma sha biyar kenan kafafuwana basu taka haraban gidan nan ba ina kwance bani da lafiya ."yadda take maganar zaka fahimci tana cikin rud'ani da tashin hankali kamo kafafuuwansa tayi cikin kuka tace "please yaya try to understand me bazan ta'ba aikata hakan ba kawai dai na fad'a maka haka ne dan ka tausaya min ka aureni amman ka yarda dani ban san komai akai ba ." "Bazan ta'ba yarda dake ba domin nasan zaki iya aikata taadanci makamancinsa koma fiyye dashi a halin yanzu ba wannan magiyar bace ta kamaceki ki fara shirin yadda zaki aiwatar da aikin dana baki idan kuma zaki tonawa kanki asiri né tun yanzu bismillah ." jikinta da muryarta na rawa tace "baxan damu ba koda asiri zai tono dan ban aikata komai ba bare naji tsoron fallasa kuma Allah shine sheidata ban aikata ba amman zaka iya bincike akan wanda ya aikata abinda kake zargina akai amman ni bani bace kuma duk inda zaa kaini zan tsaya ne akan gskyta bazan ta'ba karban laifin da bani na aikata ba ." a natse ya soma daga kafafunsa dan wucewa ya barta dan ya gaji da jin sautin muryarta da kukanta yana shiga kanshi over ,yaga tana qoqarin jan gwiwowinta domin biyosa ya kalli securities din dake tsaye a wajen "karku sake ku barta ta shigo ciki "okay yallabai an gama ya shege ciki ya barta durkushe tana kallonsa tmkr wani sabuwar halittta a wajenta ."mikewa tayi tare da cure hannayenta waje daya tana bugawa da juna bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin ta yau ba har ga allah bata san haka abun zai rikice ya dawo kanta ba ta dauka idan ta fad'a masa haka zataci bulus ne ashe masefa zai zame mata ashe bazataci bulus ba wahala zata sha ?"me yasa batayi shiru da bakinta ba ?me yasa ta gaza hakuri har sai data fito ta fad'a masa shirinta gashi ta kai kanta ta baro ? kaicona ni nuzla bakina ya janyo min matsefa na tarowa kaina bala'i da kaina ta sauke ajiyar zuciya tare da furzar da zazzafar iska daga bakinta ." "Ai kam wallahi sai dai yayi mata duk abinda zai mata idan ta kama ma ya mikata ga hukuma amman bazata ta'ba aikata abinda yake bukata ba sannan bazata ta'ba karban laifinta ba sai dai idan kasheta zaayi akasheta ta yarda amman bazata cika masa burinsa ba, shi idan har da gaske yake baya qaunar maryam din ya aikata lahira da kashi ba sai ya had'a daita ba da sauri ta juya ta soma tafiya kamar zata tuntsura kasa sai kace mahaukaciya ta shigo gidansu inda ta iske mahaifiyar tsaye cikin zullumi ." Tana ganinta ta qaraso gareta tana tmbyrta nuzla ta zauna akan kujera jagwaba tana fidda numfashi duk tmbyr da mahaifiyarta take mata bata kulata ba illa hawaye dake zubar mata "wani laifi kikayi wa adam ?tayi shiru kawai batare da tace uffan ba hjy salema tace "to da alamun laifin mai girma kikayi masa yasa har ya biyoki "kamar ta bayyanawa mahaifiyarta halin da take ciki kafin ya damkata hannun hukuma a kashe mata ita a banza a wofi amman ta kasa dan gaskiya bazata iya ba domin tasan irin qaunar dake tsakaninsu kasancewarta auta a wajenta ,banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa tare da dafe kanta dake mata wani irin sara Kmr zai rabe gida biyu hjy salema ta barta ta koma dakinta dan ta fahimci laifi tayi masa mai girma wanda yasa ta kasa furta wa ." Nuzla ta rufe idanunta gam tana jin yadda maganarsa ke tashi acikin kunnuwanta da zuciyarta so take ta sakawa gangar jikinta hakuri da jarumta har zuwa waadin daya dibar mata ya cika amman ta kasa bata jin zata iya, a halin yanzu ma ba mgnr aurensa bace a gabanta illa mafuta lallai tana bukatar mafuta ta mike tsaye tana zariya acikin parlour'n "ko na gudu ne na bar gidan ne ?ta tmbyi kanta ,gudunki bashine mafuta ba nuzla hakan ma qara min laifi zai yi idan kuma maganar ta fito shikenan kin tabbata mai laifi a wajen kowa dakinta ta shiga tayi zaman dirshan tana saqa da warwara ni dai wallahi nasan bani na kashe mubina ba haka zalika banyi yunkurin kashe mrym ba ,"shin ta ina zan fara ?ni kaina ina bukatar gano wanda yayi hakan , ta lumshe idanunta tana tunani dan dole tayi bincike dan gani wacce tayi yunkurin kashe mrym kuma ko wacece acikin estate dinsu take km itama tana son adam ne Kmr yadda take son shi jikinta ya dauki zafi sosai ." Zaune mr ata yake akan kujera kushin dake d'akinsa yayi zurfi cikin duniyar tunani yayinda hankalinsa gabadaya ke sake tashi a duk sanda ya tuna da maganar aurensa da mrym sai ya dinga jin hankalinsa na sake tashi , yayinda a kullum ya daura kwayar idanunshi akan yarinyar sai ya dinga jin tsananin tsanarta ,shi da kansa ya kasa sanin takamaimain dalilin dayasa yake jin tsananin tsanarta haka dan bazai ce dan rashin tsawonta bane da kuma kasancewar ta fara bane ya janyo haka yanayinta dai ya taimaka wajen tsanarta ne ,duk yadda yake qoqarin yakice tsanarta da sanyata ko kadan acikin ransa zuciyarsa taki amince da zamanta a tsakaninsa tafe tafe har tunaninsa ya kawo kan zanen wukar dake ajiye akan bedside dinsa wanda aka kashe mubina daita kuma ake qoqarin kashe mrym dashi shine ya zana ya ajiye a wajensa kafin a mika wukar ga hukuma ." ahankali ya sauke naunauyen ajiyar zuciya ya sake gyara zamansa sosai akan kujerar da yake zaune tunanin duniya yayi akan wacce tayi karfin halin shigo masa gida da taadanci , baya da tabbacin ko nuzla ce domin kuwa har ya gama kallon mai shi ta camerar d'akinsa bai iya gane ko wacece ba zargin nuzla kawai yake bisa yanayin jikin wacce ta shigo da kuma furucin bakinta amman bashi da tabbas akanta bincike ne kawai zai tabbatar masa daita ce ko kuwa wata ce dabam ta kashe mubina km tayi yunkurin kashe mrym "idan wata ce dabam meye dalilinta ?meye hujjarta ? me yasa take yunkurin aikata hakan ?iya tunaninsa yanzu ya fara gane wasu abubuwa akan me kisan wala akanshi ake yi kisan kmr yadda kwakwaluwarsa take haska masa wala kuma wani laifin suka aikata mata take masu dauki dayday ,cikin sanyi jikin nan nasa tamkar mara laka ya matso ya kunna CCTV camera . idanunsa kawai ya zubawa camerar yana kallon wacce ta shigo masa gida cikin bakaken kaya wondo da riga gabadaya babu inda ta bari wanda zai kafa hujja akanta amman dai tabbas yanayinta ya nuna macece "to wacece wannan yarinyar ?tunaninsa ma yadda ta iya shigowa securities din bakin kofar shigowa basu ganta ba ? ko da yake ta yuwu wani abun tayi masu amfani dashi domin gusar da hankalinsu dan kuwa duk tashin hankali daaka shiga bacci suke basa ma cikin haiyacinsu har sai da aka taimaka masu ,tunda yake a rayuwarsa bai taba ganin mai kaifin baseera irin na yarinyar ba Sannan tunda yake bai taba samun kansa cikin damuwa irin na lokacin ba ,sam sam ya qasa kwanciya yayi bacci sai wurin karfe biyu saura bacci barawo yayi awon gaba dashi ." bangaren nuzla ma yadda taga safiya haka taga dare ga wani zazzafan zazzabi daya rufeta kafin gari ya waye ta sake yin wata doguwar rama jikinta ya dauki zafi kamar garwashin wuta dan haka dole da gari ya waye aka kira doctor ya dubata nan ya tabbatar masu da damuwa ce dan har jininta ya hau ya wuce kaida yayi ja hankalinta akan yawon tunani sannan ya daura mata drip ya kama gabansa hjy salema ta tsura mata ido kawai tana kallon yadda numfashinta ke fita da kyar ta riko hannunta cikin nata zafin jikinta ya ziyarci tafin hannun hjy salema bata son ganinta cikin damuwa da tashin hankali duk sai taji itama ta shiga damuwa yanzu da tana da dama data cire mata ciwon ta dawo dashi kanta "nuzla !."ta kira sunanta ta bude idanunta dake lumshe ta zubawa mahaifiyarta "meke damunki ko akan hisham ne ?ta gyada mata kai kawai alamun "eh! . "Halan akan maganar adamu yazo jiya ?ta sake gyada mata kai kawai dan bazata iya magana hjy salema ta numfasa kana ta cigaba da magana "me yasa zaki saka maganar aranki har haka ?tunani shine abu na farko dake fara nukurkusa rayuwar dan adam ,kiyi hakuri ki fallawa allah komai shi keyi a lokacin da yaso haka shi Ke hanawa alokacin daya so fatana Ki barwa allah lamarinki Kiyi addua abinda yafi zama alkhairi atsakaninki dashi Allah ya tabbatar mana, amman ina kyautata zaton zaki ji dadi agidansa zaki samu kwanciyar hankali a hannunsa domin hisham yaron kirki ne amman dai mu cigaba da addua mu barwa allah komai nuzla ta runtse idanunta kawai tana ji da abinda ya dameta ." tun safe mami da mrym har ma da nana hauwa'u suka shiga kitchen suna had'awa ata breakfast suna hira ,mami ta fito tana amsa wayar hajiya nuriyya wanda adaidai lokacin ata ya sauko hannunwansa duka acikin aljihun wondonsa, sanye da riga brown colour mai hannun long sleeve da dogon wando baki "eh ke dai nuriyya abinda ya faru kenan wallahi acikin estate din nan ne amman yanzu tunda ya dawo in sha allahu bazai wuce a saka sati uku zuwa hudu ba ba ,eh babu damuwa tunda open ticket zakuyi nan ata ya wuce yayi nufi hanyar dakin jim dinsa domin motsa jiki ." Har yayi taku biyu ya soma jiyo sautin magana kasa kasa kuma abinda yaja hankalinsa shine sunansa da yaji an kira ,ya dan dawo baya kad'an ya tsaya ya kasa kunne yana jin tautaunawarsu "matar yaya adamcy ikon allah miko min kayan ingredient din can na zuba ko ke kadai zaki hadawa mijinki breakfast na cire hannuna na kama gabana?"kai sister kina son kasheni da raina ." "dan nace matar yaya adamcy ikon allah shine zan kasheki da ranki ?mrym ta gyada mata kai alamun Eh ! ai in sha allahu sai anyi wannan auren ko ana so ko baa so kuma muna bayan ki kamar doro ki zuba mulkinki son ranki a gidansa dan kinci dubu sai ceto babu abinda zai faru "Allah yasa sister dan irin mijin da nake so kenan . "gashi kuwa kin samu kin yiwa sauran mata zarra ,na yiwa sauran mata zarra ko na fisu shiga matsala ?kina ganin dadi zanji a gidansa ni tun yanzu na fara tunanin yadda tunani da damuwa zai haukatani a gidansa ga rashin sonshi da bana yi ga matsalar taurin kai da wanne zan ji ? ." kina bani mamaki wani lokacin kamar ba mace ba ai ina gaya miki tsab zai sauke komai mrym ta girgiza mata kai kawai tana cewa "taimaka ki zuba min maggie dai dan ni ban san dalili ba duk yadda zan saka maggie a miyya sai yayi yawa ." "gsky matsalarki kenan sister mman da sannu zaki qara samun gogewa agidan yayana ,wannan yaya dai ana sona dashi shi kuma baya sona,ana son na shiga gidansa shi kuma yace aa wanne zaayi aciki ? "Ke manta dashi wuyarta ayi auren ,ko da yaushe sister haka kike fad'a min wani lokacin sai naji na amince da samu natsuwa ,wani lokacin kuma sai naji hankalina yayi kololuwar tashi ni kaina zan so na ganni a matsayin matarsa dan nasan da sannu zan iya son shi da yana son kenan matsalata a halin yanzu rashin són da ....." saurin datse harshenta tayi da karfi sakamakon ganin mutun tsaye ta bayan nana hauwa'u daman ta juya da niyyar fuskantar nana hauwa'u ne shirunta yasa nana hauwa'u tace "lafiya sister kikayi shiru ? bata iya bata amsa ba illa numfashi data dauke da karfi tana cigaba da kallon bayanta ." ya tako a natse ya shiga cikin kitchen din sosai kamshin daddan turare da takun da nana hauwa'u taji yasa ta dan juyo ,ta dan tsorata da ganinsa nan take gabanta yayi wani irin mummunar fad'uwa amman sai ta dake ta bude baki da sauri tana cewa "san ..sannu ya.. "saurin d'aga mata hannu yayi yana qara had'e fuska , nana hauwa'u tayi taku biyu zata bi gefensa ta wuce domin ta tsira da lafiyarta taji yace "munafukar allah Koma ki tsaya wato kina d'aya daga cikin masu bawa wannan guntuwar mummunar yarinyar kwarin gwiwar aurena ? tayi saurin girgiza masa kai alamun a'a "zan kifa miki mari yanzu idan kika sake girgiza min kai koni saanki ne ? ta sake girgiza masa kai cikin tsananin tsoro ." "Kika ce da zarar anyi aure shikenan?idanuwanta sukayo waje wani gumi ya soma tsatsafo mata akan hanci ,sannan kika ce ta manta dani wuyarta ayi auren ni zaa manta dani ?yayi maganar a matukar tsawace cikin bacin rai ,dan allah yaya kayi hakuri nifa ba wani abu nake nufi da hakan ba ina qoqarin gyara au...."ai wani mugun kallo da yayi mata batasan sanda tayi shiru ta qara shiga hankalinta ba ,kinga nayi miki kamata da irin mazan da zarar anyi aure shikenan ?ko kinga nayi miki kama da bawan mace ?ta girgiza masa kai alamun a'a ki shiga hankalinki wallahi idan ba haka nayi sadaka dake na bawa duk wanda naga dama aurenki mu huta sha sha banza da wani katon bakinki a wajen ." ita kam mrym hannuwanta duka tasa ta rufe fuskarta sakamakon hawayen daya cika mata ido idan akwai abinda ta tsana a kalamansa gareta bai wuce munzantata ta hanyar zagin halittar da Allah yayi mata "Ke kuma na dawo kanki nan da wasu kwanaki zaki zama mata agareni ban isa na hana hakan faruwa ba amman kamar yadda kika furta tunani da damuwa ne zai haukataki a gidana tabbas haka ne domin bakinciki da damuwa zaki aura bani adam ba ,daman tunda kika shiga rayuwata kema kinsan bazakiyi farinciki arayuwarki ba, har karshen rayuwarki a wahala zaki qare a gidana gara ma kije kiyi kuka da Kururuwan a fasa auren nan shine kawai mafuta agareki da kwanciyar hankalinki nonsense kawai da bata san me take yi ba ,yanzu ke kina ganin kin dace dani ?common maggie baki iya sakawa acikin abinci ba sai an taimaka an saka miki stupid girl kawai wallahi gara ki taimaki kanki tun wuri yana gama fadar hk ya juya ya fita daga kitchen din yana jan tsaki ." kuka mrym ta qarasa fashewa dashi ta koma bayan kofar kitchen ta hade kanta da bango tana jin wani irin zafi mai radadi duk da yadda take jin rashin sonshi amman haka ta bawa zuciyarta hakuri ta karbi aurensa amman shi burinsa yaci mutuncinta ya tozarta tasan yadda ya fad'a haka ne zai kasance rayuwar bakinci zatayi a gidansa zai hanata kwanciyar hankali da walwala ,zai hanata sukuni da jin dadi cike da jin haushi nana hauwa'u tace meye kuma abun kuka ? kina jin tsoron yaya fiyye da kaida ,"shiyasa naga kin iya mutsa masa alokacin da yake magana yake ci min mutunci , ko kin iya taka masa burki alokacin da yake cin zarafina ?tayi mgnr cikin bancin rai tana mai juyowa gbdy ta fuskance nana hauwa'u hawaye na zuba akan kuncinta." "Sarai kijin abinda ya fad'a yanzu ,kuma Kinsan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a ,shikenan nan ni haka rayuwata zata qare , kisa hannu sister ki saurari zuciyata kullum cikin bugawa take da karfi kin kuwa san abinda nake ji ?"gano yanayin tsoronki yasa yake miki haka wallahi ni ace nice zai aura bazan dauki abubuwansa ba ,"ki daina zugani sister yana fad'a min duk maganar daya ga dama, yana tozartani a duk sanda yaso , lallai ya kamata nayi kuka nayi kururuwan ataimakeni a kawo min dauki fasa auren ."nan tana gama fadar haka ta fice fuuuuuuu ta bar kitchen din ." kai tsaye dakinsu ta shige ta fad'a saman gado ta kwanta ruf da ciki sai nana hauwa'u ce ta qarasa hada masa breakfast."wuni ranar babu abinda mrym take sai cika take tana batsewa tana jan tsaki tana tunanin mafutar da zatasa a fasa auren ta huta abinda mami ta kasa ganewa bayan rashin son da yaya adam baya mata har da kasancewarta farar mace sol mara tsawo ne dan tasan yadda bai son farar mace yafi son chocolate colour yar doguwa mara kiba baa siyar da tsawo data siya ,baa siyan baki da ta koma baka Kmr yadda yake só tunda baya sonta kuma babu duk abinda yake bukata daga macen da zai so tô meye amfanin auren ?gara itama ta kawowa kanta mafuta tana kwance ta zabura ta mike tsaye ta fito ta nufi dakin mami lokacin karfe biyar daidai na yammaci" Mami na zaune a dakinta abakin gado kunneta manne da waya maryam ta shigo duk jikinta a sanyaye kallo daya mami tayi mata ta fahimci akwai damuwa dan haka ta katse wayar da take ta hanyar cewa "khadija zan kiraki zuwa anjima sannan ta ajiye wayar a gefenta tace "lafiya maryam naga kin shigo wani iri? duk da wuni yau na lura bakya cikin walwala , hawaye mrym ta share tace "gsky mami na gaji da abinda ya adam yake min ,ina ganin lokaci yayi da komai zai zo karshe ,numfashi mami ta sauke cikin tsigar rarrashi "haba maryam haba diyata ki daina fad'ar haka ,kece fa karfin gwiwana idan baki auresa ba nasan hk zai qare rayuwarsa bai yi ba kiyi hakuri wata rana sai labari ." "Amman mami ni haka zan qare rayuwata yaya baya fahimtar nima biyayya kawai zanyi ?nasani mrym amman ina ji ajikina wata rana Adamcy zai sauya zai zo har gabanki neman afuwan abubuwan da yake miki ido mrym ta zaro waje tace "mami ko kin manta halinsa ne ?"ban manta ba maryam amman na yarda da allah kuma Kinsan lamarin ubangiji ya wuce nan karkiyi mamaki wata rana ya zamo bawa agareki barin ma idan kin haihu dashi kuma gani a tsakanimu muddin ina raye bazaki shiga uku a gidansa ba ,ajiyar zuciya maryam ta sauke haka ne mami lamarin ubangiji ya wuce nan nima ikonsa ne yasa har zan zama mata agaresa ." "Haka mami ta zauna ta dinga tausar maryam tana bata baki har mrym ta saki ranta ta manta da batun wulakanci ata ta cigaba da harkokin gabanta ranta fari kwal washegari aka tsaida ranar dazaa daura auren ata da mrym hisham da nuzla nan da sati hud'u masu zuwa kamar yadda mami ta tsara shima dan alfarma cousing sister dinta nuriyya ne domin tana son yaranta suyi hutu tazo dasu gbdy bugu da qari lokacin zai yi daidai da hutun karshen shekara wanda daman kusan lokacin da yan'uwanta dake kasashen duniya ke zuwa hutu kenan bancin hk ai da kwanaki goma kawai zata saka ayi a wuce wajen shi kam mr ata kam ko ajikinsa dan babu ruwansa da ko sati nawa zaa saka idan ma an ga dama a daura a ranar ba damuwarsa bace ." A hankali yake saukowa daga saman mattakala jikinsa sanye da complete black suit yayinda kafafunsa ke sanye da brown shoe's agogon rolex ke daure da tsintsiyar hannunsa ,idanunshi na manne da wani hadadden farin glass ,a hankali ya cigaba da takowa cikin isa da izza alamun shi din wani ne a fadin nigeria ,yana saukowa sanyayyen kamshin turarensa REED ya soma tashi ta koina kamshin turarensa ne ya kaiwa hancin maryam ziyara da sauran jamma'a wurin sakon fitowarsa . Maryam ta dago idanunta a natse ta tsura masa tana kallonsa tun daga sama há qasa tamkar ranar ta soma ganinsa arayuwarta ji tayi gabanta na wani irin mugun bugawa da karfin gaske, hakan nan yau ta tsinci kanta da kasa dauke kwayar idanunta akansa sister dake zaune a gefenta ta bita da kallo tsab domin dai ta fara fahimtar wani abu akan maryam a din a game da yayanta a tun dawowarsa daga kasar france duk da ita taki yarda da zarginta tana nuna mata alamun bata son danuwanta amman kuma ita kar take kallonta domin kuwa akwai dinbin son shi makale a ranta da kwayar idanunta wanda itama bata san tana yi ba . " "taya zaka samu miji kmrshi kace wai baka so ai sai dai idan abun yafi karfinka nmj da mata suke nema har suke rububi akansa itam saa taci da kuma darajan mahaifiya if not har abada sai dai ta tsaya akansu abbas da anas shi kuwa kallo ne daga nesa dan fin karfi kam yafi karfin aurenta ."daga inda yake yana iya jiyo sautin muryoyin mutanen dake zaune a bangaren dining area, a natse ya tsaya idanunshi karrrr akan sister dinsa da maryam wacce ta zama tamkar doluwa a wurin rike da cup din tea a hannunta tana kallonsa abinda yafi tsana kenan kallon kurulla daga mace ,kallo daya yayi masu ya dauke kwayar idanunshi akansu yana busar da iska daga bakinsa tare da furta "nonsense "! a fili wanda hakan daya furta yasa maryam tayi saurin dawowa haiyacinta tana sauke naunayen ajiyar zuciya sai dai ta qasa dauke idanunta akanshi ta cigaba da kallonsa" bai tsaya akoina ba kai tsaye dinning área ya nufa yana shan kamshi , har ya samu wuri ya tsaya tare da soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa ,Still maryam bata dauke kwayar idanunta akanshi ba ,sister ta zungureta da sauri "ke ki dawo hankalinki mana wannan kallon da kike masa kin dai san halinsa , idan yaga dama sai ya sakaki kinyi bayanin wannan kallon dalla dalla ."numfashi maryam ta sake saukewa da karfi tana waskewa ta shafa gefen fuskarta tace "wani irin kallo kikaga nayi masa "? ni gbdy ma hankalina baya cikin gidan nan ." "yana ina shi hankalin naki ?nana hauwa'u ta tmbyeta tana tsareta da idanunta ,domin dai ita tasan gskyr abinda ta gani kenan kallon yayanta take amman tana kokarin waske mata "ki yarda sister da gaske shi kika ga ina kallo ?maryam ta tmbyeta tana qara shafa gefen fuskarta nana hauwa'u ta gyada mata kai alamun "eh!"zai iya kasancewa haka idanuna na kansa amman kuma hankalina ba akansa yake ba, mai ma zan tsaya kallo ajikin mutumin da ba mutunci garesa ba ?"tayi mgnr a hankali." "me kika ce sister naji kamar kinyi mgn ?"no no bance komai ba ,kinga sister dauko wayarki ki daukar mana abincin nan kar na manta ban daura breakfast din dana ci a social media ba ,ta fadi haka ne saboda ta shashantar da zargin sister akanta "okay ni nayi laifi kenan ?tô wallahi bada ni ba , matsawar bai bar parlour'n nan ba babu hoton wani abinci da zan dauka, idan kin matsu ki dauka da kanki wayarki ce bazan hanaki ba ta janyo wayarta dake ajiye ta mika mata ta tashi ta bar gurin gabadaya karta jaza mata balai da sassafe." A hankali maryam ta shiga daukar abinci gefe guda kuma tana faman satar kallonsa ta kasan idanunta, ba qaramin kyau yayi mata ba cikin shigar suit ,da alamu ma barin garin zai yi ko kasar gbdy karaf kamar ance ya waigo idanunsu ya tsarke cikin juna da mugun sauri ta dauke idanunta zuwa wani gefe tana sauke numfashi sama sama dogon tsaki yaja tare da furta stupid girl sannan ya samu wuri ya zauna batare da ya kalli inda sauran mutanen da suke zaune akan kujerun dake zagaye da dining table ba hakan kuma ya faru ne sakamakon zattukansu dake shiga kunnuwansa suna yi masa kuwa ." kallo daya mami tayi masa ta dauke kanta tare da girgiza kai sannan ta tura masa plet din abinci gabansa tare da black coffe wanda ya zame masa jiki a hankali ya dauki cup ya kai bakinsa ya kurbi tea kadan yana lumshe tsumammun idanunshi yana dan motsa kafarsa daya akan tayis magana baba qarami ya cigaba da yi cikin zafin rai sai dai "on expecting suka ji sautin muryar ATA yana cewa "babu abinda zaa bawa kowa sai abinda naga dama shima a siffar albashi ko kyauta zan bayar kamar yadda na saba .""yayi mgnr tmkr ba daga bakinsa ta fito ba hankali kwance ya cigaba da kurban tea yana lumshe ido ." "mai kake qokarin kace adam ?kana nufin mu babu komai namu acikin dukiyar ko me ? yes of course uncle domin babu shi acikin kundin da dad yake rubuce rubucensa aciki , amman mai yasa tun tuni baka taso da wannan maganar ba sai yanzu ?yanzu né naga ya dace nayi magana tunda naga ita wannan uwartaka batasan abun arziki ba, idan kowa yaja bakinsa yayi shiru saboda jin tsoronta da gudun magana toni bana jin tsoronta kuma bana gudun magana ,zanyi mgn km dole a kasafta abani rabona bazai yuwa kayi mana karfa karfa akan gumin da mahaifinmu yayi wahala ya tara tsawon shekaru ba ." "babu abinda zan bayar..., ."ya sake maimata mgnr daya fada yana sakin spoon din hannunsa hakan yasa hankalinsu yayi matukar tashi gab gab !! baba qarami yaji gabansa na wani irin faduwa gbdy parlour'n ya dauki shiru tmkr babu wasu hálittu a wurin "koda ma akwai dukiyar babu abinda zan cire na bawa kowa tunda babu shi a rubuce idan kuma kayi trying wani non..."shiiiii mami ta furta tana daura dan yatsanta akan lip's dinsa dan dakatar dashi domin tasan halin kayanta karshe kalmar nonsense ne zata fito daga bakinsa "wai meye haka kake yi adamcy ? baba qaramin sa'anka ne"? "Karka manta kanin mahaifi ne me yasa ma sai anan zaa yi discution din wannan matsalar dan kawai a daga min hankali ? ta juya inda baba qarami ke zaune "karki fada min hk sannan abu na gaba ki fada wa d'anki yayi bincike mai kyau akan abinda na fada tabbas akwai dukiyarmu acikin dukiyar ubansa wanda byn mutuwar mahaifinmu muka barshi a hannunsa idan kuma ba hk ba komai zai iya faruwa idan wani abu ya faru ki kuka da kanki karki yi kuka da kowa." yana gama fadar haka ya mike cikin tsananin fushi yaransa maza biyu salim da sultan suka mike suna hararar ata kafin daga baya suka marawa mahaifinsu baya . Hajiya zualai ta mike tsaye cikin tsananin tashin hankali tana binsu da kallo gabanta na faduwa tasan yana son kunno da damuwa ne sbd rashin amincewar auren adamcy da hindu da kuma makudan kudaden da yayansa sukai qoqarin hadamewa adamcy ya hana ,ATA ya kai hannunsa ya riko tsintsiyar hannunta "sweetheart ki zauna "ta zauna cike da sanyin jiki tana duban kyakkyawan tilon dan nata nmj kwaya daya da allah ta mallaka mata "karki damu sweetheart da mgnrsa everything will be fine tunda ni bani da wani business dashi so karki saka wani abu aranki ,ban san meye damuwarsa ba ."? " ban san me yasa yakewa kudi mugun só haka ba ."? duk ribar dake shigowa ta AGC ina iyakar kokarina ana cirewa kowa hakinsa na bashi kuma sweetheart a qokarina na kar company ya ruguje kullum hannun jari nake qarawa batare dasanin kowa ba kuma su waye ke kokarin karya company ? yaransa né kullum cikin sata suke sannna yanzu yazo da wani batu this time around sweetheart sai dai ki yi hakuri I can take it dan bazan dauka ba wallahi baba qarami na mugun son kudi duk ma yafi sauran karbar kudi a kamfani amman yanzu yazo yace ga zance ga magana agc ne dai yanzu na soma zuwa kula dashi bazan yanke zuwa ba bare su samu damar yin babakeri da dukiyarmu ." " adamcy ni nasan baba qarami ba kudin yakewa ba, tunda bai taba mgnr wasu kudade ba sai yau na dai lura tunda aka fito da batun mgnr auren da maryam ya canza , amman nasan ba komai yake damunsa ba so yake ka auri diyarsa hindu ."shiru adam yayi yana sauroronta yana tsakurar abincin gabansa batare da ya furta komai ba dan babu ruwansa da mgnr "ko zaka taimaka adam ka had'asu duka biyu ka auresu"? "What ?" ya furta da mugun karfi yana sakin spoon din hannunsa "mami ta lumshe masa ido "kayi tunani akai kaji adamcy nah "am done am leaving kiyi min addua fatan alkhairi ya fada yana mikewa da d'an hanzarin ya soma tafiya cike da kuzari hannunsa daya cikin aljihun wondonsa." tabi bayansa da kallo tana kiran sunansa cikin tsananin tashin hankalin "adamcy !adamcy !!! Ka tsaya kaji me zance adamcy ."amman ina bai juyo ba bare ya tsaya yaji mai zatace,itama tasan adaidai wannan yanayin da yake ciki bazai tsaya ya saurareta ba domin maganarta ce tasa zuciyarsa ta yunkuro har ya kasa sauraranta shiru tai tana dafe goshinta cike da takaici da kuma mamakin halin biladam ."mutane sam sam babu tsoron allah aransu "shekara da shekaru baka tashi dauko maseefa ba sai yanzu dakaga yaro zai yi aure kazo da wata magana ." Tana cikin wannan halin maryam ta qaraso hannunta rike da glass cup da magani ta mika mata "ki cire damuwa aranki mami ki sha magani lokacin shan maganinki yayi mami ta dago kanta ta kalli mrym yana daya daga cikin abinda yasa ta kwadai tawa danta aurenta domin zai samu natsuwa daita muddin tana raye sai ta zama uwar gidansa km uwar yayansa ".na gode maryam da kulawar da kike bani "haba mami kullum sai kinyi min godiya karki manta ni din fa dolenki ce haka kema dolena ce duk abinda nayi miki tmkr nayiwa mahaifiyata ce "haka né maryam amman duk da hk na gode sosai allah yayi albarka kinci abincinki ko kuwa kin tsaya tallatawa duniya "?mrym taí murmushi tace "kai mami naci !"kina ji ko mrym kiyi kokari ki rage son social media din nan idan ba hk ba bazuku shirya da adamcy ba kasancewar shi mutun ne da yake da raayi dan allah ki daina kmr yadda na sha fada miki "in sha allahu mami zan rage tare suka baro parlour'n ." ****** Karfe 11:00 daidai na safiyar laraba nuzla zaune a parlour'nsu ita kad'ai cikin tunani da zullumin abu biyu aurenta da hisham da kuma aikin da ata ya bata wanda ita sam bata jin zata iya aikatawa ita da kyankyaso ma tsoronsa take ji bare akai ga kissan mutun ai tasan duk runtse duk wuya bazata iya ba kullum tana gida bata fita koina duk da tana buqatar fita yin shopping din abubuwan buqatanta amman haka ta hakura ,tun kwanaki uku da suka wuce waadin da ata ya bata suka cika amman shiru babu wani sammacin daga yansanda haka zalika babu wanda yazo mata da magana makamanciyar zarginsa akanta dan haka ta dan samu natsuwar zuciya ta mike tsam ta shiga dakinta ta shirya cikin kananan kaya ta daura abaya a saman kayan tayi roling kanta da mayafin abaya ta dauki turare ta feshe jikinta ta dauki handbag dinta ta rataya ta fito ta shiga dakin hjy salema tana zaune tana lazimi akan dadduma dan ta idar da sallar wallaha kenan ." "momy zan dan je shooprit na dawo murmushi jin dadi ta sakar mata dan yaushe rabon ta fita kullum tana kunshe a daki cikin damuwa "sai kin dawo nuzla allah ya tsareki ta bata amsa da haka cikin halin farinciki "akwai kudi a hannkin ne ?ta waiwayo tana dubanta "akwai kudin da yaya Ibrahim ya tura min cikin account dina dasu zanyi amfani to shikenan sai kin dawo ta juya ta fita daga dakin tana kiran bolt dan bata jin yin driving ." a hankali take taka qasa har ta fito bakin get din estate dinsu fuskarta a daure kana ganinta zaka fahimci tana cikin damuwa kadan tayi tafiya tana kiran mai bolt taji a inda yake kawai taga motar yansanda a gabanta nan take taji gabanta yayi wani mummunar bugawa da matsanancin karfin gaske ta sauke wayar kunneta batare data kashe ba ta tabi gefe zata wuce cikin tashin hankali tana adduar allah yasa ba wajenta suka zo ba amman ga mamakinta mutun biyar suka fito suka sha gabanta suka tsaya ta kallesu daya byn daya cikin tashin hankali kafin ta kai ga bude bakinta duk suka fito mata da ID card dinsu daga gaban aljihu suka nuna mata daya daga cikinsu yana cewa "sunana inspector Almustapha hasan umar da fatan kece nuzla ? Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 24 Qoqarin cire tsoro da fargaban dake tattare da jikinta tayi ta aro jarumta ta sanyawa jikinta tace "Eh yes nice nuzla fatan dai lafiya kuka tsayar dani ? "Ki adana tambayarki tukunna muna gayatarki zuwa office dinmu yanzu ."akan wani dalili kenan kuke gayyatata ? idan munje zaki ji komai ,kamar tayi musu taurin kai amman sai taga d'aya daga cikin 'yansanda na qoqarin fito da handcuff daga cikin aljihu yana cewa "zaki wuce muje ta girma da arziki ko kuma sai mu saka miki handcuff mu wuce dake ta karfin tsiya ." ba tayi mutsu ba dan ta rigada tasan da komai dan tun tuni take jiraye dasu saboda dama tasan hakan na zuwa saboda tun rabuwarsu da yaya adam tasan ya zuba tsaro sosai akanta ta yadda duk wani motsinta arayuwarta yana sane dashi ,haka ma yansanda, dan tayi imani anan din ya bada umarnin aka mata dan da suna son kamata cikin tonon silili da har ciki zasu biyota ,ba tayi ma tunanin zata wuce lokacin daya bata batare da ta shiga hannun hukuma ba." sosai zuciyarta ta shiga rudani taji wani gagarumin bakinciki ya rufe mata kahon zuciya kuma tayi imani matukar tayi gardama dasu haka zasu da'ba mata handcuff su wuce daita , ta ma godewa Allah da ba har cikin estate dinsu suka shigo suka tafi daita ba ai da kuwa ta shiga ukunta ." Ahankali ta soma daga kafafunta domin isa inda motarsu take jikinta na karkarwa a duniyarta idan akwai abinda ke firgitata shine hukuma tana tsanani tsoron shiga hannun yansanda, duk da tasan ba wani laifi tayi ba ,dan abinda har yasa suka gayyace din akanshi bata aikata ba ."tafiya take tana tunani da mamakin wanda ya aiko su "me ta yiwa yaya adam da zafi har haka daya kasa yafe mata ? shin laifi ne dan tace tana son shi?dan dai tasan hukuncin zafin furta masa kalmar só ne ya janyo mata wannan tashin hankali, tayi masa runtsuwa da Allah bata aikata abinda yake zarginta akanshi ba amman ya kasa yarda daita "shin tayi masa kama da wacce zata iya kisan kai ko yunkurin kisa ne ? zuciyarta ta dinga mata zafi tana mai sake tabbatarwa kanta lallai yaya adam baya sonta, bayan soyayya ta aure har da soyayya ta yanuwantaka ma baya mata gashi ita duk duniya babu wanda take so sai shi ." "anya bazata rushe wannan wahallalliyar soyayyar ba ta dawo qiyayya da tsana mai tsanani ba "? ji tayi jikinta yayi sanyi matuqa dan bata jin zata iya wannan aika aikan ,jikin nuzla a sanyaye yansanda suka sakata a bayan mota tare da wasu jami'an tsaro mutun biyu inda zuciyarta ke wani irin bugawa da karfin gaske sakamakon bakincikin sakata a tsakiyarsu da sukayi tun anan idanuwanta suka canza kala tana kallon tafkeken get din estate dinsu aka wuce daita ,tafiya kadan sukayi suka iso police station."direban motar yayi parking ya kashe motar sannan suka firfito suka shiga ciki suka karbi duka kayanta sannan aka bude wani daki wanda babu kowa aciki suka sakata ciki suka maida kofar suka rufe kukan bakinciki ne ya kufce mata ,ta soma rera kuka tana jin wani irin zafi acikin ranta saboda ta duba hagu da dama babu inda zata zauna duk inda ta kalla qazanta ne da zarnin fitsari uwa uba duhu ." Aqalla ta kusan awa biyu tsaye tana jiran azo a fara tuhumarta domin a tunaninta da sunzo zasu fara jeho mata tamabayoyi tana basu amsa idan sun gano bata da laifi su saketa ta kama gabanta batare da sanin kowa ba sai taga sun shareta sun ma shiga wata tsabgar dabam har wata awa daya tazo ta wuce basuyi lokacinta ba ,wanda zuwa wannnan lokacin kafafunwanta sun fara sandarewa da tsayuwa ahankali tayi qasa ta tsuguna a cimintig dakin tana hawaye yayinda bakinta ya soma furta adduar neman dauki ." Shi kuwa ATA lokacin da sakon samun nasarar kamata ya isar masa yana zaune a parlour'n mami tare daita dan bai jima da shigowa ba lumshe tsumammun idanunshi yayi sannan ya motsa labbansa da kyar "ina fatan babu wanda yaga lokacin da kuka wuce daita ?okay sai nazo ya fad'a tare da jan boyayyan numfashi ya sauke ,okay zaku iya fara aikinku kafin na shigo amman karku ta'ba lafiyar jikinta ,sun dauki Kmr minti goma suna magana yana gama waya ya ajiye wayar a gefensa yana jijjiga kafarsa daya mami wacce kwayar idanunta Ke kanshi a tun sanda ya fara wayar yace ." "Yaakayi adamcy nah naga kayi wani iri ko akwai damuwa ne ?cikin kwantar da murya yace "no sweetheart yunwa nake ji ,bari nasa aka ..."haba sweetheart karki saka kowa please ni ban san me yasa kike yawon sako wasu cikin lamarina ba" to sarkin korafi ,kai dai da wannan halin naka Allah yasa ka canza ,kullm kai kenan cikin bakin hali naga ranar da zaka canza bazaka barni naji da tsufana ba tun kana yaro nake hidima da kai har gashi ka tsufa ta qarashe mgnr cikin salon tsokona tana hade rai ." Ya dago a sukwane ya tsura mata idanuwanshi "yanzu ni ne na tsufa sweetheart?sosai kuwa kai yanzu tunaninka baka tsufa ba ?haba haba !!sweetheart allah idan ba fad'a akayi ba babu mai cewa na wuce 40,dan ni wallahi jina ma nake Kmr .." "kai dan Allah kama mana baki shima gyara ne ,da babu gyara da kasan kai ba yaro bane "wel ko babu gyara zan zama Kmr yaro dan gadon jikin mai kyau nayi " "A wajen kenan ? Ya sake tsaita idanunshi akanta sosai yace "wajenki mana! shakiyi kawai ya dai kamata ka rage wadan nan abubuwan dan ka kusan zama baba nan da wani lokaci ,nan da nan ya hade rai Kmr wanda aka fadawa sakon mutuwa duk da tsananin son haihuwa da yake amman kwata kwata baya qaunar haihuwa daga mrym ya gwamaci ya qare rayuwarsa babu haihu akan ya haihu daita ". Ahankali ya bude bakinsa zaiyi magana mami ta katseshi dan tasan ba alkhairi zai fad'a ba "ina son zuwa yanzu ka bawa mrym matsayi mai girma acikin zuciyarka ,ya sake kallonta cikin rashin fahimtarta "Eh !nasan abinda nake yau idan ka runtse idanunka da zumar bacci ka matso daita kusa da zuciyarka zaka ga abubuwa masu yawa akanta" ya dage girarsa daya yana dubanta dan ya fara gano rikicin tsufa ya fara kama mahaifiyarsa idan ba hk ba ina shi ina wani kusantota da zuciyarsa yaji me ?bai gama mgnr zuci ba ya sake jiyo sautin muryarta ". "tunda ta zama mahadin rayuwarka dole zuciyarka zata dinga bibiyarta " numfashi ya sauke da karfi dan yasan ba abune mai yuwuwa ba shirunsa ne ya bata amsa mgnrta "ta gyara zama kai dai kayi qoqarin yau kawai ka kusantota da zuciyarka idan Allah ya kaimu gobe zan tmb..."sweetheart yunwa !"Okay bari na tashi sarkin korafi "thank you my sweetheart Kiyi sauri please dan yunwa nake ji sosai har cikina ya fara zafi "dariya ma ya bata a duk sanda taji ya fadi haka sai taganshi tmkr yana yaro ,adamcy kenan ko yaushe zai san ya girma ? kullum idan yana gabanta tmkr qaramin yaro yake dawowa ." Jallof din kuskus wanda yaji hanta da nama da ugu ta kawo masa ta ajiye agabansa tace "bismillah sarkin korafi kallonta kawai yayi yana girgiza kai sannan ya fara ci a natse ta zauna a kujerar dake fuskantarsa tana kallonsa hatta cin abincinsa dabam ne ,yana ci tana yi masa hirar yadda take son bikinsa ya kasance shi dai bai ce uffan ba ya cigaba da kwasar abinsa bayan ya gama cin ya mike ya haura saman d'akinsa wanka yayi ya canza kaya marasa nauyi ya zauna abakin gadonsa ya kunna system ,ahankali sakonnin abokan kasuwancinsa ke shigowa wasu ya amsa wasu kuma ya wuce ." Washegari yana zaune akan daya daga cikin kujerun dinning sanye da wondo da riga long sleeve sai dai ya dan nade hanuna rigar kadan ta yadda zaa iya ganin hadadden agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ,yayinda mami ke tsaye a gefensa tana qoqarin saving dinsa ,ta kallesa zaune shiru ya hade hannunwansa waje daya tace "jiya da nace ka rufe idanunka tare da kusanto mrym da zuciyarka , fad'a min daka rufe idanunka me ka gani ."Kai sweetheart "nasan mrym ka gani alokacin daka rufe idanunka ko ba haka ba ?" ni ba wata mrym dana gani sai princes dina na gani ." " kada kayi min karya dan nasan baka iya karya ba "tunda Kinsan bana karya ya kamata ki yarda dani wallahi ni banganta ba Kinsan wani abu a duk sanda na runtse idanuna princess dina nake gani wata rana cikin farinciki wata rana cikin damuwa nifa jikina yana bani yarinyar nan ba karya bace gsky ce km ba aljana bace tana nan acikin duniyarmu sai dai a ina take? " yaushe ne zan ganta ?shine bansani ba amman nasan zamu hadu shiyasa nake jin Kmr a fasa wannan auren "kai sakarai menene ya kawo batun a fasa aure kuma daga magana ?" Kamar yayi dariya ganin yadda magaarsa ta d'aga mata hankali "wannan auren fa sai an daurashi babu makawa zaku rayu tare har ma wata rana zaka amince daita tare da furta wa mrym kalmar so na tabbatar maka da haka "tunda ya fara cin abinci bai sake cewa uhm ba bare uhm uhm har ya gama ya goge bakinsa da tissue ya mike tsaye yana qoqarin yi mata sallama suka jiyo sallamar baba babba fuska cike da damuwa mami ta bar ATA ta qaraso wajensa a inda yake tsaye dan ko zama bai samu damar yi ba kallo daya mami tayi masa ta fahimci yana cikin damuwa suka gaisa adaidai lokacin da ATA ya qaraso ya gaishesa cike da girmamawa sukai shiru mami ta dubesa tace "baba babba ka zauna mana bari akawo maka breakfast ." Yace " zulai ba sai na zauna ba nazo ne na sheidawa adamu tun jiya baa ga halimatu ba daga zuwa siyaya nan da nan hankali mami ya tashi "baa ganta ba to ina taje ?kuma an kira layinta bata d'auka ba ?wallahi kwana mukayi kiran layukanta guda biyu shiru abinda yafi daga min hankali bata saba irin haka ba ,kuma duk runtsi ka kira wayarta zaka sameta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun mami ta furta tana cewa "Allah ya cecemu " ATA ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa yaga lokaci ya fara tafiya ya bude bakinsa da kyar yace "baba babba muje daga waje yana gama fadar haka ya nufi kofar fita suka bar mami cikin tsananin damuwa ." tare suka jera har haraban estate din baba babba yana sake masa bayanin tashin hankali da suke ciki "ka kwantar da hankalinka baba nasan inda take "wani irin naunayen ajiyar zuciya baba babba ya sauke yana dubansa a tsanake tare da neman qarin bayani ."wani dan bincike zaayi akanta da zarar an kammala zata dawo gida "shiru baba babba yayi yayinda zuciyar tsohon ya shiga bugawa fiyye da kaida domin kai tsaye kwakwaluwarsa ta hasko masa binciken da zaayi akanta muryar tsohon a sanyaye yace "to allah yasa muji alkhairi" ameen !ATA ya furta atakaice anan suka rabu yayi masa sallama ya nufi inda motacinsa Ke jiransa dan tun fitowarsa aka gyara tsayuwar su , tun kafin ya qaraso escort dinsa dake tsaye tmkr mashi suka yo kanshi cike da girmamawa ya shiga mota suka bar gidan ." Bangaren nuzla kuwa gaba daya duniyar ce ta cakude mata waje daya bata ta'ba sanin haka tashin hankalin irin wanda take ciki yake da ciwo ba"ta dauka zafi da ciwon rashin son da yaya adam ya nuna mata shine damuwa mafi tsayi arayuwarta a she qaramin abu ne damin kwana daya tal da tayi acikin dakin kurkun da take ciki ya ninkashi sau babu adadi ,tana durkushe bisa gwiwowinta tare da rufe fuskarta da tafukan hannunta taji motsin ana bude qaramin kofa ,bata bude idanunta ba bare taga masu shirin budewa ,wata murya taji ta doki dodon kunnenta cikin tsawa tana bata umarnin ta fito sai lokacin ta bude idanunta da suka kumbura tsabar kukan data kwana tanayi ." Koda ta motsa qafafuwanta dan mikewa sai taji ta kasa yunkurawa dan sun qara sandarewa kamar dotse ,hannunta ta kai ta rike karfen kofar sannan ta kai dayan hannunta ta riko kafarta daya ta yunkura da kyar ta mike tsaye ,ahankali ta fito wani qaramin daki aka nufa daita, babu laifi yafi wanda ta fito tsafta kujeru biyu tagani sai table dake tsakiyarsu ."tun kafin abata umarnin zama ta zauna dan kafafuwanta bazasu iya cigaba da daukarta ba ,mutumin daya shigo daita ya fita byn second biyar wata police mace ta shigo fuskarta a hade har tafi na farko ban tsoro da razanarwa duk da bata aikata komai ba amman zuciyarta ta cika da tsoro mai tsanani ." Idanunta na kan nuzla ta ajiye wukake har guda uku akan table din gabanta sannan ta zauna tana fuskantarta ,nan nuzla ta sake tsurewa hankalinta ya sake tashi wasu hawaye masu zafi suka samu nasarar gangarowa daga kwarnin idanunta ." Bayan mintuna goma police ta soma da tmbyr sunanta ta dago idanunta dake zubar da hawaye ta bata amsa sannan ta cigaba "yanzu dai sheidar da muka samu daga bakin danuwanki ya kore duk wata hujjar da muke nema akan masu amfani da wannan wukar wajen kisa da fari ko zamu san dakilinki nayi kisan ? Nuzla tayi shiru dan bata da amsar da zata bata sai dai ta dago ta zuba mata idanunta tana kallonta hawaye na zuba daga kwarnin idanunta ,ganin yadda matar ta soma huci tana fito da jajayen idanunta yasanya hankalin nuzla qara tashi ba shiri ta soma mgn cikin rawar murya "ni ..ni ban kashe kowa da wannan wukar ba, hasalima ni a yanzu na fara ganinta "amman ai kin ta'ba turawa yayanki adam sakon zaki ga bayan matar da zai aura ko me zaki iya cewa akan haka ?babu abinda zan iya cewa akan haka baya ga qaddara , kuma nasan tana iya fadawa akan kowa ,a garin na tsoratar dashi akan tsananin soyayyar da nake masa wannan matsalar ta faru dani ." "kenan kin tura masa sakon cewar zaki ga bayan matar da zai aura ? ta runtse idanunta wasu ruwan hawaye masu zafi suka zubo mata ta gyada mata kai "Eh! na tura masa amman ban aikata komai ba"karya kike karki wahalar da hukuma domin yin hakan yana qarawa mai laifi laifinsa dan haka ki fad'a mana gsky domin kawowa rayuwarki sauki " Nuzla ta girgiza mata kai jikinta na rawa "Allah ki yarda dani ban san komai ba "da fari kin kashe mubina wacce ta kasance yar uwa agareki kin kashe sadiya dake aiki tare da yayarki shahida yanzu kuma kinyi yunkurin kashe mrym shiru tayi kawai tana tunani wacece sadiya kuma ?ta dai san mubina da maryam amman sadiya kam bata santa ba ." "Kin kashe mubina yaruwarki dan ta furta tana son adam haka zalika kun hadu da sadiya a hospital kafin rasuwarta itama ta furta tana son adam kin yunkuro kan mrym ita kuma dan ta amince zata auresa kin kashe mutun biyu din nan adalilin sun furta suna son abinda kike so ko ba haka ba ? Ji tayi zuciyarta ta tsaya CAk ta daina aiki na wani lokacin kafin daga baya taci gaba da bugawa ji take magaarta ba'a kunneta kadai ya tsaya ba har cikin zuciyar ta take jin komai saboda dacin kalmar ." "kuka ta saki mai cin rai meke shirin faruwa dani ?ta furta a fili cikin tashin hankali da firgice ,wai ita ake zargi da laifin da ba taji ba bata gani ba kallonta tayi da idanunta da suka koma kmr an diga jini acikinsu , tace "me zakice akan haka ?daga kalmominsa komai ya sauya mata ta gane ita din ba kowa bace sannan ta soma fahimtar bata isa tace zata ma kaddarata wayo ba ,yau din taxo mata da tashin hankalin da rudani ya zatayi da kaddara da ta fada mata " ?duk yadda yarsanda taso ta amsa laifinta amman taki dan haka ta mike ta fice ta bada umarnin a canza mata daki zuwa wani dakin dabam ." Ai tana shiga dakin hawaye nadamar furucinta ya kufce mata domin har gara dakin farko daaka sakata dan wannan bashi da maraba da kabari yayinda zarninsa da warinsa da duhunsa ya zarta duk wani wari da mutun ya ta'ba ji tana kuka tana istigifari" Allah na tuba Allah ni bawar ka ce ya Allah kasani ban aikata laifi mai muni hk ba amman na kudurta yinsa ka gafartamin ban isa na maka wayo na hana faruwar kadarata ba " Allah ka kawomin sauki cikin wannna tashin hankali". kuka tayi sosai ,sai dai duk rintse bazata taba karban laifin da bata aikata ba ."Ahankali kwakwaluwarta ke son tuno mata wacce sadiya dake aiki da aunty shahida da tunanin wanda zai iya aikata wannan taadanci acikin danginsu a daura mata , sai dai duk tunaninta kwakwaluwarta ta kasa gano kowacee sadiya da kuma wanda yayi amfani da damarta yayi mata haka ,hakika bata da makiyi kamar shi kuma ya cutar daita ya zalinceta ba kuma zata ta'ba yafe masa ba ,wajen bazai isheta zama ba dan hk ta gwamaci ta kwana acikin zarni da kazantar waje tana kwance taci kuka ta koshi idonta sunyi lulu dasu ." Qarfe biyu daidai na rana ya fito daga cikin makeken office dinsa kai tsaye hanyar massalacin dake cikin ma'aikatan ya nufa yayi sallar azahar sannan ya bawa direbansa da masu tsaronsa umarnin tafiya police station babu bata lokaci kowannensu ya zama ready yana qarasa isowa aka bude masa mota ya shiga suka dauki hanyar police station yana shiga kai tsaye da cp Amir suka hadu suka tsaya suna magana akan nuzla suna gama magana cp yayi gaba zai masa iso wajen dpo ."tun kafin ya kai ga shiga dpo ya mike ya fito da kanshi cikin girmamawa yau ga matun kamar adam tariq abdullahi acikin station dinsu dan kasuwan daya fi kowani dan kasuwa kudi ya shiga office din suka zauna cp ya basu waje suka gaisa sannan suka soma tattaunawa akan nuzla ". "ranka ya dade mai zai hana awuce kotu kawai ?ciza lip's ATA yayi yana girgiza kai muryarsa a matukar raunane yace "a'a nan ma ya isa banason aje ga kotu fatana ma ya zamanto babu hannunta ciki ,amman yanzu abi mataki na karshe ayi amfani da sheidar hannunta "muma shine last option dinmu domin shi zai warware komai ya runtse idanunshi hankalinsa na sake tashi babu wanda yake tausayi Kmr mahaifinta da mahaifiyarta yayyenta da kuma masoyinta hisham ya tuna halin daya gansa yau din gbdy baya cikin natsuwarsa haka ma yan'uwanta ya sauke naunayen ajiyar zuciya yana cewa "ko zan iya ganinta ?why not ranka shi dade "inspector runke !ya kwallawa yarsandar dake kan kanta kira cikin girmamawa ta shigo sai data sara masa sannan ta kame waje daya "jeki fito da yarinyar nan wacce akawo jiya "Okay sir ta fad'a tana juyawa cikin sauri ." Tana fita ATA ya kalli dpo "amman babu wanda ya ta'ba lafiyar jikinta kawai gsky nike bukata ?"yallabai babu wanda ya ta'bata yarinyar ma bata da rigima tunda aka kawota take kuka, very gud kar wanda ya ta'ba lfyta in sha allahu yadda kace haka zaayi batayi ma rashin kunyar da zaa ta'ba lafiyarta ba kawai dai taki amsa laifinta ne ya qarasa mgnr adaidai lokacin daaka shigo daita kallonta kawai yayi yana mamakin yadda kamaninta ya canza acikin kwana daya da yinin datayi ga dai shi babu alamun duka ajikinta amman cizon tsoro yayi mata yankan qauna ga dotti ya soma zama ajikinta tana ganinsa ta fashe masa da kuka tana cewa "dan girman allah yaya adam ka ceceni kasa a fitar dani daga nan wallahi idan na cigaba da zama anan mutuwa zanyi wallahi ban aikata komai ba ." ATA dake kallonta ya sake hade fuska babu wata alamun tausayi bata damu da yanayinsa ba dan tasan halin miskilancinsa da zafin zuciyarsa dpo Karan kanshi ya tausaya mata ya nuna mata wajen zama ta zauna ATA ya tsareta da idanunshi yana kallonta yayinda ita km ta cigaba da sheshekar kuka "har yanzu kenan baki shirya fad'ar gsky ba ?ban aikata komai ba me yasa zan amsa laifin da ban aikata ba wallahi kasa a tsananta bincike ni nasan ko waye acikin estate dinmu yake amman ni ban aikata ba ,wani kallo yayi mata sannan ya mike tsaye zaa yi bincike na karshe akanki kiyi adduar babu hannunki dan muddin ya zamoto kece zaki qarasa rayuwarki a inda yafi nan muni yana gama fadar haka ya bada umarnin a fitar daita tana kuka tana kiran sunansa aka fice daita ya kalli dpo yana sake jadda masa kar ta'ba lafiyar jikinta har sai an gama bincike yayi masa kyauta sannan ya wuce ." ***** bayan tafiyarsu alhj alqasim ummah suna hira da maryama tace da zarar kin qare bautar kasa kema zanyiwa alqasim magana ya nema miki aiki mai kyau ta yadda zaki samu damar taimakawa aunty ,dan Allah ummah kiyi masa maganar idan ya dawo kinga yace qasar ma zasu bari kinga idan yasan da maganar wata killa zai barwa wani sallahu". " in sha allahu maryama zanyi masa mgn kuma nasan zai min wannan alfarma bare kuma naga alamun kin kwanta masa arai murmushin jin dadi maryama tayi tace "ai duk saboda ke ne ummah darajanku naci banci haka ai bazan taka matsayin ko daura kwayar idanuna akanshi ba ". hirar sukayi sosai cike da so da kulawa wata ya qare ummah ta saka ran zuwansu alhji alqasim amman shiru har wani wata ya kai goma dan haka ta fidda rai da ganinsa koda ummah tayi hirar da maryama ta rausayar mata da kwayar idanunta domin ita a ganinta haka masu kudi suke da fad'ar abu su fasa mussaman idan bai shefesu ba "ummah karki wani damu da rashin zuwansu tunda daman su suka saka kansu ba wani ne ya sakasu ba ." Satin da suke ciki ya qare babu dalilinsu sai da aka sake shiga wani sati sai ga wayarsa yana sanar da yaya sadam yana nan zuwa ranar lahadi ranar suna jumaa dawowarta kenan daga wajen aiki ta samu labarin zuwansu daga bakin ummah ai kuwa dadi kmr ya kasheta da murna ta shiga side dinsu tana sanar da aunty cewar ranar lahadi zasu zo dan daman ta fad'a mata taimakon da ummah zatai mata sosai taga farinciki a fuskar aunty daman ita kadai take tausayawa a rayuwarta tana son ta taimakawa mahaifiyarta amman bata da hali ,dan zanen da take ba wani manya kudi yake kawo mata ba sakasancewar sai kayita bin office office na masu kudi dan ba kowa ya gama saninta ba bare su nemeta dan kansu, gashi tana son fitar da mahaifiyarta cikin wahalar da take ciki amman bata da iko sai dai ta mika lamuranta zuwa ga Allah dan ya kawo masu saukin halin da suke ciki. ranar lahadi aka sake maimata irin hidimar daakayi masu a wancan ranar sai dai kuma wannan zuwan nasu akwai qarin abubuwa masu yawa daakayi karfe goma da yan mintuna motarsu ta tsaya a sabon titi market street wannan zuwa babu driver da babban dansa yusif da kuma kanwarsa Kausar sai dady da yake zaune a bayan mota ranar kamar wacan ranar yaya sadam ne ya tarbosu zuwa cikin gida sai dai shi Yusif bai shigo ba ya tsaya a haraban gidan yana amsa waya ."sakina aunty salma da aunty hassana da yayanta da baba gali duk suka fito tarbonsu ita kuwa maryama sai ta koma dakin ummah duk da tana bukatar farinciki wa rayuwarta amman sai ta boye kanta ."Kausar tafi yusif surutu dan ita take ta haba haba da su sakina da Islam da kaulat har ma da shukura da bata ta'ba ganinsu ba umma ta fito suka gaisa ta tmbyesu hanya ." Wannan dalilin yasa ta fito daga dakin umma dan karta kwatanta na kwana baya sai dai ta kasa shiga cikinsu ta rabe can nesa dasu byn ta gaishe da dady ta fito ta zauna a tsakar gidansu hannuwan yusif acikin aljihu ya shigo bakinsa dauke da sallama wacce ta makale a fatar bakinsa ganin maryama ya tsayar masa da sallama ya tsura mata ido jikinta ya bata ana kallonta dan haka ta dago a natse domin ganin mai kallonta nan take ta firgita ta qara gyara zamanta da daidaitawar mayafinta." ya tsura mata ido sosai yana kallonta ahankali yace "sannu !" sautin muryarsa ta doki dodon kunnenta amman ta kasa maida masa da sannun da yayi mata sai sunkuyar da kanta tayi dan bata son yawon kallo shine ma dalilin da yasa take yawo da nikaf duk inda zata dan sai mutane suyita kallonta wai tana da kyau da sauri ta mike ta nufi hanyar side dinsu ya dan lekota adaidai lokacin data waiga suka hada ido jin alamun tafiya yasa ya dawo da natsuwarsa sannan ya shiga cikin parlour'n umma da sallama tana ganin shigarsa ta dawo dan bata son tayi nisa ummah tazo tana nemanta ai kuwa tana zama tajiyo sauti muryar ummah tana kiran sunanta jiki a sanyaye ta shiga parlour'n ta durkusa." Kausar na ganinta ta fadada murmushinta ta riko hannunta "mamana ta bani labarinki ta fad'a hannunta na cikin nata maryama tayi murmushi wanda Ke bayyana kyawunta tace "da fatan tana lafiya? tana lfy tana can tana kewarki tace kin fini kyau da kunya har ma da qoqarin karatu da fari na karyata amman yanzu na gasgata a ganin da nayi miki a karon farko ,alhj alqasim da ummah sukayi murmushi yayinda yusif sai kallon maryama yake bai ce komai ba Islam kam sai wani yatsina fuska take jin yadda kausar ke yabon maryama ,alhj alqasim yace "ku bamu waje kuje kuyi hira "maryama muje wajen mamanki mu gaisheta lumshe idanunta tayi tare da cewa "to ! Hannun kausar na cikin na maryama suka fice Islam na biye dasu a baya maryama ta lura da irin kallon da yusif yake mata dan haka tasha jinin jikinta ,suka shiga side dinsu kausar tabi falon da kallo sannan ta dawo da kallonta kan maryama "tabbas nayi farinciki da ganinki a matsayin wacce mamana ta yaba da halinta har ma naji qaunar yin kawance dake ."maryama tayi murmushi kawai dan ita bata iya doguwar hira ba sai dai acikin ranta taji dadi ,ko bakya sona da Kawa ?ya zaayi naki sonki da qawa ai daman ke qawata ce kuma yaruwata ,ta rike hannuwan maryama da'ace acikin gari kike da yanzu ana nan ana hada gumi akanki maryama bata fahimci maganarta ba sai dai ta fahimci tana yi ne akan kyawunta murmushi tayi tace "akan me zaa hada gumi akaina ." Ta gyara zama "kyawunki yafi karfin zama acikin geto area bakowane acikin geto area hk zai iya cewa yana sonki ba saboda sanin kinfi karfinsa ko kina da samari ?"Sosai ta bawa maryama dariya ta kuma girgiza mata kai alamun bata da dan ganinta shi ya fiye mata sauki akan tace sun gudu sun barta ne ko kuma an kwace mata ,ai dole samari suji tsoron zuwa irin wannan kyau Masha allah wallahi ba wasa nike ba tun kafin na ganki momy ta fad'a min tayi min kyakkyawar qawa jinta kawai nayi domin ina jin babu wata macen da zan iya qawance daita anan amman ganinki na sha mamaki banda qawa zaki iya zarce komai agareni maryama tayi murmushi kawai tace "na gode ." "Kinga yayana yusif? Ta tambayeta tana kallonta "ko da yake ba sai anji a bakina ba maryama ta tsura mata idanu kawai tana kallon kausar cikin rashin fahimta dan ta fuskanci kausar nada yawon magana sosai ita kadai take kidinta take rawarta,dan ko tmbyr manufar abinda ta fad'a batayi ba ta rabu daita suka cigaba da hirar geto area ."acan kuma parlour'n umma alhj alqasim da baba gali da yusif da yaya sadam suna zaune bayan sunci abinda aka kawo masu saí alhj alqasim yace "ka gane wannan ?ya nuna masa yusif da hannu baba gali yace "yusif ne mana ya zaayi na kasa ganesa, a'a to yaron yanzu ne kwana kadan idan baka gansu ba sai kaga sun qara girma yusif yayi murmushi ya basar bai sake cewa komai ba ." Bayan tashin ummah dady ya dube baba gali yace "Gali wato zuwan da mukayi wancan karon wani ikon allah mai dakina mustafshira tun ganin maryama sai taji qaunar yarinyar har taji tayiwa danta shaawarta a matsayin matar aurensa dalilin da yasa banzo kenan ba tun wancan watan danayi alqawarin ba yusif baya nan yaje canada wannan dalilin yasa na tsaya har sai ya dawo sannan zamu zo tare ,yaron yaso yaki wai tayaya zai zo geto area neman matar aure amman sai na shawarcesa daya daure yazo ya gansu gbdy wacce tayi masa sai ayi maganarta ." Baba gali yayi murmushi zuciyarsa cike da farinciki yace "gsky abu yayi kyau mutun uku suna nan babu wacce akayi mgnr aurenta Islam da sakina sai maryama wacce take bautar kasa sauran biyu din km tun daga secondary basu cigaba ba amman dai ni ina son sakina ta cigaba alhj alqasim yayi shiru yana kallon Yusif yace kai duk gasu nan wacce ka tarar anan itace Islam din da nafisa ko ?baba gali yace a'a sakina wacce ta shigo karshe itace maryama "to kaji yusif itace sakina sai Islam wacce ta shigo karshe itace wacce mahaifiyarka tayi maka shaawar duk yayana ne babu wacce bazan yi murna idan ka aminta daita ba ,kai ma bazaa takuraka ba idan kaji babu wacce tayi maka sai a hakura ." Yusif yayi shiru yana tsotsa keya yace " zabin momy shine zabin da yayi min dan haka maryama itace ta shiga raina a kallon farko danayi mata alhj alqasim ya washe baki yana murmushi baba gali ba dan ranshi yaso ba yace to shikenan duk da daman akwai maganar wani dake sonta amman dai babu komai sai abashi hakuri alhj alqasim ya tsayar da idanunshi akan baba gali "da kuma kace babu wanda yake nemanta da aure? ya tmbyesa cikin mamaki shi kuwa yusif ido ya ware sosai dan shi wallahi yayi mata ko sama da kasa zasu hade sai dai ya hakura ya bar masa ." Baba gali yayi sauri yace "ai kasan samarin yanzu ba wani serious yayi ba amman sharesa kawai dan sama sama yake ma zuwa yusif ya sauke ajiyar zuciya alhji alqasim yace "shikenan ayi mata magana tayi miji shi wannan babu zuwa sama sama yazo kenan ayi mata magana sai muje mu gaisa da mahaifiyarta koda yaya sadam ya fad'awa umma murna har da sujja tayi ita kuwa Islam cikin kunci ta shige bangaren su byn ta gama ji sakina kam ko ajikinta dan ita tana son maryama bata dai san meke sata jin tsanarta ba ,maryama da kausar suka fito suna hira ganinsu yasa shi ya tsayar da hankalinsa akanta tabbas ta hadu yayi mamakin samun mace kamarta gata yarinya qarama just 20 amman ta hada abubuwa masu yawa dan ya darata da kusan shekaru shatakwas a duniya" Alhj alqasim ya bukaci ganawa da maryama ta shigo a natse ta zauna tare da takwashe kafafunta kanta sunkuye yayinda yusif yake ta kallonta bai ta'ba sanin akwai baki mai kyawun da tafi fari ba sai akanta ko da yake bazaa kirata da baka ba sai dai chocolate colour" maryama ina son nayi miki wata tmby guda daya kuma ina son ki sanar dani tsakani da Allah ki sanar dani gsky ki daukeni tmkr mahaifi ne yake tmyrki ita dai shiru tayi tana tunanin irin tmyr da zai mata domin bata kawo komai aranta ba ko hasashen abinda zai tmbyeta "maryama ya'ya zamanku yake acikin gidan nan "? Ta tabbatar akwai abinda alhj alqasim ya gani yasa har yayi mata wannan tmyr tabbas bata da tacewa ba zata iya fad'ar irin bambamci da abubuwan da ake mata daga bangaren baba gali da aunty hassna har ma da sauran yanuwansu wadan da suka kasance yanuwa ga mahaifinta tunda daman duk mutumin da bashi ya haifeka ba ,dole sai an gane kuma bai zama lallai ya soka ba ,ya qara mata tmbyr ganin bata da niyyar cewa komai hakan kuwa ya qara sa zuciyar yusif mace wa akanta gbdy ganinta yasa ya manta da husna yarinyar da suka dauki tsawon shekaru daita kawai taimakonsa bai kawota gidansu ba daya san shikenan ya tafka asarar samun maryama ." Ya sake tmbyrta a karo na uku cikin sanyayyar muryarta tace "ban san ta inda zan fara ba amman dai bani da matsala muna zaune da kowa lafiya tayi mgnr tana sunkuyar da kanta shi kuwa yusif ya kasa dauke idanushi akanta alhj alqasim yayi shiru na dan wani lokaci sannan ya shaki iska yace "har mamanki ?ta sake gyada masa kai duk muna lfy bamu da wata matsala da kowa acikin gidan nan ita kam bata ga dalilin da zai sa ta fitar da sirri gidansu ,su din yanuwanta ne duk da basu dauketa a haka ba ." yayi shiru yana nazarinta shi dai ya fuskanci akwai matsala daga hasana har gali amman gashi ta boye masa yayinda zuciyar maryama ta dinga raya mata ta sanar masa gsky zaman da suke wanda naci ma da taimakon umma suke samu amman ina bazata iya ba ." Wannan hali nata yasa yaji lallai ta qara shiga ranshi duk nmj daya sameta yayi saa a duniya domin macen dake iya rike sirrinta itace mace da haka ya gama yace ayi masa iso wajen mahaifiyarta a natse Umma tayi masu iso zuwa wajen aunty ta tarbi bakinta yadda ya kamata dan katuwar tabarma ta shimfada masu, alhji alqasim ya jima yana kallon aunty cikin tsananin tausayawa sannan ya dubi Yusif muryarsa sanyaye yace "ga mahaifiyar maryama suka qara gaisawa shima yana satar kallonta da alamun ya gano kyawunta maryama ta dauko duk da bata cikin sukuni amman fatar jikinta ta ya'yan masu kudi tana nan lafiya lau kyakkyawar fata mai sheki babu abinda ta rasa wajen auna kyakkyawa , hanci baki mai kyau idanu kausar kam kusa daita ta koma ta cigaba da zuba mata surutu nan da nan hira ta barke sosai atsakaninsu " Alhj alqasim ya gano dansa na bukatar kebewa da maryama dan kallon da yake mata babu sauki yace "maryama fitar da wannan matsoracin yaga cikin geto area daga nan akwai abinda zai fahimtar dake ta dan yi murmushi tare da dago idanuta suka hada ido da yusif wanda yayi zuru da idanunshi akanta aranta tace "bashin me naciwa bawan allah nan yaketa bina da kallo? bai yi tsammanin zata iya fad'ar haka ba dan hk yace mata "bashin gaisuwa mana baki gaisheni ba sai lokacin ta fahimci a fili tayi mgnr ai kuwa da sauri ta mike ta fice daga parlour'n jamar dake zaune a wajen sukai dariya yayinda yusif ya mike ya fito tana tsaye a tsakar gidan rungume da hannunwanta ya qaraso inda take tsaye "ina kwana ta fad'a tana sunkuyar da kanta sakamakon idanunshi dake yawo a sansar jikinta "yanzu ne ina kwana ? to ai bashi ka biyo kuma gashi na baka." Shiru sukai na dan lokaci ta sake sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta ko zan iya tmbyarki ?kai kawai ta gyada masa tare da yin shiru tana mai jin tsanani kunya most especially idan ta fahimci sanar daita kalmar só zaayi ko mgnr aure dan ma wayewar karatuta ta rage mata wasu abubuwa ,amman duk da hk a shirye take da irin tmyr da zai mata dan kallon yayanta take masa tunda mahaifinsa yace ta daukesa tmkr mahaifi kunga kuwa dole ta daukesa matsayin yaya agareta muryata a sanyaye tace "nima ina da tmby idan kayi naka ka gama ?ya danyi taku kadan yana shirin barin wajen domin canza waje" muje daga can ta biyosa cike da natsuwa cikin tafiyarta kamar bata son taka qasa ." Ya tsaya tare da tsura mata idanunshi ya gyara tsayuwa hade da rungume hannunwansa a qirji "Kinsan tambayar da nake son nayi miki ?ta girgiza masa kai tana mai sake dukar da kanta "kina da saurayin da kike so ?ta dan dago idanusu suka tsarke cikin juna tayi saurin dauke nata tana cewa "acikin ranta kar dai abinda nake tunani ne zai tabbata ?kamar tace tana da mlm yahuza dan saukakawa kanta sake shiga wata rayuwa amman sai ta tsinci kanta da ce masa "a'a bani da kowa kin san kuwa kina da kyau sosai ?tace ina dai ji mutane na fad'a amman ni dai nasan bani dashi ,kiji tsoron allah yadda yayi maganar yasa tayi murmushi har fararen hakoranta da wushiryarta suka bayyana ." "Kina da matukar kyau ,Ke rayuwarki ce kawai a irin wannan area amman siffar ki da halinki suna manyan unguwa ne kinfi dacewa da zaman acan nasha mamakin dana ganki anan ?tayi murmushi "to saboda me zakayi mamaki dan na kasance a irin wannan unguwar ?",su mutane dake rayuwa acikinsa su ba mutane bane ?ya sake tsareta da idanunsa ganin karfin halinta akan maganarta "har wani dagewa kike da tmby okay ai an kusan daukeki tunda baba ya amince ? Shiru tayi tana nazarin maganarsa ai an kusan daukeki tunda baba ya amince domin kawar da maganar tace "dady yace zaka fahimtar dani wani abu me zaka fahimtar dani ?yayi shiru murmushi akan fuskarsa yace "matsalarki kunya ni kuma tsoro ta dan yi Jim ,a ina na zama matsala ?bai bata amsa ba sai kallon gabansa daya cigaba da yi daga bisani yace "ni baki tmbyeni ko ina da yammata ko bani dashi ba ?ta dan daga kafadanta alamun babu ruwanta da hakan domin wannan babbar maganace tama fi karfinta me ma ya kai ta ga wannan tmbyr ? "kodan saboda baki damu da yayanki ba ? "A'a? "Ya a'a da kin damu dani nasan zaki tmby ko yaya abinda ya shafi rayuwata mussaman Kiyi koyi da irin tmbyr danayi miki akan samari " nan da nan taji wani iri da alamun zai yi rigima da jan magana idan ba haka ita ina ruwanta da wasu yammatansa "karkiji da wai sai kin mun irin tmbyr da na miki zaki bar nan idan ba haka sai dai na tasa keyarki na wuce dake " ta zaro ido tana kallonsa da mamaki wannan shi ake kira karfin hali barawo da sallama "to shikenan bari na tmbyeka sai dai ba tmyr ka zanyi akan kana da yammata ko baka dashi ba dan nasan kana dasu aruru wata killa ma kullum sai kayi budurwa sama da hudu "dariya mai dan sauri yayi yana kallonta "lallai sai kace wani na mamajo yadda ya fadi mgnr ya bata dry dan hk daga dryr bata sake cewa komai ba sai shine ya cigaba da cewa "ni nan da kika gani matsoraci ne tsoron mata ne dani ban ta'ba cewa ina son ko mace daya ba ,ba dan kuma bana ganin wadan da nake so ba sai dan kawai dana tunkaresu da maganar só sai naji gabana yana faduwa ." Murmushi tayi "lallai ka cika matsoraci ta fad'a acikin ranta ya dan kyaleta amman gashi momy ta gaji da zamana haka ta samomin wacce zan aura "gsky kaji kunya kai yanzu mata ma kake jin tsoro a yadda zamani ya samu cigaba,sai kana yiwa mace kallon macen arziki sai kaga ashe ba haka bane ta dan yi jim ,"ina tmbyrka a ina matsalar take kace matsalarka tsoro ni kuma kunya a wani fannin kenan ?shiru ya biyo byn tmyrta har ga allah bata kawo komai ba saboda bata tunanin hadadden saurayi kamarsa zai ji wani abu akanta har ma ta burgesa sam bata kawo akanta ba haka take biyewa zancensa ." Ya katse mata tunani da cewa "daace zuciyar kowa zata fitar da matsalarta dana tabbatar zamu samu fahimtar juna har ki fahimci dady da kuma kin gane zabin da momy ta tay min "tayi shiru a ganinta mgnrsa bata dace daita ba bata san komai akan rayuwarsa ba ya sake katse mata tunani "kin shirya cire kunyar ki ni kuma na cire tsoro dan ki samu amsar tambayoyinki .?ta dan tabe baki " ni wai waya fad'a maka ina da kunya ya zaro ido "Subhallah Au baki da kunya ?tayi murmushi "to ai kaine wallahi ni ne wallahi me ?"wai na cire kunya sai kace kunyar takalmi ce ya danyi murmushi ya tsaida idanunshi akanta ita ma shi take kallo dan tana tunanin zai fadi matsalarsa ne ganin yaki dauke idanunshi akanta yasa tayi qasa da idanunta ta fara shan jinin jikinta domin irin kallon da yake mata mai fassara ne ." "Maryama wacce momy na ta zabar min ita ce daidai da rayuwata kuma tana kusa dani yardarta abbana yake nufin a matsayin na fahimtar daita soyayyata ya dan gyara tsayuwa "kece zabin abbana kece zabin momy sannan kece zabin kanwata ta sauke kanta ta qasa tsayuwar da kafafuwanta wata shuumar kunyarsa ta mamayeta ji take tmkr ta nitse a wajen daman manufarshi kenan agareta amman ta tsayar dashi tana ta dogon zance dashi ya qara fuskantarta "kece kadai naji duk duniya tun a kallon farko soyayyarki ta doki zuciyata da wani shauki ganinki a karon farko kaunarki ta mamaye ni yardarki itace yarda da abba yake nufi ki bani yardar soyayyarki ni kuma zan nuna miki hallacin so zan fayacce miki irin soyayyarki da take cikin raina ." Kamar ruwa ya cinyeta haka ta koma a wajen tmkr ba itace Ke hira ba ita kanta hirar datayi a awaanin abaya datasanin yinta take ,da kyar ta daga idanunta ta kallesa ganin gbdy idanuwanshi suna kanta yasa ta sake gyara mayafinta "ki daure ki sanar dani abinda zanjewa da momy domin ta samu sukuni momy na tana matukar qaunarki kullum tana kewarki da alfahari da halinki domin tace bata ta'ba ganin diyar talakawa da irin jarumtarki ba fannin hali da tarbiya da ina ganin momy ta dauki abun da zafi amman ganinki ya tabbatar min ni kaina zanyi alfahari dake idan kika kasance mata agareni kin dace da rayuwata ." Hakikanin gsky sai dai taki yusif saboda gudun rashin tabbacin samunsa ba dan bai cancanta ba har zuciyarta kalamansa sun dan wanke mata mikin dake daskare a zuciyarta na rashin mlm yahuza da abinda akayi mata amman duk da hk bazatai ganganci amsar wata soyayya a yanzu ba ina ma tana da tabbacin samunsa ? kinyi shiru kice min wani abu "batare dasanin ba kawai taji kalmar allah ya tabbatar mana da alkairi,kenan kin amince zaki auri matsoraci ?kai ma ka yarda zaka auri mai kunya tana gama fadar hk ta bar wajen da d'an saurinta ta boye abayan windowsu tana sauke numfashi ita ba wai tana jin sonshi bane aa ta gaji da rayuwar gidansu km tana son ta dauke mahaifiyarta daga cikin gidan suyi rayuwar farinciki kuma taga alamun zata samu a wajen Yusif ," Da zasu wuce aka shigo da kayan abinci masu uban yawa umma ta kara masu godiya yayinda maryama bata bari sun qara yin wata hira da Yusif ba duk da shi yaso suyi sallama amman taki duk mutanen gidan suka fito har yammatan gidan a tunaninsu zai ce yana só nan kuwa basu san tuni ya gama amayar da abinda ke ransa ba, suna tsaye a tsakar gidansu daga nan maryama bata qara taku daya ba ta koma side dinsu har bakin mota suka rakasu baba gali bai saba boyewa aunty salma komai ba dan ya kwashe abinda ya faru ya fad'a mata sakina na zaune tana jinsu aunty salma tayi shiru hankalinta a matukar tashe tace kai wani irin mutun ne da bai san ciwon kanshi ba ? ga sakina bazakayi mgnrta ba gsky wannan hadin bazai yuwu ba kenan rasa yahuza ma cigaba ya kawo mata ? "to ai kece da baki ruguza mgnrsa ba ai da dole cikin yayanki zaa aura shiyasa naso ki barta dashi Ke kuma kika matsa ." "Tô ai sai ka nuna masu akwai wanda take so idan yaso duk abinda akayi akan mlm yahuza sai a kwance kaga dole nasan zai dauki shukura ko sakina tunda iyayensa anan suke son ya zabi matar aure baba gali yayi shiru aikin gama dai Ya gama shiyasa komai nake gaya miki ki dinga bi ahankali gashi nan da kanki kin rusa rabon yayanki dan da tuni yusif rabon yayanki ne aunty salma tayi shiru tare da cewa "yanzu ma bata baci ba nan da dan wani lokaci kadan zai fasa ya kalleta ai nasan zaki iya amman hakan zai sa iyayensa su gane akwai wata sannan mutane ma zasu zagemu ."tsaki taja kai ka damu da wannan in har kana son yayanka da arziki ya zama dole wannan karon ka bani hadin kai baba gali yayi murmushi to ai ki bada himma da haka suka kawo karshen hirarsu tá tashi ta dauki mayafinta ta nufi gidan alfa Tayi saa bata samu kowa ba duk abinda ya faru ta sanar dashi yayi murmushi yace "kada ki damu Ke ai mutumi yar arziki ce bakya rabuwa damu duk runtsi kuma da yarda allah zan taimaka miki ki tashi kije ko kaffara bazan yi ba wallahi sai yusif ya auri sakina ko shukuran Kike so ,cikin farinciki ta koma gida duk yadda sukai da alfa ta sheidawa baba gali ya kuma yi murna dan shi kanshi da baya son tana zuwa bin malamai dan yasan har dashi takewa amman yaji dadin na wannan karon tunda yar shi guda jininsa zata taimaka ." duk mutanen gidan suna zaune a tsakar gida Maryama na zaune kusa da umma ganin kamar zaa tautauna akan yusif yasa ta yunkura ta mike nan kuwa taji sun fara tautaunawa akanshi tana tafiya tana tsinkayo maganarsu har tayi nisa ta daina jin komai ."da misalin karfe tara na dare sai ga kira daga baba gali bata kawo komai aranta ba sai mgnr yusif zai mata ,tana isa ta gaishesa ya amsa yana gyara zama yace "wai me ya hadaki da mlm yahuza ne ?tambayar tazo mata a bazata domin irin haka bata ta'ba hadata dashi ba, koda suka rabu bai kirata ya tmbyeta ba sai yanzu data manta dashi tace "babu komai dan ban san abinda nayi masa ba daya canza da shukura" to ai ba soyayya bace a tsakaninsu da shukura ita kanta salma rashin fahimta ne ku dawo Kmr yadda kuke dan dazu da kanshi yazo neman ki" "Nemana kuma me kuma zai min ai ni na rigada na yafesa har abada ,aa maryama ban sanki da fushi ba Kiyi hakuri idan ya dawo ki samu ku sasanta kanku kinji bai kamata ba dama shi irin wannan sabanin ai dole yana zuwa a mijin da zaka aura ,ido kawai ta zuba masa kafin daga baya ta sunkuyar da kanta kasa ahankali ta furta to "baba ina kuma alqawarin da kayiwa abban kausar ?yayi shiru yana dan nazari "maryama da na zama qaramin mutun ta bangaren mahaifin mlm yahuza ai gara na zama ta bangaren alqasim maude domin shi zai min uzuri kuma idan na hada yusif da yaruwarki sakina ko shukura nasan komai zai wuce ." Tayi shiru kawai hawayen takaici suka nemi zubo mata daga idanuwanta gbdy ta rasa abun yi kawai ta mike ta koma banger su ta fad'a dakinta ta kwanta ta kudundine kanta ta fara rusa kuka mara sauti dan tasan wannan ma ya zama ba rabonta ba tunda ma baba da kanshi ya furta mata haka yanzu ita hk rayuwarta zata qare cikin kunci da wahala "me ta tsare masu da basa qaunar cin gabanta? duk wani abu da suka san zai zama cigaba arayuwarta basa so ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 25 Allah sarki maryama kwana tayi kuka har sai da garin allah ya waye sakamakon haka fuskarta ta kunbura ita kanta ta rasa dalilin me yasa take kuka rashin yusif da zatayi ne ko kuwa dawowar mlm yahuza ne ?a zahirin gsky duk bbu ko daya aciki dalilin zubar hawayenta ,zubar hawayenta bai wuce na rashin qaunar da baba gali yake nuna mata kiri kiri ba, lamarinsa yana mugun daure mata kai ." Tarasa gane kanshi ,mai hakan yake nufi da aikatawa? anya ma kuwa baba gali yana cikin haiyacinsa dan kwananan abubuwan da yake sun qara shan bambam dana da ? al'amarin ya damu maryama har yasa kwalkwaluwar kanta Ke neman tarwatsewa ,da gaske dai baba gali da sauran dangin mahaifinta basa qaunarsu sai ma a yanzu ta qara gane cewa ba dalilin haduwar iyayenta bane silar qiiyayyarsu garesu daman can basa qaunar mahaifinsu ." Babu kuzari ajikinta haka ta tashi da safe aunty da habib suka damu sosai da ganin sauyi atattare daita idanuwansu na kanta lokaci zuwa lokaci suna lura da damuwar da take baibaye daita sai dai basu ce mata komai ba sanin ko sun tmyeta zata fad'a masu babu komai, amman ita maryama tana lura da yanayinsu nason yi mata magana ." aikinta data saba na safe tayi bayan ta kammala ta shiga wanka wanda zuwa lokacin Auty ta gama girki ta fito cikin doguwar rigar tana zama aunty ta kawo mata nata abincin tasa abincin agaba tana tsakura yayinda zuciyarta ke mata tuni da abubuwan da suka faru jiya atsakaninta da yusif ta jisa dabam akan mlm yahuza ,ko kadan zuciyarta ta kasa daina tunaninsa ba wai dan tana sonshi ba dan gsky daga haduwarsu jiya bata ji cewar tana son shi ba ta dai amincewa aurensa ne saboda ta samu saukin rayuwa ,soyayya kuma tasa aranta bayan sunyi aure zata so shi daman ita kuma ba dabiarta bace saurin zurmawa soyayya ." Tana tsakurar abinci sannu ahankali har taci rabi ta dauki plet din da taci abincin ta kai inda suke yin wanke wanke ta dawo ta nufi hanyar dakinta tana qoqarin shiga aunty ta kira sunanta cikin muryarta mai tsananin tausayawa agareta ta juyo a natse tare da amsawa sannan ta dawo inda take zaune ta durkusa agabanta ,aunty ta dubeta sosai ta sauke numfashi tace "yanzu princess har akwai damuwar da zata dameki ki kasa fad'a min ? Nan da nan ta rikice domin dai bata son fad'a mata komai sannan bata son tasan ma tana cikin damuwa dan ita a ganinta gara ta boye damuwarta muryarta a matukar sanyaye tace "aunty ai bana boye miki komai kuma Kinsan idan akwai abinda Ke damuna kece mutun ta farko da zan fadawa tunda bani da wacce ta fiki ko babu komai adduarki nada matukar mahimanci agareni "yanzu zaki iya rantsewa da Allah babu abinda ke damunki ."? Maryama tayi shiru dan bazata iya rantsewa ba kuma bazata iya sanar daita ba dan zata fita shiga damuwa ita kuma bata qaunar ganin damuwarta wallahi akan taga aunty cikin damuwa gara ita ta qare rayuwarta aciki ,duk maganar da aunty ta keyi ba tace uffan ba illa ta sunkuyar da kai kawai tana sauraronta zuciyarta na karkarwa , duk yadda aunty taso taji wani abu daga bakinta amman taki ita dai ta karbi qaddarata na rashin yusif." Haka ta kasance acikin gidan zuciyarta babu sukuni kwana uku da faruwar abun sai ga mlm yahuza yazo gurinta har da bata hakuri yana mai jinjina abinda yayi mata ,yace shi kanshi yayi mamakin abinda yayi ,wai shine yake kin kulata kuma shine yayi soyayya da shukura ? yana magana Kmr zai yi kuka wanda ita ahalin da take ciki bata jin tausayinsa kuma bata jin zata karbe shi ta barwa duk wata mai so kai auren ma ta hakura dashi har abada ." duk hirar da yake mata baya mata dadi wani irin tsanar shi taji yana shigarta sannan duk nacinsa haka ta wuce ta barsa ta koma cikin tana tunanin yadda alamarin zai kasance shin idan yusif yaji hukuncin baba gali ya zai yi ?."zai amince ne ko kuwa dai shima zaa kawar masa da tunaninsa ne kamar yadda akayiwa mlm yahuza? " bani da gata bani da kowa sai allah da kuma mahaifiyata ta sheidawa kanta haka ." "mai zai hana ki fadawa mahaifiyarki gskyr lamari sannna ki tashi tsaye da addau zuciyar ta ,ta fad'a mata haka? zan dai tashi da addaua amman bazan iya fadawa aunty komai ba dan zata fini shiga damuwa gara idan maganar ta fito taji daga sama ta kwanta shiru tana kallon saman dakin hawayen na gangarowa ta gefen idanunta ." Kuka take har da shesheka wanda bata ma san sautin muryar kukan na fita ba, cikin haka aunty ta turo kofar dakin ta shigo ganinta haka yasa taji wani gagarumin tashin hankali da sauri ta qaraso kusa daita ta zauna tana kiran ainihin sunanta "maryama ! a matukar firgice ta dawo natsuwarta ta mike ta zauna tana goge hawayenta da hannuwanta duka ,aunty ta tsura mata ido kawai tana kallonta dan gbdy rasa abinda ke mata dadi arayuwarta take idan taga maryama cikin damuwa ." A dan fusace tace "kukan me kike yi ?wani irin bugawa qirjin maryam ya shiga yi nan take ta shiga kokuwa da numfashinta dake barazanar daukewa sakamakon kukan da take sannan ahankali ta shiga girgiza wa aunty kai alamun babu komai "babu komai kike kuka haka maryama ?"yanzu bazaki fad'a min damuwarki ba ?"Ke kenan kullum cikin damuwa cikin zubar da hawaye nasan acikin kwanakin nan akwai abinda ya faru wanda kike boye min meye shi sannan waye yazo wajenki ."? hawayen da take kokarin maidawa suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri ta shiga gogewa wasu na sake gangarowa cikin muryar kuka ta soma magana "da fari dai mlm yahuza ne yazo "mlm yahuza kuma ?me yazo yi?tayi mata tmbyr a jere tana dubanta qirjinta na bugawa da karfin gaske "wai ya dawo ! shiru aunty tayi tana nazarinta sannan tace "shine dalilin shigarki damuwa ?maryama ta girgiza mata kai tana cewa "bashi bane! "to menene ni ?" abinda Ke damunki nake bukatar sani "ban san me yasa baba gali baya qaunata ba ta qarasa mgnr tana zubar da wani hawaye "Kawai dan baya qaunarki shine zaki zauna kina kuka kina damun kanki ?ai ba dole sai ya soki ba, rayuwar nan fa da kike ganinta ba kowa bane zai soka, sai ku fito ciki daya da mutun yace bai sonka bare shida dan uwa yake a wajen mahaifinki ." aunty ta kamo hannunta daya cikin nata sannan ta kai dayan hannunta tana goge mata hawaye "ki cire wannan damuwar ki manta da batun bai sonki wata rana sai labari kuma maganar dawowar mlm yahuza karta daga miki hankalinki tunda nan kusa zakuyi aure da yusif naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana sake matso ruwan hawaye idanunta "Allah sarki aunty ai shima ya zama ba rabona ba ta fad'a a kasan ranta zama aunty tayi tana rarrashinta har bacci ya dauketa sannan ta mike ta bar dakin ." ***** A yammacin ranar litini wanda yayi daidai da kwanan nuzla uku a police station labarin halin da take ciki ya samu jama'ar dake rayuwa acikin abdullahi estate kowa ya shiga damuwa matuka amman banda hindu dan ita murna tayi sosai dan ta fahimci itama tana cikin masu son abinda take so , hisham kam yafi kowa shiga damuwa yayinda hjy salema banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa da zubar da hawaye ." "Ya'yan hjy salema suna zaune gbdynsu a cikin parlour'nta cikin jimami har hisham wanda ya fita haiyacinsa ATA ya shigo bakinsa dauke da sallama ,baa kai ga amsa masa sallamar da yayi ba hisham ya tashi a matukar fusace ya soma magana cikin zafin rai "me ya kawo ka ?" me kake takama dashi ?ya tmbyesa .ATA ya zauna yana duban screen wayarsa" laifin me nuzla tayi maka? me ta tsare maka ?komai zata maka ai bata cancanci kayi mata haka ba ? zaka iya yiwa nana hauwa'u haka ko zaka iya yiwa zabiba haka ?" ATA bai kulasa ba dan yasan baya haiyacinsa so ya rigada ya zautar dashi." "Mutumin banza dan rainin hankali kawai da bai san mutuncin na gaba dashi ba ,kace baka son yarinya amman gashi akanta kasa an kama yarinyar mutane ATA bai dago idanushi ba ya cigaba da kallon screen din wayarsa yana cewa "ka shiga hankalinka hisham zaka iya fad'ar komai na barka dan nasan a haukace kake ,amamn idan ka sake hadani da yarinyar nan zan ajiye haukan soyayyar dake damunka a gefe nayi maka wulakanci." "Kai ne dai mahaukaci amman ni lafiyata lau "hisham zamu samu matsala !mun dade bamu samu ba ,nace kana sonta !! baka sonta me yasa zaka sa akama nuzla ?nan zuciyar ATA ya motsa ya somawa hisham wani kallo mai tattare da tashin hankali ganin kar abun ya zama fad'a a tsakaninsu baba babba ya takawa hisham burki ." ahankali ATA ya soma warware komai da sakon da nuzla ta aika masa dashi "nayi wannan bayanin ne saboda hjy da kuma baba Babba sai ku yanuwanta dan kusan dalilin da yasa ta shiga hannun hukuma "ban bada umarnin ayi mata komai ko a ta'ba lafiyar jikinta ba ,abinda yafi zama mai mahimanci shine bincike kuma ana kanyi abinda nake son gbdynmu mu fahimta yana da kyau mun san daga inda matsalar take wacece ta kashe mubina ? "wallahi ni ba akan yunkurin kashe wannan yarinyar yasa na damka nuzla hannun hukuma ba dan ko nana hauwa'u aka kama da laifin kisa ko yunkurin kisa da kaina zan damkata ga hukuma haka zalika nuzla qanwata ce Kmr yadda nana hauwa'u take a wajena ,tayi kuka tayi rantsuwa akan bata aikata ba amman wacce ta aikata tana tare damu kuma nasan muddin ba nuzla bace hakika muna tare da mai yin kissan dan haka da zarar an kammala bincike da kaina zan dawo daita gida mu san abun yi amman ya zama dole mu san wacece ta kashe mubina acikinmu ." parlour'n ya dauki shiru duk suka zuba masa ido kawai suna kallonsa da sauraronsa bayan kamar minti goma ATA ya numfasa sannan ya kalli inda hajiya salema take zaune tana faman kuka "kuyi hakuri hjy km ki kwantar da hankalinki matsawar babu hannun nuzla acikin zakiyi farinciki yana gama fadar haka yayiwa baba babba sallama ya nufi kofar fita yana zabgawa hisham harara ." tsaye hindu take tare da jingina jikinta da bangon dakinta ta hade hannuwanta duka waje daya ,sosai tayi nisa cikin duniyar tunanin yadda zata kawar da maryam a doron duniya tun kafin akai ga daura masu aure da adam ,dan ta gwamaci ta kasheta idan yaso itama akasheta kowa ya rasa adam din gbdy ." ji tayi an dafa kafadarta ta juyo a hankali idanunta ya sauka akan baba qarami ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana runtse idanunta yayinda gabanta Ke dokawa da wani irin karfi "karki illa kanki akan wannan dan iskan yaron da bai san mutuncin mutane ba "kafi kowa sani baba ina mutuwar son shi wannan maratuncin da dukkanin rayuwata kuma kafi kowa sanin bazan iya rayuwa babu shi ba, amman kana ji kuma kana gani kana da ikon da zaka sa umarni kawai zaa bashi ya aure ni amman kaki kayi komai akai wallahi baba ji nake kamar na mutu ta kamo hannun baba qarami ta kai daidai saitin qirjinta yaji yadda qirjinta ke bugawa da sauri sauri ." gbdy ya sake shiga rudani duk tunaninsa ya tsaya ya rasa ta ina zai fara ga matsalarsu ta kamfani da kullum cikin rigima ake ga qaddarar data dade da fadawa diyar daya fi so da qauna "idan bazakayi komai akai ba ni zanyi koma nace na fara zan kuma cigaba daga inda na tsaya dan bazanyi asararsa ba sai dai duk mu taru muyi asararsa ,wallahi idan ban kashe mrym acikin estate din ba zan shirya inda zan kasheta "tsaki yaja yana cewa "ban san me yasa kike son Kiyi kisa akan wannan dan iskan yaron ba baba qarami ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ." matsawa tayi kusa dashi ta qarasa bakin gadonta tana jan zanin gadon tana sake shimfidawa "hakika zanyi abinda yafi kissa akanshi idan akwai ,kuma zan mutu amman kafin na mutu duk sai na rabashi da masu sonshi idan kuma nayi nasara asirina bai tono ba zan mallakesa idan kuma ban mallakesa ba shima zan kashesa a karshe na kashe kaina da kaina shikenan na mutu cikin salama ta qarasa mgnr tare da kwanciya tana mai kamkame jikinta waje daya wani son ATA ne Ke sake ratsa koina a sansar jiknta yayinda tsumammiyar soyayyarsa data dauki tsawon shekaru tana yi masa ya dinga taso mata kuka ta fashe dashi dan tana son rage wa kanta radadin dake makale a tsokar dake qirjinta a fusace baba qarami ya fice ya bugo kofar dakin da karfi har sai da qararrawar zuciyarta ta amsa ." Ammi da nana hauwa'u diyana humaira suna zaune a saman kujera,yayinda maryam ke zaune a qasan carfet humaira na yi mata kitso hirar abinda ya faru da nuzla suke kadan kadan suna mamakinta diyana tana cewa "wallah gara da yaya adam yasa aka ka mata ni yanzu nake tunanin ma itace ta kashe mubina "babu mamaki dan mutun abun tsoro ne inji cewar humaira ." "A'a karki ce haka diyana Allah ne kadai yasan wanda ya kashe mubina tunda ita ba anan aka kasheta ba kuyi wa yaruwarku kyakkyawan zato , mami Kiyi tunani da kyau da irin wukar da akayi yunkurin kashe maraym da ita aka kashe mubina , me yasa zakiyi zarginta ?sannna akan wani dalili har zata aikata hakan akan mubinarmu bayan gabadayanmu muna son mubina nana hauwa ta tmyta ? Wannna fa ba zargi bane tunda yaya adam yasa aka kamata kunsan akwai wata a kasa babu rami me ya kawo rami ."? "Ni kuma nafi tunanina akan yaya adam ne inji cewar humaira "akan yaya adam kamar ya ? duk suka kalleta fuskarsu da alamun tambaya "ai ta dade tana son shi kusan ranar da mubina ta furta agabanmu cewar tana mutuwar son yaya adam hankalinta ya tashi . duk suka natsu suna sauraron humaira ta cigaba ai bayan mun rabu ni ta fad'a min amman alaokacin cewa tayi tunda mubina ta rigata furtawa ita ta hakura sai kwatsam sai ga mutuwarta ni tun lokacin naso na fasa maganar amman nayi shiru gudun abinda zai je yazo ."nana hauwa tayi shiru kafin daga baya ta numfasa bata tunanin nuzla zatai haka dan ko byn mutuwar mubina ta dade tana jin mutuwar ,ita kam maryam ta yarda da hakan dan lokacin da akayi yunkurin kasheta kowa yazo amma ita bata zo tayi mata jaje ba ." "Lallai mami danki yayi kasuwa dan ita karon kanta a ynzu ta fara jin son shi aranta amman kuma meye a attare dashi da kowa Ke son shi haka ? tana jinsu suka cigaba da hira batare data tsoma bakinta ba ."suna cikin hirarsu ATA ya sanya hannunshi ya turo qofar falon tare da sallama akan labbansa duk da bai bude muryarshi sosai ba,maryam dake kallon kofar shigowa ta dago fararen idanunta suka sauka cikin nashi sanda yake takowa cikin falon mami na masa duban mamakin dawowarsa adaidai lokacin sosai ya dauki hankalin maryam dan yayi wani fresh ya qara kyau kaman wani sabon matashi amma fa fuskar nan tashi tana nan kamar koda yaushe babu annuri a hade da miskilancin wanda na yanzu ya qaru " Kallo daya yayi mata tai saurin janye idanuta akan shi shima ya maida kallonsa kan mami fuskarshi babu yabo babu fallasa"Lafiya dai ko adamcy Nah naga ka dawo by this time ?"Lafiya qalau sweetheart ..." Ya fadi alokacin da yake qoqarin zama a saman daya daga cikin kujerun falon idanunshi na kallon sama suka hada baki suka gaisa ya amsa da "Lfy ! kawai "Adamcy yanzu me ake ciki akan halimatu ne ? ni kaina yanzu bazance komai ba sai abinda hukuma suka ce " ya fad'a yana furzar da iska yanayin yadda yay mgnr kamar yana cikin damuwa." "Me za'a kawo maka? "coffe " to maza mrym tashi ki kawo masa" badan ranshi yaso ba yayi shiru dan ko yace zai yi mgn damuwa kawai zai qarawa kanshi."ranar da nuzla ta cika kwana biyar aka kira ATA daga police station bayan yaje aka tabbatar masa an kammala duk wani bincike kuma ansamu bambamci a wajen gwajin zanen hannu ,dan nuzla da hannun dama take amfani yayinda mai kisan da hannun hagu, bugu da qari ba zanen hannunsu daya ba dan haka zai iya tafiya daita "to shikenan a fito daita ya fad'a lokacin daaka fito daita shi kansa ya tausaya mata tana ganinsa ta durkushe a gabansa ta kamkame kafafuwansa ajikinta saurin dauke numfashi yayi sai dai tausayinta ya hanashi zareta kafafuwansa ajikinta duk da dottin da jikinta yayi ." Murya cikin kuka ta soma mgn "yaya na fad'a maka ban aikata komai ba wallahi bani bace kasa aka kawo ni nan kalli jikina yaya ni kaina bana son ganin kaina haka dan allah karka barni anan ka tafi dani gida ka tausaya min kafin na mutu da kyar ya samu ya zare kafafuwansa yana sauke numfashi ya mike tsaye yana mikewa dpo hannu "na gode sosai idan na koma gida zan kira akwai maganar da zamuyi "okay yalla'bai sai najika zumbur nuzla ta mike tsaye tana kuka "dan allah yaya karka barni wallahi bani bace dpo yayi murmushi yana cewa "ai ki kwatar da hankalinki yau a gida zaki kwana wani irin naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana masa godiya ATA yayi gaba ta biyosa da sauri ." Suna shiga cikin estate dinsu kai tsaye hanyar gidansu suka nufa sukai parking masu tsaronsa suka firfito shima ya fito suka nufi cikin gidan a parlour'n suka iske hjy salema da wasu yanuwanta mutun biyu da gudu nuzla ta qarasa ta fad'a jikinta tana kuka itama tana kuka ta rungume diyarta tana shafa bayanta ganin irin kukan da suke yasa ATA ya juya ya kama gabansa alkwari ne kuma ya cika ranar kam murna wajen hjy salema da yanuwanta baa magana sai da kira doctor domin lafiyar nuzla tare da allurar." Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah kullum kwanakin bikin ATA da maryam qara matsowa yake har yau ya rage sauran kwana bakwai kuma har lokacin zuciyar ATA bata rusuna ba salim da mb har ma da hisham ango suke yin duk abinda ya dace dan shi dai ATA yace bazai bata kudinsa akan auren maryam ba kuma babu abinda zai yi na event duk kuma wanda ya kashe kudinsa kar yace dan shi yayi ,dan bai aike kowa ba duk sun jisa amman babu wanda ya tankasa mb da hisham sunyi rabon iv sun kai duk inda ya kamata ace sun kai sosai shirye shirye yayi nisa amman babu ruwan ango dan ko tautaunawa baya yarda suyi dashi da zarar sun soma mgn zai bar wajen ." Yau tun safe maryam ta tashi jikinta a sanyaye ji take kamar zata rasa rayuwarta komai take gabanta na faduwa abu na tashin hankali dana farinciki duk sai taji gabanta ya yanke ya fadi har kasan mararta take jin ga zuciyarta dake tsinkewa shiru kawai tayi kwance har zuwa lokacin da mami ta shigo "maryam bacci kike yi ne ?ta tmbyeta tana shigowa dakin sosai ta yunkura ta tashi daga kwanciyar datayi tana cewa "a'a mami ba bacci nake ba na dai dan kwanta ne ."akwai abinda zan miki ne ?mami tayi murmushi tana dubanta dan ta lura tunda aka shiga satin bikinsu take cikin damuwa ." "akwai abinda ke damunki ne ? Ta girgiza mata kai alamun a'a "ki sanar dani idan akwai abinda Ke damunki ni din tmkr mahaifiya ce agareki ? ta sake girgiza mata kai alamun a'a sai dai kallo daya zaka mata ka fahimci akwai damuwar dake damunta ,ki cire damuwa aranki kinji maryam babu abinda zai faru sai alkhairi ta lumshe mata idanunta alamun ta gamsu "maza tashi ga mukulin mota kije gidan shahida yanzu ta kira wai kije tana son ganinki anya kuwa zan iya tuki nan mami ? bana jin zan iya dan bani da kuzari ajikina ,to shikenan bari nayiwa nura direba mgn ya kai ki ." "to mami amman bari naje nayi masa magana da kaina tare suka fito maryam ta fice ta bar mami da nana hauwa'u a parlour'n zuwa haraban gidan akan idanun hindu ta fito dan haka tayi adduar samun nasara da aiwatar da nufinta akanta domin kusan wata guda kenan tunda aka saka lokacin aurensu take neman hanyar da zasu samu kebewa ." bayan maryam ta fad'a masa zai kaita gidan aunty shahida ta juya ta koma ciki domin ta qara shirya kanta a parlour ta tsaya kusa da nana hauwa'u "sister muje ki shirya ki rakani." a'a babu inda zani maganarku ta matan aure zakuyi ina ni ina rakiya kinga je ki kawai sai kin dawo allah ya tsare hanya" ganin mami zaune a wajen yasa maryam bata sake cewa komai ba ta shige ciki .yayinda hindu ta qaraso inda nura yake zaune tana cewa "mlm nura ina son na dan aike ka ko akwai abinda zakayi ne ?tayi masa tmbyr dan tasan me zai yi adaidai lokacin "hajiya mryma zan kai unguwa okay to shikenan karka damu allah ya tsare ta juya zata koma ciki ,kina bukatar wani abu ne ? Ta tsaya cak ta dan juyo fuskarta a sake "daman abu nake son a karbo min anan bakin titi amman tunda fita zakayi karka damu ,aa baa yi haka ba kawo nayi sauri na karbo miki kafin ta fito ta mika masa kudi dan cake zaka amso min amman mai chocolate ya karba kudin ya nufi babban get din estate din da dan saurinta ita kuma ta shiga gidansu domin ta shirya ."akan idanunta still maryam ta fito kafadarta makale da jaka tana neman nura direba tayi sauri ta fito tana cewa "mrym amarya fita zakiyi ne ?ta waigo bayanta a hankali ganin hindu ta saki fuska sai dai mgnr datai mata yau din ya dan bata mamaki dan sam batayi tsammani ba dan ba abokiyar maganarta bace domin dai kusan duk kallon mai girman kai suke mata kasancewar ta girmesu km bata shiga cikinsu " "Eh wallahi fita zanyi nura direba ne zai kai ni gashi na fito ban gansa ba ko ina ya shiga ,Allah sarki okay muje na saukeki mana nima fita zanyi ta fad'a tana qoqarin shiga motarta da kamar bazata shiga ba amman sai tayi tunanin karta ga Kmr tayi mata wulakanci dan haka ta yanke shawarar shiga idan yaso direban aunty shahida ya dawo daita ta bude dayan bangaren ta shiga ta zauna hindu ta tada mota suka fice daga gidan koda nura direba ya dawo kai tsaye gidansu hindu ya nufa ya bada sakonta ya dawo zaman jiran fitowar maryam ." Ahankali suke tafiya hindu na jan mrym da hira "Maryam amarya adamcy kenan gashi yazo amman naga baki fara shirin komai na amare ba, wallahi ban fara ba dan bana cikin natsuwata "to me kuma Ke damun amarya ko fargaban kasancewa da angonki ne ? maryam tayi murmushi kawai "Ke kuwa me zasa kiyi fargaba alhalin auren soyayya zakuyi ?ko auren soyayya ne dole kaji wani iri dan aure ba wasa ba, kenan gskyr labarin danake ji daga bakin mutane daban daban na kina son adamcy gsky ne ? zuciyar maryam a dake tace "eh hk ne muna son juna ." "Na tambayeki ? "Ina jinki ! mu ajiye maganar wasa zaki aure adamcy ne saboda kina son shi ko kuma zaki auresa ne dan biyayya wa mahaifiyarsa ? "zan aureshi ne dan ina son shi "akan wani dalili kenan zaki so shi ? tambayar tabawa maryam mamaki amman sai ta kawar da mamakinta tace "akan dalilai masu yawa ."ko Kinsan akwai wacce ta fiki son shi da son mallakarsa wacce zata iya komai akansa ? "Eh nasani "! "Wacece ?ke mana na samu labarin kina mutuwar sonshi Kmr Kiyi hauka afirgice hindu ta juyo gareta tana cewa "tabbas bakiyi karya ba ina mutuwar son shi irin son da zan iya yin komai akanshi dan haka abinda zan iya ce miki ki rabu dashi ki kuma fasa aurensa saboda adamcy raina ne akanshi babu abinda bazan iya yi ba ". "ni kuma akan na rabudashi na bar miki gara na rasa raina." shine nima abinda na gani kenan, kuma nake tunani akai, kmr mutuwar ce zata fiye miki sauki akan ki cigaba da rayuwa a doron duniya , dan zan kasheki tun wa'adin kwanakin mutuwarki bai cika ba, zanyi sanadin rasa ranki batare da kin shiryawa hakan ba, ta karasa mgnr cike da matsanancin zafin rai tana fitar da hucin kishi. "wai meye haka ne hindu kike kokarin aikatawa ruhin da bai d'aukar miki laifin komai ba? "gsky zan gayawa mami . "ba sai kin rayu ba tukun zaki gaya mata ina tabbatar miki daga nan sai kabarinki, domin kuwa zan miki aika aika ,zakiyi mutuwa mafi muni da rad'ad'in azaba wanda ko makiyinki yaga gawarki sai ya koka miki "aikin banza kawai daman da wata manufa kika daukoni a motarki ? "Yes of course da wata manufa na dauko ki mana ,amman da yake Ke jaka ce kika qasa ganewa tana gama fadar hk taja wani irin wawan birki sannan taja motar aguje ta soma hajijiya da motar akan titi bata tsaya akoina ba sai atsakiyar titi , ta fito da hanzarinta, kafin maryam tayi wani yunkurin fitowa daga cikin motar , tuni har hindu tayi lock din motar gbdy , ta tsaya rike da kugunta tana dubanta tana murmushin mugunta ,"wai meye hk ne hindu ? "mutuwa kenan !" "ki budeni karki kasheni da wasa nake miki wallahi bana son shi nima zan auresa a dole sbd mahaifiyarsa "hhhhhhhhhhhh karyarki yarinya ai wasan ya rigada yazo karshe sai ki jirasa a lahira har zuwa sanda zai iso gareki so that kwa auri juna acan inda wata katuwar tanka mai ta nufo motar gadan gadan a matukar tsorace maryam ta saka wata razananniyar k'ara me sauti "tana toshe kunnuwanta duka tare da runtse idanunwata ....... Mmn sudai 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 26 hankalin maryam ya qara tashi Kuka take sosai da iyakacin karfinta tana furta duk wata adduar data zo bakinta domin neman cikawa da imani dan gabadaya ta sadaukar da rayuwarta akan mutuwa zatayi yayinda hindu ke tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tana sakar mata murmushi farinciki tana kallon yadda motar ke tahowa wajen motarta da maryam ke ciki ." maryam ta kamkame jikinta sosai tana mai sake fashewa da wani gigitaccen kuka jira kawai take taji saukar motar akanta amman sai taji shiru sai ma jiniyar motar ' yansanda ta jiyo dan haka da sauri ta ware idanunta dan tabbatarwa kanta gaske ne ?ganin motar yansanda ta sha gaban motar yasa ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi atare ,yayinda mutumin dake ciki motar ya soma qoqarin fitowa domin ya tsire amman cike da hanzari yansanda suka samu nasarar damke bala ,cikin tsananin tashin hankali yake masu bayanin komai dan gabadaya ya gama rud'ewa " Yayinda hindu ke tsaye awaje kamar an dasata tsabar firgitar da tayi zufa ce kawai ke karyo mata dan kana kallonta zaka fahimci yadda hankalinta yayi mugu mugun tashi , gashi tana son guduwa kamar yadda bala yayi qoqarin yi amman ta kasa aiwatar da hakan har sanda ' yansanda suka samu nasarar daba masa ankwa a hannuwansa tana tsaye kikam kamar mashi ." Zuciyar hindu ta shiga bugawa da matsanancin karfi nan take ta shiga sake sake hade da jerowa kanta tmby "wa yasan shirinta ?wa ya turo 'yansanda ?"yaakayi suka san inda zata aiwatar da shirinta akan maryam ?ita dai tasan daga Allah sai bala da zasu yi aikin tare suka san komai dan hatta babanta bata bari ya sani ba ." shiru tayi kawai har zuwa lokacin da yansanda suka qaraso zuwa inda take tsaye suka tsaya a gabanta a wulakace ta d'aga kanta tana kallonsu d'aya bayan d'aya tare da bude bakinta zata soma zazzaga masu ruwan bala'in 'bata mata shirinta da sukayi amman sai taga daya daga cikin police din dake tsaye a gabanta ya ciro I'd card daga gaban aljihunsa yana nuna mata kasancewar babu uniform ajikinsu da alamun cid ne ." wani dogon tsaki taja tana cewa "ai ni ba makauniya bace, ko baka fito da I'd card dinka ba nasan ku din yansanda ne "? dan sanda ya gyada mata kai kawai yana kallonta a tsanake kafin daga baya ya soma magana "da fari ki miko mana key motar hannnunki a fito da wacce kikayi yunkurin kashewa " furzar da iska mai zafi tayi daga bakinta kafin daga baya cike da maseefa tace "bazan bayar ba ,dan tunda nayi niyyar kawar da maryam daga duniya a yau din nan sai nayi babu fashi idan yaso nima daga baya akasheni tana qarasa maganar tabi gefensa zata wuce har tayi taku biyu taga wata gajeruwar macen yansanda ta harde mata kafafu sai gata dim a kasa ta zube bisa gwiwowinta inda key'n hannunta ya fadi kasa ." Macen yansanda ta qaraso inda hindu take wargaje a kasa cikin azaba ,kallo daya zaka ma macen yansanda kasan babu rahma a fuskarta ta d'auki keyn daya fadi ta mikawa d'ansandar dake tsaye a kusa daita"ungo naziru maza ka fito da yarinyar" ya karba keyn daga hannunta da sauri ya nufi inda motar take ." Macen yansanda ta fito da ankwa daga cikin aljihunta tana duban hindu a tsanake kafin daga bisani ta soma qoqarin kamo hannunta domin da'ba mata ankwa amman hindu ta fixge tana zabga mata harara "ki miko hannunki na saka miki ankwa ko kuma na harbe kwakwaluwar kanki yanzu ." wani murmushin bakinciki ya bayyana akan fuskar hindu "bazan so faruwar haka ba ,dan bazan so na bar duniyar nan batare dana kawar da mutun biyu din nan a duniya ba,wannan hatsabibiyar yarinyar da kuma wanda zai aureta, duk da na shiga hannu amman ban yi nadama ba ,dan ni kadai nasa me nake ji a zuciyata yadda zan rasashi dole itama ta rasashi ." Ta sake yin murmushi wanda kana gani na takaici da bakinciki né da rashin cimma buri "duk da na shiga hannun amman nasan zan fito dan mahaifina zai yi iya qoqarinsa sannnan zai kashe ko nawa ne akan yaga na fito tana gama fadar haka ta mika mata hannuwanta duka , sai da suka kalli juna da sauran yansanda nan take suka fahimci yanayin cewar hindu bata cikin hayacinta ,ta daba mata ankwa a hannuwanta tana cewa "duk abida kike taqama dashi wanda yasa muka bibiyi rayuwarki har zuwa yau din nan ya fiki kuma yafi mahaifinki komai ." "idan taqamar mahaifinki nada kudi ya zartashi dan haka kisani matsawar bashi ne ya lamunce ki fito ba ubanki bai isa ba ,kuma bashi da kudin da zai fito dake oya muje ."ta qarasa mgnr alokacin da aka qaraso da maryam wacce ke kuka har lokacin ga wata zufa dake tsatsafo mata a dukkanin ilahirin jikinta kallo daya zaka wa maryam ta baka tausayi ." Wani wulakantaccen kallo hindu tayiwa maryam sannan ta yunkura ta mike tsaye cike da d'agawa da isgilanci ta kalli macen yansanda tace "koma waye shi ina mai tabbatar miki mahaifina yana da karfin ikon da zai sa shi ya lamunce a fito dani ta qarasa maganar tana sake watsawa maryam mugun kallo "Ke kuma ki jira fitowata wallahi karon mu bazai yi kyau ba, bazan ta'ba barin kiji dadin rayuwarki ba, baqar makira wallahi nice ajalinki ki rubuta ki ajiye ." wasu hawaye masu zafi suka gangaro acikin idanun maryam hankalinta ya qara tashi fiyye da lokacin da take cikin mota ,yayinda zufa ke sake karyo mata muryarta a raunane. tace "police kunji abinda take fad'a wai zata kasheni itace ajalina "ki kwantar da hankalinki babu abinda zata iya miki daga hannunmu sai kotu zaa kaita daga kotu kuma sai gidan kurku kinga babu wata hanyar data sauran mata "karya kake munafukin Allah bani ce zani kurku ba uwarka ce zata kurku shegu matsiyata kawai tass tasss!! taji saukar mari har sau biyu ajere akan kuncinta nan da nan ta rikice ta dinga zaginsu tana tsine masu albarka mrym tana kallo aka tasa keyar hindu da bala abayan motar yansanda ita kuma aka sakata cikin wata motar aka d'auki hanyar gida daita ." Acikin mota hindu ta kalli macen yansanda taja wani dogon tsaki ta bude baki zatayi magana kenan taji sauka mari tasss!! ta sauke mata wani lafiyayyun mari "kina sake bude mana wannnan rubabben bakin naki zan qara miki wasu marukan dan haka ki kama kanki ki bari salin alim mu kai ki office idan ba haka ba zan sakar miki harsashi yadda taga matar tana mgn tana zazzaro mata idanuwa tana huci tasan da gaske take zata iya aikata fiyye da haka amman bata jin zatayi shiru ." Ta dinga kallon matar zuciyarta na cigaba da yi mata zafi ranta da zuciyarta na wani irin tafasa ta dinga zagin yarsadar can kuma tayi shiru tana son sani waye yyi mata wannnan shishigi da katsalandar cikin rayuwarta ? cure hannuwanta tayi waje daya tana bugawa da juna batayi tsamanin shirinta zai ruguje haka ba ta dauka zatayi komai ta gama babu wanda yasani taci bulus ,wato mutuwar maryam ya tafi a banza bata kawo abun zai zame mata haka ba ." Suna isa police station ta ciro wayarta daga cikin jaka zata kira number babanta amman taji an bata warning tare da kwace komai dake hannunta aka turata cikin wani qaramin daki wanda aka tanada domin masu laifi irin nata sannan suka maida kofar suka rufe garam ."kukan bakinciki bata cima burinta ba gashi kuma ta shiga hannun hukuma ya kufce mata ,dan haka ta soma maganganu cikin zafin rai tana zage zage tana tsine masu amman babu wanda ya kulata har sai data gaji dan kanta tayi shiru ta fara bin d'akin da take ciki da kallo kusuruwa kusuruwa banda duhu da zarni ba abinda ke tashi ciki ,ga kukan tsoro tun yanzu data kasance ranar allah ce ina ga dare yayi ? tsayuwa tayi taki zama dan bata ga wajen zama ba koina ta kalla kazanta né shiru tayi kawai tana tunanin mafuta ." Cikin wani irin tashin hankali maryam ta shiga part din hajiya zulai tana kuka a parlour'n ta iske nana hauwa'u da mami zaune suna ganinta gabadayansu suka mike cikin tsananin damuwa suka isa inda take mrym ta zube jikin mami tana yi mata bayani abinda ya faru gaban mami yayi wata irin faduwa "yanzu d'an rashin imani hindu tayi qoqarin kasheki ? ta qarasa mgnr tana mai sake kamo maryam din zuwa jikinta ta rungume tana cewa " yanzu ina hindu take ? police sun wuce daita ." Mami ta dafe kanta cikin yanayi na tsarkakkiya da shiga tashin hankali ,cikin tsananin' bacin rai mami ta zaunar da maryam ta soma magana "aikuwa wannna karon bazan yarda ba ,bazan zuba ido su kashe min ke ba ,"wannan ma ai rashin sanin darajan d'an adam ne ,wallahi da nasan police station din aka kaita da sai naje naci ubanta inji cewar nana hauwa'u " zagi kam babu wanda hindu bata sha shi a wajen nana hauwa'u ba, ita kuwa mami har da kwallar takaici ta zubar tana mai jin tausayin maryam wacce har lokacin kuka take ." Suna cikin wannan halin na tashin hankali ATA ya turo kafar parlour'n ya shigo tare da sallama duk da bai bude muryarshi sosai ba fuskarshi kamar koda yaushe, cike da ladabi ya gaishe da mami yana mai zama akan kujera idanunshi a runtse ta amsa tana masa bayanin abinda ya faru "yanzu da wani abu ya faru da maryama shikenan taci bulus " "Ina fa taci bulus ". ya fad'a haka acikin ransa amman a filli yace "ai ni data samu nasarar kasheta ma da ta taimakawa rayuwata "ya fad'a yana ciza gefen lip's dinsa da d'an karfi yanayin yadda yayi maganar ya bala'i daurewa hajiya zulai kai ,tayi matukar mamakin jin abinda ya fad'a, ba ita ba hatta nana hauwa'u tayi mamakinsa kuma taji babu dadi aranta "yanzu abinda zaka fada kenan adamcy ? yayi shiru kawai yana lumshe idanuwanshi "rayuwar mutun kake fadar haka kamar rayuwarta baa bakin komai yake ba "?me zan fada sweetheart da wuce haka nifa kasancewarta a raye babbar matsala ce arayuwata ." "Ka kuwa san abinda kake fada adamcy "? "iyakar gskiyata kenan na fada sweetheart kuma kin san bana fadar abinda bashi né acikin zuciyata ba ,wannan kawai ya isa ki fahimci irin rashin son da bana mata ,wallahi da zata mutu da gaske da zanfi kowa jin dadi " ni kake fadawa haka adamcy ?a gabana kake wulakata min 'ya dan baka da mutunci na rantse da girman allah sai na sa'ba maka akan wannan maganar kuma matsawar baka d'auki mataki akan abinda akayiwa maryama ba sai ka had'u da fushina da baka gani ba ." maryam ta sunkuyar da kanta kasa tana sheshekar kuka zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske wani irin tsoro ne ke ziyartar zuciyarta bata ta'ba sanin qiyayyar da yake mata ta kai haka ba sai yau din nan cike da fushi mami ta cigaba da magana "idan banda rashin mutunci irin naka agabana adamcy ,nice fa da kaina na zaba maka maryam yau ko aljanna ce maryam nace ka aura ai baka mata fatan mutuwa ba bare diyar mutun diyar ma tawa ko ka manta matsayin maryam ne a wajena "? Yana jin mami yayyi shiru dan duk abinda ta fad'a din ya sani "wallahi ban ta'ba sanin rashin mutuncinka ya kai haka ba sai yau ,mutun sukuntu guda kuma jininka da ubanta da ni uwarmu d'aya ubanmu d'aya fa, amman dan rashin mutunci kayi mata wannan fatar ,wallahi yadda zakayi farinciki da mutuwar maryama nima nasan zakayi farinciki idan na fadi na mutu "ya bude baki zai yi magana tayi saurin katseshi ta hanyar cewa "wallahi idan ka sake min wata maganar banza a nan zan iya kafa maka hakora "bai ce uffan ba ya mike tsam ya haye samansa, jiki a matukar sanyaye mami ta mike tana goge kwallar idanunta ta nufi hanyar d'akinta." tashin mami ya bawa maryam damar rushewa da wani kuka "banason na kawo damuwa acikin familes ,sister ya zaa yi a fasa auren nan kowa ya huta ? nana hauwa'u ta rungumeta tsam ajikinta tana rarrashinta"sister ki duba yadda yake nuna tsanata qarara wannan wani irin kiyayya ne haka me na kashe masa ?"."yasan adadin mutane dake bukatar aurena aka daukeni aka bashi ba dan ya cancata ba ?" wallahi gara na mutu tun kafin zuwan auren nan dan nima zanfi bukatar mutuwa ina jin kamar na kashe kaina da kaina kowa ya huta har ma dashi mai tsanartawa dasu masu bukatar ganin rayuwata ta tagayyara dan nasan aurena da yaya Adam babu abinda zan tsinta acikinsa sai bakinciki ?ta qarasa mgnr tana sheshekar kuka ." "maryam ! nana hauwa'u ta kira sunanta "me yasa kike fadar haka ai bashi zaki duba ba "sister wa zan duba ?zan rayu tare dashi ?karki manta tare zamuyi rayuwa dashi kuma acikin gida daya idan ma ta kama a daki d'aya idan damuwa yake kunsa min ni kadai zan shanye ,haka zalika idan farinciki ne ni kadai zan ji duk wani abu da zan tsinta acikin gidansa akaina zai qare kina tunanin zanyi farinciki a gidan mutumin da baya sona ?"bana jin akwai halittar da yaya adam ya tsana kamar ni, a wasu lokutan na Kan zauna nayi tunanin me yasa yake tsanata haka ?ta sauke numfashi mai hade da sheshekan kuka ya Adam yayi mugu mugun tsanata sister ." "Na fada yanzu ma zan sake fad'a aurena dashi babu abinda zai haifar sai damuwa domin kuwa bazai yi yadda kowani magidanci yake a gidansa ba ,bazai dauki duk wani responsibility dina ba,zai watsawa mami qasa a idanunta domin zuciyarsa bata tattare da tsoron kowa ko shakkun kowa na sha jin yadda yake fadawa ya hisham da yaya bello cewar baya sona ,nima idan banki auren ba sister me kike son nayi ?ni da akwai yadda zanyi na tsaida maganar auren nan wallahi da nayi domin nafi bukata hakan ko kuma mutuwata dan wallahi zan so faruwar haka da dai na kasance a gidansa abar wulaqantawa ." nana hauwa'u ta riko hannuwanta duka cikin tsananin damuwa tana cewa "tabbas akwai ciwo sister ciwo kuma mai zafi acikin zuciyarki nasan yaya Adam bai sonki sister amman bazan daina baki shawara akansa ba domin ina ji ajikina zai canza zaki canzasa sister ."maryam ta girgiza mata kanta alamun "a'a ! bazan iya ba sister bazan iya canzasa ba ,yaya adam yafi karfina yafi karfin hada rayuwa dani babu wanda yasan abinda Ke ransa gabadaya acikin halayensa bai gama fitowa dashi fili ba saboda babu wanda Ke rayuwar akarkashinsa ,sister zuciyata zata buga matsawar aurena ya tabbata dashi nasan nan gaba kadan zan mutu dan bazan cigaba da rayuwa mai dadi ba ". "kiyi addua sister dayawa anyi irin aurenku karshe kuma yayi kyau kuma anyi farinciki ki hasasowa kanki haka ki daina tunanin bad things a tsakaninku ."at every step sister ta ina kike hango min jin dadi ki duba irin abubuwan da yake ta yaya kike son nayi scricfied din rayuwata akanshi ?"nasani sister amman ki bari ayi ki gani daga ranar ki fara Kirgawa day by day wata rana soyayya zata kasance a tsakaninku wallahi inada wannan tabbacin kirki zubawa mami kasa acikin idanunta domin kuwa ta yarda dake ta fad'a ta sake jadaddawa cewar zaki mata biyayya bazaki zuba mata kasa a ido ba dan allah karki karyar da yardar data tayi miki ." "mami tayi alkwarin muddin tana raye sai anyi auren nan kuma sai kin samu farinciki a gidan yaya kuma ma shi ya Adam ya amince zai aureki har yau din nan bai ce ya fasa aurenki ba "bisa umarnin mami ba ?cewar maryam tana duban nana hauwa'u hawaye na turereniyar zubowa bisa kuncinta "ina ..!ina jin bazan .."sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da maganar gabanta na wani irin faduwa da karfin gaske." dan allah ki bar maganar nan haka sannan ki bar kuka nan tashi muje d'aki ki kwanta ki huta jiki a matukar sanyaye da taimakon nana hauwa'u ta mike tsaye tana jin wani irin sanyin a gabobinta tana jin kafafuwanta sun gaza daukarta nana hauwa'u ta rikota sosai ta makaleta a gefen jikinta suka nufi daki ." ATA ya sauko tsaf cikin wata dakakkiyar gezner tamkar ranar zaa daura masa aure dinki ya balain yi masa kyau takalmin kafafunsa cover shoes ne yayi matukar dacewa da shigarsa kanshi babu hula sai agogon fata dake daure da tsintsiyar hannunsa ahankali yake taka step yana saukowa yana duba agogon hannunsa har zai fita sai kuma ya dawo baya ya dauki hanyar dakin mami, ya tura kofar dakin a natse ya shiga ya isketa zaune hannunta rike da waya wanda ya nuna masa alamun waya ta gama tana ganinsa ta sake hade fuska tamkar bata ta'ba dariya ba dan kalamansa sun ta'bata sannan sunyi mata ciwo matuka a tunaninta ko mai aikinta bata cancanci adam yyiwa mummunar fata haka ba bare diyar danuwanta wanda su kadai iyayensu suka haifa suka bari a duniya." cikin kankanin alokacin yaga sweetheart dinsa ta canza ganin irin kallon da yake mata yasa ta kawar da fuskarta aranshi yace "har abun ya kai haka ?."shiru yayi kawai yana dubanta a tsanake shi a ganinsa babu wani laifi acikin maganarsa dan so ba karya bane haka zalika rashin so ba karya bane , hakuri yake son ya bata amman daya tuna akan maryam ne sai yaji ya fasa ,yayinda ita mami hakurin tayi tsammanin ya shigo ya bata dan shi take bukata daga garesa amman sai taji sautin muryarsa can kasan makoshi kamar koda yaushe yana cewa "sweetheart ni zan fita amman bazan wani jima ba" bata juyo ta kallesa ba bare tace masa wani abu jiki a sanyaye ya fice daga gidan gbdy can qasan zuciyarsa cike da bakinciki da fargaban shirun sweetheart dinsa dan a duk sanda tayi shiru haka matsaloli ne zasu biyo baya ." Daga shi sai direbansa acikin mota kira ne ya shigo wayarsa yana duba screen din wayar sunan aunty shahida ya gani bai dauka ba dan yasan kararsa mami ta kai wajenta yana kallo har kiran ya katse wani kiran ya sake shigowa sai datayi masa kira biyar bai dauka ba haka aunty khadija kiranta biyar har suka isa station kiransa suke yi amman yaki dauka ya fito daga cikin mota kai tsaye office din dpo ya nufa ya tareshi cikin farinciki ya mika masa hannu suka gaisa yana nuna masa wajen zama da hannunsa a hankali suka fara tautaunawa akan hindu." "ranka shi dade yarinyar nan bata da mutunci ga rashin kunya ga bakinta baya mutuwa an kawo mata abinci ma ta kwafar tana zagin wanda ya kawo mata tun daaka kawota bakinta bai yi shiru ba sai tsinewa mutane take "dubansa ATA yayi yana cewa "baku ladabtar daita bane shiyasa "ai yalla'bai na dauka kamar wancar yarinyar ce da kace kar ataba lafiyar jikinta shiyasa nayi masu gargadi amman dai tasha mari a wajen inspector romoke numfashi ya sauke "abinda ya kawoni yanzu ina son a tsanata bincike akanta fiyye da wanda akayi akan nuzla idan ta kama da duka duk ayi mata domin ta amsa laifinta ." "bare ma wannnan yarinyar cikin sauki zata amsa laifinta dan ta tabbatarwa da jami'an da suka kamota muddin ta fito sai tayi ajalin yarinyar dakasa a bibiyeta ga dukkanin alamun itace mashekiyar da muka dade muna nema ATA ya gyada kai kawai yana saurarensa."dpo ya cigaba da magana "ko akawo maka ita ne ?ya fadi haka ne ko zai bukaci ganinta kamar yadda ya bukaci ganin nuzla." ya girgiza masa kai kawai alamun baya bukata "abinda nake so bana son maganr kamata ta fita zuwa koina har ku gama bincikenku akanta sannnan bana son kowa yasan inda take har sai ta fad'a maku itace ta kashe mubina cikin girmamawa ya amsa masa da to "matsawar ta amsa itace ta kashe mubina ina son tasan girman laifin data aikata ku kaita kotu batare da sanin kowa ba alqali ya yanke mata hukunci daidai da laifinta a turata kurku wannan shine kawai abinda nake bukata "in sha allahu yalla'bai zaayi duk yadda kake so "tare da dpo suka fito yana sake jadaddawa dpo baya son tana tsare ya fito da kudi masu yawa kamar wancan ranar ya damkawa dpo sannan ya wuce ya tafi ." Ahankali yake takawa har ya isa cikin dakin mami ya sameta zaune a saman abun sallah tana jan carbi kana kallon idanunta kasan kuka tayi kuma ba kadan ba ya qarasa ya zauna a gabanta ya riko hannunta daya cikin nashi yana kiran sunanta "sweetheart!"da kyar ta dago kunburarrun idanunta ta tsura masa sannan ta zare hannunta cikin nashi tana cigaba da jan casbaha jikinsa ya sake yin sanyi bai ta'ba ganin wannnan yanayin atattare daita ba sai yau duk abinda zai mata bata taba daukar zafi dashi irin haka hasalima a inda abun ya faru anan take barinsa ." Ahankali ta mike tsaye ta koma bakin gado ta zauna shiru yayi kawai yana kallon yatsun kafafunta kafin daga bisani ya yunkura ya mike tsaye ya isa inda remut din ac yake ya dauka ya kunna saboda zafin da yake ji ya zauna kusa daita ta sake mikewa ta fito daga dakin ta barshi zaune yabi bayanta da kallo sannan ya biyo bayanta ,koda ya fito parlour'n bai ganta ba sai sautin muryarta yajiyo sama sama daga dakinsu nana hauwa'u dan haka ya haye samansa." Tun bayan fitar hindu hajiya aljannatu Ke kwance tana bacci ,acikin baccinta ne tayi mafarkin wai ga wasu mutane sun zagaye hindu wanda batasan ko su waye ba ,macen dake cikinsu taje ta samu tana tambayarta lafiya suka zagaye ta amman tayi mata shiru tana kallonsu zasu wuce daita tace "ina zaku wuce min da yarinya ?da wannan kalmar ta farka daga mafarkinta tare da kallon sugura dake zaune akan dadduma da alamun ta idar da sallah né tace "sugura ina hindatu ?"ai tunda ta fita bata dawo gidan nan ba "ta fad'a mata haka sannan ta cigaba da laziminta bandaki umma ta shiga tayi alwala ta fito tayi sallah tana idarwa tace "wallahi duk jikina ciwo yake "sannu Atu " dake haka suke kirata ." "yauwa sugura dauko min wayata na kira naji inda take "sugura ta mike ta dauko mata wayar ta mika mata ta fita atu ta soma neman layin hindu sai dai abu daya aka fad'a mata a karon farko "switch off ta sake maimaita kiran the same thing tayi shiru rike da wayar tana jin wani iri ajikinta da tunanin inda taje dan ita ba mai yawon leke leke bace acikin estate din bare tace a dubota koda yaushe tana gida idan kaga ta fita zata siyan abu ne ko kuma da shiga gidan hjy zulaihat ."wasa wasa har dare babu hindu ba alamunta nan fa hankalin mahaifiyarta dana yayyunta ya tashi nan da nan baba qarami ya fita nemanta tare da sauran yan'uwanta amman duk inda suka je basu ganta ba ,dan haka suka qarasa police station mafi kusa dasu sukayi report sannan suka dawo gida cikin matsanancin tashin hankali." Har washgari baa ga hindu ba koda hjy zulai ta samu labarin abinda ya faru batayi sanya a gwiwa ba ta d'auki kafafunta taje gidan baba babba tayi masa bayani komai ,shine ya kira baba qaramin koda ya shigo ko kallon inda mami take bai yi ba sai bayan da baba babba ya sheida masa aiko cikin tashin hankali da zafin rai yake tmbyrta police station din daaka wuce daita "ina zan sani tunda daga sama allah ya kawowa maryam dauki "bangane hausar baki sani ba "iyakar abinda nasani kenan na fada sai ka bazama zuwa duk wani police station dake kusa da nesa domin nemanta idan kuma angata lokacin ni kuma zan shigar da qarar abinda ta aikata ." wani mugun kallo ya watsa mata yana cewa "ki kalleni da kyau zulai kinga nayi miki kama da irin wadan nan mutane ?kisani ni ba wannan shashan bane da danki ya garkame masa 'ya kwana da kwanaki bai dauki mataki akai ba dan haka wulakancinki da isarki ta tsaya akansa ke kuma ki tsaya a iyakarki.." idan ba haka ba me zai kayi ?bai yi magana ba illa nunata da babban dan yatsansa da yayi alamun gargadi sannan ya juya kamar zai tashi sama naunayen ajiyar zuciya baba babba ya sauke yana cewa "kiyi hakuri kin rigada kinsan halinsa "nasani amman a haka yake son na bawa d'ana umarnin ya auri hindu ?ai wallahi dana bari adamcy Ya auri hindatu gara nuzla bancin hisham dake tsakani nan suka cigaba da tautaunawa akan matsalar ." ATA ya sauko a natse cikin shigar suit a hankali yake takowa yana kallo koina a parlour'n har ya qarasa saukowa , babu kowa parlour'n har sweetheart dinsa bata nan ,wanda adaidai lokacin daya sauko daita yake fara cin karo agabanta zai ci abinci har sai ya bar gidan take tashi ta shiga ciki wani lokacin kuma ta cigaba da zama amman yau babu ita babu alamunta ." kallon dining yayi da alamun an gama shirya masa breakfast numfashi ya sauke ya nufi hanyar dakinta ya shiga bai ganta ad'akin ba ,dan haka ya samu waje ya zauan a bakin gado yana jijiga kafarsa a tunaninsa ko tana ciki bayi kusan minti goma yana zaune amman shiru ,ya mike tsaye ya fito yana neman layinta kiran na shiga amman bata dauka ba, layin nana hauwa'u ya kira tana dauka yace "ina sweetheart ? okay ya fad'a takaice yasa kai ya wuce zuwa office bai tsaya bin takan abinci ba ." Bangaren baba qarami da yayansa duk wani office din police na kusa dasu sunje amman babu labarin hindu duk inda suka je sai ace ba nan aka kawota ba dan haka suka bazama zuwa headquarters sukai report ,da yamma koda ATA ya dawo bai iske mami ba sai dai tasa an a shirya masa dining amman bata tsaya ba tunin ya gano manufar mami akanshi tashin hankali kenan wanda baa saka masa rana idan kowa zai iya barin rayuwarsa ya hakura amman banda sweetheart dinsa bazai iya ba zai iya komai akanta zai iya sadaukar da farincikinsa gareta ." wanka ya shiga byn ya fito ya sauya kaya zuwa na shan iska ya sauko ya shiga dakin mami tana zaune tare da maryam tana shirya mata kaya a kwaba tana ganinsa ta dauke idanunta zuwa kan maryam "Yauwa maryam kwashe wannan kayan ki maida su sama, jiki a sanyaye ta dauki kayan ta ajiye kamar yadda mami ta buqata sannan ta maida murfin kwaban ta rufe ta raba ta gefensa ta fice daga dakin ." Ya sauke numfashi "ammm sweetheart "kada kace min komai please dan banason jin komai daga bakinka yadda na zuba maka ido kaima ka zuba min ido kowa yayi tsabgar gabansa kayi abinda kaga ya fiyye maka arayuwarka mami ta fad'a tana nuna masa kofa .."sweetheart "dan allah adamcy ka bar min daki tunda ba kai ka gina min shi ba fita kafin nayi maka abinda bazai mana kyau ba "sweetheart ." ya fad'a a karo na biyu zuciyarsa cike da matsanan cin tashin hankali "ka fita adamcy ka fita bana son ganinka fita ta fad'a tana kawar da fuskarta ." "Da gaske dai sweetheart dinsa bata son ganinsa me yayi da zafi haka ?a ganinsa shi bai yi laifin komai ba juyawa yayi ya fita yana waiwayenta yana jin kuna acikin rashi tun daga lokacin mami ta fita harkarsa shi kuwa abun ya damesa idan ya sauko yaga bata nan baya tsayawa karya wa zai wuce office washegari ya kasance weekend yana saukowa kai tsaye dakin mami ya shiga ya sameta zaune ya gaisheta cike da ladabi ta amsa tana qoqarin mikewa saboda har lokacin tana jin zafi da radadin abinda yayi mata har tayi taku biyu taji ya riko hannunta "dan girman allah sweetheart kiyi hakuri da abinda nayi ya fad'a cikin rawar murya." wani sanyi dadi taji ya lullubeta daman abinda take bukata kenan daga garesa sai dai taki kallonsa ahankali ya dawo gabanta ya tsugunna bisa gwiwowinsa "ina mai neman afuwarki sweetheart ki yafe min nima ba yin kaina bane ki fahimceni wallahi bana jin son yarinyar nan araina ." "amman sai kayi mata mummunar fata ?ta fad'a abun na ta'ba ranta ayi ganganci da rayuwar yarinya tankar mai fa adamcy wallahi a tunanina ko dabba na ajiye a gidan nan akayi mata haka bazaka fad'a haka ba bare mutun wacce kasan tana da mahimanci arayuwata" ta qarasa maganar adaidai lokacin da aunty shahida da aunty khadija suka turo kofar dakin suka shigo shiru kawai tayi tana dubansu ." A natse suka qarasa shigowa cikin dakin sosai suka samu waje suka zauna mami ma ta zauna tana dubansu daya bayan daya "mami kin tashi Lfy?lafiya lau ya kwanan yaran ?"duk suna lafiya suka amsa mami ta dubi babbar diyarta tana cewa "a yau nake sa ran jama'a zasu fara sauka domin zuwa bikin adamcy da maryam amman sakamakon abinda yayi na janye maganar aurensa da maryam ya d'ago kanshi da sauri ya zuba ma mami idanunshi ." "Ku sheida na yafe masa duniya da lahira yaje ya kawo min wacce yake son ya aura ita kuma mrym in sha allahu zan samo mata wanda zai min biyayya ya aureta" wani sanyi dadi ya lullubesa na farinciki jin maganarta ta farko amman kuma a karshe yaji wani irin tarin damuwa na shiga zuciyarsa matsowa yayi daf daita yana cewa "sweetheart ai na baki hakuri dan allah kiyi hakuri "na hakura adamcy amman da wani abu yaje ya sameta a sanadiyyarka kazo kana murna da jin dadi gara a fasa ." Shiru yayi ya kasa cigaba da magana "mami dan darajan allah kiyi hakuri tunda yayi nadama har ya baki hakuri sannan babu abinda zai samu maryam zata cigaba da rayuwa kamar kowacce yar adam Kiyi hakuri ki yafe masa kin rigada Kinsan halin adam bai iya magana ba duk maganar data fito bakinsa haka yake cabawa inji cewar aunty khadija wani mugun kallo ya wurga ma mai hade da harara ." "Me yasa bazai zama mutun na farko da zai ji ciwon abinda akayi mata ba? maryam fa matar da zai aura ce, matar da zai raba duk wani farinciki da akasin haka ce daita ,kuma yaruwa mafi kusanci da rayuwarsa amman ya dinga nunawa duniya baya sonta , wallahi ina matukar qaunar zamansu tare amamn tunda abun ya kai ga haka nima na hakura sannan bana fushi dashi na yafe masa duniya da lahira ya kawo wacce yake so ta qarasa mgnr kuka na kwance mata .."cikin muryar kuka aunty shahida da khadija suka durkushe agaban mami suna kuka suna bata hakuri "dan allah mami Kiyi hakuri karki bari a fasa auren nan bayn an gama komai ." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 27 Cikin muryar kuka mami tace "har yau na kasa fahimtar me yasa adamcy baya son maryam ?me maryam ta rasa ? me yasa yake jin idan ta mutu zai ji dadi zai huta?" ta qarasa mgnr tana goge hawayenta "Kiyi hakuri mami zai sota in sha allahu nan suka dinga rarrashin mami shi kuwa ATA ya qasa cewa komai sai ma ya mike cikin yanayi na tashin hankalin ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye akanshi ya bar d'akin zuwa nashi yana furzar da numfashi mai zafi ." ko bayan fitarsa hakuri sosai aunty shahida da aunty khadija sukai ta bawa mami da kyar suka samu ta sauko ta hakura "kiyi hakuri mami ki yafe masa sannan ki kwantar da hankalinki muddin muna raye adam bashi da wata mata sai maryam kuma bazamu ta'ba barin tasha wahala a gidansa ba sai inda karfinmu ya qare ."sanyayyen numfashi mami ta sauke tana mai sake gyara zamanta tare da riko hannuwansu cikin nata "na yafe masa dan ko baku nemar masa yafiya ba zan yafe masa domin iyaye ne kadai suke iya yafewa ya'yansu batare da ya'yan sun nemi yafiya daga garesu ba ,gaba dayanku allah yayi maku albarka allah kuma ya albarkaci rayuwar ya'yanku kuje ku cigaba da shirye shiryen biki ina alfahari daku ta qarasa mgnr tana murmushi ". wani farinciki ne ya mamaye zukansu suka mike suka fito daga dakin mami zuwa d'akin ATA alokacin yana kwance flat akan kujera yana fidda numfashi sama sama ."Jin motsin shigowarsu ya sashi bude idanunshi da kyar sai dai bai mike ba har sanda suka samu waje suka zauna suka tsura masa idanuwansu suna kallonsa, kusan mintuna goma suka d'auka suna kallonsa da nazarinsa sannan aunty shahida ta kira sunansa "adam !" yana jinta amman yaki amsawa sai ma sauke ajiyar zuciya yayi tare da furzar da zazzafar iska daga bakinsa " "kana jina fa adam ?"eh ina jinki ki fad'a abinda zaki fad'a ya fad'a a takaice tare da mikewa ya zauna yana kallon wani bangaren dabam yana ciza gefen lip's dinsa yayinda idanuwanshi suka canza kala dan bai ta'ba shiga tashin hankali irin na yau ba ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye ,"shi kuwa me zaiyi da maryam arayuwarsa ?ai har abada bazai ta'ba sota ba zai dai yi biyayya wa mahaifiyarsa ." Aunty shahida ta danne abinda taji na haushin abinda yayi mata yanzu ta soma magana cikin fushi "wallahi adam kabi duniya ahankali da girmanka da komai amamn ka dinga sa mahaifiyarka kuka a zatonka yadda kake yiwa mami zaka ci bulus ne ?cikin yanayi na tashin hankali ya waigo ya tsura mata tsumammun idanunshi dake cike da matsanamcin tashin hankali duk da magana yake son yi amman ya kasa bude bakinsa dan haka ya runtse idanuwanshi kawai yana janyo wani irin numfashi mai zafi yana fesarwa ya maida kanshi jikin kujera ya kwantar ." "tsawon shekaru fa take binka akan aure ,ka mance kaine kaki fito da mata har yasa ta yanke wannan hukuncin akanta ?"iyaye ne kadai suke son ganin cigaban ya'yansu mami na son ganin gobenka tayi kyau ne yasa ta hadaka da mrym sannan karka manta kai ma aure zakayi yanzu kuma zaka haihu yaya zakaji duk ranar da kacewa d'anka ko 'yarka ga abinda kake so suka ce aa ba zasu maka biyayya ba abinda suke só shi zasuyi ? "to ni yanzu me nayi kuma ?ya fad'a a matukar hassale tare da gyara zamansa ya bude idanuwanshi a hankali ya zuba masu ya cigaba da motsa labbansa "yarinyar nan ce bana só kuma bana jin zan sota ,sai kuma na kasa fad'ar albarkacin bakina ko ana so dole ne ? yayi tambayar a dan fusace yana kallonsu ,ku tsaya na tmbyeku daga Ke har khadija auren dole mahaifinmu yayi maku ?"sukayi shiru suna kallonsa dan basu da amsar da zasu bashi "gbdynku kuna son mazajenku kuka auresu to me yasa sai ni dana kasance nmj zaa wa auren dole kuma a hanani mgn ?". "amman ai ba dole sai ka fad'a a gaban mami ba ,wannan kalmar da kake fad'a ita Ke sa mami jin wani abu aranta , dannewa ya kamata kayi ka rungume maryam ."har yanzu baku bani amsar tmbyta ba tukun kafin ku shigo da wata ,auren dole akayi maku ?"zuba masa idanu sukayi kowannensu da abinda yake sakawa aransa ,ahankali ya lumshe tsumammun idanunshi tare da sanya hannunsa daya a saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take beating very fast "gbdynku bazaku iya fahimtar quna da radadin da nake ji acikin zuciyata ba ,so ne dai na fad'a bana sonta kuma wallahi ko yanzu aka fasa auren nan murna zanyi mutun daya ce kawai ta samu kyakkyawan mazauni anan itace mafarkina ,me zaayi da wannan guntuwar yarinya yarinyar Kmr agwagwa kawai fari ne ya taimaketa ya qarasa mgnr yana cigaba da shafa zuciyarsa yana lumshe ido ." "Wani haushinsa ya kama aunty khadija ranta a matukar bace tace "Idan zaka manta mafarkinka ka manta ka sanya mrym a zuciyarka dan wannan auren mutuwa ce kawai zata ra.."Kafin ta qarashe maganar ya jefa mata wani mugun kallo wanda yasa tayi gaugauwar yanke maganarta babu shiri ,dan girman allah adam kayi qoqari kasanya maryam ko kad'an a zuciyarka "bazan iya ba"ya fad'a atakaice "zaka iya adam kayi qoqarin kwatantawa please." "bama da ikon waye zamu so waye zamu fad'a soyayya dashi bazan iya yi maku karya cewar zan sanyata a zuciyata ba daga baya kuga akasin haka dan bazan iya karya maku zuciya daga baya kuji haushina ba ,kuyi hakuri kawai bazan iya ba ,sannan kusan wani abu a kullum ina fad'a maku amman kun kasa fahimtata kuskure zaayi a auren nan yakamata abar maganar auren nan haka mu cigaba da rayuwarmu daita irin ta yan'uwantaka." "zamuyi rayuwa daita ta har abada shine maanar aure, akwai abubuwa acikin rayuwar aure,aure ba abu bane na takaitaccen lokaci idan anyisa anyisa kenan sai fatan mutuwa ce zata raba zata bukaci farinciki ni km bazan ta'ba bata farinciki ba saboda ni kaina zuciyata bata tare da farinciki komai zuciyata a rufe take da soyayyar wata wato mafarkina kenan ,itama ina neman adduarku allah ya yaye min tunaninta na huta yayi maganr Kmr zai zubda hawaye . yayi shiru tare da rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana jin wani irin tuttukin bakinciki." "to Allah yaye maka tunaninta kai bama tunaninta ba ni zanyi addua allah ya mantar da kai ita gbdy kaji ka tsaneta fiyye da komai a duniya inji cewar aunty khadija ,numfashi kawai ya sauke yana kallonta a dage batare da yace komai ba dan shi yasan ba abune mai sauki ba ya mantata.yanzu ga shirye shiryen biki zaa shiga daga jibi ya kenan ?" "babu ruwana da duk wani abinda zaayi na shirin biki ,ni dai abinda nasani aure ne na amince zan aureta amman batun wani shirye shirye babu ruwana" har maganar rabon iv ?"ya ina fad'a maku bani da wata damuwa da komai da zaa gudanar kuna qara shigo min da wani maganar rabon Iv ."yayi mgnr da fushin zuciya . "rabu dashi aunty shahida duk abinda ya dace salim da hisham sunyi ,kai kuma kaje can ka karata da mugun halinka allah ya ganar da kai mu zamuyi komai kuma aure babu fashi sai an cikawa mami burinta sai dai idan mutuwa zakayi ka mutu nonsense kawai "bai sake cewa komai ba har suka mike suka bar d'akin ya koma ya kwanta lamo yana kallon saman d'akin ,ranar yini yayi kwance a d'aki cikin tsananin damuwa ." da misalin karfe takwas na dare ya sauko kamr yadda aka saba an shirya masa dining da kalolin abinci dabam dabam ya zauan akan kujera shiru babu mami haka nan ya kasa ci ya kai hannu ya shafa kanshi zuwa fuskarsa duk tsananin yunwar da yake ji ya kasa sakawa cikinsa komai ya cigaba da zama shiru sai kusan karfe tara mami ta fito daga dakinta sanye ciki riga da zani na atamfa super tana kwallawa auta da maryam kira atare suka fito daga dakinsu suna amsawa mami ta dan yi taku zuwa dining area taja kujera ta zauna tana cewa "maryam zuba mana abinci jikinta a sanyaye ta bude kular farko tana tmbayarta "mami me zan zuba miki ?" " bani rice ma ya isa amman kadan zaki zuba min ta zuba mata ta ajiye agabanta sannna ta zuba abinda tasan ATA yake so rice and stew da miyar kayan ciki da cowslow ,ta zuba shinkafar a plet dabam haka ma miyar daban tayi masa ta ajiye a gabansa sannan ta zuba nasu ita da nana hauwa'u ta dauka ta wuce." Ahankali mami take cin abinci amman ATA ko kallon abincin gabansa bai yi ba saboda haushin mami taki kallonsa ballatana yaga faraarta taki furta komai garesa idan zasu hada ido sai ta dauke kanta sosai ya shiga damuwa hankalinsa ya tashi "to me yayi mata da zafi haka ?shi kam bazai ta'ba boye felling dinsa akan maryam ba yadda zuciyarsa bata sonta haka bakinsa bazai qasa furtawa ba sai dai tayi hakuri dashi ." Ganin yaki ci yasa mami taji babu dadi aranta ta dauki spoon ta sanya cikin abincinsa ta sake tura masa tana tsaresa da idanunta jiki a sanyaye ya sauke numfashi zuciyrasa na sake karyewa allah sarki sweetheart yasan bazata iya dogon fushi dashi ba ,haka ya dinga cusawa cikinsa abinci tana tsiyaya masa ruwan lemu sai data ga ya koshi sannnan ta mike ta soma tafiya ya dago kanshi yana kallon bayanta zuciyarsa cike da tausayinta ya sani cewar tana matukar son maryama ,da wani ne yayi abinda yayi mata koda kuwa acikin ya'yanta ne sai ya hadu da fushinta fiyye da yadda ta dauka dashi amman shi allah ya saka mata hakuri dashi komai zai mata tana shanyewa har ma ta kasa daukar dogon fushi dashi." tashi yayi ya haye saman d'akinsa babu laifi zuciyarsa ta d'an samu natsuwa." Da misalin karfe hudu na ranar baki suka fara sauka a gidan mami murna a wajen mami ba'a magana ranar a kasalance maryam tayi komai daga karshe ta shige daki ta kwanta ta huta dan ta samu zuciyarta da gangar jikinta su samu natsuwa da suka rasa tun da taga jama'ar sun fara sauka hankalinta ya tashi jikinta yayi sanyi ."washegari aka fara shirye shirye biki , zaune suke a falon aunty shahida masu gyara jiki nata faman shafa masu dilka ajiki yayinda yanuwa suka zagayesu ana hira daga maryam har nuzla kana kallonsu zaka fahimci suna cikin damuwa da rashin son auren dan fuskarsu kamar zasuyi kuka gidan mami ya sake cika da yan'uwanta har yau friday da zaayi kamu mutane suna cikin zuwa ." a wani hadadden hall akayi kamu amare sunyi kyau sosai sai dai ango ATA bai je koina ba yana kwance a gida ,bangaren maryam ita kadai ce zaune akan kujerar daaka tanada dominsu dan juyin duniya aunty khadija tayi dashi amman yaki zuwa aranshi yace "ko bikin da yake so ne zaayi bazai je wani kamu ba bare wanda zaa masa na dole ."mrym kuwa juya kai kawai take zuciyarta a jagule bare idan ta kalli hisham da nuzla yadda hisham Ke jefa mata kallon soyayya da kaffa kaffa daita sai taji kamar ta daura hannuwanta duka aka ta saka ihu ko taji saukin zafin da zuciyarta take mata ta sake kallon hisham taga ya makale nuzla sai d'aukarsu hoto ake amman ita nata ango ya wulakantata." aunty shahida tayi mata duban tsanake nan da nan ta fahimci halin da take ciki ta qaraso inda take zaune tana cewa "Ki kwantar da hankalinki mrym da rashin zuwan adam kema Kinsan halinsa gara rashin zuwansa daya zo ya kunyata mu ta hanyar wulakanta mu amman muddin muna raye bazakiyi bakinciki a gidansa ba."maryam tayi narai narai da idanu zatai kuka "qul karki daga hankalinki bare Kiyi asarar hawayenki da zarar an daura shikenna ya zama naki na har abada a hankali ta dinga rarrashinta har ta dan samu natsuwar zuciya sai dai taji haushi da bakinciki rashin zuwansa domin dai so yake lallai sai duniya tasan irin auren da zasuyi ." bayan an gama kamu amarya maryam ita kadai a bayan mota direba yajata suka dauki hanyar zuwa gida yayinda hisham da nuzla suke zaune abayan tasu motar direbansu na qoqarin kunna mota hisham ya kafeta da ido sosai Kmr zai cinyeta kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kamo hannunta cikin nashi yana kallo yace "Woow my nuzla gsky lallen yayi kyau my wife waya miki shi ? hade rai tayi sosai tamkar bata ta'ba yin dariya ba a tsawon rayuwarta tana zame hannunta cikin nashi tace "ka tsaya iya matsayinka karka sake ta'ba min jiki dan wannan jikin ba naka bane "na waye "? ya tambayeta yana matsota sosai Kmr zai shige jikinta "tambayarki nake "jikin waye ?"stil dai shiru tayi masa " jibi iwar haka kina cikin gidana watakilla ma muna kwance acikin bargo daya makale da juna "wani kuka ta fashe da shi tana qara matsawa ". " to to!! shikenan na bari Kiyi hakuri amman dai Kinsan dole zamu kasance tare? tsaki taja ta kawar da fuskarta gefe a haka suka qaraso gida ."mota bata tsaya a koina sai a kofar gidansu bayan motar ta tsaya ta fito hisham ya biyota suka jira yana yi mata magana amman taki kulashi tana qoqarin shiga gida ya riko hannunta daya cikin nashi ta juyo a matukar fusace tana kallonsa shima kallonta yake with a broad smile a fuskarsa sai itace ta dauke kanta tana lissafi yadda zata gudu ta bar shi da wahalarsa ". "anya kuwa zata iya gudu ta bar iyayenta bayan a yanzu bata iya zuwa koina ta kwana batare dasu ba ?ta tambayi kanta nan take zuciyarta ta bata amsa da" wannan shine mafuta a gareki idan komai ya natsa sai ki dawo wanda zuwa lokacin dole kowa ya hakura ." ta sake kallonsa taga har lokacin ita yake kallo yana murmushi wanda bata san ko na meye ba ."cike da jin haushi ta fix hannuta tana mai bakinciki dan komai ya faru da rayuwarta shine sila shekara da shekaru bata ta'ba tunanin barin iyayenta ba sai a dalilinsa ita kam tsakaninta dashi sai dai allah ya isa da wannan bakinciki ta shige gida ta barshi tsaye yana kallon bayanta ". Sai bayan data shiga gida sannan ya juya ya wuce kai tsaye wajen ATA ya wuce koda ya shiga parlour'nsa yana tsaye akan dadduma yana sallar magrib bai zauna ba shima bathroom ya shiga ya dauro alwala ya fito ya bisa sallah ,bayan sun idar ya fara tsokanar ATA "ango ango !!amman gsky kai dai anyi dan iskan ango ,wallahi baka kyautawa maryam ba, ka barta ita kadai allah sarki wallahi na tausaya mata, wallahi abokina kabi a hankali ina guje maka ranar da zaka rufta "wani dogon tsaki yaja yana watsa masa harara tare da cewa "ka maida hankalinka jikinka da wannan shirmen da kake yi karka sake min maganar auren nan" hisham yayi murmushi yana cewa "ai hankalina yana jikina nan dai yayita jan ATA." Nuzla tsaye a dakinta hawaye na zubo daga kwarnin idanunta alokacin da take daukar abubuwan amfanita masu mahimanci tana tuna rayuwar kuncin da iyayenta zasuyi idan suka laluba basu ganta ba ,bayan kamar awa daya nuzla ta fito zuwa babban parlour'nsu koina ta kalla mutane a parlour'n yan'uwan mahaifiyarta gbdy zaune kai tsaye ta shiga dakin hjy salema bata dade ba ta fito ta rasa yadda zaayi ta sake fita dan haka ta koma ciki d'akinta tana tunani hanyar da zata bi ta kubta daga wannan wahallen auren ." byn Kmr mintuna goma ta sake fitowa har ta kai bakin kofa aunty maijidda tace "ina zaki kuma adaidai wannan lokacin ? Ta fad'a tana kallon agogon dake manne a falon ,nuzla ta dan diririce sannan tace "yaya hisham ne ya kirani yana waje" tana gama jin abinda ta fad'a ta juya tayi d'akin da baki suke ita kuma nuzla ta samu damar fice wa daga gidan gabadaya ." yan'uwan hjy salema suna ta kikiniyar da hadahadar abincin gobe diner sam babu wanda ya fahimci nuzla bata gidan har karfe goma sha biyu na dare ."Hjy salema dake zaune a bakin gadonta haka nan jikin ta ya dinga mata wani iri ,ta fito ta shiga dakin nuzla bata ganta ba dan haka ta juya ta fito daga dakin tana tmbayr aunty rabi wacce ta kasance diya kanwarta ce "umma bansa inda take ba amman bari na dubata a dakinta "ai daga dakin nata nike bangata ba shiyasa ma na tambayeki ." to bari naje na tmbyi aunty maijidda ko tasan inda taje da sauri ta wuce hjy salema." A bakin kofar fita daga parlour'n suka hadu da aunty maijidda "Yauwa aunty maijidda ina nuzla ko ta fad'a miki inda zata "eh d'azu tace min zata wajen hisham amman bari na kirata nan ta soma qoqarin kiran layin nuzla sai dai numberta na shiga bata dauka dan haka ta kira layin hisham tana tmyrsa nuzla amsar daya bata yasa ta shigo d'akin hjy salema da mugun sauri ta isketa tsaye cikin faduwar gaba ." Aunty maijidda batayi magana ba ta cigaba da kallon hjy salema "maijidda ko nuzla ta fad'a miki inda zata ?ta bude bakinta kenan zata bata amsa idanunta suka ci karo da envelop asaman dress mirrow din hjy salema an rubuta wannan sakon na umma da abba ne kallon da takewa envelop din yasa hankalin hjy salema ya kai kanshi " gabadayansu gabansu ne ya shiga dokawa dan basusan me Ke kunshe a cikinsa ba tun baa kai ga budewa ba hjy salema ta soma furta kalmar "innalilahi inna ilahi rajiun azuci da fili dan ta gama shiga rudani "hannun aunty maijidda na rawa ta dauka ta bude envelop ta soma karantawa a fili hannunta da jikinta na wani irin wara ." _Assalamu alaikum iyayena nasan aloakcin da zaku nemi ni ku rasa zaku ji babu dadi acikin ranku amman ina mai baku hakuri da neman afuwarku akan halin damuwar da zaku shiga a dalilina na tafe ne adalilin bana son aurena da yaya hisham na fito maku da manufata amman kun kasa fahimtata dan haka na yanke shawarar barinku ba dan raina yaso ba ina sonki ummanah ina sonki fiyyr da komai haka kai ma abbanah ina sonka zanyi kewarku sosai_ rabi ta nike takadar ta mayar cikin envelop din tana kallo hjy salema data zube kasa jinta ne ya dauke dip sakamakon abinda wasikar Ke dauke dashi duk wani kuzari da karfin jiki babu atattare da ita baya ga tashin hankali "ji take kmr ba ita bace anya nuzlarta ce kuwa ta ajiye mata wannna sakon ? Aunty rabbi duk ta rude sai zufa take fitarwa nan da nan aka kira baba babba da yayyen nuzla maza har ma da hisham da ATA aunty rabi tace baba "kaji wani sabon tashin hankali nuzla ta gudu ta mika wa yaya Ibrahim wasikar ya duba ,hannu hjy salema ya kama dan ta kasa motsin kirki binshi takeyi kmr rakumi da akala har uwar dakanta ya kamota yana qoqarin zauna daita taki zama tana fashewa da wani gigitaccen kuka tana furta sunan "nuzla! "ku nemo yarinyata dan allah ku nemo yarinyata abinda kawai take iya furtawa kenan " "Ki kwantar da hankalinki hajiya zaa nemota yanzu ki zauna ki samu natsuwa ta girgiza masa kai tana mikewa ta fito tana kuka tana kiran sunan nuzla dole ya biyota damuwace karara ajikinsu, dukkan su da abinda suke sakawa cikin sanyi muryarshi wanda koda yaushe a haka take cikin sanyi ATA ya dinga kwantar wa da hjy salema hankali da tabbacin zaa ganta sai lokacin tadan dawo da ga mummunan mafaarkin da take dan gani take tamkar a dream ne ,, ta dan dawo haiyacinta sai dai kalmr INNALILLAHI INNAILAIHI RAJIUN take maimaitawa " Numbobin yanuwa da abokan arziki aka shiga kira sai dai koina sai ace bata je ba duk suka rude kar ma hisham yaji labari duk ya rude ya rasa inda zai sa kansa idanunsa suka kada sukayi jajir gbdy ya nemi natsuwarsa ya rasa ji yake kamar zuciyarsa zata buga."gabadaya yan mazan babu wanda aka bari duk sun bazama nemanta hisham kam baya fahimtar komai duk maganar da salim yake masa baya shiga kunnuwanshi shiyasa yaji Kmr ya fita daga cikin motar ya taka da kafarshi watakilla nashi gudun zai fi na motar duk jikinsa tsuma yake kwakwaluwarsa ta hargitse kamar hauka zai kamashi a haka suka qaraso babban titin unguwarsu suna gama tsayawa ya fito da sauri yana dube dube amman babu ita babu alamunta ." Numberta ya dinga kiran taki shiga har karfe biyun dare basu ganta ba suka dawo gida cikin damuwa baba babba yace kowa ya tafi kawai makwancinsa sai gobe aga abinda zaayi ."ranar kwanan zaune sukayi duk hankularsu a tashe hjy salema kuka kawai take zainab da aunty maijidda ce masu dan dauriya matar salim kuka take hjy salema duk ta rikice masu sai sunan nuzlata take kira ,hisham kwana yayi yana kiran layinta gbdy ya zare sai salim ne ya dinga kwantar masa da hankali ." Washegari duk esatate din ya hargitse da labarin guduwa nuzla fad'ar irin tashin hankali da suka shiga bata baki ne yan biki sun cika gida babu abinda ake sai jajantawa juna ATA ya bada cigiyarta a duk kafafen sadarwa, lokacin da iyayen hisham suka qaraso daga masaukinsu dan su ba zaune suke a qasar ba hankalinsu ya tashi matukar most especially mahaifinsa sakamakon jin mummunar labarin abinda ya faru dan kallo daya yayiwa hisham ya fahimce sam hankalinsa bai jikinsa ga wata katuwar rama da yayi acikin kwana daya ." amman ita mahaifiyarsa byn tashin hankali data shiga har 'bacin rai ta tsinci kanta ciki ranta ya baci matuka bare da ta samu labarin akan bata son d'anta ne ai sai taji soyayyar da takewa nuzla din ta juye zuwa tsana mai karfi " Nana hauwa'u na zaune acikin dakinsu tare da maryam da diyana har ma da humaira , gabdayansu suna cikin jimamin abinda nuzla ta aikata "humaira tace "bansan me zai sa na gudu na bar iyayenta akan zaa aura min wanda banaso ,kowani iskanci mata sune kan gaba ku duba kuga shi nmj komai zaayi masa bazai ta'ba guduwa ya bar iyayensa ba amman sai kaga mace wai ta gudu wallahi nuzla really disappointed me ." "maganarki gsky ai ko maryam ta isheta darasi gashi dai bata son yaya adam amman haka ta daure ta karbi kaddararta cikinsu babu wanda bata fadi albarakcin bakinta ba suna cikin wannan halin aka turo kofar dakin aka shigo hade da sallama gabdayansu suka waigo bayan suka kalli kofar dakin domin ganin wanda ya shigo ,hajiya zulfa'u suka gani sanye cikin doguwar riga na alfarma hannuwanta da wuyanta da yatsun hannunta duk gwal nd tayi kyau matuka sai dai kana kallon fuskarta zaka fahimce bata cikin natsuwa ." Ta qarasa shigowa sosai yayinda gabadayansu suka maida hankalinsu gareta suka gaisheta cike da girmamawa ta danyi murmushi wanda kana ganin kasan na karfin hali sannan ta amsa , ahankali ta samu waje ta zauna agaban nana hauwa tana cewa "ku bani waje zanyi magana da nana hauwa'u gaban nana hauwa'u yayi wani irin faduwa ta hade hannuwanta waje daya tana wasa da yatsun hannunta har zuwa sanda suka fice daga dakin ". "nana hauwa'u!" ta kira sunanta tare da jawo hannunta ta zaunar daita kusa daita bisa kujerar da take zaune akai "meye matsayina a wajenki ? tmbyr ta dan bawa nana hauwa'u mamaki amman dai ta bude baki ta bata amsa da "mahaifiya !" na gode mahaifiya zata iya yanke kowani irin hukunci akan diyar ta sai dai ni bazan yi haka ba sai dai na neman alfarma a wajenki ,nana hauwa'u tayi shiru kawai tana sauronta." hjy zulfa'u ta cigaba da magana "ina neman alfarmar ki auri dana kuma yayanki hisham " cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoro abinda take shirin aikatawa ta dago da kanta ta tsura mata ido cike da tashin hankali "nasan zaki iya min fiyye da haka ,ki taimkeni kar na kunyata a gobe nazo da tarin jama'a ban san me zance masu ba idan baa daura auren nan a gabe ba ,cikin tsananin tashin hankali da firgici da tsinkewar zuciya da tsoro tare da kyarma nana hauwa'u ta fuskanci kanwar mahaifinta" dan Allah karki bani kunya nana hauwa'u ki amince min zaki samu dukkanin kulawa a gidan hisham cikin zuba mata ido tace "mumy yaya hisham..! karki ji komai kawai amincewarki nake nema " Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 28 ..... Hajiya zulfa'u ta sake riko hannun nana hauwa'u gam cikin nata tana cewa "karki ji komai aranki hisham zai kula dake bazai ta'ba wulaqantaki ba wani yanayi nana hauwa'u ta dinga ji a gbdy ilahirin jikinta, kyarma da jikinta yake ya sake qaruwa ,babu abinda yazo mata alokacin kamar rayuwar maryam da yayanta adam yadda yake nuna rashin qauna garara agaban ko waye ,duk da mami dake tsakaninsu hakan bai sa ya hakura ya rungumeta a matsayin matar da aura ba." ta daure ta cije amman tunaninta na zuwa kan maryam da yayanta ta fara hawaye saboda tasan me zai iya faruwa daita matsawar ta amincewa wannan auren ita kad'ai tasan yadda take jin zuciyarta a halin da take a lokacin wani irin tsananin tsoro ne ya shigeta ." Kukanta ya d'aga hankalin hjy zulfa'u, jikinta ya soma kad'awa kamar mazari tana jin tsoron karta ki amincewa da muradinta amman duk da haka ta sanyawa jikinta jarumta tace "dan allah nana hauwa'u karki ce mun a'a rashin amincewarki zai sa naji kunya.wannan buqatar bawa ni kad'ai zakiyi ba har da martabar danginmu zaki yiwa kuka nana hauwa'u ta cigaba da yi har da shesheka tana mai tausayawa kanta ." " tana son taki amincewa amman kuma bazata iya karya wa mumy zuciya ba tunda tasan ba ita kadai bace budurwa da bata yi aure a family ba ta tsallake kowa ta miki kokon baranta zuwa gareta ahankali ta d'ago idanunta dake cike da ruwan hawaye ta zuba mata "sosai ta tausayawa yanayin da hjy zulfa'u ta shiga dan a shirye take tayi komai akan amincewarta." "Nasan kina tunanin halin da zaki tsinci kanki né a gidan hisham amman kisa aranki duk abinda zai faru na wani lokaci ne da sannu zaki zama tauraruwar agidansa idan kuma kikaji bazaki iya zama dashi ba ki fad'a min idan yayi miki wani abu na rashin kyautatawa just give me a call aurenku bazai qara ko second daya ba zan raba "ta fad'a tana jin d'acin kalmar aranta dan bazata so aurensu ya rabu zataso su kasance da juna har karshen numfashinsu." Still dai shiru nana hauwa'u tayi tana zubar da hawaye "ki tausaya min diyata kar naji kunya ." ire iren sambatun da take mata kenan wanda ya haddasawa nana hauwa'u jin tausayinta mai tsanani bugu da qari ita din mutun ce mai mahimanci arayuwarta sannan taji dadin kalamanta tana ganin abun zai zo mata da sauki ta hanyar mumy muryarta a matukar sanyaye tace "mumy mami fa? "ina ..ina ganin ya kamata muji ta bakinta ?ta qarasa mgnr muryarta na rawa cike da in ina tare da sake sunkuyar da kanta ." Hajiya zulfa'u ta d'aura hannunta daya akan nana hauwa'u tana shafawa tana jin wani irin sonta na shigarta fiyye da soyayyar dataji tana yiwa nuzla, har cikin bargon zuciyarta take jin nana hauwa'u wanda abun ya hade mata ne soyayyar mahaifinta da kuma na d'anta tilo da take dashi wanda a yanzu bata da kamarhi a duniya "nana hauwa'u maminki tasan da komai hasalima gurinta na fara zuwa har ga allah aunty zulai ta amince, tace daman burinta kenan taga kinyi aure kafin allah ya dauki ranta taga yan jikokinta na wajenki kullum adduarta fatan miji na gari take miki ,gashi kin samu domin hisham danuwanki yafi kowa cancata dake nmj né da idan mace ta samesa zataji dadin rayuwa dashi ,domin kuwa miji na gari né allah ya hadaki dashi ta amince dari bisa dari kawai a nemi amincewarki Ta dago kanta tana kallonta murmushi tayi ga kuma hawaye na gangaro mata tace "shikenan mumy tunda mami ta amince nima na amince kuma nayi miki alkwarin zan zauna lafiya dashi zan kawo miki farinciki arayuwarsa zakiyi farinciki da kasancewarmu ." Nan take hajiya zulfa'u ta rungumeta tsam ajikinta cikin tsananin farinciki tana hamdala a fili "Alhamdulillah diyar albarka na gode nana hauwa'u ,kin tabbatar min da ina da matsayi a wajenki kuma zakiyi farinciki a gidan hisham in sha allahu bazakiyi kuka ba 'allah yayi miki albarka ta riko hannunta Tare da d'agata tsaye ta soma tafiya daita, binta kawai take har lokacin da suka fito zuwa falon gidan wanda a daidai wannan lokacin da karfe shadaya na safiyar ranar ta buga babban falon baba babba ya cika da gabdaya ahalin yaya Alhaji Abdallah." dayawa daga cikinsu zukantasu na cikin da tsananin tashin hankali bangaren baba qarami wanda har lokacin bai san inda diyarsa hindu take ba ,haka baba babba wanda ya rasa diyarsa a daren jiya bangaren mahaifin hisham shima zuciyarsa cike take da damuwar halin daya baro dansa ciki haka hajiya salema tunda ta zauna hawaye kawai take gogewa wasu na sake zubowa haka zalika uban gayya ATA da zaa yiwa auren dole tun daya zauna idanunshi ke kallon sama tunani kawai kwakwaluwarsa keyi ." babban parlour'n ya dauki shiru na kusan mintuna goma sha biyar kowannensu da abinda zuciyarsa take saqawa ,baba babba yayi gyaran muraya sannan ya fara magana a tsanake "zan fara da jajantawa kanmu halin da muka tsinci kanmu a ciki wannan lokacin amman nasan allah yana tare damu ,fatanmu allah ya bamu ikon cin jarabawar data fad'a mana nida dan'uwana" . "ni ai ikon allah da kuma rashin qarar kwana ne kawai yasa har yanzu ban mutu ba akan rashin hindu inji cewar baba qarami jin abinda baba qarami ya fad'a cike da damuwa yasa ATA sauke kanshi ya kallesa kawai yana ta,be baki at the same time zuciyarsa na tsananta bugawa yana jin ina ma shine hisham da nuzla ta gudu ta barshi , ina ma shima wannan guntuwa shegiyar yarinyar ta gudu ya huta tunda itama ba son shi take ba "zaune amman zuciyarsa bata gaji da adduar samun sausauci daga wajen allah ba ". " in sha allahu allah zai bayyana su gabdaya suka hada baki suka ce "Ameen allah ya kawo mana mafuta sun dade suna tautaunawa akarshe baba babba yace "yanzu ya zamuyi ? "dawa zaa maye gurbin nuzla a wajen hisham domin dai bazaa fasa d'aurin aurensa ba ?ya qarasa maganar adaidai lokacin da hajiya zulfa'u ta shigo falon hannunta rike dana nana hauwa'u tana cewa "karku damu ga wacce zata maye gurbin nuzla a wajen hisham nan domin kuwa na nemi alfarma a wajen diyata nana hauwa kuma ta amince da zata auri hisham tsakanin da allah ." Da wani irin saurin hjy salema da kanta ke duke ta d'ago tana kallon fuskar nana hauwa'u zuciyarta cike tashin hankali mara misaltuwa yayinda idanuwanta suka sake cikowa da ruwan hawaye, kallo daya nana hauwa'u tayi mata ta fahimci halin damuwar da take ciki ga dukkanin alamun bata ji dadin hukuncin ba ,ahankali tayi kasa da kanta dan bazata juri kallon cikin kwayar idanunta hjy salema ba dan wani irin tausayinta ne ya lullubeta ,itama bata só haka ba sannan ba yin kanta bane babu yadda zatayi , da ahlinta su kunyata gara ta rungumi qaddarar auren yaya hisham ,kuma ma ai asirinsu zata rufa gabadaya har ita nuzla domin idan basu na gida da suka san ta gudu ba babu wanda zai sani ". Kafin hjy zulfa'u ta sake magan tuni ATA wanda hankalinsa ya tashi matuka da jin maganarta yace "da gaske nana hauwa'u kin amince ko kuwa kina son yiwa mutane wasa da tunani né "?jikin nana hauwa'u a matukar sanyaye ta jinjina masa kai jikinta na kyarma jin yadda jikinta Ke rawa yasa hjy zulfa'u ta rikota sosai ta had'eta da jikinta saboda tsabar farinciki data haifar mata "amman dai nana hauwa'u kin kyauta Allah kuma yayi miki albarka allah yasa ki gama da duniya lafiya lafiya inji cewar baba babba ." "Gsky kin kyauta sam ban yi tsamanin zaki mana haka ba hakika kin fitar da alhalinki jin kunyar duniya ,allah yayi miki albarka yasa ki gama duniya lafiya yadda kika rufa mana asiri kema allah ya rufa miki asiri duniya da lahira hajiya jamila mahaifiya ga aunty abida ta fad'a cike da jinjina mata." gabadaya mutanen dake parlour'n addua suke mata tare da gode mata amman ban hjy salema da mami wacce tayi alkunya ,yayinda ita hjy salema bakinciki né Kmr ya kasheta ,duk da irin qaunarta ga nana hauwa'u sai taji a yau babu ita ta juye zuwa qiyayya mai zafi "me yasa zata amince da wannan auren bayan diyarta ce tafi cancata da auren hisham ?"ko bama haka ba a tunaninta ko auren wasu zaayi dabam ya kamata a d'aga shi sakamakon rashin diyarta da tayi amman hankalin kwance suke bayyana farincikinsu ." wani sanyin dadi ne ya lullube nana hauwa'u jin dadin yadda ahlinta sukai alfahari daita ."muryarta a matukar sanyaye tace "me yasa zakuyita gode min dan Allah ku daina gode min nayi saboda kare martabar gidanmu né ,bazan so ahlina suji kunya ba a idon duniya ba halin yanzu abinda nafi buqata daga gareku shine addua kuma kunyi min "ta qarasa maganar muryarta na rawa hajiya zulfa'u tayi saurin cewa "yar albarka karkiyi kuka idan kikayi kuka nima zanyi ". Cike da zafin zuciya take cigaba da kallon hjy zulfa'u da nana hauwa'u dake drama dan abinda ta d'auka kenan ,ahankali ta mike tsaye ta tsaya a yayinda bakinciki da zafin zuciya ke kutimemeya daita ita kam nana hauwa'u kunyata ce ta kamata da kuma kunyar hada ido da hajiya salema ta sauke ajiyar zuciya sannan ta soma magana cikin fushi "hakika baku min adalci ba ,kowa anan yasan yadda mukayi fama da nuzla akan hisham "yanzu da abinda zaku saka min kenan ?diyata ta gudu saboda bata són auren nan amamn shine zaa dauki wata a maye gurbinta daita ni ko oho kenan shikenan na rasa diyata ?."ta qarasa mgnr tana wani irin kuka" kusani bazan ta'ba manta wannan ranar ba a tarihin rayuwata yadda aka sauya nana hauwa'u da nuzal tana gama fadar haka ta nufi hanyar fita cikin gagarumin tashin hankali." ATA da yayi mutuwar zaune ya mike tsaye zumbur ya soma takowa zuwa inda nana hauwa'u take tsaye, kansa nayi masa wani irin sara ya qaraso ya tsaya gaban nana hauwa dake kallon kasa yasa hannu ya d'ago ha'barta ya zuba kwayar idanunshi cikin nata yana kallon cikin kwayar idanunta da hawaye ke kwance acikinsu sakamakon jin furuncin hajiya salema ." Muryarsa a kasalance ya soma motsa labbansa "daman kina son hisham ne ?ta girgiza masa kai alamun a'a "to me yasa zaki amsa zaki auresa ?ta sake girgiza masa kai "ki bude baki Kiyi min magana yayi maganar a tsawace wani tsoro né yayi ma nana hauwa'u diran makiya taji kmr ta saki fitsari a wajen tsabar tashin hankali da sauri ta bude baki tace "a'a?"!To kiina hauka ne ko kin fara shaye shaye ne ?gabanta ya dinga bugawa gbdy duk wata gaba da allah ya halitta ajikinta rawa take kallo daya zaka mata ka gane hankalinta a matukar tashe yake "kin kuwa san irin hatsarin da zaki jefa rayuwarki ciki ?jikinta na rawa ta girgiza masa kai "kin kuwa san me ake nufi da aure ?aure na nufin mutuwa ce kawai zata raba ko kinsan auren da duk baa ginasa akansa soyayya ba baa samun farinciki acikinsa ,maza maza ki fad'a masu cewar kin fasa wannan auren yana gama maganar ya juya zai fita daga d'akin tayi saurin shan gabansa ta durkushe a gabansa ta rike kafafunsa da hannuwanta "kayi hakuri yaya bazan iya ba na rigada nayiwa mumy alqawari kayi min addua tare da fatan alkhairi , kai ne fa ka hada auren hisham da nuzla ba dan tana sonshi ba sai dan ka faranta masa kuma babu wanda yayi maka mutsu bare jayayya akan hukuncinka me yasa alokacin bakayi tunanin auren da duk baa ginasa akan soyayya ba baa samun farinciki?ni da nuzla duk abu daya ne a wajenka idan har zaka iya yanke hukunci akan nuzla kowa yayi na'am dashi kai ma ka amincewa hukuncin mumy akaina". Numfashi ya janyo da kyar ya fesar yana qoqarin janye kakafusa ta sake rikewa gam tana zubar da hawaye "please yaya karka ki amincewa mumy bata takura min ba ni na amince daga qasan zuciyata kuma zan zauna da yaya hisham tsakanina da Allah." "Auta me yasa bazaki fahimta ba ?"me yasa zakiyi sacrifice din rayuwarki akan farinciki wasu ?idan Ke zaki iya rayuwar kunci ni bazan iya ganin rayuwarki cikin kunci ba ,bazan so rayuwarki ta qare a wahala ba, ciwon zuciya né zai kasheki saboda zai ta kunsa miki bakinciki né tunda ba kece zabinsa ba "kayi min addua kamar yadda kowa yayi min shine kawai abinda nafi buqata ahalin yanzu ta qarasa mgnr tana shesheka kuka runtse idanunshi yayi tare da dafe kanshi dake cigaba da sarawa "akwai damuwa auta ,akwai zafi da radadi ,yau ace nmj ne Ke son mace komai mai sauki ne, na yanke hukunci akan nuzla ne sanin zatayi farinciki tunda hisham na sonta ke fa ?" bai ta'ba kawowa rayuwarsa ke ba, sam sam bai ta'ba tsara rayuwarsa dake ba idan kina kallon mumy na sonki ba shi ya zamanto zakiyi farinciki a gidansa ? "please yaya !ta fad'a tana wani irin kuka mai d'aga hankali kalmamin mumy da ta dinga fad'a a wannin data gabata wanda mami ta fad'a mata ne ya dinga dawo mata daki daki ,tunda har mami ta amince da aurenta da yaya hisham bazata ta'ba kin auren nan ba, domin tayi imani ace yaya hisham ba na gari bane mami bazata yarda da hadin ba hannunsa yasa ya d'agota yana share mata hawaye dake gangaro mata sannan ya rungume ajikinsa yana d'an dukan bayanta" wannan shine karo na farko da yayanta yayi mata haka a tun tasowarsu " daman haka yake tsananin sonta ?daman akwai ranar da zai nuna damuwarsa da kulawarsa gareta "?shiru tayi ajikin yayanta tana sauke numfashi ." Ahankali ya zareta ajikinsa ya zuba mata idanuwanshi itama shi take kallo hawaye na sake cikowa a idanunta "shikenan auta allah yasa albarka yana gama fad'ar haka ya juya Jiki babu kwari ya fice daga d'akin cikin wani irin yanayi na tashin hankali "shi dai har ga allah wannan hadin bai yi masa ba babu yadda zaiyi ne kawai ." Sunkuyar da kanta kasa tayi ta kasa hada idanu da jamar dake falon babu wanda bata burge ba hatta baba qarami ya jinjina mata domin yasan ba kowa bane zai iya yin abinda tayi haka muke fata a kowani lokaci idan mukayi umarni ya kasance kunyi mubaya'a wannan shi zai sake tabbatar mana da irin tarbiyar da muka baku mun gode da biyayya da hukuncin da muka zartar akanki dan haka ina miki albishir da cewar zaki samu farinciki inji cewar hajiya zulfa'u ta kamota zuwa jikinta "my dear dan Allah ki ramin bala direba zai kai wani waje " kai kawai ya gyada mata sannan ya ciro wayarsa ya soma neman layinsa yayinda tayi hanyar waje da nana hauwa'u ta barsu suna cigaba da tautaunawa har d'akinsu inda ta d'aukota ta maidata tana cewa "bani wasu mintuna zan dawo yanzu kai kawai ta gyada mata sannnan hjy zulfa'u ta juya ta fita daga dakin alokacin bala direban ya iso yana tsaye a haraban gidan ya juya kan mota yana jiranta yana ganin fitowarta yayi saurin fitowa ya bude mata gidan baya ta shiga motar ta zauna tana bashi umarnin inda zai kaita ya amsa mata da "tô!."ya rufe mata murfin motar ya shiga mazaunin direba ya tada mota suka fice daga haraban gidan ." Hjy zulfa'u na fita daga dakin nana hauwa'u ta kwanta lamo ranta duk babu dadi tunani ne ya lullubeta ita kanta tasan gsky yayanta ya fata mata aure ana ginasa ne akan soyayya domin samun zaman lafiya kuka nana hauwa'u ta fashe dashi wanda har maryam da diyana suka shigo bata sani ba mrym ce ta isa wajenta tare da dafe qirji tana cewa " Sister lafiya me ya faru ?kuka ta cigaba dayi batare da ta bata amsa ba dan girman allah ki fada min me ya faru ." Diyana ta riko hannunta "me ya sameki hk kike wannan uban kuka haka "nice zan maye gurbin nuzla a wajen yaya hisham "what ?suka had'a baki ta kwanta ajikin mrym da tafi diyana shiga tashin hankali hawayenta take ji ajikinta ta ma rasa me zatace "nima shikenan rayuwata tazo karshe nasan yaya hisham bazai so ni ba tunda nuzla yake matukar só? mrym ta d'agota daga yadda ta kwanta ajikinta "wai wa ya zarta da wannan hukunci ?"shigowar da mumy tayi d'azu nan tayi musu bayanin komai "am very sorry kema da laifinki taya zaki amince mata inji cewar diyana ." "yaya zanyi bazan iya zuba mata qasa a ido ba mumy ta wuce hk awajena bani ba nasan ko ke tayi wa mgn zaki amince mata bugu da gari mami ta amince diyana bata sake cewa komai ba tunda taji mami ma ta amince ,mrym kam rarrashinta take tana karkafa mata gwiwa "tunda mami ta amince ki kwantar da hankalinki kece fa ke bani kwarin gwiwa kina són naji bani da wannan kwarin gwiwar né ."?ta girgiza kai "tô dan girman allah kiyi hakuri kiyi shiru mu barwa allah komai ." bangaren ATA zuciyarsa a cunkushe ya shiga d'akinsa bakinciki abinda nana hauwa'u da auren dole da mahaifiyarsa zata masa na sake ninkuwa ,wani irin zafi zuciyarsa ke masa zuciyarsa na matukar zafi ya bud'e qaramin fridge dinsa ya d'auki gorar ruwa tare da kafawa a bakinsa sai daya shanye tas sannan yayi wurgi da roban." Ahankali ya zame ya zauna akan kujerar kushin "wai me yake faruwa dani né komai ya zama worst agareni shine tambayoyin daya cigaba dayiwa zuciyarsa sam ruwan bai sanyaya masa ransa ba dan damuwarsa na nan bata ragu ba babu abinda yake bukata kamar sigari dan irin sarawar da kanshi yake a yau din nan dole ya had'a da sigari idan ta kama har da giya a hada masa dan yana buqatar ya bugu iya bugawa ya kira daya daga cikin yarasa yace ya kawo masa ta'ba sigari kwali ashirin yana gama wayar ya kwanta yana jiran Peter ." Bai dade da kwanciya ba aka soma knocking kofar falon yana daga kwance runtse idanushi daga shi sai wondo baki da riga hamles ash colour ya bada umarnin shigowa peter ya shigo cikin falon hannunsa rike da leda cike da girmamawa ya rusuna ya gaisa da ogansa ATA ya yunkura ya mike zaune ya amshi ledar had'e da bude wata durowa dake gefensa ya zaro bandir din fararen yan dubu day day ya mika masa sannan ya bude ledar ya zaro kwalin sigari ." karba peter yayi ya cigaba da tsayuwa "kaje ka siyo min giya kwalba biyar mai kyau ka kawo min yanzu yanzu ."ya fad'a yana d'aura sigari abakinsa Kallonsa peter yayi cike da mamaki dan tabar ma ya jima bai aikesa ba ". "amman boss ....." just leave "babu shiri peter ya juya da sauri ya fice daga falon sigari ya soma zuka ko kafin peter ya dawo ya shanye kwali biyu yana kan na uku cike da girmamawa zai ajiye masa yace ya bashi kwalbar giya biyu yasa sauran a fridge ya nuna masa fridge sannan yace d'auko masa glass cup ya d'auko ya mika ya kama gabansa yana janyo masa kofar ." ATA ya kashe wayoyinsa gabadaya sannan ya balle kwalba giya ya tsiyaya a glass cup ya kai bakinsa bai ji komai ba dan babu abinda yafi bukatar alokacin kamar ya bugu ,yana son ya manta komai ciki kuwa har da mafarkinsa ya shanye tass ya sake tsiyaya wani yana sha yana zukar sigari wani irin zuka yayi wa sigarin yana kwantar da kanshi akan kujerar da yake zaune sai daya dauki second biyar sannan ya d'ago ya kalli sigarin hannunsa daya kusan qarewa ya sake kaiwa bakinsa ya zuga da kyau ya d'auki cup din giya ya shanye yana fesar da hayakin sigari ." sosai ya bugu ya fita haiyacinsa can ya mike yana layi ya shiga d'ayan d'akinsa ya d'auko tanga memen hoton zanen princess dinsa ya rungume tsam a qirjinsa yana jin wani tsantsar soyayyarta na ratsashi "ina ...ina sonki princess wai a ina zan ganki ne? " ki fada min inda zangaki mana yana magana yana kallon hoton ya fito falo ya zube akan kujera rungume da zanen a qirjinsa daga nan wani bacci mai nauyi ya daukesa bai sake sanin halin da yake ciki ba ." Hisham yana zaune yana faman kiran layin nuzla mahaifiyarsa hajiya zulfa'u ta amshe wayar hannunsa tana dubansa "zaka kashe kanka ne akan yarinyar data gudu saboda bata sonka ko me ?"haba mumy ko nuzla ta gudu dan bata sona still akwai yan'uwantaka a tsakaninmu" ban son iskanci ba yanuwantaka ba kune ma kashin awaki qarewar yan'uwanta duk yan'uwantakan dake tsakaninku ya kai ta nida mahaifinta ? "karka manta nida mahaifinta uwarmu daya uban daya dan haka wallahi Kayi maza ka cireta aranka ai dana san gantalliyar yarinyar nan bata sonka bazan kashe kaina akanta ba "mumy ki barni naji da damuwa dake damuna please "damuwa ai ta qare kamar yadda aka saka ranar daurin aurenka a gobe tabbas a gobe zaa daurashi "Yauwa mumy har kin sa naji dadi bari na tashi na fita nemanta ko allah zai sa na ganta ." Wani dogon tsaki taja tana dubansa "hisham ka natsu da kyau zaa daura aureka ne amman da wata ba nuzla ba kuma acikin family din nan kamar yadda muka yanke hukunci "what mumy ? haka nake nufi dan allah mumy karki min haka wallahi ni nuzla kawai nike so bazan iya rayuwa da wata ba ,dan allah kar abinda tayi yasa ki yanke wannan hukunci akwai kuruciya a tattare da nuzla wallahi bata da wayon kanta ." " min shiru a nan kuma karka sake min maganar wata nuzla idan ba haka zaka hadu da mummunar baci raina da baka ta'ba gani bata da wayon kanta tasan ta gudu ta bar gida "? tana gama fadar hk ta tashi zata bar falon ya riko hannunta cikin nashi duk ilahirin jikinsa babu inda baya rawa hatta hannunsa dake rike da hannun mahaifiyarsa kirrrma yake yana sake damke hannunta da kyau "ki tausaya min ,ni zaki duba mumy da halin da zan shiga nuzla wata abace mai daraja acikin rayuwata karki maye min gurbinta da wata cike da jin haushi ta fixge hannunta "for the last time karka sake min maganarta sha sha kawai da bai son ciwon kansa ba yarinya ta gudu ana gobe daurin aurenku amman ka tsaya kana fad'a min tana da daraja acikin rayuwarka tunda ta gujeka na tsaneta Ka shirya karka manta karfe hud'u daidai zaa tafi diner "what? ai kasan da zuwa wajen diner dan hk karka bata lokaci tana gama fadar haka ta bar dakin kai tsaye wani haddaden office din gyaran jiki ta nufa ." Nan da nan ya kira salim cikin tsananin tashin hankali bayan sun gaisa ya fad'a masa halin da yake ciki salim din ma kwantar masa da hankali ya dinga yi" kayi hakuri da hukuncinsu hisham ya rude ya rasa abinda Ke masa dadi amman me yasa zaa min haka bayan an bada cigiyarta a kafafen sadarwa to dawa zaa hadani auren "?shiru salim yayi na second goma sannna yace "nana hauwa'u " "Wata irin zabura hisham yayi yana cewa "what !? wace nana hauwa kenna ?ya fad'a a rude idanunshi suna qara canza kala tsabar tashin hankalin da yake ciki ganin irin rudewar da yayi salim yace "ka natsu ka sausautawa kanka, haka rayuwa take hisham kullum tana zuwa da sauyi sauyi bisa izinin allah wanda bawa bai isa ya canzawa kansa qaddararsa ba hisham kayi hakuri nana hauwa dai da kasani kanwa ga ATA ." "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ya shiga furtawa yana maimaitawa rike da waya salim ya dade yana rarrashinsa da yi masa nasiha yanzu dan rashin Imani mai yasa zaa bani nana hauwa'u?me zanyi daita ya qarasa maganar ya hadiye wani abu daya tsaya masa a makoshi "ka taimaka hisham karka kunyata iyayenmu karka manta mutane bilaadadin ne zasu halarci dauren auren nan kuma kowa ya rigada yasan dauri aure biyu zaayi ita kanta nana hauwa'u dan kar kimar gidana ta zube yasa ta amince "shiru yayi kawai ya sauke wayar a kunnensa yana kallon saman dakin ." Yana cikin wannan halin dad dinsa ya shigo da sauri ya kalli mahaifinsa cike da rauni ya mike alokacin da dad dinsa ya zauna kusa dashi hisham ya riko hannunsa yana cewa "abba kaji mumy wai zaa daura aurena da nana hauwa'u dan allah abba kada ka bari a daura auren nan ya qarashe maganr cikin tashin hankali da bacin rai ,cikin zuba masa ido abban shi yace "me yasa zaa bari ?kanshi ya shiga girgiza masa tare da hade hannunwansa waje daya da nashi yace "saboda banasota a bawa wani ita amman banda ni." hisham gsky auren nan fa kamar an daura shi an gama babu wani mahalukin daya isa ya hana wannan daurin auren gara ma ka kwantar da hankalinka tunda ka jurewa auren wacce bata sonka ai sai ka jurewa wacce zata taimakawa rayuwarka sannan wacce zata cire iyayenka cikin shiga kunya "pls abba "kai babu fashi dole sai ka aureta cikin jin haushi ya mike ya shige d'aki ya rufo kofar da karfi ." Hajiya salema ta zube a kasa tana cigaba da hawaye a gaban baba babba dake zaune yana qara karanta wasikar da nuzla ta ajiye musu sannan ya d'ago ya kallesu gbdy "kar ma sake ganin kowanne acikinku ya shiga damuwa akan nuzla tunda ta zabi barin gida tô ina ganin ta ciremu daga cikin mutane masu mahimanci ne arayuwarta dan haka muma yana da kyau muyi saurin cireta daga zuciyarmu a firgice hjy salema ta dago ta kallesa tace "amman alhj kana gani wannnar maganar daka fada babu wani gyara acikinta taya zamu haifi yarinya da cikinmu ace kuma mu manta da ita "?kafin ta qarasa mgnr har baba babba ya mike ya shige d'akinsa dan yaji bakinciki abinda tayi acikin mutane ."hjy salema fashewa tai da kuka suma ya'yanta mata suka fashe da kuka zukatansu nayi musu zafi kamar zata fito." Mmn sudaisi 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 29 Ahankali yaya Ibraheem ya shigo parlour'n hankalinsa yayi matukar tashi sakamakon yanayin daya ga mahaifiyarsa da yan'uwansa ciki ,hajiya salema tana kuka aunty amina da aunty zainab suna tayata kuka tamkar ransu zai fita ,sai daya numfasa sannan ya fara magana a natse "amina ,zainab bana son wannan kukan ,idan kuna kuka ya kuke son hajiya tayi ? kune fa ya kamata ku dinga bata kwarin gwiwa da rarrashi amman sai ku tasata gaba da kuka ". "Sam yaya baka ta'ba duba damuwarmu ."koda wani lokaci laifinmu kake kallo idan bamu taya mahaifiyarmu kukan ahalin da take ciki ba me zamuyi ?" Inji cewar amina "shikenan mun rasa nuzla shi kuma hisham an bashi wata amadadinta yarinyar nan fa bata son shi aka takura mata gashi ta gudu an barmu da matsalarmu nasan ko mutuwa tayi basu da asara "zainab ta qarasa mgnr tana zubar da hawaye." Zainab tasa gefen mayafinta ta goge hawayenta kana ta cigaba da magana "kai ma yaya kasan ba'a kyauta mana ba kuma koda wani lokaci baba abayansu yake baka san abinda hajiyarmu take ji acikin zuciyaarta ba , wallahi matsawar baa ga nuzla a rayuwarmu a haka zata qare ,tabbas raywarmu zata qare cikin damuwa amman wallahi kowa sai ya d'and'ani kud'arsa dan wallahi i bazamu yarda ba wannan d'aurin auren bazaa d'aurashi ba sai an nemo mana nuzla zumunci ya dade bai lalace ba kowa yayi ta kansa kawai .." "Kada kuyi haka amina gara mu mika komai zuwa ga allah "yaya Ibrahim ya fad'a yana kamo hannuwansu ya zaunar dasu akan kujera suka zauna suna zubar da ruwan hawaye ,ya kamo hajiya salema itama ya zaunar daita yana dubansu ,kallo daya yayi masu ya gano cewar gabadayansu basa cikin haiyacinsu "sam sam kalmanku basu min dadi ba kuma kun bani mamaki dan banyi tsamanin wadan nan kalaman zasu iya fitowa daga bakunanku ba ,kun kuwa san yadda naji da kuka fadi lalacewar zumunci ? dan allah ku dawo hankalinku sam baba bazai ji dadin duk wani abu da zaku kunno kai dashi cikin ahlinsa ba ." Ya maida hankalinsa sosai ga hajiya salem yace "hajiya Kiyi hakuri ki barwa allah komai ita rayuwar dan adam cike take da qudirin ubangaji kala kala ,dukkan rayuwa rubutacce alamari ne daga Allah duk wani d'an adam ya kamata yasan wannan ,haka Allah ya qaddaro nuzlah ba matar hisham bace duk yadda yake sonta yake muradin aurenta bazai aureta ba wata zai aura ,haka zalika itama nuzla ba abokin rayuwarta bane muyi fatan allah yasa hakan ya zama alkhairi agaresu ,ita kuma nana hauwa'u kuyi mata fatan nasara a rayuwar aurenta ita kuma nuzla allah ya karkato mana da hankalinta ta dawo gida." hawaye ne ya gangaro daga cikin idanun aunty zainab da aunty amina bakinsu ya kasa furta komai sai kuka ita ma hajiya salema ta qara sautin kukanta sosai ,babu abinda bakinta ke furtawa sai ku nemo min yarinyata sosai jikinta ya dauki zafi rarrashinta kawai suke amman taki yin shiru bakinta ya cigaba da furta ku nemo min yarinyata "hjy ki barwa allah komai sannan ki kwantar da hankalinki ayi komai dake in sha allahu ana gama bikin nan zaa cigaba da neman nuzla ." sanyayyen ajiyar zuciya ta sauke ga kuma hawaye na gangarowa akan kuncinta jin bai biyewa mahaifinsa da yace kowa ya cireta arai ba muryar cike da sautin kuka tace "Allah yayi maka albarka babu abinda yake damuna kamar rashin nuzla yau da diyata tana tare dani aka samu wannnan sauyin bazan ji 'bacin rai haka ba ,dan Allah ka nemo min nuzla zuciyata na cike da kewarta ,nayi nadamar goya masu baya alokacin da zaa hada auren nan ,banci na amince da yanzu yarinyata na kusa dani cikin kwanciyar hankali wallahi nayi nadama ku nemo min nuzla dan bazan iya jurar rashinta ba." yaya Ibraheem ya dafe goshinsa yana jin zafin zubar hawayen mahaifiyarsa tana matukar bashi tausayi ya zai yi ya nemo nuzla ta ina zai fara ?sautin qarar wayarsa ce tasa ya sauke hannunsa ya ciro ya duba a gaban aljihunsa ya duba a hankali ya mike tsaye yana cewa "ku samu wani abu ku bawa hajiya taci sannan ku hada mata da maganin zazzabi tasha jikinta yayi zafi daywa zan dan fita amman bazan dade ba dan Allah ku cire damuwa da kudirinku ayi komai daku sannna kuyi qoqarin kwantarwa hajiya da hankali ".ya qarasa fada tare da ficewa daga parlour'n ya bar hjy salema da ya'yanta." Cikin mintunan da basu wuce talatin ba sai ga hjy zulfa'u ta dawo masaukinta da meera mai lalle da make up ,ta shigo falon bakinta dauke da sallama tana cewa "my dear ina son yake ?"bai dade da shiga daki ba, ban san me ke damun hisham ba kinga yadda ya d'aga hankalinsa ya dinga hadani da allah akan lallai sai an fasa auren nan dan rashin sanin ciwon kai irin nashi ." "rabu dashi zan sauke masa duk wani abinda yake kanshi tana gama fad'ar haka kai tsaye dakin da yake ta nufa ta tura kofar ahankali ta shiga yana kwance idanusnhi a runtse cikin tsnanin tashin hankali ."yaji motsin shigowarta amman yaki bude idanunshi har sai data qarasa shigowa sosai ta tsaya akanshi tana kiran sunansa "hisham !da kyar ya bud'e idanushi ya zuba mata cikin tsananin damuwa "tashi muje kayi min rakiya" "zuwa ina kenan mumy ?kai dai ka tashi muje ta miko masa tafin hannunta ya mike da kyar yana cewa "dan girman allah mumy kiyi hakuri ki bar maganar auren nan nuzla ce rayuwata bazan iya rayuwa babu ita ba wannan yarinyar da zaa hadani aure daita bazata ji dadin rayuwa dani ba saboda ba ita zuciyata take so ba ,"bana son maganar banza hisham yarinyar data rufa min asiri kake fada min haka akanta idan baka kiyayeni ba zan mugun saba maka akanta amman mumy kina ganin ya kamata ki tsani nuzla irin ha .."? "Kada kace komai dan banason jin komai daga bakinka matsawar tozarci né ga nana hauwa'u a halin yanzu bana ji bana gani ita kawai nake só itace rayuwata yanzu tunda zata rayu da kai kuma zan iya yin komai akanta dan ita zan iya sadaukar da farincikina hisham tashi muje ta sake miko masa tafin hannunta zuciyarsa cike da tashin hankalin ya sanya hannunsa cikin nata ." suka fito zuwa parlour'n zasu wuce dady yana waya tace " my dear sai mun dawo ya d'aga masu hannu suka fito suka shiga gidan baya suka zauna yayinda meera mai lallae ke zaune agida gaba gama zamansu keda wuya direba yaja motar suka fice ahankali motar ke tafiya hajiya zulfa'u na cewa "hisham ka kular min da nana hauwa'u kada ka wulakanta min 'ya dan bazan lamuncewa hakan ba ,daidai satin zuciyarsa ya dafe dan zafin maganarta yake ji "ples mumy ki bar maganr haka zuciya zata tarwatse numfashi ta sauke da karfi bata qara cewa komai ba ." kai tsaye abdullahi estate suka nufa bayan sun firfito daga cikin motar suka shiga gidan hajiya zulai falon gidan cike da mutane ,ana ganinta falon ya hargitse da hayaniya nan aka fara gaishe gaishe ana ga uwar ango da amarya shi kam hisham kanshi na kasa duk yadda abokan wasansa ke jansa bai dago kashi ya kalli kowa ba kusan ya matsu mumynsa ta sallamesa ya kama gabansa ,sai da hjy zulfa'u ta gama taja hanunsa suka nufi dakin nana hauwa'u inda ta iskesu zaune cirko cirko cikin zullumi . suna ganinsu suka tattara hankalinsu ga mumy da hisham , ahankali hisham ya daura idanunshi akan nana hauwa'u sai dai kallo daya yayi mata ya dauke kwayar idanunshi akanta ita kam ta bala'i kafeshi da idanunta tana son gano yayinsa amman kallo dayan data ga yayi mata ya d'aga mata hankali wanda yasa gabanta ya dinga dukan tara tara ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta muryata a matukar sanyaye tace "mumy barka da dawo ."yauwa diyar albarka sannuki da qoqari kinji allah yayi miki alabarka ,allah ya jikan mahaifinki "Ameen!" nana hauwa'u ta amsa tana cigaba da wasa da yatsun hannunta yayinda gabanta Ke cigaba da faduwa." " meera ga guri ki zauna ki fara aikinki ga wacce zakiyiwa lalle ."ta nuna mata nana hauwa'u "lalle zaayi mata to shi meye na zuwa dashi ?ya d'ago a natse ya kalli hajiya zulfa'u fuskarsa da alamun tambaya , shiru tayi masa tai masa nuni da kujerar dake fuskantar nana hauwa'u kin zama yayi ya cigaba da tsayuwa ,meera ta fara hada lallen da zatayi wa nana hauwa'u "ka zauna mana ka wani tsayawa mutane aka "ni mumy abinda ban fahimta ba me zanyi idan na zauna ?". "ina son ayi mata lallen agabanka "what !? ya fad'a a hargitse ta gyada masa kai cike da mamaki yake kallonta nana hauwa ta sauke numfashi ta d'ago ta d'an saci kallonsa "mumy ki fahimceni ko ina son auren nan bazan zauna acikin mata ba bare bana só shiru mumy tayi zuciyar na rawa kafin ahankali ta motsa labbanta tace "ni zaka fadawa haka hisham ?"Shikenan na gode amman ka zauna kamar yadda na buqata ."gsky mumy sai dai Kiyi hakuri dan wallahi bazan iya zama ba "yana gama fadar haka ya juya cikin tsnanin damuwa ya nufi kofar fita "hisham! hisham !! hajiya zulfa'u ta dinga kiran sunansa amman ina tunda ya nufi kofar fita bai juyo ba, ta gyada kai kawai tare da samun waje ta zauna zuciyarta na mata wani irin zafi ." "Mumy ! Nana hauwa'u ta kira sunanta muryarta a sanyaye ta d'ago tare da zuba mata idanunta "dan allah karki damu ki kwantar da hankali karki yi fushi dashi dole kowaye ya tsinci kanshi cikin halin da yaya hisham ya tsinci kanshi ya shiga damuwa ,a yanzu rarrashi yafi buqata ba takurawa ba "ta qarasa maganar tana mai sunkuyar da kanta tare da danne kukanta "na gode sosai diyar albarka in sha allahu muddin ina raye sai kinyi farinciki agidan hisham "murmushi nana hauwa'u ta sakar mata ba dan tana cikin farinciki yin murmushi ba sai dan ta kwantar da hankalin mumy ." Ahankali meera ta fara zana mata jan lalle yayinda mumy Ke jan nana hauwa'u ajiki ta hanyar yi mata hira su kansu diyana da humaira har ma da maryam mumy ta burgesu matuqa ,ana zanawa nana hauwa'u lallen mumy na yabawa "Woww gsky lallen nan yayi matukar kyau meera ai kudin lallenki yafi karfin yadda kika caza dole ma na qara miki kudi ."gabadayansu sukai dariya meera tace "na gode hajiya koda meera ta gama mata bata wuce ba dan zata tsaya tayi mata make up din zuwa wajen dinner kowacce ta kama gabanta domin shirya kanta aunty shahida tazo ta d'auki maryam ta wuce daita domin shiryata ." karfe uku daidai aka fara tsara wa nana hauwa'u kwaliya sosai tayi kyau cikin doguwar rigar less red wanda mumy ce ta kawo mata daman kuma ta tanada ne dan nuzla komai red tayi amfani dashi kasancewarta fara sol tayi kyau sosai abun sai wanda ya gani shima a 'bangaren hisham red din yadi yasa ba qarami had'uwa yayi ba nana hauwa'u gani take ba ya ita amma tana ganin hisham ta raina kanta saboda wani irin kyau da yayi mata ya zarta kyau sosai ." Tsura masa ido tayi tana kallonsa tsaye shi kuwa ko kallon inda take bai yi ba illa ma cigaba da amsa wayar da'aka kirasa yayi ,wata qawar mumy ce ta riko hannun nana hauwa'u ta kawota kusa da yaya hisham suka jero suka shiga mota zuwa hall koda suka shiga mutane suna ta d'aukansu pic jikin nana hauwa'u yayi sanyi sakamakon kalon baza da yaya hisham yake mata ji tayi kamar ta hana daukar hoton amamn bata damar aikata haka duk tajita a takure kamar ta koma gida ." Bangaren maryam kuwa an tsara mata kwaliya ta ban mamaki tayi kyau iya kyau cikin wani hadadden lace farin anyi mata dinki weeding gwan duk wanda ya daura kwayar idanunshi akanta sai dai yace Masha allah dan kyau kam tayi shi sai daukarta a hoto ake kafin angonta ya bayyana yayinda ango na can a buge mb, salim ,yasir suna tsaye akanshi sun zuba masa idanunsu cikin tsnanin tashin hankali dan sun razana da ganin halin da yake ciki hannunsa ya kai daidai saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take bugawa da karfi yayinda gefensa hoton zanen princess dinsa ne yana kallonta yana zukar sigari." Ahankali ya dauke gajiyayyun idanunshi da suka canza kala saboda bugawar da yayi akanta ya dan waresu akansu yaga still shi suke kallo kwalban whisky's guda uku agabansa inda yake dagasu daya bayan daya yana sha yana zukar sigari cikin tashin hankali ,idanunshi sun qara rikidewa sunyi ja sosai ,ganin bashi da niyyar daina shan giyar yasa a matukar zuciye mb ya ture cup din daga gabansa yace "why ATA ?" akanka aka fara irin wannna auren ?wallahi ka sani shan wannan abu bazai amfaneka da komai ba don't forget mami yau tana cikin farinciki kuma ta tara jamaa me kake tunani zataji idan taganka cikin wannan halin ?kana son heart attack ya kamata ne ?." 'Dago jajayen idanunshi yayi ya kalli mb bai ce masa komai ba ya kunna sigari ya kai bakinsa yana zuka yana kallon wani bangaren dabam "wannan wani irin kaskanci ne haka ATA kalli fa ,kalli irin rayuwar da ka jefa kanka daga shan sigari ka dawo giya ni har yaushe ka fara shan giya ?"ban sani ba kuma babu ruwanka da rayuwata haka ya kamata nayi ko na zama wannan ciwona ne ni kad'ai babu ruwan kowa dani ." "why ATA? saboda wata soyayyar banza zaka kashe kanka akan wata yarinyar banza da ba gaskiya bace kana qoqarin 'bata rayuwarka, ka manta da wannan yarinyar ka kama wacce aka baka ka d'aura rayuwarka daita "salim !"ya kira sunansaa tsawace shiru salim yayi yana dubansa ya dauki kwalban giya ya kai bakinsa sai daya shanye tass sannan ya fuskancesu "akan mafarkina nake yi wannan abu ko ba akanta bane ni dai abinda nasani soyayyar da nake mata gaske ce kuma har abada domin Itace duniyata tana cikin nan a duk inda take nasan itama tana jin yadda nike ji acikin zuciyata." "dan allah princess ki tausaya min bazan iya rayuwa babu Ke ba , idan babu Ke bazan iya cigaba da rayuwa ba ,ya mike da kyar yana layi ya dauki kwalbar giya ya fasa sannan yace "an hadani aure da wata guntuwar yarinya ita kuma nana hauwa'u an hadata da heart attack ,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace idan hisham ya cutar da nana hauwa'u zan yanke komai dake tsakanina dashi wallahi wallahi I promise to make his life in to hell he will end his life in prison a firgice suke kallonsa zukatansu na duka tara tara idan kuma ban kaishi prison ba zan kashesa matsawar ya cutar min da yaruwata ." ya nufi kofar bedroom dinsa sauran kadan ya fadi mb yayi saurin kai hannu zai tarosa ya buge masa hannu yana cewa "don't don't touch me just leave my room ya fad'a yana shigewa dakinsa yana shiga ya kwanta flat akan bed tamkar wani matacce ." Dakin suka shigo gbdy suka rufa akanshi kamr zasuyi hauka mb ya hauro har saman gadon ya dagosa ya kwantar dashi ajikinsa ya kai hannu ya kamo fuskarsa yana dan marin kuncinsa tare da kiran sunansa "ATA ka tashi please karka zama haka yayi maganr yana kuka me yasa zaka mana haka ?" salim da Yasir ma sunansa suke kira "wannan fa ya rigada ya bugu babu inda zai iya zuwa kamata yayi a fadawa mami "wa zai iya wannan karfin halin ?wa zai iya tun karar mami da wannan maganar ?bazan so mami ta gansa cikin wannna halin ba inji cewar yasir "to meye mafuta yanzu me zaa bashi ya dawo daidai ?abu daya ne zaa iya bashi shine kokin shi kuma yana fara shanta matsala ne arayuwarsa gara kawai duk mu kwashe duk wani kayan maye dake dakin mu barsa yayi bacci idan ya farfado zai dawo daidai ." Ahankali ya motsa lip's dinsa "I can't marry this stupid girl I can't marry her coz she's not my type shine maganar da yake fitowa daga bakinsa "yanzu me zamu cewa mami ?a gaya mata gsky kawai yasir je kazo da mami ."Okay ya fad'a yana mikewa tsaye ya nufi kofar fita tare da mami suka dawo ai tana ganinsa ta daura duka hannuwanta bisa kanta ta fashe da wani irin kuka tana kallonsa tana furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun tana qoqarin zubewa kasa ganin gaba d'aya ATA baya cikin haiyacinsa ,dan tuni bacci yayi awon gaba dashi jikinsu a sanyaye ganin mami na neman zaucewa suka tarota suna cewa "kiyi hakuri mami Kiyi masa addaua " yanzu abinda adamcy zai min kenan ana gabe daurin auresa?" yanzu ka kyauta min adamcy ? "gsky bai kyauta ba mami amman Kiyi hakuri girgiza kai mami tayi sannan ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta mike da kyar ta fice daga dakin ."da kyar take jan kafafunta ta sauko ta tashiga 'daki tana kuka Allah ya taimaketa babu kowa acikin dakin domin mutane duk sun wuce zuwa hall ta kulle dakinta kuka mami take sosai ta kira aunty shahida kiran na shiga amma bata 'dauka ba dan haka ta kira aunty khadija ita kuma wayarta a kashe mami tarasa abinda Ke mata dadi sai da zaa fito da maryam aunty shahida ta lalubo wayarta nan taga missed call din mami yafi goma cike da jin tashin hankali ta soma neman layinta mami ta dauka cikin yanayi na damuwa tace "shahida !". "Naam mami ya naji muryarki haka wani abu na damunki ne ?babu komai shahida ku wuce da maryam hall yau ma dai kamar jiya ita kadai zata zauna "shiru aunty shahida tayi kafin daga baya tace "mami ina adam din yake ?hakan nan mami ta kasa fad'a mata halin da yake ciki tace "yana kwance babu yadda yake bashi da lafiya ina maryam din take "gata nan a kusa dani "bani ita aunty shahida ta mika mata waya ,ta karba tana jin faduwar gaba mai tsanani". "hello mami !" maryam ykk ? lafiya lau mami ya naji muryarki kamar kinyi kuka ? babu komai maryam fatan kinci abinci ? ta gyada mata kai tana cewa "Eh naci numfashi mami ta sauke "kina jina mrym ? tace "eh mami ina jinki "nasan zaki fahimceni zaa wuce dake hall yanzu yau ma kamar jiya Ke kadai zaki kasance bana son kisa damuwa acikin ranki kinji ki dinga tuna kina dani "to mami !" ta fad'a hawaye na cika idanunta aunty shahida ta girgiza mata kai alamun karta yi kuka jiki a sanyaye ta mikewa aunty shahida wayr sukai sallama da mami ." Shiru aunty shahida tayi tana tunanin yadda yau ma maryam zata zauna ita kadai batare da ango ba ,bata ki maganar mami ba domin tasan rashin mafuta yasa ta fadi hakan amman ita dole ta nemo mafuta dan baza bari maryam ta zauna ita kadai ba ko hisham daya tsinci kanshi da auren nana hauwa'u acikin kwana daya ya yarda ya amince har ma sun isa hall bare adamcy da aka dauki sama da watanni ana abu daya ,sosai kwakwaluwarta ta shiga tunanin abunyi zuciyarta ta bata shawarar ta nemi salim ya maye gurbin ango tunda daman jiya babu wanda ya gansa ." da sauri zuciyarta ta amince da haka nan da nan ta shiga neman layin salim kira daya tayi masa ya dauka adaidai lokacin da suke shirin shiga mota dan zuwa hall "yaakayi my aunty ?kana ina salim ?gamu muna shirin zuwa hall ,yauwa salim dan allah kazo ka maye gurbin adamcy babu dadi maryam taje wajen diner ita kadai kafadansa ya daga alamun babu damuwa yace "okay shikenan an gama aunty ya yi discounneting din kiran yana duban sauran abokan tafiyarsa tare da yi masu bayani ,gsky aunty ta kawo shawara wallahi maryam na bani tausayi dan allah ya hadata da wani irin mutun mai shegen taurin kai, bari mu jira a fito daita sai mu mubi bayan motar ku, suna tsaye aka fito da maryam salim ya bude mata bayan mota ta shiga ta zauna shima ya shiga ya zauna aka rufe murfin mota yayinda mb da sauran abokan ango suka shiga motocinsu suka bar gida ." Tamkar ango da amaryarsa salim yayi active suka jera har zuwa mazaunin ango da amarya aunty abida ta kallesu ta kwashe da dariya tana kallon mahaifiyarta ,"mumy kinga abinda nagani kuwa ?na gani abida jiya bai zo ba ga yau ma ,ai halin adam sai ahankali ,shiyasa nake ganin da wahala ki iya shawo kanshi ya auri sultana"kai mami karki hada sultana da wannan yarinya sultana ta kereta a komai duk yadda zamuyi ta shiga gidansa sãi nayi idan allah ma ya taimakemu sai ya sota kinga komai zai zo mana da sauki ato allah yasa ,wannan lamari yayiwa abida dadi dan haka ta dinga jinta cikin tsananin farinciki ." Hall ya cika makil da jama'a ta bangare dabam dabam maryam tayi shiru tana rike da jaka yayinda masu hoto da vedio suka dinga daukarsu hoto har sanda aka kira hisham da amaryarsa zuwa fili ahankali ya mike atare suke daga kafafunsu suka tsaya a fili tamkar wasu gumaka hajiya zulfa'u ta shigo da 'kawayenta da ankonsu iri daya ta dinga likawa nana hauwa'u 1k amma ko kalon hisham bata yi ba MC ne yayi magana wai ya yaga hajiya iya amarya takewa liki ." murmushi tayi tace mishi "ai itace tafi cancata yar albarka yar gidan arziki gaba da baya irin albarka kaga dole ita ta dace da naiwa liki" aikuwa gurin ya 'dau shewa da tafi mutane wasu suce " wannan haka yake hajiyarmu Allah ya 'kara arziki hisham kuwa ya cika makil dan ganinsa tozarci ne abinda mumynsa tayi masa suka koma suka zauna aka kira maryam da angon bugi,maryam dake zaune wasu irin hawaye masu ciwo suka zubo mata ta yunkura ta tashi tsaye salim ya rike hannunta cikin nashi saurin kallonsa tayi sam bai damu ba ya kauda kanshi kawai ya soma tafiya daita ba dan ta soba ta dinga daga kafafuwanta ." da zata taka step ya tsaya ta sauko ahankali yana daga mata rigarta d'an kar ya hardeta abun ya burge mutane mc kuwa ya dauka angon gaske ne nan ya fara zuba "kai wannan ango yana ji da matarsa yana son matarsa see love ai nan hankalin mutane ya sake karkata kansu aunty abida tace "dama shi ya aureta muka huta dan sunfi dacewa dashi sultana kuma da adamcy "ke dai kina qaunar sultana da wannan mai shegen taurin kan tsiya "duk zai daina ne bari dai ya shigo hannun mace ." sosai salim ya kwashi rawa tare da maryam lokacin da aunty abida ta tashi taje liki byn tai liki ta kai bakinta daidai kunne maryam "karshe mai naci kenan da kin nuna baki raayi kamar yadda ATA yayi da yau baki wayi gari da aron ango ba wannan kawai ya isheki misalin irin halin bala'i da zaki shiga a gidansa "har aka gama taron aka watse aunty abida tana mata habaici wanda bata san dalilinta nayi mata hakan ba salim ne ya maida ita gida kai tsaye ta fito ko kallon inda yake batayi ba tashige gida ta rabu dashi dan taji haushin hannunta daya rike shima bai damuba yai tafiyarshi gida mrym tana shiga dakinsu kuka ta saka ranar yadda maryam taga rana haka taga dare ga kuka datasha kamar ranta zai fita." Karfe daya daidai ata ya farka daga baccinsa ya mike da kyar ya shiga bathroom yayi wanka ya dauro alwala ya fito ya sanya vest da boxer sannan ya daura jallabiya mai garen hannu akai ya qarasa inda daddumarsa yake ya tada sallah bayan ya idar da salolinsa ya zauna yana tunanin awannin daya kwasa yana bacci , can ya mike ya fito zuwa falonsa ya bude fridge bai ga whisky dinsa ba ya kalli inda ya ajiye kwalayen sigari ko karan sigari daya bai samu ba ya maida murfin fridge din ya rufe da karfi yana jan tsaki ." ya koma ya zauna ya zubawa zanen princess dinsa idanu yana kallonta yana zaune mami ta turo kofar dakin ta shigo idanunta ya sauka akanshi idanunshi sunyi wani irin girma ta zauna a kusa dashi bai yi magana ba har sanda ta soma mgn "adamcynah ka tashi ?"eh na tashi! ya fad'a kawai yana duban zanensa yanayin yadda ya amsa kamar yana jin haushinta." ta numfasa kana tace "me yasa baka tashi lalata rayuwarka ba sai alokacin bikinka ?me ya kaika shan giya adamcy ?yanzu ka kyauta min kenan ?ka kunyatani acikin mutane kowa sai tmbyrka yake ka kuwa san adadin karyar da nayiwa mutane ? "ni fa bikin nan bashi da wani mahimanci agareni dan Allah sweetheart ki daina min magana akanshi sake daga min hankali yake "jin haka yasa ta canza magana "me zaa kawo maka? "shiru yayi yaki cewa komai dan idan ya bude bakinsa ba abinda zai ce a kawo masa sai giya da sigari su kawai yake buqata "bari naje na kawo maka abinci ta fad'a tana mikewa ta shafa kanshi sannan tayi gaba ." Tana fita Ya kira yaronsa yace ya siyo masa giya amman wacce tafi duk wanda yake sha karfi da sigari yana ajiye wayar mami ta dawo dakin ta ajiye masa plet din abinci agabansa kaci yanzu da zafinsa ta wuce bai ci abincin ba har sanda yaronsa ya kirasa ya dauka yana cewa "ka shigo mana " mami tana falo okay ina zuwa ya mike tsaye ya sauko lokacin daya sauko mami ta tashi ta shige dakinta ya fita "ya ka dade ?yallabai go slow yafi yawa a shagon siyar da giya fiyye da shagunan siyar da abinci bare adaidai wannan lokacin "okay kaje kawai ya karbi ledar hannunsa kwalba biyar ne aciki sai kwalayen sigari ya dawo dakinsa ya ciro daya ya balle bai tsaya sirkawa ba ya kafa abakinsa bai sauke ba sai daya shanye tass sannan ya daura da sigari haka yayita sha har karfe biyu da rabi ya koma bedroom dinsa wanda alokacin ya shanye kwalba hudu yana kan ta biyar ." ***** Washegari sunday ya kama daurin aure hisham bai tashi ba mumy ta dinga kiransa a waya gajiya yayi da kiranta ya dauka ya mike zaune yaji dalilin takura masa da take yi, yana dauka ta rufeshi da bala'i "wallahi hisham ka kiyayi fushina idan ba so kake nayi maka baki ba wallahi ka natsu ka shiga hankalinka ka bari ayi komai a gama lafiya "yanzu mumy me nayi ?daurin aure ne a daura mana ai ba lalle sai naje ba "okay ni zaka fadawa haka ?" to dan girman allah karka zo "da taimakon salim hisham ya shirya tsaf cikin wata dakakkiyar shadda gezner fara sol koda suka fito mutane sun cika acikin haraban estate din ." Ahankali mb da sauran abokansu suka shigo falon ATA kowannensu sanye da farin yadi mai shegen tsada ,basu ganshi ba dan haka mb ya tura kofar bedroom dinsa anan ya gansa kwance a kasa shame shame tamkar matace ,da wani irin sauri ya qarasa inda yake kwance ya durkusa a gabansa yana cewa" Kai adam ka tashi mana lokacin zuwa daurin aure yayi fa "ya fad'a yana kallon kofar shigowa dakin "kai yasir kuzo ku ganshi ya qara shan giya ya bugu fiyye da jiya ya sake kallon fuskar ATA yana shafa fuskarsa ," kai wai meye haka ne ?subuhallah ya bugu kuma? inji cewar salim da yasir da suka shigo atare cikin tsananin tashin hankali." " kamo shi mb yayi yana cewa "ku taimaka min mu daga shi gbdy suka kamo shi zuwa kan bed dinsa suka kwantar dashi suka dinga jijiga shi" ka tashi dan girman allah lokacin daurin aurenka yayi ,amman shiru kake jin ATA dan ko motsi baya yi numfashi ma da kyar yake fitarwa yasir ya kai hannu ya bude idanunshi yana kiran sunansa," kai ku duba fa kugani kwayar idanunshi sun dauke inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kai abokina ka bude idanunka muna tare da kai dan allah karka min haka bana son na rasaka ."mb ya fad'a cikin tsananin tashin hankali mara iyaka . "kana jina abokina ka bude idanunka yana magana yana jijiga shi amman har lokacin ATA bai motsa ba bai ma san a halin da yake ciki ba duk yadda sukayi su tashesa amman abun yaki cikin tashin hankali mb yake kallonsa gabansa na faduwa acikin kwana biyu kacal da soma shirye shiryen biki ya zare ya fita haiyacinsa bai ta'ba tsamanin zai shiga wannan halin ba da shi karon kashi ya shawarci mami a hakura da auren kawai kowa ya huta ." sosai mb yaji babu dadi ganin halin da amininsa yake ciki da sauri mb ya nufi kofar fita daga dakin kunnensa manne da waya yana cewa "hello sadiq kana ina ? "dan girman Allah ka ..ka taimaka min ATA nan ya zayyane masa komai cikin tashin hankali eh kazo da allurar please ya katse kiran ya koma cikin dakin har lokacin kwayar idanunshi bai dawo daidai ba ko dan sambatun nan na bugaggu bai yi ba ." suna tsaye sadiq ya shigo ya fara dubasa "yana da rai numfashinsa ne yayi nisa sakamakon buguwar da yayi amman zan masa allura nan da wasu yan awanni zai dawo daidai ya ciro sirinji daga cikin bakar jakar daya shigo dashi ya hada duk allurar zaiyi masa bayan yayi masa ne suka fito daga cikin dakin dukkaninsu jikinsu a sanyaye inda zuciyar mb Ke bugawa da karfi kamar wasu kurame haka suka sauko babu ango, ganin mami yasa duk suka dan saki fuska dan karta gane akwai abinda yake faruwa sai dai kallo daya tayi masu ta fahimci akwai matsala tun kafin su kai ga fita ta nufi hanyar dakinsa ." Tana shiga dakin yana kwance a buge Kmr jiya ta tsura masa ido bata ko liftawa ga wani tashin hankali data tsinci kanta ciki wanda bata ta'ba jin irinsa ba ,bta ta'ba nadama da danasani ba sai a safiyar yau din nan ,gabadaya jikinta ya dauki rawa kasa dauke idanunta tayi akanshi wadan da tuni sun rikice suna qoqarin zubar da hawaye cikin wani irin salo na yan shaye shaye taji yana kiran sunan "my princess kece rayuwata kece duniyata kinki bayyana min kanki saboda baki sona laifin me nayi miki ?yadda yayi maganar da sunan da yake ta faman kira ba qaramin rudar da mami yayi ba ,da sauri ta fito daga cikin dakin tana goge hawayen nadama da danasani sam sam bata ga laifinsa ko jin haushinsa ba domin itace sila jefa rayuwarsa cikin wannan halin ." mutane masu mahimanci suna zaune acikin massalaci dake cikin estate din abdullahi auren Adam Tariq abdullahi aka fara daurawa tare da maryam abdulra'uf akan sadaki kankani bisa umarnin mami sannan aka daura na hisham Muhammad sani tare da nana hauwa'u tariq abdullahi duk yadda hisham yake son yayi jarumta amman a karshe sai da kwalla ta zubo masa jin an daura aurensa da wata ba da nuzlarsa ba .wani irin bakinciki ne mara misaltuwa ya lullube zuciyar hisham hannunsa salim ya rike cikin cool voice yace "ka sausautawa kanka sannan ka sanya aranka daman can nuzla ba matarka bace ." Ana gama daurin aure maroka suka fara shela acikin mutane hamdala mami tayi alokacin daakce mata an daura auren sai dai zuciyarta bata cikin jin dadi sannan bakinta bai daina ambaton sunan Allah ba maryam kam fadawa tayi jikin aunty khadija tana fashewa da kuka mai karfi "aunty khadija ta soma rarrashinta kukan murna da kukan bakinciki maryam take bakincikinta yaya adam baya sonta na farinciki kuma burinta ya cika ta auri abun qaunarta ."hajiya zulfa'u ta kira salim cewar suzo da hisham bangaren hjy zulai suka shigo a tare da abokan ango hisham ko kallon inda nana hauwa'u take bai yi ba nan masu daukar hoto dake biye dasu suka shiga aikinsu anyi hotuna sosai ." Da misalin karfe biyu na rana mami ta shiga dakin ATA tare da mrym yana kwnace adduoi ta dinga yi tana shafa masa a fuskarsa yayinda maryam ta qaraso ta kafeshi da ido tana kallonsa tana jin wutar sonshi na qaruwa acikin zuciyarta qoqarin mikewa yake nan mami ta kama masa ya tashi ta jingina masa pillow a bayansa kallonsu kawai ya tsaya yi kafin ya rufe idanunshi yana sauke ajiyar zuciya "adamcy nah yau ka zama cikakken mutun ina cikin farinciki an daura aurenka da maryam sannna ina cikin bakinciki irin halin daka jefa kanka ciki ta qarasa mgnr tana kuka ". "meye kuma abun kuka bayan burinki ya cika ?ya fad'a yana goge mata hawaye "kukan murna da bakinciki ne , yau ina cikin farinciki da bakinciki ka taimaki rayuwar mahaifiyarka karka canza daga adamcy data sani ,rayuwa qaddara ce sannan kai muslim ne ka yarda da qaddara kayi farinciki da auren nan ka barwa allah komai "numfashi ya sauke baya jin zai yi wani farinciki da wannna auren maryam kam idanunta na kanshi har sai da taji sautin muryar mami ta doki dodon kunneta "maryam jeki hado masa tea ki kawo masa ta fice daga dakin." Bayan fitarta da kyar mami tasa shi ya tashi ya shiga yayi brush da wanka sabbin kayansa ya saka lokacin da mami ke fesa masa turare maryam ta turo kofar dakin ta shigo mami ta karfi cup din hannunta da kanta ta dinga bashi a baki tana masa nasiha ita kam mrym duk hankalinta na kanshi sai faman kallonsa take shi kanshi mamakin irin kallon da take masa yayi wanda kallo ne mai dauke da tsantsar soyayya acikin lokaci kankani...." Mmn sudais 💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗 *AYSHA A BAGUDO* WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube. Page 30 Ahankali ya d'auke kwayar idanunshi zuwa wani bangaren dabam yana jan tsaki dan bazai iya cigaba da kallonta ba "me yasa sweetheart take masa haka ?tasan baya son ganin yarinyar atare dashi amman ita burinta bai wuce taga sun kasance a waje d'aya ba." "dan Allah adamcy ka cire damuwar nan aranka ka kwantar min da hankali ahalin yanzu babu abinda nake buqata kamar natsuwarka da kwanciyar hankalinka ,duk duniya babu wanda zai so maka kwanciyar hankali da farinciki kamar ni mahaifiyar ka saboda nice nafi kowa sanin ciwonka ." "daga ni har kai da duk wani mai qaunarka babu wanda zai so ka qarasa rayuwarka haka batare da ka ajiye iyali ba , sannan zamanka kai kad'ai illa ne ga rayuwarka, idan wasu sun yarda da kai akan baka aikata komai na sa'bo ,wasu bazasu yarda ba, wasu zasu d'aukeka a matsayin mai neman mata ne duba da irin tarin dukiyar da allah yayi maka ,dan haka kayi hakuri ka rungume wannan rayuwar domin itace qaddararka dan adam bai isa ya canzawa kanshi qaddararsa ba." sosai ya fad'a cikin kogin tunani hankalinsa ya bar duniyar da yake wanda hakan ya bawa maryam damar cigaba da kallonsa son ranta tana jin tmkr ta fad'a jikinsa ta rungumeshi ta rarrashi kayanta ,jin saukar hannun mami jikinsa ya sanyashi dawowa cikin natsuwarsa ya d'ago kanshi ya zuba mata idanunshi dake cike da matsanancin damuwa ." "Ina neman alfarmar a wajenka a karo na biyu " wata irin razana yayi yayinda zuciyarsa ta soma bugawa da karfi kamar zai fasa qirjinsa domin bai san wace irin alfarma zata sake nema a wajensa ba ,bai ce mata komai ba ya cigaba da kallonta da tsumammun idanunshi yana mai allah allah yaji abinda zata fad'a." "na gode maka da alfarmar da kayi min na farko na amincewa auren maryam da kayi alfarmar ta biyu ka taimakeni adamcy kayi min alkwarin bazaka sake kai kwalbar giya bakinka ba bare sigari " tayi maganar Kmr zata zubar da hawaye dan tuni kwayar idanunta sun canza kala ." Wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi ya sauke atare dan bai d'auka abinda zai fito daga bakinta ba kenan, ya d'auka zatayi masa magana ne akan tarewar yarinyar "kayi dan Allah dani amadadin giyar da zaka yita sha kana buguwa gara ka rike addua adamcy ,jikinsa yayi sanyi da jin maganarta ya risinar da kanshi kasa batare daya bude bakinsa ba a ransa yace "wannan rayuwarta ce ,ciwona ne ". ta cigaba da kallonsa shi kuwa bai ce mata uffan ba dan baya son yayi mata aqawarin da bazai cika ba ,bugu da qari baya son a shiga rayuwarsa a barshi da damuwarsa kawai sannan abar shi ya sha giyarsa da sigarinsa son ransa domin a halin da yake ciki su kad'ai ne abinda suke rage masa rad'ad'in damuwarsa ." Kallonsa maryam ta cigaba da yi ko kifta idanunta bata són yi akanshi "kallonsa kad'ai ya isa ya harzikawa mutun brain dinsa ,namijin duniya ne ko daga yanayinsa ,wani murmushin farinciki na samun nasara ya subuce mata "duk Kinsa da aureta gashi dai allah ya bata sa'a a karshe ta zama mallakinsa na har abada, domin tasan muddin mami na numfashi a doron duniya bazata barshi ya wulakantata ba bare akai ga maganar saki atsakaninsu zasu rayu tare har karshen numfashinsu dan haka zata iyawarta da komai ta makallakesa har ma ta zama wani sashin na rayuwarsa ." Duk da ba kulata yake ba bare kallota amman da kyar take iya control din kanta akanshi don kallonsa yana cikin abinda ke sata fita haiyacinta tama rasa a duniyar da take ,a duk lokacin da tayi saa ya kalleta kuwa hakan na matukar sata natsuwa ,ta lumshe idanunta acikin ranta tace "adamcy nah ni kad'ai ,komai naka yayi min ilarka dai baka son rainin da zafin zuciya uwa uba tsanar mutane na babu gaira babu dalili ." Kamar ance ya d'ago kanshi dake risine yaga idanunta akanshi ,a zaunen da yake ransa ya fara 'baci ,zuciyarsa ta dinga tafarfasa sakamakon kallon da take masa na kurrulla irin kallon daya fi tsana arayuwarsa ,numfashi ya sauke ahankali tare da sake kau da kanshi muryarsa a tsarke ya kiran sunan da yake kiran mahaifiyarsa dashi "sweetheart !"ya'akayi adamcy nan? "ta amsa cike da tsananin kulawa "Kece wa yarinyar nan ta bar d'akin nan" a d'an firgice mami tace "wace yarinyar kuma ?" Shiru yayi yana sake 'bata rai mami ta kalli gabadaya parlour'n babu kowa daga ita sai shi da maryam ne acikinsa "kenan dai maryam yake nufi ?"adamcy matarka ce fa ?"oh my god sweetheart ki kalli kiga irin kallon rainin hankalin da take min ." yayi mgnr a d'an tsawa ce mami ta waiga ta kalli maryam wacce tun soma maganarsa tayi saurin d'auke idanunta akanshi ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta ." "Ba nasara akayi akaina ba ni naga damar amincewa aurenta dan naga sai wani kallon gani gani take min ,wallahi tun da wuri ki ja mata kunne kar taga an d'aura min ita ta nemi ta dinga min kallon iskanci idan ma tana tunanin wani abu acikin ranta wallahi tayi maza ta cire dan hakan ba abu ne mai sauki ba ." "Da me zan ji ?aurenta da aka min dole ,ko da kallon iskanci da take min ? amman barni da zazzafar qaddarar data rufta min shekaru goma sha .." yayi shiru yana sauke zazzafan numfashi ,ya gyara zamansa tare da kai hannuwansa duka ya rufe fuskarsa dashi yana jin kamar yayi kuka kafin daga bisani ya cigaba da sakin bakaken maganganu masu zafi da ta'ba zuciya duk magiyar da mami take masa akan yyi shiru bai yi ba har sai daya samu natsuwa sannan ya saurara inda ya kwanta akan kujera ya juyar da kanshi gefe yana sauke numfashi ." mami ta kallesa na second biyar sannan ta juya ta kalli maryam dake tsaye gabadaya ta rasa me zata ce ."yayinda maryam Jiki a matukar sanyaye ta matsa daga kusa dasu tare da juya masu baya tana jin faduwar gaba mai tsananin , tsanarsa gareta yana matukar d'aga mata hankali sosai taji bacin rai ,taji kamar ta fice daga d'akin mummansa ganin yadda ya juya baya ko mami yaki kallo ." mami ta qara matsowa kusa dashi tace "Adamcy ka daina zafafa kiyayyar matarka a gaban idanunta saboda ban fidda rai wata rana shakuwa mai qarfi na iya shiga tsakaninku ba dan haka ka dinga qoqarin dannewa ka barwa zuciyarka please " tana gama fadar haka ta mike tsaye ta qarasa inda maryam take tsaye tare da riko hannunta suka fito daga d'akin." Suna fita mami ta soma qoqarin rarrashin maryam ,tayi saurin cewa mami "karki wani damu mami banji komai araina ba," idan da sabo na rigada na saba da halinsa fatana allah yasa aurenmu ya zame mana alkhairi arayuwarmu gabadaya."shiru tayi kafin ta cigaba da magana "mami ni dai ki qara tayamu da addua akan wacce kike mana duk da har yanzu yaya adam bai amince dani ba amman yau kawai naji wani sanyi da samun 'yanci a zuciyata ." Murmushi mami tayi dan tun tuni ta fahimci wani abu akan maryam din hakan kuma yayi mata dadi domin ko babu komai zatayi hakuri da duk wani wulakanci d'anta cike da farinciki tace"na gode sosai maryam in sha allahu zan cigaba da yi maku addua allah yayiwa rayuwar aurenku albarka allah ya azurtaku da samun zuria masu albarka ko ni yau zuciyata ta rage nauyi duk da rayuwar da adamcy ya d'auko ya rage kashi sabain na farincikina amman duk da haka naji zuciyata ta rage nauyi saboda nayi imani ko bayan raina zaki kula da rayuwar dan'uwanki ." "Maryam adamcy rayuwata ne Kiyi hakuri dashi , Kiyi hakuri da halinsa ki kular min dashi "in sha allahu mami zanyi iyakar qoqarina " na gode maryam allah yayi miki albarka "ameen na gode mami allah ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani "Ameen Ameen mryam shiyasa nake qara sonki akwai ki da hakuri dasanin yakamata ."suka cigaba da takawa ahankali suna magana har suka sauko qasa fuskarsu d'auke da murmushin farinciki ." Bayan saukowar mami ta aika akira mata hisham dan tun safe yana bangaren baba babba tare dasu salim tana zaune a d'akinta yayi sallama sai data bashi izinin shigowa sannan ya turo kofar d'akin ya shiga kanshi a risine a kasa kallo d'aya zaka masa ka fahimci jikinsa a mace yake , hisham ya rusuna ya gaishe da mami cike da girmamawa ,ta amsa masa cike da kulawa tana nuna masa kan kujera amman yaki zama ya zauna akan daddumar daya gani a shimfide akan kafet." "Hisham ya akaji da taro ?kamar bazai amsa ba amman ya kasa ko babu komai mami tana da kima gareshi bazai ta'ba yi mata banza ba,dan haka ya bude bakinsa da kyar yace "alhamdulillah mami ya naku ?to Alhamdulillah hisham allah yayi maku albarka gabadayanku, allah kuma ya baku ikon cinye jarabawa rayuwar, kowani bawa rayuwarsa tattare take tafiya da jarabawa iri iri ." "Kayi hakuri akan sauyin daka samu ka dauki hakan a matsayin jarabawa da kuma qaddara, auren auta yana daga cikin qaddararka wanda baka isa ka goge faruwar hakan ba ,abinda nake son ka fahimta Idan allah bai nufeka da samun wani abu arayuwarka ba sai ka gode masa domin allah sonka yake kuma duk abinda allah ya qaddara shi zaka samu, abinda allah bai qaddara zaka sameshi ba duk yadda abun ya kusantoka at end of the day bazaka sameshi ba duk kuwa son da kake yiwa abun ." "Wannan kuma duk hukuncin ubangaji ne , idan da yau mun sanya hakan acikin zukantamu da zamuyi rayuwa cikin jin dadi cikin annashuwa batare da wata damuwa ba ,idan mun samu allah ne ,idan mun rasa allah ne" wama tasha una illa anyasha allahu rabbul alameen duk yadda kaso idan allah bai so ba bazai ta'ba yuwa ba ." "wannan hukunci ne na allah ,allah yasa hakan shine mafi alkairi wata killan ma idan ka samu auren nuzla arayuwarka ta zame maka maseefa da tashin hankalin da sai kayi nadama ,ta zama bala'i arayuwarka yanzu rashinta sai ya zame maka alkhairi arayuwarka kayi hakuri da sauyin da allah yayi maka da sannu zaka ga irin sakayya da allah zai maka domin duk wanda ya yarda da allah allah zai isar masa ." "idan kuma akwai alkhairi a tsakaninka da nuzla sai kaga anan gaba ka qara daita wannan duk kadan ne daga hukuncin ubangiji fatanmu allah ya zaba mana abinda yafi zama alkhairi arayuwarmu kar allah ya barmu da zabinmu "duk wannan maganar da mami take kanshi na kasa ya kasa d'ago kanshi har sai data dasa aya ta hanyar saka masa albarka sannan ya d'ago yayi mata godiya ya mike a natse ya fice daga gidan gabadaya." Karfe biyar daidai motoci guda goma na alfarma sukai parking a kofar gidan mami domin d'aukar nana hauwa ,mutanen da suka zo gabadaya sun kasance kawaye ne ga hajiya zulfa'u ,kowacce cikin shiga ta alfarma domin kallo daya zaka masu ka fahimci kudi ya zauna ajikinsu shigar kowace tana wane na wane , sai dai mami tace hisham take son yazo ya d'auke amaryarsa da kanshi lokacin da sakon ya samesa yaji abun wani iri ranshi ya 'baci matuqa ." "duk kawayen mumynsa da abokansa da suka tafi d'aukota basuyi ba sai shi da kanshi yaje kamar wata zinariya ?yayi wa kanshi tmbyr yana jan tsaki bana jin zan iya zuwa dan nasan nauyi kawai mami take són d'aura min ya lalubo wayarsa yana qoqarin kashewa kiran mami ya shigo "ya salam !"ya furta a fili yana mai dafe kanshi kiranta né yayita shigowa har sai daya d'auka ,yana d'auka tace "hisham d'ana kazo ka d'auki matarka " babu yadda ya iya dole ya amsa da "tô mami ganinan zuwa"ransa a matukar 'bace ya tashi ya shirya cikin wani d'anyen voyal fari sol ya shiga d'akin hjy zulfa'u ya fad'a mata inda zashi sannan ya fito ya kamo hanyar zuwa abdullahi estate." zaune nana hauwa'u take agaban mahaifiyarta sanye da fararen kaya tun daga kan takalmi mayafi pos din dake rike a hannunta agogo komai na jikinta fari ne sol jikinta lullube cikin mayafi , shape din fuskarta kawai ake iya gani ,wani irin qamshin jikinta Ke fitarwa mai sanyin dadi da sanya natsuwa tare da kwantar da hanakali yayinda yan'uwata mata ke zaune akan kujera kowace cikin shiga iri d'aya ." nasiha mai matukar ratsa jiki mami take mata tana tunatar daita hakin daya rataya a wuyanta cike da gamsuwa nana hauwa take gyada mata kai tana zubar da hawaye adaidai lokacin ATA ya shigo d'akin sakamakon kiransa da mami tayi bai qarasa inda suke ba ya samu waje ya tsaya ya jingina bayansa da bango d'akin ya rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana kallon nana hauwa'u dake zubar da hawaye yayinda aunty shahida ta mike daga mazauninta tana faman rarrashinta tana goge mata hawaye ." Ahankali hisham ya turo kofar dakin ya shigo ya tsaya yana jin wani iri a gabadaya ilahirin ajikinsa kafafuwansa sukai masa nauyi ya kalli inda ATA yake tsaye rabonshi da ganinsa yau tsawon kwana uku kenan ,numfashi ya sauke yana qoqarin danne abinda yaji yana taso masa kafin ahankali aunty shahida ta qaraso inda yake ta riko hannunsa ta zaunar dashi kusa da nana hauwa'u agaban mami ." "hisham ga amanar nana hauwa'u nan na danqata a hannunka ba dan ina tunanin zaka cutar daita yasa na damka maka amanarta ba sai dan yanayin rayuwa da kuma yadda aurenku ya kasance, aure ne da babu wanda yayi tsamanin faruwarsa amman dake haka allah ya qaddara babu tsimi babu dabara sai ya kasance ,kema nana hauwa'u ga amanar hisham d'ana na damka miki, kisan mahimanci amana ko ban gaya miki ba aure amana ce atsakanin ma'aurata kuma duk wanda yaci amanar dan'uwansa allah bazai barshi ba." " na tabbatar d'ana hisham bashi da matsala idan naga wata matsala daga gurin ne zaki kuma ki kuka da kanki dan bazan ta'ba d'aga miki kafa ba ko baki uzuri ba dan haka ki kiyaye "aunty shahida dake durkushe kusa dasu tace "hisham ga amanar auta nan allah ya tayaka riko "aunty khadija da zabiba ma dai abinda suka fad'a kenan "shi dai ya shiga ukunsa yanzu mumynsa ta gama damka masa amanarta kafin ya fito tana jadda masa ko rama taga nana hauwa'u tayi sai ya hadu da mummunar fushinta ,yanzu kuma ga mami dasu aunty shahida shi ya suke son yayi da rayuwarsa ?" shifa baya jin zai iya rike wata amana amman babu yadda ya iya muryarsa a sanyaye yace "in sha allahu mami zan kiyaye allah ya qara girma ya qara lafiya" Ameen Ameen hisham allah yayi maku albarka ." Banda kuka babu abinda nana hauwa'u Ke faman yi wanda hakan Ke sake d'aga hankalin ata kwata kwata irin wannan rayuwar bata burgeshi zaa akai mutun gidan miji amman yana kuka irin haka kamar zaa kai shi kabari ,a tunaninsa wannan zalinci ne sam bai kamata a had'a irin wannan auren ba gara idan nmj ke so komai na zuwa da sauki canza rayuwar mace ba abu bane mai wahala ga d'a nmj amamn canza raayin nmj abune mai bala'i wahala ahankali yaga an mikar da nana hauwa'u tsaye shima hisham ya mike suka jero." Kamar ance nana hauwa'u ta d'aga kanta idanunta ya sauka akanshi tsaye cike da sanyin jiki ta soma tahowa zuwa inda yake tsaye yana ganin haka ya kau da kanshi gefe yana sauke numfashi har suka qaraso inda yake bai waigo ba ,nana hauwa'u ta kasa wucesa kowa yayi mata fatan alkhairi tare da damka amanarta a hannun hisham amman banda shi tasan halinsa shirunsa yana nufin abubuwa dayawa a gareta dan haka ahankali ta dawo ta duka agabansa tana masa sallama sautin kukanta na tashi." jikinsa yayi sanyi gayayyun idanunshi ya ware akanta still tana durkushe tana kuka yayinda tafin hannunta ke kife a saman kafarsa wani abu ya had'iye mai d'aci daya tsaya masa a makoshi bai ta'ba sanin cewar yana qaunar qaramar kanwarsa ba sai da aka samu wannan canjin ,babu yadda zai yi daita né domin itace da kanta ta amince, da tursasata akayi sai dai ayi bala'i da zaayi amman bazai yarda ba ,kukanta ya dinga ta'ba zuciyarsa bai san lokacin da ya kira sunanta ba "nana hauwa'u!" Kanta ta d'ago wanda ke cike da ruwan hawaye ta zubawa yayanta tattausan murmushi ya sakar mata kafin ya mika mata hannunsa alamar ta kama ta mike tsaye ,da wani irin sauri ta kama hannunsa tana ganin kamar a mafarki yake mata murmushi "ina mafarkine ko kuwa ? tayi maganar a fili tana kuka " menene auta ?murmushinka yaya wannan shine karo na farko danaga irin wannan murmushin akan fuskarka" ya qarasa mikar daita tsaye ya kwantar daita akafad'arsa yana shafa bayanta " kiyi hakuri kukan ya isa haka auta "lafewa tayi sosai ajikinsa Kmr wata baby "yaya ka yafe min ban bi umarninka ba "karki damu dani ki kula da kanki ". shi kuwa hisham zuba masu ido yayi yana jin wani zallar 'bacin rai na ratsashi "ki daina kuka auta idan kinga da matsala ki kirani babu wani uzuri da zanwa hisham shima kuma yasan halina bazai yi any thing nonsense ba "wani irin kallo hisham din yayi masa kamar yace masa "me zai yi idan aka samu matsalar sai ya duba idanun mutane dake wajen mami bazata ji dadi ba hka sauran yanuwata da suke da kima a idanunshi ,sannna idan ya fad'a haka mumynsa bazata d'aga masa kafa ba idan taji labari ." ATA ya kamo hannunta ya saka acikin na hisham ya damke waje d'aya "ga amanar auta please ka kular min daita fiyye da yadda zaka kula da kanka" shiru hisham yayi masa yaki cewa komai, Jiki babu kwari suka fice daga d'akin, aunty shahida da aunty Khadeeyja da zabiba na biye dasu suna qarasowa parlour'n hisham ya zare hannunsa cikin nata yayi gaba shiru tayi kawai tana duban bayansa kawayen hajiya zulfa'u mutun uku da suka tsaya suka mike tsaye maryam ta qaraso ta rungume nana hauwa'u tana cewa "shikenan sister zaki tafi ki barni" ta qarasa mgnr tana fashewa da kuka "ai baku rabu ba mrym tunda duk mazajenku 'yan gidan nan ne ,kusan kullum suna nan inji cewar hjy nurriya." Da kyar aka 'bam'bare maryam ajikin nana hauwa'u hjy sumayya ta riko hannunta suka fito zuwa haraban gidan ta bud'e mata bayan mota ta shiga ta zauna ta rufe murfin ,yayinda hisham ke qoqarin qarasawa wajen abokansa hjy summaya ta kwalla masa kira ya dawo ya tsaya gabanta "shiga"mumy kuje kawai daita zan biyoku "aa hisham ba'a yin haka shiga kawai sai wani daga cikin abokanka yajaku "kai !"ya furta a fili sannan ya shiga ya zauna ko kallon inda take bai yi ba ." Su biyu ne zaune abayan motar sai salim a mazaunin direba hawaye yaki tsayawa a idanun nana hauwa'u,wani sabon kuka ne ya kufce mata sanda suka fito daga estate dinsu suka hau titi ,gefe tayi da kanta tana damke hannuwanta cikin juna "salim kasan wani abu ?salim dake tuki yace "aa sai ka fada "wai ATA ke bani amana" salim naji haka ya manna ipod a kunnensa ya cigaba da tuki "aikin banza sai kace shi ya iya rike amanar' yar wasu da yake son shi a rike masa amanar kanwa, mutun sai shegen son kan tsiya sai kazo kasani dole na rike maka amana." kunnuwan nana hauwa'u ya jiyo mata maganarsa acan kasan makoshi kamar ta juyo inda yake sai kuma ta fasa ta cigaba da kallon titi ya sake motsa bakinsa kmar zai yi magan sai kuma yayi shiru ya ciro wayarsa dake ringing yanayin yadda ya amsa ta fahimci yaya amar ne "kaga amar dan allah ku barni da damuwata kowa amana amana !! wai me kuke nufi dani ne ?" me yasa bakuje kuncewa ATA ya rike amanar maryma ba sai ni zaku dameni da wata amana saboda kun rainani ?"dan girman allah ku barni na huta naji da damuwata no no!! bazan fa gane ba wayar salim ce ta d'auki qara ya danna iPod din dake makale da kunneshi yana cewa "okay mumy an gama har ya gama wayar musayar magana hisham yake akarshe dai ya kashe yana furta aikin banza kawai ." Tafiyar mintuna ta kawosu ikeja gra atare suka qaraso gbdynsu har abokan ango sanda salim yayi parking a haraban gidan hajiya sumayya tayi parking a haraban gidan, hisham ne ya fara fitowa yayi gaba ,jiki a matukar sanyaye nana hauwa'u ta fito hjy sumayya ta qarasa da sauri ta riko hannunta cikin nata suka biyo hisham abaya cikin natsuwa har zuwa bakin kofar shiga parlour'n hajiya zulfa'u tana zaune cikin kawayenta ." wata kawarta marry wacce ta kasance yoroba ta mike da sauri hannunta rike da cup wanda Ke cike da ruwa ta tsaida nana hauwa'u abakin kofar shigowa ta zuba mata ruwan akafafunta tana cewa "barkanki da shigowa gidan d'ana yadda kika shigo cikin koshin lafiya haka zaki qare rayuwarki cikin koshin lafiya ,gidan nan bazai miki zafi ajiki ba ,gidan nan zai zame miki tamkar ruwan sanyi ne yadda muka ga wannan ranar allah ya nuna mana sabuwar shekara munzo suna haka akarshe ta rungumeta ajikinta ." ta shigo daita parlour'n kai tsaye marry gaban hajiya zulfa'u ta nufa da nana hauwa'u ta duka a gabanta hjy zulfa'u ta kai hannunta ta d'agota ta zaunar daita a gefenta kamar yadda hisham ke zaune abokansa gbdy suka shigo nasiha tayi masu mai ratsa jiki abokan ango na jiran abasu amarya su wuce daita gidanta mumy tace su wuce sai tayi sati anan gabadaya sukai mata sallama suka kama gabansu ahankali ta riko hannun nana hauwa'u ta nufi dakin dake kusa da nata suna shiga ta zaunar daita a bakin gado tare da cewa" ina zuwa ."!bata jima ba ta dawo hannunta rike da cup ta mika mata "ki shanye!" babu mutsu ta karba wani abu ta gani kamar zuba ta kafa kanta ta shanye tana yatsina fuska "akwai d'aci né ?"ba sosai ba "!ta bata amsa da hakan "okay bari akawo miki abinci nasan da wahala idan kinci wani abu ta juya ta fita ." Ahankali ATA ya juya zai bar d'akin mami aunty shahida da aunty khadija suka dawo d'akin "yauwa a she ma ya nan mu koma magana zamuyi da kai "bai ce masu uffan ba ya koma ya tsaya tare da tura duka hannuwansa acikin aljihun wondonsa ,aunty khadija da aunty shahida suka zuba masa ido suna tunanin ta inda zasu fara masa magana ahankali ya lumshe tsumammun idanunshi na second biyu sannan ya budesu fes akansu tare da tsura masu ido alamun yana sauraronsu " . "adam !" aunty shahida ta kira sunansa bai amsa ba illa tsura mata idanunshi da yayi "me yasa ka zabi ka 'bata rayuwarka akan auren nan ?giya fa adam meye hadinka da shan giya saboda allah ? kai babu wanda ya isa da kai kana ganin mahaifiyarmu zata zaba maka abinda zai zame maka matsala né arayuwarka?mami kullum só take taga cigabanmu amman kai da yake mara mutunci né kullum qoqarin kake ka 'ba.""dan allah malama ya isa haka nasan da wannan nasan tana son cigabanmu amman me zanyi da wuce hkn?yayi shiru yana fesar da iska zata zauna yace "meye next dan ina son naje na huta ya katseta ta hanyar fad'ar haka numfashi ta sauke kawai batayi mamakin abinda ya fad'a ba dan tasan halinsa zai iya ma fadar abinda yafi haka ." Aunty khadija tace "dan allah adam karka qara shan gi..."nifa bazan daina shan giya ba kawai ku barni da rayuwata tunda ni kad'ai damuwarta ta shafa abarni da damuwata kawai ,fuskarsa a daure ya cigaba da magana "wai me yasa kuke manta wani bazai iya ji da ciwon wani ba ?"wannan ciwona ne ni kad'ai abarni kawai naji da ciwona yana gama fadar haka ya juya a fusace ya bar d'akin yana fesar da numfashi."mami ta girgiza kai Kawai cike da taikaci take masa addua. A parlour'n mami na biyu suka kusan cin karo da maryam da sauri taja baya gabanta yayi wani irin mummunar faduwa sannan ta d'ago ta saci kallonsa adaidai lokacin daya d'ago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro da qaunar da take masa ne , wani irin mugun kallo yayi mata mai firgitarwa sannan yaja tsaki yana furta" nonsense"! a fili ya wuceta jiki a sanyaye tabi bayansa da kallo "ya rabbi me zanwa wannan bawa naka ya soni ?rashin qaunarsa gareni yana damuna ya allah ka nuna min hanyar da zanbi ya soni ." Kai tsaye samansa ya hau ranar yau din ata jinsa yake dabam ,jinsa yake kamar an sauyashi daga adam din daya san kanshi zuwa wani adam din dabam ,wani irin bakinciki ke ratsa shi wanda ga duk wanda yasan shi yasan aininhin zahirin fuskarshi zai ga alamun komai ya qara sauyawa agaresa, domin sauyawar yafi na da muni fuskar nan tashi sam babu rahma attare daita ta dawo tamkr ta kumurcin macijin ." Har karfe bakwai sauran wasu mintuna nana hauwa'u na zaune a bakin gado ta zabga tagumi sosai tayi shiru tayi zurfi cikin tunani jefa jefa tana zubar da ruwan hawaye da kallon kular abincin daaka kawo mata da ko bud'esa batayi ba ,tun baaje koina ba ta fara kewar gida wani irin ta dinga ji a ilahirin ajikinta tasan adaidai wannan lokacin da take cikin kad'aici da auren soyayya tayi da dole tasan mijinta yana kusa daita yana rarrashinta bazai barta ta kasance ita kad'ai ba ,amman da yake bai sonta ya bawa banza ajiyarta yayi zamansa a parlour'n ."karfe bakwai da minti goma ta mike tsaye ta shiga bathroom din dake manne da d'akin ta dauro alwala ta fito ta gabatar da sallar magrib tayi adduointa ta sake komawa ta zauan kamar yadda take a d'azu tana cigaba da zubar da hawaye ." hajiya zulfa'u ta turo kofar dakin ta shigo bakinta dauke da sallama yyinda hannunta ke rike da wani cup ba irin na d'azu ba,nana hauwa'u tayi saurin goge hawayenta ta bud'e baki da kyar ta amsa mata sallamar da tayi "har yanzu kina nan a zaune diyata ?"ki rage kayan jikinki mana ki sha iska."nana hauwa'u tayi murmushi kawai d'an bata da wannan kwarin gwiwar bare ta samu karfin zuciyarta aikata haka , burinta a yanzu bai wuce taga yaya hisham ya saki fuskarsa kamar yadda yake mata ada kafin ta zama mata agaresa ba ." tana buqatar sakin fuskarsa ko kadan ne daga garesa ,ahankali ta zare mayafin jikinta ta ajiye cike da jin kunyar hjy zulfa'u,cup din hannunta ta miko mata tana cewa "ungo ki shaye "a natse tasanya hannuta ta karba cike da girmamawa ta kafa kai ta shanye tana yatsina fuska dan kamar irin na d'azu ne kawai kalarsu ne ba iri daya ba ta mika mata cup tana cewa "na gode mumy allah ya qara girma "dan ko bata fad'a mata ba ta fahimci irin maganin da take bata "karki qara yi min godiya dan na baki abu ni fa mahaifiya ce agareki ,ki saki jikinki dani kinji ki cin abinci dana sa akawo miki ?tayi shiru tana tunanin amsar da zata bata kafin tayi mgn har hjy zulfa'u ta qarasa ta bud'e kula abincin yana nan Kmr yadda aka kawo mata "ya baki ci abinci ba ?ki cire komai aranki kice abinci kinji "nana hauwa ta gyad'a mata kai alamun taji " idan kinyi wanka ga kaya can ki canza "tana gm fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin ." Wani abinci hjy zulfa'u tasa aka sake kawo mata wace ta kawo abinci na fita ta dawo dakin wanda kafin ta fita a dakin sai data lallabata dan dole ta fara cin abinci bata wani ci daywa ba ta mike ta shiga bathroom tayi wanka da alwala ta fito ta sauya kaya tayi sallah ishai byn ta idar ta kwanta a gefen gado tana kukan , ita kanta kukan ya isheta haka amman da zarar ta tuna yanayin yaya hisham sai kukan ya sake dawo mata ." hisham daya shigo dakin yaja tsaki karo na farko da yaji ya tsani kukan da take duk da yasanta tun tashinta yasan yadda mami take ji daita ya santa da saurin kuka but ba irin haka ba ,tasan bata són shi me yasa ta amince aka daura masu aure ?dan yasan itama raahin sonahi né yake sata kuka, lalle ko akwai aiki dan wannan na cikin dalilin da zai sa yaji ya qara tsanarta shi kuka idan bana nuzla bane ai aikin banza né a wajensa ,nuzla itace macen da zai iya jurar komai nata tasoshi ko karta só shi he does care wannan alqawarinsa ne ko a wani hali take zai jure matukar akanta ne saboda yana matukar sonta bai zauna ba ya juya ya fice daga dakin daman mumynsa ce ta tursasa masa shigowa ." ****** Da misalin karfe goma na dare ranar lahadi maryama na zaune a d'akinta akan kujerar roba tana zane domin yanzu yana cikin abinda ya fara rage mata damuwa da ta zame mata jiki ,yusif kuwa tuni ta fidda shi aranta da dawowarsa da rashinsa duk daya ne a wajenta ,shi kuwa baba gali tun sanda yayi mata maganar sauyi akan yusif taji duk duniya babu wanda ta tsana kamar shi hatta gaisuwar da take shiga bangaresa ta gaishesa ta daina zuwa ,ko ganinsa tayi a waje gaisuwar sama sama take masa tunda ta rigada ta tabbatarwa kanta baya qaunarta ,ta kuma tabbatarwa kanta baba gali makiyinta ne da keda fuska biyu har ma gara aunty salma dashi ita daman can bata ta'ba nuna tana qaunarsu ba, amman shi baba gali wani lokaci yana nuna yana sonsu ,akan ya'yansa ne ma wani lokaci suke fuskantar tsana shi kuma wannan daman ta ajiyesa a matsayin uban wani da ya'yan wani akwai bambamci ." Ta numfasa sannan ta dakata da abinda take tare da tura bakin pencil a bakinta tana tunani "life goes on maryama karki qara yarda ko amincewa wani d'a nmj arayuwarki da sunan soyayya, ba lalle sai da aure zaki yi rayuwa ba ,ko da aure ko babu zaki rayu dan haka ki natsu ki qara kwantar da hankalinki ki qare bautar kasa ki samu aiki mai kyau wanda zaki kula da kaninki da mahaifiyarki ki ajiye wani batu na aure dan muddin aunty salma aunty hassana baba gali da sauran yanuwan mahaifinki na raye bazasu bari kiyi aure ba "na karbi qaddarata allah ka bani ikon cin jarabawa sanyayyen numfashi ta sauke ta cigaba da abinda take." Washegari ya kama monday tun da asuba ta tashi tayi sallah bata koma ba ta shiga ayyukanta data saba ,bayan ta gama tayi wanka tayi shirin na fita aiki ta fito parlour'n alokacin bakwai da wasu yan mintuna , ta isa inda ta hango mahaifiyarta zaune tana jiran fitowarta ta zauna kusa daita tana gaisheta "aunty ina kwana ?kin tashi lafiya sarauniyata?alhamdullai qaunata ,aunty ta tura mata kofin koko da kosai gabanta ahankali ta soma sha i har ta kammala ta dauki kofi da faranti data ci kosai ta kai shi kitchen zata wanke aunty tace "barshi ki kama hanya ki wuce lokaci ya fara tafiya tayi mata sallama ta fito ta shiga side din umma suka gaisa sama sama tayi mata addua ta fito ." Abakin kofar fita gidan taga baba gali zaune yana sauraron radio ta gaishesa cikin murya mai jin nauyinta ya amsa ta cigaba da tafiya ta jiyo sautin muryarsa yana kiranta ta juyo tare da amsawa ta nufi inda yake zaune yana sauraron radio ta durkusa ta sake gaishesa akaro na biyu ya kalleta sosai sai daya jinjina kai sannan yace "maryama saboda na yanke miki hukunci da abinda yafi dacewa dake shine kike nuna halin damuwa saboda bani na haifeki ba ?". Ta kallesa kawai saboda ita bata san abinda tayi da zai nuna baiyyanar da damuwarta ba maganar bashi ya haifeta ba ai kowa yasan wannan domin da shi ya haifeta bazai mata bakinciki ba amman sai ta kawar da wannan tace "baba ni ba fushi nike da hukuncinka ba sannan banga abinda zai sakani damuwa ba saboda nayi imani rabona bazai taba wuce ni ba matukar yusif mijina ne babu tsumi babu dabara zai aureni idan kuma ba mijina bane nawa mijin zai zo shi kuma ya auri matarsa bare ma ni tuni na manta da babinsa yanzu kai ya kamata kasan abinda zaka fadawa mahaifinsa akan alkwarin da kayi masa ."ya dan gyara zama "wani alkawarin? Tayi shirin domin bazata iya fad'a ba tunda shine yayi alkwarin tuna masa din me zatayi ?duk abinda kike nufi maryama ba abinda zai kawo dakushewar soyayyarki da alhj alqasim abinda ya sanar dake na tabbatar dani ya fara zance amman idan kika duba kunyar mahaifin mlm yahuza babban mutun ne acikin unguwar nan ba qaramin kuskure nayi ba wajen saurin amincewa buqatar alhj alqasim daya zo daita tsakanin ke da sauran yammatan gidan nan kinga shi mlm yahuza Ke yagani yace yana so dan haka Ke din ce wacce yake so ba shukura ba daace zai karbi shukura amadadinki dana bashi ita Ke kuma kin auri yusif ." Shi kuma nasan alhj alqasim zai karbi shukura ko sakina adalilin rashinki tun da daman shi zuria gidan nan yake bukata dan haka ki natsu ki kwantar da hankalinki wannan ba wata matsala bace tunda ni zan tunkaresa da maganar komai ta sunkuyar da kanta kawai tana jinsa tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ita yanzu bata jin mlm yahuza acikin ranta tunda tagansa da shukura har abada babu ita babu shi ko mutuwa zaiyi akanta wallahi bazata auresa ba sannan wannan magana ce kawai baba gali yake batun soyayya tsakanin mlm yahuza da shukura sunyi kawai dai anje an warware aiki ne komai dake faruwa da sanin aunty salma ita Ke shirya komai ." Sarai baba gali ya karanceta dan hk muryar a fusace ya cigaba da mgn "tunda naga kamar kin kamu da soyayyar yusin din allah ya baku zaman lafiya da yusif ita kuma shukura ko sakina allah ya kawo masu nasu rabon "uhm kawai ta furta dan tasan ya fad'a haka ne ba har acikin ranshi ba ,ta dago ta girgiza kai cikin takaici irin rayuwarsu "ni baba bana ja da maganarka a yau ida ka shirya aura da kowacce daga cikinsu ga yusif kayi ." ya sauke ajiyar zuciya yana cewa tô shikenan na gode na tabbatar daman bazaki aikata abinda zai jawo min zagi ba su yusif din zasu zo karshen satin nan dan mun gama magana da mahaifinsa cewar shukura zai aura shima yusif din ya amince da hakan dan haka ko yau mlm yahuza ya kiraki ki amshesa kije ." Nan taji gabanta ya fadi jin wai abba ya amince da kuma amincewar yusif daman yusif ba soyayyar gsky yake mata ba tabbas duk maza mayaudara ne babu nmj dan goyo kalamansu daya haka salon yausararsu daya haka ta mike tsaye jiki babu kwari ga lokacinta daya bata mata ga bakinciki daya kunsa mata abun yayi mata yawa ,bakinta na rawa tace "baba Allah ya tabbatar da alkhairi sai dai ka fadawa mlm yahuza ya nemi matarsa a gaba dan ni a halin yanzu gbdy babu mgnr aure a gabana bazan yi aure ba har karshen rayuwata tana gama fadar haka ta soma daga kafafunta bayanta yabi da kallo yana kwabe baki alamun matsalarta." Yau sunyi very busy a wajen aiki dan daga maakatarsu kwasasur akayi zuwa ma'aikatan man petir dake apapa saboda kwarewar wasu daga cikinsu ranar haka tayi aiki cikin sanyin jiki da wahala ita ba soyayyar yusif bace damuwarta tunda daman bata fara son shi ba mamakin baba gali ne ya addabeta tmbyr duniya subai'a tayi mata tace babu komai ."bayan an tashi daga aiki ta fito bakin get ta tsaya tana jiran fitowar subai'a su wuce gida ,ta tura hannunta cikin jakarta zata ciro nikaf dinta adaidai lokacin wata mota reven rover ta sanyo kai zata shiga cikin ma'aikatan ,gani tayi motar taja ta tsaya motar bata shiga ciki ba haka zalika bata juya ba mutumin dake zaune a bayan motar taga ya fito jikinsa sanye da suit bakake." da wani irin sauri ta dan matsa gefe ,shi kuwa fuskarta yake kallo daga inda yake tsaye cike da faduwar gaba tabbas wannan fuskar idan ba mafarki yake ba fuskar da mai gidansa yake gani ce acikin duniyar mafarkinsa ."duk da fuskar zane ce ,amman ya rantse da wanda ke busa masa numfashi itace wace zuciyar mai gidansa take muradi kasancewa tare daita, gbdy idanunwansa sun rufe akanta baya ganin tarin jama'ar dake gurin burinsa ya isa gareta tana qoqarin sanya nikaf taji ya rike mata hannu jikinsa na wani irin kirrrma kafin tayi wani abu taga ya janyo hannunta da sauri zuwa cikin ma'aikatan qoqarin fixge hannunta take cikin tsananin tashin hankali amman yaki sakar mata hannu ." Ana zan dataka sai a book 2 in sha allahu wadan da suke bibiyarmu a arewabooks inshaallahu zasu cigaba da ganin update dinmu kmar yadd muka saba ." Alhamdulillah Mmn sudais