BOSS LADIES WRITERS*~ KE GABATAR MA KU👇 _🔥💫THE PRISONERS🔥💫_ ~TAKUN🔥🔥🔥ƘARSHE~ Daga Alƙalamin Boss Bature Dedicated To Aunty Kubra😍 _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty❤._ _______________________✍️ Bayan ƴan mintuna Pravin ya fito daga toilet fuskarshi a jiƙe da ruwa kamar wanda ya ɗauro alwala, maimakon taga 6acin rai akan fuskarshi sai taga akasin hakan, wani irin shu'umin murmushi yake sakar mata, hakan ba ƙaramin 6ata mata rai ba, ɗaure mashi fuska tayi haɗi da kau da idonta daga kan shi, taci gaba da cin abincinta. Gefen ta ya zauna"idan akwai wani punishment din daya fi wanda kika bani a yanzu, A shirye nake dana kar6e shi, Ni dai buri na ki yafe min mu shirya tsakanin mu, My Sarah bazan juri fushin ki ba" daɗin baki Pravin yaci gaba dayi mata, tun da ya fara magana Hajiya Saratu bata dube shi ba. Abincin ta take ci, hannu takai zata ɗauki apple ciki Jerin kayan marmarin dake shaƙe a plate da sauri Pravin ya ruƙe hannunta yana faɗin"Bai kamata kina share ni ba, tun ɗazu nake yi maki magana kinyi banza kin ƙyaleni inata zuba kamar aku," a marairaice ya ƙare maganar, ranta ya 6aci ta tsani tana cin abinci a takura mata, a harzuƙe ta fuskance shi da niyar ta 6al6aleshi da masifa sai dai kafin tayi hakan yai saurin shammatarta ya haɗe bakinshi da nata, kafin tayi yunƙurin janye bakinta yayi saurin zagaye hannayenshi ya ruƙe qugunta ruƙo bana wasa ba, still bata daina kiciniyar raba kanta dashi ba sai dai yaci ƙarfinta, lokaci ɗaya ta soma jinta a yanayin da bata shirya kar6arshi ba, kissing ɗinta ya fara yi cikin ƙwarewa yake sarrafa ta, har yayi nasarar zuge zip din rigarta slowly ya zame wuyan rigar har zuwa kan flat stomach dinta, abunda ya jima bai samu damar yi da ita ba, numfashinshi har wani hauhawa ya ke yi kamar mayunwacin zakin da yaga nama, zame tonge dinsa yai daga cikin bakinta ya shiga manna mana mayataccen kiss tun daga kan wuyanta har izuwa saman big boobs dinta da suke acike fam, ƙoƙarin 6alle hannun bra din yayi asusuce yakai hannu zai yi grabbing dinsu kamar daga saman Yaji ta bangaje shi da ƙarfin gaske har sai da Ya faɗa kan mattress din, da sauri ta maida bra din ta gyara wuyan rigarta daya kwale mata, idanuwanta sun kaɗa jawur sun ƙanƙance fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin sai faman huci take yi alamun 6acin rai. Lumshe idanuwansa yayi tsabar takaici da ƙululun baƙin cikin da yaji na katse mashi enjoyment dinsa da ta yi ne yasa shi fitar da ruwan hawaye suka soma gangarowa saman kuncinsa, muryarshi ƙasa ƙasa ya furta "Meyasa za ki yi min haka? Kin hana ni jin daɗin rayuwata sai kace ba mijin ki ba, gaba ɗaya kin juya min baya ta 6angaren bani hakkina, Saratu ba ki yi min adalci sai naci wahala kafin nake samu ki bani haɗin kai, ada ba haka ki ke yi min ba kin canza, Idan laifi nayi maki ki faɗamin mana" zuciyarshi na tafarfasa ya ƙare maganar. Gaba ɗaya abincin Ya fita aranta, yunƙurin amai ta soma yi da gudu ta nufi toilet ta shiga, ranshi ya 6aci gani yake kamar don saboda kiss din da yayi matane yasa take yin amai saboda tana ƙyamar shi. Daƙyar Ya iya miƙewa zaune ya jingina bayanshi da headboard idanuwanshi sun kaɗa jawur, Ya rasa gane dalilin da yasa ya gaza haƙura da ita duk irin wulaƙancin da take yi mashi, ga dukkan alamu ya manta da abun da ya kawo shi ɗakin. Kusan mintuna biyar kafin Hajiya Saratu ta fito daga toilet, hannunta ɗaya dafe da saitin zuciyarta, Cak ta tsaya da tafiya ta ɗaura idonta akanshi, kamar yadda take kallonshi haka shima ya ke kallonta, ba ta yi mamakin ganin hawayen dake akan fuskarshi ba, aranta ta furta"jarababbe kawai" a fili kuma tace"dama ka shigo ɗakin ne donka takura min da jarabarka ne"? Meyasa ita wadda ta taya ka kwana adaren jiya bata biya maka buƙatarka ba? Kai ne fa da kanka ka faɗamin cewa tafi ni Iya tarairayar miji ko ba haka ba"? Ta faɗa tana jifar da shi da harara. Dafe kanshi yayi da hannu ɗaya, sai yanzu ya gane dalilin dayasa tayi mashi wulaƙancin nan, Kishi ne ke damunta, duk da yasan bata gasgata abun da ya faɗa mata ba. Cikin sanyin murya yace"kin 6ata min rai jiya shiyasa na faɗa maki hakan saboda kiji abunda naji, amma ba dagaske nake ba, duk da baki ƙaunata ni bazan iya haɗaki da wata ƴa mace ba, saboda ke kaɗaice acikin zuciyata har abada, shiyasa nake haƙuri dake duk wulakancin da zakiyi min bazan iya cin amanarki ba......." Yana magana hawaye na cigaba da wanke fuskarshi. Duk irin zafin da ta ɗauka sai taji jikinta yayi sanyi, lokaci ɗaya tafara sassauta fushin fuskarta, koda Pravin Ya fahimci raunin da zuciyarta tayi sai yai amfani da wannan damar ya ƙara sanyaya muryar shi haɗi da marairai ce mata fuska Yaci daga da cewa"bansan meyasa ki ke son 6ata min rai ba, burinki ki ƙuntata min, bayan ba haka mu ka yi wa juna alƙawari ba, kada ki manta Saratu, ƙaunar da nake yi maki itace tasa nabar dangina saboda kin nuna baki ra'ayin zama a india ahaka na amince na biyoki Nigeria, kuma na zauna a family house dinku saboda kin buƙaci kinfi son zama tare da ƴan uwanki, babu irin gorin da ba'ayi min ba akan ina zama gidan surukaina amma saboda son da nake yi maki yasa na jure duk wani wulaƙancin da nake fuskanta, naci gaba da zamana, har muka tara zuri'a, ban ta6a buɗe baki na faɗa ma wani cewa bada son raina nake zaune gidan surukaina, ke ce ki ka nuna kina so ni kuma saboda ƙaunar da nake yi maki yasa nake yi maki biyayya" dakatawa ya ɗanyi da yin maganar yana binta da kallo, tsantsar nadama yake gani akan fuskarta. "Idan naga dama zan Iya sakin ki, In kama gabana saboda ni ban dogara dake ba, da Allah na dogara ki daina tunanin dukiyarki take sanyawa ina atare dake ba haka bane ko ɗaya, Ni ƙaunarki nake yi don Allah ba don wani ba in ba haka ba ai da tuni na koma ƙasarmu". Ƙafafuwanta ne suka Gaza ɗaukarta, a daddafe ta nufi mirror chair ta zauna akai tana fuskantar shi. "Saratu ki faɗamin kin daina sona ne"? Yanayin yadda yayi mata maganar, ba ƙaramin karya mata zuciya yayi ba. Runtse idanunta ta yi, ita kanta ta rasa gane meyasa take yi mashi haka? kuma a yadda ta ke jin shi babu abun da ya canza na daga ƙaunar da take mashi. Jin motsin shi yasa tayi saurin buɗe idanuwanta, saukowa yayi daga kan gadon ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Yana share hawayen shi da hanky. Har ya ruƙo handle din ƙofar Aranshi yana Allah Allah ta dakatar dashi yaji ta ambaci sunanshi"Pravin" shu'umin murmushine ya bayyana akan fuskarshi, a hankali take tafiya tana tunkararshi, da sauri ya 6oye murmushin fuskarshi Ya juyo yana dubanta tamkar mai fama da ciwon ido, unexpected tayi hugging dinshi ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, muryarta ƙasa ƙasa ta furta"I'm really sorry, my hubby. I've realized my mistake, and I won't hurt you any more" Kwantar da kanshi yai kan kafaɗarta Ya zagayo da hands dinsa ya ruƙo waist dinta, yaushe rabon da yaji ɗumin jikinta haka harya manta sosai yayi tighting ɗinta, Yana shaƙar ƙamshin turaren jikinta, bai ta6a tsammanin zaiyi nasara akanta ba, sai gashi cikin sauƙi ya yaudareta da kalamansa. "Ki yi min alƙawarin ba zaki ƙara 6ata min rai ba? sannan zaki dinga bani haƙƙina akai akai, duk time dana buƙace ki" ya faɗa batare daya raba jikinshi daga nata ba. "Bazan iya yi maka alƙawari ba, kasan ɗan adam ajizine, dole wata rana mu samu sa6ani bawai fatan hakan nake yi mana ba, but in sha Allah zanyi ƙoƙarin ganin na kawar da duk wani abu da zai 6ata maka rai" Ƙara ƙanƙameta yayi, hada manna mata kiss kan kafaɗarta. Tsawon mintuna kafin ya raba jikin shi daga nata, Ya ruƙo hannunta acikin nashi, fuskokinsu ɗauke da murmushi. "Ina fata kanka bai yi maka ciwo, naga idanunka sun kaɗa jawur" "Kada ki damu, dama kece damuwata kuma Alhamdulillah yanzu komai ya wuce tun da kika kar6i laifin ki, fatana shine Allah Ya dawwamar da zaman lafiya a tsakanin mu" "Ameen my husband" daɗi yake wai yau shi hajiya saratu take kira da hubby da kuma sunan mijinta, Ya manta when last yaji hakan daga gare ta. Janyo hannunshi tayi"ka dawo mu zauna mu ci abinci a tare, nasan kana jin yunwa" Girgiza mata kai yayi"no bana jin yunwa my wife" ya faɗi hakanne saboda cikinshi acike yake, Hajjaty ta bata shi lafiyayyan abinci yaci ya ƙoshi babu yunwa atare dashi. "Namanta ban faɗa maki ba" a hanzarce ta kalle shi tana jiran jin ƙarashen zancen "Game da abun da ya faru jiya, dangane da shigowar maciji gidan nan........" a tsanake Pravin Ya labarta mata komai, hatta ƙaryar da yayi masu Senate Lateef bai 6oye mata ba, a ƙarshe yace"na faɗi masu hakanne donsu ɗauki abun serious, saboda bana son abunda zai cutar min dake da kuma ahlinki, shiyasa nayi masu ƙaryar cewa kin kwana idonki biyu" Tun da ya fara maganar, Yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai, a ruɗe ta furta"Wai kana nufin yaya Hateem shi ya tura da jet aka dauko sheikh imam from sudan to Nigeria? Sannan shi macijin dama mutun ne!? Kuma a gidan Owais dake acikin estate din nan Yake zaune....." Hankali amatuƙar tashe ta furta maganar. Jinjina kai pravin Yayi"ƙwarai kuwa duk abunda kika ji na faɗa maki dagaske ne, yakamata mu ɗauki tsastsauran mataki idan ba haka ba owais da prime minister zasu ja mana bala'e garin son taimakonsu, In ba haka ba taya zasu taimaki Yaron dake canza halitta Ya koma Maciji? Ni dai nafi tunanin wasu miyagunne daga cikin abokan hamayyar Jam'iyar su baba Obie suka shirya maƙarƙashiya donsu kashe baba, shiyasa macijin Ya faɗo gidan nan maimakon sauran gine ginen dake akusa da gidan owais din......" a firgice hajiya Saratu take faman zazzare idanunta duk tabi ta ruɗe, maganganun da Pravin Ya faɗa mata sun yi matuƙar yin tasiri Acikin Zuciyarta, Jiki na 6ari ta nufi ƙofa zata fuce don taje ɗakin baba obie, Ko mayafi babu akanta, da sauri pravin ya ruƙo hannunta a haushine ta juyo tana kallonshi. "Bari in ɗauko maki mayafi," ya faɗa tare da sakin hannunta, Ya juya cikin takun sauri ya nufi closet dinsu, jim kaɗan Ya dawo hannunshi ruƙe da mayafinta Ya lullu6a mata shi akanta, da sauri ta fice daga ɗakin. Fitarta keda wuya Pravin Ya tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya mai matuƙar razanarwa sautinta tamkar ba daga bakin shi take fitowa ba. Lokaci ɗaya ya haɗe fuskarshi tamkar bai ta6a yin dariya ba, Ya juya cikin ɗakin Ya nufi gaban mirror Ya tsaya yana kallon fuskarshi, kafin Ya zura hannu ya zaro wayarshi daga aljihun suit dinsa. Pressing dinta ya soma yi, kafin Ya kara wayar a kunne. da kakkausar Murya Ya furta"mugun Bawa komai yana tafiya yadda muka tsara!!! Yana ƙarasa faɗar hakan, Bai Jira amsar da mutumin zai bashi ba yai rejecting call din, akan mirror Ya ɗaura wayar, ya juya da sauri ya fuce daga dakin yabi bayan hajiya Saratu. *💋UNAISAH❤* Idan muka koma 6angaren Unaisah tamkar mai gadi haka ta tsare Danish, duk wani motsinshi akan idanunta, a yanzu haka tana daga kwance gefenshi ta ɗaura kanta saman chest dinshi, ta aza hannunta saman flat stomach dinsa ta natsu tana shaƙar ƙamshinsa, sai faman lumshe idanunta take yi wani irin bacci ne ke ƙoƙarin fisgarta, lokaci yana ta tafiya ba tare data ankare ba ko sallah bata yi ba, gaba ɗaya ta shagala ta saki jikinta, ba zato ba tsammani tajiyo muryar babban mutun Yana faɗin"Allah Yasa ya farka" rass taji gabanta ya faɗi, da ƙarfi ta ware manyan idanuwanta tare da yin wuff ta miƙe zaune tana kallon glass door din a hankali ƙofar ta soma zugewa, a hanzarce ta rarrafa ta faɗo daga saman gadon ta shige cikin labulan ɗakin ta la6e kamar wata 6arauniya, jikinta sai kerma yake yi kamar wadda tayi ma sarki ƙarya. Gaba ɗayan su ne suka shigo ɗakin tun daga kan Prime minister, sheikh Imam, chief owais, Big guy da salsabeel sai Boss Man, a bakin gadon nashi suka dakata da yin tafiyar idanuwansu akan Danish dake a kwance. Unaisah dake a la6e bayan labule zuciyarta ce ta soma bugawa tunawa da ma6allin rigarshi data bari a buɗe, tasan zasu iya gani kuma zasu gane wani ya shigo ɗakin, sai faman cizon yatsanta take yi, tayi danasanin shigowa ɗakin. "Har yanzu bai farka ba ko"? Prime minister ne yayi maganar Yana duban fuskar salsabeel. "Eh Yalla6ai, amma idan kana buƙatar Ya farka sai atada maka shi, Inyaso daga baya sai ya koma baccin" "A'a banaso na takura mashi, zan jira har zuwa lokacin da zai farka" da mamaki akan fuskar Boss man yace"ya akai ma6allin rigarshi suka cire"? Sai da ya ambaci hakan su ka yi saurin kai idanuwansu kan Ƙirjinshi dake a buɗe, lamarin Ya ɗaure masu kai. "Ko Shi ya buɗe da kanshi? Ko wani ne Ya shigo" Prime minister ne yayi tambayar da alamun ruɗu akan fuskarshi. Sheikh Imam Yace"bana tunanin shi ya buɗe da kanshi, sai dai wani iko na Allah ko kuma wanine Ya shigo ɗakin bayan fitar mu" "Wanene zai shigo? Yaran gaba ɗaya na tattarasu a ɗakinsu Unaisah, Ummi tana aɗakinta, babu yadda za'ai ma ta Iya ƙetare Iyakarta, Ƴan uwansu maza kuma tare dasu muka tafi masallaci balle ace ko sune suka shigo" big guy ne ya kora jawabin. Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba Chief owais da baice komai ba, A hankali yake bin ɗakin da kallo kafin Ya sauke idanuwanshi kan bedsheet din gadon dake a yamutse alamar wani ya hau gadon. "His bedsheet is squeezed. which means someone came into the room after we left," chief ne ya furta maganar, nan take suka kai dubansu ga zanin gadon, Ya yamutse sosai. "Amma wanene Ya shigo" Acewar Boss,"Karfa ace wani mugun abunne" Damuwace ƙarara akan fuskar Prime minister, ya dubi Shiekh Imam dake a gefenshi"Ni dama hankalina bai kwanta ba tun da muka tafi masallaci muka barshi shi kaɗai a ɗakin" Cikin kwantar da murya sheikh Imam Yace"In sha Allah babu abunda ya faru dashi, Ina da tabbacin hakan" Shiekh Na rufe baki Big guy yace"Sir, please give me a chance to check the CCTV footage, that way we'll be able to find out if someone else entered the room.( Ka bani dama in bincika cctv footage, ta hakan zamu Iya gane wanda ya shigo ɗakin idan har mutunne") Shiru Chief Owais Ya ɗanyi har Ya buɗe baki zai bashi amsa karaf idanuwanshi suka sauka akan labulan dake lilo Yana mutsi nan take Ya fahimci mutunne Ya la6e aciki "There's no need to check the CCTV." Ya faɗa tare da ɗaga Voice dinsa Ya furta"Come Out!" Rass taji gabanta Ya faɗi, duk da ranta bai bata da ita Yake yin maganar ba. "I'm commanding you to come out from behind the curtains. Don't make me repeat myself," babu wasa akalamansa. Jin wannan maganar yasa gaba ɗayansu su ka kalli direction din da chief owais Yake kallo, Tsantsar mamaki ne akan fuskokinsu ganin labule Yana motsi. "Amma koma wanene wannan jikinshi zai gaya mashi, kayi kuskuran shigowa ɗakin nan" big guy ne ya furta maganar. Prime minister kuwa Ya ƙura ido Yana jiran ganin wani me ƙarar kwanan ne. Tsawa Boss man Ya daka da karfi tare da fadin"zaka fito ko sai mun harbe ka da harsashin bindiga" Ƙiris Ya rage ta saki fitsari a wando, tuni ta haɗa uban gumi, jikinta ya hau yin kerma, ita da ba mai laifi ba amma ta firgita kanta, hakanan ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba, gani take kamar in suka kamata a ɗakin zasu zargi wani abu, kodan saboda ma6allin jallabiyarta data cire masa, zasu iya tsammanin da wata manufar tayi hakan. "Bawan Allah ka fito salin alin ka bayyana kanka tunkafin mu fusata" acewar big guy, shiru babu alamun na cikin labulan zai motsa. Moving quickly Chief Owais Ya nufi labulen yayin da yake nannaɗe hannun Rigar shi, har ya miƙa hannu zai damƙi wuyan mutumin ta cikin labulen muryar Boss man ta dakatar da shi. "Sir, Unaisah ce," cak Ya tsaya tare da juyawa yana kallon Boss, gaba ɗaya mutanan dake a ɗakin shi suke kallon cike da mamakin taya akai yasan wanene. "Raina ne ya bani itace, kuma ita kaɗaice zata Iya shigowa ɗakin nan don ta duba ɗan uwanta" Ya faɗa tare da ɗaga muryarshi ya furta"Unaisah come out" A hankali kowan nan su Ya ɗaura idanuwanshi kan labulen. Janye labulen tayi ta fito tana faman zare gray eyes dinta, nauyin haɗa ido dasu taji da sauri ta duƙar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. "Jari mai kasada, da ace kinbari chief ya shaƙi wuyanki sai dai ki ganki a Emmergency room" Big guy ne yai maganar da zolaya, gaba ɗayansu suka saki murmushi, prime minister yace"idan na fahimta wannan itace Yarinyar nan ko" Ya faɗa idanuwanshi akan fuskarta, Boss Man yace"itace My daughter" Sheikh Imam Yace"Tabarakallahu ahsanul khaliqin, zonan ƴata mu gaisah" yai maganar tare da miƙa mata hannu. ɗagowa ta ɗanyi ta kalli chief dake a gefenta, face mask din fuskarshi Ya hana ta ganshi da kyau, sai dai kyawawan idanuwanshi. Tana faman zazzare idanuwanta haɗi da ƙyafƙyaftasu ta nufi sheikh iman, ta ɗaura hannunta asaman nashi daya miƙa mata. "Unaisah ko"? Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh. "Meyasa kina ji muna magana ki ka yi shiru baki tanka mana ba kamar wata mai laifi, ai ba wani abu bane don kinzo duba ɗan uwanki" Shiru tayi bata ce komai ba, duk ta kama kanta kamar wadda tayiwa sarki ƙarya. "Zonan surukata" prime minister ne ya kirata, da sauri ta wurga eye balls dinta kan fuskarshi rass taji gabanta Yai mugun faɗuwa, har saida ta zaro ido waje ta saki baki tana kallon ikon Allah, duk sun fahimci dalilin ruɗawarta. da sauri ta kalli Boss man ta kuma kalli Salsabeel dake atsaye fuskarshi ɗauke da murmushi "Baki ji Yana magana ba? Kije ku gaisah" acewar Salsabeel Zuwa tayi gaban prime minister ta tsaya muryarta adabarbarce ta furta"Ina kwana," Murmushi yasakar mata Ya ɗaura tafin hannunshi saman sumar kanta "Ba ki yi breakfast bane? Ko baki duba time ba, Naji kina fadin Ina kwana bayan rana tayi" cikin kulawa yayi mata maganar. Muryarta kamar ta salihar baiwa ta furta"mantawa nayi,' "Okey, surukata Ina fata kina lafiya"? "Lafiyalou" "Naji dadin haɗuwa dake, ke fa"? Ɗaga mashi kai tayi"nima" "Unaisah" Boss ne ya kira sunanta, ta juya tana kallonshi. "Sunan shi prime minister, uncle na chief namu, kuma shine ya kira sheikh Imam don Ya duba lafiyar ɗan uwanki" Da sauri ta maida kallonta ga prime minister, farin cikin yasa taji hawaye sun cika mata idanuwanta, miryarta na rawa ta furta. "Mun.... gode, Ubangiji Allah yasaka maka da gidan Aljanna, kamar yadda ka sanya mu farin ciki kaima Allah Ya faranta maka, In sha Allah duk idan nayi sallah zanyi maka addu'a'. Murmushi kowan nan su yasaki, musamman prime minister har cikin ranshi yaji daɗin kalamanta. "Nagode surukata," Juyawa tayi da sauri ta dubi sheikh imam. "Baba mungode, Allah ya saka maka da mafificin Alkhairinsa" addu'o'i ta dinga yiwa sheikh imam, Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya shafa sumarta da hannun shi tare da cewa"Nagode da addu'arki agare ni, kina da kaifin basira, kuma kina da hankali, Iyayenki sun baki Tarbiya, Allah yayi maki albarka tare da sauran ƴan uwanki" amsa mashi tayi da ameen, haƙiƙa taji daɗin kalaman sheikh imam, ƴan hawayen da take 6oyewa cikin idanuwanta tuni sun fara gangarowa kan kuncinta. "Unaisah, saura chief namu, yakamata kiyi mashi godiya" Boss Man ne ya faɗa yana nuna mata shi, tamkar mai jin shakkar shi ta juya tare da ɗaura idanuwanta kanshi, Yana daga tsaye ya goya hannayenshi on his broad chest, harta ɗaga ƙafa zata nufe shi Big guy yai hanzarin dakatar da ita ta hanyar yi mata Magana. Nufota yayi adai dai bayan ta ya dakata tare da duƙo da kanshi saitin kafaɗarta Yayi mata raɗa. "You don't need to thank him, saboda baya so, but be kind to him. If you give me the chance, I'll guide you. Cikin sanyin murya ta amsa amshi da toh. "Good Girl," Ya ambaci hakan tare da ɗago da kanshi, babu wanda yaji me suke tattaunawa. Boss Man Yace"Unaisah zoki wuce ki tafi ɗaki ki yi sallah, Yanzu za'a kawo maku lunch ɗinku" amsa mashi tayi da toh, kafin ta nufi ƙofar room ɗin ta fuce da sauri. Kafin wani ya kuma yin magana acikinsu, Danish dake akwance Yaja dogon Numfashi, Yatsun ƙafarshi suka soma yin kerma da na hannayensa nan take suka fahimci ya farka daga bacci, wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskar prime minister. Salsabeel Yace"Ya farka, Yakamata akawo mashi abincin Yanzun" "Wani kalar abinci zai Iya ci"? big guy ne ya tambaya. "Abinci mai ruwa zaifi yi mashi sauƙin wuce wa ta maƙoshi, don bazai Iya tauna abu mai tauri ba" "Okey, bari naje na kawo mashi" big guy ya faɗa tare da juyawa a hanzarce ya fuce daga ɗakin. Fitarshi keda wuya, Wayar Chief ta fara Ringing, gaba ɗaya suka ɗago suna kallon shi Prime minister yace"Wanene ke kiranka" Curo wayar yayi daga aljihu Ya duba screen din kafin Ya bashi amsa da cewa"Dad Lateef ne" "Okey, idan kana buƙatar ka shirya kafin mu tafi can gidan ka tafi ɗaki, in sha Allah kafin ka dawo na kammala bashi abincin mu sai mu fara zuwa gida" Chief ya furta"okey," kafin ya juya ya nufi room door din, bayan fitarsa Sheikh Imam Yace"atare zamu tafi gidan baban naku, Inason in gaishe da aminina da sauran mutanan gidan" Prime minister Yace"Toh," Shigowa ɗakin Big guy yai hannayen shi a ruƙe da tray madaidaici, kan carpet din gefen gadon Ya daurashi, kafin Ya haye saman gadon Yayi ma salsabeel alamar yazo Ya taimaka mashi, atare suka ɗaɗɗago da Danish suka jinginar da bayanshi jikin headboard din gadon bayan sun sanya mashi pillow, Yalwatacciyar sumar kanshi ta sauko kan shoulders dinshi. "Baba, ko zaku je gidana ka huta, kafin in kammala bashi abinci, in yaso daga baya zamu zo tare da Chief owais, sai mu wuce gidan baban" Jinjina kai Sheikh Imam Yayi, Hakan yayi nima inaso in canza kayan jikina, Wa zai kai ni gidan"? Big guy yace"Aikina ne wannan" ya faɗa tare da saukowa daga kan gadon, Yace da sheikh su tafi Ya sauke shi a mota, Sallama sheikh Yayi ma Prime minister kafin fitarshi saida Ya faɗa cewa idan sunga wani abu badai dai ba dangane da Danish su kira shi awaya su sanar da shi. Prime minister Ya amsa mashi da toh haɗi da yi mashi godiya, bayan fitarsu, wayar boss tayi ringing, da sauri ya zaro daga aljihu, sunan chief ne ya bayyana akan screen din da sauri yai Ya kara wayar a kunnanshi. Bayan sun kammala yin wayar Ya dubi Salsabeel. "Chief Yace ka koma gida wurinsu khadeeja" Amsa mashi yayi da toh, "Yalla6ai zan wuce, In sha zuwa gobe zan shigo in ƙara duba jikinshi" cikin girmamawa yayi maganar Yana duban Prime minister Fuskarshi asake yace"Allah yakaimu Lafiya, Amma nayi tunanin kaima agidan nan kake zaune" Salsabeel Yace"a'a, gidanmu daban, Ina kula da sauran Ƴan uwanmu ne" "Akwai sauran Yaran kenan bayan wanda ke acikin gidan nan"? "Eh yalla6ai" "Allah ya tayaku ruƙo, Sai Allah Yakaimu" "Ameen" ya fada tare da kallon boss yayi mashi sallama. "chief yayi magana da Jami'in da zai yi driving dinka, Yana awaje Yana jiranka" Amsa yayi da toh, kafin Yasakai Ya fuce daga ɗakin. Ya rage saura prime minister da Boss man sai Danish da ke asaman gadon. "Yalla6ai zan taimaka maka mu bashi abincin" Prime minister yace"Okey," Boss man ne ya ɗauki tray din abincin Ya ɗaura shi daga gefen gadon, Ya ɗauki robar madara Ya cire murfin a cup ya tsiyaya madarar, kafin Ya miƙa ma prime minister yasa hannu ya kar6a haɗi da furta mashi thanks. Abaki ya kanga ma Danish sai dai yaƙi buɗe bakin ya rufe shi gam. Ajiye robar milk din boss yayi, tare dakai hannu ya ruƙo la66ansa ya buɗe mashi baki daƙyar, a hankali milk din take shiga bakinshi hankalin prime minister ya kwanta ganin yana swallowing dinta, duka ya shanye, murmushi yasaki yana kallon boss man yace"naji dadi daya sha, ka ƙara mashi da yogurt" Martanin murmushin Boss yayi mashi kafin ya kar6i cup din ya zuba mashi yogurt ya miƙa ma hateem, cikin ikon Allah danish ya shanye, sai da ya tabbatar daya cika mashi cikin shi tukunna yace. "Bari nabarshi haka, kada naci ka mashi ciki," Hateem ne ya faɗi hakan idanunsa akan fuskar Danish wani irin kallon so da ƙauna yake jefa mashi. Sauke tray din boss yayi kan carpet, kafin ya ɗago yana kallon hateem daya ƙurawa danish ido kamar mai karanto wani abu akan fuskarshi, tun ɗazu yake ta son ya tambayeshi wani abu sai dai ya kasa, gani yake kamar raini ne yayi magana da mutun mai babban muƙami irin Hateem. Daurewa yayi muryarshi da alamun jin shakkar furta maganar yace"yalla6ai..." kallon da prime minister yayi mashi ne yasa shi saurin haɗiyar maganar. Murmushi ya sakar mashi tare da cewa "I'm listening to you, and I heard you mention my name. Why did you go silent? Is there something you want to tell me?" Sunnar dakai ƙasa Tajo yayi"bakomai subul da baka nayi wurin furta sunan" "Ban yarda ba, please tell me what you want to talk to me about. Kada kaji nauyin yi min magana, I'm a human being like everyone else." Da sauri boss ya ɗago da ido ya kalleshi, haƙiƙa yana matuƙar mamakin sauƙin kan prime minister Hateem, tun da yake arayuwarshi bai ta6a tsammanin akwai wata rana wadda zato zo har ya sami damar ganawa da shugaban ƙasar Nigeria sai gashi cikin ikon Allah ya haɗu da mutun bai ruƙe da babban muƙami na shugaban ƙasar canada ƙasar da tana ɗaya cikin Manyan ƙasashen duniya da suke da tarin jama'a da wadatar arziƙi... Yayi zurfi acikin tunaninshi muryar prime minister ta katse shi"kayi shiru baka ce komai ba," Sosa ƙeya ya ɗanyi da hannunshi kafin ya furta"am....dama yalla6ai tambayace nakeso nayi maka idan ka bani dama, amma dan Allah kada ka ɗauka da wata manufa" Da fara'a akan fuskar Hateem Yace"kada hakan ya dame ka, Nifa ɗan siyasane, tambayoyi har marasa kan gado ƴan jarida sunayi min kuma in basu amsa dai dai dasu, ballanta kuma kai dana yaba da hankalin ka, duk mutumin da Owais ya yarda dashi toh nima na yarda dashi, don haka kada kaji komai na baka damar yi min kowace irin tambaya ce" Ajiyar zuciya boss man ya sauke, har cikin ranshi yaji dadin kalaman prime minister, kuma ya ƙara jin ƙaunar mutumin aranshi. Sai dai duk da haka nauyin shi yake yi, daƙyar ya iya buɗe baki yace"yalla6ai, naji kamar ance baka ta6a haihuwar ɗa namiji ba, ƴa'ƴan biyu duka mata ne shin dagaske ne"? Boss Na ƙare maganar yayi saurin kau da idonshi gefe ɗaya saboda kunyar tambayar da yayi mashi Shiru prime minister ya ɗanyi, na ƴan mintuna yana maimaita maganar taj acikin zuciyarshi, yayin da yake kallon fuskar danish "Am sorry Sir, idan tambayata ta 6ata maka rai" acewar Tajj. Calmly Hateem Ya soma magana ba tare da ya kau idon shi daga kan fuskar Danish ba. "Ka fama min raunin da yake kwance acikin zuciyata, tsawon shekaru da suka gabata, bana son tuna haukan da nayi, da hawayen dana zubar, da kuma ƙunci da raɗaɗin dana fuskanta saboda rashin da nayi na abun da na ƙwallafawa rai........" tuni yanayin fuskarshi ya canza zuwa matsananciyar damuwa, yayin da yake yin maganar farin ruwane kwance acikin fararen idanuwanshi. Hatta tajj dake sauraronshi, Jikinshi yayi mugun yin sanyi tunkafin Ya ƙarasa jin zancen nashi Numfasawa prime minister yayi before saying"I've lost so much that I still haven't forgotten him. I loved him more than I love my children now, and I've never stopped missing him. I know if I tell you that, you'll think it's crazy." He said it with a smile on his face. ("nayi babban rashi da har yau bana manta shi, inason shi fiye da ƴa'ƴan da nake dasu a yanzu, kuma har yau ban ta6a cire shi araina ba, nasan idan na faɗa maka zaka ji abun wani iri" ya faɗa fuskarshi da murmushi.) "Bayan gimbiya mujeedat ta yi haihuwa ta biyu ta haifi Yazrin, a ƙalla ta ɗauki shekaru bata sake haihuwa ba, tunda Allah ya bani ƴan mata har biyu, sai na ƙwallafa rai ga son samun ɗa Namiji har tsakar dare inayin nafilfili akan Allah ya bani ɗa namiji, cikin ikon Allah a lokacin da banyi tsammani ba, Allah ya kar6i addu'ata, Matata ta samu ciki a daren ranar ko runtsawa banyi ba.. though I wasn't sure if it was a girl or a boy, nidai kawai nasanyawa raina namiji ne.." dakatawa yaɗan yi da yin maganar, tajj ya natsu yana sauraronshi, tun yana daga tsaye har dai yakai ga janyo kujerar gaban mirror ya ajiyeta daga gefen gadon ya zauna yana kallon prime minister. Cigaba da magana yayi"tun kafin a haife shi na fidda mashi suna, na tsara mashi kalar rayuwar jin daɗin da zaiyi, hatta makarantar da zan sanya shi da komai ma na rayuwarshi sai da na rubuta a diary din dana ajiye domin shi kawai, ita kanta gimbiyata mamaki ta dinga yi ganin yadda na haukace akan son abunda ke acikinta, har fadi take yi na fahimci kafi sonshi akan sauran yaran dana haifa maka, idan ta fadi hakan sai dai nayi murmushi, ba ita kadai ba hatta family dina na Canada dana Nigeria sai da suka shaida ƙaunar dana ke yi mashi, duk rana ta Allah saina kirasu awaya nace su tayani da addu'a Allah ya sauki matana lafiya, saida na addabi kowa da zancen cikinta, mahaifina har tsakar dare nake tada shi daga bacci ince mashi ya tashi yayi nafila ya taya matana da addu'a......" shiru ya ɗanyi idanuwanshi akan agogon hannunshi. Tajj duk ya ƙagara da sonjin ƙarashen zancen. "Ban ta6a kawowa raina cewa yaron zaizo duniya amace ko zai mutu bayan an haife shi, kana Naka Allah Yana nashi, sai gashi an haife shi babu rai, wallahi bazan iya misalta haukan da nayi ba a asibitin da ta haihu, likitan daya fara furta mun zancen an haifi yarona babu rai da hannu biyu na cakumi wuyan rigarshi na shaƙe shi tamkar zan kashe shi daƙyar dangina suka raba ni dashi, na dinga yi masu sambatu ina fadin karya sukeyi min ni yarona bai mutu ba da ranshi, daga ni har mahaifiyarshi ba'a bari munganshi ba, ita bata acikin hayyacinta bacci takeyi, ni kuma an hana in ganshi gudun kada in haukace masu saboda sun fahimci na mutu akan ƙaunarsa, tun bayan 2 weeks da faruwar lamarin, Ina kwance gadon asibiti Ina jinyar zuciyata, duk na fita hayyacina sai sambatu nake yi ina fadin ina yarona baba kana gani za'a raba ni dashi, ni nasan ɗana bai mutu ba, baba ina jin bugun zuciyarshi acikin zuciyata, ire iren kalaman da nake fadi masu ba ƙaramin raunata masu zuciya nayi ba, babu wanda bai zubar min da kwalla ba, haka suka dinga lallashina sunayi min nasiha, daƙyar suka shawo kaina har suka samu na haƙura nabarma Allah komai sai gashi yanzu tamkar ba'ayi ba" Prime minister Hateem ya ƙare maganar yayin da hawaye ke ƙoƙarin gangarowa saman kuncinshi, da sauri boss man yayi saurin share mashi hawayen don bazai juri ganin babban mutun kamar prime minister yana zubar da hawayensa akan idonsa. "Nayi kuskure dana yi maka tambayar nan, ka gafarceni yalla6ai, ni kaina jikina yayi sanyi kuma banji daɗin yanayin da na jefa ka ba, da ace nasan maganata zata fama maka raunin dake acikin zuciyarka wallahi daban furtata ba" cikin sanyin murya murya Boss man Yayi maganar. Cikin karyayyar murya yace"kada ka damu, ay yanzu komai ya riga daya wuce," Ƙarfin hali taj yayi wurin furta"yalla6ai ko zan Iya sanin sunan baby boy din da ka rasa" He smiled a little before saying, "Sunanshi *OMAIR BIN HATEEM OBINNA* wannan shine sunan da nayi niyar sanya mashi, Allah bai nufa ba" Maimaita sunan taj yayi"suna mai daɗi, ubangiji Allah ya baka mafiyin abunda ka rasa, In sha Allah zan tayaka da addu'a" "Nagode sosai" "Yalla6ai, zan fada maka wani abu, ni tunda nake arayuwata ban ta6a ganin mutun mai babban muƙami mara girman kai irin ka, A yanzu haka da muke yin magana sai nake jin tamkar a mafarki ne Murmushin gefen fuska prime minister ya saki jin abunda taj yace. "Ba kai kaɗai ba, mutane dayawa suna mamakin halina, ni ta inda na banbanta da sauran, bani da girman kai, kuma bana ɗaukar kaina wani, duk idan na tuna cewa mu dukkanmu bayin Allah ne, kuma babu wanda yafi wani awurinshi sai wanda yafi jin tsoronshi sai in ƙara jin ni ba wani bane, idan na shiga cikin takalawa sai in manta wanene ni, zan saki jiki dasu muyi mu'amala tamkar bani da ko sisi, haka zalika idan na shiga cikin masu kuɗi sai inji dai dai nake da su, yanzu haka da nake atare dakai, kallon aboki nake yi maka" zaro ido taj yayi fuskar shi da alamun mamaki. "Ni kuma yalla6ai" Ɗaga mashi kai hateem yayi alamar eh, wani irin farin cikine ya lullu6e Taj sai faman sakin murmushi yake yi jin prime minister ya kira shi da sunan aboki. A hankali Hateem Ya mayar da idanuwanshi kan fuskar Danish, ya miƙa hannu ya shafi gefen fuskarshi. "Allah ya jarabceni da ƙaunarka, Ina fata ka zama alkhairi arayuwata, zan cigaba da yi maka addu'a Allah Ya baka lafiya, bana so in koma ƙasar canada batare da ka buɗe idanuwanka kayi tozali dani ba" cikin sanyin mirya ya ƙare maganar, ba zato ba tsammani yaji saukar yatsun hannun danish acikin nashi wata irin cakuma yayi ma hannun prime minister ya ƙanƙame shi, hankalin Taj ba ƙaramin tashi yayi ba, har ya yunƙura zai raba hannun Danish daga ruƙon da yayi ma Hateem, da sauri ya girgiza mashi kai alamar a'a, komawa yayi ya zauna still hankalin shi bai kwanta ba, idanun shi akan hannayensu dake harɗe cikin na juna, lamarin yayi mugun ɗaure mashi kai ganin mutumin da ko yatsan shi bai iya ɗagawa amma yayi ƙarfin halin ruƙe hannun mai girma Hateem. Tun da ya kafe hannun Danish dake a ruƙe da nashi da ido, bai ko ƙyafta ba, wani irin yanayi yake ji atattare dashi mara misaltuwa, ga wani bugu da zuciyarshi take yi mashi, gaba ɗaya ya shagala da kallon hannayensu na tsawon awa batare daya ankara da gudun da lokaci ke yi ba Motsin buɗe ƙofar ɗakinne Yaja hankalin boss ga kallon mai shigowa, Chief Owais ne Yake nufo su cikin shiga ta tsadaddun suit launin ash colour, wani irin sanyayyan ƙamshin turarene ke fita daga jikinsa, tunkafin Ya ƙarasa garesu idanuwanshi suka sauka akan hannayen prime minister dake a ruƙe dana Garkuwa, walking gently ya nufi bakin gadon ya ɗan dakata da yin tafiya, miƙewa Boss yayi tare da sarah mashi. "Uncle am ready, yakamata mu tafi suna jiran mu, tun ɗazu suke kira awaya" tamkar baisan furta maganar yayi ta. Shiru babu alamun prime minister zai amsa mashi. Boss man ne yace"Sir, wani abu ne ya faru wanda ya ɗaure mana kai, yanzun nan kafin ka shigo Danish Ya damƙi hannun prime minister Ya ruƙe shi sosai, ina da tabbacin shine dalilin dayasa ya shiga yanayin nan" Ɗage girarsa yai alamar yaɗanyi mamaki kafin ya furta"Okey, kayi mashi magana ta yadda zai ji ka" Boss ya amsa da toh, sannan ya je daga gefen prime minister yadan russina tare da cewa"Yalla6ai, Chief Ya shigo Yana son yin magana dakai" Tamakar bazai ɗago ba, A ƙalla sai da ya ƙara mintuna biyar cuf tukunna A hankali Ya dago da fararen idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur da su tamkar mai fama da ciwon ido. Zagayowa chief yayi ta 6angaren da prime minister yake a zaune Ya tsaya yana duban fuskarshi. 'Uncle are you okey," ya tambayane ganin yadda idanuwanshi suka yi ja. Can ƙasan maƙoshi sound din muryarshi ke fita"Owais, kaga yadda ya ruƙe min hannuna? meaning, he feels what I feel about him." "Uncle, don't let that bother you, zamu dawo ne anjima sai ka ƙara duba shi. Jinjina mashi kai yai ba tare daya furta komai ba, shi kanshi chief yana mai al'ajabin ƙaunar da Uncle Hateem ya ke ma Danish. Ganin yaƙi sakin hannun Danish, yasa shi sake furta"uncle, we ave to go" Magana chief yakeyi mashi amma gaba ɗaya hankalinshi na akan danish, ganin babu alamun zai motsa yasa chief, ruƙo hannunshi cikin kulawa yai mashi alamar ya tashi su tafi, yunƙura prime minister yayi da niyar ya miƙe daga saman gadon sai dai wani iko na Allah Danish Yaƙi bari ya raba hannun shi da nashi. Muryar mai girma Hateem na rawa ya furta"My son, Yaron nan Yaƙi sakin hannuna, baison in tafi nabar shi" "Uncle, kada hakan ya dame ka" chief ya faɗa, tare dakai hannu ya damƙi hanun danish daƙyar ya 6an6areshi daga ruƙon da yayi ma hannun hateem, shatun akaifun danish har saman fatar hannun prime minister, wurin yayi ja. Hakan ya sosa ran Chief Owais, baiji daɗin yakushin da Danish yayi mashi ba, shi kuwa Hateem ko kaɗan baiji zafi ba, baima lura da yakushin ba. Chief da boss ne suka kwantar da Danish, tare da lullu6a mashi bargo har saman ƙirjinshi, kafin suka bar ɗakin, bawan Allah prime minister yana tafiya yana waiwayon ɗakin, gani yake kamar idan ya tafi bazai ƙara ganin shi ba. __________________________✍️ BARI MU ƊAN KOMA BAYA MUJI MEKE FARUWA A 6ANGAREN SU ARMY BOY DA TIGER. Bayan Gari Ya waye suna akwance Saman Sofa, sun saki baki da hanci suna sharar bacci, ba zato ba tsammani Muryar Khadeeja ta farkar da su, Daga can saman bene ta kware murya da ƙarfi tana fadin"Wayyo Allah, Mayu sun kwanar mana agidanmu, wai ku ba zaku tafi gidan ubanku ba" A firgice Suka farka suna faman mutsustsuke idanuwansu, kafin suka kalle ta, a lokacin harta nufi bene tana saukowa down, Sumar kanta a hargitse babu kayan mutunci a jikinta Rigar baccin jiyace bata cire ta ba, dai dai gwiwarta rigar ta tsaya mata, hannunta ɗaya ruƙe da qugunta, ta dambara janbaki saman la66anta har kan kumatunta, ga wani man baki data shafa sai ƙyalli yake yi. Kallon juna su ka yi fuskarsu babu walwala, Army boy yace"Allah ya wadaran naka Ya lalace wannan masifaffiyar yarinyar Allah Yayi mana maganinta, saboda jaraba baccin ma bazata bari mu ƙarasa shi cikin dadin rai ba, Ni dai harga Allah an takura min, yakamata sir ya bamu iznin komawa gida" Takaici Ya hana Tiger cewa komai, Jira yake kawai Ta ƙaraso Yaji me zatace masu Da gudu ƴan uwanta suka fito daga ɗakunansu, suka biyo bayanta, A tsakankanin sofas din khadeeja ta dakata da yin tafiyar tana jifarsu da matsiyacin Kallo Tace"mayu masu cinye ma mutane abincinsu, Yanzu sai ku girka mana abunda zamu ci" zaro ido su ka yi suna kallonta. Mamaki take basu, A iya sanin su dayawa mata suna jin shakkar sojoji amma ita wannan mai kunnan zoman babu alamun tsoronsu a fuskarta. Tsawa Army boy Ya daka mata"ke karki kuskura ki ƙara kiran mu da sunan mayu idan ba haka ba zan harbe ki da bindiga" maimakon taji tsoron maganarshi saita galla mashi harara tana fadin"Ai wallahi sai kun girka mana abun da zamu ci, tunda kuka cinye mana sauran abincinmu na jiya" Dafa kafadarta hawwa tayi"dan Allah ki ƙyalesu, Ki zo mu koma ɗaki, ki yi wanka ki canza kayan jikinki," murguɗa mata baki tayi"ni babu inda zanje, wallahi sai sun girka mana abincin da zamu ci, saboda Yunwa nake ji" Girgiza kai sojojin sukayi suna kallonta kafin suka kalli sauran ƴan uwan nata, "Jiya bamu samu damar Yin magana daku ba, muna fata kun tashi lafiya" Atare suka hada baki wurin amsa masu da lafiyalou" Tiger Yace"Ku fada mana sunayenku muna son ji" Namijin cikinsu ne Ya fara Yin magana. "ni sunana MUBEEN" Jinjina kai tiger yayi"Ke fa" Ya nuna Macan dake a gefenshi, Fara ce sol tana da kumatu da ƴar kiba "RUBINA" "Suna mai daɗi, Kefa mai idanuwan ƴan chaina, ya fada da zolaya yana nuna ta gefen rubina "YASMIN SUNANA" "Good Girl, and You " Da ido Ya nuna Ƴan matan dake ruke da hannun junansu ɗaya Doguwa ɗaya madaidaiciya "Ni sunana Hibba ita kuma Sarah" "Masha Allah, Naji dadin haduwa daku, Allah yayi ma rayuwarku albarka" amsa mashi sukayi da ameen Khadeeja masifaffiya tace"ƙwarama da baku tambaye ni sunana ba, don ba fada maku zanyi ba" murmushi suka saki ba tare da sunce mata ƙala ba. Bubbuga ƙafafuwanta tayi"ni dai yunwa nake ji, ku tashi ku shiga kitchen ku girka mana abinci" Army yace"bamu Iya girki ba, Ko kin ganmu da zannuwane ɗaure a ƙugunmu? Harara ta watsa mashi Tiger yace"Yar uwa khadeeja, baku da maiyi baku girkine a gidan"? Hawwa ce ta bashi amsa da cewa"yayanmu salsabeel shine yake girka mana abinci" Zaro ido Tiger yayi"kina nufin wannan ƙaton mutumin"? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh Sarah tace"ba koda yaushe yake girka mana abinci ba, yaya omar yana kawo mana daga gidan su," sun gane wa take nufi, wato Big guy shi ne suke kira da Asalin sunan shi Umar. Kallon agogo Army boy yai a lokacin ƙarfe goma sha biyu na safe. "Da alama sun manta yau basu kawo maku abincin da wuri ba, Ya za'ai kenan"? Da sauri Mubeen Yace'ai akwai yogurt da madara a frigde, hada bread a store, Idan muna jin yunwa kafin akawo mana abinci su muke ɗauka mu ci," Ran khadeeja Ya gama 6aci, Bubbuga ƙafafuwanta tayi hankalinsu ya dawo kanta, idanuwanta rufe ta soma zazzaga masu masifa tana fadin"ni wlh bazansha yogurt da bready ba, ai kune kuka cinye mana sauran abincinmu a kitchen, wlh idan baku je kun girma min abunda nakeso ba zan kira yaya Omar awaya in fada mashi kun ci mana abincin mu" Aruɗe suka hada baki suna fadin"Me yai zafi, Kinji munce bazamu girka maki ba ne? Nuna masu hanyar kitchen tayi da hannunta"ku tashi ku shiga ku dafa min abinci" Agajiye suka miƙe tayi gaba suka bi bayanta sune har cikin kitchen. Ƴan uwan dake a falo, saman sofa suka zauna, su kansu ba zasu Iya da rigimar khadeeja ba, Sara ce ta ɗauko masu Robobin madara, Ta miƙa ma kowan nan su, suka zauna suna sha Daga falo suna jiyo sautin muryar khadeeja dake acikin kitchen. "wainar kwai zaku soya min" ta fada tare da buɗe kofar store ta dauko masu egg container ta kawo masu shi akan Countertop ta daura shi. Cikin kwantar da murya Tiger yace"khadeeja wannan kwan yayi maki yawa ina laifin a soya maki biyar" harara ta galla mashi"ai bani kadai zanci ba, hada Ƴan uwana suma suna jin yunwar" roba ta ɗauko masu inda zasu kaɗa kwan hada abun kaɗawar, Kafin ta nufi freezer tana fadin"hada Chicken pepper soup zaku yi mana, Sannan Ku soya mana kifi mubeen yana son ci" Bin ta da kallo su ka yi baku nan su a buɗe kamar sakarkaru haka suka bi ta da kallo. Kaji ta ɗauko Guda Uku Manya manya masu tsokoki ajikinsu ta ajiye masu Tace"chicken peper soup zakuyi mana, akwai kayan miya da kayan ƙamshi duk zan ɗauko maku su" hankalinta kwance takeyi masu magana, har wani ƙyafkyafta masu idanu takeyi. Daƙyar tiger ya iya bude baki yace"Yar uwa khadeeja, bakomai muka Iya girkawa ba, Kuma wannan abincin yayi yawa, ga kwai ga kuma kaji"? Zum6ura mashi baki tayi"wanda yasa kuka cinye mana abincin mu na jiya," ta faɗa tare da juya masu baya ta nufi cikin store, gabansu har faɗuwa yake yi, Jim kaɗan ta dawo hannunta ruƙe da Manya manyan doyoyi guda uku ta ajiye masu aƙasa tana faman yin nishi tace"idan kun gama girka wadannan saiku fere doyar ku soya mana ita da kwai" Baki abuɗe suke sauraronta Komawa cikin store tayi sai gata ta kuma dawowa hannunta ɗauke da ƙaramar roba, dankalin turawane acikinta "Chips zaku soya mana da shi" ta ajiye robar, har ta juya zata koma Army boy yayi saurin shan gabanta, Muryarshi a tausashe Yace"khadeeja, Ya isa haka, wai ke meke damunki? Mu fa mazane ba mata ba, bamu Iya girki ba, Bindigogi muka Iya ruƙewa, taya zaki kwaso wannan uban kayan abincin kice mu girka maki"? Fashe mashi tayi da kuka tana bubbuga ƙafa tace"wallahi idan baku girka ba saina fada ma Yaya omar kun cinye mana abinci, Kuma In ƙala maku sharrin kun ta6ani" Waro ido waje su kayi har saida gabansu Ya fadi jin abunda tace, Ita kanta da tayi maganar bada wata manufa ta furta ta ba. Lallashinta suka soma yi"shikenan, Munji zamu girka maki, Yanzu ki koma falo ki zauna, ashagwa6e tace toh, kuma zan dinga leƙowa ina duba ku" amsa mata sukayi da toh Bayan fitarta daga kitchen din tiger yace"Allahumma ajirni filmusibati wa aklikni khairan min ha, Yarinyar nan ba ƙaramar makira bace" Army boy yace'ai duk laifinka ne, kaine jiya kasa na kwaso masu abincinsu da duk hakan bata faru ba, yanzu gashi ta daura mana wannan uban aikin" "Idan laifina ne kaima hada laifinka ai, tunda atare muka cinye masu abincinsu" Ran kowan nan su Ya 6aci, tamakar zasu rufe juna da bugu "Faɗa ku ke yi ko"? Muryar Khadeeja ce ta fargar dasu, arude suka hada baki wurin fadin"A'a aunty, Muna yanke shawarane akan meya kamata mu fara girkawa" Murmushi ta saki har dimple dinta Ya lotsa, Hannunta ɗaya ruƙe da Robar milk da take sha. "Idan ma faɗa ku ke yi ku kuka sani, Nidai ina jiran abinci, kuma wallahi Kafin In shanye madarar nan ku gama min girki na, idan ba haka ba hmmmm kunsan sauran" Ta fada tare da juyawa ta fuce daga kitchen din. Army ya ɗaura hannayenshi biyu saman kanshi"mun shiga uku, wannan wata irin bakar rana ce"? Tiger yace"Ba surutu Ya kamata mu tsaya muna yi ba, Mu fara mata girkin kada ta shanye madarar" Tu6e rigunansu sukayi, Ya rage saura wandunan kakinsu a jikinsu, sham sun manta da bindigogin su da suka ajiye afalo. Kamar mata haka suka fara aikace aikace, wanke nama, Fere doya, Gyaran cefane, da yankan kayan lambu suna haɗa uban gumi zufa ta ko'ina, da waya sukeyin amfani wurin yin browsing yadda akeyin chicken paper soup da sauran abunda basu Iyaba, duk bayan ƴan mintuna sai khadeeja ta leƙo kitchen don taga idan suna yin aikin yadda ya kamata, bayin Allah kamar ba sojoji ba, ta takura masu ta addabi rayuwarsu Yayin da take zaune a falo cikin ƴan uwanta, Hawwa tace"khaeeja baki kyauta masu ba, dan Allah Ki yafe masu aikin yayi masu yawa" Gatsina mata hanci tayi batare da ta tanka mata ba Sarah taja guntun tsoki tana kallonta tace"kinji haushin rayuwarki, kuma wallahi saina fada ma Yaya Jazz abunda kika yi masu" Banza tayi dasu tamkar bata ji me suke fadi ba, Yasmin tace"please ku daina yi mata magana, Itama bayin kanta bane, Lalurace Yaya jazz fa yace mu runka hakuri da yar uwarmu" Hibba tace"duk da haka halintane, Deeja tafiye rashin jin magana, bata da haƙuri, saina fada ma Yaya salsabeel" Duk wanda yayi magana saita kalli la66ansa Robar yogurt din dake a hannunta ta ajiye kan carpet, Ta yunƙura ta miƙe tana yin miƙa, duk suka bita da ido, bindigar da ta gani sakon kujera takai hannu ta dauka ta saita su da ita tana fadin"wallahi dukan ku sai kun mutu, banzaye kawai, Har ni zaku dinga yi ma faɗa" Dariya suka saki gaba ɗayan su, saboda basu san meye amfanin bindigar ba. Hawwa tace"dalla malama Ajiyeta a ƙasa, Kada ki lalata masu abunsu" Harara ta watsa mata tana faman cije la66a tace"ta kanki zan fara hawwa Jiya Hada kulleni adaki don kada In futo waje, yau idan na kashe ki bazaki sake Yi min haka ba Tana ƙare maganar ta daddage ta ruƙe bindigar dakyau, Tana ƙoƙarin harbawa, Mubeen yayi saurin Janyo Hawwa gefe daya, ba zato ba tsammani harsashin bindigar Ya harbi jikin kujarar inda Hawwa take zaune, Wani irin Hayaƙi ya fita Wurin da bullet din ya shiga nan take ya fashe.(😳) Nan fa ido Ya raina fata, Gaba ɗayansu sun rude sun gigice, Amatuƙar firgice suka mimmiƙe tsaye suna faman zare idanuwansu Dariya tasaki tana fadin"kunyi tunanin bansan yadda akeyin amfani da ita ba ko? To ai na ta6a ganin video a wayar Ya omar, wasu suna kakkashe mugaye da ita, ɗaya bayan ɗaya kuma zan kashe ku yanzun nan" Ta faɗa Tana saita su da ita, fashewa sukayi da kuka suna yi mata magiya, saboda rashin hankali Ta kara sakin wani harsashin kaitsaye ya sauka a tsakankanin ƙafafuwan Rubina, Baiwar Allah Kuka hada majina, sauƙin ma bai ta6a fatar ta ba. Maza suna a kitchen suna girki, sun bar psycho afalo tana aiki, duk irin girman sautin harbin bindiga basu ji ba, Mubeen Ne ya watso da gudu Ya shigo kitchen din ya ɗaga murya Yace"ga khadeeja can ta daukar maku abunku tana harbin mu" gabansu ne yayi wani irin mugun faduwa, aguje suka fito daga kitchen din adai dai lokaci ta saita kan Sarah jikinta sai kerma yakeyi Tsawa Tiger Ya daka Mata, da sauri Ta juyo da bindigar ta saitasu tana dariya tace"Ajalin ku ne ya fito daku daga kitchen, dama haushinku nake ji, Jiya kunkashe min jazz dina" Hankalinsu idan yai dubu toh Ya tashi, Khadeeja ta saka su a tsaka Mai wuya, Ga girki sun baro a kitchen Ga wani tashin hankalin dayafi gigitasu Dole suka zube kan gwiwowinsu muryoyin su na rawa suke yi mata magiya"dan Allah Anty khadeeja ki rufa mana asiri, wlh bamu kashe maki jazz dinki ba, Yana nan da ranshi, yaji sauƙi raunin jikinshi ya warke, Ki taimaki rayuwarmu ki ajiye bindigarnan aƙasa....." tamkar zasu fashe da kuka haka suka dinga roƙonta, zuciyarta kamar ta kafuran farko babu alamun sassauci tace "Nafa san me nake Yi, baku isa ku raina min wayau ba, Idan dagaske Ya jazz bai mutu ba toh Yana ina"? Fuska amarairaice Army boy yace"Yana asibiti, likitoci suna duba lafiyarshi," Ƙasa ƙasa da murya Tiger yai mashi raɗa"kai dole fa mu nemi mafita wallahi, Idan ba haka ba zata Iya kashe mu ko ta kashe ƴan uwanta tun da ba hankali gareta ba, ga kuma Abinci mun bari kan gass" Army boy yace"to ya zamuyi! Ni wallahi komai ya kwance min," "Gulmata kukeyi koh"? Ta fada tana jifarsu da harara Atare suka girgiza mata kai alamar eh, tace"idan ma gulmata kukeyi daga yau Idan na kashe ku bazaku sake yi ba" "Ku lallashi yar uwarku, zata Iya ja mana bala'e daga mu har ku" Tiger ne yayi maganar Yana kallonsu Hawwa. Duk wanda yayi yunkurin buɗe baki zai bata haƙuri da bindiga take saita shi, Kwatsam Wayar Tiger Ta soma Yin ringing, adabarbarce ya zura hannu ya zarota daga aljihun wandonshi, duk sun rude, ganin sunan Major ya bayyana ne yasa hankalinsu Ya ɗan kwanta, Picking call din yayi tare da kara wayar akunne Ko sallamar major bai amsa ba, Ya furta"Jazz Ya Jikin Naka"? On the other hand Muryar Major da alamun mamaki yace"Jazz Kuma? Baka ga sunan wanda Ya kira ka bane"? Tiger bai kula maganarshi ba yaci gaba da fadin"Kamar ka sani tun safe khadeeja take son Yin magana dakai, Ai saida na fada mata baka mutu ba lafiyarka ƙalou amma taki jin maganata" Tun da ya ambaci sunan Jazz khadeeja ta jefar da bindigar kan carpet, ta nufe shi tana fadin"Bani shi muyi magana" jiki na 6ari Army yayi saurin Miƙewa ya damƙi ƙeyarta yana fadin"bashi bane don ubanki, Har mu zakija ma bala'e, masifaffiya kawai, Kin bi kin ƙuntata rayuwurmu kin hanamu sakat, wlh baki isa ba, Aɗaki zan kulle ki," kuka tadinga yi mashi tana zagin shi, ɗaukarta yayi ya nufi saman bene da ita, Daki ya shigar da ita ya kwantar saman gado, Ya fito da sauri yaja ƙofar Ya datse ta da mukullin daya gani ajikin ƙofar, Ajiyar zuciya ya sauke kafin Ya nufi falon, A lokacin Tiger Ya kammala yin wayar da major, Ya miƙe dasauri Yaje ya dauki bindigar ya hada da ɗayar da suka ajiye kan sofa, duka biyun Ya turasu karkashin dining table Kallon sauran yaran su ka yi"ku koma ku zauna Yanzu zamu kawo maku abincin" amsa masu sukayi da toh, Jiki asanyaye suka zauna duk basu ji dadin abunda khadeeja ta aikata ma sojojin ba "Dan Allah kuyi hakuri Idan mun 6ata maku rai" sarah ce tayi masu maganar Murmushin yaƙe suka sakar mata"kada ku damu, ai munyi maganinta yanzu" juyawa sukayi atare suka nufi kitchen, abun da suka daura kan gass harya fara ƙonewa shaf shaf suka ƙarasa Yin girkin. Khadeeja dake adaki, Sai kuka takeyi tana bubbuga ƙofa da hannunta kamar zata 6alleta, sumar kanta duk ta rufe fuskarta Gajiya tafara Yi da buga ƙofar, Ta Juya zata je ta kwanta karaf idanuwanta suka sauka akan Wayar dr jazz da suka bari kasa, Ga kayanshi daya bari riga da wandon shadda, jiki na 6ari taje ta dauki wayar, duk da bata Iya amfani da ita ba sai da tayi ƙoƙarin kunnata, saboda ta haddace Yadda jazz yake latsawa agabanta, Cikin sa'a ta kunna wayar haskenta Ya kawo, Gefen gado ta zauna tana yin shessheƙar kuka Ta soma kacaccala mashi wayar, kasancewar babu password a wayar Yasa ta samu damar dannata son ranta, batare da saninta ba ta shigar mashi contact dinsa adai dai kan sunan My Mom ta latsa Kira, Ringin wayar ta fara Yi, Khadeeja ta natsu tana jiran jin wazai Yi magana kamar yadda taga Ana yin amfani da ita ayi communicating Kiran wayane Ya shigo layin Mom turai, a lokacin tana acikin bedroom dinta ita da sir mubarak akwance saman gado, ita kadai ce idonta biyu, shi Sir mubarak Ramuwar baccin dabaiyi ba jiya yake Yi. Jin wayarta na ruri ne Yasa ta sauko daga kan gado, taje gaban mirror ta duba sunan mai kiranta Mamakin ƙarara akan fuskarta ganin sunan My Own Son Ya bayyana akan screen din wayarta Murmushi tadan saki tana fadin"Allah Sarki My son, Ciwo Ya hana kazo inda nike shiyasa ka kirani awaya, bari Naji me Yake buƙata" ta faɗa tare da ɗaga wayar ta kara a kunnanta, hada ƙoƙarin yin sallama. Shessheƙar kukan Khadeeja ne Ya fara cika kunnanta, Zaro ido waje turai tayi muryarta da alamun ruɗani ta furta"Wacece ke kuka"? *Daga Alƙalamin Boss Bature🫶* *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura* 3196407426 First bank Bature Hafsat Muhammad, *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida* _~*✊💋BOSS LADIES WRITERS✊💋✊*~_ _🔥💫THE PRISONERS🔥💫_ ~TAKUN ƘARSHE~ Daga Alƙalamin Boss Bature Dedicated To Aunty Kubra💋 _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty❤._ _______________________✍️ Shessheƙar kukan Khadeeja ne Ya fara cika kunnanta, Zaro ido waje turai tayi muryarta da alamun ruɗani ta furta"Wacece ke kuka"? "Khadeeja ce, Ina Jazz ɗina Yake" kafin Turai ta bata amsa kiran Ya katse, abun ya ɗaure mata kai, Ya akai wayar Jazz taje hannun mace? Maimaita sunan khadeeja tayi aranta kafin da sauri ta fito daga dakin ta nufi bedroom dinsa. A lokacin suna daga zaune gefen gadon shi, Shi da Ibad dake bashi abinci abaki, hannun ibad ruƙe da plate with spoon, har yayi wanka ya sanya jallabiya a jikin shi. Shigowa mom Turai tayi dakin gaba daya suka dago suna kallonta. Ajiyar zuciya ta sauke fuskarta da fara'a ta ce"My son, how's your body? I hope you're getting better now." In a cool voice yace"Mom da sauki, ina samun kulawa a wurin ƴan uwana, yaya Zaki ma bai jima da fita ba" Murmushi tasaki tana kallon Ibad tace"our last born, Sannu da ƙoƙari, kana Ji da ɗan uwan nan naka" Ta6e baki yayi kafin yace"to ya zanyi mommy, daddy ya 6allo mana aikin Jinya, Yana can kwance Kinyi mashi wanka Yana bacci, Ya ya Zaki kuma ya gudu ya barni da aikin bashi abinci abaki" Tuntsirewa tayi da dariya, shima jazz ɗin dariyar yake Yi, shi kuwa ko ajikin shi bilhakki dagaske Yake Yin maganarshi. Tsagaiwata tayi da yin dariyar tace"Ibad na fahimci maganata ta tsaya maka aranka, Nifa ba daddynku nayi ma wanka ba, Taimaka mashi nayi ya rage kayan jikin shi, idan ba haka ba ni taya zan Iya yi ma shi wanka ƙato dashi, Kallarni ka gani Ƴar ƙarama dani" hura mata hanci yayi batare da yace komai ba "Jazz where's your phone"? Ta faɗa tana kallon shi. He was silent for a while, Yana ƙoƙarin tuna inda Yabarta. "Mom, kamar nabarta a gidan Yaran da nake Kula da lafiyarsu" Miƙa mashi wayar tayi"Duba ka gani, wata yarinya ta kira da layinka, tana kuka, wai jazz dinta take nema" Da mamaki akan fuskarshi Ya kar6i wayar, Yana duban Kiran da akayi da layinshi, tunkafin Ya danna kiran ranshi ya bashi cewar Khadeeja ce. Da sauri Ya kira layin, ringing uku ta ɗauko tana fadin"Ni ku ƙyale ni tun da ba zaku bani muyi magana da Ya jazz ba, kun wani isheni da kira," Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarsa, jin muryar deejan sa, mom turai da Ibad sun tsareshi da ido suna kallon fuskarshi. "Khadeeja ni ne fa" a kwance take kan gado Jin muryarshi Yasa Ta yi zumbur ta miƙe zaune tana fadin"Ya Jazz dama baka mutu ba"? da wani irin farin ciki ta furta maganar. Murmushi ya saki tamkar yana a gabanta yace'ban mutu ba My deeja, lafiyata qalou, Yanzu haka ina agida, wannan layin da kika kira, Na mom ɗina ne" Shagwa6a ta sanya mashi" I hate U ya jazz, Shine ka manta dani, duk nabi na tashi hankalina akanka ashema kana gida" "No, it's not like that, Khadeeja. I miss you. I've been thinking about you tun time din dana dawo hayyaci na" Kallon juna mom Turai da Ibad su ka yi alokaci ɗaya, kafin suka maida dubansu gare shi. "Faɗamin Kin yi breakast da safe kuma kin sha maganinki"? "Ni ban sha uban komai ba, babu wanda ya bani, waɗancan ƙattan da aka bar mana agida jiya suka cinye mana abincin mu, yau kuma na sanya su dole su girka mana, aiko suka shiga kitchen suna yi, basu sani ba na ɗauki bindigarsu nadinga tsoratar dasu hawwa......." hankalinta kwance take kora mashi jawabi, a firgice ya ɗago da ido yana kallon Mommyn su, ga dukkan alamu suna jin maganar da deeja take Yi mashi," Muryarshi a ruɗe ya furta"Dagaske kike ko wasa"? Dariya tasaki kafin tace"Wallahi dagaske nake maka, don ma sun min wayau sun kulleni a ɗaki, ai da tuni na kakkashe su" Zaro Ido Ibad Yayi, Mom Turai tayi dariya, gani su ke yi kamar zolaya ne abun da yarinyar take faɗa ma jazz, shi kuwa yasan zata aika, Fiye da haka ma shiyasa ya ɗauki maganar ta serious. "Khadeeja, Ina fata baki raunata kowa acikinsu ba" "Wlh ban kashe kowa ba, ai na faɗa maka sun ƙwace bindigar" Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke "Dan Allah My baby girl kada ki ƙara yunƙuri ɗaukar bindiga kinji ko? "Toh," "Yawwa ai nasan kina jin magana ta, idan har kina so na zo gidan karki ƙara rashin ji," muryarta a ladab ce tace"In sha Allah" kamar wata mai hankali "Good Girl, Kafin nazo kiyi wanka, Kici abinci ki ƙoshi," tace "Toh" "Namanta ban tambaye ki ba, Where did you find my phone?" "Aɗaki kabarta saman kayanka, nan na ɗauke ta" "Okey, pls Ki ajiye min inta, kada kice zaki yi wasa da ita" "Toh, Idan kazo gida zaka gyara min gashin kaina kuma kayi min kalar kitson kalaban nan da ka ta6a yin min" Da sauri ya ɗago suka hada ido da mom Turai. Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Eyyeh, Lallai ashe Jazz har kitso ka Iya yi ma mace, gama wayar ka bani labari" da zolaya ibad yace "mommy kin huta, da zuwa saloon, daga yanzu Jazz zai dinga yi maki gyaran gashi" miƙa mashi hannu tayi suka tafa kamar wasu abokai. Duƙar da kai Jazz yai"Khadeeja sai anjima, please take care of your self for me" "You too," sallama su ka yi da ita. Kunya duk ta kama shi, sai faman sunnar dakai ƙasa Yake Yi. "Jazz kai muke sauraro ni da mommy" ibad ne yai maganar. Fuskarshi a yamutse ya furta "Khadeeja ce yarinyar da daddy ya baku labarin ta, She's mentally ill. There's no love between us. ina kula da ita ne saboda rashin lafiyarta" mom turai da raha tace "Don't lie to me. I'm your mom and I understand you. Yarinyar nan dai sonta kake Yi" shiru yayi bai ce komai ba, don yasan da wuya ta fahince shi, zolayar shi suka dinga yi tun yana ɗaure fuska har yakai ga sakin dariya. ______________________✍️ A hankali Motar su Ta shigo gidan, bayan jami'in yayi parking, Salsabeel Ya fito daga ciki Yayi mashi sallama kafin ya nufi ƙofar shiga falo. Yana shiga falon ya hango su Hawwa zazzaune kan carpet, An jera masu kayan abinci saman Tray, komai da Khadeeja ta ba sojojin Umarnin su girka masu saida suka girka shi, tun daga kan Chicken pepper soup, fried fish, Chips, wainar kwai, Doya da kwai. Gyaran murya yayi masu tare da buɗe baki Yayi sallama, A hanzarce suka ɗago suna kallonshi, aiko da sauri suka miƙe da sauri hada gudu suka nufeshi, ɗaya bayan ɗaya yake rungumarsu a jikinshi. "Ya salsabeel Ina kaje tun jiya baka dawo ba, Ka tafi kabar mu da kewarka" Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Eyyah am sorry, nima nayi kewarku, ay min afwa wani uziri ne Ya ruƙe ni, amma tunda na dawo yanzu komai ya wuce" Yayi maganar idanuwanshi akan fuskokinsu "Ina Khadeeja"? Nan fa suka haɗa baki suna bashi Labarin Ta'asar da Khadeeja tayi ma sojojin da aka bar masu. Hankalin shi ya ɗan tashi sai dai baiyi mamakin abun da Khadeeja ta aikata masu ba, ya riga daya san halin kayanshi. Jin motsin tafiyar mutane yasa shi saurin kai idonshi inda suke. Fitowarsu kenan daga kitchen, wanke wanke Suka tsaya yi a kitchen din sun gyara komai da suka 6ata, har sun maida suturarsu. Wani ɗan iskan kallo suka watsa ma Salsabeel, Hakan Ya tabbatar mashi da ransu Ya 6aci sun harzuƙa. Tamkar mai jin shakkarsu ya furta"Am...dan Allah Kuyi haƙuri, Yanzu na shigo gidan su Hawwa suke bani labarin abun da khadeeja ta aikata maku, banji dadi ba, Yalla6ai ne bai bani damar dawowa da wuri ba, da duk hakan bata faru ba....." Fuskokin su babu annuri ko miskala zarratin Tiger yace"malam bamu buƙatar Jin komai daga bakin ka, tun da ka dawo gidan falillahil hamdu, Ka ci gaba da kula da ƴa'ƴanka, Mu kaga tafiyar mu sannan duk abun da ka gani badai dai ba kada ka tuhumi kowa, Khadeeja ce sila" Rai a6ace Ya ƙare maganar, Ya nufi Dining table Ya duƙa ya dauko masu bindigoginsu. Army boy yace"Zan baka shawara, Yarinyar nan ku gaggauta kai ta Gidan Mahaukata, can ne Yafi dacewa da ita, Idan ba haka ba wata rana zaku kuka da kanku, don wannan tafi bomb bala'e" Army na kammala yin maganar suka nufi ƙofar fita daga falon, da sauri salsabeel Yabi bayansu yana basu haƙuri. "Dan Allah Ku tsaya, bai kamata muyi irin wannan rabuwar ba, nasan ban kyauta maku ba, amma dan Allah kuyi hakuri kada ku ruƙe mu aranku" Ta6e baki su ka yi, Tiger yace"hmmm bakasan masifar da yarinyar can taso taja mana ba, shiyasa har kake da ƙwarin gwiwar Yi mana magana, Badan Allah Ya kawo mana mafita ba, da yau mu dukan mu zamu baƙunci lahira" Jiki asanyaye Salsabeel Yace"ina ƙara baku hakuri, Allah Ya huci zuciyarku" "Dama ahuce take, bamu hanya mu wuce" matsa masu hanya yayi, duk bai ji ɗadin abun da ya faru da su ba. har suka fuce bai daina bin bayansu da kallo ba. Sai da yajiyo tashin motarsu, tukunna ya sauke ajiyar zuciya, Ya juya ya kalle su Hawwa. "Awani ɗaki suka Kulle ta"? Sarah ce Ta nuna mashi kofar dakin, Azafafe Ya nufi upstairs, Yana isa bakin ƙofar Ya sanya hannu ya murɗa key din. Tsabar 6acin rai ko sallama baiyi ba ya faɗa ɗakin, a gaban mirror ya taras da ita zaune, ta sanya undy ta jashi har saman kirjinta, ga dukkan alamu wanka tayi shine ta zauna tana gyara jikinta kamar wata mai hankali. Gyaran murya yayi mata, zumbur ta miƙe tana faman ƙyafƙyafta idanuwanta, hannayenta biyu ta ɗaura asaman kanta kafin tace "sun faɗa maka abunda na aikata"? Takaici ne Ya ishe shi wato har tasan ta aikata badai badai ba. "Meyasa"! Aɗan tsawace Ya jefa mata tambayar, Ta6e mashi baki tafara yi alamar zata fashe mashi da kuka da sauri Ya zare mata ido haɗi da cewa"Yi min shiru! kar in kuskura Inji kukan ki," da buɗar bakinta sai cewa tayi"ai dama ba ka so na, Kafi son su hawwa, shiyasa kake min fada" sassauta fushin fuskarshi yayi tunawa da karancin hankalinta "Am sorry, raina ne Ya 6aci, bawai bana sonki ba, pls ki daina rashin ji dan Allah" Washe mashi baki tayi "Nadaina, bari na ɗauko maka wayar Ya jazz, na kira shi har mun gaisa ashe bai mutu ba Yana nan da ranshi" ta faɗa tana dariya ta juya ta nufi gado ta dauko wayar taje ta miƙa mashi Yasa hannu Ya kar6a. da mamaki yace "Taya akai ki ka yi waya dashi"? Watsa hannu tayi"nima bansani ba, na daddana saina kira," Call log Ya shiga, numbar farko data bayyana ta Mom turai, Ya danna ma Kira, Bayan ta ɗaga wayar cikin girmamawa salsabeel Ya gaishe da ita, daga bisani Ya tambayeta Ya jikin jazz, tace mashi da sauki, bata tambayi wanene shi ba sai ta ba Jazz wayar suka cigaba da yin magana, Hankalin shi ya kwanta Jin muryarshi raɗau tamkar bai ta6a yin ciwo ba, sun jima suna yin wayar har jazz ya tuna mashi da maganin khadeeja kafin suka yi sallama Ya adana mashi wayar a hannun shi Tattara Yaran yayi a falo, hada shi suka zauna suna kwasar girkin da Su Tiger suka Yi masu, dama da yunwar shi Ya dawo, aikuwa dai sunyi kullu wash rabu hani'an, su mama Tiger An Iya girki, sai santi su ke yi, musamman khadeeja, bakinta dama dama da maiƙo. *🌹ZEENATU🌹* Baiwar Allah, Ta hana zuciyarta sukuni, tun lokacin da tayi masu Benazir la6e a toilet, kunnuwanta suka jiyo mata maganganun da suka tsaya mata aranta, haƙiƙa tayi danasanin sauraransu, don tun safe take faman jinyar zuciyarta, kiri kiri taki cin breakfast dinta, har lunch bata ci ba, yini tayi a cikin bedroom dinta da raɗaɗin abun azuciyarta, Tani tayi ƙoƙarin shawo kanta donta faɗa mata meke damunta taƙi ta sanar da ita, ba irin lallashin da ba ta yi mata ba amma taƙi sakin jikinta. A yanzu haka tana daga kwance saman prayer mat, ta lullu6e jikin ta da dogon hijabinta launin milk, daga gaban dardumar qur'anic stand ne an bude shi alamar karatu take cikin yi bacci yayi awon gaba da ita. Damuwar halin da take aciki Ya hana Tani samun sukuni, fargabanta kada ace wani abunne ke shirin faruwa da ita shiyasa ta canza mata. Shigowa ɗakin tayi domin gyara mata bedroom din, karaf idanuwanta suka sauka akan zeenatu dake ƙudundune tana bacci. Cikin takun sauri Tani ta nufi dardumar, aranta tana fadin'baiwar Allah, daɗina da ita duk halin da zata shiga bata mantawa da yin ibadarta" Zuƙunnawa tayi agaban prayer mat din, muryarta ƙasa kasa ta ambaci sunanta. "Zeenatu! Zeenatu! Ki tashi ki koma kan gado ki kwanta, kwanciya kan prayer mat, bai da amfani jibi yadda ki ka ƙudundune kanki duk kin takure kanki" Tani sai zuba takeyi babu alamun zeenatu zata farka, "Oh Oh ni wannan baccin naki bame ƙarewa bane da alama, dan Allah ki tashi" still bata tanka mata ba. Hannu ta ɗaura saman jikin zeenatu ta bubbugata, nan ma taƙi farkawa, lokaci ɗaya Tani ta fara Jin fargaba acikin zuciyarta, hankalinta yayi mugun tashi, a ruɗe ta ɗaga murya tana ƙwala mata kira da sauti mai karfi"Zeenatu! Zeenatu! Nashiga uku, Wayyo Allahna, meke faruwa dake ne, Zeenatu dan Allah ki tashi" jikinta na rawa ta soma kiciniyar tu6e mata hijabin data ƙudundu ne kanta aciki daƙyar ta samu ta yakice hijabin ta nannaɗeta gefe daya kan darduma, koda Tani ta ɗaura idanuwanta akan jikin zeenatu saida gabanta Ya faɗi, ganin wata irin zufa dake tsastsafo mata ta ko'ina, Rigar jikinta ta manne ma fatarta, sumar kanta kuwa duk ta yamutse babu gyara, shafa wuyanta Tani tayi nan fa taji yaɗauki zafi sosai. A gigice ta miƙe ta watso da gudu ta nufi babban falon gidan, a lokacin Dr shureim Yana daga zaune kan Sofa, Benazir tana a gefenshi, fuskarta ɗauke da murmushi take kallon shureim dake bata labarin ƙuruciyarta. Kamar mahaukaci haka Tani ta nufo su ta zagayo ta gaban Sofas din, kusan atare suka dago suna kallonta da alamun ruɗani akan faces dinsu Dr shureim Yace"Tani! Lafiya? Meke faruwa"? Sai faman yarfa hannu take yi duk tabi ta ruɗe. "Pls ki buɗe baki kiyi mana magana" acewar Benazir, daƙyar ta iya tattara natsuwarta wuri guda, da karfin hali ta furta"Zeenatu ba lafiya! Tana acan daki rai hannun Allah, kwata kwata bata motsi..." kafin ta ƙare maganar, da gudu Dr shureim da Benazir suka nufi part dinta, tsabar sauri mayafin jallabiyar Benazir har faɗuwa yake yi kan kafaɗarta da sauri take sanya hannu ta gyarashi, Tani tana abiye da bayansu. Suna shiga ɗakin idanuwansu suka sauka akan zeenatu dake a kwance magashiyan tamkar bata numfashi. Slowly dr shureim ya zube agabanta kan gwiwowinsa, ya sanya hannayenshi biyu ya tallabo da kanta ya ɗaura saman laps dinsa, Benazir ta zuƙunna gefenshi, fuskokinsu da alamun ruɗu suk soma ambaton sunanta"Zeenatu! Zeenatu"! "Tani, bata da lafiya ne"? Benazir ce ta jefa mata tambayar Muryar Tani tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi ban sani ba nima, yanzu nashigo ɗakin na taras da ita a kwance, nayi tsammanin ko bacci ta ke yi, amma dana kira sunanta na bubbuga jikinta taƙi farkawa nan fa na gane babu lafiya atare da ita" A faɗa ce Benazir tace "Tayaya za ki ce bakisan meke damunta ba? Bayan ke ce kike kula da bedroom dinta" Tani dake kallon Benazir duk tasha jinin jikinta "Bansan ya zanyi maki bayani ba, ba laifi na bane, tun safe nake fama da ita akan ta fadamin meke damunta taƙi ta sanar dani, na rasa gane kanta ta ƙuntata kanta aɗaki, ta hana kanta sukuni yinin yau" hawaye har sun fara sauka kan fuskar Tani. Jiki asanyaye Benazir tace"bari naje na faɗa ma su Mommy abinda ke faruwa" A firgice Tani tayi hanzarin dakatar da ita ta hanyar shan gabanta muryarta na rawa ta ke ambaton" inna lillahi wa inna ilaihirraji'un, dan Allah ki rufa min asiri kada ki faɗa masu abunda ke faruwa, wlh zasu Iya korata daga gidan nan, ba lallai su fahimce ni ba, Alhaji musa baya raga mana akan Zeenatu, Idan yaji wannan maganar babu makawa zai kore ni ne" Cikin rashin fahimtar kalaman Tani, Benazir tace"dan Allah malama ki bani hanya in wuce, kina ganin yarinya babu numfashi sannan ki hana in fadama Iyayenta, hakan bazai yiwu ba dole suji ko dan akira likitan ya duba ta" a tsiwace Benazir tayi maganar, tare da bi ta gefen Tani ta nufi ƙofar fita dakin. Zubewa Tani tayi saman gwiwowinta hannayenta biyu asaman kanta, yayin da hawaye ke yin sintiri akan kuncinta. "Dr shureim nasan kai zaka fahimce ni, dan Allah ka hanata fita daga dakin nan, wallahi idan ta faɗa masu halin da ake ciki, bani kadai zata ja ma bala'e ba, duka ma'aikatan gidan nan zata shafa" Ɗagowa dr shureim yayi, launin idanuwanshi har sun canza kala, muryarshi adidashe Ya ambaci sunan benazir, Harta ɗaga ƙafa zata ƙetare kofar ɗakin tayi saurin cin burki jin kiran shureim. Juyowa tayi miryarta da faɗa tace"yaya shurem kada ka biyewa matar nan, akan me zata hana afada masu halin da ƴarsu take aciki, so kike mu rufa maki asiri, mu zuba ido muna ganin yarinya bata motsi har wani abin da ba'a fata ya faru da ita ko"? Fashewa Tani tayi da kuka, abun duniya ya isheta. Cikin sanyin murya dr shureim yace"Sister calm down ur mind, Zeenatu suma tayi ki miƙo mun ruwa in yayyafa mata, sannan kada ki sanar da kowa, mu jira muga awani yanayi zata farka, Idan ba lafiya dole mu sanar da mutanan gidan don akira mata doctor" amsa mashi tayi da toh, da sauri ta nufi ƙaramin fridge dake a dakin ta buɗe ta ɗauko bottle water taje ta miƙa ma shureim yasa hannu ya kar6a. Kowan nan su fargaba ce azuciyarsa, musamman Tani jikinta yaƙi daina yin kakarwa Kusan sau uku dr shureim Yana yayyafa mata ruwa a fuskarta batare da ta motsa ba, Har sun fara fidda rai a lokacin da ba su yi tsammani ba suka ga Taja dogon numfashi tare da sauke shi, da wata irin kasalalliyar murya ta firta"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" Atare suka hada baki suna ambaton sunanta"Zeenatu! Zeenat" Firgigit ta ware blue eyes dinta akan fuskokinsu, launin farin idon ya canza sosai Wata irin nauyayyar Ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke "Zeenatu, fada min meke damunki"? Tani ce tayi maganar Cikin kwantar da mirya Benazir tace"Sister ɗina, baki da lafiya"? Da ƙyar zeenatu take buɗe idanuwanta sunyi mata nauyi saboda kukan da tasha, fuskarta tayi jawur. "My zeenat" jin miryar dr shureim yasa tayi saurin wurga eye balls dinta akan fuskarshi, wani sabon kukan ne ya kufce mata tamkar ranta zai fita, duk tabi ta rikitar da su. Hada baki su ka yi wuri lallashinta da kwantar mata da hankali daƙyar su ka shawo kanta, tayi shiru tana faman ƙyafƙyafta masu idanuwanta waɗanda ke ajiƙe sharkaf da ruwan hawaye. "Please faɗa min meke maki ciwo"? Dr shureim ne yai maganar, Duk sun tsareta da ido Daƙyar ta iya buɗe baki ta furta"Yunwa nake ji" sunyi mamakin jin abunda ta fada masu badan sun yarda da maganarta ba, "Tani, dama zeenatu bata ci abinci ba? Shiru tani tayi tana faman zare idanuwanta, banezir ta jefa mata kallon tuhuma kafin tace" Ɗazu da safe ke kika ce tace akai mata breakfast dinta a ɗaki Kenan baki kai mata ba "? Girgiza kai tayi Tani tayi"Na kawo mata abincin, Itace taƙi ci, ba yau ta fara yi min hakan ba, Idan wani abu na damunta bata cin abinci, kona tursasa mata akan dole taci, sai tace min in tafi zata ci, da zarar nabar ɗakin take daukar abincin ta shiga toilet da shi tayi flushing dinshi" har saida Dr shureim ya ɗan zaro ido jin abunda Tani tace, Zeenatu ta haɗe fuska ga dukkan alamu bata da gaskiya, Miƙewa benazir tayi da sauri ta nufi toilet jim kaɗan sai gata ta fito daga ciki fuskarta adaure babu walwala tace"Zeenatu baki kyauta mana ba, Fisabilillah haka ake rayuwa? Don wani abu na damunka sai kaƙi cin abinci? Maimakon ma in ba ci zakiyi ba ki bata ta mayar a kitchen sai ki zubda lafiyayyan abinci, kinsan fa ba kyau Almubazzaranci" Rufe ido zeenatu tayi, har lokacin bata ɗago da kanta daga kan laps din dr shureim ba. "Tani ki ci gaba da yin haƙuri da ita, In sha Allah zata daina very soon yanzu ki koma kitchen ki haɗa mata wani abincin ni zan bata da kaina" Muryar Tani asanyaye tace"To" kafin ta juya da sauri tabar dakin "Sister, nabar wayata daki ko zaki dauko min" Benazir ta amsa mashi da toh, kafin ta fuce daga dakin, Ya rage da ga shi sai zeenatu, dama da biyu ya aiki benazir ta ɗauke mashi waya. A hankali ya tallabo kanta ya ɗaura shi kan ƙirjin shi, tamkar ƴar baby haka ya ruƙe ta. Wata irin kunyarshi ce ta kamata, taƙi bari su haɗa ido. "My zeenat, haka za mu yi aure kina yin min rigima? Ya kikeso inyi da rayuwata idan baki gyara halin nan naki ba"? Turo mashi pink lips dinta tayi batare da tace komai ba, murmushi yasaki yana mai mamakin ƙuruciyar zeenatu. "Faɗa min waya ta6a min ke"? Daƙyar ta ɗan iya buɗe ido ta harare shi kafin tayi sauri kau da idonta gefe, nan take ya fahimci wani abu. "Hakan na nufin ni na 6ata maki rai? Ko kinji maganganun da muka tattauna nida sister benazir ɗazu da safe"? Muryarta da shagwa6a tace" I heard everything, ya Shuraim! I won't marry you, because you lied to me. You told me that you had never been in love, bayan ba haka ba ne, sannan ka nuna min hotona amatsayin hoton da ka ke yawan kallo a phone din ka, ashe ba haka bane hoton wata ne daban, Why ya shureim? What did I do to deserve that?' she said, giving him a suspicious look. Aranshi ya ayyana zeenatu matsala, tun yanzu ya fara jin shakkar kishinta . "Ka tsare ni da ido baka ce komai ba Sannan har fadi kake yi wai ba zaka ta6a samun madadinta ba even if u get married" ranta a6ace ta ƙare maganar hawaye nabin fuskarta, hannunta ɗaya dafe da saitin zuciyarta. Tun da take yin magana ya natsu yana bin fuskarta da kallo har saida ta gaji don kanta ta dakata da yin maganar tukunna ya samu damar bata amsa Calmly ya furta"My zeenat, baki fahimci kan zancen namu ba, shiyasa babu kyau yiwa mutun la6e, kalli yadda kika takura kanki akan abunda baki da tabbaci kansa" harara ta jefa masa"yaya shureim ni fa ba kurma bane, Ina ji ai," ta faɗa tana nuna mashi kunnanta da hannu. Murmushi yayi mata, ita ko sai ƙara haɗe mashi fuska take yi. "Bana son 6acin ranki zeenatu, don haka zan faɗa maki gaskiyar abunda na 6oye maki, saboda ina burin na aureki duk wani sirrina ya kamata ki sani, amma bana so ki faɗa ma kowa" Jinjina mashi kai tayi alamar Toh, shiru yai yana yanke shawara da zuciyarshi, ƙwara ya faɗa mata gaskiya idan ba haka ba zata ci gaba da yi mashi kallon maƙaryaci kuma ba sonta ya ke yi ba tun da yana da wadda yake kallon hotonta kullum bayan haka zata cigaba da yin jinyar zuciyartane tun da ita haka Allah ya halicce ta da kishin tsiya. "Dangane da hoton dana nuna maki naki, tabbas bashi nake kallo ba, hoton ƴata ne nake kallo....." tsabar firgita da jin maganarshi yasa zeenatu ta zabura ta sauka daga jikinshi ta koma tana fuskantar shi, idanuwanta azazzare, maganar ta daki kunnanta tamkar a mafarki taji ta. "Yaya shurem na shiga uku, ƴa fa kace, dama ka ta6a yin aure hada baby" Girgiza mata kai yayi"a'a, Ni ban ta6a yin aure ba, na samu yarinyar bata hanyar aure ba...." bai kai ga ƙare maganar ba yaga ta ɗaura hannayenta biyu saman kanta alamar ta shiga uku. "Ya shureim dama kai ɗan iskane" dafe kanshi yai da hannu ɗaya "Idan ba zaki natsu ki saurare ni ba, zan tashi nabar ɗakin nan" da sauri taja baki tayi shiru. Tuni yanayin fuskarshi ya canza sam baya son tuna abunda ya faru a rayuwar shi, tamkar yana faman raunin dake a zuciyar shi ne Numfasawa yai kafin ya ɗaura da cewa "Bayin kai na bane, zan Iya cewa ƙaddarace ta afka min har hakan ya faru, a yanzu haka da nake baki labari, Yarinyar bata araye tun tana jaririya ta rasu, Tsakanina da mahaifiyarta bamu ta6a yin soyayya ba, daga ni har ita ba mu ta6a tsammanin zamu yi mu'amala da junan mu har takai mu ga aikata sa6on Allah, mun fuskanci matsanancin tashin hankali, abun da ya faru zeenatu shine silar ƙuncin rayuwar da na shiga..... ' Duƙar da kanshi ƙasa yayi tamkar mai neman gafara, hawaye tuni sun cika idanuwanshi, sam bayason tuna baya saboda tsohon raunin dake acikin zuciyarshi. Jikin zeenatu yayi mugun yin sanyi, har cikin ranta ta yarda da maganar shi, ta kuma ji tausayin shi. "Yaya shureim na yarda da kai, please forgive me for what I said. Rashin sani ne kuma nayi danasani, dan Allah ka daina zubar da hawayen ka, I know it's hurting your heart, amma kayi haƙuri" Matsawa tayi kusa dashi ta sanya tafin hannayenta biyu ta share mashi hawayen dake akan fuskarshi, wani irin tausayinshi ne ya kamata, da sauri ta rungumoshi ya ɗaura kanshi saman kafaɗarta itama ta ɗaura nata kan asaman tashi kafaɗar. "Yaya shureim ita babyn taka an riga haihuwarta kafin Ni"? Cikin rauni na murya ya furta"da ace tana araye da yanzu ta girmeki" cikin sigar lallashi take ɗan bubbuga bayanshi da hannayenta, ba tare da sun raba jikinsu ba taci gaba da tambayarshi Ya sunanta"? "*FATIMA*" atakaice Ya bata amsa "Allah sarki Ƴar uwata fatima, Allah yajiƙanta" "Ameen" "Ita maman babyn naka, meye sunanta" shiru yayi don baison furta sunan. Fahimtar hakan yasa tayi saurin canza akalar zancen nata "Yaya shureim idan aunty benazir ta kawo maka wayarka zaka nuna min hotonta dan Allah" "Zan nuna maki" A hankali ta ɗago da fuskarta, haɗi da daura idanuwanta akan fuskarshi, ta dafe kafadunsa da hannayenta Ido cikin ido suke kallon juna "Idan mukayi aure nima zan haifa maka ɗiya, bama ɗaya ba Ƴan biyu zan haifa maka, sai mu sanya masu sunan Fatimarka" tunkan ta ƙare maganar tayi saurin dukar da idonta ƙasa Shi kanshi yayi mamakin maganar data furta mashi, saboda kunyar dake gareta amma ya fahimci tausayin shi ne Ya kamata. Shafa sumar kanta yai da hannun shi ɗaya"nagode da kulawarki agare ni," da buɗar bakinta sai cewa tayi"ya shureim pls ka sanar da daddyna da daddynka maganar auranmu, suyi sauri su daura mana aure, don in haifa maka fatima" Dariyace ta kubce mashi, cikin jin kunyarshi Zeenatu ta yi saurin miƙewa ta nufi gado ta haye ta kwantar da kanta Abun da basu sani ba, benazir tana la6e tana sauraronsu, hannayenta biyu ruƙe da Tray din abincin zeenatu data kar6a a hannun Tani Hankalinta idan yai dubu toh ya tashi, har sai da gabanta ya fadi, Jin zeenatu nayiwa shureim zancen aure, aranta tace"taya ma haka zata yiwu? Soyayya tsakanin Ya shureim da zeenatu ƴar cikinsa? Anya kuwa zeenatu tasan ainihin shekarun dr shureim? Lamarin ya ɗaure mata head. Shiga dakin tayi da sallama abakinta, dr shurem ne ya amsa mata sallamar, ta ƙarasa kan carpet din gefen gadon ta ɗaura mata tray din Idanuwanta akan fuskar Dr shureim, ya lura da kallon da take yi mashi sai dai bai kawo komai aranshi ba "Ina wayar" Cikin aljihun jallabiyar jikinta ta zaro wayar ta miƙa mashi, Ya kar6a yana fadin"nagode sister," "Yayana, wani abu ya farune bayan fitana? Naga zeenatu a kwance kan gado" "Taji sauƙin abunda ke damunta, dama ba wani ciwo bane" gyaɗa kai benazir tayi"Okey, mu taimaka mata taci abincin" Atare suka zauna da zeenatu suna bata abinci abaki, Hankalin benazir yaki kwanciya sai satar kallon dr shureim da zeenatu takeyi afakaice batare da sun ankara ba, har wani kallon ƙauna taga suna jefawa junansu, ita dai abun ya tsaya mata aranta, ya girmi tunaninta....... *❤HAJIYA ADAMA🤍* A zaune take kan mirror chair, ta ɗauki wankan riga da zane na zallar leshi launin ruwan toka rigar tayi matuƙar yi mata kyau, ta ca6a adon zabba da awarwaro a hannunta, head dinta kala ɗayane da takalman ƙafarta black colour, Hand bag ɗinta tana ajiye saman gadonta itama launin takalmanta ce. A tsanake take shirya kanta, bayan ta gama shafe shafenta, ta kai hannu ta ɗauki turare tabi ko'ina na jikinta ta feshe, miƙewa tayi ta nufi gadon inda ta ajiye mayafinta, ta ɗauka ta yafa shi a kafaɗa, kafin ta ruƙo handbag din. Tana ƙoƙarin juyawa Uncle abdallah Ya doko sallama hannunshi ɗauke da baby junaid sunyi shiga kala ɗaya ta shadda blue sky. Murmushi tasakar mashi, da fara'a akan fuskar uncle abdalla yace"madam shanyar da ki ka yi ta bushe tun ɗazu ba ki je kin dubo ta ba" Farfari tayi mashi da ido"am sorry my husband, nabarku kunata jirana awaje" From head to toe yake binta da kallo har zuwa kan head din data ɗaura, komai nata burgeshi yake yi, Hajiya adama ta Iya ɗaukar wanka. Baby junaid sai faman lumshe idanunsa yakeyi sam baya fahintar komai biji biji yake ganinsu baccine ke neman yaci ƙarfinsa "Kullum ƙara kyau kike yi, faɗamin menene sirrin"? Still fuskarta da murmushi tace"bani da wani sirri daya wuce kai, Mijina, saboda kulawar da kake bani da tarairayata da kakeyi sune suke ƙaramin kwanciyar hankali da natsuwar da nake samu har kake ganin ina ƙara kyau" Lumshe idanuwanshi yayi tare da waresu kan fuskarta. "Shiyasa nake ƙara ƙaunarki acikin zuciyata, samun mace irinki abune mai wuya a duniyar nan, kin haɗa komai hajiyata, kyau, nasaba, ilmi, abu mafi jan hankali agare ki, tsaftarki, da Iya girkinki, idan nace zan lissafa maki kyawawan ɗabi'unki da halayanki to kuwa zamu kwana batare dana kammala karanto maki ba" Tsabar jin dadin maganarshi ce tasata yin dariyar farin ciki "Kana ƙara huramin kaina fa," "Ba hura maki kai nakeyi ba, Kin cancantane my wife" "Thank u dear, for loving me and for everything" har cikin zuciyarta take fada mashi kalaman "Yakamata mu tafi, baby junaid fushi yake yi damu, munƙi kai shi wurin mommynsa" ya fada yana dariya Kallon fuskar baby junaid hajiya adama tayi, tuni bacci yai awon gaba dashi, Ya langwa6e kansa saman chest din uncle abdallah. "We will miss him. I love my grandson bana son rabuwa dashi sai dai ba yadda zanyi dole na maida ma mamansa" yanayin fuskarta ne ya canza zuwa damuwa, " jin kaina nakeyi tamkar ban ta6a haihuwa ba saboda rashin Uzair, abun yana ta6a min zuciyata, shi kaɗai nake gani inji dadi, da kuma ɗan uwansa tajuddeen da baby angel dinmu Yanzu duk babu su ..." cikin jin ƙunar rai ta furta maganar, jikin uncle abdallah yayi sanyi, Shi kanshi abun yana damunshi. "Tunda na haifi uzair ban sake samun damar da zan haihu ba, saboda matsalar dana samu, mijina meyasa ba zaka kar6i shawarata ba? Nifa inason ganin jininka" idanuwanta sun cika tab da ƙwalla. Ɗaure fuska uncle abdalla yayi, tamkar bai ta6a yin dariya ba "That's enough! Bana so kina min maganar nan! Stop trying to pressure me into getting married. I have no intention of doing it, ke kaɗai kin ishe ni, kada na kuskura naji kin sake tada maganar," Yana ƙarasa maganar ya juya da sauri ya fuce daga falon, Bin bayanshi tayi, a harabar ajiye motocinsu, ta same shi tsaye ya jingina bayanshi jikin motar, harya kwantar da baby junaid, a back seat. Agabanshi ta tsaya tana ƙoƙarin shanye damuwarta tace"am sorry, idan ranka ya 6aci, bazan ƙarayi maka maganar ba," Batare dayace mata komai ba ya nuna mata murfin motar, buɗewa tayi ta zauna a front seat, Ya zagaya ta other side ya zauna a driver's seat, key yayi ma motar, a hankali yayi reverse ya karya kwana ya fitar dasu daga cikin gidan, tunda suka haura kan titi babu wanda yayima wani magana acikinsu, kowa da abunda yake saƙawa aran shi, idanuwan hajiya adama sun kaɗa jawur dasu, jefi jefi takan kai idonta ta cikin mirror din motar ta kalli baby junaid dake akwance yana sharar baccinsa, mutuwar son yaron takeyi, sam batason rabuwa dashi sai dai ba yadda zatayi. A hankali motarsu ta ƙaraso bakin gate din gidan Uncle ɗan Iya, Horn su ka yi Baba mai gadi Ya buɗe masu ƙofar su ka shiga daga ciki, bayan uncle abdallah yayi parking din motar, cikin kulawa ya dubi fuskar Hajiya adama "My wife," kallon shi tayi fuskarta a yamutse babu walwala "Kinsan ina sonki, and bana son 6acin ranki, zan Iya yin komai danganin na faranta maki rai, dalilin dayasa bazan dauki shawararki ba saboda gudun in jefa rayuwarmu cikin hatsari, ke kanki kinsani samun mace tagari wahala ne dashi a duniyar nan, ina jin tsoron in auro wadda zata yi silar tarwatsewar farin cikin mu, ko in auro maki Yarinya da zata raina ki, Ina fata kin fahimce ni"? Ajiyar zuciya ta ɗan sauke fuskarta ɗauke da murmushi tace"na fahimce ka, mu shiga daga ciki" ta fada tare da buɗe murfin motar ta fito ta buɗe mazaunin baya ta ɗauko baby junaid ta rungume shi a kirjinta, ta rufe kofar, atare da uncle abdallah suka nufi entry hall na shiga gidan Uncle abdallah Tunkafin su ƙarasa Aneelerh da zahra suka fito fuskokinsu dauke da fara'a sun dauki wankan Atamfa riga da skirt, ɗaurin ɗan kwalinsu kala ɗaya, Aneelerh ta yafa Mayafi akanta, yayin da zahra ta daura nata mayafin kan kafaɗarta, "sannunku da zuwa, Ina wuninku," zahra ce tayi maganar, Uncle abdallah Ya amsa mata da Lafiyalou, Fatan mun same ku lafiya" ya faɗa yana kallonta tace"Lafiyalou," Kafin ta kar6i baby junaid daga hannun Hajiya adama, rungume juna sukayi ita da Aneelerh "Mommy sannu da zuwa, nayi murnar ganinku," Aneelerh ta fada tana murmushi ta dago da kanta, Itama hajiya adaman murmushin ta sakar mata "Surukar arzuƙi, kullum ƙara kyau kike yi," cikin jin kunyarta ta dan dukar da kanta tana fadin"daddy Ina wuni Ya gida Ya aiki" Uncle Abdallah Yace"lafiyalou daughter, fushi nake yi dake, kinƙi zuwa kiga gidan mu" "Naso zuwa mommy adama ce tace nabari zata zo kawo shi, badan haka ba ai dani zan zo dauko shi daga nan ma har inga gidan, amma ay min afwa in sha Allah zan fidda lokaci ni da zahra mu shigo gidan" yaji daɗin maganarta Zahra tace"mu shiga daga ciki," ta fada tare da basu hanya suka nufi ciki, A lokacin Mami tana cikin jera masu abinci a dining, Ummi kuma ta fito daga daki jikin ta sanye da hijabi, tana ganinsu ta nufesu fuskarta dauke da annurin farin ciki, Itama mami ta ajiye jeran abincin da take yi ta nufesu da fara'a suka gaisa da junansu, kafin suka zazzauna saman sofa, fira suka fara ta6awa a tsakaninsu, Zahra da Aneelerh suka basu wuri, Ɗaki suka shiga a saman gado Zahra ta kwantar da baby junaid tana fadin"Baby boy dinmu Yaji hutu, sati biyu kacal har ƙiba ya ƙara, fatarshi tayi kyau" Aneelerh tace"ni kaina na lura da canzawar da yayi, gaskiya mommy adama ta iya raino, kalli kumatunsa sunyi 6ul6ul da su" gaba daya suka sanya dariya "nasan baby junaid ba ƙaramin ta'asa yayi masu ba, Allah kadai yasan adadin madarar da ya shanye masu" cike da shakiyanci zahra tayi maganar tana jan kumatunsa da hannunta Aneelerh tace"kamar wanda yasha ƙwaya sai bacci yake yi yaƙi farkawa duk surutun da muke yi, Allah na gani nayi kewar babyna" daga gefen gadon suka zauna suna kallonshi kamar zasu hadiyeshi, farin cikin ganin shi ne Ya cika su "Auntyna bari naje kitchen in dauko mashi Cake dinsa nasan zai yi farin ciki idan Ya ganshi" Miƙewa zahra tayi jiki na rawa ta fuce daga dakin. Fitarta ɗakin keda wuya Baby junaid Ya fara mutsi mutsin farkawa daga bacci, tunkan Ya buɗe idanuwanshi Ya fara yin sambatu yana fadin Ni wurin mommyn baby zanje, ni ku kaini gidan mamana" Dariya Aneeerh tasaki batare da tace komai ba, ƙarasa buɗe idanuwanshi yayi Biji biji Ya fara ganinta kafin ya ƙara ware idanuwan akan fuskarta, zazzaresu yayi tamkar yau ya fara ganinta, muryarsa da shagwa6a ya furta"Mommyna, bacci nake yi ko mafarki" tuntsirewa tayi da dariya tare da sanya hannayenta biyu ta daukoshi ta daura shi kan laps dinta haɗi da rungume kanshi saman kirjinta "Baby mommy ni ce, ba mafarki kake Yi ba, mommy adama ta dawo mun dakai kana bacci" Fashe mata yayi da kuka Ya ƙanƙameta da hannayensa biyu, Hankalinta atashe ta ke fadin"My baby boy meyasa keke yin kuka? Maimakon kayi farin cikin ganina, ko ba ka so dawowo gida bane"? Cikin shessheƙar kuka yace"mom..my wallahi bazan ƙara zuwa gidansu kwana ba, Ni bazan ƙara tafiya in barki ba, duk inda zamuje sai dai mu tafi atare......" bata bari ya ƙare maganarba tai saurin toshe masa bakinsa da tafin hannunta, gudun kada su Hajiya adama su jiyo sautin kukanshi da maganarshi "sorry my baby boy, Nima bazan ƙara bari kayi nesa dani ba, kayi hakuri idan hakan ya 6ata maka rai" dakyar ta lallasheshi Yadaina yin kukan Shafa sumar kanshi tayi da hannunta"yanzu fada min me ya faru bayan zuwanka gidan" tamkar baison furta maganar yace"Bakomai" dariya ta yi donta fahimce ranshi a6ace yake "Tunda bazaka fadamin ba, Ni zan fada maka meya faru bayan tafiyarka" ƙura mata manyan idanuwanshi yayi fuskarshi babu annuri "Idan dare yayi bana Iya bacci saboda rashin ka atare dani, nayi maraicinka my baby boy, bani da aikinyi sai tunaninka, dakai nake kwana dakai nake tashi, har mafarkinka nake yi, idan abun ya dame ni sosai, sai in dauki pillow Ina kuka ina Kiran sunanka, wayyo Allah baby junaid dina ka tafi kabarni....." da wasa takeyin maganar tana kwatanta mashi yadda ta ke yin kukan, Murmushi taga ya fara sakar mata hakan ba ƙaramin dadi yai mata ba "Mommy kema kinyi kuka da bana nan" Ɗaga mashi gira tayi alamar eh, dariya yasaki har fararen haƙoranshi suka bayyana tar dasu "Wallahi naji dadi, ke ma kinji abunda naji," wannan maganar da yayi mata ta bata dariya. Shigowa ɗakin zahra tayi hannunta ɗauke da plate daga saman shi chocolate cake ne, an ajiye cake knife daga gefe ɗaya. Akan table zahra ta daura mashi cake dinshi, kafin ta zauna daga gefen Aneelerh "Ashe Ya farka, rigimamme naga sai haɗe min fuska yakeyi, ko ba ka ji dadin ganina bane"? Washe mata baki Yayi idanuwanshi akan cake din data kawo mashi yace"na wanene wannan"? Aneelerh na murmushi tace"naka ne, aunty zahra ce ta haɗa maka" Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskarshi, da sauri ya sauka daga kan laps din Aneelerh Ya rungume Zahra yana fadin"I miss U sis zahra," dariya suka saki, Zahra tace"yau naci albarkacin cake, Har ana fadin Anyi missing dina, toh nagode Nima nayi kewarka our baby boy," ta fada tana shafa sumar kanshi "Ni zan yanka cake din" Ya fada Tare da raba jikinshi daga nata, da zumuɗi yakai hannu zai dauki wukar aneelerh tayi saurin rigashi daukarta"Ni zan Yanka maka" ba musu ya amsa mata da toh Zahra dake kallonsu gwanin ban sha'awa tace"Aunty Aneelerh ki cigaba da tayani addu'a Allah Ya bani miji nagari inyi aure kafin in mutu, wallahi inason ƴa'ƴa idan ina kallonki ke da baby junaid sai inji dama ni" Fuskar Aneelerh dauke da murmushi tace"in sha Allah zahra, zan cigaba da tayaki addu'a, very soon kema zakiyi aure har ma ki haifa mana babies" "Ameen Ya Allah Auntyna, Bari in dauko wayata Inyi maku hoto" acewar zahra, Ta miƙe da sauri ta fuce daga dakin, har zata gifta ta falo tajiyo sallamar Abie da Uncle dan Iya, da sauri takai idonta kansu, atare suka shigo fuskarsu dauke da fara'a suka nufi su uncle abdallah, Kau da idonta tayi da sauri ta nufi bedroom dinta ta shiga, akan gado ta dauko wayarta, ta ɗan dakata tana daddana wayar, wi-fi ta kunna ta shiga whatsapp dinta, messages ne suka fara shigowa ta ko'ina, wasu sakonnin daga abokan aikinta wasu kuma daga mutanan da suke mutunci dasu, Shagala tayi da karanta sakonnin mutane, har tazo kan sakon da Hajiya saratu ta tura mata tun jiya da marace bata gani ba sai yanzu, Gajiyar aikin da su ka yi ne ya hanata hawa whatsapp din jiya. Tsabar zumuɗi yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin buɗe chat dinsu Unexpected Tayi tozali da hotunan da hajiya saratu ta tura mata, Na twins dinta, Sunyi matuƙar yin kyau hotunan a ƙalla sunkai guda biyar, Hoto na farko a london suka yi shi, Hoto na biyu sunyi shi a ƙasar dubai, sauran hotunan an dauke shi a dakin taron da aka gabatar da shagalin birthday din baba obie, Jiya kenan" Abun kallo ya samu, Komawa zahra tayi gefen gadon ta ta zauna tana mai mamakin turo mata hotunansu da hajiya saratu tayi? Takasa gane me take nufi da hakan. Message ta gani daga ƙasan hoto na ƙarshw da sauri ta soma karanta shi kamar haka *Daga Alƙalamin Boss Bature🫶* *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura* 3196407426 First bank Bature Hafsat Muhammad, *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida* ~TAKUN ƘARSHE~ _______________________Boss Bature✍️ Rubutun dake a ƙasan hoto na ƙarshe ta karanta kamar haka _"If you had the chance to choose between them, which one would you like?"_ A ruɗe zahra take kallon screen din wayar, a ƙalla ta maimaita karanta sakon yafi sau a ƙirga, duk tabi ta ruɗe ga wani farin ciki daya lullu6eta duk da bata gane me hajiya saratu take nufi ba. Miƙewa tayi jiki na rawa ta fito ta nufi dakin Aneelerh. Tana shiga ta taras da su suna Cin cake, Ita da baby junaid. Jin motsin shigowarta yasa duk suka ɗago suna kallonta. "Zahra, meye faru naga kina murmushi"? "Aunty na, duba ki gani abun da hajiya saratu ta rubuta min" miƙa ma Aneelerh wayar tayi, bayan ta kar6a ta soma duba hotunan, Baby junaid dake cin cake Ya ce"Aunty Zahra, Kin iya cake, Yayi daɗi, Idan Angel dina ta dawo gida, zaki hada mata kalarshi" ɗaga mashi kai zahra tayi"me zai hana my baby boy, ai dole baby Angel taci cake" Murmushi yasaki"thank u sis zahra" Ɗagowa Aneelerh tayi ta ɗaura idonta kan zahra dake atsaye tana kallonta. "Na taya ki murna, wata'kil burinki ne zai cika, a fahimtana, Hajiya saratu tana son haɗa ki da ɗaya daga cikin ƴa'ƴan ta shiyasa ta baki za6i" Cike da kokwanton maganarta Zahra tace "Anya aunty Aneelerh? Gaskiya bana tunanin hakan, tayaya ma zata hada ni da ɗanta? Ni da ba yar kowa ba, nifa nasan masu kudin nan basa auran bare sai dai yasu yasu jinin arziƙi" cikin sanyin murya ta furta maganar"kuma ni waɗannan sunfi karfina wallahi, ko lokacin da muke zuwa gidan yi masu hidima basu yi ma mutane magana suna da girman kai, idan muka gaishe dasu da hannu suke amsawa, ko kallo ba mu ishe su ba" Dariya Aneeleeh tayi"kin bani mamaki zahra, sai kace bake bace kike da burin auran Chief owais, sai gashi yanzu kina maganar ƙannansa sun fi ƙarfin ki" Dariya zahra tayi"ki gane mana, Chief Yafi ƙarfina nesa ba kusa ba, Haukana kawai nake Yi, daga baya kuma na zauna nayi ma kaina karatun tanatsu, Na lallashi zuciyata na haƙura na barma Allah za6i" Aneelerh na murmushi tace"Yanzu dai zoki zauna daga gefe na, In taya ki za6an wanda Ya dace dake, duk da naga kamannin su ɗaya ban iya banbanta su" Zama zahra tayi daga gefenta, hankalin baby junaid baya akansu, Ya samu cake sai ci yake yi duk ya 6ata bakin shi. Ƙura ma hotunan ido su ka yi"zahra idan hasashena ya zama gaskiya wani irin farin ciki za ki yi? "Mara misaltuwa" amsar da zahra ta bata kenan. "Za ki zama ɗaya daga cikin surukan Baba Obie, Uwa Uba ɗan gidan Hajiya saratu minister of health, gashi itace autarsu, gaskiya zaki more wlh gata ta ko'ina zaki samu idan familyn suka kar6e ki hannu biyu" da fara'a akan fuskarta ta yi magana. Zahra bata ce komai ba, Ita dai gani ta ke kamar hakan ba mai yiwuwa bane "A cikin su wanene ne yafi kwanta maki a rai"? Aneelerh ta jefa mata tambayar "Aunty aneelerh nabar maki za6i dan Allah, Ni kaina bana iya banbanta su, amma kamar wannan shine Zayn idan kika kalli fuskarshi da kyau zaki fahimci yana da masifa" ta faɗa tana ɗaura yatsanta kan face din Zayn. Shi kuma wannan shine zaid a hasashena, Yafi zayn saukin kai. Aneelerh tace ƙwara mai saukin kan, akan mai masifar, amma fa kamar yafi kyawun sura. Zahra tace"Eh, hakane, zayn yafi zaid. "Nidai nafi yi maki sha'awar zaid, indai yana da kyakkyawar zuciya" Shiru zahra ta ɗan yi kafin tace"An ta6a faɗamin basa jin magana, kamar suna kula mata, Har page dinsu na insta na ta6a shiga, suna yawan ɗaura hotunansu da matan banza masu bayyana tsiraicin su" Yanayin fuskar Aneelerh ne Ya canza zuwa damuwa. "Zahra kin tabbatar basu jin magana"? Ɗaga mata kai zahra tayi alamar eh Kwa6e fuska Aneelerh tayi"akwai matsala, but mommynsu tasan da hakan"? "Bana tunanin ta sani, saboda mutane suna jin shakkar yi mata magana kinga kuwa babu wanda zai Iya tunkararta da wannan maganar mara dadin ji" "Banji dadi ba zahra, Har na fara yi maki murna amma yanzu sai naji abun ya fara fita raina, bazan hana ki za6ar wanda kikeso ba acikinsu, Idan Allah yasa sanadin shiriyarshi ce sai kiga ya shiryu ta silarki, babbar matsalar shine ace baya sonki, da ace idan ta haɗa kun zaku son juna har ma son shi ya rinja yi naki tabbas zai Iya canza kanshi, amma idan ke ki ke son shi baya sonki baki Isa ki iya tanƙwarashi ba sai dai wani iko Na Allah" Jinjina kai zahra tayi ta gamsu da bayanin Aneelerh sai dai bata Jin zata Iya haƙura da damar da take da ita, Allah na gani ta jima tana son Hajiya saratu da ya'yanta duk wani abu da zai hadasu son shi ta ke yi. Cikin sanyin murya tace"Auntyna, addu'arki nake buƙata nima zan dage da addu'a, Idan Har dagaske zata hadani da daya daga cikinsu toh Allah yasa ya zama alkhairi agare ni da kuma shi kanshi wanda zata haɗani dashi din, Idan yana da kyan hali zanyi farin ciki, imma akasin hakan zan dauki hakan amatsayin ƙaddarar rayuwata, Allah na gani Ni bazan Iya janye tayin da tayi min ba" Dafa kafaɗarta Aneelerh tayi"Zahra, bana so ki jefa rayuwarki inda zaki ƙuntata, babban kuskure ne ki auri miji mai neman mata, Ni nafison kiyi aure inda bazaki ta6a yin danasani ba, ko dan saboda Ƴa'ƴan da zaki haifa yakamata kiyi nazari kafin ki yanke hukunci" Damuwace ƙarara akan fuskar zahra, Ga samu ga rashi. "Nagode da shawararki auntyna, but ni yanzu bansan wani amsa zan bata ba, gashi na riga da na bude sakon zata ga alamar nagani" Shiru Aneeleerh tayi naɗan wani lokaci kafin Ta furta"Ki bata amsa da sunan wanda ya birgeki, zamu jira muga martanin da zata mayar mana" Amsa mata tayi da toh, ta kar6i wayar daga hannun Aneelerh, sunan zaid ta rubuta ba tare data ankare ba keyboard Ya canza mata sunan ya koma zayn, ahaka ta tura message din. Bayan ta kammala ta soma daukarsu hotuna tare da baby junaid, sun dauki lokaci a dakin kafin suka fito falo don ay fira dasu, Hajiya adama da uncle abdallah sun ji dadin tarbar da akayi masu, An mutuntasu an kuma karramasu kamar kada su tafi, ga lafiyayyan abincin da su zahra suka girka masu, sunci sun ƙoshi sun kuma sha fira, wuraren marece suka bar gidan. *Shin Meke Faruwa A Obie Estate 🔥🔥🔥* Bayan fitowar Chief owais da Prime minister Tare da Boss man, jami'ai suka yi gaggawar bude masu motar da za su shiga. Ta ƙofar baya suka bi wadda zata 6ular dasu zuwa cikin Obie estate, kasancewar Gidan Owais shine ƙarshen ginin dake acan bayan estate din, Gate dinsa Biyu, akwai gate na gaba wanda zai fitar dakai titi, Gate din baya kuma zai shigar dakai Cikin estate. Prime minister Ne Ya buƙaci Yana son su fara zuwa gidanshi don su taho da sheikh imam kafin su wuce gidan baba Obie. Da matsakaicin gudu motocin suka ƙaraso babban katafaren entry na gidan prime minister dake a tsare da jibga jibgan canadian polices da sojoji. A harabar Ajiye motoci su ka Yi parking, A hanzarce Sojoji suka nufo motar, Tare da buɗe masu ƙofa. Kusan atare suka fito, ba tare da bata lokaci ba, su ka ɗunguma zuwa babban falon gidan. A lokacin Nazli tana zaune saman Sofa ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Hankalinta na akan laptop dinta, Yayin da Yazrin Take zaune a gefenta hannunta ruƙe da tsadaddiyar Wayarta. Ba zato ba tsammani, sallamar su prime minister ta ratsa kunnuwansu. Yazrin ce tayi saurin ɗagowa da idonta yayin da ita Nazli tayi tamkar bata ji sallamar su ba, dama halintane idan tana aiki a laptop ba ƙaramin abu ke Iya dakatar da ita ba. Tsantsar farin ciki ne akan fuskar Yazrin, da mamaki ta furta"Big Bro"! da sauri Ta miƙe ta nufe shi, tunkafin ta ƙaraso Chief ya buɗe mata hannu alamar tazo gare shi, hartana tuntu6e garin sauri duk zumuɗin ganin shi ne, prime minister Yace"bi a hankali daughter ba guduwa zaiyi ba" sai faman washe mashi baki take Yi, hugging dinsa tayi, ya ɗaura hannayenshi biyu asaman Bayanta Yana ɗan bubbugashi ahankali Ya furta"Long time no see, I missed You so much" Ɗagowa tayi da kanta tana fadin"I miss you too, rabin raina You forgot about us, and you stopped coming to Canada, ko kiran wayarka akayi baka picking" voice dinta tamkar zata fashe mashi da kuka Ta ƙare maganar. Ɗaura hannunsa yayi kan mayafinta"Am sorry, Kuna araina, aiki ne Ya 6oye ni, amma hakan ba yana nufin aikina yafi ku mahimmanci ba, Ina fata kin fahimce ni" jinjina mashi kai tayi alamar eh. Boss man Dake atsaye Yana kallonsu yayi mamakin yadda owais Yake Yi mata magana, bai ta6a ganin yana sakar ma mace fuska haka ba sai Yau da Allah Ya kawo su gidan Prime minister, Hakiƙa Ya yaba da Haɗuwar daular, sai yaji tamkar Yabar Nigeria ne, ga wani ni'imtaccen sanyin A.c mai ratsa hudojin fatar mutun, ya yaba da kyawun Yazrin, Jefi jefi yakan dan saci kallon falon, badan Ya fito daga gidan chief Owais ba, da Allah kadai Yasan ƙauyancin da taj zaiyi agidan prime minister. "Mu shiga daga Ciki mutumina" Muryar prime minister ce ta fargar dashi daga tunanin da yake saƙawa aranshi, Murmushi ya saki, Hateem Ya ruko hannunshi suka nufi jigunannun royal sofas din Falon masu numfashi Ƴan ubansu afagen haɗuwa. Yazrin ta ruƙe hannun chief Owais acikin nata, Har suka samu wuri suka zauna saman sofa, Lokacin da Taj yai tozali da Nazli Har saida gabanshi Yadan fadi, aruɗe Yake kallonta sai ya dinga ganin fuskar Danish akan fuskarta, Prime Minister ya lura da rudanin dake akan fuskarshi, gyaran muryar da yayi mashi ne yasa shi yin saurin kallon shi, da ido yai mashi alamar ya yaganta, jinjina mashi kai Taj yayi, suka sakar ma juna murmushi. "Nazli" Prime minister ne Ya kira sunanta, A hankali Ta dago da fararen idanuwanta ta daurasu akan fuskarshi. "Dad, welcome back" ta fada ba tare da ta kau da idonta daka kallon shi ba. "Yawwa, Baki ga mutanan da nazo da su ba" sai lokaci ta kalli Boss man tamkar bata son yin maganar ta furta"Hey, How are you" Fuskarshi da fara'a yace"lafiya lou fatan na same ki lafiya" Amsa mashi tayi, harzata dukar da kanta Yazrin tayi saurin cewa"Sister, baki gaishe da big bro ba" ba tare data kalle shi ba tace"Okey" Iya abunda ta furta kenan. Tsantsar mamaki ne akan fuskar Boss man, ko a mafarki bai ta6a ganin mace mai izza irinta ba, bai ta6a tunanin za'a Iya samun macen da zata kau da idonta daga kallon chief owais, sai akan Nazli. Chief owais tamkar shima baisan da zamanta ba, hankalinshi na akan wayar hannunshi daya ruƙe Yana daddanawa "Nazli, ki gaishe da Yayanki" babu wasa akan fuskar Hateem Yayi mata maganar, tun daga kan Yanayin yadda ya furta mata maganar zaka fahimci ranshi ya sosu da abunda Nazli tayi Batare data dago ta kalli chief owais ba ta furta"ya kake" Banza yayi da ita, har saida prime minister Ya ambaci sunanshi tukunna Yace"Uncle kada hakan Ya dame ka, ka bar ni da ita, dai dai nake da ita" cikin nuna isa Yayi maganar. Daure fuska Yazrin tayi, ranta ya 6aci bata ji dadin abunda Nazli tayiwa Chief fa, Kodan saboda baƙon da suka zo dashi aganinta bai kamata tayi hakan ba. Miƙewa tayi tare dakai hannu ta dauki laptop dinta, ko sallama babu ta nufi upstairs, sautin takalmanta har cikin kunnuwan su. Bayan tafiyar Nazli, Gimbiya Mujeedat ta sauko down cikin shiga ta alfarma, tunkafin ta ƙaraso take sakar masu murmushi. "Marhaban bika, My Son In-law, Long time bamu haɗu ba, dama kana a kasar," ta jefe mashi tambayar tare da samun wuri ta zauna tana fuskatar su. Ɗagowa chief Owais Yai tare da kallonta, da murmushin gefen fuska ya furta"ban jima da dawowa ƙasar ba, nayi laifi ban leƙo mun gaisa ba, sai yau Allah Ya nufa" taj dake kallon gimbiya mujeedat afakaice Ya jinjinawa haduwarta, mace kamar kanta aka fara tsara kyau ta haɗu ga Iya dattako. "Sannu da dawowa Mijina, Ina fata anyi nasara"cikin kulawa tayi maganar tana kallon Hateem, lumshe mata ido yai tare da ɗan jinjina mata kai alamar eh Dauke idonta tayi daga kan fuskarshi ta dubi Taj, baiyi tsammani zata kula shi ba, amma sai yaga ta sakar mashi murmushi tana fadin"barka da zuwa" yace mata yawwa. "Mijina baka fadamin wanene wannan ba"? "Sunanshi tajudeen, abokin aikin Owais ne" "Masha Allah, malam Taj, naji dadin haduwa dakai, Ya aiki"? Yace mata lafiyalou," sun ɗan ɗauki lokaci suna tattaunawa kafin daga bisani, Prime minister Yace da ita"Sheikh Imam Yana aciki"? "Eh, tun ɗazu daya zo, na kaishi masaukin da aka tanadar masa," "Okey, bari na shiga wurinshi" ya fada tare da miƙewa ya nufi Hanyar zuwa part din da shiekh Imam Yake. Kafin dawowarshi, Biyu daga cikin masuyi masu hidima suka shigo falon, Hannayensu ruƙe da ƙayatattun trays, daga saman an jera kayan abinci kala kala da drinks" Cikin girmamawa suka gaishe da su tajudeen, kafin suka sauke farantan kan lallausan carpet din dake awurin. "Big bro, fadamin me kake son ci, zan zuba maka da kaina" yazrin ce tayi mashi maganar, girgiza mata kai yai alamar a'a, zuciyarta ajagule tace"Pls, kada abunda sis nazli tayi maka Ya 6ata maka rai, kariga da kasan halinta" calmly ya furta"okey" daga haka bata ƙara yi mashi magana ba, zuƙunna tayi batare da girman kai ba tace da masu hidiman da suka kawo abincin ku tafi ni zan yi serving dinsu, tafiya sukayi, Ita kuma ta zauna ta dauki lemu me sanyi ta tsiyaya shi a cup ta zuba ma Taj ta miƙa mashi. Har cikin ranshi yaji dadin hakan, kuma ya yaba da hankalinta, tun anan Ya fahinci tafi sauƙin kai Akan Ƴar uwarta Nazli, nan take Ya tuna da Halin Danish miskilancinshi sak kalar Na nazli ne, Aranshi yace Komai nasu kala daya kamar ɗan uwanta" "ya owais, zan je na dawo" yazrin ta fada Tana kallonshi, amsa mata yai da ok, da sauri ta nufi upstairs. Bayan taj Ya kammala shan lemun, ya fara shan fresh fruit din da aka kawo masu. Elevator Yazrin Ta hau, ta sauke ta a second floor, moving quickly Ta nufi ɗakin Nazli, a buɗe ta samu ƙofar, zura ƙafarta keda Wuya ta fara Cin karo da takalman Nazli a tsakar daki, Ga mayafinta kan floor, Da sauri takai idonta kan katafaren gadonta, tana daga kwance doguwar sumar kanta ta lullu6e mata bayanta. Cikin sanyin murya Yazrin ta soma Yin magana tana tunkararta. "Sister, Meyasa kika za6i ki ƙuntatawa zuciyarki? kina sonshi amma meyasa kike ja mashi aji"? Shiru Nazli bata tanka mata ba, babu lamun zata motsa. "Ni banga amfanin 6ata mashi rai da ki ke yi ba, da hankalinki da tunaninki, gaban baƙon daddy, kike nuna ba'a isa dake ba, wannan ba ɗa'a bace, shi kanshi daddy ranshi ya 6aci da abunda kikayi," dakatawa ta danyi da yin maganar tana kallon Nazli dake kwance tamkar maiyin bacci. "Nasan kina jina, ban damu ba dan kin share ni, Nidai shawara nake baki a matsayina na ƴar uwarki mai son farin cikinki, kada kiyi wasa da damarki, mata dayawa suna hauka akan son Ya owais, basu ta6a samun damar yin tozali dashi ba, amma ke cikin sauƙi Kin same shi, Kina ƙoƙarin Yin watsi da damarki, bana son kiyi danasani sister," har cikin zuciyarta take furta kalaman. "I thought when you saw him, you would rush to hug him and tell him how much you missed him, but sai naga akasin hakan, wai yaya owais kika share kamar wani tsaran wasan ki, ki daina ganinshi kamar wani tsaranki, kafin a haife ki shi aka fara haihuwa" Shiru Nazli bata motsa ba, Yazrin taci gaba da cewa"Ki cigaba da ja mashi aji, wata rana zakiyi danasani, Allah yasa Ya auri wata bake ba...." kafin Ta ƙare maganar A fusace Nazli Ta yunƙura ta miƙe zaune Ta rarumi laptop dinta dake agefenta, daga Inda take ta daddage ta wurga ma Yazrin ita, da sauri Yazrin Ta tarbe laptop din da hannu biyu, fuskarta dauke da murmushi tace"kinji haushin magana ta ne"? Kaɗan kika gani, sai ma ranar da za'a shafa fatihar auranshi, Haukan da za ki yi sai yafi wannan" wurga mata laptop din Yazrin tayi kafin ta juya da gudu ta fuce daga dakin ganin yadda Nazli take huci. A hankali ta ɗaura kanta saman pillow, haɗi da lumshe idanuwanta, red lips dinta sun ciza launinsu, ita kadai tasan irin radadin da take ji aduk lokacin da tayi ma owais haka, ita aganinta batayi laifi ba, shi yakamata yazo inda take don ya nemi afwarta akan tsawon lokacin daya ɗauka ba tare daya je canada ba, Alƙawari ne ta ɗaukarwa kanta idan har baizo wurinta Ya wanke kanshi ba ita kuma har abada bazata ta6a kula shi ba, koda an shafa fatihar auran su!!! Don ita ba irin matan da namiji Yake juyawa bace, macace mai aji, mai kuma Ji da kanta, zata iya haƙura da komai akan izzarta. Idan muka koma Falo, Bayan ƴan mintuna, Prime Minister Ya shigo falon tare da Shieikh Imam, sai kuma gimbiya Mujeedat, miƙewa Chief Owais Yai shima Taj Ya miƙe, suka yima Gimbiya mujeedat sallama kafin suka dunguma zuwa harabar ajiye motocin gida, jami'ae suka buɗe masu ƙofa suka shiga, Ajere motocin suka nufi gidan baba Obie. *BABA OBIE* Bai jima da farkawa daga bacci ba, jikin shi yayi tsauri, wani irin azababben zazza6i ne Ya lullube shi, har sai da Senator Lateef ya kira family doctors din su, domin duba lafiyar mahaifinsu, a ƙalla likitocin sun ɗauki tsawon mintuna talatin akan shi suna ƴan bincike binciken su, kafin daga bisani suka tabbatar masu da cewa Firgici ne da tsoro ke damun shi, Idan Har ba'ayi gaggawar kawar mashi da abunda ke razanar da shi ba, zuciyarshi zata Iya bugawa, Jin wannan maganar daga bakin likitocin yayi matuƙar ƙara ɗaga hankulansu, musamman Hajiya saratu duk tabi ta ruɗe, hannayenta biyu asaman kanta take ambaton Inna lillahi wa inna ilaihirraji'un, mun shiga Uku, Ƙiri kiri ana so aga bayan uban mu. Bayan tafiyar Likitocin, gaba ɗayansu suna adakin Obinna, zuciyoyinsu cike da jimamin sakamakon ciwon shi, ya kasa ta6uka komai, duk ya yamutse tsufanshi Ya ƙara bayyana, Senate lateef ne ya taimaka mashi ya shiga bathroom yai wanka, ya fito ya canza suturar jikinshi, Kafin Ya shimfiɗa mashi darduma, acikin dakin yai sallar da bai samu damar yi ba, sam babu natsuwa atattare da shi, bayan Ya kammala Yin sallar ne, senate Ya ruƙo hannunshi, Ya zaunar dashi kan lallausan carpet, da sauri His excellency abdul razak Ya miƙe daga kan arm chair din da Yake azaune Ya nufi Kayan abincin da Hajjaty ta kawo mashi, Ya sanya hannu biyu ya ɗauko su yaje ya ajiye farantin gaban Baba obie. Saukowa Hajiya saratu tayi daga gefen gadonshi, ta zauna gefenshi idanuwanta acike tab da hawaye take yi mashi sannu. "Babana Allah Ya baka Lafiya, Ka daure ka ci abinci, sai kasha maganin zazza6in da likita Ya bada abaka" cikin kulawa tayi mashi maganar, a raunace ya ɗago da idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur dasu Ya ɗaura su akan fuskar Saratu na tsawon mintuna biyu, kafin ya kau da idon Ya dubi Senate Lateef da ke ƙoƙarin zama gefen gadonshi, A hankali Ya maida idonshi akan fuskar His excellency deen da Pravin waɗanda ke A zaune kan carpet. Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi, kafin ya ware su kan fuskar Twins dake zaune kan carpet kamar wasu mutanan kirki, sun yi zaman cin tuwo kowa da abun da Yake saƙawa aranshi. "Sannu baba, Allah Yabaka Lafiya," su twins ne sukayi mashi ya jiki, kafin sauran mutanan dake adakin suma sukayi mashi Ya jiki, bai samu damar amsa masu ba, Sai dai bin dakin da yake yi da kallo. Muryarshi adisashe Yace"Hateem baizo bane ko baku fada mashi halin da nake aciki ba"? Shiru su ka yi jin, kowa yana jin fargaban fada mashi abunda Prime minister Yayi. "Kunyi shiru bakuce komai ba! ina Owais? Yace min zaizo yau ya akai ban gan shi ba"? fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa Ya furta maganar. Hajiya saratu ce tayi ƙarfin halin buɗe baki, ta labarta mashi abunda Pravin Ya fada mata dangane da tura jirgi da hateem yayi zuwa Sudan dan adauko Sheikh imam Ya duba jikin Yaron daya rikiɗa Ya koma maciji. Tsabar 6acin raine tsantsa akan fuskar Obie, Senate Lateef yace"tun safe babu wanda ya kira awaya cikin su don ya tambayi ya ka kwana, Gaba ɗaya sun ɗaura burin duniya akan Yaron da muke zargin Abokan hammayar mu ne suka turo shi donsu tarwatsa zuri'armu" afaɗace senate Lateef Yayi maganar His excellency deen Yace"gaskiya bamu ji daɗi ba, Hateem bai kyauta mana ba, yayi abu gamon kanshi batare daya nemi sha'awar mu ba, ni narasa gane meke damunsu daga shi har Owais din idanuwansu sun makance basa ji basa gani indai akan taimako ne, toh gashinan dai suna ƙoƙarin jefa rayuwar mahaifinmu cikin matsala, Fisabilillahi Ina amfanin hakan"? Ya ƙare maganar tare da jan dogon tsoki. Tun da suka fara magana, Pravin Yake ta tsuma, tsabar zumuɗun su ƙare maganarsu don ya samu damar tunzura su, ganin Deen Ya dasa aya a maganarshine ya samu ƙwarin gwiwar cewa "Yakamata ayi gaggawar ɗaukar mataki akan Yaya Hateem, Shina fi ji, duk da ba fata nake Yi ba, amma idan wani abu Ya same shi, Ba iya family din mu Ya shafa ba, Nigeria gaba daya ya shafa, ƙasar da yake mulka bazasu ta6a sassauta mana ba idan wani abu ya samu shugabansu, koda kuwa kwarzane ne Ya fito akan fatarshi sai sunji ba'asi" maganar pravin ta ƙara ɗaga masu hankulansu, babu wanda yai wannan tunanin saida Ya furta tukunna suka ankara da gangancin da suka Yi. Ganin yadda suka ɗaga hankalinsune Yasa shi ƙara samun kwarin gwiwar cigaba dayin magana. "Ga kuma mahaifinmu babu ƙoshin lafiya, ba zamu zuba ido muna ganin wani bakon abu na neman yi mashi illa ba, dole mu dauki mataki, wallahi indai akan baba ne sai inda ƙarfin mu Ya ƙare, dole Yaron Yabar estate din nan, ai nan ba gidan marayu bane" ya faɗa yana mai nuna 6acin ranshi Senate Lateef Yace"Sannan, shi kanshi Owais din zamu Yanke alaƙarshi da Yaran! Babu shi babu su, shi kuma Hateem tunkan Aje ko'ina, acikin satin da zamu shiga Ya tattara Ya koma canada, don ba zamu bari Yaja mana bala'e ba, Idan muna son ganinshi koda duk weekend ne zamu iya zuwa canada wannan ba damuwarmu bace, awurinmu tamkar zuwa kano ne" Duk maganar da sukeyi akan kunnan Baba Obie, yayi shiru Yana sauraronsu, abincin ma Yagaza cin shi, hajiya saratu sai lalla6a shi takeyi akan yaci amma Yaƙi Ya, Ranshi Ya 6aci matuƙa, bakomai yafi ƙona mashi rai ba face rashin zuwan Hateem da Owais, bayan sunga halin daya shiga adaren Jiya, maimakon su mayar da hankali wurin kwantar mashi da hankalinshi, sai suka ta'allaƙa wurin Kula da abun da Ya cutar da rayuwarshi, me hakan Yake nufi? "Baba dan Allah kaci abincin idan ba haka ba Hankalina bazai kwanta ba" hajiya saratu ce tayi mashi maganar yayin da take miƙa mashi abincin data ɗebo a cokali, kawar da kanshi gefe ɗaya yai batare daya furta mata magaba ba. "Grandfa, please kaci abinci, gaba ɗaya mun damu da halin da kake aciki" zaid ne yayi maganar. Kafin wani Ya kuma furta magana, Suka soma Jiyo dirar motoci acikin Estate din "May be sune suka ƙaraso" Acewar His excellency abduk razak. "Anya kuwa sune? Naji ɗazu Yaya deen ya kira Yaya sharafuddeen nafi tunanin shine Yazo" Pravin ne yai maganar, dakatawa su ka yi da yin magana, gaba ɗaya hankalin su ya koma akan ƙofar dakin, sunyi matuƙar ƙagara da son ganin wanene zai shigo. Knocking ƙofar dakin Akayi, Pravin Ya ɗaga murya tare da cewa"ku shigo daga ciki" Lokacin da ƙofar ɗakin ta buɗe, Prime Minister Hateem Ne Ya fara shigowa yana maiyi masu sallama, Chief Owais Yana abiye da bayanshi, su kadai suka shigo, Boss man da sheikh Imam suna acan babban falon gidan suka zauna saman sofa. Tun da suka shigo dakin kowa yayi shiru yana binsu da kallo, su kansu sun fuskanci babu Lafiya, cikin girmamawa Hateem yabi ƴan uwanshi ɗaya bayan ɗaya ya gaishe da su, fuskokinsu babu walwala suka amsa mashi, chief Owais ma Haka yabi kowan nan su ya gaishe da shi, banda Pravin, baya acikin jerin mutanan da suka kai matsayin da zai iya gaishe da su, tunfil azal basu jituwa, shiyasa hajiya saratu take matuƙar jin haushin Owais, saboda ƙiyayyar da yake nunawa mijinta, ko yanzu daya gaishe da ita daƙyar ta amsa mashi tana faman yamutsa fuska. A hankali ya zauna daga gaban farantin kayan abincin baba Obie, wanda tun da suka shigo ɗakin idanuwanshi suke akan fuskokinsu, Idan ya kalli prime minister sai Ya kalli Owais, har gaishe da shi su kayi bai amsa masu ba, hakan ba ƙaramin ɗaga hankalin prime minister yayi ba, don wannan alama ce dake nuna cewa mahaifinshi yana fushi da shi. da sauri Zayn da zayn suka haɗa baki wurin gaishe da Prime minister, bayan ya amsa masu suka gaishe da chief Owais, shima ya amsa masu fuskarshi babu walwala, daga haka babu wanda ya ƙara furta magana, munafuki pravin a fakaice yake sakin shu'umin mirmushi, wato haƙarsa ta cimma ruwa Baba Obie, Ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Owais, kamar yadda yake kallon shi shima haka yake kallon shi "Hateem, meyasa tun safe bakazo gida ka duba ni ba"? Baba obie ne Ya jefa mashi tambayar. Daƙyar Ya iya buɗe baki Yace"Kana araina baba, nasan ban kyauta ba na rashin zuwana, ka gafarce ni" "Baka fada min me ya dakatar dakai daga zuwa ba? Shi nake son ji" Da sauri Zayn da zaid suka miƙe ganin irin kallon da hajiya saratu tayi masu alamar su tashi su tafi, salin Alin suka fuce daga dakin A tsanake Prime minister Ya labarta mashi abun da Ya faru. "Saboda wa kazo ƙasar nan"? Jim ya ɗanyi kafin Ya furta"saboda kai babana" "Taya za'ai nayarda da maganar ka Hateem? Abun da Ya cutar dani daren Jiya shi ka tsaya taimako, tun safe kana can kana yi mashi hidima, yayin da ni kuma nake kwance ba lafiya" Tuni prime minister Yasha jinin jikinshi, duk sai yaji ba dadi, zuciyarshi ta karaya "Baba bansan baka da lafiya ba, dan Allah kayi hakuri idan na 6ata maka rai, amma ka riga da kasan halina kuma kaine kake ƙarfafa min gwiwa akan yin taimako, ka sha fada mana tun muna yara idan muka ga mutun na buƙatar taimako to mu taimaka masa da abun da muke dashi, kada mubarshi hakanan, Yaran nan bayin kanshi bane, ƙaddarace ta afka mashi, baida kowa marayane, Yana buƙatar waɗanda zasu tallafi rayuwarshi.... "Kafin Ya ƙare maganar, Pravin yayi kuskuran katse shi da cewa "yaya kai ne baka fahimta ba, Yaron nan maƙiya ne suka turo shi don su tarwatsa zuri'armu, idan ba haka ba ta ina mutun zai Iya rikiɗa ya zama maciji? Sannan ya rasa inda zai faɗo duk gine ginen dake a estate din nan na kusa da gidan Owais din bai shiga cikin su ba sai nan zai faɗo"? Daƙyar Ya ƙare maganar, ganin wani mugun kallo da chief owais Ya watsa mashi, nan take Ya haɗiye yawu ya soma ƴan kame kame Rai amatuƙar 6ace yace"malam, fuce kabar ɗakin nan, meye alaƙarka damu da har zaka katse Prime minister Yana magana, wannan abune daya shafi dangin mu bana ka ba" Tsabar mamakin kalaman Owais Yasa kowan nan su Ya dube shi, musamman Hajiya saratu ta muzanta da jin cin mutuncin da Owais Yayima mijinta. Babu kunya Pravin Yace"Owais kai har yanzu yarone, duk abunda zaka fada min ba zan ji haushi ba, Ina yi maka uziri, kuma magana da kaga Inayi don in kare dangin ku ne saboda halaccin da kuka Yi min....." Azafafe Owais Ya yunƙura Ya miƙe tsaye, Yana naɗe hannun rigarshi tamkar Mayun wacin zaki haka Ya tunkari Pravin, An rasa wa zai dakatar dashi, kafin Owais ya ƙaraso Pravin yayi saurin nufar ƙofa ya buɗe ya fuce yana huci Ya maida ƙofa Ya datse. Juyawa owais yayi ya koma inda ya tashi ya zauna. Da buɗar bakin Prime minister sai cewa yayi"My son ka yi abunda Ya dace" wannan maganar Ta hateem ta ta6a zuciyar Hajiya saratu Ranta a6ace tace"yaya hateem, kana goya mashi baya saboda Yaci mutuncin mijina"? Prime minister bai tanka mata ba, bai kuma ɗago da ido Ya kalle ta ba. Hakan Ya ƙara 6ata mata rai, harara tadinga jefawa Owais Ko kallo bata ishe shi ba, baima san tana yi ba. Shi dai baba Obie, Ya zubawa sarautar Allah ido, don wannan fadan Yafi ƙarfin shi. His excellency abdul Razak ne Yace"Owais, Kai muke sauraro muna son jin ƙarin bayani dangane da Yaron daya rikiɗa da kuma Yarinyar dake atare da shi" Kusan mintuna da Yin maganar abdul Razak Kafin Ya furta"Marayune su goma sha ɗaya nake ruƙo a hannuna, dukansu agidana suke da zama, a ƙarƙashin kulawata," Iya abunda Ya furta mashi kenan "A ina ka tsince su"? Shiru yayi bai bashi amsa ba Har saida His excellency abdul Razak Ya maimaita mashi maganar a tunaninshi kobai ji mai yace bane "Sojojin america ne suka tsince su A daji, shine suka damƙa case dinsu a hukumarmu, saboda Yaran sun faɗi cewa Su Ƴan Nigeria ne, ɗaya daga cikin Yaran ma akwai mahaifinta mun same shi, muna zargin masuyin garkuwa ne suka sace su daga Ahlin su, shi kuma yaron aljanune suka shige shi a dajin sune suke canza mashi halitta, wannan shine Iya abunda nasani dangane da su" atakaice Ya ƙare bayanin. Gyaran murya senate Lafeef Yayi kafin Ya soma magana "Mun riga da mun Yanke hukunci, Bamu buƙatar Yaran su ci gaba da zama a estate dinmu! Saboda Lafiyar mahaifinmu, sannan mun yanke alaƙarka da su, shi kuma prime minister zai koma canada adai dai date din da aka bashi umarnin komawa, don ba zamu lamunci gangancinku na son taimako Ya jefa rayuwar Ahlinmu cikin matsala ba, don ni har Yanzu ban yarda da Yaran ba, tunkafin ma in gansu Hankalina bai kwanta da su ba, tayaya za'a tsinci Yara adaji sannan akawo su estate dinmu? Meyasa su sojojin american basu ruƙe su ba a hannunsu ba? Saboda sunsan ba alkhairi bane shiyasa suka manna maku su" fuskar shi babu annuri yayi maganar. Hankalin prime Minister Ba ƙaramin tashi yayi ba Jin abunda suka ce, kasancewar shi mutunne mai biyayya ga yayyan sa ko kara suka ajiye mashi bai iya ƙetare wa, mutun ɗaya ne zai Iya dakatar dasu wato mahaifinsu sai dai ga dukkan alamu shima Yana goyan bayan hukuncin da suka Yanke, Muryarshi asanyaye ya furta"kada kuyi min haka, saboda ku nazo ƙasar nan a ƙalla nakusa shekara ban samu damar zuwa gida ba, Yanzu Idan na koma bansan ranar dawowa ba, Baba ka sanya baki a maganar nan" His excellency Deen dake zaune Yace"Idan saboda mu kazo ƙasar nan, kada ka damu, ka tafi kawai mu zamu zo inda kake, idan ma takama duk sati zamu Iya shigowa Canada kasan bamu da matsalar abun hawa" ya faɗa yana ƙara jaddada mashi"zamu Iya barin aikinmu mu ɗauki hutu saboda kai, munyi maka alƙawarin hakan, zamanka a ƙasartamu ne bamu yarda da shi ba, don ba zamu yi gangancin da zaka cutu ba har wani abun Ya same ka, Idan ka manta wanene kai bari in tuna maka, prime minister na ƙasar canada" duƙar da kanshi ƙasa yai hawaye tuni sun cika idanuwanshi, bakomai yake jimawa ba face Yaron daya ƙwallafa ran shi, yasan idan harya haura ƙafa yabar ƙasar nan da wuya su sake haɗuwa, watakil ma daya daga cikinsu yabar duniyar batare da sun yi tozali da juna ba. Jikin Chief owais yayi sanyi laƙwas, hankalinshi na akan prime minister, shi kadai Yasan damuwarshi His excellency abdul Razak ya numfasa kafin ya ɗaura da cewa"kai kuma Owais, ba zamu hana Ka Yin aikin ka ba, sai dai babu zancen Yara su cigaba da zama agidan nan, ka kaisu gidan marayu ka haɗa su da wadanda zasu cigaba da rainonsu" Takaici Ya hana Chief Owais furta masu komai, gaba ɗayansu hankalinsu ba akwance Yake ba. A hankali Baba Obie Yake kallon fuskar Prime minister data Chief owais, ga dukkan alamu Ya fahince su sai dai Yana jin tsoron wani abu Ya same su ta silar taimakon da suke Yi, shiyasa bai dakatar dasu senate lateef ba. "Baba, dan Allah kace wani abu, nasan zaka fahimce ni, wallahi Ina ƙaunar Yaron, baka ganshi ba Yana kama dani da Nazli, komai namu iri ɗaya kamar ni na haife shi" muryarshi tamkar zai fashe da kuka yayi maganar, basu ta6a ganin raunin prime minister ba sai Yau da Allah Ya jarabce shi da ƙaunar wani bare "Hateem! Wannan bai shafe mu ba, kowani ɗan adam yana da masu kama dashi a duniyarnan, shi kuma mugun mutun ba'a gane shi a suffar shi yakan shiga cikin mutanan da yake hari yayi rayuwa dasu na tsawon lokaci Yana kyautata masu rana ɗaya yake tarwatsa su da makircin shi, na fadi wannan maganar ne don ni har yanzu ban yarda da yaron ba, dashi da sauran ƴan uwanshi, mutanan da aka tsinta a daji, wama yasani ko ƴa'ƴan aljanu ne kuka dauko mana" senate Lateef ne ya faɗa Yana watsa hannayen shi. A hankali prime minister Ya zura hannu cikin aljihu ya ɗauko wayarshi, wadda tun safe rabon shi da ita, a gida yabarta gudun kada atakura mashi da kiraye kirayen waya, sai ɗazu da suka shiga gidan Ya kar6eta daga hannun gimbiya mujeedat. Layin Sharufudeen Ya dannawa Kira, bugu uku Yai picking, "Ina agida, dan Allah kazo, idan ba haka ba komai zai Iya faruwa" On the other hand muryar sharafuddeen Ta amsa mashi da toh, gani nan zuwa, ka kula min da kanka" amsa mashi yai da toh kafin yai rejecting kiran "Meye amfanin Kiran Sharafudden da kayi? Dakai dashi duka a ƙarƙashin ikon mu kuke, mune agaba daku" cikin nuna isa senate lateef Ya furta maganar Cikin sanyin murya Hateem Yace"nasan da hakan Yaya, amma shi zai Iya fahimtar zuciyata fiye da kowa, kuma zai kwantar min da hankalina" "Kana nufin mu bamu Iya kwantar maka da hankalinka? Kodan saboda shine shaƙiƙinka"? A harzuƙe senate Lateef Ya furta maganar Da sauri Baba Obie Yai masu gyaran murya gudun kada su fara Yi mashi ƴan ubanci abun da Ya tsana arayuwarshi. Gaba ɗaya Hankalinsu ya dawo kanshi"Ya Isa Haka! ya Isa, bana son nasake Jin wani Ya furta magana acikin ku" Shiru sukayi batare da wani ya kuma cewa Uffan ba "Baba abincin fa Yana hucewa, Yakamata Kaci" hajiya saratu ce tayi maganar cikin nuna damuwarta Kallon Owais yayi nan take Ya fahimci me Yake nufi Hannu owais Ya sanya cikin plate din da hajiya saratu ta zuba mashi abinci Ya soma ɗebowa Yana bashi abaki Yana ci, Hakan Ya ƙara 6ata mata rai, wato ita ta bashi abinci da hannunta Yaƙi Ci sai Owais daya fi ƙauna, shi ya za6a ya bashi abinci Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi tana fadin"Baba Allah Ya ƙara Lafiya, Ni zan wuce ɗaki" bata jira amsar da zai bata ba tayi saurin fucewa daga ɗakin. Senate latef ma ranshi ya sosu, duk irin rashin ɗa'ar da Owais Yayi ma Pravin baba obie bai dakatar da shi ba, after that Ya sanya shi bashi abinci abaki, bayan Hajiya saratu itace tafara Yunƙurin bashi amma Yaƙi kar6a, ba tun yau ba ya saba nuna banbanci akan Sauran Jikokinshi da Owais, Hatta Ya'yan Hateem Yafi Ji da su akan nasu me hakan ke nufi"? Aranshi ya saƙa maganar (Nidai nace na shiga uku, Kada afara Ƴan uba A family Obinna, Rikicin zai haɗe mana) Yayin da chief Owais Yake ba baba Obie abinci abaki, Ya tsare shi da ido Yana bin shi da kallon so da ƙauna kamar zai haɗiye shi, Lemu mai sanyi ya zuba mashi a cup Ya miƙa mashi, Ya sanya hannu Ya kar6a Yana sha, har cikin ranshi Yaji dadin hakan aduk lokacin da ranshi ya 6aci indai Owais Yana atare dashi wani irin sanyi ne yake ratsa zuciyarshi tuni yake neman damuwar Ya rasata. In a respectful voice Chief Ya soma yi mashi magana, ta yadda babu mai iya jin su. "Kai kadai ne zaka Iya fahimtata, saboda kai ka raine ni tun ina ƙaramina, aduk lokacin da na sanya buri akan abunda nakeson cimmawa kaine kake ƙarfafa min gwiwa don ganin nakai ga matakin nasara, babana kada ka bari wannan karan in faɗi ƙasa, yakamata ka sanya baki awannan maganar, kasan bazan ta6a kawo wani abu da zai cutar dakai ba, Haƙƙina ne in kareka daga dukkan wani abun farmaki, yaran nan mutanene kamar kowa, basu da niyar cutar da kowa, saida na zurfafa bincike akansu na tabbatar da hakan tukunna na kawosu cikin gidana, bazan Iya yin nesa da su ba, Kuma bazan Iya dakatar da hukuncin da iyayena suka zartarba, amma kai zaka Iya dakatar da su,' cikin tausasa harshe Ya ƙare maganar tare da ruƙo hannayen baba obie acikin nashi, Ya ruƙe su sosai. "Baba, Yaran nan basu da kowa, suna buƙatar wadanda zasu tallafi rayuwar su, nasani ba dole saini zan taimake su ba amma na riga dana daukarwa kaina alƙawarin bazan ta6a rabuwa dasu ba, A yau ina so ka nuna min ƙaunar da kake Yi min, da goyan bayan da kake bani, baba kada ka bari arabani da yaran nan ko a tursasamin akan in fitar da su daga gidana......." yanayin yadda owais yake yi mashi maganar yayi matuƙar karya mashi zuciya, tuni jikinshi yayi sanyi laƙwas, launin idanuwanshi har sun ɗan canza kala. Shi kadai Yake jin me owais Yake Fadi mashi, sauran saidai su bi da ido, prime minister dai tunda ya dukar da kanshi kasa bai ƙara dagowa ba, shi kadai Yasan abunda ke damun shi, zuciyarshi tafarfasa take yi tamkar ana rurata da garwashin wuta, Aranshi ya ayyana koda zai bar ƙasar bazai daina bin diddigin rayuwar yaron ba, bazai ta6a bari Ya wulakanta ba. Lumshe ido Obie Yai a hankali ya ware su kan fuskar Owais "Zanyi tunani akai" atakaice Ya furta mashi maganar, ajiyar zuciya chief owais ya sauke, ya riga dayasan ƙaunar da yake mashi bazai Iya jurar 6acin ranshi ba "Allah ya ƙara maka lafiya kakana, da anjima kafin ka kwanta bacci zanyi maka tausarnan dana saba yi maka duk idan nazo nigeria, nasan zaka ji daɗi" Dariya baba Obie Yai har hakoransa suka bayyana fafare ƙyal da su "Owais ka iya fadanci, kasan duk wata hanya da zaka faranta min, Allah yabarmin kai jikana" amsa mashi yai da Ameen. daga haka basu ƙara Yin magana ba, sai dai kallon juna da sukeyi jefi jefi, su sanate lateef sun zama Ƴan kallo, kamar hotuna haka suka zauna zugudun suna kallon su. Bayan wani lokaci Jiniyar Motoci ta karaɗe Estate din, nan take ransu Ya basu cewar Mai girma sharafudeen ne Ya ƙaraso gidan, tun abakin entry hall din shiga falo, Security details dinshi suka dakata da take mashi baya kamar yadda ya basu umarni, shi kadai Ya shiga Gidan Cikin shiga ta alfarma tsadaddiyar shaddace a jikinshi launin kore, duk Inda Ya gifta masu aikin gidan a gaggauce suke russinawa su gaishe dashi kamar zasuyi mashi sujjada, A main falo din gidan Yaci karo da sheikh Imam tare da Taj zaune saman Royal sofa, Hankalinsu kwance suke tattauna fira atsakaninsu, sunyi jiran ganin mutanan gidan shiru basu fito ba har sun fara tunanin kodai babu lafiyane? Musamman lokacin da pravin ya fito daga dakin baba obie ko kallo basu ishe shi ba, har kallonsu yayi amma yaƙi tanka masu, hakan ya sosa zucuyarsu, haka itama hajiya saratu tazo ta wuce ta falon bata bi takansu ba, har ƙwara su twins sun gaishe da sheikh Imam, suka kuma gaida Taj kafin suka wuce. Zuwan sharafudeen Obinna, Ya faranta masu rai, tunkafin Ya ƙaraso garesu Yake Fadin"wa nake gani kamar babana Imam malik," miƙewa Imam yayi ya nufe shi suka rungume juna kafin suka raba jikinsu "Ashe rai kanga Rai? Baba Imam sai yau zansa ka a idona? Gaskiya nayi fushi" Ya faɗa Yana haɗe fuskarshi Dafe kafaɗarshi sheikh Imam Yayi"Masha Allah, Sharafuddeen Bana ƙasar, shiyasa baka ganina akai kai, amma yanzu tunda nazo in sha Allah zan dinga shigowa Villa muna gaisawa' Sharafudeen na murmushi Yace"Idan ma bakazo ba, Ni zanzo har inda kake, wallahi nayi farin cikin ganinka, tun yaushe kazo ƙasar" Shiekh Imam Yace"Yau da sassafe Nayi sammakon shigowa ƙasar, saboda kiran da ɗan uwanka yayi min" "Masha Allah, Ina fata komai lafiya" Sheikh Imam Yace"lafiyalou, Ga abokin Aikin Owais Ku gaisa da shi" Ya faɗa Yana nuna mashi tajudeen dake azaune, kamar ya sanshi haka Ya nufe shi da fara'a, da sauri Taj Ya miƙe suka rungume juna, haƙiƙa yasha ruwan mamaki, bai ta6a ganin mutane masu ruƙe da babban muƙami da suke da sauƙin kai irin Hateem da ɗan uwansa sharafuddeen, yajima yana mamaki da al'ajabinsu, kowa nasu ne basu ɗauki duniya da zafi ba. Raba jikinsu yayi daga na juna"yalla6ai sannu da zuwa, Ina wuni, Ya hidima da jama'a, ubangiji Allah ya taimaka" "ameen mutumina, Ina fata na same ka Lafiya"da mamaki Taj yake kallonshi jin ya kira shi da sunan mutumina kamar yadda yaji ɗazu Hateem Ya kira shi da sunan Ganin alamun ruɗu akan fuskarshi yasa mai girman sharafudeen cewa"Owais Ya fada min komai dangane dakai, ganinka ne kawai ban ta6a yi ba, nasan zakayi mamaki dana gane ka ba tare dana tambaya ba" ya faɗa yana sakar mashi murmushi, shima taj din murmushin yayi har cikin ranshi ya ƙara ƙaunar Chief owais. "Babu isasshen lokaci, In sha Allah zan samu time din da zamu tattauna dakai" ya fada Yana bubbuga kafaɗar taj da hannunshi. "Toh Yalla6ai, nagode sosai" kallon shiekh Imam yai"baba mu shiga daga Ciki" yai maganar tare da ruƙo hannunshi suka nufi part din baba obie, Zama taj yayi akan sofa, fuskarshi ɗauke da murmushi, Ji yake tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha, acikin ranshi ya furta"Allah nagode maka da haɗani da mutanan kirki acikin rayuwata" Wayarshi Ya zaro daga aljihu ya soma tunanin Kiran Big guy don Yaji awani hali su Unaisah suke aciki sun ci abinci ko kuwa. Kiran na shiga big guy yayi picking "Ya mutumina kana Ina ne? Na dawo gidan na taras baku nan" "Mun shigo gidan baba Obie ne mu dukanmu muna anan" "Okey, Ina fata komai na tafiya yadda yakamata" "Taya zan sani, nifa ka ganni nan a falo, Ina zaman jiran fitowarsu, Allah yasa dai mu ji alkhairi, don kuwa naga wannan ba'indiyan da kake bani labari sai mazurai yake yi, ko gaishe mu bai yi ba" Sautin dariyar big guy ne Ya karaɗe kunnuwanshi "Itama wannan matar, mai kama da su chief owais ta fito tagan mu bata gaishe damu ba" "Dama ya za'ae ta gaishe dakai, taga baƙuwar fuska, matar da bata sakar ma bare fuska, sai dai shi sheikh Imam din ne dai bata kyautaba tun da aminin baban su ne, wata'ƙilma bata ganku bane shiyasa bata gaishe da shi ba" Boss yace"nima nayi tunanin hakan" "Shi kuma wannan gabjejen ƙaton dangin su kirishna, kabarshi kawai, mutumin banza, baida mutunci, shi da yazo cin arziƙi yayi kane kane a dangi" da zolaya big guy yayi maganar, taj yayi dariya cike da nishaɗi yake sauraron shi. "Very soon zamu yi mashi korar kare daga family din, tun da ba gidan ubansa bane" acewar big guy gaba ɗayansu suka tuntsire da dariya Bayan sun tsagaita Boss man Yace"dama na kirane don inji lafiyar ƴa'ƴana" "Kai dai fadi gaskiya, Ko dai ka Kira Kaji Lafiyar Jarin ka, Ifrituwar Yarinya wlh ɗazu data la6e a bayan labule, naso ace ka bari chief Ya shaƙi wuyanta, Yasin sai tayi jinya a gadon asibiti, Yarinya sai ƙiriniya kamar ansanya mata battery" fashewa taj yayi da dariya "Cin mutuncin Ya isa haka, Na lura baƙin ciki kake Yi da ita shiyasa ka sanya mata ido, Ni dai yanzu fada min suna ina. Sai da Ya Mula Yasha Iska tukunna Yace"Sun ci sun ƙoshi, kowannansu Ya koma dakinsa, harma sunyi wanka sun canza sutura, Na rakasu dakin Danish sun ganshi, Yanzu haka kowan nan su Ya koma dakin shi," Ajiyar zuciya Boss man ya sauke"Alhamdulillah, Naji dadin jin hakan, inataso in tambaye ka ka tuntu6i 6angarensu Salsabeel"? "Bakasan meya faru ba" nan fa big guy ya kwashe duk abunda Ya faru Ya sanar dashi, hankalinshi Ya dan tashi "Bawan Allah jazz, abu baiyi dadi ba, Allah ya bashi Lafiya, In sha Allah zamu fidda lokaci muje duba shi, Har Yanzu suna a asibitin ne"? " Na kira Major Waya Ya fada min cewa An sallame su, Jikinshi yayi kyau da sauki, naso na kira jazz din awaya ashe ya mantata acan gidan Yaran, sai dai muka gaisa da shi ta wayar Major har nayi mashi Ya jiki" Boss Yace"ka kyauta, Nima zan kirashi zuwa anjima kafin muje gidan nasu, amma fa yakamata Yaran nan a ƙara masu tsaro" Big guy yace"Nima nayi tunanin hakan, Jira nake komai ya lafa Yaron nan Danish Yaji sauƙi kafin mu tattauna akan yaran idan za'a haɗesu gida ɗayane ko kuma za abarsu acan din, but Yanzu zan tura da jami'an da zasu basu tsaro in sha Allah" Sunjima suna tattaunawa atsakaninsu daga bisani sukayi sallama da junansu. ________________________✍️ Gaba ɗaya Sun hallara, Bayan Shigar Mai girma sharafudeen da Sheikh Imam, Cikin girmamawa da karramawa suka Yi mashi Kyakkyawar Tarba sanin matsayin shi awurin mahaifinsu Obie, kusan aminine shi, Ya jima Yana yi masu hidima da ta shafi 6angaren addinin islama, shiyasa suke girmama shi suna ganin ƙimar shi da darajar shi acikin idanuwansu, Baba Obie Yayi farin Cikin Ganin shiekh Imam har Yana fadin Ya akai Prime minister bai shigo da shi ba, shiekh Imam Yace shi ne Ya buƙaci Zama a falo, Obie Duk da bai jin dadin jikinshi sai da Ya miƙe adaddafe da taimakon chief owais daya ruƙo shi, ya samu damar rungume imam malik, fuskokinsu ɗauke da matsanancin farin ciki sunyi matuƙar yin kewar Junansu, Mai girma Sharufudden tuni ya nufi ƴan uwanshi tun daga kan senate lateef, duk wanda Ya miƙa ma hannu suka gaisa daga bisani sai Ya yi hugging dinshi, Har yazo kan Hateem wata irin runguma yayi mashi tamkar zai maida shi ciki, Hateem yayi murnar ganin ɗan uwan nashi yasan shi kadaine zai fahimci zuciyarshi ya kuma share mashi hawayen shi, bayan sun kammala Ƴan gaishe gaishen nasu, Sheikh Imam malik ya fara Yi masu addu'o'i kamar yadda yake yi masu duk inyazo gidan, hakan ba ƙaramin daɗi yake yi masu ba, amsa mashi suka dinga yi da ameen ameen, har ya gama yin addu'o'in nashi, baba obie yace yaji dadin zuwanshi yana da tabbacin zai taimaka mashi wurin warware matsalar data ke ƙoƙarin kunno kai a zuri'arshi, Imam Malik yace shima yaji dadin zuwa Gidan kuma in sha Allah komai zai tafi dai dai, bi'iznillah, amma kafin su fara zaman tattaunawar, duba da gabatowar sallar Magrib Yana ga su bari su yi salla, harma da Isha'i kafin su dawo ayi zama na musamman don asamu maslaha, gaba ɗaya sunyi amanna da maganar Imam malik, ba tare da 6ata lokaci ba, kowannansu ya dauro alwala, suka fito atare suka ɗunguma zuwa harabar ajiye motocin gidan, sojojine suka take masu baya har zuwa masallaci, acan masallaci suka haɗu da Sir Mubarak tare da Zaki sunji dadin ganin shi tun daren Jiya daya tafi suna tsaka da yin firar yaushe rabo sai yanzu Allah Ya haɗa su dashi, bayan sun fito daga masallaci suka tsaya suna ƙara gaisawa, anan Sir mubarak Ya sanar da su uzurinshi na rashin zuwa gidan, sai dai bai sanar dasu game da zargin jazz da yai har takai shi ga bugunshi yadai ce masu Jazz Ba lafiya sun kwana asibiti Jiya sai Yau suka dawo, Hankalin baba Obie Ya tashi jin cewa Jazz din shi baida lafiya, duk yabi ya rude, har saida Sir mubarak Ya kira mashi jazz a waya yaji muryarshi da sauƙi har yana zolayar shi yayi missing din ganin gemun shi, shifa lafiyarshi qalou jinyace tadan lokaci, kada yai tunanin zai riga shi mutuwane shima sai yaci zamaninshi ya tara ya'ya da jikoki, dariya baba obie yayi sosai, sun ɗan jima suna yin wayar kafin Ya miƙa ma su hateem wayar duk suka yi mashi ya jiki ya amsa masu da sauƙi, hatta imam malik saida yayi waya da jazz hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Jazz ba ganin yadda suka nuna damuwarsu akanshi, bayan sun kammala yin wayar ne sir mubarak Ya amshi phone dinsa Ya tura aljahu, ɗaya bayan ɗaya suka shiga motocinsu, a jere suka nufi Estate dinsu......✍️ *❤UMMIN AMERICA❤* Moving quickly yake tattaka stairs, tun kafin ya ƙarasa ƙofar room dinta, sautin daddaɗar Muryarta dake yin qira'ar karatun alƙur'ni mai girma ya ratsa kunnuwanshi, har saida ya lumshe idanuwamshi saboda yadda karatun nata ya ratsa zuciyarshi, sautun tamkar ana busa sarewa tsabar daɗinta, daƙyar ya samu damar tattara natsuwarshi da kamalarshi ya nufi ƙofar, ya sanya hannu yaɗan yi knocking dinta, shiru babu alamun zata dakata da yin karatun balle harya ya sanya ran zata bashi permission din shiga ciki, kusan sau biyar yanayin knocking shiru taƙi tanka mashi, A ƙarshe ya yanke shawarar buɗe ƙofar da kanshi, A hankali Ya zuge ta, tana ƙarasa buɗewa Ya haura ƙafarshi cikin ɗakin bakinshi ɗauke da sallama, yayin da idanuwanshi ke kallonta, tana daga zaune saman darduma, dogon hijabin dake ajikinta launin maroon yayi mata kyau, ya bayyana ainihin wacece Ita, bakomai ne ya karya mashi zuciyarshi ba face ruwan hawayen da suka wanke fuskarta sharkaf, Eye lashes dinta sun cukurkuɗe dakyar take Iya kallon Qur'anin data buɗe tana karantawa, duk da sanyin A.c na ɗakin hakan bai hana ta zubda gumi ba...... Ya fahimci batasan da shigowarshi ɗakin ba, hakan yasa shi ɗaga murya ya furta sunanta"UMMI!" Ras Taji gabanta ya faɗi don sai taji tamkar muryar Sheikh Imam ce Ta ambaci sunanta, a wani irin firgice ta yunƙura ta miƙe tare da yin saurin kai idanuwanta da suka kaɗa jawur kan fuskar shi, wata irin nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke ganin Big Guy ne , fuskarshi sanye da face mask. Ganin irin kallon da yake yi matane yasa tayi saurin share hawayen fuskarta. Wani irin tausayintane Ya kama shi, bai ta6a jin ta burge shi ba irin yau. Calmy Ya furta"Am sorry, na shigo maki ɗakin without asking for ur permission, na kwankwasa ƙofar shiru baki buɗe ba, shiyasa na yanke shawarar shigowa" Shiru tayi bata ce mashi komai ba, aranta taɗanyi mamakin tausasa harshen da yayi wurin yi mata magana, don tun ranar da suka fara haɗuwa ta fuskanci baida sauƙin kai, musamman jiya da ta ƙure ma su batul sanyin A.c Ya rufe ta da faɗa kamar ubanta abun ya ƙona mata rai, ta kuma yi mamakin zafin kanshi don tun da take arayuwarta wani namiji bai ta6a yi mata hakan ba saboda kyawun surarta da ke jan hankalinsu.. "Kin yi shiru baki ce komai ba"? Muryarshi ce ta fargar da ita, adabarbarce ta furta"badamuwa" Goya hannayensa yai kan chest dinsa Ya nufe ta har sai da yaje dab da ita tukunna ya dakata "Dama kin iya karatul alƙur'ani? da sanya hijabi"? "Kamar yadda ka gani" ta bashi amsa atakaice" Lumshe idanunshi yadanyi before ya furta"kin kusa tafiya da imanina, inason mace me ilmin addini" "Ni bani da ilmi, Idan ma abun da ke aranka kenan to ka daina, Ni karuwa ce, zaifi ka fuce min daga ɗaki tun kafin in rinjayi zuciyarka" fuskarta adaure babu annuri ta furta maganar. Dariya yai ta cikin face mask dinsa sautin ke fita, "Da ace kinsan wanene Ni, da baki furta wannan maganar ba, domin kuwa ke bakomai bace akaina" yanayin yadda ya furta maganar yaɗan so ya jefa ta aruɗani, sai taji Muryar tamkar ba ta shi ba. tafin hannayensa biyu ya daura akan gefe da gefen fuskarta, nan taji wani irin abu ya ziyarci zuciyarta "Na damu da halin da kike aciki, shiyasa nazo don na dubaki, ɗazu muna a falo, naga yanayin da kika shiga ganin Imam malik, kin san shi ne"? Aharzuƙe Ta janye hannayensa tana girgiza kai tace'bansan shi ba, Yau na fara ganin shi, Ni da ba'a Nigeria nake ba taya zan san shi ma" ta faɗa tana haɗe fuskarta. "Hakane, amma meyasa kika gudu kina kuka"? Rai a6ace tace"Idan wannan ne ya kawo ka ɗakina, Dan Allah Ka fuce ka bani wuri," Gyaɗa kanshi yai"Shikenan, nadaina, am sorry idan na 6ata maki rai, kamar yadda na fada maki, Na damu dake ne, wunin yau baki ci abinci ba, Kin hana kanki sakat, Ki faɗamin meke damunki"? Yamutsa fuskarta tayi kafin tace"babu abun da ke damuna, kawai bana son kowa atare dani, bana son takura, kuma bana jin yunwa shiyasa ban nemi abinci ba" atsiyace ta ƙare maganar, ya natsu yana kallon small lips dinta tamkar na jinjiri "Haƙƙin mu ne mu kula da cin ki, dan Haka dole ki ci abinci ko kina so ko bakya so," ya faɗa yana ɗaga mata gira Harara ta galla mashi"babu wanda ya isa yayi min dole, ciki dai nawa ne idan naga dama zanci abincin basai an tursasa min ba" "Kidaina yi min magana da tsawa, kodan saboda kinga na damu dake ne"? Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh, "Da zaka fuce ka barmin ɗakina da hankalina sai yafi kwanciya" Shiru ya yi jimm tamkar baiji dadin maganarta ba, tayi tunanin zai tafi amma sai ta ga ya sanya hannun shi na dama ya ruƙo face mask din fuskarshi, slowly ya zame shi Wata irin furgita tayi lokacin da fuskarshi ta bayyana, Har saida ta ja da baya da baya ta kusa faɗawa mirror chair ta dafe ta da hannu ɗaya, idanunta amatuƙar zazzare take kallon shi tamkar ƙwayar zasu faɗo ƙasa la66anta na rawa ta furta"da.....ma kai ne? tayaya akai ka shigo gidan nan"? Wani irin shu'umin murmushi ne ya bayyana akan fuskarshi, kalar na tantiran ƴan iska, waɗanda suka shahara afagen iya shaidanci Lokaci ɗaya suffarshi ta ƙara bayyana, faffadan kirjinshi Ya buɗe sosai. Zame rigar jikinshi yayi, wani irin murɗaɗɗen damtsen hannu ne dashi, gaban kirjinshi kuwa da bayanshi zanan tattoo ne 6aro 6aro, kai daga ganin wannan ko acikin shaidanun ibliss ne shi, Lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai, ya gigitar da ita, jikinta ya soma yin kakarwa, duk tabi ta ruɗe, asaman gadonta Ya jefar da long coat dinsa Muryarshi tamkar ta mashayin giya ya furta"Kin tsorata ne"? Sam takasa furta magana, tamkar an ɗaure maƙoshinta, yanayin yadda numfashinta ke fita da ƙarfi kirjinta har sama da ƙasa yake yi, Tuntsirewa ya kuma yi da dariya, haɗi da tausasa harshenshi Ya furta"ba fa yau kika saba gani na ba, ni ne dai naki ɗin nan da kika sani" Yawu ta haɗiya Kutt! Sautin Ya fita, daƙyar Ta Iya tattara kalmomin dake akan harshenta ta furta"tayaya akai ka shigo gidan nan dake atsare da Jami'an isod, Bayan haka ko'ina akwai CCTv cameras saƙo da lungu, dan Allah ka faɗamin ta wace ƙofa ka shigo, kuma ya akai ka sanya kalar kakinsu? sannan kayi min suffar big guy" a razane take jefa mashi tambayoyin, abunne yafi karfin kwalwarta, mutun kamar aljani, takasa yadda da cewa shine, gani takeyi kamar mafarkine takeyi Cikin Takun Izza Ya nufeta, dab da ita ya tsaya, tare da ɗaura hannayenshi kan bayan kujerar da ta jingina bayanta. Can ƙasan maƙoshi Ya furta"Ummi, kinsan wanene ni, akan buƙatata zan iya yin komai, nagaza jurewa ne shiyasa na tako da kaina nakawo kaina inda kike....." da ƙarfi ta furta"baka bani amsar tambayar da nayi maka ba"? "Kada ki ƙara yi min magana kina ɗaga min murya" atsorace ta jinjina mashi kai Alamar toh Lumshe idonshi yadanyi na wani lokaci kafin ya furta"Idan kin yarda dani ki daina tambayata bana so, duk abun da nayi nayine saboda ke" ajiyar zuciya ta sauke, lokaci ɗaya taji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta, kuma nan take taji ta aminta da kalamanshi, ɗaura hannayenta tayi saman kafaɗunshi, tana faman lumshe idanu ta furta"'I'm glad to see you, My controller, saboda a ƙuntace nake, bana Iya fita koda kofar gate ne, sun hana rayuwata sakat saboda aikin da nikeyi masu babu shige babu fuce, tamkar prison haka nake jin kaina" Shu'umin murmushin gefen fuska ya sakar mata, tare da kashe mata ido ɗaya, hakan ba ƙaramin jefa ta yanayi yayi ba, A hankali Ya ruƙo ƙasan hijabin jikinta, ya yaye shi tare da jefar da shi kan gadonta, ruƙo gaban jallabiyar jikinta yai da hannu biyu, tun daga sama ya direta ƙasa, batare daya zuge zip dinta ba, sai da ya rage daga ita sai pant da bra tukunna Ya dakata, yana duban fuskarta, numfashinta harya fara canzawa, da wani irin huci yake fita, baiyi mamakin ganin cukowar kirjinta ba, yana ɗaya daga cikin abunda yake ƙara gigitar dashi akanta, idan zai shekara baya tare da ita, duk ranar da ya dawo gareta, baya ganin ci baya sai dai ci gaba, dirin jikinta natural ne. Ɗaura hannayenta tayi saman kafaɗunshi, yai saurin hade bakinsu wuri guda tamkar zasu cinye harsunan junansu, Dungurugum ya ɗauketa da hannayenshi, ya nufi toilet da ita, yana shiga ƙofar ta datse. wani irin sautin gurnanine ya soma fitowa mai haɗe da nishinsu tamkar namun dawa suna fafatawa, kafin wani lokaci sautin sambatun ummi ya karaɗe ɗakin haɗi da ƙarar da take saki tamkar zata fasa bango............." *Daga Alƙalamin Boss Bature💋✍️* Mu haɗu Jibi Idan Allah yakaimu da rai da Lafiya🌹 *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura* 3196407426 First bank Bature Hafsat Muhammad, *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida* ~TAKUN ƘARSHE~ _______________________Boss Bature✍️ *😈PRAVIN😈* A kwance Yake saman gadon Hajjaty, Idanuwanshi suna fuskantar Ceilling, tsantsar 6acin raine akan fuskarshi, ranshi ya 6aci da korar karan da Chief Owais yayi mashi agaban su senate lateef, bakomai yafi ƙona mashi rai ba face yadda suka gaza dakatar da shi, hakan ya ƙara tabbatar mashi da cewa shi bakowa bane A family din, Kwandon shara yafi shi amfani, tsawon lokacin da yake akwance babu sallah babu salati, Yana ji anata kiraye kirayen sallar magrib har aka fara na isha'i bai motsaba, yaci alwashin sai Ya tarwatsa zuciyar owais, yajima yana da wannan burin Allah bai bashi ikon yin hakan ba, amma yanzu yafara tukfa da warwara akan ta wace hanya zai 6ullo don ganin ya karya mashi zuciya"? Miƙewa yayi daga kwancen da yake, ya jingina bayanshi da pillow, fuskarshi babu annuri ko misƙala zarratin, tunani yaci gaba dayi akan ta wace hanya zai ta6a zuciyar chief owais ta yadda zai azabtar da rayuwarshi, yayi zurfi acikin tunanin shi motsin buɗe ƙofar toilet ya fargar da shi, hajjaty ce ta fito sanye cikin jallabiya ta ɗaure kanta da mayafi, alwala ta ɗauro, ganin shi azaune ne yasa tayi saurin furta"Pravin! Me kake yi har yanzu baka tafi masallaci ba? Ai nayi tunanin zan fito na taras babu kai aɗakin" shiru yayi bai tanka mata ba sai dai binta da yayi da idanu kamar wani mazuru. "Magana nake yi maka, ko akwai wani abu ne dake damunka? Naga 6acin rai akan fuskarka" Saukowa yayi daga saman gadon Ya nufe ta yana huci ya soma magana"Ni da wancan Uban ƴan Ji da kan ne, Harni zai kora daga ɗaki agaban Iyayenshi ba tare da sun tsawatar mashi ba"? Adabarbarce ta furta"bangane akan wa kake magana ba" Dogon tsoki Yaja kafin Ya kwashe duk abunda Ya faru Ya sanar da ita.... Cikin sanyin murya tace"Owais bai kyauta ba, amma kaima da laifin ka pravin, meyasa kake son shisshige masu ne? Tun da sun nuna basu so to ka daina mana, Ka tsaya A iya matsayinka na surukinsu......" wata irin gigitacciyar tsawa Ya daka mata, Har saida taji gabanta ya fadi, ta shiga zazzare idanuwanta akan fuskarshi Ya canza mata tamkar ba shi ba. Nuna ta yayi da yatsan hannun shi"Idan ba zaki kwantar min da hankalina ba, toh kada ki kuskura Ki yi abunda zai ƙara harzuƙa Ni" Muryarta Na rawa tace"Naji amma dole na fada maka gaskiya pravin, mu dukan mu muna fuskantar wulakanci daga wurin waɗanda basa ƙaunar mu a family din nan, kuma ba komai ya jawo hakan ba face zaman da kake Yi agidansu...." Idanuwanta acike tab da ƙwalla ta ƙare maganar. Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi na wani lokaci ba tare daya furta mata komai ba, har saida ta fidda rai da zaiyi mata magana tukunna Taji Yace"Naji zanyi tunani akan maganar, Yanzu akwai wani taimako da nake son Kiyi mini My wife," natsuwa tayi tana sauraron shi don jin me zaice mata. "Kinga ni bani da halin da zan Iya shiga cikin su don jin me zasu tattauna atsakanin su tunda owais yana nan bazai bari naje ba, Inaso kiyi min recording duk abun da zasu tattauna tun daga farko har ƙarshe" tsantsar ruɗanine akan fuskarta. "Akan wani dalili? Meye naka aciki da kake son jin sirrinsu"! Idanunta azare ta furta maganar. Matsawa yayi dab da ita, da yake ɗan duniyane sai ya sassauta muryarshi ta yadda zai shawo kanta. "My wife, mutanan sunyi mana halacci daga ni har ke, ba zamu so wani abu da zai cutar da su ba, ai kinga abun da Ya faru Jiya" daga mashi kai tayi alamar eh. "Maƙiyane suke ƙoƙarin halaka Baba Obinna, shiyasa suka Turo da macijin nan don Ya hakalar da shi" waro idanuwa waje tayi tamkar kwayar zata faɗo ƙasa. "Bashi kaɗai ba, Kowa Na family din nan zata shafa, abunda baki sani ba, Macijin Mutunne fa" dafe ƙirji tayi da hannu ɗaya amatuƙar ruɗe take kallon shi. Komai daya faru saida pravin Ya sanar da ita, hada maganar zuwan sheikh imam da canza halittar Danish, baiwar Allah duk tabi ta ruɗe tasha jinin jikinta. Muryarta na rawa ta furta"Inna lillahi Wa'inna Ilaihirraji'un, Afakaice Pravin Yasaki shu'umin murmushi, ganin Ya fara Yin nasara akanta, Yaci gaba da cewa"abun da nakeso na fahimtar dake, Ni ƙoƙari nake yi don ganin na taimaki rayuwar Ahlin nan, wallahi bana son abun da zai cutar da su, shiyasa nake shisshige masu don jin meke faruwa a tsakaninsu ta hanyar hakan nake taimaka masu wurin shawo matsalar dake addabarsu, ɗazu dana shiga dakin owais Ya hankaɗoni waje, zan wuce ta falo naga sheikh imam da wani mutum ban kulasu ba, saboda shi kanshi sheikh Imam din Ina zargin hada shi cikin masu shirya maƙarƙashiya a cikin family din nan" Girgiza kai hajjaty tayi"a'a pravin, bana tunanin hakan, Ina kyautata mashi zato, saboda shi aminin obinna ne, kuma yajima yanayi ma family din nan hidima, gaskiya Imam malik bazai iya yarda ahaɗa baki da shi don cutar da familyn obinna ba" Ta6e baki pravin yai kafin yace"hmm bakisan halin malaman nan ba, yawancin su fuska biyune dasu, A fili musa a zuci fir'auna, duk wanda fa kika ga ya ra6i familyn obinna ba alkhairi bane ya kawo shi" "Kana nufin hada mu kenan?" Hajjaty ta jefa mashi tambayar da buɗar bakinsa sai cewa yai"ai mu mun riga da mun zama jini ɗaya da su, ina magana ne akan ire irensu Imam malik masu zuwa kar6ar zakka" Shiru hajjaty tayi tana nazarin maganar shi, kafin tace"yanzu shi yaron yana agidan owais, tare da sauran yaran daka fada min"? "Ƙwarai kuwa, Ya kawo mugun abu ya ajiye agidansa, babu fa wanda yasan yazo ƙasar nan, shigowar sirri yayi, kedai kawai Allah ya shiga tsakanin mugu dana gari amma fa akwai matsala idan har basuyi gaggawar ɗaukar mataki ba......" ya faɗa yana mai nuna damuwarshi. Ruƙo hannayenta yai acikin nashi"My wife, Ki bani haɗin kai don ganin mun taimaki ahlin nan kodan saboda halaccin da su ka yi mana, Inaso muyi masu gwanintar da zasu yi alfahari da mu wata rana" wasa wasa pravin yadinga tunzurata har yasamu nasarar shawo kanta. Cikin sanyin murya tace"In sha Allah, zan baka haɗin kai mijina, zamu haɗa hannu don ganin mun yaƙi duk wani mugu dake da mummunar manufa akan zuri'ar baba Obie" da ƙwarin gwiwa ta furta maganar, babu wasa a kalamanta. Wani irin daɗine Ya ziyarci zuciyar pravin yayin da yake kallonta. "Zan tayasu da addu'a, ubangiji Allah Ya kare su daga sharrin maƙiya da mahassada, Ya Allah duk wani mai mugun nufi akan zuri'ar baba Obie, Ya Allah Ka toni asirinsa, ka hana shi zama Lafiya, Bayin Allahn nan ni ban ta6a ganin mutane masu kyakkyawar zuciya irinsu ba, amma ahaka wasu bakin ciki su ke yi da ci gabansu......" har cikin zuciyarta take furta maganar, don ita harga Allah tana ƙaunar familyn baba Obie, tana matuƙar sonsu bata son duk wani abu da zai cutar dasu koda kuwa Hajiya saratu ce. "Yanzu abunda za'ae, kiyi sauri Ki yi sallar, Idan Kika Kammala ki ɗauki wayarki ki tafi second falo, ina da tabbacin acan zasu zauna suyi tattaunawar, ki riga su zuwa ki saƙa wayar inda ba zasu gani ba, bayan kin danna recording, Inyaso daga baya idan suka tafi saiki koma falon ki ɗaukota ki kawo min, yaya sharafuddeen ma Yazo gidan, naji jiniyar shigowar motocinsu, Har leƙawa nayi ta window naganshi" Amsa mashi tayi da toh, ta nufi closet din kayanta ta dauko Hijab ta tura a jikinta, saida ta kabbara sallah tukunna Pravin ya shiga toilet domin yin alwala, a ɗakin yai sallar magrib da isha'i kafin Ya gama sallar, tuni hajjaty ta fuce daga ɗakin, zama yayi kan darduma yana ta yin saƙe saƙe acikin zuciyarshi, Kamar yadda ya tsara mata haka ta aiwatar, tun kafin su shiga falon hajjaty ta riga su zuwa ta kunna recording da dabara ta shiga falon kamar tana gyara shi, a hankali ta ajiye wayar a karkashin sofa table, kafin ta fito daga falon ta nufi kitchen domin shirya masu abun da zasu sha. Bayan tafiyar hajjaty, da ƴan mintuna Gaba ɗayan su suka shigo Second Falo din wanda ya kasance na musamman dake A gidan Baba Obie, an wadata shi da Luxury Furniture ba kasafai suke amfani da shi ba, sai Idan za su yi zaman tattaunawa tukunna ake buɗe shi, wani irin ni'imtaccen sanyin A.c ne ka ratsa cikinsa, dare ne tamkar da rana saboda wadatattun Chandeliers masu haska ko'ina sako da Lungu, Idan ba agogo Ka kalla ba ko sararin samaniya ba zaka ta6a gane dare ne ba a gidan baba Obie. Bayan kowan nan su ya samu wuri ya zauna saman sofa, Sheikh Imam ya fara buɗe masu taron da addu'a, kafin daga bisani, baba Obie yaba Owais damar yi masu bayani dangane da Yaran da yake ruƙo a hannun shi. A tsanake Ya labarta masu tun daga farkon zancen har zuwa karshe kamar yadda Ya fada masu ɗazu. Mutum ɗaya ne baisan da zancen ba, Lokacin da abun ya faru baya agidan sai yanzu yake ji daga bakin Owais. "Owais dama bayan yaran dake acan gidan da Jazz yake Aiki Akwai wasu A gidan ka" Fuskar Sir mubarak da alamun ruɗu ya furta maganar. Jinjina mashi kai Owais Yai alamar Eh, nan take ya yanke shawarar sanar dasu dangane da abun da ya faru tsakanin shi da jazz jin cewa sun san da zancen yaran, bayan ya labarta masu, kowan nan su ya jinjina ma lamarin sai dai har yanzu mutun uku basu Goyi bayan zaman Yaran a estate din ba. Sheikh Imam ya ɗaura da cewa"naji daɗin taruwar da mu ka yi anan kuma ina fata zamu samu maslaha, da farko dai Yaran ba masu cutarwa bane, ba abun da ku ke tsammani bane, Ni shaida ne akan hakan, Mutane ne su kamar kowa, hatta shi kan shi Yaron da yake rikiɗa cikakken mutunne, kamar yadda Owais ya faɗa maku Ni da kaina na duba shi, kuma nayi magana da shaiɗanun jikin shi, wataƙil ko dan baku ta6a ganin mutun ya rikiɗa bane akan idon ku, shiyasa abun Ya ruɗar daku, Amma Ni nasha gani akan idona mutun ya rikiɗa Koya 6ace Idan muka ja mashi ayar Allah....." ya ɗan dakata da yin jawabin yana kallon su, Senate Lateef ya haɗe fuskarshi babu annuri ko misƙala zarratin shi fa yana akan bakan shi. Duk sun natsu suna sauraran sheikh Imam sai da yakai Aya tukunna Senate Ya fara magana rai a 6ace"Ni bazan ta6a goyan bayan tsintattun Yaran su zauna a family din mu !! Bazai yiwu ba wallahi, Saboda Shi jiya mahaifin mu ya kusa zaucewa adaren jiya bai runtsa ba, Da firgici Ya kwana, sannan itama saratu bata runtsa ba a zaune ta kwana saboda gizan da macijin keyi mata, A haka akeson a Ƙaƙaba mana su a family? ya jefa tambayar yana kallo su sheikh imam babu wanda yai yunƙurin dakatar da shi "Ai daga ji babu Alkhairi Atattare da su yakamata aduba maganar“ ya faɗa yana mai ƙara jaddada maganar shi. Gaba ɗaya idanuwansu akan shi, sai da ya ƙare maganar, His excellency abdul Razak Yace"Ni ban hana ataimake su ba, Amma bazai yiwu su zauna mana a estate dinmu ba, tun da yaran basu da asali, me zai hana a ɗauke su akaisu Orphanage home dinmu dake anan garin Abuja, In yaso sai mu dinga tallafa masu, amma fa ban da wannan yaron mai fama da aljanu ba zamu lamunta da zaman shi agidan marayu ba, zai iya cutar da mutane, kawai aware shi shi kaɗai yayi rayuwarshi har zuwa lokacin da zai samu warakar lalurar shi" Tun da suka fara magana Shiekh Imam da chief owais suke bin su da kallo, Shi dai Prime minister ya rasa ta cewa ganin yadda suka haƙiƙance akan ƙin amincewa da zaman yaron, Mai girman sharafuddeen ma yana sauraransu sai dai hankalin shi yafi karkata akan ɗan uwanshi, ya fahimci hankalin shi ba a kwance yake ba dama shi tul fil azal bai cika son rikici ba mutunne ma'aboci son zaman lafiya bayason hayaniya. Gyaran murya baba Obie Yai masu, hankalinsu ya dawo kanshi. "Kun gama magana"? his excellency deen yace"Eh baba, mu kawai Yaron ke bamu son zaman shi acikin estate dinmu, su sauran Yaran ni bani da ja akansu, tun da su lafiyarsu ƙalau suyi zamansu agidan owais din ko akai su gidan marayun mu...." kafin Deen ya ƙare maganarshi, senate lateef yai hanzarin tarar numfashinshi da cewa"bazai yiwu ba, Nifa ban lamunta da su zauna a estate din nan ba, sannan dole ayanke alaƙar su da danginmu, idan taimakon nasu ya zama dole zamu haɗa masu kuɗin da zasu ishesu suyi rayuwarsu, shi kuma Prime minister Hateem satin da zamu shiga ya hanzarta barin ƙasar nan, zaifi mana kwanciyar hankali, tun da na fahimci idanuwanshi sun makance akan yaron da bai hada alaƙa da shi ba" ya faɗa fuskarshi aɗaure, yayin da yake kallon Prime minister Yaci gaba da cewa"Sarai kaga abunda ya faru adaren jiya, amma ka kau da idonka, damuwarka akan yaron ce ba akan mahaifinmu ba, maimakon tun da asussuba ka kamo hanya kazo gida donka duba shi ka ga ya yakwana jiya sai ba ka yi hakan ba duk kabi ka zauce akan yaron da bakasan asalin shi ba...." Tsabar yadda senate ke magana har wani gumi yake fitarta, duk da sanyin A.c na falon, Lamarin yayi mugun ɗaurewa Sheikh Imam kai sai faman jinjina kai yake yi, maganganun senate ba ƙaramin fusata Chief owais su ka yi ba, tun da ya duƙar da kanshi ƙasa bai ɗago da shi ba, ƙoƙari yake yi don ya lallashin zuciyarshi idan ba haka ba komai zai Iya faruwa!!. Senate yaci gaba da cewa"kai kuma Owais," ya faɗa yana nuna shi da hannu"ka 6ata min rai! Meyasa ka ke yin komai gamon kan ka? ba tare da ka nemi shawarar mu ba? ko dawowarka Nigeria Yakamata ka sanar damu, amma sai ba ka yi hakan ba kamar kai ke da kan ka, sannan ka kwaso mana wasu tarkace acikin family batare da ka sanar damu ba, me hakan ke nufi? Bamu da amfani ne ko bamu isa dakai ba ne?" a zafafe Senate Lateef yayi maganar yana duban chief owais, wanda yayi shiru yana sauraron shi batare daya yi yunƙurin tanka ma shi ba. "Allah Ya huci zuciyarku, Na fahimci gaba ɗaya ranku Ya 6aci dangane da abunda ya faru Jiya Ina mai baku hakuri amadadin Owais" mai girma sharafuddeen ne yayi maganar yana mai tausasa harshen shi. "Bai kamata kan wannan maganar mu ɗaga hankulanmu ba, Owais dai muke iko dashi, Sannan Kune manyan Family duk abunda kuka zartar dolen mu ne muyi biyayya akai, ko munaso ko bamu so," Jin maganar sharafuddeen yasa senate yafara sassauta fushin fuskarshi, hatta sauran sun ɗan samu natsuwa. "Baba, Hukunci ya rage naka, Kai muke sauraro duk abunda ka zartar dangane da yaran nan wallahi zamuyi maka biyayya" in a calm voice sharafuddeen ya faɗa yana duban baba obie. Gaba ɗaya hankali ya dawo kan Baba Obinna, dake zaune kan sofa, sandar shi tana a jingine da sofa hand. sun ƙagara da son jin amsarshi, saboda shi kaɗaine mai faɗa Aji. "Mubarak!" da sauri sir Mubarak ya ɗago ya kalleshi cikin girmamawa ya amsa mashi da na'am baba. "Banji kace komai ba" Murmushin gefen fuska Sir mubarak ya yi kafin yace"Baba, ni bani da matsala wallahi, yaran nan ba akaina zasu zauna ba, owais ne ke kula dasu akan me zan damu? Na yarda da shi kuma nasan bazai ta6a kawo abunda zai cutar da zuri'armu ba, Ni dai inayi mashi fatan Alkhairi duk shawarar da ka yanke zamuyi biyayya" Chief yaji daɗin maganar sir mubarak, dama yasan bazai bashi matsala ba. "Aminina, naji kayi shiru, inaso naji daga gare ka" baba obie ne ya faɗa yana duban Imam malik. Murmushi ya saki, Yana mai fara'a yace"wannan abu na ku ne na Ƴan siyasa, Kun san yanda ake jefa ƙuri'a waɗanda suka fi rinjayi, maganarsu yakamata aɗauka, Nidai anawa ganin kenan, Yaro dai bame cutarwa bane, jarabtace ta ubangiji babu wanda yafi ƙarfin Allah ya jarabce shi acikin mu, shi kuma owais Jinin ku ne Ku kan ku kun yaba da hankalinsa, ni banga wani abu da zaisa ace za'a yanke alaƙarshi da yaran ba yakamata aduba maganar nan" cikin Hikma Imam malik yake yi masu magana, har cikin ranshi baison yaji suna maganar korar yaran daga familyn Obie. Jinjina kai Baba Obie yayi kafin ya kai dubanshi ga sharafuddeen. "Meye ra'ayinka dangane da yaran"? "Baba, Ni bani da matsala, kamar yadda yaya Mubarak Ya faɗi, Nima haka, Kafin mu yanke hukunci yakamata mu yi wa kan mu adalci dasu kansu Yaran, Abun da Ya faru da ɗan uwansu bayin kanshi bane, Allah ne yake jarabtarsa, gaba ɗayanmu musulmai ne kuma munyi imani da ƙaddara mai kyau ko mara kyau, so yakamata mu kar6i yaran nan hannu biyu mu rungume su, Sannan Yaran nan fa ba muke ɗaukar ɗawainiyarsu ba, ba agidan mu suke zaune ba, Agidan owais suke zaune shi ne ke kula dasu kuma shine ke da alhakin duk wani abu da zai faru, babu yadda za'ai araba owais da yaran nan! Saboda Bincike su ke yi a kansu, Hukumar Sojin america suna da sanya hannu akan case dinsu, bazai yiwu owais ya rabu da su ba...." jin wannan maganar ta sharafudeen yasa senate ɗaure fuska, gani ya ke yi kamar hada baƙar magana sharafudeen ya gaya mashi daya faɗi cewa agidan owais suke zaune kuma shi ke ɗaukar ɗawainiyar shi, maganar ta sosa ran shi, Deen da abdul razak sun fara aminta da kalaman sharafudeen akan zaman yaran. Bayan Sharafuddeen Ya kammala maganarshi, Baba Obie Ya ambaci sunan Hateem, A hankali ya ɗago da idanunsa waɗanda suka kaɗa jawur da su, Muryarshi adisashe ya furta"Bani da abin cewa, duk hukuncin da aka yanke baba zanyi biyayya" Shiru su ka yi na wani lokaci babu wanda ya ƙara furta magana acikinsu falon yayi tsit kamar mutuwa ta gifta. Shigowa falon hajjaty tayi da sallama a bakinta, hannunta biyu ruƙe da faranti daga saman shi Tea pot ce tare da cups, daga bayanta Abla ce tare da Sophia kowan nan su ya ruko tray na kayan abinci, Amsa masu sallamar sukayi cikin girmamawa suka sauke trays din kafin suka gaishe da su sheikh Imam da sauran mutanan falon, da fara'a suka amsa masu, kafin daga bisani suka fuce daga ɗakin. Babu wanda yai yunƙurin ta6a kayan abincin, kowa kanshi ya ɗauki zafi. "Aminina, bismillah" Obie ne ya furta hakan harya yunƙura da niyar ya zuba mashi Tea a cup da sauri Imam malik yace"Alhamdulillah, kafin na baro gidan Hateem na cika cikina babu yunwa atare dani," Cikin kulawa obie yace"Ban yarda ba, amma tun da kace haka, Bari na zuba maka tea din kasha, nasan zaka ji dadin shi, Hajjaty ce ta haɗa shi" Sheikh Imam na murmushi yace"na fahimci ba ƙaramin ji kake da matar nan ba" Murmushi obie yai batare dayace komai ba. Owais ne ya miƙe ya nufi tray din ya dauki tea pot ya tsiyaya masu tea a cups din yabi kowan nan su Ya miƙa mashi, ba tare da ya zuba nashi ba ya koma ya zauna. "Ba za ka sha ba"? Hateem ne yai mashi maganar, Calmly ya furta"bani buƙata" Bayan kowan nan su ya kur6i tea din, baba obie ya soma magana yana duban fuskokin su. "Na yanke shawara....." bai ƙarasa maganar ba, ganin yadda suka ɗago suna kallonshi Ya fahimci sun ƙagara da son jin mai zai ce ne. "Dangane da abun da ya faru jiya, na ruɗe ne shiyasa harna firgice, amma yau da Owais ɗina yayi min bayani na fahimce shi, na yarda yaron mutunne kuma ba mai cutarwa bane, tun time da abun ya faru har ya shigo gida na, ya samu damar da zai iya cutar da mu amma bai yi hakan ba, sannan naga ƴar uwarshi taje gare shi ta lullu6e shi da rigarta tana kuka tana rokon shi akan ya canza halittar shi ya zama mutun, nayi mamaki ƙaramar yarinya bata ji tsoron tunkarar shi ba a suffar maciji, sannan baiyi yunƙurin sarar ta ba, hakan ya ƙara tabbatar min da cewa mutunne da gaske......" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar Owais da Hateem da sauran masu goyan bayan zaman su, In ka cire Senate lateef donshi har ga Allah bai yarda da yaran ba. Numfasawa baba obie yai, kafin yaci gaba da yin maganar sai da ya fara kur6ar tea din hannun shi. "Na amince su cigaba da zama a estate din mu"! A matuƙar ruɗe Senate lateef ke kallonshi da tsantsar mamakin yadda ya amince da zaman tsintattu a zuri'ar su, zuciyar shi ta sosu sai dai bai yi kuskuran katse mashi maganar shi ba, wani irin annurin farin ciki ne ya bayyana akan fuskar Hateem da sauran magoya bayan zaman yaran a estate din. "Amma abu ɗaya ne ban yarda da shi ba"!! ya faɗa Yana Shafa gemunshi da hannu ɗaya, yayin da idanuwanshi ke akan fuskar Hateem da chief Owais, kamar yadda yake kallonsu haka suma suke kallon shi. "Hateem, bana so wani abu Ya ƙara shiga tsakaninka da Yaron, babu kai babu shi, ban amince ka taka inda yake ba Har ka koma Canada," Ras yaji gabanshi yai mugun faɗuwa, baisan sa'adda ya sauko daga saman sofa ya dawo kan carpet ya zauna, motsa la66ansa ya soma yi da niyar yin magana da sauri sharafuddeen Yai mashi gyaran murya nan take Ya fahimci me yake nufi, ƙoƙarin haɗiye damuwarshi yayi, In a cool Voice yace"Shikenan baba, Na amince, amma dan Allah Ina neman alfarma awurinka" a marairai ce yayi mashi maganar. "Ina sauraronka" "Nayi ma Gimbiya mujeedat alƙawarin zan kawo yaron gidana don ta ganshi....." da sauri senate ya katse shi"mugun abun zaka kai gidanka? Inda iyalanka suke? Wannan wani irin gangancine"? Deen yace"yakamata aduba lamarin nan fa, gaskiya ba zamu lamunta ba hauka kake yi da zaka ɗauki mutun mai hatsari ka kai gidanka? What if something happens?" he said in a tense voice. "In sha Allah Ba abun da zai Faru, Nidai kawai ay min alfarmar dana nema" ranshi aƙuntatace yayi maganar. "Hateem Kayi haƙuri, tunda Yaron baida lafiya, ba yadda za'ai ma ya Iya taka ƙafarshi balle har Yaje gidanka, sai dai Idan Yaji sauki kafin lokacin da zaka koma canada" Imam Malik ne Yayi maganar yana dubanshi Jinjina kanshi ya ɗanyi, ba tare da ya ce komai ba. Baba obie dake kallon shi ya fahimci babu nutsuwa atare dashi, cikin kwantar da murya yace"Hateem, kada hakan ya dame ka, kasan ina son farin cikin kowan nan ku, ba zanso abun da zai 6ata maka rai ba, dalilin dayasa na raba ka da yaron saboda lalurar dake atare da shi, bana so wani abu ya cutar min dakai...." gyaɗa kai yai"bakomai baba nagode" cikin sanyin murya ya faɗi hakan. Murmushi sheikh imam ya saki yana fadin"aminina yakamata kaga yaron nan da Hateem ya ƙwallafa rai akai, dama sauran yaran, zaku sha mamakin kamanninshi da Hateem, daku kanku" ya faɗa yana nuna su Deen, ba yabo ba fallasa suka dube shi batare da sun ce ƙala ba. Baba obie ya ɗan yi jim na wani lokaci kafin yace"aminina, acigaba da bashi kulawa ta musamman, Idan yaji sauƙi Allah ya raba shi da abun dake damun shi, in sha Allah zamu je mu duba shi, zamu taya shi da addu'a, Allah ya yaye mashi abunda ke damun shi" Sheikh imam ya amsa mashi da ameen aranshi yayi mamaki yadda suka nuna basu buƙatar ganin yaran duk da ya fahimci kamar suna gudun haɗuwa da danish ne saboda lalurar shi. Duba agogo sharafuddeen yayi"dare yana ƙara yi, Ina so zan wuce" Baba obie ya dube shi"zaka iya tafiya tun da inada madadinka," ya faɗa yana nuna chief Owais da cup din hannun shi Murmushi sharafudeen yasaki tare da kallon Owais a fakai ce ya kashe mashi ido ɗaya, murmushin gefen fuska chief ya saki ganin abunda daddynsa yayi masa, ba tun yau ba ya saba yi mashi hakan sometimes tamkar aboki yake ɗaukar shi. Gyaran murya Senate lateef yai hankalinsu ya dawo kanshi, fuskarshi babu walwala ya furta. "Hateem, kada ka manta, akwai taron da zamuyi a National Assembly, domin gabatar da jawabi da kuma ganawa da kakakin majalissar wakilai" "Ina sane da wannan" atakaice Hateem ya furta hakan. Sharafuddeen yace"bayan haka zamu ziyarci national Mosque, da kuma National Christian Centre, akwai kuma ganawa ta musamman da zaka yi da sarakunan gargajiya daga sassan kasar mu, after that zaka halarci State Dinner (Liyafar cin abincin dare) tare Ni A Villa" Sheikah Imam yace"babu hutu kenan Hateem zai fara yawo, ko da yake haka ya dace tun da ba kowani lokaci ake samun damar zuwa ƙasar ba, ƙwara ka za gaya gari nima dai hadani za'a je villa wurin liyafar ko ba agayyace ni ba sai na je don nasan za'aci kaji" da zolaya sheikh imam ya fada yana murmushi maganar shi ta ba su nishaɗi, gaba ɗayansu suka sanya dariya. Sharafudeen yace"aikune kan gaba baba, kai zaka buɗe mana taro da addu'a" sheikh imam yace masha Allah nagode da karramawarnan" Baba obie yace"Idan da hali ma, yakamata ku leƙa masarautar yarbawa ku gaishe da dangin mariganya ƙudirat, da kuma masarautar kano suma yakamata aje masu da Hateem, sannan zaka ziyarci National museum dake a lagos, da kuma Yankari Game reserve.... "Tunkan baba obie ya ƙare maganar, Hateem ya furta"baba duk ni zan halarci waɗannan wuraren daka lissafa? Bani da isasshen lokaci, On saturday next week zan koma canada, ina buƙatar hutu" fuskarshi a yamutse yayi maganar. Senate yace"dole ne kaje ko kana so ko baka so, mu zamu jagorance ka, Tun da ka shigo ƙasar tamu, dole ka zaga dangi, ka kuma ziyarci wuraren buɗe ido," gyaɗa kanshi yai har cikin ranshi baison yawace yawacen nan badan komai ba sai don saboda Danish baisan yayi nisa da estate din, duk da an yanke alakarshi da yaron zaifi mashi kwanciyar hankali idan har yana akusa da inda yake rayuwa. "On friday zamu shirya maka family dinner, na bankwana" acewar Deen. Muryarshi asanyaye ya furta "Allah yakaimu lafiya" suka amsa mashi da ameen. Sun dauki tsawon lokaci suna tattaunawa a tsakaninsu har wuraren ƙarfe sha ɗaya Na dare, Kafin daga bisani sheikh Imam ya rufe masu taron da addu'a, daga nan su ka yi wa junansu sallama, Har bakin entry Hall, Baba obie yayi masu rakiya, Hateem Ya shiga mota tare da sharafuddeen, Sheikh Imam tare da Boss man suka shiga mota ɗaya, suma sauran kowa Ya nufi Gidan shi dake a estate din, banda chief Owais, baba obie Ya ruƙe shi, yace shi zai taya shi kwana yau tunda shi yakawo abunda ya tsoratar da shi babu musu owais ya amince mashi domin shima yayi kewar kakan nashi. Tun acikin mota, Sharafuddeen yake tausar Hateem akan yayi haƙuri dangane da hukuncin da baba Obie ya yanke mashi na raba shi da yaron, sannan ya kwantar da hankalin shi, ya yi mashi alƙawarin ko bayan baya ƙasar zasu kula da rayuwar yaron, ba zasu ta6a bari ya wulaƙanta ba, kalamanshi sun tausasa zuciyar Hateem, shi abinda yafi damunshi raba shi da akayi da yaron, yanzu shikenan bazai sake zuwa inda yake ba, har ya koma canada , abun ya ta6a zuciyarshi baiso haka ba, har cikin gidanshi sharafuddeen ya shiga, suka gaisa da gimbiya mujeedat, ita kadaice bata runtsa ba saboda rashin dawowar mijinta, Su Yazrin tuni sun nutsa a baccin su, bayan sharafuddeen yayi masu sallama ya fito daga gidan security detail dinshi suka buɗe mashi mota ya shiga, batare da 6ata lokaci ba, suka nufi Aso Villa domin komawa ga muhallinsa. Bayan barin su gidan da kusan mintuna talatin, Hajjaty ta lalla6a taje ta ɗauko wayarta data ajiye ƙasan table, jiki na rawa ta nufi dakin don ta kaima pravin, tana shiga ta taras da shi yanata faman yin zarya adaki kamar mai fama da ɗan kanoma da basir, duk ya ƙagara da son jin abunda suke tattaunawa, jin sallamarta yasa shi yin saurin tambayarta ina wayar, da sauri ta miƙa mashi, yasa hannu ya kar6a tare da kunna recording din, ya soma sauraron tattaunarsu, hajjaty dake kallon shi, ganin yadda yake tsuma zufa ta wanke fuskarshi yasa tace mashi lafiya, rai a6ace ya jefar da wayar saman gado yana fadin wannan wace irin masiface? Wato dole dai sai yaran nan sun zauna a estate din nan, wallahi bazai yiwu ba, duk yadda zanyi saina yi silar barin su, nasan owais ne ya tunzura obie har ya amince da zaman su, saboda ya makance akan ƙaunar shi, Idan sunsan wata basu san wata ba....." yana huci yai maganar, hajjaty dake kallon shi, tsantsar mamaki ne akan fuskanta, harta fara kokwanton anya pravin baida wata manufa akan yaran? Meyasa ya tada hankalin shi akansu? Tayi zurfi a tunaninta taji ya buɗe kofar ɗakin Ya fuce waje, Jiki asanyaye ta nufi gefen gadonta ta zauna tare da kwantar da kanta, tayi tsammanin zai dawo dakin amma sai taji shiru, ranta ne ya bata cewar ko ya tafi dakin hajiya saratu ne hakan yasa ta ja bargo ta lullu6e jikinta.... *❤EX-PRISONERS❤* Bayan Sun kammala Cin dinner dinsu, sam sun kasa runtsawa saboda tunanin ɗan uwan su Danish, ɗazu da marece sun je duba shi, Yanzu ma kuma Bayan sun sanya kayan bacci a jikin su sun yi shirin kwanciya, ɗakin shi suka nufa, gaba ɗayan su ne a kawaye da gadon shi, sun yi tsaitsaye cirko cirko suna kallon shi. Unaisah da Batool sun sanya kayan bacci kala ɗaya Riga da wando launin black gray, rigar tana da hula duk sun lullu6e kawunansu da ita, Jemimah da Azeeza ma kalar nasu sleep dress din iri ɗaya ne Yar gown ce dai dai gwiwa ta tsaya masu launin pink colour, sun daure kawunansu da head scarf, Praveen da Hanna launin nasu farare ne riga da wando masu zanen flowers ajikinsu. Hala zalika Mazan ma kowan nan su yana sanye da kayan baccin sa. Tun suna daga tsaye har dai suka kaiga samun wuri gefe da gefen gadonshi suka zazzauna, banda Gabriel dake atsaye ya goya Azeeza a bayan shi saboda makantar daren ta, duk da lalurar ta fara sauki yanzu, tana gani ba laifi saboda hasken dake gauraye da gidan tamkar da rana, yana ƙara ƙarfafa mata ganinta sai dai babu clear amma takan iya shaida fuskokin su, shiyasa bata damuwa yanzu bama kowa yasan tana da lalurar ba sai ƴan uwanta..... Fuskokinsu babu walwala, yayin da suke kallon shi, musamman Haris hawaye tuni sun jiƙe fuskarshi. "Allah ya baka lafiya ɗan uwana rabin raina, Danish na tausaya maka, Ina jin raɗaɗin da ka ke ji acikin zuciyarka, In sha Allah ƙarshen wahalarka ne Yazo" murya arauna ce Haris Ya furta maganar, idanunsa akan fuskar Danish dake akwance tsakiyar gadon kamar matacce. "Danish, ban sani ba ko kana ji na, dan Allah ka kwantar da hankalinka, kada ka ta6a sanya damuwa akan abunda ke faruwa dakai, ko jiya da muka guje ka don ba mu san kai bane, amma Yanzu mun riga da mun sani, kuma in sha Allah, a kowani hali na rayuwa duk runtsi duk wuya muna a tare dakai, har ƙarshen rayuwar mu" Batool na ƙarasa faɗar maganar ta fashe da kuka tamkar ranta zai fita, da sauri ta kifa kanta saman mattress din daga gefen hannun shi, ta ɗaura nata hannun akan nashi. "Batool ki daina yin kuka, zaki ƙara karya mashi zuciyarshi, saboda Ina ji araina yana sauraron mu ba bacci yake yi ba" cikin kwantar da murya Unaisah ta furta maganar, idanuwanta akan Batool cikin shesshekar kuka tace"ya wahala sosai, ko motsi bai iyayi, mu kallon shi kawai mu ke yi, shi ka ɗai yasan raɗaɗin da yake ji acikin zuciyar shi, sai yaushe ne zaiji dadin rayuwarshi"? Cikin jin ƙunar rai ta furta maganar tare da dago da kanta idanuwanta sun kaɗa jawur.. Fashewa da kuka Azeeza da jemimah su ka yi, sautin su ya karaɗe ɗakin, Naufal Yace"Dallah meye haka? Kuka shi zai mana maganin damuwar ɗan uwan mu ne? Ku bar mu muji da abunda ke damunmu mana" zuciyarshi a jagule yayi maganar, Muryar Jemimah da shessheƙar kuka tace"Ni wallahi tausayinshi nake ji, bawan Allah, lokacin da muna a daji bamu lafiya shi ya rinƙa ɗawainiya damu har muka ji sauƙi....." kafin ta ƙare maganar, parveen cikin raunin murya ta katse ta da cewa"Idan muna jin yunwa shi yake sama mana abinci, sannan Ya hana idonshi bacci duk don saboda mu, amma meyasa mu muka kasa taimaka mashi awannan halin"? Muryarta na rawa ta jefa masu tambayar. "Saboda bamu da yadda zamuyi Parveeen, addu'a ce kadai zamu Iya taimaka mashi da ita," acewar Javed shima fuskarshi ayamutse take. "Ba iya addu'a ba javed, Idan muka tona asirin miyagun mutanan can da suka ƙasƙantar da rayuwarmu, Ina da tabbacin zamu Yi nasarar kawo ƙarshen matsalar Danish damu kan mu, don kuwa nasan har Yanzu suna nan suna bibiyar rayuwarmu bazasu ta6a ƙyalemu ba kodan saboda kada mu tona masu asiri dole subi diddiginmu" sajeed ne Yai maganar.. Unaisah ta natsu tana kallonsu, ba tare data tsoma baki ba, saboda ita a halin yanzu ta fahimci wani abu, tun da har jami'an isod suka gano salsabeel to kuwa tana da tabbacin sun san komai game da rayuwarsu!! Kallonsu kawai su ke yi. "Ƙwara kowa yasan me suke aikatawa, mu faɗa masu kawai, su taimaka su rabamu da su, Su ƙyale ɗan uwanmu yayi rayuwarshi cikin salama" Hanna ce ta faɗa tana faman tada jijiyoyin wuyanta. Calmly Unaisah ta furta"ku daina surutu kuna hana shi natsuwa, yakamata mu je mu kwanta, tun da mun ganshi inyaso gobe da safe sai mu dawo mu ƙara duba shi" Shiru su ka yi, ba tare da sun motsa ba saboda basu sun yin nesa da shi, da da halima a ɗakin shi za su kwana, yayin da su ke cigaba da kallon shi tamkar zasu haɗiye shi, tsananin tausayin shi suke ji ga wata irin ƙaunarsa da su ke ji. Parveen da Jamimah sai hamma su ke yi, ita jamimah hada gyangyaɗin bacci. "Please ku tashi mu tafi ɗakunan mu" Nawfal ne yai maganar, tare da miƙewa ya zagaya ta 6angaren da garkuwa yake akwance ya duƙar da kanshi ya manna mashi sumbata akan forahead dinsa, ganin hakan yasa Jemimah yin sauri rarrafawa tsabar iyayi saman chest dinshi ta haye tukunna ta manna mashi sumbata kan cheek dinsa har sau biyu, murmushi kowan nan su yasaki abun ya ƙayatar da su. Ƙarasa hawayewa gadon Batool tayi har zuwa gefen Garkuwa in a cool voice ta furta"ɗan uwana rabin raina, idan kana saurare ni, nayi kewarka sosai, Allah ya baka Lafiya sanyin idaniyata" gefen fuskarshi ta manna ma kiss, kafin ta sauka daga kan gadon, da sauri Haris ya zagaya ta inda su nawfal suke a tsaye daga gaban gadon ya russina tare da ruƙo hannun Danish ya buɗe tafin hannunsa A hankali ya sumbace shi kafin Ya furta"ko ban faɗa maka ba, nasan kasan da irin ƙaunar da nake yi maka jinin jikina, Allah ya tashi kafaɗunka" bayan Haris Ya saki hannun shi, Javed Ya miƙe ya nufi Side da danish yake, Ya manna mashi kiss a forehead nashi. "Big bro, our guardian, Allah ya baka lafiya" ya faɗa cikin nuna tausayawarshi. Sajeed dake agoye da Azeeza, Ya matsa kusa da Danish,Ya sauketa daga gefen gadon, da rarrafe ta lalubo Danish ta ɗaura fingers dinta saman fuskarshi ta shasshafa shi, duk suna ta kallonta. Haris da zolaya yace"kada ki lashe mana ɗan uwa, Kiss ɗaya zaki manna mashi ya wadatar" kusan sau uku ta sumbace shi, biyu kan cheek dinsa, ɗaya kan tsinin hancin shi, bayan ta gama nata, Sajeed ya ruƙo Hannun shi kamar yadda Haris yayi, a hankali Ya sumbace shi gently ya furta"ka kula mana da kanka our super star, zamu kwana da tunaninka, gobe da sassafe zamu zo duba lafiyarka, garkuwar mu" Murmushi duk suka saki, wani irin daɗi suke ji, mayar da goyan Azeeza Sajeed yayi akan bayan shi. Hanna ma ta sumbace shi, Ya rage saura Unaisah, dake zaune tayi zugudun kamar mai tunanin wani abu. "Genie saura ke" acewar jemimah idanuwanta sunyi luhu luhu saboda baccin da take ji. "Unaisah we are waiting for u, ki yi mashi kiss kamar yadda muka Yi mashi kafin mu tafi" Sajeed ne yai maganar, tamkar bata ji me suke cewa ba, tayi kasaƙe tana faman wurwurga eye balls dinta. Dafa shoulder dinta Batool tayi"Sister, Kin yi shiru, ki motsa mana, Ko kin manta abun da muka ce zamuyi idan mun fita daga ɗakin Danish" Haris Yace"menene za ku yi" da sauri tace"karatu ne zamu yi kafin mu kwanta bacci" Ya furta okey, Jiki asanyaye Unaisah ta ƙarasa haurawa kan gadon, crowling slowly ta nufi Danish, koda ta ƙarasa inda yake a kwance, saita sanya hannu ta zame hular kanta, nan take nannaɗaɗɗiyar sumar kanta ta warwaro ta sauko kan kafaɗunta, rumfa tayi mashi da gashinta ta yadda ba zasu Iya ganin sumbatar da za ta yi mashi ba. Sajeed Ya buga ƙafa yace"ba mu yarda ba wlh, You are trying to be smart Unaisah, dole ki janye sumar kanki mu gani da kyau" Ya faɗa yana sakin murmushi. Haris yace"kiyi yadda kowa yayi" Batool da su javed sai murmushi suke saki, shiru tayi bata tanka masu ba. Babu Mai Iya ganinta acikinsu, ɗaura tsinin hancinta tayi akan nashi, numfashinsu ya soma kokawa dana juna, hatta bugun zuciyarshi saida ya canza, dogon wuyan shi ta fara manna ma sumbata har zuwa kan chin dinsa ta sumbace shi a hankali kafin slowly ta ɗago da kanta, ta sumbaci forehead dinsa, ta dawo kan eye lids dinsa ɗaya bayan ɗaya ta sumbace su, tana ƙoƙarin kai mashi sumbata kan soft lips dinsa ba zato ba tsammani taji an damƙo sumar kanta, da ƙarfi ya ɗago da ita, A firgice ta juyo don ganin wanene Ya katse ta...... Rass taji gabanta Ya faɗi ganin Big Guy, wata irin kunya ce ta rufeta, da sauri ta sanya tafukan hannayenta ta rufe face dinta, su Haris dake atsaitsaye sai tiƙar dariya suke yi, ashe tunda ta dukufa tana sumbatar danish suka jiyo motsin buɗe ƙofa, suna kallon shi yai masu alamar suyi shiru da bakinsu, nan fa kowan nan su Yaja baki yai shiru, Lamarin ya ɗaure mashi kai, don bai fahimci me ta ke yi ma danish din ba, yadai ga tayi mashi rumfa da sumar kanta, Cikin sanɗa yaje gaban gadon Ya daddage Ya damƙo gashinta kanta. "Ki ji tsoron Allah Jari, Faɗa min kike Aikata ma bawan Allahn nan" fuskar shi ɗauke da murmushi yayi maganar yana bin ta da kallon tuhuma, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi Ni ba ƴar iska bace, ba abun da kake tunani bane, Ka tambaye su ka ji" ta faɗa tare da ɗago da kanta a lokacin ya sakar mata gashin kanta, duk tabi ta ruɗe, gani ta ke yi kamar kallon ƴar iska yake yi mata, tun akan abun da Ya faru ɗazu da suka kama ta a ɗakin Danish ta cire mashi ma6allin gaban rigarshi, shiyasa take fargaban kada ace kallon yar iska yake yi mata. Sunnar da kanta ƙasa tayi, fuskarta a tur6une babu annuri, sai faman ƙyafkyafta idanunta take Yi "Ƴan uwan Jari, ku fada min me take aikatawa tunda ita bazata fadamin gaskiya ba" Ya fada Yana nuna su Sajeed Da hannun shi Har suna hada baki wurin maimaita sunan JARI, da shagwa6a66iyar Murya Jemimah tace"Unaisa ɗin mu ce Jari" Big guy yace"Yeah, Ita nake nufi, ko bakusan cewa ita ɗin Jari bace"? Da mamaki suka girgiza mashi kai gami da tambayarshi ma'anar jari. "Shi Jari wani abu ne da idan ka sanya shi zaka samu riba, yar uwarku jari ce gare mu baki ɗaya, tun da muna ƙaruwa da ita, kamar dai yanzu da take koya mana wani baƙon abu...." tunkan ya ƙare maganar Unaisah tai saurin furta"wlh bani na faraba ai, Naufal ne Ya fara Yi mashi kiss, kowa yayi nice ma ta ƙarshe, Kuma ni bama kiss nake mashi ba, Falaƙi da nasi nake karanta mashi..." a shagwa6e ta ƙare maganar. Dariya suka saki gaba ɗayansu, bayan sun lafa, Big guy yace Ku tashi muje in rakaku ɗakunan ku, Dare Yayi sosai, Yakamata kuna bacci da wuri saboda karatun asubahi da ake koya maku" amsa mashi su ka yi da toh, yakai hannu ya ɗauki Jemimah, kafin su bar ɗakin saida Kowan nan su yayi mashi addu'a suka tottofe mashi jikinshi, har sun fita Unaisah ta dawo ɗakin da gudu ta lullu6e garkuwa da lallausar bargonsa, kafin ta kashe switch din dakin yai duhu, ta kunna mashi bedside lamp, tamkar karta bar ɗakin haka take ji, addu'o'i ta tottofa mashi tun daga ƙasa har sama kafin tabi bayan su suka nufi bedrooms din su. Sai da big guy ya tabbatar kowan nan su Ya shiga dakin shi, tukunna Ya nufi hanyar da zata kaishi part din da room dinsa Yake agidan. Fitarshi keda Wuya, Unaisah da Batool, suka fito daga ɗakin su, Hannayen su ruƙe da plates sun rufe su, abincin da suka ajiyema Ummi ne, tun ɗazu suka shirya zuwa dakinta don su kai mata abinci sun kasa saboda fargabar awani hali zasu taras da ita, duba da yanayin da ta shiga ɗazu na ganin sheikh Imam, Batool ce ta bada shawarar su ɗebi abinci su kai mata, tun lokacin da aka kawo masu dinner dinsu, Suka ɗibar mata plate biyu na abinci, A ɗakinsu suke 6oye mata shi sai yanzu su ka samu damar fito da shi. Cikin sanɗa suke yin tafiya suna ƴan waige waige kamar wasu munafukai, fargaban su kada wani ya gan su, basu san cewa duk wani motsin su akan idon jami'an isod dake kula da CCTV room ɗin gidan. A hankali suka haura second floor kaitsaye suka nufi ƙofar dakin ummi, cike da fargaba Batool take zazzare ido, don har yanzu mugun jin tsoron ummi take yi, gashi ta damu da ita kamar yunwar cikinta. "Sister, Ni zan jira ki awaje, ke sai ki fara shiga" cikin muryar raɗa batool tayi ma unaisa maganar. Harara unaisah ta jefa mata" waye ya kawo shawarar mu kawo mata abincin"? Yamutsa fuska batool tayi"Ni ce," "Don haka ke zaki fara shiga, Ni dama hankalina bai kwanta da mu zo kawo mata abinci ba, wata'ƙil ma taci abincinta tun ɗazu, mu ne ba mu sani ba" "Shikenan, Mu koma ɗaki sai mu cinye" Dariya Unaisah tasaki tana kallon batool tace"ai wallahi yadda kikasa muka ajiye mata abincin nan sai mun kai mata shi, Kuma ke zaki miƙa mata da hannunki" ta faɗa tana nuna ta da girar ta, jikin Batul harya fara kerma tsabar tsoro, idanunta suka ciko da ƙwalla. "Nidai mu koma ɗaki, sai in cinye abincin" a tsorace ta faɗa. da zolaya Unaisah Tace"You are just a coward, ai na lura shakkar aunty ummi kike ji, gashi duk kin damu da ita, Yinin yau tun bayan data shige daki kika ga bata fito ba shikenan kika addabe ni da tambayar Aunty ummi, bata ci abinci ba, tana adaki, ko awani hali take aciki, ni narasa gane meyasata kuka, yen yen yen haka kika isheni, shine yanzu kuma mun kawo abincin kike kokarin zillewa" murguɗa mata baki batool tayi batare da tace mata ƙala ba. Knocking ƙofar Unaisah tayi daga ciki suka jiyo Muryar Ummi ta furta"Come In" Tura ƙofar Unaisah tayi kafin ta shiga da sallama abakinta, Batool tana abiye da ita sai fama 6oye kanta take Yi. Kusan atare suka ɗaura idanunsu akan shimfiɗeɗan gadonta, tana daga kwance ta ɗaura kanta saman pillow, yayin da eyes dinta ke akan apple laptop dinta da ta ajiye saitin inda take fuskanta, wata yar gown ce a jikinta, shara shara kana Iya hangen inners dinta, tsayin rigar bai wuci gwiwar ƙafarta ba, gashin kanta a yamutse yake mai uban yawan gaske, ya cunkushe wuri guda, yanayinta da kasala a jikinta babu kuzari. Kamar an danna masu full stop haka suka dakata da yin tafiyar suna faman binta da kallo, jin shiru sunyi mata sallama basu shigo bane yasa taɗan ɗago da idanunta waɗanda suka rikiɗa suka koma launin Ja, Su kansu da su ka yi tozali da idanunta saida suka sha jinin jikinsu, wani ɗan iskan murmushi tasakar masu haɗi da ɗage masu gira ɗaya tace"meyasa ku ke kallona? Ba zaku shigo ciki bane"? Kallon juna su ka yi cike da al'ajabin jin sautin muryarta tamkar ta gardin ƙato wanda yasha ya bugu da giya. "Aunty Ummi baki da lafiya ne"? Unaisah ce ta furta maganar, a kasalance ta miƙe zaune haɗi da jingina bayanta kan gadon, kafin ta furta"Lafiyana Lau, menene ku ka kawo min" ta tambaya yayin da take kallon Batool data 6oye kanta bayan Unaisah. "Abinci ne" buɗe ido ta yi alamar tadan yi mamaki . "Wanene Yayi tunanin kawo min abinci acikin ku"? Ta faɗa tana nuna su da yatsanta. Cikin muryar raɗa Batool tace"Dan Allah ki ce mata ke ce bani ba" Murmushin mugunta Unaisah tayi jin abun da ta raɗa mata, Da gangan tace "Batool ce, tun ɗazu da kika tafi ɗaki kina kuka ta hana kanta sukuni, ta dinga damuna da tambaya akan Aunty ummi shiru bata fito taci abincin ta ba, ta tafi tana kuka bansan awani hali take ba, Pls sister mu ajiye mata abinci mu kai mata" Lumshe idanu ummi tayi, har cikin ranta taji dadin jin hakan. "Ku shigo daga ciki," ta faɗa tana nuna masu gadonta da hannu, Unaisah ce tayi gaba Batool tana abiye da bayanta kamar wata mara gaskiya, taji haushin faɗa matan da unaisah tayi "Bani plates din" ta fada tare da mike masu hannu ta kar6i plate din hannun Unaisah, ta ajiye akan gadon, ta kar6i na hannun batul ta ɗaura shi kan side drawer tana fadin"tun da kun kawo min abincin, ku zaku bani a baki in ci" duk idan tayi maganar sai sun kalli fuskarta, bakomai ne yake ɗaure masu kai ba, face sautin muryata daya canza kamar na wadda tasha giya, ga idanuwanta sun yi ja. "Aunty Ummi sautin voice dinki Ya canza, Idanunki ma suna yi ja sosai, ba ki jin daɗin jikin ki ne"? Cikin kulawa Unaisah tayi mata tambayar, ƙamshin turaren ummi duk Ya buɗe ɗakin. "Nothing is bothering me. Maybe it was my crying that made my voice change." She said, trying to bring her voice back to normal. "Meyasa ki kuka ɗazu da kika ga sheikh Imam"? unaisah ce ta ƙara jefa mata tambayar da zolaya tace"Unaisah kin cika bin ƙwaƙƙwafi, Kina min tambaya kamar Ƴar jarida, Ku zo ku zauna Yau muyi fira" ta faɗa tana nuna masu mattress. Unaisah ce ta fara hawa gadon, Kafin Batool ta haye gadon tana mai jin shakkar haɗa ido da ummi, suna fuskantar juna da ita, Batool tana agefen Unaisah, Ummi tana fuskantarsu. ta lura kamar Aunty Ummi batason tambayar da take Yi mata dangane da sheikh Imam hakan yasa taja baki shiru. da fara'a akan fuskarta tace"Banyi tsammanin kun damu dani ba, har na fidda rai da zanci abinci, gashi wata iri yunwa nake ji kamar inci ƴan hanjin cikina...." ta ƙare maganar tana ya mutsa fuska ta buɗe plate din gabanta, ashaƙe yake da tsiran nama, yanka yanka yaji kayan haɗi sai maiƙo yake yi ga kayan lambun da aka yayyanka mashi, sai ƙamshi yake yi, sun kura mata ido suna kallon ta. "naji daɗin tsiran nan da ku ka kawo min, wa zai fara bani abaki" da sauri Unaisah tace"Batool" ta faɗa tare da ruƙo hannun batool ta ɗaura shi kan plate din, Hankalin batool ba ƙaramin tashi yai ba, fuskarta duk ta yamutse itafa atakura take jin kanta har yanzu bata manta abunda ya faru tsakaninta da ummi ba a daren Jiya, gani takeyi kamar bata ƙaunarta. "Babe, Ki bani tsiren miyau na Ya gwada" ta faɗa tana ɗage mata gira, hada sakar mata murmushin gefen fuska Daurewa batool tayi, ta ɗauki tsiran hannunta na kerma takai shi bakin ummi, Unaisah na dariya tace"wlh batool tsoron ki take ji aunty ummi," ruƙo hannun batul ummi tayi ta ƙarasa tura naman abakinta, har wani lumshe ido takeyi, tana taunarshi ta ce. "Na lura da hakan, Amma kada ki damu zamu saba ne" Ummi ce tayi maganar, sanya hannu unaisah tayi cikin plate din tsiren ta dauko ta tura ma ummi abaki, Idan batul ta bata ita ma sai ta bata abaki, wani irin ƙaunarsu ce ta ɗarsu acikin zuciyarta, A hankali take satar kallonsu afakaice, don bata son su gane tana kallonsu. Bayan sun kammala bata tsiren suka buɗe dayan plate din me ɗauke da chips, shima suka bata har tana tambayarsu sunci nasu abincin ne? Suka ce mata Eh sun ci, duk da haka saida ta ɗebi chips ta tura ma kowan nan su abaki, Cike da nishadi suke tauna. bayan sun gama, Unaisah ta ɗauko masu Juice me sanyi suka sha. Ganin sun fara yunkurin tafiya ne Yasa tace"why baza ku tayani kwana ba"? Waro ido batul tayi tunawa da abinda Ya faru Jiya, Murmushi Ummi ta sakar mata, Ta fahimci tsoro take ji kada ta ƙara Yi mata irin na jiya hakan yasa tace "Asaman gadona zamu kwana, kafin muyi bacci har kallo zan kunna mana a laptop," jin hakan yasa batul taji hankalinta ya kwanta. gaba ɗayan su suka haye gadonta, unaisah ta takura ma Ummi akan tana son ta gyara mata gashinta, adole ummi ta ɗauko mata comb, da ita da batool suka kama gashin kanta suka dinga sharce shi bayan sun kammala, ta basu ribbom babba suka ɗaure mata gashin daƙyar saboda yawanshi gashi taurine dashi donma tana gyarashi da mayuka masu sanya laushin gashi. Gefe da gefenta suka kwanta, ta kunna masu kallo a laptop, cikin nishadi su ke yi, da zarar anzo wurin da za'ae kiss ko makancin hakan take yin saurin rufe masu idanuwansu da tafukan hannayenta, hakan ba ƙaramin dariya yake basu ba, Saida dare Ya fara nutsawa ta kashe kallon, a lokacin bacci mai nauyi yai awon gaba da su, ta sauko daga kan gadon ta kunna masu bedside lamp kafin taje ta kashe hasken ɗakin ya rage saura na fitilun gefen gadon, ta dawo ta kwanta a tsakiyarsu. A jiyar zuciya ta sauke, tare da ɗaura eye balls dinta tana kallon fuskar batool dake ta sharar baccinta, A hankali ta daura hannunta kan hular batul ta zameta, gashin kanta ya bayyana, shafashi taci gaba dayi tana binta da kallon ƙurulla, gani take kamar ta ta6a sanin mai kama da ita, sai dai ta gaza tuna wanene ko wacece ke kamanceceniya da ita cikin mutanan da tayi tarayya da su. Lumshe idanuwanta tayi yayin da ƙwalwarta ke tariyo mata wani abu can daya ta6a faruwa a arayuwarta wanda yayi silar tarwatsewar Farin Cikinta, baƙin tarihin da har bada bazata ta6a mantawa da shi ba, Ya lalata darajarta da ƙimarta Ya zubar mata da mutuncinta a idon jama'a, wasu kalmomi ne suka soma yi mata yawo acikin kanta. _Nayi danasanin kasancewarki Ƴata, wallahi da ace nasan da zuwan wannan ranar da tun kina acikin ciki zanyi silar da za'a 6arar dake_ Tuna wannan maganar yasa ta fashe da wani irin matsanancin kuka tamkar ana zare ranta, sham ta manta da su Unaisah dake bacci. Cikin muryar bacci batul ta furta"aunty ummi kuka ki ke yi"? Da sauri ta haɗiye kukanta, Hannunta ɗaya atoshe da bakinta, ta runtse idanuwanta. Idanun batul biji biji ta buɗesu, akan fuskar ummi, hankalinta ya tashi matuƙa ganin yadda fuskarta ta jiƙe da hawaye, muryarta na rawa ta furta"aunty.... ummi, baki da lafiya? Meke damunki"? Daƙyar ta iya buɗe ido ta kalli batool dake kallonta batare da tace mata komai ba. Duk da shakkarta da Batool take ji hakan bai hanata jin tausayinta ba, hankalin ta ya tashi matuƙa da ganin yanayin da ummi take aciki. Hannunta na kerma ta ɗaura shi saman fuskar ummi a hankali take share mata hawayen dake sintiri kan kuncinta. "Aunty ummi ki daina kuka dan Allah, bana son ganin ki cikin damuwa" Muryarta adisashe ta furta"meyasa kika damu dani? Ko Kin manta abunda nayi maki jiya"? "A'a ban manta ba, ni kawai ina ƙaunarki kuma bana son ganin kina kuka" tayi mamakin abunda batul tace mata. "Don't worry, I'm feeling better. Go back to sleep." ta faɗa tana ƙoƙarin danne damuwarta. "Bazan Iya bacci ba, idan bakiyi ba," kalaman batul sun sanyaya mata zuciya. "Ki sanyani inyi baccin" matsawa batul tayi dab da ita. Da ƙarfin hali ta rungume ummi sosai tayi tighting dinta, ta daura hannayenta saman bayanta, itama ummi ta daura nata hannun asaman bayan batool ta ƙanƙameta, wani irin yanayi ta soma ji mai wuyar fassaruwa hatta bugun zuciyarta ya canza, ta rasa gane dalilin faruwar hakan, Yau ne karo na farko data fara rungume Batool ajikinta amma wani iko na Allah sai ta dinga jin kamar ta ta6a rungumarta, ita kanta Batool din sai da taji canzawar bugun zuciyarta daurewa kawai take yi amma sai take ji kamar su dawwama ahaka ita da ummi batare da sun raba jikin su daga na juna ba. Ƴan addu'o'in da Unaisah ta koya masu, ta soma karantowa tana tottofa ma ummi. Wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, lokaci ɗaya ta nemi damuwarta tarasa, Ahaka bacci mai nauyi yayi awon gaba da su rungume da juna kamar zasu koma mutun ɗaya..... (Nima kuma na rungumi Alƙalamina) Mu haɗu Gobe Idan Allah yakaimu da rai da Lafiya🌹 *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura* 3196407426 First bank Bature Hafsat Muhammad, *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida* ~TAKUN ƘARSHE~ _______________________Boss Bature✍️ *The Unexpected call📞📲* *❤CHIEF OWAIS✊* A tsaye yake a gaban dressing mirror, cikin shiga ta pajamas Maroon colour, yayin da baba obie dake zaune saman gado ya ƙura mashi ido yana kallon shi, A hankali yakai hannu ya ruƙo roban massage oil Ya juya suka haɗa ido da shi, murmushi baba obie ya sakar mashi yana fadin"sannu da ƙoƙarina, tun ɗazu nake kallon ka, kanata laluban mai bayan ga abunan akusa dakai bansan me kake tunani ba daya ja hankalin ka. Murmushin gefen fuska chief owais ya sakar mashi, kafin ya nufe shi yana fadin"grandpa, kaima kaso ka wahalar dani, maimakon ka fadamin ka ganshi sai ka barni ina ta neman shi" dariya Obie yai cike da nishaɗi yau jin shi yake tamkar wanda akayiwa albishir da gidan Aljanna saboda zuwan Owais Ya faranta zuciyansa. Daga gefen shi chief owais Ya ɗaura Massage Oil din, Baba obie Ya juya mashi bayansa ta yadda zai ji dadin yi mashi tausar dama daga shi sai short a jikin shi. "My Grandpa, Ka tsufa sosai, bayanka yayi tamoji tamoji" da zolaya chief ya furta maganar. "Ba dole na tsufa ba, shekaru sun ja Owais" in cool voice ya fada A lokacin Owais Har Ya fara shafe mashi bayan shi da message oil din tare da yi mashi tausa, A hankali yake matsa fatar bayan shi yana murzata Runtse idanunshi yai haɗi da cije la66ansa Chief har leƙen fuskar baba obie yake yi, ya fahimci kamar yana jin zafin tausar da yake yi mashi ne. "Wash! Allah na! Owais kabi A hankali, wannan hannaye naka kamar na samudawa, kana murza min baya kamar yadda kake damƙar mugu idan ya aikata laifi" ƙumshe dariya chief yai jin sambatun da baba obie Yake yi mashi. "Baba, saboda lafiyarka nake yi maka hakan, naga kana runtsa ido kuma kana cizon la66anka, Hakan na nufin kana jin zafin tausar, Amma idan na gama yi maka zaka ji daɗin jikin ka......" ɗaga muryarshi yayi da ɗan ƙarfi ya furta"toh.. Toh.. Naji yanzu saura ƙafafuwan da ƙirjina amma dan Allah kabi a hankali kada ka shaƙe min zuciyata, dama ya lafiyar gwiwa" "Kana bani nishaɗi My Grandpa, Amma kayi min laifi...." kafin Ya ƙare maganar Baba Obie yace"Laifin me kenan"? Ya fada tare da Juyawo Yana fuskantar shi, Ya ɗaura bayan shi kan pillow, tare da miƙe ƙafafuwan shi yana duban Owais. "Kafin In bar Nigeria ka yi min alƙawarin Zaka dinga kula Min da lafiyarka, Har family doctors din mu nayi ma magana akan su dinga duba ka akai akai, dama tun time dana faɗa masu hakan sai da dr Alex Ya faɗa min cewa kaine baka basu damar da za su duba ka, da zarar sunyi yunƙurin bincika lafiyarka sai kace masu kashe ka suke son yi meyasa"? Ya jefa mashi tambayar Yana bin shi da kallo, hands dinsa na akan ƙafafuwan baba obie da yake yima tausa Shiru yayi mashi batare da ya furta komai ba. "Ba ka da abun cewa, shiyasa ka yi min shiru kana kallo na ko"? da zolaya yayi mashi maganar, baba obie yai murmushi tare da hararar shi yace"Bawai na rasa abun cewa bane, kawai ina tunanin yadda kake nuna damuwa akaina, Idan kaga na faɗa masu haka toh ni lafiyana ƙalou bana buƙatar a bincika ni," ya faɗa yana shafa gemun shi da hannu ɗaya Shiru Owais yayi mashi batare daya furta komai ba, ya maida hankali akan tausar da yake yi mashi. "Nayi kewarka sosai, Meyasa ka yi nesa dani? Abun da baka ta6a yi min ba owais, ka riga da kasan yadda na ƙwallafa rai akanka, sai da takai ga ko bacci nake yi ina sambatu a kan ka, ko na kira layin wayarka baka ɗagawa meyasa Owais? Ko dan kaga na damu dakaine" ya faɗa yana kwa6e mashi fuska kamar zaiyi mashi shagwa6a, chief owais dake kallon shi aranshi ya ayyana rigimar tsufa ta motsa, A fili kuma ya furta"Ba haka bane, Kamar yadda ka damu dani nima haka na damu dakai, ko aiki nake yi kana arai na, Grandpa kasan yanayin aikin mu ɗaga waya wuya yake min wasu lokuttan ma bana sanin an kira ni.... " bai kai ƙarshen maganar ba ya dakata yana kallon ikon Allah ganin baba obie yana kwaikwayon maganar shi, gaba ɗayansu suka sanya dariya. "Are you making fun of me? I won't speak anymore" obie na dariya yace"ka yi haƙuri jikana, Muryarka ce da daɗin sauraro, shiyasa ƴan mata suke haukan su kai kuma kana yi masu rowar kan ka, faɗa min menene Sirrin ko akwai wani abu da kake sha wanda yake ƙara mata daɗi" calmly ya furta a'a, daga Allah ne" "Amma kasan wani abu"? Girgiza mashi kai owais yai. "Dawowar nan da kayi, Ka canza min Owais, Ka ƙara Girma kuma Ka ƙara Kyau" "Shiyasa ka ƙura min ido Kana kallona ko"? fuskar Obie da murmushi Yace"ai ba laifi bane don na kalli Jikana, kai ɗin mallakina ne, Halak malak, Mahaifinka ma ya sallama min kai tun kana ƙaraminka, Ni ke kula da kai, gaskiya Owais Ka more ni sosai, komai nawa akanka Yake ƙarewa, duk inda zan taka tare dakai nake zuwa.... " tun daya fara maganar, Chief ke sauraron shi, A lokacin Ya kammala Yi mashi tausar, Har ya mayar da man kan mirror. Hayewa yai saman gadon, Ya kasance Suna fuskantar Junansu. "Ban taba tunanin zan kai wannan lokacin araye ba, bani da burin daya wuce inga girmanka, graduation ɗin ka, harma da auran ka da ƴa'ƴan ka, Sai gashi cikin Ikon Allah da raina da lafiyana, Ka girma ka kammala karatu harma kana aiki, sai dai auran ne har yanzu baka da niyar yin shi balle har in sanya rai da zan ga jikokin da zaka sama min" ruƙo hannun shi chief yai acikin nashi ya ruƙe shi gam, kafin ya soma yin magana a tsanake. "Kada hakan Ya dame ka, in sha Allah nan bada jimawa ba, Mafarkin ka zai zama gaskiya, ko dan saboda farin cikin ka zan yi ƙoƙarin yin hakan" lumshe do baba obie yai wani irin farin ciki ne ke ratsa zuciyar shi. "Allah Ya nuna mana lokacin, zanyi farin ciki mara misaltuwa, kuma za'ayi shagalin bikin da ba'a ta6a yin makamancin shi ba," duba agogo Chief Yai"baba dare yayi sosai, Yakamata mu kwanta mu huta, Gobe da Safe In sha Allah zan ƙara yi maka tausar, don kaji daɗin jikin ka" amsa mashi yayi da toh, kafin ya soma ƙoƙarin gyara kwanciyar shi, saukowa owais yai daga kan gadon Yaje ya kashe switch din dakin, Ya dawo ya kunna masu fitilun gefen gadon, daga bisani ya haye ya kwanta gefen baba obie, daga kwance suka cigaba da yin fira sama sama, har bacci yafara daukar owais, Jin shiru yadaina magana yasa baba obie juyowa yana duban shi, shafa gefen fuskarshi yayi tare da sumbatar shi kafin yayi mashi addu'a ya tofe shi, ya janyo masu lallausan duvet Ya lullu6e rabin chest din su.........❤ *(After Some Days)* Bayan wasu ƴan kwanaki, tun ranar da Baba obie ya yanke alakar Prime minister da Danish bai sake gigin zuwa inda yake ba, Yabar komai a hannun sheikh Imam da chief Owais, saboda a halin yanzu baida lokaci, ba azaune yake ba, ranar lahadi suka fara halartar National mosque tare da manya manyan malaman addini suka gudanar da taro, aranar litinin kuma Ya ziyar ci majalissai dokoki ta Nigeria, sunyi zaman tattaunawa da ƴan malissa a ƙarƙarshin jagorancin senate president lateef, tare da kakin majalissai wakilai, sun karrama Hateem a matsayin babban baƙonsu, sunji dadin tattaunawar da sukayi dashi kasancewar shi mutun daya iya mu'amala da mutane duk inda aka zauna dashi sai an ƙaru da baiwar da Allah yayi mashi na iya tsara kalami, ga farin jinin dake gare shi, gidajen jaridu basu da abin yaɗawa daya wuce ziyartar national assembly da prime minister yayi, komai daya tattauna da shawarwarin daya bama shuwagabannin Nigeria, saida ƴan jarida suka yaɗa shi a social media, duk aranar ya ziyarci gidajen marayu da gidan Yari, yayi masu kyaututtuka naban mamaki wanda ya gigita mutane zunzurun kuɗi ya bayar da za'a tallafi rayuwarsu da shi, aranar talata yabar garin abuja shi da Iyalan shi da ƴan uwan shi tun daga kan senate lateef his excellency deen and his excellency abdul razak tare da Sharafudden da hajiya saratu, Sir mubarak da kuma muƙarrabansa na ƙasar canada, Chief of staff, national security advisor, 6angaren masu ba su tsaro Royal canadian mounted polices and Nigerian Soldiers. kasancewar A privet jet din mai girma sharafuddeen suka yi tafiyar basu jin wahalar zuwa ko'ina, arana ɗaya sai suje har sama da gari uku, ƴan mintuna jirgin yake sauke su suje inda zasu je, kafin marece su lula zuwa wani state din. Wuri na farko da suka fara ziyarta bayan barin su abuja, masauratar yarbawan jihar lagos suka fara sauka an mutuntasu an kuma karramasu sanin matsayinsu a ƙasar, kafin suka Wuce Garin Kano, anyi masu kyakkyawar tarba, kwana ɗaya su ka yi awashe garin ranar da zasu baro garin saida suka biya kasuwannin kano da gidajen tarihi da gidan gwamnati, daga bisani suka ziyarci jihar bauci, a katafaren wurin shaƙatawar nan me suna Yankari anan suka yaɗa zango tare da gwamnan jihar, haƙiƙa Prime minister ya mori lokacin shi a Nigeria, yaji dadin yawon buɗe idon da suka je tare da ƴan uwanshi, sai dai abu ɗayane bai goge ba a tunanin shi wato Danish, da shi yake kwana da shi yake tashi, ko abinci zaici saiya tuna da shi, aranshi ya ayyana inama ace hada shi suka taho yawon nan da Allah ne kaɗai yasan irin farin cikin da zai yi. A ranar Alhamis suka dawo Birnin Abuja amatuƙar gajiye, friday za'a shirya mashi family dinner, Ranar sataurday Hateem zai bar Nigeria agurguje zasu koma Canada. ____________________________✍️ Idan muka koma 6angaren su Unaisah cikin ƴan kwanakin nan wata irin shaƙuwace ta shiga tsakaninsu da ummin america, musamman Batool sun kulle da ita, Har karatun kur'ani ta fara ƙoƙarin koya masu ranar da suka ji ta yi masu ƙira'a tsantsan mamaki ne ya kama Unaisah, don ita bata ta6a tsammanin ummi ta iya karatun kur'ani ba sai gashi tana yi mata ƙarin karatu cikin suratul baƙra, har tambayarta tayi aunty ummi dama kin iya karatu, sai tayi dariya tace mata hadda gareta ai, tun tana ƴar shekara goma sha bakwai ta haddace alkur'ani mai girma, Unaisah ta jinjina mata aranta ta ayyana amma ya akai take aikata sa6on Allah bayan ita din mahaddaciyar alƙur'ani ce, wata kil kuma wata jarabtar ce ta ubangiji Allah wa'alamu. Damuwarsu ɗaya ayanzu Ɗan uwansu Danish yaƙi dawowa dai dai, Har yau babu wani cigaba kamar kullum yana akwance idanuwanshi arufe wanka da cin abinci su boss ne ke taimaka mashi, da kuma salsabeel dake zuwa dubashi kusan kullum sai yazo, tare da shi ake ɗawainiyar kula da garkuwa, haka zalika sheikh imam kusan agidan yake wuni, wurin yi mashi addu'o'in da zasu bashi kariya, Hatta Ƴan uwan shi su Sajeed sai da Imam malik Ya koya masu addu'o'in da zasu dinga yi mashi hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba, sau uku suke zuwa duba shi a ɗakin shi don suyi mashi addu'a safe rana da dare, Ita unaisah har tsakar dare tana zuwa ɗakin shi ba tare da sanin kowa ba, duk ta ƙagara ya yadawo hayyacin shi, akwai abubuwa da dama da take son yi mashi albishir, na farko tana so ta faɗa mashi dangane da prime minister Hateem dake kama da shi na biyu abun arziƙin daya fara fito mata a ƙirji, ta riga ta yanke shawarar fada mashi idan ya dawo normal, ta hana kowa yagansu a 6oye take ɗaure su da mayafi ta matse su don karsu bayyana agani, abunda bata sani ba, batool tuni ta ganota duk in zata shiga toilet tsakar dare don tayi masu kallon ƙurulla sai batool tayi mata la6e, ta dinga tiƙar dariya kamar cikinta zai ƙulle. Tun ranar da ummi tayi tozali da sheikh imam bata ƙara bari sun haɗu ba, da zarar yazo gidan take komawa ɗaki ta zauna ko bakin ƙofa bata fita har sai ta shaida tafiyar shi tukunna take saukowa down stairs. A 6angaren su Benazir, since last week taso zuwa gidansu Aneelerh Allah bai nufa ba, saboda rashin samun layin Abie din Aneelerh, Alhaji ubaid yayi trying layin shi baya shiga, kuma shi kaɗaine dama yake da numbar shi, Adole Benazir ta haƙura da zuwa gidan su tun da bata da hanyar da zata samu address din su, bata ji dadi ba gashi har Mamie tafara yi mata zancen komawarsu Jos, don ma alhaji ubaid yace ba yanzu ba sai sun cike wata ɗaya ai da tuni sun jima da komawa, mamie bataso hakan ba, saboda ita bata son suna zama gidan Alhaji musa, badan bata jin daɗin gidan nashi ba sai don saboda ranta dake raya mata cewar ba don Allah yasanya suka zo gidan shi ba, don kawai yaji daɗin juyasu son ranshi shiyasa yake son su zauna masa agida, taci alwashin indai Alhaji ubaid bai basu damar komawa joss ba cikin watan nan to zata kama hanya ta tafi ne koda ita kadaine! Sauƙinta ɗaya Hajiya sarah tana janta ajiki matar tana da mutunci duk in tadawo daga office sai ta ware masu lokaci sun shiga garden ita da mamie donsu tattauna kan abunda ya shafi rayuwarsu da ta ƴa'ƴan su, ba ƙaramin ɗebe mata kewa take yi ba. Haka Itama zeenatu bata da matsalar komai ayanzu, Benazir ta zama tamkar ƙawarta, har gyara mata gashi takeyi tayi mata kwaliya, dr shureim ne yake daukarsu a motarshi su fita yawon shaƙatawa, kullum sai sun fita yawo ko gajiya basayi. To meya fi ransu? Nima da zan samu mai fitar dani yawon binshi zanyi. A 6angaren Pravin kuwa, Takaicin duniya Ya ishe shi, tun da yaji cewar baba obie ya amince yaran su cigaba da zama a estate dinshi duk irin wahalar dayasha wurin ganin ya tunzurasu donsu ƙi amincewa da shi amma abanza, baƙin ciki da hassada ne ke damun shi, Ranshi ya 6aci matuƙa ya kuma ci alwashin sai ya raba alaƙar yaran da chief owais, burin shi kawai su bar estate din. Ko ita hajiya saratu a yanzu tadaina damuwa da zancen yaran tun da taji hukuncin da baba obie ya yanke sai ta sanyama zuciyarta salama, idan pravin yai yunƙurin tunzurata don taje ta tada maganar a wurin baba obie, sai tace mashi itafa yanzu bata su take ba, tun da ba'a kanta suke zaune ba, Owais shi zai kula da komai. Idan ta faɗi hakan sai yaji tamkar ya rufe ta da bugu. Kullum tunaninshi ta wace hanya zai 6ullowa lamarin??? Alhamdulillah Jikin dr. Jazz yayi sauƙi, da taimakon ƴan uwanshi da suke bashi kulawa, har gida yake shiga don ya gaishe da Baba Obie, sannan yaci gaba da zuwa gidan su khadeeja kamar yadda ya saba zuwa domin duba lafiyarta. Idan muka koma wurinsu Aneelerh, shiru har yau zahra tana zaman jiran sakon Hajiya saratu harta fara tunanin kodai dama wasa take yi mata ne? Ko kuma tayi mistake ne wurin tura mata hotunansu twins don ta za6i ɗaya? Tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi ta riga data ƙwallafa rai akan su twins shiyasa duk ta damu kanta, kullum ne saita duba chat dinsu da hajiya saratu har tsakar dare duk don taga kota tura mata amsar maganarta amma shiru kake ji har yau, ganin yadda ta ɗaga hankalintane yasa Aneelerh kwantar mata da hankali tace taci gaba da addu'a idan rabonta ne zata samu, sannan tayi mata uziri watakil tamantane ko kuma ta shiga busy a aiki shiyasa bata samu damar bata amsa ba, Aneelerh Ba ta jima da fada mata hakan ba, Sai ga mahboob yazo masu da labarin tafiyar da sukayi zuwa wasu states din nigeria, Jin hakan yasa taji sauƙi acikin zuciyarta. Hajiya adama tun bayan da suka kawo baby junaid, kusan kullum saita kira donsu gaisa dashi har video call suke yi, ta jima tana mamakin yadda junaid yake yi mata surutu idan ta kira shi awaya, amma lokacin da aka kai masu shi kamar wani salihin bawa baya surutu sai in yana son cin wani abu tukunna yake buɗe baki yace abashi, nan take ta fahimci yafi son zama wurin mommynsa, yanzu tasama ranta dangana bazata ƙara raba shi da maman shi ba, idan tana son ganin shi ita za ta je gidan ko kuma ta gayyaci aneelerh tazo mata da shi, yanzu haka Aneelerh ta fidda masu lokacin da zasu je gidan ita dasu mami da ummi hada su uncle ɗan Iya gaba dayansu zasu je kai masu ziyara, tun da ta sanarma hajiya adama farin ciki kamar ta zuba ruwa ƙasa tasha, taji dadin zancen zuwansu................ Atakaice kenan abubuwan da ke faruwa atsakanin family din kowani 6angare. *💋BABE UNAISAH ANGEL❤* fitowa tayi daga toilet, Jikinta asanye da bathrobe fara ƙal ta ɗaure igiyoyin rigar saitin waist din ta, fatar jikin ta da alamun lemar ruwan wankan da tayo, A hankali take tafiya tana tunkarar Dressing Mirror, ta wutsiyar ido take kallon Batool dake akwance saman gadon su, tana fuskantar ceilling tamkar maiyin bacci, alhalin nan kuwa idonta biyu.... On mirror Chair Unaisah ta zauna, fuskarta babu annuri babu walwala, kamar bata da ƙoshin lafiya ko wani abunne ke damunta wanda yayi silar canzawarta. Body lotions din su ta ɗauko ta buɗe murfin, ta soma bin ko'ina na jikinta tana shafe shi da mai. Bayan ta gama shafa man, ta feshe sako da lungu na jikinta da turare, ƙamshin shi ya buɗe room din, hatta Batool sai da ƙamshin Ya ziyarci Hancinta. Sumar kanta ta soma gyarawa, ta busar da ita tabi da smoothing serum ta cuccuɗata, tunkafin ta kammala kunnuwanta suka Jiyo mata sautin knocking ƙofar room dinsu da ake Yi daga waje. "Batool, nasan idonki biyu, je ki leƙa ki ga wanene ke yi mana knocking, may be ko aunty ummi ce," Fuskar Batool Ayamutse ta buɗe idanuwanta, ta sauko daga saman gadon tana miƙa haɗi da yin hamma ta nufi ƙofar, ƴar rigar dake a jikinta bata wuce gwiwarta ba. Buɗe ƙofar ɗakin tayi, tare da leƙawa ganin big guy ne yasa tayi saurin zuwa ta dauko Mayafi ta lullu6e kanta kafin ta dawo bakin ƙofa ta kuma leƙawa tana fadin"Barka da safiya Ina kwana" Kamar kullum da face mask a fuskarshi ya amsa mata da lafiyalou, yakike fatan na same ki lafiya' bayan sun gama gaisawa yace"ina Jari "? "Tana a ciki, Yanzu ta fito daga wanka, ko in kira maka ita"? Ɗaga mata gira yai alamar eh, juyawa tayi da sauri ta shiga dakin, A lokacin Unaisah ta koma gaban Closet dinsu, tana laluban Suturar da zata sanya, Jin motsin shigowar ta yasa ta juyo tana kallon Batool "Wanene"? "Big guy ne Yake son ganin ki" "Ni kuma"? ta faɗa da alamun mamaki"ni nama yi tsammanin boss man ne, Ko me zai faɗa min bari dai naje naji dame yazo" Ta faɗa tare da ɗaukar Hijab ta zura ajikinta, Ta nufi ƙofar dakin cikin girmamawa ta gaishe da shi ya amsa mata da fara'arsa "Batool ta fada min kana nemana, gani toh" yadda tayi maganar taso ta bashi dariya. "Kina wani abune"? Girgiza mashi kai tayi"a'a, ba abunda nake yi" "Yawwa My baby Girl, Kin tuna maganar da muka ta6a yi dake last week"? Shiru tayi tana faman ƙyafta ido a ƙoƙarinta nata tunano maganar da sukayi "Namanta, ka tuna min mana" Numfasa yai kafin yace"ba kince kinaso kiyi ma chief namu godiya ba game da alkhairin da yake yi ma ki" murmushi tasaki tare da cewa na tuna. "Good, Yanzu abun da nake so dake, Kinga ni ke ɗawainiyar kai mashi abinci har ma da gyara mashi room din shi, saboda bai yarda da kowa ba Yana da wuyar sha'ani, Nima don ya aminta dani shiyasa ya yarda ina masa aiki a part dinsa, abun da Yakamata Yanzu ke nakeso Ki cigaba da zuwa part dinsa kina yi masa hidimar kai mashi abinci, breakfast lunch and dinner, sannan yana yawan shan coffee, a rana sau shida nake kai mashi, gyaran daki kuma sau biyu ne safe da dare before ya kwanta bacci, sai kuma gyaran falo dinsa da toilet dinsa da dressing room din shi hada gym room dinsa......" tunda yafara kora mata jawabi, ta zaro mashi idanu waje tana kallon shi, ganin kamar ta ruɗene Yasa shi sassauta muryarshi yace"Ko ba ki Iya aikin mata bane"? Murmushin yaƙe ta sakar mashi tare da cewa"Na Iya, amma naji kace Yana da wuyar sha'ani kuma bai yarda da mutane, Tayaya zai yarda Ina zuwa part dinsa yi mashi aiki"? Ta jefa mashi tambayar tana duban shi. "Kada ki damu, zai yarda da ke, abun da yasa kika ga Na baki wannan aikin saboda ta hanyar kyautata mashi ne kaɗai zaki Iya biyanshi da ɗawainiyar da yake yi maku, tun da shi ba'ayi mashi godiya baiso," Jinjina kai tayi kamar tana fahimtarshi, "Shikenan, Yaushe zan fara zuwa yi mashi aikin"? Murmushi yasaki jin ta amince fatan shi Allah yasa Chief Ya yarda da ita. "Yanzun nan zaki fara aikin, Gyara mashi Room dinsa, baya aciki daga sallar asuba ya nufi gidan kakansu Obie, kafin Ya dawo please ki tabbatar kin gyara mashi ko'ina na part dinsa, before ki gama ni kuma zan kawo maki breakfast din shi, duk idan nakai mashi abinci sai na tsaya nayi serving nashi kema haka za ki yi, nasan kina da natsuwa chief baison mutun mai ƙazanta yana son mai tsafta, kullum ki tsaftace jikinki da suturar ki kafin ki shiga part dinsa.... " wani kallon take bin da shi a fakaice. "Baka da matsala dani, In sha Allah zanyi komai yadda ya dace," Har cikin ranshi yaji daɗin maganar data furta mashi, "Mu je in nuna maki ɗakin" da sauri tace"Ai ban gama shiryawa ba, ka bani mintuna yanzu zan dawo" amsa mata yayi da toh, da sauri ta koma ɗakin a lokacin batool ta shige bathroom tana wanka. Shaf shaf ta nufi glass wardrobe dinsu, ta shirya kanta cikin Turkish gown launin Yellow, rigar tayi mata kyau ta kuma bi shape din jikinta, tana da belt a tsakiyar ta, tayi rolling mayafi akanta, kafin ta ɗauko Cashmere slippers mai gashi gashi launin yellow ta zura a ƙafarta. Bayan ta kammala kimtsawa, Ta fito daga ɗakin, Shi kanshi Big guy daya kalle ta sai da gabanshi Ya faɗi ganin kyan da tayi, satar kallonta ya dinga yi batare data ankara ba. Tafiya suka soma Yi, tana abiye da bayanshi, tayi tsammanin upstairs zasu hau amma sai taga Ya nufi elevator, Zaro idanu tayi ganin inda zasu shiga, tunda take arayuwarta bata ta6a hawa elevator ba sai yau, wani irin daɗi take ji, musamman da suka shiga daga ciki, tayi sama da su A hankali ta sauke su a second floor, kofar ta zuge, fitowa yai daga ciki da sauri tabi bayanshi, abakin kofar ɗakin nan data ta6a zuwa kwanaki taga wani mutun Yana motsa jiki nan yakaita nan take ta gane cewa shine ɗakin kuma mutumin da tagani shine chief dinsu. Abakin door room din suka dakata da yin tafiyar, "Ƙofar tana da password, ba zaki Iya shiga ciki ba tare da kin sanya password din taba, sai kuma idan shine ya baki iznin shiga" ɗaga mashi kai tayi alamar toh. "Amma yanzu babu security din ƙofar zaki iya shiga, sai dai ki kula please banda 6arna" dariya tayi tana fadin"6arna kuma sai kace wata ƙaramar Yarinyar" "Nasan ki da ƙiriniya, shiyasa na faɗi hakan" Yamutsa mashi fuska tayi batare da tace komai ba, Ya buɗe mata ɗakin Yace ta shiga ta fara aikin idan ta kammala yana s falo Yana jiran ta" amsa mashi tayi da toh, sai da taga Ya bar part din tukunna tayi sallama ta shiga daga ciki. Kamar yau ta fara ganin dakin, dama time din farko data fara shiga bata samu damar ƙare mashi kallo ba, har mamaki takeyi idan ta tuna mai rai ne ke rayuwa a dakin, Kamar baza'a mutu ba, komai ka kalla mai tsadane da inganci furniture din dakin har daukar ido suke yi idan ka kalle su, tsabar haɗuwarsu. Ga wani sanyin A.c mai haɗe da ƙamshin room freshner har cikin hancinta take shaƙar shi. A ƙalla ta 6ata tsawon mintuna, kafin ta soma tambayar kanta, meya kawo ta dakin? Don ita bata ga abun da zata gyaraba, babu datti ko kaɗan komai a gyare yake kamar yau aka fara amfani da ɗakin, har ƙwara bedsheet dinsa Ya tattare alamar anyi amfani da shi. Ɗaura idanunta tayi akan Toilet dinsa, daga inda take tana kallon komai dake aciki ta jikin glass din bangon , atsaftace yake komai na cikinsa fari ne ƙal. Ruƙe qugu tayi da hannu aranta tana fadin"Ikon Allah, To ni meye amfanin zuwana part dinsa? Me ake so nayi! Bayan babu wani abu da zan gyara, ni wannan dakin ma in nawane ai say yayi sati kafin in gyara shi" Ta jima atsaye ba tare da ta ta6uka komai ba, tunawa da big guy dake jiranta a falo, ne yasa tayi saurin nufar gadon chief, Ta soma gyara shi, bayan ta gama ta koma tana jera mashi turarurrukansa da body lotions dinsa da yayi amfani da su da safe, cikin ƙanƙanin lokaci ta gama gyara ko'ina na part dinsa.. Fitowa tayi daga part dinsa ta sauko down, Babu kowa A falon, Ƴan uwanta duka suna a bedrooms dinsu. "Kin gama gyaran"? a hanzarce Ta juya Baya jin muryarsa, Big guy ne ya nufe ta hannun shi ruƙe da haɗaɗden wooden tray madaidaici daga saman lafiyayyan breakfast ne. "Na gama," "Madallah sannu da ƙoƙari" tace mashi yawwa, "Yanzu ki biyo bayana muje dakin, inaso na gwada maki yadda za ki yi serving din shi abincin" amsa mashi tayi da toh, Sai da ya fara tafiya tukunna tabi bayanshi, har suka haura second floor, bayan sun shiga ɗakin ya ɗaura tray din kan wani ƙayataccen table, kafin ya dube ta yana fadin"kin yi ƙoƙari Jari, haka kika Iya gyaran ɗaki"? Murmushi tasaki jin ya yabe ta, aranta tace dama can a gyare yake. Batare da 6ata lokaci ba, ya soma kwatanta mata yadda zata gaishe da chief da kuma yadda zata tambaye shi me yake buƙata ta zuba mashi, hada yadda zata zuba mashi abincin duk sai da ya koya mata, ya yaba da hankalin ta shiyasa bai kawo ma ranshi cewa zata yi mashi kwa6a ba. "Zan tafi Jari, please Kada ki bani kunya, Kiyi komai awanyance, Inaso Chief ɗinmu Ya yaba dake" ya faɗa yana kallonta, "In sha Allah, zanyi ƙoƙari" "Good Girl" Juyawa yayi da sauri Ya nufi ƙofar fucewa daga falon, tsaye tayi tana yanke shawara da zuciyarta. Maimakon tayi abunda yace mata, sai ta Fito cikin sanɗa kamar 6arauniya tana ƴan waige waige ganin babu big guy ne yasa ta saki jiki, da sauri ta sauko down stairs ta nufi bedroom ɗin su, tunkafin ta shiga ta soma kwalawa Batool kira. Batool dake a zaune kan mirror chair, har tayi wanka ta sanya Pakistan ajikinta, Riga da wando, launin blue sky, ta sauko da sumar kanta har tsakiyar bayanta masha Allah. Jin kiran da Unaisah take ƙwala matane yasa tayi saurin miƙewa tare da juyawa tana kallonta da mamakin ganin yadda take haƙi "Lafiya"? "Toilet zan shiga sister, uziri gare ni, gashi big guy ya sanya ni yin aiki a part din Chief dinsu, Dan Allah ki taimaka ke ki yi aikin" tana magana haɗi da dafe cikinta. Adabarbarce Batool tace"to ai ni bansan dakin shi ba, sai dai ki nuna min" "Muje in nuna maki" ta faɗi tare da yin saurin zuwa gaban closet din kayansu ta ɗauko mata mayafin pakistan dinta, sai da tayi mata rolling din shi tukunna ta Ruƙo Hannunta. Gaba tayi Batool tabi bayanta suka shiga elevator, su batool basa banbana sai bin elevator din take Yi da kallo "Sister menene wannan? "Sunanta Elevator, Na'ura ce dake ɗaukar mutun daga sama takai shi ƙasa ko daga ƙasa takai shi sama, tafi sauƙi akan bene, Kin ga shi yana gajiyar da mutun amma ita wannan tsaye kawai zakiyi tayi sama dake, bari na gwada maki yadda zakiyi amfani da buttons dinta, Nima a wurin big guy na gani da muka shiga atare" A tsanake tayi mata bayanin yadda zata Yi amfani da ita. Murmushi Batool tasaki"meyasa baki ta6a nuna min ba? Ai da bazan ƙara hawa bene ba, duk in zanje dakin aunty ummi kona Danish, sai dai in hau elevator" Unaisah tace"indai wannan ce har sai kin gaji da ita, don daga yau kece zaki dinga zuwa gyara ma chief dakinsa sannan ki kai mashi abinci" A matuƙar ruɗe Batool ta furta"Ni kuma"? Ta faɗa tana zare idanuwanta. "Ƙwarai kuwa, big guy yace ta wannan hanyarce kadai zamu Iya biyanshi abunda yayi mana, wato mu dinga kyautata mashi..... " cikin kwantar da murya tayi ma batool bayani. Fuskar Batool da fara'a tace"indai wannan ne babu damuwa, zan dinga kai mashi abincin in gyara mashi ɗaki kullum in sha Allah" Murmushin gefen fuska Unaisah ta saki, Aranta taji daɗin amincewar da Batool tayi, Dama da biyu tayi hakan, saboda batason tana kusanta kanta da wani Namiji, ta san halin mutuminta sarai, duk ranar da Allah ya farfaɗo da shi ya risƙeta a ɗakin chief tabbas komai zai Iya faruwa. Fitowa su ka yi daga elevator din, A bakin ƙofar ɗakin nashi, Unaisah ta sanya hannu ta buɗe, suka shiga daga ciki, tun da Batool ta daura idanuwanta akan haɗuwar ɗakin nan fa tabi ta ruɗe ta rikice kamar wuyanta zai balle saboda yadda take ƴan leƙe leƙe, tambayoyin tadinga jefa ma unaisah menene wannan? Ya ake amfani da shi. "Kinga kiyi abunda ya kawo ki, a sannu zanyi maki bayanin komai, Yanzu dai zan tafi in barki, ai na fada maki toilet zan shiga, ki natsu ki saurare ni kada ki yi mashi kwa6a, mutunne mai son mace mai tsafta da natsuwa, nasan duk kina da wannan, dan Allah kada ki bani kunya my sister," "In sha Allah" "Yawwa My baby Girl, Idan chief din Ya shigo cikin girmamawa zaki gaishe da shi, kina ji na ko"? Ɗaga mata kai tayi alamar eh, taci gaba da koya mata komai dangane da yarda zata yi serving din shi. Daga bisani tace"toh, Sister ni zan tafi, ki yi zamanki ki sha A.c kafin chief Ya ƙaraso" tana fadin hakan tayi saurin fuce wa daga dakin. Batool ta samu abun kallo, haka ta dinga ƴan leƙe leƙe tana yi mashi yawo a ɗakin shi. Bayan Unaisah ta sauko down stairs bedroom dinsu ta koma, fuskarta ɗauke da murmushi, har ta ƙagara Batool ta kammala aikin ta dawo don taji meye faru bayan chief Ya shiga ɗakin? Abu ɗaya take zullumi kada Batool tayi mashi kwa6a. Tunani ta soma yi mai yakamata tayi yanzu? Ɗazu dai da asuba sunyi karatun alƙur'anin da ake koya masu da wasu littattafan addini, sannan sunyi breakfast dinsu, shiyasa sauran duk basu fito daga ɗakin su ba, saboda baccin da bai ishe su ba. Lokaci ɗaya ta tuna da i phone ɗinta, Jiki na rawa ta nufi bedroom din su, tana shiga ta nufi inda ta ajiye ta, ta ɗauko wayar tare da backpack ɗin Unaiza. Saman gadonsu ta haye, ta sanya hannu ta zuge zip din jakar ta soma ƙoƙarin lalubo sim din, sam ta manta inda boss man ya sanya mata shi, ranta ne ya bata cewar ta bincika littattafan dake abackpack din wata'ƙil a tsakiyarsu ya zura sim din. Nan take ta zazzago da Textbooks din Ciki, tare da Diary din Unaiza, buɗe su ta dinga yi tana neman sim din har tazo kan Diary din Shafin farko data buɗe hoton Unaizah ne, Lokaci ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi ganin fuskarta, tayi kyau a hoton kamar ka kira sunanta ta amsa maka. Tunda ta ƙurama hoton ido ko ƙyaftawa batayi ba, A hankali ta daura hannu tana shafa fuskarta, yayin da idanuwanta su ka cicciko tab da ƙwalla. Taso ace zata Iya karanta labarinta data rubuta a diary din sai dai raunin zuciyarta bazai barta ta Iya karantawa ba, A hankali Ta furta"I love You so much our lovely sister, Allah yaji ƙanki" Tana ƙoƙarin rufe diary ɗin, Ba zato ba tsammani, Sajeed Ya faɗo dakin sam babu sutura a jikin shi sai ɗan gajeran wando, sumar kanshi ta yamutse kamar yadda fuskarshi take a yamutse babu annuri babu walwala ko sallama baiyi mata ba, Ita kanta data kalle shi sai da gabanta ya faɗi ganin yadda ya faɗo mata ɗaki da short. Muryarta na rawa ta furta"Sa... jeeed!? Lafiya ka shigo min daki babu sallama meke damunka!? ta jefa mashi tambayar tana kallon shi, babu alamun zai amsa mata har saida ya haye kan gadonta Ya zauna Yana fuskantar ta, la66ansa Na rawa Ya furta" I had a dream..." Ya faɗa yana ƙoƙarin tattara natsuwarshi A matuƙar ƙagare tace"Wani irin Mafarki kayi ne daya rikitar dakai haka" Ruƙo hannunta yayi acikin nashi ya matsa shi kafin cikin sanyin murya ya furta. "TWIN SISTER ƊINA!!" Rass Taji gabanta yayi mugun faɗuwa tunkafin ma taji ƙarashen zancen. "Sister tun bayan da muka baro prison muka tsinci kanmu a Daji, kafin Allah ya kawo mana ɗauki muka bar dajin Zuwa america, ban ta6a yin mafarki da ita ba, tamkar ma namanta da itane don ko tunaninta bana yi, amma Yau bayan mun kammala Yin breakfast, dama bacci bai isheni ba, na koma ɗakin na kwanta cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awon gaba da ni, kwatsam nayi mummunan mafarkin duk da kin ta6a fadamin babu kyau mutun yayi bad dream ya faɗa ma wani amma wannan mafarkin kamar wani tuni ne da Allah yake yi min akan Ƴar uwata da kuma sauran yaran da ake azabtar da rayuwarsu a gidan kurkukun ƙaddara....... " a yayin da yake yin maganar hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jikin unaisah sai tsume yake yi "Ina sauraronka, ka faɗamin me ka gani a cikin mafarkin naka"? "Naga abun da ya fi ƙarfin idanuwana, saboda bala'e kukan da nikeyi acikin mafarkin har a zahiri sautin shi yake fita batare da sanina ba, har sai da naufal ya farkar dani daga baccin ya ke faɗa min.... " shiru ya ɗanyi na wani lokaci suna kallon juna idanunsu azazzare yayin da bugun zuciyarsu ke hauhawa. "A Cikin mafarkin da nayi, naga sister dina GABRIELLA, tare da wasu Yara sanye cikin jajayen uniform kalar namu, ko'ina na jikinsu Jiƙe Yake da Jini, Hannayensu da ƙafafuwansu a daure suke da igiyoyi, hatta bakunansu an toshe su da jan ƙyalle, na dinga ihu ina kiran sunanta, bata iya yi min magana sai dai hawayen jinin da ke fita acikin idanuwanta.... Sister bansan ya zanyi ba, Ni da farko na fidda rai da ita amma a yanzu inason ganinta inason nasan awani hali take aciki, tana araye kota mutu? Duk da bana kawowa raina cewa bata arai.... " daƙyar Ya ƙare maganar wani irin kukane yaci ƙarfinsa, da sauri ya kifa kanshi saman kafaɗar Unaisah, Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, ta rasa gane meyasa har yanzu ba su yi wani yunƙuri na ruguza kurkukun ƙaddara ba, tabbas sunyi ganganci saboda kowani ɗaƙiƙa ɗaya da suka 6ata barazana ce arayuwar sauran yaran dake a Prison. A hankali ta daura hannunta saman bayanshi, Cikin sanyin murya tace"bansan ma me zance ba, ni kaina na girgiza da jin mafarkin da kayi, amma abin da nakeso in tuna maka mafarki ba gaskiya bane, ba lallai bane abunda ka gani ya zamana gaskiya, zaiyi wuya... " lallashin shi taci gaba dayi, Jikinshi duk ya saki babu kuzari kamar wanda yayi ciwo, hada zazza6i ke kokarin kama shi. ɗago da kanshi tayi daga kan kafaɗarta ta talla6o fuskarshi da hannayenta biyu, dakyar yake iya buɗe runannun idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur da su. "Dan Allah, ka daina kuka, bana son ganin ɗan uwana a wani hali na damuwa, bana jin daɗi" Muryarshi na rawa yace"sister, ba zaki gane ba ni kadai nasan abunda nake ji, wannan mafarkin ina jin shi dagaske ba wasa ba, ni dai kawai ki shirya mana abunda ya kamata muyi" Shiru tayi tana tunani aranta na tsawon mintuna batare da ta kau da idonta daga nashi ba tace"Sajeed, ka kwantar da hankalinka, In sha Allah komai yakusa zuwa ƙarshe, Yunƙurin da zamuyi zai zamanto TAKUN ƘARSHE a tafiyar mu, A yanzu ba za mu Iya yin komai ba in har Danish bai samu Lafiya ba, Shine jagoranmu kuma garkuwarmu, su kansu mutanan dake kula damu burinsu Danish Ya farfaɗo daga muguwar kasalar da yake fama da ita...." "Har yanzu bangane me kike nufi ba, shin mu ba zamu Iya tona masu asiri bane? Sai Danish"? "Wani asiri Zamu Tona masu? Bayan sun riga da sunsan komai dangane da rayuwarmu!!" A firgice Sajeed Yake dubanta da alamun mamaki Ya furta"ke kika faɗa masu"? Girgiza mashi kai tayi"a'a bani na faɗa masu ba, amma ina da tabbacin sunsan komai, kuma akwai shirin da suke Yi shiyasa suke buƙatar Danish. Fuskarshi da alamun ruɗanin kalamanta yake kallonta. Fahimtar hakan yasa tace mashi zan yi maka bayanin komai, Amma Ba yanzu ba, Ni dai burina ka kwantar da hankalinka, Sister dinmu kuma zamu cigaba dayi mata addu'a, Har zuwa lokacin da zamu ɗauko ta" Kwantar mashi da hankali taci gaba dayi har saida taga Ya samu nutsuwa tukunna tace "Ka ta shi ka shiga toilet ka wanko fuskarka duk ta 6aci da hawaye" in a cool voice Ya amsa mata da toh, Ya sauko daga kan gadon Ya nufi toilet din ɗakin su Ya shiga ciki. Har saida taga Ya maida ƙofa Ya rufe sannan Ta kau da idonta, cigaba da neman sim din tayi, sai da ta tarwatsa littattafan A ƙarshe ta gano shi cikin ƙaramin aljihun backpack din, Ajiyar zuciya ta sauke, kafin Ta dauki wayar ta sanya sim din, power button ta danna nan take screen din wayar yayi haske. Contact ta shiga anan taga phone numbers waɗanda dr laura ta yi mata saving akan waya, Murmushi tasaki tana tunanin wani time yakamata ta kirata awaya su gaisa"? Kafin Ta yanke shawara, Sajeed Ya fito daga Toilet fuskarshi da lemar ruwa ya nufe ta idanunsa akan wayar hannunta, tun kafin yayi magana ta dago da wayar tana nuna mashi tace"Ka tuna wannan wayar"? fuskarshi babu walwala yace"Na tuna, Itace Dr Laura ta america ta baki ko" daga mashi kai tayi"ina fata kanka baiyi maka ciwo"? Cikin kulawa tayi mashi maganar, zama yayi daga gefen gadon kafin yace"yana yi min amma da sauƙi," "Ko in kar6o maka magani"? Girgiza mata kai yayi alamar a'a"basai nasha ba zanji sauƙi in sha Allah" Diary din dake ajiye gefenta yakai hannu ya ɗauka, har zai buɗe shi tayi saurin fisge shi, Tamkar walkiya wasu hotuna guda biyu ƙananu suka faɗo daga cikin diary din babu wanda Ya lura da su a tsakaninsu har hotunan suka sulale kan floor. "Bazan bari ka bude shi ba, saboda Zai Iya fama maka raunin dake a zuciyarka," ta faɗa tare da tattara textbooks din da sauran kayan da ta fiddo daga jakar ta mayar da su ciki. Miƙa mata hannu yayi"tun da kin hanani ganin diary din, Bani wayar Hannunki," babu musu ta miƙa mashi. Danna danne ya soma yi duk tana kallon shi. "Unaisah, kinsan wani abu"? Da sauri tace A'a "Ina ji araina na ta6a ruƙe waya, Kalar wannan, Kamar Mommyna ne ta siya mana nida twin sister dina" Waro Idanu waje tayi jin abunda yace, Da mamaki tace"Sajeed, Zaka Iya tuna wani abu dangane da rayuwarka? Naji kana fadin ka ta6a ruƙe waya kalar wannan mai tsada"? Jinjina mata kai yayi"bakomai zan Iya tunawa ba, Yanzu ne naji abun Yanayi min yawo akaina, Amma tabbas nima na ta6a mallakar I phone nawa nakaina hada Laptop, Sannan mahaifiyarmu Farace daddynmu kuma kalar skin dinmu gare shi chocolate colour......" tunda yafara magana Take binshi da kallon mamaki da al'ajabin ta yadda akai har ya fara tuna wani abu dangane da rayuwarshi, bayan ta ta6a tambayar shi a lokacin suna a prison yace mata bazai iya tunawa ba, wata'kil Allah ne Ya nufa sihirin da matsafan suka yi mashi zai warware shiyasa yafara tunanowa, Hankalin shi na akan wayarta yaci gaba cewa"muna kama da daddynmu Ni da sister ɗina, Idan bazan manta ba, Mahaifin mu Attajirin mai kuɗine... " muryarta a ruɗe tace"Zaka Iya Tuna sunan shi? Ko sunan Mommyn ku? Da sunan Country din da kuke rayuwa? A ƙagare ta furta maganar. Shiru ya danyi, Yana kallon Screen din wayarta da yake daddanawa. "Bansan asalin sunan shi ba, amma kamar yana da nick name da ake kiran shi da shi, Ni kamar Big Boss Ne Namanta, mommyn mu kuma sunanta umm......" duk yadda yaso ya tuna sunanta ya kasa. Cike da zumuɗi ta dafe kafadarshi"bro, Kayi ƙoƙari ka tuna dan Allah, Koda bayanzu ba, waɗannan bayanan da su zamuyi amfani wurin gano su wanene Azzaluman da suka sadaukar da mu" Jinjina mata kai yayi"zanyi ƙoƙari na tuna, amma ko Yanzu naga daddyna wallahi zan gane shi saboda kamanninmu sun 6aci da shi Yana da Kyau, hatta ƙirar jikina kalar nashi ne da sumar kaina, bani da banbanci da shi sai dai na girman jiki da shekaru" Ɗaga hannayenta sama tayi"Ya Allah Ka bayyana mana bayin Allah nan, Da mahaifin Unaizah Jan wuya, da dukkan waɗanda suka sadaukar da mu, wallahi muna kwaɗayin Ganin su ko don mu tarwatsa zukatansu" addu'o'i ta dinga yi yana amsa mata da ameen. "Da ace zan Iya tuna Phone number din mommyna da mun jaraba kiranta, saboda na ta6a haddace layukan wayarta dana Daddyna amma nasan zaiyi wuya mu same su. Cikin sanyin Murya Ya ƙare maganar, Unaisah tace"Sajeed, koda ka tuna layin wayarta wallahi ba lallai tana amfani da shi ba, tun da mugayene babu Allah aransu, kamar yadda Iyayen Unaizah suka hana tasan komai nasu, kuma zai Iya kasancewa Hakane" "Kin faɗi gaskiya, amma duk da haka zan jaraba rubutawa mu gani," ya fada tare da daddana wayar Ya rubuta number dayake tunanin ta mommynsa ce, duk suka ƙura ido suna jiran ganin in zata shiga, Muryar na'ura ce ta sanar da su cewa Number da suke kokarin kira badaidai take ba, dafe kai yai da hannu ɗaya"nayi mistake sister bazan iya tuna ainihin yanda number din yake ba" fuskarshi yamutse yayi maganar. Ganin Yana rubuta wata number ne yasa tace mashi"wannan fa"? "Layin wayatane zan kira" natsuwa sukayi suna jiran jin in zai shiga, Har saida gabansu Ya faɗi Jin Wayar Na yin ringing, duk da basu da tabbacin Idan Number dai dai Ya sanyata, kallon juna su ka yi da alamun mamaki, Har kiran ya katse ba'a ɗaga shi ba, Suka sake kira nan ma ba'a yi picking ba.... "Mu bari zuwa Anjima sai Mu ƙara Kira, Allah yasa layin dai dai muka Kira," acewar Unaisah Sajeed Ya amsa mata da ameen. *❤MOM SARAH🤍* Su biyu ne zaune Asaman wasu Hadaddun kujerun shaƙatawa dake a bakin Swimming pool Area na gidan, Daga tsakiyar su table ne mai ɗauke da Mugs guda Biyu na coffee suna sha suna fira, Hajiya Layla ta sanya arab gown ta yafa mayafi akanta, yayin da ita kuma Hajiya Sara ta dauki wankan kimono robe, babu mayafi akanta zallar gashin kanta ne ta saki har saman gadon bayanta launin Ja. "Har yau ina mamakin Yadda Kike rayuwa da Mijin ki, mutun babu fara'a babu annuri, gaskiya Ina jinjina maki" Hajiya layla ce tayi maganar. Murmushi hajiya sara tayi"bana damuwa da hakan, Saboda nature din shi ne, Sai ka Iya zama da shi zaka gane wanene shi, Yana da sauƙin kai, fiye da tunaninki" ta6e baki Hajiya laila tayi"ahakan"? Jinjina mata kai tayi"ƙwarai kuwa, saboda Yana kyautata min, kuma yana nuna min so, tun lokacin dana aure shi bai ta6a canza min ba, nasan yana da wuyar sha'ani sai dai ba kamar yadda kika zata ba, ban ta6a neman abu a wurin shi na rasa ba, ko baida shi zaiyi min ne balle ma Yana da shi din, Baya son 6acin raina, Sannan yana bani kulawa, wani lokacin idan muna atare sai in dinga jin kamar ma bamu daɗe da yin aure ba saboda yadda yake tarairata...." tun da hajiya sarah tafara kora ma hajiya layla bayani take ta faman yamutsa fuska, ba haka taso taji daga gare ta ba, tun ɗazu take ƙoƙarin bugun cikinta don taji ya take haƙurin zama da Alhaji musa sai dai wani abu data fahinta dangane da Hajiya sarah irin matan nan ne masu shegen wayau, ba su bari aji sirrin mijin su, baka ta6a jin aibun mijinta abakinta sai dai Alkhairinsa. Mug din coffee ta dauka ta kur6a zuciyarta ajagule, bayan ta ajiye mug din tace"amma a ganinki abunda Alhaji musa yake yima Mijina ya dace? A matsayin shi na yayanshi ya dinga juyashi son ranshi"? Girgiza kai Hajiya sarah tayi"Ni kaina ban goyi bayan hakan ba, ko lokacin da ya bashi umarnin yazo daku joss sai da nayi kokarin dakatar dashi sai yace min indaina sanya mashi baki akan abin da ya shafi danginshi, gaskiya banji daɗi ba, amma abunda ke ɗaure min kai, meyasa shi Alhaji ubaid ɗin Yake yi mashi biyayya? Bayan shine ke babba"? Ɗaure fuska Hajiya layla tayi tamkar bazata tanka mata ba tace"may be ko dan arziƙin Shi bai kai na musan ba shiyasa yake liƙe ma shi, kinsan idan mutun nada arziƙi ko shine ƙarami agida babba yake komawa" "Bana tunanin haka, amma dan Allah ki yi haƙuri da halin mijina" ta faɗi hakanne don ta fahimci ran Hajiya layla a6ace yake da abunda Alhaji musa yayi masu. "Bazan 6oye maki ba, ina jin haushin Yadda Mijinki Yake juya mijina, wannan ba ɗabi'ar arziki bace, Yana da girman kai da izza, nazo gidan nan ne bada son raina ba, Alhaji Ubaid shine Ya takura min akan muzo, da wallahi ko ƙeyata bazaku gani ba" a fusace ta faɗa tana haɗe rai, jin wannan maganar yasa Hajiya sarah ta sassauta muryarta"Allah Ya Huci zuciyarki, nasan bai kyautaba.... " Kwa6e fuska Layla tai batare da ta kuma cewa komai ba. "Na lura kamar ranki Ya 6aci" acewar Sarah, Murmushin yaƙe Layla tasakar mata"komai ya wuce ai, Tun da na faɗi ta cikina, kinsan ni ban iya 6oye damuwata ba" Martananin murmushin sarah tayi mata, tsawon mintuna babu wanda ya ƙara yin magana acikinsu sai dai su kalli juna suyi murmushi. Sai daga bisani Layla tace"Inataso in tambayeki Omar Ɗin mu tsawon lokaci ban sanya shi a idanuwana ba" Hajiya sarah tace"Ni kaina bansan meya ruƙe shi A america ba, baya son zama nigeria saboda daddyn shi da basa jituwa, Amma yana kokarin kirana awaya wannan karanne ma ya dau lokaci nima kona kira shi bana samun shi, sai idan shine Ya tuntu6e ni" Har layla ta buɗe baki zatayi magana Ta hango Zeenatu dake tunkarosu sai sauri take Yi, Riga da wandon jean ne a jikinta, Kanta babu mayafi, Yau ne karo na farko Da hajiya layla tafara ganin zeenatu tana yawo babu mayafi a jikinta. "Dama zeenatu tana yawo babu hijab ba mayafi a jikinta" jin haka yasa sarah ta dubi inda hajiya layla take kallo ita kanta mamakine Ya kamata. "Sai dai idan wani abunne Yaja hankalinta har ta manta bata sanya mayafin ba" Sai faman sakar masu murmushi take yi, Cikin girmamawa ta gaishe da su atare suka amsa mata. Mom sara tace"daughter Kin dubi jikin ki kafin ki fito daga ɗaki"? da sauri takai hannu ta shafa kanta taji babu mayafi, duk tabi ta ruɗe tana faman zazzare idanu, kunyar duniya ta kamata. "Mom, wlh bansan babu mayafi ba, ashe haka na fito, namanta da hijab din saman gado, Bari na koma in dauko" Gaba ɗaya suka sanya dariya Layla tace"Ki kwantar da hankalin ki, ai ba wani abu bane don kinyi yawo a cikin gidanku babu mayafi, amma dai yakamata kina kulawa tunda kin girma" ta fada tana kallon kirjinta da suke aciki kamar zasu fasa rigar, dukar dakai ƙasa zeenatu tayi wani irin kunyarsu take ji "Bari na koma in dauko mayafin" Har zata juya Mom sara tace"ke zonan" da sauri ta dubeta, Da ido hajiya sarah ta nuna mata wayar hannunta"me kike yi da ita"? "Oh namanta, Ita na kawo maki, Ana kirana da baƙuwar number a lokacin ina a toilet, ban samu damar yin picking ba shine na kawo maki ki duba mai kiranki" A ruɗe Sarah tace"kamar ya ana kirana? Wayar wacece"? "Tawa ce" "Sai kuma kice ni ake kira"! "Mommy ai ni bana amfani da ita, tun da na kar6eta a hannun ki nace maki zan ba yaya shureim ya tura min hutunan su to su kadai nake kallo, ni banma lura da sim awayar ba" Miƙa mata hannu sarah tayi"bani wayar" bayan ta kar6a ta soma bincika layin dake akan wayar don ita kanta batasan akwai sim ba, sai yanzu da zeenatu take fada mata. "Layin Mtn ne akan wayar, amma wannan number da aka kira ki da ita bansan wanene ba, ki koma ciki, Idan na shigo zan duba mai kiran naki" Amsawa tayi da toh, da sauri ta juya ta nufi cikin gidan cike da fargaban kada Yaya shureim yaganta da ƙananun kaya. Har saida ta 6ace ma ganinsu tukunna suka kau da idanunsu daga kallonta. "Zeenatu tana burgeni, Idan ina kallonta sai in runka tunawa da Yarinyar Benazir" Sarah dake kallonta tace"yarinyar da baki damu da ita ba? A yadda naji labari baki ta6a ganinta ba saboda baki zumunci dasu" "Hakane, Amma ayanzu da zan ganta babu abun zai hana in rungumeta, saboda nayi danasanin watsin danayi dasu" Sarah tace"kinyi babban kuskure, Baki kyautaba, Sai kace ba jininki ba, Ai ni da jikatace wallahi koda ban son mahaifinta saina ƙaunace ta, laifin wani baya shafar wani" Shiru Layla tayi batare da ta sake cewa komai ba, Ita kadai tasan takaicin da take ji duk idan ta tuna yadda taƙi Tajuddeen da Yarinyar shi...... Bayan zeenatu ta shiga gidan, Cikin sanɗa take tafiya gudun kada Dr shureim Yaganta ahaka, babu kowa hanyar data biyo sai lalla6awa take yi kamar wata 6arauniya, adai dai lokacin dr shureim ya fito daga bedroom din shi sanye da jallabiya, Babu rawanin larabawan da yake naɗawa akanshi zallar sumar kanshice har saman wuyanshi ta nannaɗe gwanin ban sha'awa. Tunda yayi tozali da bayanta Ya ƙura mata ido yana kallonta, kwata kwata ranshi bai bashi cewar zeenatu ce ba, saboda bai ta6a ganinta da ƙananun kaya a jikinta ba, sun matseta duk da bata da ƙiba kayan sun mata kyau. Da sauri Yabi bayanta Kamar yadda take Yin tafiya cikin sanɗa shima haka Yabita da sanɗar har cimmata, "Zeenatu"! Kaitsaye kiran ya daki kunnata, A firgice ta juyo idanuwanta azare take kallon shi, wata irin zabura tayi da niyar ta watsa da gudu sai dai kafin tayi hakan yayi sauri ruƙo waist ɗinta ya dawo da ita jikin bango, Ya dafe da hannu ɗaya yana binta da kallon mamaki. Da sauri ta daddafe kirjinta da hannu biyu don kada yagan mata abunta, ta kasa jurar hada ido da shi, Kunyar shi duk ta kamata, Juya mashi baya tayi tana fuskantar Bango, muryarta da shagwa6a ta furta"ni fa bansan babu mayafi na fito ba," Koda tayi maganar hankalinshi na akan bayanta data juya mashi, sumar kanta yabi da kallo, ƙamshin turarenta sai shigar mashi hanci yake yi Jin yayi shiru bai tanka mata bane yasa ta juyo don ganin me yake yi, karaf suka haɗa ido cikin na juna, kallon juna suka cigaba dayi kamar zasu haɗiye kawunansu tsabar so da ƙauna, Bai ta6a yi mata kyau irin na yau ba saboda sumar kanshi daya bari babu Arab turban dinsa, haka shima tayi mashi kyau yau daya ganta da ƙananun kaya. daƙyar Ya iya tattara natsuwarshi Ya furta"Kin yi min kyau" murmushi tasaki tana faman ƙyafƙyafta mashi blue eyes din ta. Ɗaura hannun shi yayi saman sumar kanta, lallausar gaske Ya shafata a hankali har wani lumshe mashi ido take Yi Can ƙasan maƙoshi ya furta"na fara tunanin yi ma Uncle maganar auran mu saboda naƙosa na mallake ki, ko dan ki haifa min fatima" shi kanshi baisan ya furta hakan ba, gaba daya yafara zaucewa da kyawun zeenatu Runtse idanunta tayi da sauri tare da ɗaura tafukan hannayenta ta rufe fuskarta alamar taji kunyar kalamin shi "Yaya shureim ni kunyarka nake ji, dan Allah kabarni in tafi ɗakina" "Ki daina jin kunyata, Ni da nake burin ki zama abokiyar rayuwata" wani irin daɗine ya ziyarci zuciyarta jin kalamin daya furta mata. Tunda yafara kallonta bai bari ya daura idonshi akan dukiyar fulanin ta ba sai da taja numfashi suka motsa tukunna hankalin shi ya karkata akan su. Yajima yana mamakin cukowarsu kamar bana yarinya ba, jin numfashinshi saman fatar kirjinta yasa tayi sauri buɗe fuskarta da idanunta gaba ɗaya lissafi na neman kwance mashi kamar zai cafko su haka yake ji ya duƙufa yana kallonsu ko kyaftawa baiyi. "Yaya shureim menene haka? Dan Allah ka daina kallona, Ka bari sai munyi aure" Ta fada tana bubbuga mashi ƙafafuwanta, ɗagowa yai da idonshi ya kalleta launinsu harya fara canzawa Matsar da fuskanshi yayi saitin tata ya daura tsinin hancin shi akan nata, nan take ta soma jin wani irin yanayi atattare da ita, Numfashinta harya fara canzawa, Bugun zuciyarta ya ƙaru, duk ta ƙagara da son jin shi a jikinta, tayi tunanin zaiyi mata irin abunda taga daddynta da mommynta sunayi wato kisssing din junansu. Kamar tasan abunda ya ke shirin yi mata kenan, saboda baya a hayyacinsa a buƙace yake da ita, Yana kokarin haɗe bakinsu, Kwatsam Benazir Ta biyo hanyar da suke da sauri take Tafiya sautin takalmanta ne suka ja hankulansu, a gigice Zeenatu ta bangaje dr shureim ta watsa da gudu ta nufi bedroom dinta. "A'u'zu billahi minasshaidanirrajim" acikin zuciyarshi ya furta hakan. *Daga Alƙalamin Boss Bature💋✍️* *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura* 3196407426 First bank Bature Hafsat Muhammad, *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida* *Something Is About to Happen* _______________________________🌹✍️ jikin shi da kasala Ya juyo Yana duban Benazir dake tunkaro shi ga dukkan alamu bata ga Zeenatu ba. "Yayana nakaina, me kake yi anan"? Tana murmushi tayi mashi maganar Sam ya kasa buɗe baki Ya bata amsa, sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi. "Lafiya? Ya akai naga idanunka sun yi ja"? Aruɗe ta jefa mashi tambayar tana duban shi. Shafa sumar kanshi yai da hannu ɗaya kafin ya furta"bakomai, Yanzu na tashi daga bacci," "Amma dai daga gani baccin bai isheka ba, cos gaba ɗaya kamar ma baka a hayyacinka" Ƙaƙaro murmushi yayi akan fuskarshi batare dayace mata komai ba. "Yayana, Maganar zuwa gidan su Aneeleeh ne Ya kawo ni, wallahi duk na damu da rashin samun layin Abie din su, har number dinsa na kar6a awurin daddy na jaraba kiran layin da wayar mom amma shiru ba'a ɗagawa" muryarta tamkar zata fashe da kuka tayi maganar. "Bana so mubar abuja batare da mun je gidan su ba" "In sha Allah zamu je, Zanyi maki ƙoƙarin hakan, abun da yakamata mu yi shine mu tura mashi da text message, may be layin nashi baya akan waya duk ranar da ya sanya shi zai ga sakon mu ne" "Hakane, tun da akwai layin awayarka ka tura mashi da sakon" Ba tare da 6ata lokaci ba, Dr. Shureim Ya zaro wayarshi, ya soma daddanata "Me zan rubuta mashi"? Ya tambaya yana kallonta. "Ka faɗa mashi Benazir ce Ƙawar Aneelerh, Matar Tajuddeen" Ya furta Okey, bayan ya gama rubutu text din Ya turama masa, Kafin daga bisani ya ɗago da ido, Ganin takura mashi ido yasa shi yi mata gyaran murya"lafiya kike kallona"? murmushi tasaki tare da fadin"yayana fada min gaskiya, meya jefa ka cikin yanayin nan" ta fada tana ɗage mashi gira, nan take ya fahimci jikin shi ya nuna halin da yake aciki, shafa kirjin shi yai da hannu tamkar zai gyara ma6allin gaban jallabiyarsa Duk yabi ya dabarbace wata irin kunya ce ta kama shi. "ina Zeenatu"? Ta jefa mashi tambayar tana bin shi da kallon ƙurulla. Galla mata harara yayi"Bansani ba, Ƴar sa Ido, Kije dakinta ki neme ta, wato dai bazaki canza halinki ba, Har yanzu kina nan da rashin jin maganarki, ' kafin ta kara furta mashi magana yayi saurin wuce ta Ya nufi bedroom dinshi, Yana shiga ya jefar da wayarshi kan gado da wata irin kasala Ya faɗa saman gadon Yana fuskantar ceilling, wani irin yanayi yake jin kanshi mara misaltuwa. Lumshe idanunshi yayi yayin da acan cikin zuciyarshi yake tariyo wani abu daya ta6a faruwa arayuwarshi Har abada bazai ta6a mantawa da wannan daren ba, wanda yake yi mashi laƙabi da DESTINED NIGHT, abun da ya faru a daren Ya tsaya mashi aranshi Ya kafa tarihin da har abada bazai ta6a gogewa aranshi ba. Ƙoƙarin canza akalar tunanin nashi yayi gudun kada ya fama raunin dake a zuciyarshi. Sunan Allah yaci gaba da ambato har saida yaji zuciyarshi tayi mashi sanyi tukunna Ya samu damar miƙewa Ya nufi toilet don Ya tsarkake jikin shi. __________________Boss Bature A hankali dankareriyar Motarsu Ta kunno kai ta cikin Katafaren Gate din shiga gidan dake a tsare da Security Officers, motace Yar Ubansu mai numfashi tsadaddiyar Gaske, Su biyune a back seat Na motar, Alhaji musa dake a hakimce Ya kishingiɗa saman seat din ta motar, Wankan boyal ne a jikin shi launin milk sun zauna mashi, daga gefen shi Alhaji Ubaid ne Cikin shiga ta shadda fara, dawowarsu kenan daga taron da suka halarta wanda akayi a head quarter na party din su. Tun kafin Security guard din dake driving dinsu yayi parking, idanun Alhaji musa masu dauke da bacci suka hango mashi Hajiya sarah da layla dake a gaban Swimming pool suna fira, ta cikin window din motar Yake dubansu, Ranshi yayi mugun 6aci, dama fuskar babu annuri ko miskala zarratin. Bayan motar tasu tayi parking a harabar Ajiye motocinsu, Bai jira Security guard din Ya buɗe mashi mota ba, da kanshi Ya buɗe murfin Ya fito Yana faman haɗe rai, fitowa daga cikin motar Alhaji Ubaid Yai, idanunsa akan Musa yace"wai meke damunka ne? Tun dazu da muka fita taron jam'iya babu annuri akan fuskarka, mutane sai rububinka sukeyi amma kai ko kaɗan basu agaban ka, Ka haɗe rai kamar wanda aka aiko ma sakon mutuwarsa... " kafin Alhaji Ubaid Ya ƙare maganar, Alhaji musa Ya ɗaga mashi hannu babu mutunci Ya furta"Ya isa haka! Bana son jin maganar nan," da sauri Alhaji ubaid Yaja baki yayi shiru, Cikin Takun Isa da izza Alhaji musa Ya haura ƙafa Ya nufi Cikin gidan. Hajiya Layla dake hangen su Alhaji ubaid tun da suka fito daga mota, da zolaya tace ma mom sarah"Matar so Ga mijin So can Ya dawo, Naga kamar ranshi a6ace Yake yakamata kije ki lallashe shi" sai data furta maganar Hankalin Sarah Ya kakarta akan su, A lokacin Har Alhaji musa Ya shige Ciki, miƙewa tayi da sauri tana fadin"Nasan bai wuci gajiya bace ta dameshi, dama da safe kafin ya fita Ya faɗa min baya jin dadin jikin shi, " tana ƙare fadan hakan Tabi bayan Alhaji musa. Bayan tafiyarta, Hajiya layla bata motsa daga inda take a zaune ba, Alhaji ubaid take Jira Ya ƙaraso inda take ganin Yana tunkarota sai faman sakar mata murmushi Yake Yi, Ita ko ta haɗe mashi fuska, don ba ƙaramin haushin shi take ji ba tunda yaƙi amincewa da zancen Komawarsu Joss. Kujerarar dake fuskantarta Yaja ya zauna. Fuskarshi da fara'a yace"uwargida ran gida, fatan na sameki Lafiya" Banza tayi da shi batace komai ba, sai ma cup da ta dauka tana shan sauran coffee dinta "Layla kina ji ina magana kinyi banza kin ƙyaleni, Ko sannu da dawowa babu" Ta6e baki tayi tare da hararar shi tace"hmmmm, me kakeso nace"? Shiru yayi baice mata komai ba, sai dai binta da idanu da yakeyi. "Ka bani mamaki, nayi tunanin mijina Namiji ne, ashe ba haka bane nayi kuskure, Ka nuna min kai ba komai bane wai ƙaninka shike juya ka son ranshi, baka jin maganar kowa In ba ta shi ba, kamar wani ubanka" rai a6ace tayi maganar. Tuni yanayin fuskar Alhaji ubaid ya canza zuwa matsananciyar damuwa, baya son mitar da Hajiya layla take yi mashi kullum haka ya ke fama da ita. "Layla bai kamata Kina gaya min magana ba, Har yanzu ni mijinki ne matsayina agareki bazai ta6a canzawa ba... " Murmushin takaici tasaki tana dubanshi tace"Ubaid! Duk abunda na faɗa maka Kaine kaja, wallahi ka 6ata min rai, bana jin daɗin ƙasƙantar damu da ka ke yi awurin musa, baya ganin girman kowa daga kai har ni, burinshi mu zama tamkar bayinshi shi kuma uban gidan mu, na rasa gane da wani yare zanyi maka magana yadda zaka fahimce ni...." muryarta na rawa ta ƙare maganar, hawaye tuni sun cicciko idanunta. Girgiza kai yai cikin sanyin murya yace"bani da amsar da zan baki, duk abunda kika faɗi gaskiya ne layla, bawai bana fahimtar ki bane, sai dai bani da yadda zaniyi, yakamata kiyi min uziri, Ni ina girmama musa ne saboda halaccin shi agareni, yayi min abubuwa da dama waɗanda bazan ta6a mantawa ba, duk wani cigaba da kika ga na samu arayuwata musa shine sila....." kasa ƙarasa maganar yayi sakamakon dariyar da layla ta saki tamkar wata zararra, jikinta har jijjiga yake yi. da mamaki akan fuskarshi yace"meyasa kike min dariya? Kin maidani mahaukaci ko"? Tsagaitawa tayi da yin dariyar ta soma yin magana. "Mijina Ina tausayin rayuwarka, Sannan Ina jiye maka ranar da zaka yi danasanin yarda da kayi da ƙaninka musa, saboda ya riga daya gama dakai! tarkon daya ɗana maka Yayi tasiri a zuciyarka, Wai kai baka amfani da ƙwaƙwalwarka ne? Idan har don Allah yake kyautata maka meyasa baya yi maka biyayya amatsayin shi na ƙaninka"!? A faɗace tayi maganar, Alhaji ubaid Yayi shiru Yana sauraronta, kalamanta sun yi mashi tsauri suna neman ruguza mashi lissafin ƙwalwarsa. "Kasan ni bana 6oye ta cikina! Idan abu yana damuna kai tsaye nake faɗi ma mutun koda kuwa bazata yi mashi daɗi ba" Ta faɗa tana mai ƙara jaddada kalamanta. "Yakamata ka farka daga baccin da ka ke yi, tunkafin lokaci Ya ƙure maka, Ni dai zan faɗamaka gaskiya koda kuwa zaka ji haushina ne, Alhaji musa ƙaninka ba ƙaunarka yake yi ba dakai da iyalanka, Baya sonmu ba don Allah Yake kyautata mana ba face sai don saboda wata manufa tashi, na faɗa maka hakanne bawai don ina zargin shi da wani abu ba, sai don saboda babu gaskiya a lamarin shi!" A zafafe Ta ƙarasa maganar, tare da kai hannu ta daki gaban table din, Bata jira amsar da zai bata ba tayi saurin miƙewa zuciyarta na tafarfasa ta nufi cikin gidan ta shige. Gaba ɗaya Alhaji Ubaid Ya rasa meke yi mashi daɗi a duniyar nan, Har cikin ranshi bayason 6acin ran layla, A cikin ƴan kwanakin nan kusan kullum sai sun samu sa6ani da ita saboda Alhaji musa, baisan ya zai yi da ita ba, a ganin shi itace ta tsani Alhaji musa shiyasa take neman 6ata mashi suna a wurinshi duk don su bar gidansa. Ya jima zaune kan kujera Hannin shi ɗaya dafe da kanshi sai daga bisani Ya miƙe Ya nufi cikin gidan. *ALHAJI MUSA💪* Bayan shigarshi bedroom dinsa, rage kayan Jikin shi yayi, ya rage saura farar shirt da short, Sai faman Cika ya ke yi yana batsewa, zuciyarshi Ta kai maƙura awurin 6aci. Hajiya sarah tana ƙoƙarin shigowa bedroom din nashi, ba zato ba tsammani taji Ya furta"Kada ki kuskura ki shigo min nan!" Ras taji gabanta Ya faɗi, abakin kofar ta tsaya tana dubanshi Yana daga tsaye Ya dafe sofa din dakin da hannayenshi. "Meyasa zaka hanani shigowa"? Cikin kwantar da murya tayi mashi maganar Tamkar bazai tanka mata ba yace"zonan"! Kamar wata ƙaramar yarinya haka ya kirata, bayan ta shiga dakin daga gaban sofa din ta tsaya tana kallon shi. Zagayowa yayi ta gabanta, ya sassauta fushin fuskarshi. "Meya hana ki zuwa wurin Aiki yau"? Cike da jin shakkar shi tace "Namanta ne ban faɗa maka ba, Jiya na ɗauki hutu saboda Hajiya layla inaso muna samun lokacin da zamu dinga zama muna fira harma mu dinga fita" daƙyar ta ƙare maganar ganin irin kallon da yake jefa mata, tuni tasha jinin jikinta. "Saboda ita kawai kika ɗauki hutun aiki? Kin fara shaye shaye ne"? A ruɗe take kallon "Kin ci sa'a bani da ɗabi'ar ta6a lafiyar mace, da kuwa yau saikin yaba ma aya zaƙinta, " mamakin maganarshi ne yasa ta zaro idanunta waje har saida ta maimaita kalmar sai kin yaba ma aya zakinta. Adabarbace ta furta"bangane me kake nufi ba"? "Bani da lokacin Yi maki bayani, amma Inaso in ja maki kunne akan matar can, bana son ganin kina sakar mata jiki kuna yin fira, wannan umarni ne daga gare ni, ban amince ki rinka ke6ance kanki da ita ba"! ɗaure mashi fuska hajiya Sarah tayi"akan me zaka hana ni yin fira da ita? Haramunne yin hakan? Ko tayi maka laifi ne? Ina buƙatar hujja. Da kakkausar Murya Ya furta"Umarni nake baki ba shawara ba, ki koma aiki gobe sannan kada in ƙara ganin kin ke6ance da ita" Ya faɗa yana furzar da huci ta hancin sa. Ta fahimci bayason hajiya layla, ta daɗe da sanin rashin jituwarsu sai dai batayi tsammanin abun yakai haka ba. Ƙwara tabi Umarnin shi ta zauna lafiya idan ba haka ba, Ita zata jama kanta" Yana ƙoƙarin juyawa tayi saurin ruƙo hannun shi acikin nata, kallo ya jefa mata mai kama da harara. "Ka yi hakuri idan ranka ya 6aci, in sha Allah zanyi maka biyayya bazan ƙara zama yin fira da ita ba" Lumshe idanunshi yayi kafin ya buɗe su Ahankali Ya furta"me kuke tattaunawa ne da ita"? Tayi mamakin tambayar daya jefa mata, saboda tasan halin shi, mutunne da bai Iya shiga shirgin mutane ba, idan yana zaune a wuri baka isa ka yi mashi gulmar wani ba, amma sai gashi yau yana neman ta fada mashi abun da suke tattaunawa da Hajiya Layla. Bayan ta kammala faɗa mashi calmly ya furta"bansan meyasa ta sanya min ido ba, bata son ganina kamar na kashe mata wani" Matsawa Sarah tayi dab da shi ta ɗaura hannayenta saman fadadan kafaɗunsa "Kada hakan ya dame ka, ni dai shawarar da zan baka, dan Allah ka basu damar da zasu koma Joss, saboda ta nuna batason zama a gidan nan" ta faɗa tana mai tausasa kalamanta. Jinjina kanshi yayi"zanyi tunani akan hakan," Ya faɗa tare da juyawa Ya nufi Katafaren gadonsa, Ya haye ya kwanta idanunsa suna fuskantar ceilling. Duk sai taji ba daɗi, ganin yanayin shi da damuwa akan fuskarshi, tasan bai wuci ƙiyayyar da hajiya layla take nuna mashi bace tasa shi shiga yanayin. "Babe, kana buƙatar wani abu ne In kawo maka"? Batare daya kalleta ba Ya furta"Bana buƙatar komai, ki zo ki kwanta a gefe na" taji dadin maganar daya furta mata da sauri ta nufi gadon tare da hayewa ta zauna kan mattress din, sai da tafara zage zip din rigarta, ta cireta kafin ta kwanta saman kirjin shi, ya ruƙo waist dinta da hannun shi ɗaya, ɗagowa tayi da blue eyes dinta tana kallon sajan fuskarshi. "Bana gajiya dakai, banƙi mu kasance har Iya ƙarshen rayuwarmu atare da kai ba, Idanunsa dake a lumshe yaɗan buɗe su A hankali yana duban fuskarta ba tare daya ware su ba. Sumbatar cheek dinsa tayi, tamkar zaiyi murmushi sai dai bai bari Ya bayyana ba, ta fahimci yaji dadin abunda tayi masa, kallon juna suka cigaba da yi, tunawa tayi da layin dake akan wayar Zeenatu, har ta buɗe baki zata fada mashi kiran da akayi da bakuwar mumber da sauri ya ɗaura mata yatsa sama lips dinta. "Ina buƙatar hutu!" murmushi tasakar mashi, tare da rungumo shi suka ƙanƙame juna, cikin ƙanƙanin lokaci bacci yayi awon gaba da shi. Idan muka koma 6angaren Zeenatu tun da ta watsa da gudu ta nufi bedroom dinta, tana shiga ta haye saman gado ta kwanta tare da rungumo pillow a ƙirjinta, fuskarta ɗauke da murmushi, wani irin so da ƙaunar yaya shureim take ji, taso ace Benazir bata katse mashi hanzarin shi ba, da yau ta kar6i first kiss dinta a wurin hubbinta, wani irin nishaɗi take ji kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, sai faman juyi take yi a tsakiyar gadon kamar me fama da ciwon ciki. Jefar da pillown hannun tayi tare da saukowa daga kan gadon ta shiga toilet, after some mins ta fito fuskarta da alamun lemar ruwa ta nufi glass wardrobe dinta, suturar jikinta ta canza zuwa riga da skirt launin dark brown, ta dawo gaban mirror ta zauna tana kiciniyar ɗaure gashin kanta da ribbom. Jin motsin shigowar mutun ɗakinta ne yasa tayi sauri juyowa don ganin wanene Benazir ce a tsaye ta goya hannayenta saman kirjinta, Kamar mara gaskiya haka zeenatu take kallonta, duk tabi ta kame kanta wata irin kunyar Benazir ce ta kamata gani take yi kamar taga abunda suke yi ita da dr. shureim. Muryarta da in'ina ta furta"am.. um.. aunty Benazir kece" dariya Benazir tayi tare da shiga ciki tana fadin"Zeenatu kenan, dole ki ruɗe babyn shureim" Waro ido waje tayi jin ta kira ta da sunan babyn shureim hakan na nufin tagansu ɗazu, da sauri ta miƙe daga kan mirror chair din tana faman duƙar dakai ƙasa "Kin bani mamaki zeenatu, Ki rasa dawa zakiyi soyayya sai yaya shureim! Kamar kin makance, May be bakisan shekarun shi ba, Ki daina ganin shi kyakkyawa kamar matashin saurayi, ya kusa sa'an daddynki... " har saida gabanta ya fadi jin abunda Benazir ta faɗa mata. Muryarta na rawa ta furta"am... aunty Benazir kina nufin yaya shureim da daddyna sa'annin juna ne"? "Eh mana, kema in banda abunki taya zaki yi soyayya da wanda Ya girme maki? yafa haife ki" Da biyu Benazir take fada matan hakan duk don tacanza mata ra'ayinta na son ya shureim, don ita aganinta bai kamata yaso ƴar cikinsa ba, badan bata son shi da zeenatun ba, sai dai bata jin zata iya bari ya auri mace mai ƙaramin shekaru amatsayinshi na tazurun daya daɗe baiyi aure ba, zaifi dacewa Ya auri babbar mace wadda takai shekara talatin. Bubbuga ƙafafu zeenatu tayi akan floor, voice dinta da shagwa6a tace. "Aunty Benazir ai ba haramun bane, cos The Prophet Muhammad, peace be upon him, married Aisha when she was very young," ta faɗa tare da sanya hannu ta rufe fuskarta cike da jin kunyarta. Dariya Benazir tayi tana dubanta da mamaki wato bazata kar6i shawararta ba tafi son Sugar daddy irin Ya shureim. "Zeenatu Ki fahimce ni, Kinfi buƙatar saurayi wanda baifi shakara ashirin da bakwai ba, Ina zaki kai Ya shureim"? "Aunty benazir dan Allah kidaina fadin haka, wallahi bana so, Inason Ya shureim ɗina, koda tsohone shi" tamkar zata fashe da kuka tayi maganar. Gyaɗa kai benazir tayi"its Okey, babyn shureim, Naji nayi shiru bazan ƙara magana ba, hakan yayi maki" Tana faman zumbura baki tace Eh, dariya Benazir tayi da zolaya take fadin"lallai ya shureim yayi kasuwa, Irin wannan So haka? Ta fada tare da samun wuri gefen gadon zeenatu ta zauna. "Ina wayarki take"? "Nabarta A cikin wandon jean dina dana cire, Bari na dauko maki" da sauri ta juya ta nufi inda ta rataya kayan. Sai gata ta dawo hannunta ruƙe da wayar ta miƙa ma Benazir, bayan ta kar6a, zeenatu ta zauna agefenta. Screen din wayar ta ƙurama ido hoton Fatiman shureim ne, nan take yanayin fuskarta ya canza, da sauri ta furta"Zeenatu! Meyasa kika daura hoton nan a wallpaper dinki"? "Saboda inason hoton ne, yaya shureim ne ya tura mun hotunanta" Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, aranta ta ayyana bazai yiwu ba, dole in sa zeenatu ta sauke hoton fateema daga wallpaper dinta. "Aunty Benazir, Ɗazu An kirani da wata baƙuwar number lokacin na shiga toilet, bansan wanene ba, har mommy nakaima wayar tace ita batasan ma da layi akan wayarba, Nima kuma bansan da layin ba" Cikin kulawa Benazir tace"waye ya siya maki wayar ne"? "Daddy ne Ya siya min, amma bani yaba ma ita ba, saboda bayason ina yawan amfani da waya zata Iya ɗauke min hankali daga yin ibada, shine yaba mommy wayar, ita kuma ta ajiye min ita, dama ni ban damu da ita ba, sai da naga hotunan fatiman ya shureim awayarsa shine naje nace ma mommy ta bani wayata zan yi amfani da ita" tunda tafara yin maganar Benazir bata kau da ido daga kallon ta ba, tayi mamakin da har shureim ya iya faɗama Zeenatu sirrin shi, hakan ya ƙara tabbatar mata da irin Ƙaunar da yake yima zeenatu. A hankali ta kau da idanunta daga kan Zeenatu, ta ɗaurasu kan screen din wayar, Call logs ta shiga, nan take tayi tozali da bakuwar number da aka kira zeenatu da ita kusan 2 missed calls, Aranta ta ayyana Uncle musa ne ya siya mata layin awaya ko kuwa tare da sim din aka siya mata wayar? Tayaya ma haka zata yiwu? Idan shine ya sanya mata sim din meyasa bai sanarma mom sarah ko ita zeenatun da akwai sim a wayar ba? Sannan babu yadda za'ai companyn da aka sayi waya su bada ita tare da sim" Zeenatu dake kallonta ganin ta ƙurama screen din ido babu alamun zatayi magana ne yasa tace"ko dai in kaima daddy wayar ya duba min mommy ma tace idan ta shigo gidan zata bibiyi layin"! "A'a zeenatu, Kada ki kai mashi wayar, nafi tunanin shine ya sanya maki sim din aciki ba tare dasanin ki ba may be ya manta bai faɗa maki ba, sannan layin da aka kira ki da shi ina da tabbacin wrong number ne suka kira" "Nima raina ya bani hakan, to ki goge min layin daga kan wayata" Benazir tace"A'a, kada mu yi saurin goge number, Mu jaraba kira don mu faɗa ma mai layin wrong number ne ya kira, Kinga ta hakanne zai iya gyara number din ya kira wanda yake son yin magana da shi" Jinjina kai zeenatu tayi alamar gamsuwa da bayaninta. "Yaushe zamu kira su"? "Yanzu zan jaraba" Danna kira Benazir tayi, duk sun ƙagara da son jin me layin ya ɗaga sai dai kash Kiran yaƙi shiga" "Ki bar min wayar a hannuna, tunda ba amfani kikeyi da ita ba, Zuwa anjima zan jaraba kiran layin" Amsa mata tayi da toh "Amma idan mommy ta tambayeni ina wayar ya zan fada mata"? "Sai kice mata ni na kar6a, ina wani amfani ne da ita" amsa mata tayi da toh. "Namanta wayata a hannun mutumin da na zauna awurinshi can ƙasar Canada" benazir ce tayi maganar Zeenatu tace"aunty dama a canada kika zauna? Ya sunan mutumin da kika zauna a wurin shi"? Shiru ta yi tamkar bazata tanka mata ba tace"hakane a canada na zauna, mutumin daya ruƙe ni sunan shi Zaki Mubarak Obinna, ɗan gidan chief of army staff bansan ko kin san shi ba" Murmushi zeenatu tayi tare da cewa"nasan ƴan family din obinna sosai, tun kafin in mallaki hankali na muna yawan zuwa estate dinsu nida mommy na, da yake suna mutunci da Hajiya saratu daga bayane daddy ya hanata zuwa Yawo dani, tun da na kammala secondry school Ya garƙameni agida, bai bari tana fita dani, har sai da Ya shureim Ya dawo da zama gidanmu sannan Ya kyaleni ina fita tare da shi. Murmushi benazir tayi"Allah sarki, kada ki damu ai yanzu tunda ina nan zamu dinga zuwa yawo sosai, Harma estate din nasu zamu Iya zuwa duk da bansan su ba amma indai na tuntu6i zaki mukayi magana da shi nasan zai gayyace ni zuwa gidansu, ya jima yana da burin inje gidansu saboda ya nuna ma Iyayen shi ni, Amma naƙi amince mashi saboda bana son zuwa nigeria a lokacin" "Idan ma zaki gidansu ƙawarki Aneeleeh dan Allah ki tafi dani, nima inason zuwa, Naji kuna magana da su mom layla akan zaku je gidan" "In sha Allah, atare zamu tafi," taji dadin maganar Benazir fatan ta Allah yasa ta samu ƙawaye agidan kawar Benazir, tana da burin ganin ta tara friends sai dai daddynta Ya hanata Yin kawaye, baison kowa ya rabeta. *❤EX-PRISONERS🌹* Shigowa ɗakin Naufal Yayi, fuskar shi babu walwala, shima babu suturar a jikinshi sai gajeran wando, sumar kanshi duk ta yamutse har saman wuyan shi, Kunsan atare Unaisah Da Sajeed suka juyo suna kallon shi Harara ya watsa ma sajeed tare da cewa"Ɗan rainin wayau, ashe nan ka shigo, kasa inata nemanka, Hankalina Yaƙi kwanciya ganin Halin da ka farka daga bacci" Murmushi Sajeed Ya sakar mashi, tare da saukowa daga saman gadon unaisah bayan ya miƙa mata wayarta ya nufi Naufal Ya rungumo shi Yana fadin"Sorry My baby Boy, Na tayar maka da hankali, ashe ka damu dani har haka? Halan ma kuka kayi saboda rashin ganina da baka yi ba" ya fada da zolaya yana shafa mashi fuskarshi. Tsoki Naufal Yaja ba tare daya tanka mashi ba Ya dubi Unaisah "Sister barka sannunki" Murmushi tayi dimple dinta biyu suka lotsa "Yawwa rabin raina, halan Sajeed ne Ya 6ata maka rai"? Yamutsa fuska yayi kafin yace"eh mana, kawai Ina kwance Ina bacci na jiyo shessheƙar kukan shi ya cika min kunne na, ba arziƙi na farka Hankali atashe na tada shi daga bacci ina tambayarshi lafiya yake kuka, Bai tanka min ba kamar wani shashasha haka yabarni ya fito daga dakin, Ina ta neman shi ashe nan ya shigo" Ya faɗa yana jifar Sajeed da harara"don yaga na damu da shi ne, Allah nan gaba idan Ya ƙara yi min haka, Bulala zan sanya mashi" Dariya su ka yi gaba ɗayansu, Sajeed yace"na fi ƙarfinka Naufal, mai buguna sai ruwan sama da rana," ya fada yana nuna mashi faffadan kirjinshi da damtsen hannunshi. Nannaɗe hannun riga Naufal yayi yana fadin"ba kai kaɗai Allah Yaba kirar karfin ba, Nima ina da ita, babu abunda zaka nuna min in banda girman jiki" Unaisah dake kallonsu kamar ta samu tv, Wayarta dake a hannunta ta danna ta shiga Camera, Ta saita su tana ɗaukarsu Video batare da sanin su ba, saboda sunyi mata kyau, sai taji inama ace hada Danish dinta da kuwa shi zai kar6i kambun faɗan nasu, domin kuwa Danish Yafi su tsayi da kuma kyawun Sura duk da suma ɗin ba daga baya ba musamman Gabriel Namiji ne. A yayin da take ɗaukarsu video, bakomai take tunawa ba face garkuwarsu, lokacin da ta risƙe shi a ɗakin Gidan kurkukun ƙaddara Kwance Yana bacci da red shirt a jikin shi, yayi mata kyau fiye da tunanin mai tunani, duk da a lokacin a matsayin giant yake saima ya ƙara yi mata kyau, tana matuƙar ƙaunar komai nashi ta ƙosa ya dawo normal mutun kodan suci gaba da bama junansu kulawa. Tayi zurfi acikin tunaninta, Shessheƙar kukan Azeeza Ya fargar da ita, da sauri ta janye wayar daga saitin fuskarta, su Sajeed dake atsaye suna kokoyi shida Naufal jin kukun Azeeza ne Yasa suka dakata kusan atare suka kalli ƙofar shigowa dakin. Kamar Mahaukaciya Haka ta shigo sanye da ƴar gown wadda bata rufe gwiwar ƙafarta ba, fuskarta sharkaf da hawaye tayi jawur da ita, rigar jikinta ta jiƙe da ruwa daga bayanta Jamimah ce atsaye ta ruƙe rugu tana faman sakin murmushin mugunta. da sauri Unaisah ta sauko daga saman gason, ta nufi Azeeza ta ruƙo hannunta tare da rungumeta tana tambayar ta lafiya take kuka Muryarta da shessheƙar kuka tace"jamimah ce ina bacci ta watsa min ruwa ajikina, shine wai take cewa nayi fitsarin kwance bayan itane ta kwarara mun ruwa a kasan rigata.... " tunkafin Azeeza ta ƙarasa maganar, Jemimah tayi saurin cewa"wallahi ƙarya take yi min, Fitsarin kwance ne tayi mana a ɗakin mu, Ni bani na zuba mata ruwa ba" Ta faɗa tana faman gumtse dariya. Cikin muryar Raɗa Naufal Yace da Sajeed"babynka tayi fitsarin kwance, Yakamata kaje ka wanke mata" harara Sajeed Ya watsa mashi tare da ingije shi, Ya nufi Jemimah, ganin Yana tunkarota Yasa ta juya da niyar ta gudu sai dai kafin ta fuce daga ɗakin, Yayi hanzarin cafkota da hannu biyu ya ɗaga ta sama yana fadin"Mugunta ko? Ai ba ke kaɗai kika iyaba kowa ma Ya iya ta, rasa kunya 6eran tanka, da wasu kunnuwanki kamar na zomanya, Jibi kumatunki duk kin shanye ma mutane madara da bonbita, Yau zanyi maganinki" Ya fada tare da Juyawa ya nufi Toilet da ita, Kuka tadinga yi mashi tana kokarin kwacewa, da gudu naufal yabi bayan shi yana fadin"please bro, Ka kyaleta yarinya ce bata da wayau" ko sauraron shi baiyi ba yaja kofa Ya datse. Azeeza dake kwance Jikin Unaisah sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi, Taji daɗi Sajeed zai rama mata abunda Jemimah tayi mata, ba tun yau ba kusan kullum sai jamimah tayi mata mugunta don taga suna kwana a ɗaki ɗaya. "Ki yi haƙuri da sister dinki, nasan halinta bata jin magana, Kunnan ƙashi ne da ita, amma please ki daina bari tana ganin kukanki, shiyasa take ƙara rainaki saboda tasaba sanyaki kuka... " Cikin sanyin murya Azeeza tace"Toh, amma kiyi mata magana tadaina jana fada, har fadi takeyi wai ni ban isa da ita Ba, maganarki kaɗai take Ji" Murmushi unaisah tayi"zan yi mata magana idan ma bata daina ba zamu fara koya mata hankali ne" Fitowa Sajeed Yayi daga cikin toilet Yana faman sauke ajiyar zuciya, fuskarshi ɗauke da murmushin mugunta. Naufal dake kallonshi yace"Mugu Ina ka baro mana jamimah"? Harararshi yayi" ka shiga ka ɗaukota, wata'ƙil ƙafafuwanta baza su iya daukarta ba shiyasa ta kasa fitowa" Ya faɗa tare da wucewa Ya nufi Azeeza, Ruƙo hannunta yayi Acikin nashi ya rabata daga jikin Unaisah Ya zauna daga gefen gadon Yana fadin"Har nagaji da yi maki magana akan ki daina bari Waccan Ƙaramar halittar tana sanyaki kuka, serious idan baki daina ba zamu 6ata" ya faɗa yana daure mata fuska. Muryarta ƙasa ƙasa tace"zan daina" Harara ya watsa mata"haka kullim kike fadamin, last warning zan baki daga yau idan na ƙara ganin hawaye akan fuskarki da sunan jamimah ne tasa ki kuka Jikin kine zai gaya maki" yai maganar tare da kama kunnanta yace"Idan kunne Yaji"? da sauri tace mashi Jiki Ya tsira" Dariya ce ta kubce ma unaisah da naufal, shima sajeed din dariyarce tazo mashi sai dai Yaƙi barin ta kubce mashi don baison raini ya fara shiga tsakanin shi da Azeezarsa, Yafi son tana jin shakkarshi. "Jemimah!" Jamimah ta"! Naufal Ne ya kira sunanta, Shiru taki ta amsa mashi, Sajeed Yace"zuciyar ce ta motsa, tana jin ka ƴar rainin wayau" Miƙewa unaisah tayi da sauri ta nufi toilet din, tana shiga ta taras da jemimah zaune cikin kwamin wanka da sajeed Ya cika da ruwan mai uban yawa, Rigar jikinta duk ta manne ma fatarta, ta ɗaure fuska sai shessheƙar kuka take Yi kamar zata haɗiyi zuciya tsabar 6acin rai. Ganin Unaisah yasa ta fashe da kuka rai a6ace ta dinga bugun ruwan da hannayenta tana fadin"wayyo Allahna Anci mutuncina, Zuciyata tafarfasa take Yi min, Genie kinga abunda Sajeed Yayi min ko? Kina gani baki hana shi ba, Saboda rashin mutunci ya jefa ni acikin ruwa" Hatta su Sajeed dake adakin saida suka jiyo maganganun da Jemimah takeyi a toilet, gaba ɗayansu suka sanya dariya hada Azeeza. "Am sorry My Little sister, Sajeed bai kyau ta miki ba, Amma kiyi hakuri dan Allah" unaisah ce ta fada Cikin lallashi da lallami Ta nufi jemimah, ta sanya hannu ta ɗaukota daga cikin ruwan, "Kinyi wanka"? Idanunta na fitar da hawaye tace"a'a ni ban yi ba" "Okey, Bari nayi maki wanka, Sai in ɗauko maki wasu kayan ki canza" Ta fada tare da cire mata rigar, shaf shaf tayi mata wanka ta daure mata jikinta da towel, Asaman bayanta ta goyo jemimah, suka fito daga toilet din, sai faman zumbura baki take Yi, Hada jifarsu Sajeed da harara. "Azeeza mu tafi dakinku, Inaso Ku shirya in yi mana hotuna da wayata" amsa mata tayi da toh, Sajeed yace"Mu ma bari muje mu shirya ayi mana hotunan, Ko mun samu na ajiyewa saboda tarihi" Yayi maganar tare da miƙewa Ya dafa kafaɗar Naufal, suka fuce daga dakin. *❤BATOOL🌹* Kusan mintuna da tafiyar Unaisah, Chief Ya shigo dakin sanye cikin shiga ta white thobe launin Sky blue, tabi shape din jikin shi, Hannun shi ɗaya ruke da wayar shi, Ya karata a kunnanshi ga dukkan alamu waya yake yi. "Yanzu na shigo gidan, In sha Allah Uncle Idan na shiga bedroom dinsa zan kira ka video call kaga fuskarshi, nasan hakan zai kwantar maka da hankalin ka" On the other hand, Prime minister yace"nagode my Son, bansan meyasa nakasa cire shi arai na ba, Na ƙwallafa rai akan shi" "Kada ka damu uncle, Nafi so ka kwantar da hankalin ka, baifi awanni daka dawo daga tafiya ba, nasan kana bukatar hutu, Idan rabon ka ne shi watarana zaku gana" "Ina fatan hakan, nagode da kulawarka, sai naji ka". "Okey" ya ambaci hakan tare da zame wayar daga kan ear dinsa. Yayin da yake tafiya A hankali yake bin ko'ina na room din shi da kallo, Kafin Ya sauke idon shi akan Glass table din dake dauke da breakfast dinsa. Ƙarasa shiga ciki Yayi, batare da 6ata lokaci ba, Ya zame jallabiyar jikin shi, Daga shi sai short Ya nufi toilet Ya shiga domin yin wanka. After 15 mins Ya fito Waist dinsa daure da white towel, a gaban dressing mirror ya tsaya da niyar ya gyara jikin shi, kwatsam A lokacin da baiyi tsammani ba kunnuwansa suka jiyo mashi sautin motsin mutun a bedroom dinsa. A hanzarce ya ɗaura idanunsa kan madubin, ta ciki ya hangota ta fito daga hanyar zuwa Gym Room dinsa kamar Aljanna, Hannunta ɗaya ruƙe da mayafinta, Ga wannan Uban gashin kan nata data ta saki saman bayanta yayi mata tamkar hijabi, Lamarin ya ɗaure mashi kai ganin matashiyar mace a ɗakin kwanansa, Wacece ita? Tayaya akai ta shigo mashi bedroom din sa? Da iznin wa"? Acikin zuciyarsa ya furta hakan ba tare daya kau da ido daga kallon ta ba, ƙarfin halin ta yayi matuƙar bashi mamaki, tsawon lokacin daya shigo dakin har ya shiga bathroom yayi wanka duk tana a ciki ko me take yi!? Gaba ɗaya Hankalinta ba akanshi yake ba, batasan ma da zaman shi a dakin ba, har ta ƙaraso tsakiyar dakin bata lura da chief Owais ba, idanunta ba su hango mata shi ba, Sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi kamar wadda tasha gudu. Ganin bata da alamun motsawa tabar mashi room dinsa ne yasa shi juyowa A hankali Ya nufe ta, sam bata ji motsin takun shi ba, saboda Ta juya mashi baya sai ƴan waige waige take Yi, duk kallon da tayima dakin nashi bai isheta ba. A lokacin da batayi tsammani ba, Taji saukar hannun mutun saman sumar kanta, Kafin tayi wani yunƙuri Ya damƙi gashinta, wata irin firgita Batool tayi, A gigice Ta fasa ƙara Sautin Ya cika kunnuwanshi dasauri ya sakar mata gashi, hakan ya bata damar juyowa don ganin wanene. Wani irin bugu zuciyarta tayi lokacin da idanunta suka sauka akan faffaɗan ƙirjinshi, da waɗannan Strong arms din nashi, ta zazzaro mashi ido waje la66anta na kerma take ambaton"INNAHU MIN SULAIMAN WAINNAHU BISMILLAH" adabarbarce ta furta hakan, kamar wadda taga wani mugun abu, Kallo ɗaya da tayi ma fuskarshi har suka haɗa ido ba ƙaramin gigitar da ita yayi ba, duk tabi ta ruɗe, Mayafin hannunta tuni ya jima da zamewa saman floor, juyawa tayi da gudu tana neman hanyar fita daga dakin sai dai takasa gane ta ina ƙofar da suka shigo take, sai faman bin bango take yi, Jikinta ya hau yin kerma kamar wadda Sanyi ya kama. Chief dake atsaye yana dubanta, Kallon mahaukaciya Yake Yi mata saboda kalmar data furta mashi da kuma firgitar da tayi kamar taga wani mugun abu, Ya rasa gane me ya ruɗar da itane, ta6e la66ansa yayi kafin Ya juya ya nufi cikin ɗakin, Batool dake ta neman kofar fita, tuni zufa ta jiƙeta yadda kasan babu A.c a dakin, Mugun tsoron shine Ya kamata hada ƙarin babu sutura a jikin shi shiyasa ta rikice da ganin al'amurransa, towel din daya ɗaure waist da shi ko gwiwarshi bai rufe ba. Jin takun tafiyar Shi abayantane Yasa ta ƙara ruɗewa, A gigice Ta juyo tana duban shi, sumar kanta ta rufe mata gefe da gefen fuskarta, har Ya sanya Short a jikin shi tare da singlet fara ƙal. Fashe mashi tayi da kuka tana fadin"nashiga uku, dan Allah ka buɗe mun ƙofa in tafi ɗakin mu, wallahi ni ba 6arawo bane, bada niyar wani abu na shigo maka ɗakinka ba. Fuskarta sharkaf da hawaye tayi maganar tana faman jan majina. Bai tanka mata ba, yama rasa bakin magana, mamakin ta ya gama kama shi, sai yanzu ya gane fuskarta a cikin Yaran da suke kula da su. Gently Ya juya Ya nufi gaban side drawer din shi, ya buɗe Ya dauko jotter da pen asaman drawer din Ya ɗaura jotter, rubutu yayi mata bayan ya kammala ya cire paper din ya tunkari Batool Ya miƙa mata takardar, gabanta na faduwa ta sanya hannunta dake kerma ta kar6a tana kallon abun da ya rubuta mata. Muryarta da shessheƙar kuka Ta furta"ai..ai.. Ni Ban Iya karatu ba, sai dai in kaima Unaisah ta karanta min" Wannan maganar da ta furta mashi ta ta6a zuciyar shi, har sai da ya ɗaura reddish eyes dinsa akan soft brownish lips ɗinta da suka jike da ruwan hawayen ta, ga wani uban gumi da ta haɗa a jikin ta, shi abun da ya ɗaure mashi kai ruɗewar da tayi kamar taga wani mugun abu, ita kanta Batool din tunfarko taso idan suka haɗu ta natsu ta yi mashi bayanin abunda ya kawota dakinsa, sai dai dalilin shaƙar da yayi ma sumar kanta ne, Yasa ta firgice mashi ta kuma fahimci bai san da maganar zuwan ta ɗakin shi yi mashi aiki ba!. Taƙi Yarda ta ɗago su haɗa ido saboda ƙwarjinin da yayi mata, gani take yi kamar zai rufeta da bugune yadda yayi mata rumfa da kirjinsa. "Dan Allah ka buɗe min ƙofa in tafi daki, zan kai mata ta karanta min" ba tare daya furta mata komai ba, Ya dafe Glass door din dakin nan take ƙofar ta soma zugewa a hankali, Jikinta har rawa yake Yi wurin yin saurin fucewa daga dakin kamar za tayi tuntu6e. Ta tafi tabar mashi Mayafinta akan floor, komawa yayi gefen gadonshi Ya zauna da sanyin jiki, wata irin yunwa ce ke addabar shi, bazai juri jiran wani yayi serving na shi ba, Da kanshi Yayi serving abunda zaici, Kakkauran tea ya zuba a cup Ya soma kur6an shi atsanake, Yayin da brain dinshi ke tariyo mashi kalaman Batool Ai ni ban Iya karatu ba, zan kaima unaisah ta karanta min, Abun Ya tsaya mashi aranshi, Duk da bai kalleta dakyau ba, zai Iya bata shekaru goma sha bakwai zuwa sha takwas, a wannan shekarun bata Iya karatu ba? Bai yi tsammanin abun yakai haka ba. Bayan fitar batool daga dakin chief, nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, tana tafiya idanunta akan paper ɗin daya bata, Har ta sauko down ta nufi dakin su. Lokacin da ta shiga bata taras da kowa ba, yanke shawarar shiga toilet tayi don ta wanko fuskarta, asaman gadon su ta ɗaura paper din, da sauri ta shiga toilet ta wanke fuskarta, fitowa tayi tareda nufar gado nasu, isarta keda wuya ƙafarta dake sanye cikin wandon pakistan ta harba hotunan da suke yashe kan floor ba tare data lura da su ba, nan take hotunan suka gangara ƙarƙashin gadon suka shiga ta yadda babu mai iya ganin su. Miƙa hannu Batool tayi ta ɗauki Paper din Ta juya da sauri ta fito daga dakin tana neman su Unaisah. Sautin Muryoyin su Tajiyo A falo suna surutu cikin takun sauri ta nufe su, tun kafin ta ƙarasa ta hango su tsaitsaye sun yima Unaisah rumfa hannunta ruƙe da waya tana yi masu hotuna, tun daga kan Haris, Naufal, Javed, Sajeed, da su Azeeza jamimah, parveen and Hannah kowannansu ya sanya sutura mai kyau ajikin shi, Unaisah ce tasa suka ɗauki wanka, don tayi masu hoto. Babu wanda Ya lura da Batool acikin su, Camera taja hankulansu, har saida Ta furta Sunan Unaisah tukunna suka ɗago da idanunsu akanta. Kallo ɗaya da Unaisah tayi mata saida taji gabanta ya fadi ganin yadda kumatunta suka yi ja alamar tayi kuka Gaba ɗaya sun lura da yanayin Batool babu walwala, Ruƙo hannunta Haris yai acikin nashi"Sister baki da lafiya ne"? Shiru tayi batace mashi komai ba, Hankalinta na akan Unaisah "Me akayi maki? Kuka ki ka yi"? parveen ce tayi mata tambayar, girgiza mata kai tayi alamar a'a. hannah ta ruƙo hannunta tana fadin"Sis Batul ki zo ay mana hoto atare dake" Fahimtar halin da take aciki ne Yasa Unaisah miƙa ma Sajeed wayar hannunta, bayan ya kar6a tace"ka cigaba da yi maku hotunan, yanzu zan dawo" Ta faɗa tare da ruƙe hannun batool, suka juya atare suka nufi ƙarshen falon inda babu mai jin su Shafa gefen fuskarta tayi da hannu tana fadin"meya faru? Chief ɗin Ya dawo"? Batare da batool ta furta kalma ba ta miƙa mata Paper din hannunta da sauri Unaisah ta sanya hannu ta kar6a, A fili ta karanta. "How did you get into my room? And why are you crying at me like I'm a monster? nayi maki wani abu ne"? Murmushin gefen fuska unaisah tayi"meyasa ki kuka? Faɗamin? Tana faman jan numfashi tace"tsoro ya bani, ya damƙi gashin kaina da hannun shi kuma babu kaya a jikinshi, short towel ya ɗaure a qugunsa.... " tun kafin ta ƙare maganar Unaisah ta tuntsire da dariya Batool dake kallonta ganin tana yi mata dariyane yasa ta ji jikinta yayi sanyi laƙwas, in cool voice tace"Nayi ƙauyanci"? tambayar da tasaba yi mata kenan a duk lokacin da take tunanin ta aikata ba dai dai Dafa kafaɗarta Unaisah tayi fuskarta da murmushi tace"My own sis ba ki yi ƙauyanci ba, "To meyasa kike min dariya"? "Saboda kin bani dariya, meye nayi mashi kuka? Ba bugu ba zagi kin fashe da kuka kamar wata ƙaramar yarinya ni danake so ki zama big girl, matar manya. "Ni dai bazan ƙara komawa ɗakinsa ba, Tsoronsa nake ji sai dai ke ki je" ta faɗa tana nuna ta da hannu. Maƙe kafaɗa Unaisah tayi"Batool ki fahimta ni bazan iya shiga dakin sa ba, bayason ana sharing aiki a part dinsa, idan mutun ɗaya ya fara shi zai cigaba da yi har sai in shi yace ya gaji baya so, nima big guy ne ya gaya min hakan. Fuskarta ayamutse ta ƙare maganar tana dubanta, itama batool din kallon ta take yi, taƙi gane cewa wayau Unaisah take yi mata. "Ya zanyi? Ni wallahi tsoron shi nake ji, baki ga launin idanuwanshi ba kalar na danish ɗinmu, kuma ma suna kama sosai don dai shi launin fatarshi chocolate ne" ta fahimci Batool ta tsorata da chief, idan tana magana yatsun hannunta har kerma su ke Yi. "A hankali zaki saba da shi, dan Allah ki daure Sister, za ki ji dadin yi mashi aiki" da wayau da dabara Unaisah ta shawo kanta, har ta amince zata cigaba da zuwa. "Yanzu idan kika koma ki fada mashi cewa, Big guy ne ya baki aikin kula da part dinsa, ke zaki cigaba da daukar ɗawainiyarsa kina gyara mashi daki da kuma kai mashi abinci, haka zaki faɗa mashi," Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"amma ba yanzu zan koma ba ko"? "Idan baki koma ba kayan abincin da kika bar mashi a ɗaki wazai kwashe su? Na fada maki bayason kazanta, sannan bai saba da wahala ba komai yi mashi akeyi" tana ƙarasa fadan hakan Taja hannun Batool suka nufi Hanyar zuwa Part dinsa, A bakin ƙofar shiga unaisah ta saki hannunta. Jiki na rawa Batool ta sanya hannu ta kwankwasa ƙofar, A hankali Ta zuge, saida ta fara dadaita natsuwarta tukunna ta yi mashi sallama, shiru bai amsa mata ba, a tsananin tsoro ce ta zura kafarta, a lokacin Harya kammala Yin breakfast dinsa, yana daga kwance saman lallausar mattress dinsa, Ya ɗaura kanshi bisa pillow, Yayin da idanunsa ke akan Laptop dinsa da yake operating Yawu ta haɗiya Muryarta na rawa ta furta"am.. dama Big guy ne yace in dinga zuwa inayi maka aiki a part dinka, kuka kuma da nayi kaine ka bani tsoro daka kama min gashin kaina" Dakyar ta ƙare maganar, batare da ta motsa daga bakin ƙofar ɗakin ba, tamkar baisan tanayi ba, yayi shiru yana sauraronta, babu alamun zai kalleta Jin shiru bai tanka mata ba, yasa ta yanke shawarar shiga dakin donta kawar mashi da kayan abincin da ya gama amfani da su. Cikin sanɗa take yin tafiya kamar 6arauniya, duk a tunaninta bacci yake yi saboda idanunsa dake a lumshe batasan cewa idonshi biyu ba kuma yana kallonta, yayi mata hakanne saboda baison Ya ƙara firgitar da ita, tunda ya fahimci ruɗaɗɗiyace ita. Tana ƙarasawa gaban table din tayi saurin kwashe kayan abincin, sam bata yi tunanin ɗaukar mayafinta data gani akan pillow ba saboda saurin da take Yi, bayan ta fita abakin bene ta tarass da unaisah tana jiranta. Murmushi ta saki tare da nufarta tana fadin"Sister, nayi mashi bayani amma kamar bacci ma yake yi, ga tray din abincin na dauko Ina zamu kai shi"? "Nikaina bansan ina ne kitchen dinsu ba," unaisah ta fada tare da kar6ar tray din"bari naje na nemo kitchen din, Ki tafi falo," amsa mata tayi da toh, da sauri Batool ta sauka daga kan benan ta nufi falo. Unaisah tana cikin tafiya, Tajiyo motsin buɗe kofar Falon, su biyu suka shigo Boss man tare da Big guy, wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta, Allah Ya taimaketa, Ta kar6i tray din daga hannun Batul da kuwa Big guy saiya gane ba ita taje yima chief aiki ba. Tunkararsu tayi fuskarta dauke da fara'a tace"Yalla6ai nagama yi mashi aikin, A ina zan ajiye tray din" Big guy yaji dadin Jin hakan daga gareta, alamar jinjina yayi mata da yatsan hannun shi kafin Yace"ai tunda naga kina yin fara'a raina ya bani cewar Kin samu kar6uwa awurin chief, bani labari daya ganki meya ce maki"? boss man dake sauraronsu murmushi ne dauke akan fuskarshi dake asanye da facemask. "Bayan na gaishe dashi Ya amsa min, sai nace mashi me yakeson ci in zuba mashi, to daya fada min saina zuba mashi na tsaya har ya cinye na ƙara mashi wani, kusan fa plate uku ya cinye ya kuma sha Tea" da mamaki Big guy ya maimaita kalmar plate uku! "Kina nufin chief shi yaci abinci har plate uku"? Ɗaga mashi kai tayi alamar Eh, saboda karfin hali irin nata ko tsoron yace zai buɗe warmer din batayi ba Boss man yace"wow, My daughter kin ciri tuta, ai ni tunda nake da chief bai ta6a yarda wata mace tayi mashi aiki a part dinsa ba saboda bayaso" Sai faman washe masu baki take Yi, "Ga tray din abincin, Yanzu saura aikin kai mashi lunch ko"? Ta tambaya tana kallon big guy Boss man yace"a'a, Sai kuma dinner, idan yakai Rana bai ci breakfast dinsa da wuriba to baya cin lunch na safen daya ci ya ishe shi sai kuma Dinner dinsa. Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta"Allah Yakaimu daren Lafiya" suka amsa mata da ameen, daga bisani big guy Ya kar6i tray din hannunta Yace tabiyo bayanshi zai nuna mata kitchen dinsu. Atare suka tafi shi kuma boss Ya wuce dakin chief, Bayan Ya bashi iznin shiga, Yana zura kafarshi karaf idanunsa suka sauka aka Mayafin dake yashe kan pillow, farat ɗaya ranshi ya bashi cewar Na unaisah ne da ta shigo kawo mashi abincin, zuciyarshi ta musa da cewar ba mayafinta bane, saboda ita yaganta da mayafi tayi rolling,! Kenan na wanene wannan"! A hankali Yakai hannu Ya ruƙo mayafin Yana dubanshi Kafin Ya kalli chief dake a kwance Ya lumshe idanunsa "Yalla6ai barka da hutawa" In a calm voice Ya amsa mashi yawwa "Naga missed call dinka awayata ina fata lafiya"? "Alright. I'm just reminding you about the plan we have for Hateem's farewell dinner tomorrow. Murmushi Boss man Ya saki"Ina sane da komai Yalla6ai, Kuma in sha Allah babu wanda zaisan da zancen zuwanmu tare da Yaran, ba zata zamuyi masu, Sai dai yalla6ai naso ace hada Danish zamuje, ko dan saboda Prime minister Hateem, Ina so su gana da junansu, har magana nayi ma sheikh imam akan ko zamu iya kaishi asibiti aduba lafiyarshi sai yace min babu abunda likitoci zasu Iya yi mashi a halin da yake aciki" cikin sanyin murya ya kare maganar A hankali chief Yaɗan ware idanunsa tare da cewa"nima nayi fatan hakan sai dai har yanzu babu wani cigaba a lafiyarshi, Allah Ya bashi lafiya" Boss ya amsa mashi da amen, kafin Ya fuce daga dakin hannun shi ruƙe da mayafin daya tsinta. ..shigar shi falo keda wuya, Idanunsa suka sauka akan Batool, dake sanye da Pakistan launin Mayafin hannun shi, girgiza kai yayi don ya riga da ya gane itace taje dakin Chief Yi mashi aiki ba Unaisah ba, baiyi mamakin hakan ba saboda Ya riga daya san halin kayansa, idan bata son yin abu babu wanda Ya isa ya tursasa mata akan tayi shi, shiyasa da big guy ya bata aikin kula da part din chief sai ta tura Batool don tayi a matsayin itane taje, dole ya ɗauki matakin akan hakan don bayason ya samu tangarɗa akan alƙawarin daya daukarwa kanshi. Batare da Batool Ta luraba, Ya daura mata mayafinta saman kanta, Kafin Ya nufi su sajeed dake ta faman daukar hotuna Daya bayan ɗaya ya rungume su sai dadi suke Ji yazo, Nan fa suka fara daukar hoto tare da shi. *🌹ANEELARH❤* A kwance take saman gado tana sharar baccinta, tun da ta sallami baby junaid ya tafi school ta koma kan gado ta kwanta bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, Can cikin baccinta ta soma jin ana ƙwanƙwasa ƙofar dakinta, da wata irin kasala ta farka tana yin miƙa, doguwar rigar jikinta duk ta yamutse, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi ƙofar tana tanbayar wanene Daga waje muryar Ana ta amsa mata da cewa"Aunty ni ce" Buɗe ƙofar tayi tare da bata iznin shigowa daga ciki. A hankali ta zuro kafarta Jikinta sam babu kuzari ta rame tayi duhu, v-neck shirt da pencil skirt ne ajikinta black and white, ta daure guntun gashin kanta da ribbom. "Aunty barka da safiya, Ina fata ban takura maki ba, Na katse maki baccin ki" ta fada tana faman duƙar da kanta ƙasa "Babu komai, Ina fata dai lafiya kike ko"? Cikin kulawa tayi maganar "Lafiylou, dama nazo ne in ƙara yi maki godiya...." kafin ta ƙare maganar Aneelerh ta ɗaure mata fuska tare da cewa"Ana bana son abunda kikeyi min, na fada maki bana son godiyar da kike yi min amma kinƙi ki daina, " Cikin sanyin Murya tace"kiyi hakuri Aunty idan na 6ata maki rai," dakyar ta ƙare maganar saboda kukan daya ciyota nan take ta fashe mata da kuka..... Lamarin ya ɗaurema Aneelerh kai Daga maganar batason godiya sai kuka? Anya kuwa ba wani abunne na daban ke damun Ana ba? Dafa kafaɗarta tayi da hannu daya"ya Isa haka, bana son kukan nan, Idan wani abu ke damunki dan Allah ki fadamin kada ki ji komai, In sha Allah zan yi ƙoƙarin ganin na taimaka maki mun magance koma menene". Yayin da Ana ke kallonta idanunta sun kaɗa jawur, fuskarta ta jiƙe sharkaf da hawaye, Muryarta na rawa ta furta"Aunty Aneelerh bakomai" Girgiza kai Aneelerh tayi"wallahi ban yarda dake ba Ana! Nifa ba haihuwar yau bace, Duk wanda Ya kalleki sai ya gane baki da koshin lafiya, kuma da akwai wani abu dake damunki, Don haka ki fada min kawai! Rashin. fadamin shi zaija maki yin danasani"! Su6ul da baka tayi wurin furta"kona faɗima babu wanda zai yarda dani, zai yi wuya afahimce ni"!! Rass Aneelerh taji gabanta ya fadi, muryarta da alamun ruɗu ta furta"Meke nan"? A firgice ta zare ido tare da yin saurin cewa"babu komai, babu komai! Na tafi sai anjima" juyawa tayi da sauri ta nufi ƙofar dakin zata fuce, sai dai kafin ta haura kafarta Aneeleeh tayi saurin ruko hannunta ta juyo da ita suna fuskantar juna Wani irin kallon kallo suke jefa ma juna batare da sanin ma'anar hakan ba "Ana! Ki faɗamin meke damunki? Menene kike son fadamin wanda kike tunanin babu wanda zai yarda dake?dan Allah kada ki 6oye min, idan ma sirri ne nayi maki alƙawarin bazan fada ma kowa ba" Numfashi Ana taja, gaba dayanta a tsoroce take babu kwanciyar hankali atare da ita "Babu komai!Nabar Girkin dana daura a kitchen zanje na duba" tana karasa fadan hakan ta zame hannunta daga ruƙon da Aneelerh tayi mata, da sauri ta fuce daga ɗakin. Bayan fitarta, Hankalin Aneelerh Yaƙi kwanciya, Ta jefata a ruɗani, ga wani bugun zuciya da take ji a kirjinta. kalmar Da ana ta fadi ta tsaya mata aranta, da tace kota fadi babu wanda zai yarda da ita meke nan"?! Tayi zurfi acikin tunaninta Wayarta dake ajiye kan side drawer ta soma ruri, a hanzarce ta juya ta nufi drawer ta dauki wayar, sunan zahra ne ya bayyana akan screen din wayar, Bayan ta ɗaga kiran ta kara a kunne kafin tayi sallama Muryar Zahra ta katse mata hanzarinta "Auntyna ya ki ke ya gida"? "Lafiyalou Sister, Bakya a gidan ne"? "Na tafi wurin aiki, har dakin ki na shigo don inyi maki sallama sai na tarar kina bacci, bana so na takura maki shiyasa ban tada ki ba" Shiru Aneelerh tayi tana sauraronta har ta ƙare maganar babu alamun zata tanka mata, Jin shiru yasa zahra cewa"auntyna kodai baccin bai ishe ki bane? Naji kinyi shiru? Numfasawa tayi tare da samun wuri gefen gado ta zauna tukunna ta samun natsuwar yi mata magana "Ban jima da farkawa ba, Har yanzu kasalar baccin bata sake ni ba, shiyasa zaki ji ni wani iri" "Kiyi wanka zaki ji dadin jikin ki" acewar zahra "Zanyi in sha Allah, yanzu dai fada min meya faru ne kika kirani awaya? Naji muryarki kamar akwai farin ciki atattare dake"? Ta fada tana murmushi tamkar suna atare da juna "Kamar kin sani auntyna, shiyasa nake ƙara ƙaunarki saboda kina fahimtata fiye da kowa, abunda Ya faru Ina awurin aiki, Hajiya sarah ta kirani awaya.... " a ƙagare Aneelerh tace"me tace maki"? "Ta faɗamin suna buƙatar za'ayi masu decoration gobe friday, Za suyi Farewall dinner, Na bankwana da prime minister Hateem, Jibi zai bar ƙasar tare da Iyalansa zasu koma Canada" Wani irin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Aneelerh"Zahra na tayaki murna, Alkhairi ne ke bibiyarki, hajiya sarah bata manta dake ba, Ashe kina aranta" Sautin murya zahra da annushuwa tace"bana tunanin zan iya runtsawa a daren yau, saboda farin cikin zan halarci family dinner dinsu, wallahi aunty naso ace tare dake zamu je amma nasan bamai yiwu bane tunda nima tace daƙyar tayi mana hanyar da zamu samu halartar taron, saboda tsaron da za'a sanyama Estate din a goben" "Kada ki damu zahra, Nima inason zuwa amma koda nasamu damar da zan biki bazan je ba, idan ma kikaje kamar naje ne, bani da damuwa nasan zaki bani labarin komai daya faru a shagalin, Harma Ki dauko min hotuna da videos don inga Ƴan family din Obinna" Zahra tace"in sha Allah auntyna, yanzu zan koma bakin aikina, Sai na dawo gidan ki kula min da kanki," "Nima ki kula min da kanki sai anjima" baya sunyi sallama Aneelerh ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe da sauri ta nufi toilet ta shiga ciki, after some minutes ta fito daga wanka, shaf shaf ta canza suturar jikinta, ta sanya Primcess vest tare da wrap skirt, ta ɗaure kanta da mayafi, da sauri ta fito daga dakin ta nufi bedroom din mami. Tunkafin ta shiga ta soma jiyo muryarta tanayin karatun kur'ani, da sallama ta shiga ciki, a zaune ta taras da mamie saman darduma sanye da hijab, idanunta akan kur'anin da take karantawa, gefen gadonta ta zauna tana jiran ta kai Aya. "Aneelerh kin tashi daga baccin lalacin"? Mami ce ta faɗa tana dubanta Murmushi tayi mata"mami bansan baccin ya ɗauke ni ba," "Na gaji da ganinki zaune a gida, zan tuna ma Abie dinki maganar aikin da Uncle ɗan Iya yace zai sama maki a asibitin Obinna, Indai dagaske yake zai yi maki hanya" "Mami nikaina nagaji da zama babu aikin, Dan Allah ki tuna mashi idan Ya dawo su yi magana asama min aikin in fara zuwa" "In sha Allah zanyi mashi magana, ai nafi son ganin cigaban ki" Murmushi suka sakar ma juna " shiru sukayi kowa da abunda yake saƙawa acikin zuciyarshi. "Dama zuwa kikayi don kiyi ta kallona"? Mami ce tayi maganar fuskarta da murmushi. "Dangane da Ana ne, mami Yarinyar nan akwai abunda ke damunta, taƙi ta sanar dani, ina ɗaki ta shigo daga yi min godiya akan kudin da muka bata ni da zahra, sai nace mata bana so tana min godiya kawai sai ta fashe mini da kuka.... " gaba ɗaya Aneelerh ta sanar da ita abunda Ya faru. Mami ta jinjina kai tana dubanta tace"tuntuni fa na lura da canzawarta, tayi baƙi ta rame kamar bata da koshin lafiyar, har tambayarta nayi meke damunta sai ce min tayi babu komai lafiyarta ƙalau Ni bansan ya zamuyi da ita ba" Mami ce ta fada tana mai nuna damuwarta. "Mami yakamata ki ja ta a jiki kiyi mata magana wata'ƙil ke ta faɗa miki tunda kin haifeta zata ji tamkar mahaifiyarta ce keyi mata magana" Shiru mami tayi na wani lokaci kafin tace"Toh, zan jaraba yi mata magana mu ji meke damunta" "Tana a ina ne yanzu"? "Ta fadamin zata je kitchen duba girkin da ta daura" Mikewa mamie tayi"muje wurinta Inji" da sauri aneelerh ta miƙe ta dauki kur'anin mami da cazbaharta ta ajiye su a ma'ajiyarsu, Kafin Tabi bayan ta suka fito daga dakin, Adai dai Lokacin Ummi ta fito daga daki sanye da dogon Hijab taci karo da su atare Fuskarta da fara'a tace"Uwa da ɗiya ina zuwane haka" "Wurin Ana zamuje, Yarinya duk ta rame tayi baƙi, Taƙi fada ma mutane abundake damunta ko ke baki Lura bane"? Jim ummi tayi kafin tace"kamar kun shiga zuciyata, fitowar nan da nayi dakin ki nake shirin zuwa don inyi maki magana game da ita, na jima da lura da hakan, duk ta canza ba kamar yadda nasanta ba farkon zuwanku gidan nan, Yanzu tayi baki ta rame babu ƙugun nan nata da kirjinta duk sun zube kamar mai fama da wata lalura," Aneelerh tace"abun da yafi ɗaure min kai da ita ummi, kwata kwata bata da natsuwa, ko magana take yi yatsun hannayenta zaki ga suna kerma kamar wadda sanyi ya kama" Ummi tace"Muje muji meke damunta," gaba dayansu suka nufi kitchen din gidan, Koda suka shiga basu ganta ba, Har ta kamma aikace aikacen da take Yi, tayi wanke wanke tayi mopping dinsa. Ummi tace"baiwar Allah gata da ƙoƙarin yin aiki, banji dadin halin da take aciki ba" Fitowa sukayi daga kitchen din suka nufi bedroom din Ana. Abakin Door room din Suka dakata da yin tafiyar, Aneelerh ta kwankwasa mata kofa, kusan sau uku Tana buga kofar kafin suka jiyo motsinta ta cikin dakin, buɗe kofar tayi tare da leƙowa tana kallon su Fuskarta a yamutse, idanunta sun yi jajir da su. Murmushin yaƙe ta ƙaƙalo akan fuskarta, cikin girmamawa ta gaishe dasu tana ƙoƙarin 6oye damuwarta "Wurin ki muka zo mu shiga daga ciki" mami ce tayi maganar, da sauri Ana ta matsa masu hanya suka shiga dakin, Daga tsaye suka tsaya tace mashi su zauna saman gadonta Ummi tace"ba zama ya kawo mu ba, zuwa mukayi don muji meke damunki Ana, meke faruwa dake ne? Duk kin canza mana kin rame kinyi baƙi! Baki da lafiyane"? La66anta na kerma ta furta"babu komai lafiyana lau madam, wallahi babu abun dake damuna" Cikin kwantar da Murya mami tace"Kada ki 6oye mana komai, Ki ɗauke mu tamkar iyayenki, dan Allah ki fada mana damuwarki, In sha Allah zamu share maki hawayenki, Mami na rufe baki Aneelerh tace"Ana please kada ki bani kunya, Saboda mun ɗauke ki da daraja shiyasa muka damu da damuwarki, Kina gani dai mami da ummi da kansu suka zo dakin ki yau duk don saboda sun damu dake, Idan kika ce babu abunda ke damunki, kinyi mana karya saboda babu yadda za'ai ki rame batare da ciwo ko wani abu ba, dole da akwai wani abu da baki son mu sani" Gaba ɗaya sun ɗaga mata Hankalinta, Cikin kwantar da murya suke yi mata magana amma sai ta dinga ganin kamar suna yi mata faɗane, Dafe kanta tayi da hannu biyu tana ambaton sunan Allah tamkar musulma. Muryarta na rawa take fadin"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, na roƙe ku ku ƙyaleni, ku tafi kawai, nagode da kulawarku agare ni,nagode" Hankulansu atashe suke ambaton sunanta haɗi da tambayarta meke damunta. Gaba ɗaya ta rikice masu, sai sambatu takeyi tana rokonsu akan su tafi subar dakinta, a karshe ta watsa da gudu ta shige toilet taja ƙofa ta datse. 😳 Kallon juna suka somayi da tsantsar mamaki da rudani aka fuskokinsu, ..mami tace"to fa, Anya kuwa lafiya"? Ummi tace"bafa lafiya, Ni dai inaga kamar hada aljanu ke damunta. Jikin Aneelerh yayi sanyi, tun datake da ana bata ta6a ɗaga mata murya ba sai yau da ta rikice masu tana korarsu daga dakinta, tabbas babu lafiya! "Yanzu ya zamu yi da ita"? Mami ce tayi maganar, Ummi tace"yakamata mu sanar da su Abie, dangane da halin da take aciki" Sun jima a dakin Ana suna yi mata magiya akan ta fito daga toilet, amma taki fitowa a karshe dole suka hakura suka bar mata dakinta.. *Daular Obie Estate* Gaba ɗaya Manyan matan Family din sun hallara a gidan Hateem domin yi masu bangajiyar tafiyar da su ka yi, musamman saboda zuwansu akayi masu shimfiɗa ta alfarma a katafaren Garden din gidan hateem, garden ne na alfarma cike ya ke da tsiro da furanni launuka daban daban masu ban sha'awa, ga wata irin ni'imtacciyar iska mai ratsa fatar jikin mutun, daga can cikin garden din akwai wani ƙaramin tafki wanda ke acike da tsaftaccen ruwa launin blue sky, inda fararen agwagi suke shawagi acikin sa, an tsara komai da kyau, a tsakiyar garden din akwai wani katafaren wurin zama, kewaye da ciyawar da aka yi wa ado, Lallausar darduma ce mai wani irin laushi a jikinta irin ta sarakuna, An kewayeta da tuntuye, yayin da suke a zaune kowaccensu ta ɗauki wanka na kece raini na mutunci, mata ne masu duniya, ajin farko, waɗanda suka gaji arziƙi tun kaka da kakanni, wayayyune masu ji da ilmin da Allah ya basu, mace ta farko Gimbiya mujeedat ce a kishingiɗe saman dardumar tayi shiga ta alfarma cikin tsadaddiyar Arab gown launin Ash colour anyi mata adon sparkling stones, masu ɗaukar ido, ta yafa mayafin saman kafaɗarta, baƙar sumar kanta ta sauko har saman dardumar da suke, daga gefenta First Lady ce Hajiya Malikat Sarauta ƴar sarkin Yarbawa jihar Lagos, Mace mai ji da kanta, mahaifiyar Chief Owais, A launin fata chocolate colour ce, taji hutu, bata da yawan fara'a, tana da ƙaramin baki ga dogon hanci, idanunta masu kyan gaske sunyi kama da Asian eyes, kayan jikinta Na yarbawa ne, Wrap around skirt ta sanya tare da farar shirt, anyi mata naɗin head akanta, tun daga kan wuyanta har hannayenta adone na zinarai, bayan Hajiya Malikat sai Hajiya Laurat uwar ji da izza, ƙanwar Alhaji Musa, Idan ka gansu atare da Hajiya malikat baka ta6a gane cewa kishiyoyine saboda kowaccensu bata ɗaukar raini, ita malikat arziki da sarauta ta gada, ita kuma Laurat Arziƙine gare su na fitar shari'a, sai dai daga ganin fuskarta zatayi rashin mutunci idan aka ta6a, daga ka kalli fuskarta zaka shaida ƙanwar Alhaji musa ce, Kamanninsu har sun 6aci da shi, hatta launin fatarsu kala ɗaya ce, Hausa fulani ce, ta ɗauki wankan shadda launin dark brown anyi mata ado, Wuyanta na asanye da sarƙar diamond, haka yatsun hannayenta zabban diamond ne masu kyalkyali da daukar ido. Mace ta gaba, Hajiya Madina ce matar senate Lateef, barumaya ce, tana da hasken fata da tarin sumar kai, hatta gefe da gefen fuskarta akwai tsagensu na rumawa, Tana da kyau iya gargado sutura tanayi mata kyau, daga ganin fuskarta tana da kyakkyawar zuciya ko ba'a faɗa maka ba, Hadaddiyar atampa chiganvy ce a jikinta tabi shape din jikinta, Itama ta dauki nata adon na zinarai. Bayan Ita sai matar His excellency Deen, Hajiya Jamila, Bafullatanar usili ce, Ƴar sarkin Jihar adamawa state, Fara ce jawur da ita, tsabar kyanta kamar ba'indiya. Daga ita sai Matar Abdul Razak, Her excellency Muhibbat, Shuwa Arab ce ƴar mai duguri, fara doguwa ga gashi har gadon baya, family dinsu sunyi ƙaurin suna a 6angaren Arziƙi, Mace ce mai ji da kyawu da wadatar arziki, tana sanye cikin shiga ta bubu gown ta lace, ta kashe ɗaurin kallabi, awarwaron dake a hannayenta na zallar zinari ne. Mace ta karshe basai nayi maku bayaninta ba, Kun riga da kun santa, bakowa bace face Aunty Masifatu Hajiya saratu, mutuniyar, wankan material ta ɗauka, gaba ɗaya ƙamshin turarensu Ya karaɗe iskar garden din hakan ba ƙaramin ƙara ma yanayin ni'ima yayi ba. Daga tsakiyarsu Katafaren Faranti ne na azurfa, mai girman gaske wanda masu hidima suka kawo masu shi, An cika shi da Soyayyun Kaji jar suya, da kayan marmari nunannu, tare da juice masu sanyi. Fira su ke yi atsakaninsu cikin harshen turanci tamkar ba su son furta magana. "Naji daɗin ziyarar da kuka kawo min, kuma naji daɗin ganinku, Sai naji dama A ƙasar nan nake zaune, saboda mu runƙa sada zumunci a tsakaninmu akai akai" gimbiya mujeedat ce tayi maganar tana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. "Ni kaina naji dadin haɗuwar da mu ka yi, bazan Iya musalta farin cikin da nake a ciki ba, Allah Ya ƙara Haɗa kawunanmu da zuri'armu" hajiya malika ce ta fada, tare da kai hannu ta ɗauki Yankan Tufa tana sha. "Canada tamkar gida take awurina ina yawan zuwa saboda business din da nake yi Acan, In sha Allah zan dinga zuwa Ina kawo maku ziyara, Har sai kun gaji da ganina" hajiya Laurat ce ta faɗa tana duban gimbiya mujeedat, murmushin gefen fuska Mujeedat ta sakar mata tare da lumshe idanunta. Hajiya Jamila tace"naji kamar kuna Bankwana, Tun Kafin jibin tayi ko kun manta da family dinner da zamu Yi a gobe? Hajiya saratu tace"Kamar kin shiga zuciyata, nima tun ɗazu maganar da nake ta so Inyi masu kenan, ai gobe muna da gagarumin shagali In Allah yakaimu da rai da lafiya, dole kowa ya halarta" ta faɗa tare da kai hannu cikin faranti Ta yago cinyar kaza ta tura abaki tana tauna Hajiya jamila na dariya tace"daɗina dake saratu baki wasa da cikin ki, Zaman mu anan kin cinye fiye da rabin kaza, shiyasa gaki nan kullim ƙara ƙiba kike yi," "Kinsama kanwar nan tawa ido" acewar Gimibiya mujeedat. "Kibarni da ita aunty, da duk wani mai sanya min ido akan cin abincina, nasan maganinku, zanyima yayyena magana su ƙara maku kishiyoyi, ƙwara ku lalla6ani ku dinga lallashina idan ba haka ba kun san sauran" dariya su ka yi gaba dayansu, "Meya yayi zafi, nayi shiru bazan ƙara tanka maki ba, Ci ki ƙoshi, Idan ma kina buƙatar ƙari zansa akawo maki" hajiya jamila ce ta faɗa tana tura mata farantin agabanta, Hajiya sarah tayi dariya da zolaya tace"Bari naja bakina nayi shiru, naga wasu sun fara haɗe min fuska saboda nayi maganar kishiya" Murmushi kowannansu ya saki, Gimbiya mujeedat tace"ko kaɗan banji fargababa, because I know who my husband is. He doesn't want to remarry; I'm enough for him." She said proudly and gently. Hajiya laurat tace"ai dama irinku ba'ayi maku kishiya, wane mutun, ballanta kuma mijinki da gaba ɗaya rayuwarsa acikin turawa yayita, ba lallai Yana da wannan ra'ayin ba, tun da suma mace ɗaya su ke aure" Her excellency Muhibbat ta murmusa tare da cewa"ni dai koban fada maku ba kun riga da kun sani, ba'ayi mana kishiya, Mijina bai ta6a gigin kula wata ƴa mace ba" Hajiya malikat dake sauraransu tace"nima nan bada jimawaba zansa mijina yayi waje da wata" ta faɗa da zolaya tana kallon Hajiya laurat, dariya suka sanya gaba ɗayansu. Hajiya Laurat tace"Ni da sharafudden mutu karaba takalmin kaza, badai mutun ba sai Allah, me raba ni da shi sai mutuwa" Yamutsa fuska Hajiya malikat tayi"alfarma fa nayi mashi ya aure ki, saboda yana jin shakkar tunkarata da zancen auranki yasa shi ƙin sanar dani sai dai naji daga saman an shafa fatihar auranku, wato yanzu kin samu wurin zama shiyasa har kike da bakin fadin mutu karaba takalmin kaza," cikin raha suke Yin firar tasu. Hajiya Muhubbat tace"ai ni ina mamakin dauriyarku da har kuka Iya haɗa kanku, babu mai jin sirrinku, Gaskiya kun burgeni, amma ni fa wallahi bana tunanin zan Iya zaman lafiya da kishiya, shiyasa tun kafin abdul razak Ya aureni saida muka ƙulla yarjejeniyar bazai yi min kishiya ba, mahaifina ma saida Yaja mashi kunne akan hakan" Jinjina kai Hajiya madina tayi'lallai abun naki azimin ne, ni kuwa dai bana jin zan Iya hana Mijina Yin aure, tun da Allah ya Halasta masu auren mata har huɗu, Idan Ya nuna yana so zan goyi bayanshi, kuma Idan Ya aurota zamu yi zaman lafiya da ita idan har ba ita bace ta bijirema hakan ba" Wani kallo her excellency Muhibbat Ta yi mata"babu zuciya a kirjinki, Shiyasa bakya kishin mijinki" "Bawai don bani da kishi bane, nafiso idan ma kishin zanyi inyi irin na matan manzon Allah SAW, ni fa da ace mijina Yana bin matan banza ƙwara ya auro mata uku a lokaci ɗaya, amma idan nace zan tauye mashi hakkin shi in hana shi auran abunda yake so to fa zan jefa shi ga halaka ne, sannan ban Isa In hana zuciyarshi son wata ƴa mace ba" Jinjina kai su kayi jin bayanin Hajiya madina badan sun fahimce ta ba. Hajiya Jamila tace"godiya yakamata muyiwa Allah daya bamu mazaje nagartattu, nagari masu ƙaunarmu tsakani da Allah, Har Yau Ina alfahari da kasancewata ɗaya daga cikin surukan dattijon Arziƙi, Allah Ya saka mashi da gidan Aljanna, Ya haifa mana zaratan maza sadaukai, Tsakaninmu dashi sai son barka" Murmushi hajiya saratu tadinga saki jin ana yabon mahaifinsu, wani irin dadine Ya lullu6eta Hajiya Muhibbat tace"Ai Zuri'ar Obi komai sun haɗa Allah Ya basu, kyau, nasaba, ilmi, wadatar arziƙi, ƙawayena har tambayata sukeyi wai babu sauran ƴa'ƴan shi da suka rage? Don su aura suma su shigo daga ciki, nace masu sai dai Jikokinsa ƴa'ƴan cikin su in suna so" dariya sukayi gaba ɗayansu. Bayan sun lafa, kowaccensu Ta sanya hannu a faranti ta dauki abunda take son ci, wasu nama Wasu kayan marmari wasu kuma lemu suke sha. _______________________🌹✍️ A hankali Motar Sir Mubarak Tashigo Gidan Hateem, A Harabar ajiye motoci yayi parking dinta, fitowa yayi daga front seat ya zagaya ta back seat Ya bude ma mom turai kofa, A hankali ta fito ta sanya atampa riga da skirt sunyi mata kyau, Ta yafa mayafi saman kafadarta, yayin dashi kuma yake asanye da Shadda. Kallon juna sukayi, da sauri ta kau da idonta gefe, hannunta ruƙe da ƴar handbag dinta Muryarta ƙasa ƙasa ta furta"dan Allah kabarni in koma gida, bansan meyasa ka tursasa min akan inzo gurinsu ba, na faɗa maka basu ƙaunata, wallahi ci mun mutunci zasuyi" Ɗaure mata fuska yayi"kar na kuskura nasake jin kin furta maganar nan! bana jin dadin yadda kike ware kanki daga cikinsu! Dame suka fi ki? Tsoron su kike ji? Baki Iya mayar masu da martani in suka gaya maki magana"? Tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace"Ina da banbanci dasu, Har Yau har gobe sunƙi mantawa da matsayina agidanku, Suna yi min kallon ƙasƙantacciya Ƴar aiki, babu abunda Ya canza" *DAGA ALƘALAMIN HAFSAT BATURE✍️*