_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ _GAJERAN LABARI📝_ NAH AISHA MOHAMMAD SANI (Xayyeesherthul-humaerath) _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ _FREE NOVEL NE AMMAN RASHIN SHARHI ZAI IYA SAWA YA DAWO NA KUDI, YANAYIN YADDA KUKA DAUKA NIMA HAKAN ZAN DAUKA✌️JUST FOR MY FANS,LOVE YOU LODI,LODI🥰❤️💃_ MARUBUCIYAR👇 KUCHAKAR KISHIYA BABU RUWAN SO AZZAWAJUL-MUKADDAR WASA DA SO KWADAYI 2020 MATAR POLICE 200 JAMEEL 200 NA YANZU: SAI NA AURI MARUBUCI PAGE 1/2 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM. _*FEJIN FARKO SADAUKARWANE GAREKU FAUZIYYA TARE DA JANNAT YAR BABA KUJI DADINKU🥰🥰🥰*_ ........Wata Yar matashiyar yarinya na hango da bazata huce shekara goma sha bakwai ba aduniya, kwance take tana barci cikin nishadi da walwala domin da zaran an kalli yadda yanayin murmushi ke bayyana afuskarta wannan ka dai ya isa laburta cewa tana cikin yanayi na farinciki,ta kankame littafin Hausa akirji tamkar tana gundu a kwace mata, mafarkine Wanda ta sabayi kamar kullum Amman ko wanne da salonsa ko na yau din ya yake? Bara mu lekye cikin mafarkin Nafeesa. "Nafeesa kin San cewa ba jin cewa akwai Wata 'ya Mace da zan so kamarki? Kina jin cewa zan iya furta Kalmar so ga Wata 'ya Mace bayan ke?, Hmm babu tantama cewa ke ce zabina sannan kuma kece burina,ina miki so fiye da yadda majnun ke son laila,ina kaunarki fiye da yadda kifi ke bukatar ruwa domin rayuwa." Cewar Nafseen da ke zaune gaban Nafeesa. Gyara zama tai tare da kara kura mai kallo tai murmushi kan ta fara da, "Da ace ana Iya kidaye adadin soyayya a sikeli na tabbata cewa wadda nake yi maka bazata taba kidayuwa ba,kamar yadda Dan Adam ba zai Iya rayuwa batare da ruwa haka Nima nake jin cewa ba zan iya rayuwa batare da kai ba, ka zamemin jinin jikina,numfashina da walwalata, ada nakan ji cewa ka fi karfina ba zan taba samunka arayuwata Amman wai yau nice tare da kai har kake furtamin Kalmar so? Dan Allah Nafseen ka rayu da ni karka barni karkacemin wannan mafarkine nake yi." Rik'o hannunta ya yi,yana kokarin yin magana. Karaf Mama ta shigo tare da bugawa Nafeesa dundu abaya. Sambatu take,"Ka kara cewa kana so na ko da sau dayane Dan Allah kar ka tafi." Dukan da Mama ta kara kai mata ne ya sa ta saurin razana tare da dawowa hayyacinta, "Mama kin kuran min shi, Mama kice ya dawo yau ya fadamin cewa yana sona mama Dan Allah kice ya dawo." Tsaki Mama tayi, "Ki bar min wannan shirmen tun kan na kai miki mari maza tashi kije kiyi sallah wawiya kawai." Kara kallon dakin tai da kyau ta ga da alamar gaske dai daga itane sai Mama, kuka kawai ta fara tana, "Mama wallahi in ban gan shi na aure shi ba mutuwa zan yi, ni kan sai na AURI MARUBUCI." ta kara fashewa da kuka. Wani irin bakin cikine ya kara tirnik'e mahaifiyarta ta, ta fice batare da tace komai ba illa azuciyarta da take fadin, "Ban San wannan wani irin bala'in so bane ga mutumin ba ba a taba gani ba, daga karatun littafi kawai, anya kuwa ba aljanune suka shiga jikin Nafeesa ba kuwa? Ya Zama dole in sanar da Abhee abin da ke faruwa adaren yau." Ta shige daki. Ita kuwa Nafeesa kara kyankyame littafin tai tana kuka sai da tai mai isanta kan ta dauro alwala tai sallah, tana idarwa ba abun da ta fara rok'a illa Allah ya nuna mata marubucinta Nafseen Sanan kuma Allah ya bata ikon auransa. Bayan ta kammala addu'ar tashi tai ta fita waje da littafinta ahannu, zama tai afilin tsakar gidan na su tare da chok a hannunta Zane ta farayi tana waka Wanda da farkon zanen duk Wanda ya kalla zai dauka cewa shirme take zanawa,Amman ahankali kyahun zanen na fitowa,da mamaki duk da kasancewar Nafeesa ba ta San Nafseen ba Amman tsaf yanayinsa da kamaninsa take zanawa,ba musu duk Wanda ya San Nafseen kuma ya ga zanen Nafeesa zai dauka cewa ta San shi kuma kyakkyawan sani ma, azahirin gaskiya ko bata taba ganinsa ba bin abun da zuciyarta ke rada mata kawai take ya yin zanen tundaga farko har karshe. Kallonsa ta tsayayi tana mai farinciki ji take tamkar na gasken ne agabanta, cikin littafan da ta fito da su ta dau daya mai suna YAR AUTA NA JAMEEL NAFSEEN, Karatu ta fara cikin nutsuwa da zakuwa akowanni feji ganin ta riski gaba, labari Indai na shi ne ko wani irin salo na tafiya da zuciyar Nafeesa. Gabadaya hankalinta ya tafi ga karatun kaninta da ba zai huce shekara Takwas bane ya fito yana buga boll ta gabanta ya huce ba tare da sanin Sa ba har ya goge mata zanen Nafseen. Ji tayi ajikinta hakan ya Sa ta saurin kallon kasanta gani tai tamkar na gasken ne ya yi hatsari hakan ya sa ta Jan dogon numfashi tare da suma awajen nan take. ✌️YAWAN SHARHI YAWAN TYPING Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ 12/1/2021 _GAJERAN LABARI📝_ NAH AISHA MOHAMMAD SANI (Xayyeesherthul-humaerath) _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 3/4 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *🥰🥰 WANNAN FEJIN SADAUKARWANE GAREKA YAYANA,ABUN ALFAHARINA,YAYA MUSADDAM😘YAYANAH YA FI NA KOWA💃ANGON MAI AWARA SON SO FISABILILLAH* MY GROUP XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH FANS GROUP INA KAUNARKU HAR CIKIN RAINA MASOYAN ASALI😘😘 Sabeer bai San lokacin da kurma uban ihu ba, "Mammah kizo Anti Nafeesa ta mutu,Mammah." A rikice Mammah ta fito tana, "Sabeer wai meyafaru ne ba yanzu ta fito karatu kalau ba?" Sabeer na kuka ya ce, "Ban San tayi zane bane na goge mata tana kallo shine ta fadi." Dafa kai Mammah tai tare da fadin, "Yah Allah! Kokarin daga Nafeesa daga wajen tai domin maidata cikin gida, da yake Mammah malamar asibitice kokari tai domin dawo 'Yartata cikin haiyacinta a Dan kankanin lokaci. Bude Idon da Nafeesa za tayi ta fara, " Mammah Nafseen dina Sabeer ya gogemin, sai ta kara fashewa da kuka." Mammah bata da zabin da ya wuce ta rarrashi 'Yartata awannan lokacin hakan ya sa ta Jan Nafeesa jiki tana shafa mata baya, "Ki yi hakuri kinji Nafeesa bai sani bane, kuma ai zanene na San zaki Iya zana Wanda ya fi wannan kyau ko?" Wani Dadi Nafeesa taji aranta nan take ta mik'e "Sabeer Bani Littafina zan tafi madarasa." Mammah ta ce, "Madarasa da littafin Hausa? Haba Maman Abhi kibari in kika dawo kyayi karatun." Nafeesa ta fara buga kafa, "Ni dai da abuna zan tafi wallahi." Tashi Mammah tai kawai tana fadin, "Allah ya kyauta." Nafeesa kuwa Hijabinta ta Sa har kasa tare da nikabinta ta yafa jakar makarantarta agefenta na hagu sannan littafin hausanta na marubucinta NAFSEEN a hannun dama wato Yar Auta. Ko da ta isa makaranta anfara karatu Neman waje kawai tai ta zauna tare da bude littafinta domin cigaba da karatu. Karatu ake yi masu Amman gabadaya hankalinta na kan littafin da take karanta, murmushi ne kawai ke bayyana afuskarta, kara gyara zama tai tare da Jan dogon numfashi ta cigaba da karatun, Malamin ne ya lura da yanayinta ganin cewa hankalinta baya tattare da shi duk da kasancewar bai hango me take kallo ba. "Ke Nafeesa, ta shi ki karantomin hadisin farkon nan da na kawo." Cikin Sauri ta ta shi arikice take maganar, "Mallam, ai Nafseen bai fadamin ba aciki." Sake baki ya yi yana kallonta kawai cen ya daka mata tsawa, "Waye Nafseen? Karatu muke ko maganar wani anan, Iye ba tambayarki na ke ba?" Sunkuyar da kai Nafeesa tai batare da ta kara kallon malamin ba. Cikin tsawa ya kara fadin, "Nace waye Nafseen?" Karaf wata yarinya ta ce, "Malam wani marubucin littafan hausane." Kara fusata malamin ya yi, "Ah ya yi kyau aiko yau zakiga Nafseen a makarantar nan ganin idonki bani littafin." Jiki asanyaye Nafeesa ta mik'a masa littafin . Yana karba ya karema littafin kallo kamar yadda aka Fada sunan marubucin Nafseen,tsaki ya yi Sannan ya fara fata-fata da littafin yana yankawa. Kuka Nafeesa ta fara yi bilhakki da gaskiya,tun tanayi ahankali har ta fara shidewa daga karshe ma ta k'ame awajen nan take. Ganin yadda tai, abun ya matukar ba malam mamaki daga yaga littafi, tsaki ya yi yana fadin, "kar in ga kowa ya fita kuzo mu cigaba da karatun mu in iskancine nawa yafi nata. Kwance take awajen cen kuma ta mik'e tare da wani irin gawartaccen kara,Malam ta nufa kawai tare da damkosa tana wani irin numfashi. Ihu ya fara yana, " Dan Allah Ku kwaceni Nafeesa za ta kasheni,wayyo Allah na." Dalibai kuwa sai dariya. Nafeesa kuwa bata fasa jibgar malam ba. Dalibanne suka kira sauran malaman dakyar aka karba Malam a hannun Nafeesa sai numfarfashi take tana kara kokarin cacumosa. Malam na samun hanya ya fice adari yana, "Wallahi Yarinyarnan ba mutum bace Ku bincika." maganar yake cikin Sauri da hakki domin ji yake tamkar zata kara damkar shi. Suko dalibai ba abin da suke ban da dariya yau Mallam yaji a jikinsa Dama ba baya ba wajen jibgar dalibai. Ita ko Nafeesa ban da kuka ba abin da take Dan arayuwanta bata taba shiga tashin hankali irin wannan ba Wai Lttafin Nafseen din ta aka yaga a gabanta sai ma take ga kamar har shi din aka taba ba Iya Littafin ba D ji take Zata Iya fada da kowa a yau dai kam. Wani Malamine yazo kusa da ita ya ce, "Nafeesa me ke damunki ne ?" aiko sai ta Kara sanya wani irin kuka cike da sauti ta ce, " Malam Nafseen dina ya yaga min ya taba min rayuwa ta yamin kacakaca da Nafseen dina Wallahi bazan bar shi ba dole sai ya ji abin da na ke ji ," kowa sai ya tsaya tsaro tsaro yana kallon Nafeesa yayin da wasu ke ganin ta haukace kuma ta hadu da bakak'e aljanu. Da kyar akasamu Nafeesa tabar wajen,biyu daga cikin Malamamsu mata aka nada domin yi mata rakiya gida ganin cewa lamarin yafi karfinsu har suka bar makarantar bata dai na maganganu ba kaman wata sabuwar kamu ,"wallahi daka rabani da Nafseen gara ka yanki naman jikina wayyo Nafseen Dina sai hakuri ake bata amma bata San ma anayi ba sai kara bankarewa da take. Da Haka har suka kai gida Mamma na daki taji sumbatu Irin na Nafeesa sai ko ta daura hannu aka tare da fadin, " innalillahi Wa'inna ilaihir rajiun me kuma yake faruwa da Nafeesa lafiya Fa muka rabu ."nan da nan hankalin Mamma ya ta shi abinka da uwa a gigice ta kara so garesu. 👍Gajeran labarine Dan haka gajerun fejis za Ku na samu,Amman yawan sharhi kan Sa in kara🥰 Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ 13/1/2021 _GAJERAN LABARI📝_ NAH AISHA MOHAMMAD SANI (Xayyeesherthul-humaerath) _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 5/6 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *👌ANAYI INA JIN DADI ANA BARI INA JIN HAUSHI MARUBUTA YAN UWANA KUNA BIRGENI FA ARADU GULMA KWAI DADI😂* _*Wannan shafin na ku ne my group members, Momin shuraim,Mrs Mubarak,Mariyata,Aisha shu'aib,Meenat,Aishatul-humaerah,kuji dadinku sharhinku na bani nishadi walle😘😘* Karasowar Da Mammah za tai nan take Nafeesa ta Fada kasa sumammiya. Ba karamin tashi hankalin Mammah da na sauran malaman ya yi ba, kokarin daukatar suke domin kai ta cikin gida. Dakinta sukaje sannan aka shimfideta kan gadonta. Cike da Mamaki Mammah ke kallon 'Yar ta ta gata nan dai domin ba suma tai ba alamu sun nuna cewa barcine ya kwasheta lokaci guda. Mammah ta ce, "Ikon Allah daga isowa gida sai wani kalan barci mai ban mamaki." Ta kalli Malaman tare da fadin, "Mun gode Allah ya saka da alkairi." Da "Ameen." suka amsa sannan sukai mata sallama. Kara gyara mata kwanciyar tai sannan ta fice daga dakin. Kamar wasa karfe biyar tayi ko alamar tashi Nafeesa ba tai ba, Mammah ta dubata gata dai lafiya Amman bata tashi ba. Ko da Abhi ya kira waya abaiwa Nafeesa, kawai Mammah cewa tai tana barci domin ta San da zaran ta Fada mai hankalinsa tashi zai mussaman yadda yake matukar kaunar 'yartasa. WACECE NAFEESA? SANNAN WANENE NAFSEEN? NA SAN MA SU KARUTU DA DAMA SUN ZAKU DA SU SAN ASALIN NAFEESA DA NAFSEEN TO GA BAYANANNE NA NAN TAFE. WACECE NAFEESA? Nafeesa 'Yace ga Malam Aminu Direba (Abhi) tare da Mahaifiyarta Dr Salima wadda suke kira da Mammah,itace yar SU ta fari sannan kaninta Sabeer mai shekara goma su biyu kadai Allah ya baiwa Iyayensu,baza asa su sahun masu arziki ba sai dai ace masu rufin asiri,domin kuwa Abhi Direba ne dake tuki gari gari wani lokacin ma sai ya yi sati baya gida,Mammah kuwa malamar asibitice da yake tayi karatu da haka suke rayuwarsu cikin farinciki da annashuwa ba tare da sun Sa son duniya aransu ba,gidan su Dan karamine iyaka arzikinsu daki biyar biyu na Mammah daya na Abhi sauram kuwa na Nafeesa da Sabeer. Daga ita har iyayenta acikin garin Yola suke da zama. NAFEESA Yarinyace mai ilimin addini da na boko tana da hankali matukar gaske ba za ace da ita kyakkayawa sannan bata sahun munana daidai gwargwado take,tun Nafeesa na da shekara goma aduniya ta fara karatun Hausa Novel kamar wasa malamin hausansu na Boko ya fara karanta musu littafin *YAR AUTA* na Jameel Nafseen tun daga lokacin Nafeesa ta fara karatu domin gabadaya ji take marubucin na birgeta, alokacin bata San miye so ba Amman ta San cewa tana son littafansa kuma a kullum bata da burin da ya wuce karantasu, YA kasance a kullum Nafeesa ta kwanta barci bata da aikinyi sai mafarkin Nafseen aduk ranar da ba tai mafarkinsa ba to ba zaman lafiya domin ba mai gane kanta in ko tayi tana tashi zata fara sabga uban kuka sai tayi mai isarta kan ta bari,har ta San menene so kuma ta fahimci cewa son Sa take tare da kudurin cewa sai ta AURI MARUBUCI, duk da Iyayenta sun sani Amman ba Yarda suka Iya domin gani suke basu da arzikin nemawa Yar su shi bare ya aura, tsantsar so mai ban mamaki bata taba ganinsa ba Amman tana Iya zana kamanninsa sak kuma akan Sa ta fara Zane sannan bata taba Zane Indai ba shi za ta zana ba,bangon dakinta ko ina ban da zanen Nafseen ba komai har zanawa tai aka maida mata shi tamkar photo, ta Sa agefen gadonta. Ko da wasa Ba ta son jin an zagi wani mai suna Jameel bare kuma Nafseen dinta kacokan ta kan iya komai kan hakan domin ficewa take ahankalinta nan take. Shin me kuke tunani zai faru ranar da Nafeesa ta ga Nafseen kuma sak ga kalan zanen da ta saba?? Wannan ke nan kadan daga tarihin Nafeesa. WANENE NAFSEEN? Wani Hamshakin Matashin marubucine,kuma mawaki sannan director,kuma producer, waanda ke zaune cikin garin Kaduna, Ya rubuta littafai da dama na Hausa da kuma wakoki kuma ya jogaranci fina finai daban daban, yana da matukar basirar rubutu mussaman na Hausa, salon Sa na matukar tafiya da mai karatu hakan ya Sa a kullum masoyansa daduwa suke duk da kasancewar yana da mata ko kadan hakan baya damun al'umma, kowacce burinta kawai ta samu Shiga azuciyar matashin saurayin nan mai tashe da zamani,baya da wulakanci ko kadan kullum kokarinsa bai huce yaga ya faranta ran masoyansa ba,hakan ke kara masa kima da daraja a idanun mutane da dama. Wannan ke nan. Cigaban labarin..... ******Afirgice ta farka abarcin ganin cewa ba kowa dakin,leka falon ma tai ba kowa hakan ya bata damar fita agidan. Tafiya kawai take batare da tasan inda take nufa ba,wani haskene ya bayyana agabanta tsintar kan ta da bin wannan hasken tai, tafiya take adaji babu ko alamar mutane bare mutum illa ita daya, ta na cikin tafiya wannan hasken ya tsaya cak,tare da fara komawa wani irin launi, me za ta gani??? Nafseen ne ke bayyana gareta.... Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ 14/1/2021 _GAJERAN LABARI📝_ NAH AISHA MOHAMMAD SANI (Xayyeesherthul-humaerath) _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 7 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM 💋💋💋 *MY GROUP MEMBERS WALLE KUNA KAHE INDO DA COMMENTS FA,INA YIN KU IRIN SOSAI DINNAN❤️❤️* Karasawa tai aguje domin riskarsa. Mik'a hannunta tai domin rungumarsa anan ta Kara wata zazzafar firgita nan take ta bude idonta kwance take adakinta Wanda tun jiya da aka dawo da ita daga makaranta bata farka ba. Sautin Kukanta shi ya fahimtar da Mammah cewa ta farka,cikin sauri ta karaso gareta tare da fadin, "Nafeesa Lafiyanki kalau ko? Ki dai na kuka kinji? Ina kina son Nafseen?" Ta girgiza kai. Mammah ta kara da , "To kina so in miki addu'ah tare da tayaki nemansa ko?" Nafeesa ta ce, "Eh, Mammah ina glass dina bana gani sosai." Cike da tausayin 'Yartata ta mika mata glass din tare da taimakonta wajen sawa. Tsabar karatun littafin Jameel da kukan rashin ganinsa yasa Nafeesa bata gani sosai sai da glass, ko da ta karanta littafinsa sau dari hakan ba zai hanata kara karantawa anjima ba,har ta kai ga takusa daina gani,da kyar aka samu damar ceton idonta tare da bata glass kuma hakan bai sa ta daina karatun ba. Bayan ta sa glass din ta tashi, "Mammah zan yi sallah." Mammah ta ce, "OK to muje in raka ki toilet din ko." Murmushi Nafeesa tai, "Tab ni dai bazaki lek'ani ba, zan Iya fa." Murmushi ita ma tai , "Shi ke nan Ummana Jekiyi ba zan lek'aki ba." Cewar Mammah. Sai da tayi wanka sannan ta dauro alwala sallarta tai cikin nutsuwa har ta idar. Kayanta tasa tare da dauko Jakarta domin tafiya makaranta. Mammah da ke shirin tafiya office ta kalleta, "Nafeesa ko karya baki ba miye na saurin haka,kuma naga ma ba lafiya gareki ba?" Ta ce, "Mammah yau fa munada lectures da safene kuma inna bari malamin ya zo ba zai bari in Shiga ba, ni jikina bana jin komai." Mammah ta mika Mata Dari biyar tare da fadin, "Ga shi nan ki sai wani abun kice sauran ki yi kudin mashin Dan kinga Abhi baya gari kudin hannuna ya kare gashi ba albashi." Murmushi Nafeesa tai, "Allah amfana Mammah." Tana fita ta samu Nafe nan kuwa ta Dane cikin sauri domin ta zaku ta shiga Skul, cikin sa'a kuwa tana isa ta fara hango yan Department dinsu da alama ba ashiga aji ba, Hamdallah tai azuciyarta, ta cigaba da tafiya. Wata Yar budurwa da bata wuce sa'arta ba ne ta tawo da sauri, "Oyoyo Habibbty har na cire ran zuwanki wallahi." Nafeesa ta galla mata harara "mai zai hanani zuwa makaranta da lafiyata." Karaf wani saurayi ya cafe da , "Ai ko da baki zo ba ma ni zan zo gidan da kai na in daukoki." Tsaki Nafeesa tai tana, "Kin ga Habibbty zo mu tafi." Har sun fara tafiya ya ja gabansu tare da fadin, "Wai ke me na miki ne ki ka tsaneni? Dan kawai nace ina sonki? In ban da Soyayya ma da kwashe kwashe me zanyi da Makauniya wadda bata gani sai da glass, ko da yake naji labarin cewa wai wani banza da bai ma San kina nan ba kike so." Nafeesa ta dago tare da fadin, "Mutansir kar ka kara ce masa banza kuma maganar makauniya da ka ke dadinta ba ni nai kai na ba ko? Kuma bance ka soni dole ba,Dan Allah ka kyalleni." "Ke dakata, ki tsaya wai akan Banza mara aikinyi Wanda ya rasa sana'a sai ta rubutu ki ke Neman min rashin kunya? To na Fada banza."cewar Mutansir yana wuce kamar an saukewa jaki kaya. Jin Zuciyata tai na bugawa zafin hakan take ji har cikin ranta yanayinta ya fara chanjawa. Maryam da ta fahimci hakan ta fara Jan ta da niyar su tafi. Har sun fara Tafiya Kawai Nafeesa ta juyo tare da bin bayan Mutansir ta sha mai gaba alokaci guda ta kai mai wasu zazzafan marika biyu afuskarta, shi ta mari Amman ita take kwalla domin jin zafin abun da ya fada kan Nafseen dinta. Kamewa Mutansir yayi awajen ya kasa motsi domin tunda yake bai tabajin mari mai dauke da radadi irin na yau ba, zufa ya farayi ta ko ina, ga fitsari na zuba, sauran abokansane suka taso suna dariya. Ita kuwa Nafeesa ko ajikinta ta cigaba da tafiya batare da ta kara waiwayo garesa ba. Sai da Mutansir ya dauki minti goma kan ya dawo haiyyacinsa, "Wallahi,wallahi kunji na rantse sai na illata yarinyarnan,illar da har ta mutu ba zata manta ba."cewar Mutansir. Sauran abokansa kuwa yan Neman ayi da suka gama shan dariyar kara zugasa sukai. Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ 16/1/2021 _GAJERAN LABARI📝_ NAH AISHA MOHAMMAD SANI (Xayyeesherthul-humaerath) _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 8 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *Wannan fejin Sadaukarwane Gareka Yaya Jamilu (Nafseen) tare da Antyna Iklima❤️Ina mai yi maku fatan alkairi tare da cigaba da rayuwar aurenku cikin farinciki,amana da Yarda,Allah Sa Anty Sa sambado mana an biyu🤣amin takwara* Karatun tai hankali kwance sunfito ke nan dai,dai gate din makaranta zasu fita wata Yarinya da zata kai shekara ashirinne ta dumfarota da sauri, bangaje Nafeesa tai har sai da glass dinta ya fadi kasa, "Maga tayi ai,ke har kin isa ki tabamin Mutansir a makarantarnan,yar matsiyata, ko me kika masa ma ya nace miki oho, da alama dai ba a barsa haka ba, anga 'Ya'yan masu dukiya ana Neman hanyar shige masu Amman tsoro ya hana,to wallahi ahir dinki, ko da gaske ko da wasa naji cewa kina son Mutansir kin Riga kin kade yarinya ba ma ke kadai ba hatta Shi wannan driban da wannan ma'aikaciyar asibitin,makauniyar banza da wofi,wata yar shila da ke ,ko inama abun so ajikinnan ? Mtsww." Cewar Fatima tare da cigaba da yiwa Nafeesa wani mummunan kallo. Tunda Nafeesa ta durkusar da kanta bata dago ba,ban da hawaye ba abunda ke zuba daga idanunta, Magana ta farayi cikin ruwan Sanyi, "Habibbty Bani Glass din nasaka bana gani." Ita kan ta Maryam sai da hawaye ya fara bayyana daga fuskarta tsabar tausayin Nafeesa da take. Karfan Glass din Nafeesa tai tare da sawa a idonta ta rik'e hannun Maryam suka cigaba da tafiya. Tsaki Fatima tai domin bata so hakan ba Sam ta lura kamar Nafeesa bataji zafi sosai ba,hakan yasata kara tunkararta cikin sauri tare da shan gabanta, Glass din fuskar Nafeesa ta kwace tare da cigaba da tafiya batare da tace komai ba. Maryam ba kokarin yin Magana Nafeesa ta rik'e mata baki, "Habbibty kar kice komai, wannan kaddaratace, kisa anafe kawai kar drebanku ya gaji da jiranki." Kallon kawartata tai cike da tausayi, "A hakan zan Sa ki Anafe bayan nasan ba gani kike sosai ba, ki bari in karbo glass din wajenta sai dreban ya kai mu duka, wani iskancin ma Dan sunga ana barinsune." Nafeesa ta kank'ame hannun Maryam , "Dan Allah ka da ki tada rikice akaina ni ba yar kowa bace kamar yadda ta Fada Amman na San cewa watarana zatayi nadamar abun da tamin,ni kawai akai ni Asibiti Gun Mammah ta nemamin wani glass din,Idon ciwo yake min habibbty wallahi ciwo ya faramin." Cikin sauri Maryam ta laluba Jakarta tare da Ciro wani karamin glass , "Sorry Habibbty barin Sa miki wannan kan muje asibitin to." Bayan ta sa mata glass din haka Maryam ta rik'e Nafeesa suka Shiga mota. Suna shiga Mota Nafeesa ta Sa hannu ajakarta tare da lalubo wani littafi mai suna *Ajaliin mace* Fasihin marubucin nan nata ne dai ya rubuta, kallon littafin tayi tare da rugumarsa tamkar mutum, wani kayataccen murmushi ta sake,domin ji take duk damuwar da ke ranta ta kau,indai tana tare da littafin da Farincikin ranta ya wallafa,rubutunsa tamkar muryasa gareta,sunansa tamkar hotonsa ne garesa, bangon littafin kuwa ji take tamkar bugun zuciyartane, ji take gabadaya ta nemi damuwar da ke ranta ta rasa,cikin murmushi ta ce, "Habibbty Dan Karantamin kinga bana gani da kyau Dan Allah, kan mu isa." Murmushi Maryam ma tayi ganin cewa damuwa ta fice daga fuska har zuciyar Kawartata,karban littafin tayi tare da fara karanto mata. Da mamaki Nafeesa ta haddace littafin tsaf a kwakwalwarta domin kan Maryam ta kai Aya Ita ta karasa mata, Maryam na kuskure wajen furuci zata gyara mata. "Kai Habibbty ai kin gama haddace littafinnan to miye kuma na sai na karanta miki?" Murmushu Nafeesa tayi, "Na haddace littafin nan tamkar yadda na haddace Al'Qur'ani mai girma,ko ina kika tabomin zan Iya karasa miki batare da na kalla ba,Amman kin San me? A kullum ina so akarantamin ko ni na karanta,domin aduk lokacin da nake sauraren kalaman banajin muryar kowa akunnena sai na Marubucina,sautin Muryarsa kadai ke sauka acikin kunnuwana, Habibbty mutane da yawa na fadin cewa karyane dan wani ya ce zai iya rasa ransa in ya rasa masoyinsa ko? To ni nasa araina cewa duk ranar da na tabbatar da cewa bazan Taba samun Yaya Nafseen ba, ba makawa zan Iya mutuwa nan take, Ina yi masa so fiye da yadda kowa ke tsammani,in ana maganar soyayya sai kije ana Sa Majnoon da Laiyla to ni ko Kadan basa gabana domin ji nake na ninnkasu natakasu a soyayyata,ko da ace Nafseen ba zai soni ba,akwai wani sirri tsakanina da shi, kuma inada tabbacin ya sani a ko ina yake ma duk da cewa ba mu San juna ba, kin san menene Habibbty?" Maryam na gyara zama domin jin me Aminiyarta ta zatace dai,dai da lokacin da dreba ya tsaya domin sun iso asibitin batare da ma sun sani ba. Nafeesa ta ce, "Yawwa Mun Iso." Suna fita Maryam ta kalli Aminiyarta ta, "Habibbty fadamin sirrin." Murmushi Nafeesa tai, "Sirrin,kina son jin Sirrin Habibbty?" Maryam ta ce, "Sosai ma ." Nafeesa ta ce, " ✌️😁 MY GROUP MEMBERS ANA TARE AYAU MA KUWA? RUWAN COMMENTS YADDA AKA SABA MUTANEN KWARAI😘😘 Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH 6STARS INDEED✨ _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 9 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM "Zan Fada miki sirrin Amman sai lokaci ya yi." Cike da Murmushi Maryam ta ce, "Allah ya kaimu zan so ko jin wannan sirri domin na San na mussamanne tamkar yadda Habibbtyna ta kasance ta mussaman." "Umm ni kam kai ni gun Mammahna." Cewar Nafeesa. Rik'e mata hannu Maryam tayi har suka shiga cikin asibitin, Mammah na ganin Nafeesa gabanta ya fadi tare da karasawa garesu cikin sauri. "Nafeesa meya sameki? Ina glass din na ganki da wani kuma? Ya naga idonki ya yi wani iri ma lafiya kuwa." Cewar Mammah. Rike hannun Mammah Nafeesa tayi , "Aa fa Mammah fad'uwa Glass din ya yi kuma ya fashe,shi ne iska ta tabamin ido ya fara hawaye." Mammah ta kalla Maryam, "Anya kuwa Ku dai fadamin gaskiya." Maryam ta ce, "Hakane Mammah da naga ta fara hawayenne yasa na bata nawa glass din ko iskanne ya tare mata." "OK To Bara in dauko dayan,Allah ma yataimaka biyu na karban mata daman." Fadin Mammah. Maryam ta ce, "Habbity kar dreba ya gaji da jira Bara in tafi sai mun hadu goben." "OK bye bye Na gode habibbtkuri aida Anty." Cewar Nafeesa tana dagawa Maryam hannu. Bai fi minti Biyar ba da tafiyar Maryam, Mammah da Nafeesa ma suka tafi gida,kasancewar dutyn rana Mammah ke da shi. Nafeesa zaune tana ta karatun littafi kamar yadda ta saba, ta kai karshe tai karo Da number Jameel Nafseen, a kullum tana ganin number nan kuma tana Sa rai da kokarin kira Amman tsoro da kwarjini ya hanata ko Da ta dau number Da niyar kira kan ya shiga zata katse,ayau kam ta cire tsoro tare da kudiri niyar kiransa, daukan number ta ta danna kira zuciyarta ce ta fara bugawa cikin sauri da mamaki maimakon numberta fara ringing sai taji cewa akashe,tun daga ranar kullum sai ta gwada kira Amman wayar nan dai akashe hakan kuma bai Sa ta fasa ba. ****Safiyar lahadi ba Boko ba islamiya hakan ya Sa ta dauko wayarta tare da bude data chatting ta fara tare da lekya group din su na mata zallah ta ji ana maganar wani film mai suna Abu Hassan, bata wani tsaya ta saurari chat din ba karaf sai taji ana fadin cewa ai Jameel Nafseen ne ya tsara labarin, tsayawa tayi da chat din tana tunani shin dama sahibin nata har Films ya ke rubutawa? . A zuciyarta take fadin, "Ya zamemin dole in nemi fina,finan da ya rubuta sannan akan su zan fara kallo." Bata gama sak'e,sak'en ba karaf sai taji wata ta turo message , "Ai yawancin Marubuta yanzu sun dawo online, Dan natabajin Yayata da kawarta na fadin cewa akwai group na Marubuta anan whatsApp kuma duk marubutannan na ciki daga manyan har yaran." Da sauri Nafeesa ta bi wannan yarinyar private, sallama tayi mata tare da fadin , "Dan Allah zaki iya min hanya in shiga group din marubutannan?." Tayo mata reply da , "Eh to nima kawar Yayatace ke rubutu tana ciki, Amman ance zallan Marubuta ake sawa ciki." Tunani Nafeesa ta tafi kan ta bata amsa, "A yau zan zama marubuciya kuma zan rubuta labari indai zai iskeni ga Nafseen,." Bayan ta gama tunanin da Sauri tayo mata reply , "Ok nima ina rubutun ai ko zaki Iya hadani da kawar Yayar ta kin?" Batare da tace komai ba, ta turo mata da number mai dauke da suna Nusaiba. Saving din number Nafeesa ta fara yi sannan ta shiga wajen kira ta kira ta. Ringing wayar ta fara har ta kusa katsewa kan Nusaiba ta dauka. Sallama Nafeesa ta fara yi mata tare da gaisuwa,sannan ta ce, "Dan Allah Anty Nusaiba so nake asani cikin group din marubuta nafara rubuta littafi Amman ina bukatar ma su min gyara." Washe baki Nusaiba tai domin irin sune yan karyan nan ma su so ace sune suka San kaza ko suka yi hanyar kaza, sai da ta gama washe bakin ta kan ta ce, "Ok karki damu da nayi rubutu Amman yanzu na daina, akwai Matar Yayana da ke yi dai kuma tana cikin group din zan bada numberki ta saki." Hamdala Nafeesa tai har cikin ranta tana mai farincikin hakan. Nusaiba ta ce, "Ko kuma ma dai kiyi min magana WhatsApp yanzu sai in Sa asakin." Nafeesa ta ce , "To na gode Anty Allah saka da alkairi." Nusaiba ta amsa da Ameen kan ta katse wayar da sauri ta fita adakin tare da nufan wani bangare, tana shiga ta ce, "Aunty Farida kizo kar inji kunya yau ta guna aka biyo Neman alfarmar shiga Group din nan na ku da kikace min akwai su Fauziya D Sulaiman da ma sauran marubuta da mawaka?" Farida ta ce, "Eh fa ya akayi to." Nusaiba ta ce , "Watace ta kirani wallahi wai tana son shiga ko tayama akayi ta sami numberta oho ni dai ki taimaka asata zan baki number ta WhatsApp." Murmushi Farida tai, "Hmm Hajiya Nusaiba ke nan bakomai ki turo za asata Allah Sa group din ma da waje Dan cike muke fam." Nusaiba ta ce, "Ni dai ataimaka kar ta rainani." Dariya kawai Farida tai kasancewar tasan halin Nusaiba da shegiyar karya da kuri Intaso karyartama cewa take ita ke rubutun ba Antynta ba. Nafeesa kuwa tuni tayiwa Nafeesa magana WhatsApp kamar yadda ta bukata. Ko reply Nusaiba ba tai mata ba kawai ta turawa da Farida Number. PC Farida ta bi Bamai Dabuwa tare da fadin, "Dan Allah asa min wannan writern sabuwace." Ya yi mata reply da , "OK bara dai in duba Allah Sa da kwai waje." Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 10 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *WANNAN FEJIN NA KUNE KUJI DADINKU MASOYAN ASALI Deeymusah,Mr Mubarak,Momim shuraim,Fatima zahra,son so fisabillah😘Allah bar min Ku* Dubawan da zai yi kuwa ya tarar group din cike yake ba damar Kara wani in ba wai wani ko wata sun fita ba. Komawa Private ya yi tare da fadin, "Ba waje fa, group din acike yake sai dai ki bata hakuri ta jira ko wasu zasu fita." Har cikin ran Farida bataji ba dadi ba Sam kawai sai ta ce, "To ni dai in an samu hali asata Dan tana da bukatar kasancewa agidan matukar gaske." Wa she gari Shiru shiru Nafeesa ta ga ba asata A group ba hakan ya sata Kiran Nusaiba,Nusaiba na ganin kiran Nafeesa ta kau da kai tare da yin tsaki, aranta take mita, "Kai wallahi Aunty bata kyautamin ba zata ja min raini." Ficewa tai fuu sai bangaren Anty Farida, tana shiga ta fara, "Haba Aunty Dan Allah, kina so yarinya ta rainani ne wai? Tun jiya kisa asata a group kin ki." Farida ta ce, "Oh ni kam dai, na bada number ta daman na Fada miki group din acike yake,dole sai wani ko wata ya fita kan asata Amman har na bada numberta." Nusaiba ta ce, "Ok shi ke nan Amman wallahi ko ta kira ma ba zan kara daukaba sai dai kawai ta gannta a group ta Kara ganin girmana ma,ba na son raini." Dariya Farida ta yi, "Allah dai ya shirya mana kai." Da Ameen Nafeesa ta amsa kan ta fice fuu kamar yadda ta shigo. ********Kwanaki nata tafiya har sati Amman ba asa Nafeesa a group ba, hakan ya Sa ta tsintar kan ta da fara rubuta wani littafi Wanda ta mai lakabi da SHI NAKE SO, kamar wasa ta Sa A group din su nan take taga an fara rububi tare da fadin cewa tayi ma su cigaba Dan Allah, har da ma su binta private suna hadata da Allah kan cewa labarin ya yi dadi ta cigaba. Mamaki Nafeesa take har cikin ranta shin itace take rubutu kamar yadda Nafseen ke yi? Shin itace ake ta rububi kan karanta labarinta,ji take tamkar amafarki domin salo da tsarin rubutun sak irin ba shi ta bi,tamkar shi ke tsara mata labarin, ba mai tunanin cewa sabuwar marubuciyace. Misalin karfe biyar na Ranar ba yan ta gama tura littafin rububin sharhi ya ragu tana kokarin kashe data da mamakinta kawai sai ganinta tayi tsimdin acikin wani group mai taken MARUBUTA. Nafeesa ba ta San lokacin da ta tashi tana murna da ihu ba tare da washe baki,kara kallon wayar tai tare da rungumarta, "Alhamdulillah, Allah na gode maka." Gyara zama tayi tare da wata nutsuwa ta mussaman ta shiga cikin group din, hira ake ba ji ba gani raha da wasa, wannan ya tsokani wannan wancen ya tsokani wancen abun gwanin sha'awa bin hirar ta fara yi ba tare da tace uffan agidan ba, sai dai ga Mamaki har yanzu bata ga alamar gilmawar Nafseen ba,Wanda ko wani suna ta gani sai ta kura ido Amman har yanzu bataci karo da shi ba. Ganin cewa da alamar duk yan gidan na da saukin kai ya bata damar yin sallama. Nafeesa "Assalam alaikum" Wani ba da ba a tantance mace ne ko na miji ba kasancewar ba suna ya ko ta ne amsa da "Wa'alaiki sallam Yan mata." Nafeesa ta yo reply da , "Ina Hini Yaya zan ce ko Aunty." Da alamar murmushi aka maido mata da amsa, "duk Wanda kika zaba kina ganin ya yi miki to ba tantama." Tsintar kan ta murmushin da ya bayyana har a zahiri tayi tare da fadin, "To ina ganin dai Yayane." "To, aiko kin canka na Yarda ke din fasihiyar marubuciyace." Ya maido mata da reply. Kan Nafeesa tai Reply Karaf...... Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 11 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM Wani ya yi sallama agidan. Alamar murmushi "Umm." Kawai Nafeesa ta tura sannan ta amsa sallamar da Mai suna Dan gidan Imam ya yi. Wancen ko ga duk alamu ya sauko domin bai kara fadin komai ba. Sauran Mutanen Gidan Mata da Maza duk sun fito sai hira ake, Nafeesa da surutu kamar wasa arana guda har ta fara sabawa da Mutanen cikin Group din Marubuta Amman gabadaya hankalinta na waje gudu damuwarta ta ga gilmawar Masoyin nata Amman shiru har ta fara fidda rai. Rufe data kawai tai domin lokacin sallar La'asar ya yi kamar yadda ta ga duk sauran yan group din na fadin lokacin sallah ya yi atashi ayi,har cikin ranta tsari da yanayin group din ya burgeta yau daya. Alwala ta dauro sannan tai sallah ta jima tana addu'o'i tana idarwa ta gyara zaman glass din ta afuska, sannan ta duba wajen littafanta gani tai kaf ta karance su duk da ta saba maimaici daman Amman taji aranta cewa tana da bukatar Sabi,hakan ya sa ta duba jakar makarantarta Kudin da Mammah ke bata na kashewa bata kashe take Tarawa daukowa tai taga dubu daya ne da ita a yanzu, tsaki ta yi, "Ni kam ma ko za su isheni in siyo oho." Janyo hijabinta tai tasa Wanda ya rufe mata jiki har kasan kafafunta,ta fito falo ba Mammah hakan ya bata damar nufan kichin domin ta San in bata falo to tana kichin. Jin alamun taku ya sa Mammah ta daga batare da Nafeesa ta isa gareta ba, Murmushi ta yi, "Ah Ammien Abhi ina zuwa da yamma haka? Ina shirin Sa Sabeer ya tasoki ki karba girkin ina son yin wani bincike." Nafeesa ta shagwabe fuska, "Ayyah Mammah agidan su Maryam zani in karbo littafina an bamu assignment kuma ma ba zan Iya ni daya ba tare zamu yi." Mammah ta ce, "To Allah ya kiyaye hanya,ki kula bana son shashanci kin sani ko? Ki kama kanki kamar yadda shigarki ta nuna kuma karki kai dare." Murmushi Nafeesa ta yi, "To Mammah in sha Allah zan kiyaye sai na dawo,Sabeer byebye." "Bye bye Anti ki siyomin chocolate." Cewar Sabeer ya na wasa Nafeesa na fita ta nufa gidansu Maryam da sallama da shiga,Aunty ce zaune afalo tana kallo, ta amsa mata da fara'arta, "Ah Yau Nafeesa ce agidan namu? Lallai munyi babbar bakuwa." Nafeesa na Murmushi ta durkusa, "Ina hini Anty?." "Lafiya lau Nafeesa fatan kina lafiya,ya su Mammah kuma?"cewar Aunty Nafeesa ta Amsa da, " Duk lafiya lau, Aunty Maryam fa." Kan Aunty ta bada amsa Maryam ta fito da Sauri, "Oyoyo Habeebbty muryarki naji kamar amafarki Ashe da gaske ke din ce." Aunty ta tashi tana, " kamar an shekara ba aga juna ba,ina jin dai miji daya zamu Baku." Dariya kawai Maryam da Nafeesa sukai. Nafeesa na ganin Aunty ta Shiga daki ta ce, "Habibbty littafi zaki rakani siyowa karya nawa Mammah nace assignment zan zo muyi, kin San in taji littafi zan siya zata hanani wai idona yanzu ma karatun aboye nake wallahi kuma ni ba zan Iya dainawa ba." Maryam ta ce, "Allah Habibbty da gaskiyar Mammah so ki ke ki rasa idanun naki gabadayane? Haba Dan Allah yakamata ki rage karatunnan fa." Rike hannun Maryam ta yi, "Dan Allah Habibbty kar Ku toshemin hanyar farincikina,karatun littafinnan kadai ke bani walwala da nishadi,Ina son karatun littafin Marubuci Nafseen kuma inda rai da rabo watarana sai na ganshi kuma na auresa muddin ina numfashi." Magana take hawaye na gangarowa daga cikin idaniyanta. Maryam ce tasa hannu tana goge mata ya yinda itama ta fara kwallan, "Ki daina Kuka Habibbty zaki gansa kuma zaki auresa in sha Allah,yanzu bara na fadama Aunty ta ba dreba motarta ya kai mu kasuwan ko?" Nafeesa ta ce, "Eh jeki dawo akwai labari Nima na zama marubuciya fa." Maryam ta fito tana dariya, "ai ke kam zaki Iya zama labarin ma da kansa ba mai rubutawan ba." Da key din motar Aunty Maryam ta dawo ahannunta yawwa, "Habibbty muje." Suna fita Maryam ta baiwa dreba key ita da Nafeesa suka shige baya tare da fadin ya kai su sabuwar kasuwa. Dai,dai gun masu saida littafi inda Nafeesa ta saba siya Maryam ta ce dreba ya tsaya. Aiko Nafeesa ta yi nasara zuwa domin sababbin littafan marubucinta har biyu sun fitofito,SO SHAMATAR ZUCI Da kuma YAN MAZA. Nafeesa ta kasa Boye farincikinta hakan yasata sai was he Baki take awajen. Sun gama siya ke nan Nafeesa ta hango shagon da ake saida Films, ta ce, "Habibbty zan siya film." Maryam ta kalleta cike da Mamaki, "Habibbty ke da bakya kallo me za ki yi da film kuma?" Harararta Nafeesa ta yi, "To na fara kallon daga yau,ni muje shagon cen mu siya." Binta kawai Maryam ta yi domin bata da tacewa. Da sallamarsu suka shiga shagon cikin fara'a kuwa mai shagon ya amsa. Nafeesa ta ce, "Films muke so Amman Wanda marubuci Nafseen ya rubuta." Murmushi mai shagon ya yi, "Ah madam an gama daman ko duk wa'inda ya rubutane Sabin fitowa Dan dazu da safe ma na karbo biyun nan,SIRRIN DA KE RAINA, NIDA KE MUN DACE, Da sauri Nafeesa ta karba tana mai yi masa godiya tare da mika masa kudin. Suna komawa Mota Maryam ta ce, " Yawwa Habibbty kin ce min kin zama marubuciya tayaya?" Dariya Nafeesa tai, "Ta inda kowa ke zama mana duk abin da zai hadani da Nafseen dina kusa gareni koma miye zan Iya ina tabbatar miki da hakan,na fara rubutu na zama marubuciya domin kasancewata da shi kawai." Maryam ta gyara zama , "Kice min kun hadu ma." "Umm haba dai ba ajima da sani ba,kuma kaf na duba cikin group din ba mai irin sunansa Abu daya na rike akullum jikina na bani cewa yana group din,ko da wannan aka barni ina jin dadi araina." Murmushi kawai Maryam ta yi domin bata da tacewa, sai da su kai Nafeesa har gida sannan suka koma na su gidan. ***Tun da Nafeesa ta koma bayan ta yi sallah kallo kawai ta Sa tanayi. Mammah ta ce, "ai da karatun littafancen gwanda miki kallonma wallahi." Nafeesa ba ta ce komai ba sai murmushi. Sai da Nafeesa ta gama kalle films din tsaf wajen 10 kan ta tafi daki ta kwanta, sha biyun Dare dai,dai ta fara mafarkin Nafseen na Online kamar da wasa ta farka,ji ta yi barcin ya bace a idonta gabadaya,wayarta ta dauko ta kunna,abun mamaki tare suka hau online awannan lokacin. Sallama ya yi agroup din marubuta kasancewar komin dare ba a rasa yan surutu aciki. Nafeesa....... Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 12 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM ☹️KO KU TUNAMIN JIYA NAYI MISTAKE NAKARASA 11 MAIMAKON 12 DAN KUNGA GUNTUNE🤣TO SHI KE NAN ABARSA A KARASHEN 11 DIN KAWAI YAU GA 12 😂😂ANATA MAGANA KAN SIRRIN DA NAFEESA ZATA FADAWA MARYAM KAR KUJI KOMAI SIRRIN NA NAN TAFE🥰🥰 Wayarta ta mutu,wani irin tsaki tayi domin batama lura da cewa chajin wayar ya kusa karewa ba sai ganin mutuwarta da ta yi adai,dai lokacin da tafi bukatar wayar Amman ba dama,ba ta San lokacin da kwalla ya fara zubo mata ba gashi ba nefa alokacin ji take tamkar An rabata da muradin rantane baki daya,kuka tayi mai isanta har barci ya dauketa batare da ta sani ba. Da Asuba kuwa Mammah na tashinta kan ta yo alwala sai da saka wayarta chaji, tsabar wayar ta kona mata rai bata kara bi ta kanta ba sai da ta gama shirin tafiya skul,ko kunnata ba tai ba, tasa acikin Jakarta kawai. Tare da suka fito da Mammah ,Ita tai Skul Mammah kuma asibiti shi ko Sabeer tun karfe bakwai ya tafi skul. Nafe daya suka shiga sai da aka sauke Nafeesa Kan Mammah ta huce asibiti. Nafeesa na Sauri zata shige Skul kicibis tai da taron mazaje sun mamaye kofar gate din makaranta, Mutansir ne da abokansa. Zagayeta sukayi suna wata irin dariya ta k'eta. "Ke Kin Isa ko? Kin yi shaharar Da har ni zaki Mara cikin mutane? Ni zaki tozarta yar matsiyata,makauniya,ke wai atunaninki Dan me nake sonki ne ma? Kin taba tambayar kan ki hakan? A kyau dai inajin Fatima ta dama ki,bare kuma azo maganar arziki yau dinnan zaki San ni kika Mara kan wani marubuci Mara aikinyi Da bai San kina yi ba, yau zan nuna miki ni wanene agarinnan, zan yi abun da ba Wanda ya isa ya fito nema miki hakki ko ahukuntani, kinfi kowa Sanin waye mahaifina bare kuma azo maganar waye ni karan kai na ." Cewar Mutansir yana zagaye Nafeesa, maganar yake cikin izza yana mai nuna mata hannu Kuka Nafeesa ta fara, "Dan Allah kayi hakuri kar Ku chutar dani, natuba Dan Allah kuyi hakuri ba zan kara ba,komai kace inyi zan yi Amman karka batamin rayuwata,ni Yarinyace ka jikaina da na iyayena karka cutar dani Dan Allah." Ta durkusa kasa tana mai bashi hakuri. Daga Mutansir har Abokanansa wata irin dariyar mugunta suka fara awajen. "Alokacin da ki ka mareni,kika ci min mutunci,kika tozartani kin tuna cewa ke yarinyace? Ai da Yarintartaki ki kai amfani ko? To ba shakka nima ayau da Yarintartaki zan yi amfani ta yadda ba wani namiji da zai so ki bare ya aureki, ko shi Wanda kike haukar akasan ina da tabbacin bare so ki ba,kin ga anyi biyu babu ko? Adalci daya zan miki, ki zaba tsakanin acide afuska da kuma umm ba sai na Fada ba ai kin gane, duk dai fuskar taki ma ba wani kyau gareta ba." Cewar Mutansir. Daya daga cikin Abokan nasa ne yayi magana, "Oga ya za ka mana hakane? Karka manta fa ita ba zabi tabaka ba ga mari ga fitsari in kai bazaka Iya ba ka bamu dama kawai mu far mata in an gama sai mu koma ga acide din kaga ba hanyar moruwa to kowanni bangare ke nan." Muntasir ya yi wata irin hamshakiyar muguwar dariya, "Mole walle ina kaunarka kwakwalwarka na matukar ja, tun kan ya Sa ido su bayyana Ku kai min ita hostel." Kara durkusa gabansa Nafeesa ta yi, "Dan Allah kayi hakuri karku batamin rayuwata Dan Allah, nace Dan Allah." Maganar take cikin kuka har ta shide ta kasa fadin komai ma. Daukanta sukai cikin hanzari tana ihu Amman ko kadan ba mai jinta domin sun toshe mata bakin, hostel din maza suka nufa dakin d Mutansir yake, ga dakin duhu baka ganin komai jefa Nafeesa sukai kan katifar tare da fita, Mutansir ya shigo yana wani banbankarewa. Kayan jikinta ya fara kokarin rabata da su,tun tana motsi har ta yi shiru illa ajiyar zuciyar da take..... Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don cigaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 11 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM 🤣🤣DAN ALLAH KAR KUYI KORAFIN GAJERANCIN FEJIN NAN Ce ta amsa tare da fadin, "Wa'alaika salam." Batare da ta lura da sunan ba. Jameel (Nafseen) ya yo reply da , "Ah ya naga kamar bakuwa muka yi agidanne." Nafeesa ta tura da alamar dariya, "Tab ai ko ni ba bakuwa bace nafi wata agidannan fa, ko kai na rigaka." Kamar yadda tai dariya Shima hakan ya yi, "Kin San Bamai? To indai kin San Bamai shi kan shi na rigasa zuwa gidannan." Xayyeesherth ce ta katse masu magana da, "Ah Ah Yaya Jamilu adai rage mana." Maganar Xayyeesherth ne ya baiwa Nafeesa damar kallon sunan da kyau kamar yadda take tsammani Jameel Nafseen ta ga an rubuta,batare da ta Ankara ba wani irin farincikine ya mamaye zuciyarta, ihu ta fara tana tsalle da rawa ta ma rasa me za ta yi illa rungumar wayar da tai tana rawa da tsallenta. Xayyeesher ya maidawo da Reply, "Ke Xayyishatu ina wasa da ke ne? Dare ya yi maza jekiyi barci manya na magana kina sako baki." Dariya Xayyeesher ta yi, "Aradu ban kwanciya yau kam sai naga ka sauka tukunna nima." "Iyee,ina fadi kina fadi to kinyi abakin chocolate din ki." Cewar Nafseen. Alamar kuka ta tura, "Haba Yaya Jamilun ba ma haka,gudnyt walle na tahi sai da sahe." Ya ce, "Yawwa Yar Albarka,Allah tashemu Lafiya." "Byebye adai kula ban da...... Bata karasa ba ta Sa emojin gudu. Dariya ya yi, " Allah ya shirya mana kai in ki ka Shiga hanuna zan baki mamaki." Nan take Xayyeesher ta sauka tana Dariya, Nafeesa kuwa tunda taga sunansa ta ma kasa maido masa da reply kallon sunan take karayi da Mamaki shin daman da gaske zata yi Magana da Nafseen aduniyarnan har suyi wasa da dariya? Ga yadda tai tunani Sam ba haka yake ba, tunaninta zai kasance mai girmankai da jijji da kai amman ko Kadan hakan bai samu ba. Mentioning Sunanta Yayi ganin cewa ta bace cikin gidan, "@Nafeesa ko dai kin bi sahun Yarinyarcen ne kinyi barcin?" Wani irin bugu taji zuciyarta na yi ganin yadda ya ambaceta cikin bazata,tana kokarin yi masa reply kenan... A yi hakuri👏bana da chajine Amman in sha Allah gobe zan yi typing awadace,Ku taba wannan Ku lashe😘😘Ina yinku masoyana son so fisabillillah🥰 Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 13 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM 🤦‍♀️🤦‍♀️ALLAH SARKI MASOYAN ASALI ATA HAKURI DANI RASHIN TYPING KAN LOKACI KUN SAN DALILI KE JAWO HAKAN😁NASAN ZAKU MIN UZURI KUMA HAKAN BA ZAI HANA NI GANIN RUWAN COMMENTS BA🥰 GAREKU MASOYAN NAFEESA FATAN BURINKI YA CIKA😁 A dai,dai lokacin da yake shirin yi mata mai gabadaya Nafeesa tai wata irin kara mai kama da na damusa,damkosa tai kawai ta fara jibga ba ji ba gani,jin ihunsa ya Sa sauran mazan da ke waje shigowa ko ajikinta kamar batai komai ba, dukansu ta farayi bilhakki da gaskiya,gabadaya sunyi Jina,jina ba kwari bare karfi,kan kace me har sun fara Jan jiki suna tserewa ahankali,gabadaya sun tsorata "anya kuwa Nafeesa ba namiji ba ce,in ko macece to ba tantama aljanace."abun da wani cikinsu ke ta fada kenan shi ko Mutansir da yafi kowa jibguwa nan take ya sume awajen. Sai da ta gama jibgarsu kowa ya tsere illa Mutansir da ke kwance ta dawo hayyacinta kallon jikinta ta farayi awani irin yanayi daga ita sai kananun kayan ciki, ta bi dakin ko ina da kallo sai shegen duhu da kyar ta kura ido sannan ta fara hango kayanta gefe guda,cikin sauri ta karasa wajen tare da dauka tana sawa,har yanzu bata fahimci meya faru ba bare abun da ya kawota dakin hakan ya Sa taketa kara hanzari wajen ganin ta bar dakin, kicib da mutum akasanta kallon da zatayi ta ga Mutansir,nan take hawaye ya fara zubo mata, jakarta ta kara hangowa gefe guda ta dauka ficewa daga dakin tayi cikin kuka, abun mamaki duk abun nan da ya faru glass dinta bai bar idonta ba koda na second daya. *****Tana fita ba inda ta nufa sai bakin titi, tsare mai Nafe tayi kawai ba inda ta nufa sai gida, Mommah bata nan Sabeer ma na Skul duk ba su dawo ba, dakinta ta huce ban da kuka ba abun da takeyi azuciyarta tana fadin, "Kaddarar rayuwata ke nan Wanda ke so na baya sona Dan Allah gangar jikina yake so,ni kuma Wanda na ke so bai San inayi ba,ban San ma ko zai soni ba, da yanzu Mutansir ya Lalata min rayuwata shi ke nan." Fashewa ta karayi da kuka can kuma ta tuna da yanayin da ta tsinci kan ta, atsorace ta tashi ta zauna tana mamakin shin to ma wai "meyasami Mutansir ne? Kar dai mutuwa ya yi? Waya hanasa ketamun haddi ina sauran Abokan nasa Shin wai me ke faruwa dani ne? Kokarin fara tuna abun da ya faru a islamiya tayi nan take kanta yafara juyawa duhu ta fara gani bata gane komai nan take wani irin gawartaccen barci ya yi awon gaba da ita. Sai karfe biyu Mammah da Sabeer suka dawo tare ba karamin Mamaki Mammah taji ba ganin Gidan abude suna Shiga kuwa ta nufi dakin Nafeesa kamar ta sani gata nan kwance "ga duk kan alamu tana wannan barcin ne data saba aduk lokacin da aka bata mata rai." Abun da Mammah ta Fada aranta ke nan tana kallon diyartata cike da tausayi. Kamar wasa har dare Nafeesa ba alamar motsi atattare da ita, Mammah ta zo har ta gaji da dubata lamarin ya sha bambam da Wanda tasaba yi. Addu'ah kawai Mammah ta shafa mata tare da janyo kofar ta fita. *****Wa she Gari da Asuba Mammah na tashi ta nufi dakin Nafeesa,tana nan dai yadda aka barta, ba Dan tana numfashi ba kai kace mutuwa tayi,Abun har ya fara damun Mammah gashi Abhi yau zai dawo hakan ne ma ya Dan sanyaya mata zuciya tafi minti biyar tana kallon diyartata kan daga karshe ta fita. Karfe uku na yamma dai,dai Abhi ya isa. Da Murmushinsa Ya shigo gidan,da gudu Sabeer ya rungumesa, Mammah na fadin, "Barka da dawowa Oga." Maganar take cike da fara'ah. Abhi ya dubi ko ina ba alamar gilmawa Nafeesa. "Niko wai Ina Ammynane?naga kowa Amman ba ita." Cewar Abhi ya na kara waige-waige. Mammah tai murmushi, "Ammynka ba Lafiya barci take,." Abhi ya ce, "Ayyah shiyasa gidan ba dadi Sam gaskiya sai na tada gimbiyata muje." Mammah batace komai ba kawai suka bi bayan Abhi ita da Sabeer, suna shiga Mammah ta fara kwalla. "Tun Jiya take barcinnan bata farka ba." Cewar Mammah cikin yanayin damuwa. Abhi ya ce, "Subhannallah, Shine baki fadamin ba? Kuma baki kai ta asibiti ba?" Mammah ta ce, "Na dubata Amman ba abun da asibiti za su Iya mata addu'a dai itace asibitin da maganin, tanayin hakan mun sani Amman wannan yanayinsa dabanne sai dai muta addu'an kawai." Sam Abhi bai ji dadin lamarin ya ma kasa magana kawai ficewa ya yi, azuciyarsa yana matukar tausayin diyarnan tasa domin tunda tazo duniya take fuskantar kalubali kala daban daban iri iri. Addu'o'i da saukan Al'qur'ani kawai suka Sa agaba. Kwannan Nafeesa shida kwance ba motsi. ****wani bangaren kuwa na Mediya cikin Group din Marubuta anata hira da ban dariya,Mussaman Nafseen da ya Sa yan Matannan d ya Sa su agaba da tsokana, kamar wasa yana kokarin tagging din gaurayen yan matan gidan, sunantane NAFEESA ya fara fitowa awayarsa batare da Sa komai aransa ba kuwa ya danna kan sunan. A dai dai lokacin Nafeesa.......... Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 14 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *UMMU AFFAN* *MARUBUCIYAR YAFI DARE DUHU* *INA GODIYA MATUKAR GASKE,ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA*❤️❤️ *SADAUKARWA GA MASOYAN ASALI BASA FUSHI DUK KWANAKIN DA ZAN DAUKA BNYI TYPING BA ZARAN SUN GANI ZASU SAMBADOMIN SHARHI INA YINKU WALLE*😘😘 Mrs Mubarak Belar maxare(Maman tima) Asma'u aji Ibrahim Fatima Zahra Fiddausi Mrs Auwal Forever. *** Ta farka , Hamdallah Mammaah ta fara. Cikin farinciki ta fita. Maryam ta rike Nafeesa, "Sannu Habibbty kin tashi?" Kan gadon ta fara bincikawa ta nemo glass dinta tare da kafawa a idonta ta gyara zaman. Da Murmushi Nafeesa ta kalleta , "Na tashi Habibbty yaushe kikazo?" Maryam ta ce, "Tun Safe kinata barcinki abunki." Waige,waige ta fara, "Umm Habibbty ina wayata naji ana kirana,ki dubamin ita." Maryam ta tashi tana, "Oh keda kike barci ina zakiji wani kiri ni kaina banji Ba bara na duba jakar nan taki." Cikin sa'a kuwa ta Ciro wayar tare da mik'a mata, "To Madam ga shi wayar ma da akashe take, ko ta ina ki ka ji kiran mu ba mu ji ba oho." Murmushi kawai tayi tare da kunna wayar kamar yadda taji aranta cewa Jameel na nemanta hakan ya sa ba inda ta fara lekawa sai Group din Marubuta, Message ko na farko d ya fara zuwa mata shine wan da sahibinta ya yi tagging dinta. Tsayawa kallon message din tayi kawai tana sakar murmushi ba tare da ta Ankara ba. Shigowar Mammah da Abhi ne ya katse ta daga duniyar ta shige acikin kankanin lokaci. Abhi ya karaso gareta tare da dafa mata kai, "Ammienah ya jikin dai, barcin nan na lafiyane kuwa?" Kallon agogon wayarta ta fara yi sannan ta dago ta kallesa, "Lah Abhi Yaushe ka dawo yau date 30 fa." Cikin fara'a yake fadin, "Eh mana nazo kinata sharban barcinki nace ko takwararaki ce tazo kuke hira taki karewa kun manta damu." "Abhina ke nan, ai da naga Kaka ko ba zan dawo ba yasin sai dai inyo maku byebye." Cewar Nafeesa tana kokarin latsa wayarta Abhi Yayi Murmushi, "Wato dai ba za a ajiye wayar nan ba ko? To maza a ajiye ayi wanka ai sallah sannan aci abinci." Shagabewa ta yi, "Umm Abhi nemana ake bara ince masu ina zuwa tam." Shafa kanta yayi yana, "Yawwa Yar Albarka Ammiena,bara mu barki da Maryam ta tayaki kintsawa Muna falo in kin gama kya fito ki karbi tsarabarki." Girgiza kai tare da murmushi kawai Nafeesa tai. Mammah,Abhi tare da Sabeer suka fita, sai Nafeesa da Maryam. Reply tayowa Jameel da , "Tab Yasin ni ba gauruwace ba,Dan dai bana da lafiyane Amman da yanzu nayi jajjagen miyar Kuka da kai." Message din na Isa Yayo murmushi , "ni ko zan jira har ki samu sauki domin inga yadda ake jajjage da mutane." Dariya Nafeesa tai wadda sai da ta fito fili ta ce, "Bara inyi wanka in dawo yau zanyi caskale da wani agidannan." Da fadin hakan ta rufe data Amman har yanzu murmushi ya kasa gushewa daga fuskarta hakwarannan kamar mai tallan makilin. Mamaki ya sa Maryam yin shiru tare da tafiya dogon tunani,domin tun da take bata taba ganin Nafeesa Cikin farinciki kamar na yau ba,duk da kasancewar kullum cikin murmushi take Amman bata cika washele baki da sunan tana dariya ba. Nafeesa ce ta dakawa Maryam duka abaya, "Dilla ni kin tafi wani tunani rikeni in tashi jikina ba kwari." Cikin Ranzana Maryam tayi tsaki, "To ai ke dince naga kinata wani kyalkyala dariya tamkar sabuwar kamu wai miye Sirrinne?" Dafa Maryam Nafeesa tai tare da kokarin tashi, "Sirrin na da tsawo Dana baki labari." Maryam ta riketa ta karasa tasowa tana, "Ina binki fa bashin wani sirrin ga wani ma na yau ni gaskiya na zaku inji sirrukannan Dan kwanakinnan salon ya chanja gabadaya." A kofar toilet din ta tsaya, "In Lokacin ki San Sirrin yayi zan sanar da ke batare da kin ankaraba Amman ba yanzu ba." Ta sake mata murmushi akarshen maganar tare d shigewa cikin bandakin. Wanka tayo tare da dauro alwala sannan ta fito tayi sallah, gabadaya yau yanayin Nafeesa ya chanja ba Magana illa murmushi da ke bayyana afuskarta. Cikin Shigarta ta Farar doguwar Riga tare da mayafinta ta fito hannu rike Dana Habibbtynta. "Oyoyo Ammien Dady,kullum kara girma da kyau Babyna ke yi." Cewar Abhi. Rufe fuska da hannu Nafeesa tayi tare da shagwabewa , "Uhum Abhina ni ka daina." Abhi ya ce, "To, to na dain a Ammien Abhi Zo in baki abinci da kaina nasan Mammah ba wani kulamin da ke take ba."karasa maganar yayi tare da bude hannunsa alamar tazo. Sabeer ya sa kuka, "Mammah kin gama Abhi ni baya ban abinci abaki Amman zai baiwa Aunty ko?" Mammah ta ce, "Rabu da su Sabeer dina Dadinta ma kowa ya san kai ne Auta ita kuwa gardiyace." Dariya Sabeer yayi yana kallon Nafeesa tare da yi mata gwalo. Nafeesa ta kalli Abhi , "Abhi ka gan su ko?" "Sharesu ke kadai zan ba tsaraba da Maryam,Amman Sabeer kam da Mammahsa sai kallo." Fadin Abhi. Gwalo ita ma tai wa Sabeer kamar yadda yayi mata. Gabadaya dariya suka sa afalon. Abhi ya fara bawa Nafeesa Abinci,kamar magani take karba cikin shagwaba harda guntun kuka, can ta tuna da tacewa Sahabinta tana zuwa. Azabure ta mike batare da ta ce komai ba ta shige dakinta aguje. Tsayawa kallonta kawai sukai sai gashi ta dawo hannu dauke da waya. Abhi ya ce, "Oh wannan waya dai, to zo ki karasa abincin ko?" Cikin shagwaba take fadin, "Um umm ni na koshi Abhi inna kara amai zan yi fa." Murmushi yayi, "Allah dai ya shiryamin Ammienna." Itama Murmushin ta yo masa tare da bude wayarta ta shiga WhatsApp . Kamar Yadda take tsammani Reply Din sa ta fara gani. "Hhhhh Lallai yau ba samu gamona ni za ayi caskale dani,ni da nake da mutane yau za ayi Dani,Oh shiyasa nakejita jin tsammi maza kam aje ayi wanka." Cewar Nafseen. Nafeesa ta gyara zama tare da fadin, "Hhh To ai dai gani nadawo ba kai ne zakayi Fada da jarumar mata ba? Muzuba mu gani,kuma ysin ni bani tsami sai dai wani." Ta kare maganar tare da murguda baki tamkar yana wajen. Cikin sa'a kuwa yana Online ya maido mata, "Yo za mu gani dai Amman da kwai yan adawata agidannan sosai gwara muje PC kin ga ko kin kayar dani ni daya zanji kunya batare da wani yaji ba." "Hhhhh To Ashe dai ana tsoro, Wanda ya Riga zuwa Pcn ma shine Jarumi." Reply din Nafeesa. Jameel.... Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 15 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM _*SADAUKARWA GA DUK MASOYAN JAMEEL (Nafseen) aduk in da suke🤗Hadda nima Yayana,Za mu yi yadda mukeso da Fejinnan❤️KAI ARADU MA HARDA MAKIYANKA😅KU KARANTA KYAUTA NA KU NE,SON SO FISABILLAH ZUCIYA DAYA❤️🙌🏻*_ Jameel ne yafara yi mata magana ta private , "Assalam Alaikum, tun yanzu gashi na fara cin nasara." Bata Rai Nafeesa tai cike da yanayin shagwaba tamkar yana ganinta ta yo masa reply, "Umm umm Yasin ta katanga ka diro ni ko ta kofa na Shigo nice dai Jarumar." Dariya yanayin maganarta ta tabashi domin yanayin shagwaba karara ya bayyana. Murmushi Ya yi , "To! To!! Yanzu fadamin tsakanin ni da ke waye Jarumin? Da sauri Nafeesa na wangale baki ta ce, " Nice." "Iye Cuwacuwa kenan kin yi sonkai Amman shi ke nan ba komai aje zuwa." Cewar Nafseen. Nafeesa ta ce, "Umm ni kam. Nafseen yace "Umm ke kam me"? Tace "a'a bance komai ba" yace "faɗi gaskiya zan siya miki sweet" nan take tace "haba kamar wata yarinya" yasa Alamun dariya "to da wace in ba yarinya ba"? Jin yace hakan kawai sai ta sa Alamun tafiya kamar dai taji haushin kiran ta da yarinya da yayi, nan take ya shiga lallaɓa ta har yana cewa "haba jaruma ya kike haka ne kamar ba jaruma ba"! Ai kuwa nan da nan ta saki wani murmushi a zahiri saboda kiran ta da jarumar da yayi ya sosa mata inda ke mata ƙaiƙayi nan take tace "umm umm to ka yarda cewa ni jaruma ce yanzu"? Yace "ai ya zama dole na yarda tunda naga kin nuna jarumtar" cikin mgnr sa sai ya haɗa da alamun gwalo a nan sai ta ƙara cewa "umm wato wayo zaka min shine ka kira ni da jaruma saboda ka lallaba ni ko"? Yace haba dai wane mutum, ai da gaske ke jarumar ce" tace "to shikenan kaci sa'a da yau idan na tayar da rikici sai ka zo da ƙafar ka ka bani haƙuri zan haƙura" yayi murmushi zuciyar sa cike da mamaki ya fara zancen zuci yana cewa "shin wannan yarinyar me take nufi da cewa sai naje da ƙafa ta na bata haƙuri" nan zancen zuci ya fito fili yace "koda yake meye ma zan tsaya wani zancen zuci muje zuwa dai koma menene zamu gani idan muna raye" Ganin shiru bai yo reply ba yasa Nafeesa fadin, "Ko dai kaji tsorone,Hhhh Gaskiya ni Jarumar gaskiyace." Tana tura masa karaf Abhi ya kwace wayar batare da taga reply din Sa ba. "Haba Ammie na tun tuni kina kan waya kamar wata mai aikin office? ga Maryam kin barta gaho ko? To na kwace wayar nan ba zan maido miki yanzu ba." Cewar Abhi. Nafeesa ta zaro Ido kan Maganarsa ta karshe cewa ba zai dawo mata da wayarba,,nan take ta tuno Nafseen, lokaci guda kanta ya fara Sarawa ta fara gani bibbiyu, zata..... Urs Xayyeesherth https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 16 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *SADAUKARWA GAREKI SISTER ZEEY YAR MUTAN ZAZZAU,ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA INA YINKI WALLE HAR CIKIN RAINA🥰* *TUKWICI GAREKI MY MAREEYA😍CAN'T LOVE YOU LESS ADDU'AHTA A KULLUM BAI WUCE ALLAH YA BAKI LAFIYA MAI INGANCI BA* 🤔🤔 *SHIN NI KADAI NA FAHIMCE CEWA A LAMARIN NAFEESA SURUKANNA NA DA YAWA,NA DAYA BA SUMA TAKE BA,KUMA BA BARCI TAKE BA🤔SHIN ME TAKE??* Zata fadi Maryam ne ta riketa Abhi ko yana amsan wayan tafiyarsa yayi bai ma tsaya ba, Maryam ne ta daga ta suka shiga daki sai kuka Maryam dinma take ta kan yi, aiko abin data sani shi ne ya faru Nafeesa faduwa tayi tamkar wata matacciya gefen Idonta sai hawaye ke fita ga shi bata numfashi,Maryam ko tasa niyyan bazata fada ma su Mammah ba sabida Ita a ganin ta yaushe suka Fita a damuwa kan Nafeesa kuma su kuma komawa gaskiya gara suyi farin ciki suma, ta dauka alkawarin bazata fada ma kowa ba in sha Allah har sai Allah yayi farkawan Nafeesa. Maryam Wayan ta,ta dauka ta kira Umminta ta mata bayani sosai kuma ta fahimta itama anan ta ce mata zata kwana da Nafeesa Ummi ta amince Mata ta ce, " Zan fada ma Abban ki kinji." Maryam ta ce, "thank you Ummi na shiyasa nake kara sonki." Ummmi dariya tayi ta ce, " yadda Kike a Zuciyata haka Nafeesa take kinga ko ba banbanci ko?" Maryam ta ce, " hakane kan Ummi ", Ummi ta ce to sai anjima ki kula da ita sosae kinji Maryam tace in sha Allah ummi." sallama sukayi ummi tadan wayan aranta ta ce, " bansan mesa Allah ya daura min son Nafeesa da tausayin ta ba ya Allah ka yaye ma wannan yarinyan ka cika mata burinta in dai shine mafi alkairi." Tana cikin wannan tunanin Abba yadawo ya tadda ta ya ce, "Lafiya kuwa Ina ta magana shiru?" Ta ce , "hmm Wlh ban san ka dawo ba." " haba uwar gida tunanin me Kike hakane Ina Maryam naji gidan shiru anan Ummi ke ba shi labarin abin da ke faruwa shima shiru ya yi ya ce, " wlh kin ga duk abin da zanwa Maryam Zanyi ma Nafisa,Allah zai cika mata burinta kuma zai yaye Mata." da Ameen ummi ta amsa suka wuce ciki . Abangaren Maryam kuwa bayan ta ajiye wayan fitowa tayi falo Mammah ke tambayarta ina Nafeesa Maryam me hanaki tafiya har yanzu? yanzuma fitowa nayi nace Maki yakamata ki koma Gida dare ya yi." Maryam ta ce, "Mammah Zan kwana a tare da Nafeesa harna Kira Ummi na fada mata kinga bata da lafiya kuma Abhi yadawo yakamata a samu Mai zama kusa da ita shine na ce zan kwana a tare da Ita." Mamma bata San Erin dadin da taji ba koba komai Nafeesa tayi dace da kawa ta gari bata San da bakin da zata godema Maryam ba. "Ngode sosai da Erin abin da Kike ma Nafeesa a lokacin da mutane da yawa suke kallon matsalanta kaman ba gaske ba amma ke kin tsaya akan Al,amarinta Maryam nagode sosai, Allah saka miki da alkairi ."tana yi tana zubda kwalla Maryam itama kukan ta Fara "Mammah Dan Allah ki daina Fadin haka ki daina kuka." hannu ta sa tana goge hawayen dake zuba a Idon Mammah, "Mammah plzz you have to and rest, stop crying kinga Abhi yadawo zan kula da Nafeesa kar ya ga kina cikin damuwa." Mammah ta ce, "to Maryam thanks so much god bless you let me letf but before I have to see Her." Maryam ta ce, "Ok Mamma amma bacci take a Haka suka shi ga dakin tare Mamma taje ta zauna a gefen Nfeesa addu'ah sosai ta Mata kan ta fita a dakin . Maryam ta kara gyara. Mata kwanciya tana, " Nafeesa Allah baki lafiya in sha Allah burinki zai cika,kuma komai ma zai wuce." . Abangaren napseen kuwa, replied yayi da look at that baby girl nifa bana tsoro sai dai aji tsorona Dan kiji ." ya tura tare da emoji na gwalo amma shiru bega reply nata ba kuma ga hiran nasu yana sashi nishadi shirun daya ji ne yasa ya Kara tura "yeeee itane Ashe taji tsoron ma.. still shiru yace "aa lafiya kuwa ina ga she have a lot to do Bari nima na sauka ."nan ya sauka. Abhi ko yana amsan wayan ya kashe shi baki daya yaje ya ajiye sai da dare yayi yadawo daga mosque shida sabeer yake cewa , "Ammyna lafiya kuwa bata fito ba ga lokacin dinner ma yayi." anan mamma ke gada masa ai bacci take ta yi ma Maryam ma zata kwana da ita nan da nan hankalin Abhi ya tashi meya faru da ita mamma ta ce. "aa ba komai kasan dai yau bata jin dadi ana bukatan ta huta ai karka damu ba komai." amma Abhi dai hankalinsa bai kwanta ba ya ce , "to bari na dubo ta amma nan suka wuce dakin Nsfeesa suka ganta tamkar ba rai a jikinta amma tana numfashi Abhi ya ce, " Maryam Allah miki albarka ." da "Ameen" ta amsa Abhi ya ce, "to kin ga tana bukatan Hutu amma ta biye ma waya kinga ma gara Dana amsa ."Maryam kirjintane ya buga taji wani hawaye na bin face nata aranta tace "Allah sarki Ahi besan rashin wayan shine ya jepata a wannan yanayin ba amma in sha Allah zanyi kokarin ganin abhi yadawo Mata da wayan amma dole saita hakura da kanta dole zan bata hakuri ta danne duk abin da zataji tayi ma Abhi biyayya ." Fita su kayi Mamma ta ce, "Maryam ta fito suyi dinner haks nan ta fito amma duk hnklnta bayi jikin ta . Nafseen kuwa ta bude data tare da zumudin ganin Erin amsan da samu wajen Nafeesa amma me sai yaji shiru Kawai ji yayi ransa ya baci ma ko group din be shiga ba ya rupe datan sai kuma ya fara tunani shi kadai "to meye ma bashi na damuwa har haka yayi kokarin cire tunanin ta aransa amma hakan be samu ba Sabida Nfeesa Yarinya ce shagwababbiya Edan yana tuna Erin yadda take masa shagwaba sai yayi murmushi kuma sai yakara cewa meke damu na ne Haka to mema zaisa na damu haka, Abu daya yake tunawa salon yarinya yana matukar birgesa gata yarinya Amman in tai wani abun babbama ba zai ba, duk abunnan bai taba ganin hotonta ba kuma bai taba tambaya ba Amman yana sawa aransa cewa kyakkyawace ajin farko kamar yadda halinta da kalamanta suke. Maryam bayan tadawo addu,a ta karama ma Nafeesa ta kwanta aiko can cikin dare wajen 2:00 taji nafeesa na "Abhhi Dan Allah kayi hakuri kabani wayana na san Nafseeen ya min reply." Nan take ta fashe da kuka , Maryam ta riketa. "Abhi ka taimaka min kaji Dan Allah Wallahi rabani da wayannan kaman Ana min baraxana da rayuwats ne Abhi plxxx ." Maryam ta ce, "haba Nafeesa ki dawo hankalinki mana Wai yau ke ce Kika tashi ba addu',ah a bakinki keda Kike yima wasu fada akan addu'ah amma ace yau kene kika tashi ba ita?" nan Nafeesa ta Fara share hawaye ta ce, " Astagfiirullah addu'a ta fara jerowa tana hawaye tana tuna abin da ya Faru Wai da gaske Abhi ya amshi wayana gaskiya bazan iya jure hakan ba. tana wannan tunanin Maryam tace , "Mata babe oya a tashi a yi sallah ko nan ta Mike tayi alwala ta rama dukkan sallanta ta dear tana edarwa tasa kuka tace, " Maryam meya hanani tafiya kuma Wai da gaske ne Abhi ya kwace min wayana Maryam Idan ya baki ki bani ne Dan Allah kar kimin wasa kinsan yadda nakejikuwa?" Maryam da hawaye suka cika mata Edo ta ce, ' nafeesa ki kwanta ki huta zamuyi maganagobe kinji." kuka Nafeesa takara sautinsa "plss Maryam kibani amsa Dan Allah." Maryam ta ce ,"promise zan fada Miki gobe amma yanzu ki samu ki huta da kyar Maryam ta lallaba nafeesa ta hakura akan sae gobe. Wa she gari Ana kiran asuba Nafesa ta Fara tashin Maryam Sabida ita bacci ko na second daya be dauke ta ba hasalima hangowa take Erin amsan da Nafseen ya tura Mata gobe Maryam na bata wayan shi zata fara dubawa nan suka yi alwala sukayi sallah Nafeesa ta ce , "to ban wayan Habibbty." Maryam ta ce, "baby girl ki saurari abin da zan fada Miki ." Nafeesa ta ce , ,"to ban wayan sai muyi maganar." Nafeesa Maryam ta fada cikin raunanniyar murya Mai dauke da damuwa nan da nan Nafeesa ta ba da attention dinta wa Maryam Sabida tasan abind a zata pada Mata yanada mahimmanci. "inajinki baby girl da farin cikin ki Dana su Abhi wanne kika fi so ?" Cewar Maryam. Nafeesa ta ce, " Na su Sabida suma koda yaushe suna hana Kansu farin ciki domin suga nasamu." Maryam ta ce to, " yanzu suma suna bukatan taemakonki da kuma kulawanki ." Nafeesa ta ce , "akan me kenan ?" Maryam ta matso kusa da Nafeesa tana , "Babe dole zaki yi hakuri da amsan wayan ki wajen Abhi Sabida farin cikin sa domin yana kallon kaman wayan na hanaki samun Hutu dole ki yadda da abin da yayi kiyi hakura ki danne damuwanki a gabansu dukda nas an da ciwo kan amma kiyi hakan Saboda su nasan edan kinyi haka Abhi zaiji dadi kin bi magna din sa yadda Kike nuna so a wayan ki nuna hakan tamkar be dameki ba Edan har Anga hakurinki wayan zai dawo wajenki soon." Tunda Maryam ke mgnan nafesa kafeta tayi da ido ko kiftasu batayi ga farin cikin ta gaban iyayenta wanne zata bi? Nafeesa ta... 😍😍MASOYA ASANI CIKIN ADDU'AH IN ANYI SALLAH PLEASE❤️TANAN NABI BUKATAR SOYAYYARKU GARENI,ALLAH BIYA MANA BUKATUNMU NA ALKAIRI👏 Urs Xayyeesherth❤https://www.facebook.com/106494781436168/ _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE 17 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *WANNAN FEJIN NAKINE DOTE HAUWA SULAIMAN😍😍BARKA DA KARA SHEKARA,INA MIKI FATAN NASARA ARAYUWARKI,MIJI NA GARI,ILIMI MAI ALBARKA INA YINKI IRIN SOSAI DINNANDINNAN*❤️ *TUKWICE GAREKI ANTYNA FARIDA MUSA (SWEERY)😍IDAN BABU KE KUSA DANI DOLE NAYI KUKA MATUKAR GASKE,BA ZAN IYA MIKI SO KADAN BA SON SO SABIDA ALLAH❤️ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA* ****** Nafeesa Ta Fara Kuka, "Habibbty Ban san ya zanyi da raina ba wallahi,kin fi kowa sanin muradin raina, Amman ba yadda zanyi farincikin Abhi da Mammah ya zarce nawa koda kuwa karshen rayuwatane zan ba su farinciki,na hakura da wayar in sha Allah na hakura." Ta rike hannun Maryam gam tana, "Zasuyi Farinciki ko Habibbty? Indai za suyi ya fi nawa mahimmanci na hakura kinji." Tsabar Tausayin Nafeesa ya gama mamaye zuciyar Maryam bata San lokacin da itama ta bige da kukan ba, sautin kukansu kadai ke tashi adakin, Nafeesa ta fara sharewa Maryam Hawayen tana, "Habibbty ki daina kuka kinji,bana so ina saku damuwa, In sha Allah zan jure dukkan radadin da zanji Dan ganin na faranta maku ki daina kukan kinji Nima na daina, Amman fa..... Kawai sai ta kara fashewa da kuka ta kasa karasa maganar da za ta yi. Maryam ta ja dogon numfashi kan ta ce, " Yawwa Habibbty Kinga mu yi shiru kar Mammah ta gane ko." Nafeesa ta kakalo wani murmushi Wanda da ka gani zaka fahimci cewa na karfin haline. Maryam ta ce, "Yawwa wai meya farune Ranar Kinje Skul Amman ban ganki ba." Nafeesa ta tsaya Chan kuma sai ta ce, "Ranar! Hmm Mutansir ne." Sai kuma tayi shiru. Maryam ta zaro ido tare da fadin, "Mutansir me? Me ya miki? Fadamin Habibbty." Abubuwan ne suka fara dawo mata cikin wani yanayi kamar mafarki,kan ta ne ya fara juyawa ta fara kallon Dakin Uku Uku. Tallefa kanta tayi da hannunta na dama tana, "Maryam ba zan Iya ba ki bar maganar nan kai na zai fice ni ban san meya faru ba." Tana gama fadin hakan ta kwanta awajen kamar yadda ta saba ba barci tayi ba kuma ba suma tai ba. "Innalillahi-wa'inna-ilaihir-raji'un." Abun da Maryam ke Iya furtawa kenan yayinda hawaye ke saukowa daga idanunta. Riketa Kawai tai tamkar wata jaririya tana kallonta gabadaya ta ma rasa me za ta yi,ba abun ta kira Mammah ba hankalinsu ya tashi. Kuka take bilhakki da gaskiya tausayin Nafeesa ya gama mamaye zuciyar Maryam ,ji take inda tanada dama da ta dawo da radadin da Maryam ke ji cikin jikinta. Chan kuma ta tuna da maganar Nafeesa, "Habibbty ba abun da ya gagari ubangiji aduk lokacin da wani Abu ya samemu addu'ah ce Kawai mafita koda ace da maganin abun ta addu'ah na kan gaba domin itace babban magani ga dukkan mumini." Tana gama tunano maganar Nafeesa ta share hawayen da ke fuskarta kan ta fara jerowa Nafeesa addu'o'i daga bisani ta dauko gorar ruwa ta fara tofa addu'o'in ciki. Bayan ta kammala Addu'o'in dago Fuskar Nafeesa tai tare da shafa mata ruwan afuska,Sanan ta bude mata Baki kadan ruwan ya samu damar shiga. Bayan ta gama shafa mata tagumi tai kawai tare da zubawa Aminiyarta ta ido,acikin zuciyarta tana rokon Allah da ya tada Nafeesa ayanzu batare da kowa ya fahimci halin da suke ciki ba. Kamar wasa Nafeesa ta kusa yin Rabin awa kwance ba motsi ba alamar motsi sai numfashi. Maryam ta rasa abun yi gabadaya zuciyarta ta jagule kwatsam ta hango inda littafan Nafeesa yake,da hanzarinta ta karasa wajen aiko ta ci Karo da Al-Qur'ani kamar yadda ta aiyya na aranta. Dauka tayi yayinda tashinta kwatsam ta bige wani littafi takarda mai dauke da zanece ta Fada kasa, batare da ta waiwaba da ta lura takardane ne kawai sai ta nufi inda Nafeesa take. Dai,dai lokacin da wannan takarda ta fada kasa,Nafeesa ji tai tamkar allura akayo mata, a hankali take fadin, "Kin Yar min da shi,ki daga min shi,nace ki daga shi." Tsayawa Maryam tayi cak kasancewar tana jin magana Amman ta rasa ta inda maganar ke fitowa. Nafeesa ta kara da"Habibbty nace ki daga min shi,ki daga min shi." Cikin dimuwa Maryam ta kalli Nafeesa tare da waigawa kallon inda Nafeesa ke nuni da hannu,wannan takardarce dai data bige batare da saninta ba. Da sauri ta karasa tare da dagawa zanene ta gani irin Wanda Nafeesa ta sabayi akullum tana fadin cewa Nafseen dinta ne. Mik'o mata hannu Nafeesa ke yi alamar ta bata zanen. Karasawa gareta tayi tare da mika mata, kamar wasa Nafeesa na karban zanen ta dawo normal tashi tayi ta zauna tare da jero addu'o'i. Bayan ta kammala ta shafa hamma ta fara" Habibbty wallahi yunwa nakeji muyi wanka na San Mammah ta kammala Abinci yanzu." Maryam da ke cikin tsananin mamaki ta ma rasa bakin magana murmushi tayi tare da girgizawa Nafeesa kai kawai. Ta shi tayi tayi wankanta tsaf Kai kace ba ita ba,Abu dayane kawai da ya tsaya mata rashin waya ga shi ta tsinci kanta da tsananin son ganin sakon da Nafseen zai yo mata,amman in ta tuna da maganar Maryam sai tai kokarin kawar da damuwarta. Bayan ta fito daga wankan zama tai bakin gado dauke da zanen sahibin nata ahannu sai kallo kawai take tana ta sakin murmushi,Allah ne kadai ya San me take aiyyanawa cikin ranta. Fitowar Maryam daga wankane ya katse mata tunani, "Habibbty abani kaya in Sa,kin San dai ba zan maida na jikina ba." Cewar Maryam. Dagowa tai ta karewa Maryam kallo cikeda shagwaba take maganar, "Haba Habibbty wannan ai wulakancine kayanma sai na baki? Yaushe ki ka zama haka,ni fa bana so Allah na Fada miki ban so." Murmushi Maryam ta yi, "To al-shagwabatu bara in dau abuna." "Eh din naji." Ta kare maganar cikin murguda baki. Maryam ko ba abun da take ban da dariya. **Bayan Maryam ta shirya tsaf riko hannun Aminiyarta tai tare da fadin, "Oya bebe Muje aci abinci tun tuni kike kukan yunwa Amman tunda kika dau Zane kin manta da komai." Sai da ta ajiye takardar zanen tamkar kwai Dan tattali kan ta ce, "Habibbty Zanennan tamkar rayuwata yake, na kan kasa ganin komai aduk lokacin da ba glass a idona Amman ban da wannan zanen kullum cikin shege yake ga idanuna,ina son zanen nan fiye da tunaninki,kinga ko ba ma yunwa ba zan Iya daina jin komai,mantawa da komai aduk sanda nake tare da shi." Maryam ta kara janyota tare da fadin, "Kinga nifa yunwa nake ji muje kawai." PSuna fita kuwa suka Tarar da Abhi Da Sabeer zaune Mammah na zuba ma su abinci. Murmushi Abhi ya yi, "Ma sha Allah,Ammie na ta fito, kinga karfan wayannsn jiya fa har kiba kika kara aiko ban baki ita yanzu kam." Daga Nafeesa har Maryam wani Ras sukaji acikin ransu,cikin sauri Maryam ta radawa Nafeesa magana akunne aiko ta sake murmushi tare da fadin, "Ina kwana Abhi,Ina kwana Mammah,Ina Kwana Little Bro." Daga Abhi har Mammah amsawa sukai cike da fara'ah. Sabeer ya ce, "Ina kwana Anty." Maryam ma gaishesu tai suka amsa kamar yadda sukaiwa Nafeesa. Mammah ta zubawa kowa na shi Nafeesa ta ce ,"'Ni bana ci na Abhi na zance." Cikin shagwaba. Abhi ya ce, "Sorry Ammiena zo muci waya isa hanaki cin abinci da Abhin ki." Kusa da shi ta koma ta zauna sannan ya fara bata abaki tana ci,ban da shagwaba ba abun da Nafeesa ke zubawa Abhinta kowa kawai sai dariya domin inda sabo an saba Da ganin halin Nafeesa in tana tare da Abhi. Suna gama cin abinci Abhi ya ce, "Oya Ammiiena ta rufe Ido,ita zan fara yiwa kyauta agidannan." Cikin Sauri kuwa ta rufe. Kwalin waya ya Ciro awata Leda kirar INFINIX Sabuwa gal, Murmushi Yayi Oya bude. Tana budewa me za ta gani,sai waya, bata san lokacin da sake wani irin ihu ba cen kuma sai ta ce, "Alhamdu Lillah, Na gode Abhi na." Ta rungumesa. Ba karamin Dadi Maryam taji ba aranta domin ta san matsalar Aminiyarta ta kau kenan. Sabeer ya ce, "Abhi to ni fa?" Murmushi Abhi ya yi, "Sabeer kai kam agogo ne na siyama domin ba ka kai rike waya ba Amman in ka kai nama alkawari." Karban agogon yayi yana Murna tare da godiya ga mahaifin nasa. Maryam kuwa miko mata wata sarka Abhi ya yi cikin fara'a yake fadin, "Na san dai duk kinfi karfin wannan Amman karamar kyautace na miki daso Allah yayi albarka." Murmushi Maryam tai ta durkusa har kasa ta karba , "Na gode Abhi Allah kara budi." Abhi ya amsa da "Ameen, kallonsa ya koma ga Nafeesa."yawwa Ammina Bana so hankalinki kullum yana kasancewa kan waya ki tuna cewa yanzu kika fara karatu indai kina son muna shiru to ban da shiririta,kuma ki kulama da lafiyar idonki,ga dayar wayar nan ki kwashe abubuwan ciki." Nafeesa ta ce, "In sha Allah Abhi na gode." Mammah ta bata rai , "ka gama da kowa wai ni ba za azo kaina bane?" Duka falon suka fashe da dariya. Abhi ya ce, "Sorry madam naki ai na mussamanne." Daga nan suka bige da hira ita kuwa Nafeesa tuni ta dauki tsohuwar wayarta tare da shiga whatsApp. Kamar yadda ta saba sakonsa take fara dubawa. Tana Shiga........... 😍😍😍ADDU'AR NAN DAI KAR AFASA MASOYAN ASALI❤️❤️ Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-18 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM 🥰🥰🥰INA KEWARKU MY GROUP MEMBERS KAMAR YADDA KUKE TAWA SON SO SABODA ALLAH, INA TSAMMANIN GANIN RUWAN SHARHI ALLAH SA KAR KU BANI KUNYA❤️😘 *SADAUKARWA GAREKI LEEMAH😍 GA GROUP DIN REALL SHAXEE FANS, THANKS FOR D LOVE ND CARE* Dai,dai da lokacin da ya sauka online . Murmushi ne ya fara bayyana afuskarta, tamkar tana gabansa take jin kan ta alokacin. Kara gyara zama tai tare da karin sakar wani murmushin mai banbanci da na farkon domin wannan na mussamanne, shagwabe fuska tai tare da yo masa repy mai nunin ga yanayin da take ciki, wato emojin Shagwaba ta fara sawa kan ta ce, "Umm Uncle Allah ni fa jarumace,kuma in ka cigaba da mun dariya kuka zan yi, mu yi baram-baram ba ma ruwana da kai,sai ka ce min SORRY Anty Nafeesa." tana gama turawa ta kalli online status dinsa minti hudu kenan da saukansa,bataji dadi ba sam har cikin ranta, wani irin yanayi ta tsinci kanta da bata san dalilin hakan ba, rufe datar wayarta tayi kawai tare da daukan Al-Qur'ani ta fara karatu, sai da ta karance Surutul TAUBA tas kan daga karshe tayo addu'o'i nan take taji wani irin sanyi na ratsa mata zuciya tare da shaukin so na mussamman, Murmushi ne ya bayyana afuskarta da ka kanga zaka fahimci cewa tana cikin wani yanayi na mussamman wanda za a iya alkantashi da shaukin SO! Ajiye Qur'anin ta yi tare da daukan jerin littafan Masoyin nata da ta saba karantawa a kullum batare da ta gajiya ba. Falo ta fito ta tattarar da Mammah,Sabeer da Maryam sun kunna wani hausa film. Har zata zauna sai ta tashi tare da gyatsine fuska tana fadin, "wannan kallon naku ma ba bari na nai karatun zai ba gwamda na fita fasej hankali kwance." ta kare maganar tare da gyara glass dinta. Ba wanda ya kulata, kamar ance ta jiyo kawai sai taga an rubuta STORY AND SCREENPLAY BY JAMEEL NAFSEEN. Gabadaya suna gani kallonsu ya koma ga Nafeesa suka bar ta T.V Wayancewa tayi cikin salon shagwaba tare da tebe baki, "Umm nama fasa fitan,anan zan yi karatun kuma kar kowa ya dameni." Mammah ta kalli Maryam kan ta ce, "Maryam Anya MARUBUCIN NAN zai yi kyau kuwa? chanja mana wani kawai." Maryam ta tashi zata chanja Nafeesa tai sauri tare da tare gaban TVn "Ayyah Mammah zai yi kyau wallahi ku tsaya mu kalla nima kallon zan yi shine ya rubuta fa." ta rufe fuskarta batare da ta kara fadin komai ba. Mammah ta dalla mata harara , "Shi wa? Ammien Abhi ki kiyayeni fa tam." Nafeesa ta tabune baki, "Umm Mammah ni yau kallo na ke son yi ko abarni ko in fadawa Abhi ya zane mana ke." Mammah ta sake baki, "Iyeee? Lallai Mamana, Allah shiryamun ke, na san zaki iya hada bom din da yafi hakama asha kallo lafiya." Gwalo ta ma Mammah tana, "Hhhh Ashe ana jin tsorona ma." Murmushi Mammah kawai tai azuciyarta tana kara jin son yartata matukar gaske,mussaman inta dubi halin da Nafeesa ke ciki ta fannin Ido tana matukar tausayin 'yartata, abu daya ke kwamtar mata da hankali yadda Nafeesa ke cire damuwoyi aranta, ta nuna kamar komai bai faru. "Laaah Mammah ba an Hana Anty kallo ba saboda idonta?"cewar Sabeer. Nafeesa ce ta kallesa cikin sauri, "To daman ni ina kallonne dan dai yau zan yi shine ake bakin ciki."karasa maganar tai tamkar zatayi kuka. Da sauri Mammah ta katseta , "Miye na kukan? ki rufamun asiri dan Allah muyi kallo na yau dai daya, ni ai ina son ganinki cikin walwala Mamana kinji, oya SMILE." Tasowa tai daga inda take tana gyara glass dinta ba inda ta nufa sai wajen Mammah kifa kanta tai akan cinyarta tare da dasa idonta ga talabijin din domin yin kallo. Mammah ta ce, "Allah Mamana mijinki ya shiga uku da son jiki, ni kam anya zakina aiki ma kuwa?" Nafeesa ta ce, "Umm bayan tare za mu je kina yi mana ko kin mantane?" Duka Mammah ta daka mata abaya , "Mara kunya kawai." Dariya Nafeesa tasa, "Umm daman so nake ki bar ni nai kallona." kallo suka farayi abin Mamaki yau ga Nafeesa gaban Tv na kallo har bata so wani yayi magana akatse mata, ban da murmushi ba abun da ke bayyana afuskarta da ka ganta zaka fahimci cewa tana cikin yanayi mai dadi, mussaman in ta ga ALI NUHU wanda yafito da sunan jaruminta NAFSEEN aciki. Suna cikin kallo dif nefa suka dauke huta,gwalalo ido Nafeesa tai tare da karewa falon kallo shin da gaske daukewan sukai ko kuma ya?. ta shi tai ajikin Mammah ta zauna tare da yin tagumi tamkar wadda akayiwa rashi,hawayene kawai ya fara bayyana daga fuskarta. Mammah tsabar Mamaki ta ma rasa bakin magana,Sabeer kawai kallon Antyn nasa yake, Maryam ce ta tashi tare da karasawa ga aminiyarta ta. Cire mata hannun tai daga tagumi tana, "Habibbty miye haka? miye na kukan kuma?" Shiru Nafeesa bata da niyar yin magana. Maryam ta cigaba d magana tare da share mata hawayen, "Haba Habibbty kan kallo wai kike kukan nan? to kalli Mammah kiga itama kukan take." Gabantane yafadi ras jin cewa Mahaifiyarta na zubda kwalla Can kuma tintsirewa da dariya tai ta tashi tana tsalle, "Yau dai naga kukan Mammahna, daman ban taba gani ba ysn." Da taga abun dai da gaskene Mammah kuka take tsayawa tai shiru kan ta durkusa gaban Mammah,hawaye ta fara share mata, "Mammah na, Allah wasa nake ki daina kuka kinji in kika cigaba nima zan yi,am sorry Mammah." ta kare maganar cikin shagwaba tare da riƙè kunnuwanta da hannu. Mammah ta kawar da kanta daya barin, Nafeesa ta riƙè hannun mahaifiyarta ta tana,"Smile Lovelyn Abhi, ni ba ruwana inya dawo ya ga kina kuka dariya zai yi yasin,kuma ma yace shi baya son mata mai kuka kinga kenan za akaro mana Anty ko?" ta wangale baki alamar murna zance ko mamaki ma. Harara Mammah ta fara bin Nafeesa da shi kan ta tashi tana, "Ki rabani da maganar Wata Anty in ba so kike inyi jajjagenku daga ke har Abhin ba." Nafeesa ta bita tare da rungumar bayanta, "Mammahna tafi ta kowa, Am so sorry please, ban san zaki shiga damuwa bane kin san da ba zan yi hakan ba, Ki yafemun kinji,kada Allah ya yi fushi dani sanadina kin zubda hawaye, Ki yafemun sannan kiyi murmushi kinji."cikin salon shagwaba take maganar Mammah ta juyo da Nafeesa gabanta tare da kallon fuskar 'yarta ta cikin salon so da kauna. "In sha Allah,Allah ba zai yi fushi dake ba tamkar yadda nima ba zan yi fushi da diyar kirki ba,ina son ki Mamana,Allah raya mun ku cikin aminci,ba na so kina damuwa da kananun abubuwa kinji,Abhinki ba kowa bane sannan Mammanki ma ba kowa bace,duk da na san kin sa hakan aranki amman a kullum ina kara yi miki tunine domin ban da burin da ya wuce rayuwarki ta inganta, na san wa ki ke so,na san burinki amman ba abunda muka isa yi,mun barwa Allah zabi,ba zan hanaki bin muradin ranki ba,amman ina so ki sani ki kara sani mutuncin ki na 'Ya mace ya fi komai mahimmanci arayuwarki,ki rike kan ki,ki san darajar kan ki ako ina ako da yaushe kuma,ki lura ,a yanzu kam ke ba yarinya bace kinji ko Mamana." Cewar Mammah tana shafa kan diyarta ta. Murmushi Nafeesa tayi , "Maddallah da samun uwa ta gari,ina alfahari da ke Mammana,ina sonki,so mara misaltuwa,Allah sa inga tsufanki." Mammah tayi gaba tana, "Allah shiryamun ke ni ma din ba abari ba a tsokanar,Maryam kawar nan taki tana bukatar ganin likita." har cikin ran Maryam tsarin gidansu Nafeesa na matukar birgeta, ba su da kudi amman sunada wadatar zuci ga rayuwa cikin farinciki gwanin sha'awa maganar Mammahne ya katse mata tunani, ta sake murmushi tana fadin, "Mammah ai inaga Asibiti za mu kai Habibbty aduba mana ita." Nafeesa ta tebe baki, "Yasin ras nake, na ma fi ku lafiya ehee." Maryam ta ce, "kyaji da shi nikam ki rakani, muje in tafi gida." Nafeesa ta ce, "Tab ai sai dare." Har Mammah zata shiga daki ta juyo tana, "Aa fa kul ta tafi gida yanzu, kina gani anbarta ta kwana tun jiya yau kuma ta kai dare,maza rike hanun Sabeer ya rakaki ku rakata." Nafeesa ta shagwabe fuska tana kokarin kuka, Mammah ta kara da, "Laa kar ki, kuskura Gobe ai da kwai makaranta kwa hadu acen amman yanzu kam Maryam na da bukatar komawa gida." Ba ason ran Nafeesa ba haka ita da Sabeer suka raka Maryam ta hau nafe. Tana komawa gida sallah tayi tana idarwa kuwa da zumudinta ta dauki wayarta tare da kunna data... Urs Xayyeesherth _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH 27 feb 2021 10:5am ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-19 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM *Jinjina Gareka Haruna Birniwa👏ina godiya da goyon bayanka gareni tare da tallafamun wajen dauruwa a hanyar rubutu mafi inganci,Allah ya kara basira da haza❤️* *Saudaukarwa gareku Deeymusah,tare da Walida Rano🥰ina yinku irin sosai dinnan* *SAI NA AURI MARUBUCI FANS GROUP,Duk da kasancewar gajren fejine amman ina tsammanin ganin ruwan sharhi🤷‍♀️* Messages ne suka fara shigo mata, zuba ido kawai ta fara yi tare da jiran sakon abincin ruhinta, da mamaki har sun gama shigowa amman ba ta ga nashi ba, sannan ko nuna alamar yana online ko ya zo online din ma babu. Wata ajiyar zuciya Nafeesa ta sauke, ta dafa hannu a bangaren kanta, tsintar kanta da karanto INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN ta yi. Nan take ta ji wani sanyi a ranta. "Allah kenan!" Abun da ta iya furtawa kenan, sannan ta kara riƙe wayar hannunta gam, group din marubuta ta leƙa, ai ko ban da zuba ba abun da marubutan ke yi kamar 'ya'yan kanya, hira cikin nishadi da barkwanci suke, wani sa'ilin su juya wa'azi ko wani bangaren na daban a cikin wannan group, kai duk tsegumin da kuke tunani to ya fi karfin hakan. Murmushi ta sake a zahiri tare da fara bin hirar cikin group din, aranta tana sa ran cewa za ta iya gamo ko cin karo da hirar masoyin nata amman kash, har ta kai ga karshe ko alamar gilmawarsa ba ta gani ba. Sallama ta yi cikin group din, cikin sa'a kuwa a amsa mata wajen mutane biyar a lokaci guda. Cikin hirar da suke kawai ta tsinduma inda aka sa daya daga cikin marubutan a gaba da tsokana, SAIFULLAHI MUHAMMAD LAWAN duk da kasancewar yana da baki amman taron dangin da aka yo masa ya sanya shi yin tsit, ita kuwa Nafeesa abun nema ya samu tuni ta shige masa fadan tare da ba kowa amsa daidai da shi. Dariya ya fara yana mai jin dadin ya samu 'yar team, tun dai ana gabzawa har da karshe fadan ya juye izuwa barkwanci da hira mai cike da nishadi da walwala, har ta rufe datarta kasancewar dare kuma gobe tana da skul, a zahirance bata da wata damuwa amman cikin zuciyarta damuwa ce fal domin tana da muradin jin lafiyar sahibinta, sai da ta yo alwala tare da sallah raka'ah biyu kan ta kwanta cike da yin addu'o'i kamar yadda ta saba kullum. A bangaren NAFSEEN kuwa, gabadaya aiki ya yi masa yawa ba shi da lokacin wani abu ban da aikin da ke gabansa, a duk lokacin da aiki ya masa yawa irin haka bai samun damar hawa social media bare ya yi chatting sai tsakar dare yayin da komai ya lafa masa, mussaman in bai gaji da yawa ba. Yau ma kamar kullum, karfe sha-biyun dare daidai ya kunna datar wayarsa domim duba sakonni yadda ya saba. Abun mamaki da bai karewa dangane da Nafeesa Cikin barcinta hakan ya zo mata, abun da ke faruwa azahiri. Daukan wayarta tai kamar yadda shi ma ya yi, messages din da yake tsammani gun abokan aikinsa ya fara dubawa tare da yi masu reply kan ya dawo kan 'yan uwa da abokan arziki. Idon Nafeesa na kan Numbersa mussaman da ta ga yana yi mata typing gyara zama tai ji take tamkar ta kwato ta ji abun da yake rubutawa alokacin, ban da murmushi ba abun da ke bayyana a fuskarta. "Iyee Antynwa? See dis rigima girl, an ki ace Antyn." Reply din NAFSEEN. Cike da yanayi irin nata na shagwaba ta ce, "Ni ko? To ma ka daina kulani, kuma ba ruwana da kai, Uncle mai kan gwangwanni kawai." Dariya maganarta ta ta ba shi har cikin ransa ya ce, "Sorry, dawo Momy Nafeesa ma ba Anty Nafeesa ba, shikenan ina mun shirya?" "Yeess mu kulla tunda da mun kunce ne ma." Nafeesa ta yi masa reply cike da dariya tana mai jin dadi. Ya ce, "Ok, to amman waye mai kan gwangwannin? Momy Nafeesa ce ko? dan ni dai na san Uncle ba ya da kan gwangwani." "Umm... Umm... Ni dai yasin ba ni ba sai dai Uncle, shi ne mai katon kai irin na gwangwani." Murmushi ya saki, har a zuciyarshi yana jin dadin yanda suke chat da yarinyar nan, ga barkwanci kamar 'yar mahauta, ga uwa-uba shegiyar shagwaba. Ya sake murmishi a karo na biyu kan ya tura mata da, "Byee Momy mai kan gwangwani aiki zan yi yanzu, kuma kin ga dare yayi sha biyu daidai, a yi barci kar Mama ta miki fada ko ki kasa ta shi sallah." Ba ta so hakan ba ko kadan domin ji take zata iya kwana sannan ta yini in dai suna hira ne ba tare da ta taba gajiyawa ba, amman a yanzu ba yadda ta iya ko dan farincikinsa yadda ya bukata dole ta sauka. "Nyt Bye, bye Uncle mai kan bera, kuma yasin ni ba na makara ni ke tashin limamin unguwarmu ma." ta rubuta ta tura masa, ji take rabuwa da shi tamkar rabuwa da numfashinta. Batare da ta bare ta ga sakon da zai turo ba ta kulle data tare da gyara kwanciya, ta so kam ta ga amsarsa amma gudun kar ya fahimci tsananin kaunar da take a gare shi ya sa ta sauka, tana jin wani sashe na zuciyarta yana mata radar ta sake kunna datar amma ta basar saboda tsaro. Duk hirar da Nafeesa tai kar ku ji mamaki in na ce maku a cikin barcinta ne batare da ta farka ba har yanzu, to shin da wa Nafseen ya yi chatting? Nafseen ce ko kuwa? Al'amura boyayyu suna da yawa wanda muna bukatar saninsu..... Kada ku gaji🥰ku biyoni a feji na gaba,love yhu oll❤️ Urs Xayyeesherth[3/16, 2:23 PM] Xayyeesherthul-humaerth: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-20 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM 🤗 *A YANZU NAFEESA XAYYEESHER AMMAN A KARSHE NAFEESA BA ZATA TABA ZAMA XAYYEESHER BA😁WANDA YA FAHIMTA YA FAHIMTA KAWAI👌* *MRS MUBARAK,AISHATUL HUMAIRA,DEEYMUSAH,WALIDA RANO,LEEMAH,JASMINE,NAPHYSERT,FATIMA MUHAMMAD,INA YINKU IRIN TOTALLYN NAN ARADU😍KUNA SHARHI INA KWAMUSAN NISHADI😍* *** Addu'ah tayi daga nan wani bacci mai dadi yayi gaba da ita tare da cigaban mafarkin Nafseen Wanda ya zame Mata jiki bata,kamar yadda taba tsallake ko da rana dayane ba tare da kallon Nafseen acikin mafarkinta ba,ba ta taba wani mafarki Wanda ba nashi ba Dan yadda har zanensa tanayi Wan da kawarta maryam take cewa ba iya soyayyan Nafseen bane a tare da Nafeesa zanen kaddaransu tamkar guda ne. Cikin darannan yana ta faman aiki kwatsam sai ga Nafeesa ta fado masa arai ba tsammani murmushi ya sake tare da fadin, " My rigima girl hmmm ko ina take nasan she looks cutie." a zuciyarta sam ya san cewa ba son Yarinyar yake da wata manufar soyayya ba,abu daya yasani kawai dai tana birge shi duk da kasance ba wai ya taba ganinta ba amman yanayinta na nunin cewa yar gidan mutuncice,haka kuma duk da karancin shekaratun hakan bai hanata nuna kamun kai da sanin darajarta na 'Ya mace ba, abu guda Jameel yana da son mutane tare gudun wulakantasu koma ya suke, hakan ya sa in yana ba masoyansa lokaci wasu kan yi ma hakan wani kallo na daban. Nafeesa kuwa tunda ta kwanta bacci bata farka ba sai da taji kiran sallah a kunnenta tashi ta yi ta shiga toilet tayi alwala tazo tayi nafila sannan tayi sallah ta jima tana addu'ah tare da rokon Allah ya cika mata burikanta tana wajen har gari ya para haske Qur'Ani nata ta dauka ta Karanta bayan ta kammala wayanta ta kalla tana murmushi ta nufi wayan tana son kallon reply din Uncle din ta. Ta kai hannu kenan zata dauka wayan kenan taji muryan Mammah na kiranta " ki yi maza ki zo ki yi break zamu yi late fa."cewar Mammah Dan turo baki Nafeesa ta yi cike da shagwaba ta ce, " to Bari nai wanka ina zuwa Mammahn Sabeer." tana kallon wayan haka ta barta a wajen tayi wanka tazo tayi break suka wuce Mammah hospital ita da sabeer kuma skull. Ana sauke Nafeesa tun a gate take zuba ido ko za ta ga habibty dinta Dan tayi missing nata. Ji tayi an rufe Mata ido ta baya ta san ba Mai yin hakan sai Maryam ta juyo da farin cikin ta tana darjya ta ce , "habibaty Miss you ." itama ta amsa mata da" Miss you more babyn Nafseen." Nafesa tayi wani fari da ido ta ce, " gaskiya yau kina son farin ciki ya hanani karatu." dariya suka sa sannan suka wuce sun rike hannun juna abin sha'awa. Sun kusa department nasu kenan sai gasu ga su Mutansir zasu wuce shida yaransa suna hada ido da Nafesa yanayin sa ya canja kana kallon idon sa kasan ya gama storata Nafesa ta fahimci hakan, shi ko yana tuna abin da tayi masa a ranan sai zufa ta keto masa bare ya ganta. Kawai nafeesa ta bata rai ta canja murya kaman Wanda ta jima bata hankainta ta ce , "kai zo nan." abokansa suka ce, " keeee lallai yau kina so ki koma gida a na kashe." Duk da kasancewar suma atsorace suke gudun dai kar ya ci masu zarafine. Mutansir ya ce, " ina ruwan Ku? Ku nace min dagani ku aka kira koni duk suka saki baki suna kallon sa,Aran su kuwa sun san dalili,tuni suka fara watsewa. Nafeesa ta ce, "duk kace su dawo ayi komai a gaban su." Mutansir ya ce, "ku tsaya kowa ya dawo ta ce."maganar yake cike da tsoro. Nafeesa ta gyara zaman glass dinta tare da gyaran murya ta ce, "kowa yazo ya dalla ma sa mari ." suka fara zare ido. Kallonsa kawai Nafeesa tayi ba tare da tace komai ba. ya ce, "wai ba magana ake mu ku ba ne?" nan da nan suka fara daya bayan daya suna wanke Mutansir da mari kafin kace me fuska ya kumbura dama duk abokan haushinsa suke ji yadda yake nuna musu isa da walakanci amman ba yadda suka iya tun da suna cin arziki. sai da Nafeesa ta tabbata ya maku sannan ta ce, " dauki takalmanka a hanu ka bace min da gani ." maryam me take idan ba dariya ba haka sauran students ma akko nan da nan mutansir ya sheka da gudu waje ba abin da kake ji sai dariya. Maryam kan hadda su faduwa kasa Dan dariyar mugunta Nafeesa ta ce, " tashi Wlh mu wuce hall nikan." Taja Maryam suka wuce ban da tafi ba abun da ake yiwa Nafeesa ,domin tayi maganin wanda ya addabi dalibai har ma da daliban kowa na da cikin Mutansir. suna shiga hall Maryam ta ce, "ke habibaty Wai meke faruwa ne dama tun a wancan ranan naga kaman akwai abin da ya faru ." Nafeesa tayi dariya tare da fadin, " wallahi nima ban san komaj ba habibaty naga dai Kawai yana tsoron hada ido dani shiyasa Kawai na ma shi haka yau amma ni bansan meya faru ba." Maryam ta ce, " aiko kin burgeni sosai wallahi kinyi maganin Dan iska,ashe ma ragone matsoraci." duka dariya sukayi tare da daukan handouts nasu su suna dubawa. Mutansir ko kunya be barsa ya kasa zama a skull s motor shi ya shiga tare da nufan gida kawai Domin kuwa Allah ya sanya Mashi tsoron aljanu, afadarsa Nafeesa ba Mutum bace Aljan ce babu tantama yana tafiya yana jin takaici Wai yar talakawa ne Zata dizga shi duk yadda yake ji kansa dinnan,har yaransa su maresa shi ke nan raini ya shiga tsakani! ....bayan an gama lectures suka fito zasu wuce gida sun ci sa'a sun samu Nafe da wuri suka shiga kowa ya nufi gida kasancewar yau baza azo daukan Maryam ba. Nafeesa na isa gida dai,dai kofar gidansu taci karo da bayan wanni sauri,bata gabansa ba amman ayadda tsarin bayan sa yake saurayine dogo madaidaici sanya da bluen shadda wadda tun daga nesa shekinta ke tashi,kamshi kuwa da ka dumfaro wajen kamshin zai maimaye hancinta. Kasa magana tayi yayin da kamshin ke shiga cikinta abu daya ta iya furtawa , "Subhnallah! Kalmar da ta furta ne ha sa saurin juyowa cike da kasaita,ban da murmushi ba abun da ke bayyana afuskarsa......... "Subhannallah,"kalmar data kara furtawa kenan. Urs Xayyeesherth [3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: https://chat.whatsapp.com/Fogl4Tv2O7C8qEJRgUaLKG _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-21 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM _*Koda ke kadai mahaifiyarki ta Haifa kada ki taba sawa aranki cewa bakya da yan uwa, tabbas akwai yan uwa aduniya da suke kasancewa tamkar garkuwa garemu yayinda wata matsala ke kokarin kunno mana,Ina matukar alfahari tare da farincikin kasancewata da ke ANTYNA FARIDA MUSA (SWEERY) bana da kallaman godiya agareki domin sunyi karanci illa fatan alkairi😍*_ 🙌😂 _*SAI NA AURI MARUBUCI FANS GROUP DA SAI NAGA MARUBUCI FANS GROUP ARADU INGA RUWAN SHARHI FIYE DA TAMBAYAR DA KUKEMUN KO IN TAFI HUTU😍*_ Kallonsa kawai ta tsayayi cike da Mamaki, Wanda ya bayyana karara afuskarta, ba kowa ta gani ba face NAFSEEN tsaye yana sake mata murmushi ba tare da ya ce ko mai ba. Ta kasa tafiya kokarin fara Jan kafarta tai domin karasawa garesa, gabadaya ratansu ba zai wuce taku takwas Amman tafiya take ta kasa karasawa garesa, ga shi kusa da ita Amman Sam ta kasa iskansa, har yanzu ban da murmushi ba abun da yake sake mata, daga fuskarsa har kayan jikinsa ban da sheki ba abun da suke. Daga hanunsa ya yi yana mata nunin cewa tazo hakan ya bata damar mika nata hanun kamar yadda ya bukata. Ta mika kenan yana kokarin rikyewa karaf ,Mammah ta ce, "Nafeeesa Miye haka? Kina hankalinki kuwa." Juyawan da zatai ba tare da ta ankare ba Ashe har ta shigo cikin gida, ba tare da taba Mammah amsa ba,saurin juyowa tai domin mika hannunta ga muradin ranta,Amman kash bata ga kowa ba. Kuka ta fara tana fadin, "Mammah ya tafi,Mammah kin koreshi,Dan Allah ki ce ya dawo Mammah zan bisa, wallahi ina son shi." Dafa kanta tai tare da kokarin faduwa da sauri Mammah ta karaso tare da tallefata, addu'ah ta fara karanto mata alokacin cikin sa'a kuwa Nafeesa ta fara dawowa, cikin raunanniyar murya take fadin, "Mammah zan kwanta ki kai ni daki." Murmushi Mammah tai , "Ok Ammien Abhi Amman Please kada ki wannan barcin mai dadewa ban so kinji?" Girgiza mata kai kawai tai. Mammah ta kaita daki,ta kwantar da ita tare kunna mata karatu. A bangaren Nutasir kuma tun da ya shiga mota yana tafiya ba abin da yake tunawa sai Nafeesa . ba abun da yake tunawa illa ranar da ya fara ganin Nafeesa. tun daga farkon kallon ta dayayi a makaranta zuwa abun da ta masa a yau , da wannan tunanin ya iso wani unguwa koda kallon unguwan kasan na masu arziki ne layin gidan su ya shigo daga farkon layin yake danna horn da karfinsa domin dabi'arsa kenan kowa yaji wannan horn din yasan Mutasir ne yadawo. mai gadi ko tunda ya fara jin horn ya fito da gudu ya fara kokarin budewa Dan yasan idan Mutasir ya iso be bude ba yau shima yasan makomansa . Yana isowa ya shiga da gudu domin baya driven a hankali bare ma yau dayake jinsa duk zuciyan shi ba dadi Talle mai gadi yana gaidashi Amma ko kallon sa beyiba nan da nan yasha jinin jikin sa. Dan haduwa gidan su Mutansir ya hadu tunga wajen gidanma bare an shiga ciki . apartment biyu ne a gidan na farkon ya nufa yana shiga Babban falon ya fara Momy" Momy" ya zauna akan kujera daya daga ciki ya kwantar da kansa tare da rufe idonsa wata matashiyar yar aiki ne ta fito ta ce, " tana sallah." Ransa ba dadi ya nufi apartment dinshi toilet ya shiga ya watsa ruwa ya dawo kan gado ya kwanta tareda Jan dogon numfashi. Tabbas ya kamu da son Nafesa har yana jin idan har baj aureta ba komai zai iya faruwa . yanzu taya zai tunkare ta gashi tsoron ta yake sosai da ace yasan zai so Nafeesa irin haka da bai mata abinda ya mata. Ban da juyi ba abun da yake agadon domin ko idonsa ya rufe ita yake kallo yanayin ta da yadda take magana yana kara birgesa a gaskiya, Dady ya dawo asan abinda za,ayi . Abun da yake ta sakawa acikin zuciyarsa kenan. L WAYE MUTASIR ? Mutasir Dane ga Alhaji Abdallah Adam da hajiya balkis Ahmad tun bayan auren su suke son haihuwa Amma Allah bai basu ba sun jima a haka tun suna rai har suka cire Alhaji ba Irin abin da beyi ba amma shiru sai kawai ya fara tunanin aure Dan Kawai yasamu haihuwa Allah da ikonsa kuwa sai ga hajiya da ciki zokaga murna wajen Alhaji tun daga wannan lokacin ya daina fita ko Ina yana tayata zama Hajiya ta samu kulawa sosai har Allah yasa ta haihu aka samu namiji Wanda yaci suna Mutasir, Alhaji ya dauki so da kauna da duk wani burin sa na duniya akan dansa akan sa ba da Wanda ba zai iya Fada ba. koda ko hajiya ce, duk da bata son Abun da Dan nata yake Amman ba yadda ta Iya domin kuwa tsaf Alhaji ya shirya rabuwa da duk Wanda yaso taba masa farincikin Dansa. haka Muta sir ya taso a sangarce besan fada ba duk abinda yayi shine daidai momy na iya kokarinta Amma Dady yafi karfinta kuma yaro duk Wanda yake nuna abin da yake yi shine daidai to yafi son shi idan an masa fada zai ga kaj ba masoyin shi bane . Daddy yaso kaishi kasar waje karatu Amma shi yace yafi son a bashi yayi anan a haka ya Karasa secondary harya shiga tertiary institutions inda ya hadu da Nafeesa, wannan kenan. Maryam ko Nafe na ajiye ta motan Kabir na parking a kopan gidan su sarai ta ganshi Amma ta basar dashi tana kokarin shiga gida yazo da sauri yasha gabanta, " haba Maryam mesa kike min haka ne kina wahalar min zuciya, narasa gane me zanyi miki ki gane irin son da nake miki kodai saj ranan da kikaji ance na kamu da ciwon zuciya ko ko na mutu zaki yadda da cewa ina kaunarki, Maryam Dan Allah ki taimaka min ki Kara bani Dama kiyi hakuri." Maryam ko kallo bai isheta ba ta ce, " Malam matsa zan wuce inaga kaman gidan mune ko?" Ya ce, " Hakane Maryam Amma ki saurareni Dan Allah ." kafin tayi wani abu Kabir ne ya Saka gwiwowinsa a kasa yana , "Maryam ki tausayi min please." ta bi ta gepan sa ta shiga gida Kabir besan sanda hawaye ya fara zubawa daga idanunsa ba kaman ba namiji ba da kyar ya kai kansa mota yaja tare da barin unguwar jiki asanyaye. Maryam na shiga gida Ummi ta dara mata fada danko duk taji abin da Maryam tayi ma Kabir "Maryam ba kyau wulakanta mutum fa idan ma baki sonsa bata haka zaki masa ba ki bi shi a hankali,ni zai ban koya miki wulakanta kowa ba." Maryam ko ban da hawaye ba abin da take Dan ita bata ga Me zatayi da soyayya ba bare tasa wani aranta harta bashi kulawa bazata iya ba gaskiya daki ta shiga ta zauna tana jin haushin Kabir har cikin Ranta, ko Nafeesa dake Soyayya ma tausayinta takeji hakan ya sa take kallon cewa soyayyarma bakidaya bata lokacine. ****** Nafeesa ko bata farka ba sak da aka fara kiran sallah magrib Mammah taji dadin hakn sosai Dan yau baccin beyi nisa ba sallah tayi duk tana jin jikinta ba dadi yana mata ciwo,ko abinci bataci ba ta dauko wayarta tare kunna data... Urs Xayyeesherth [3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-22 BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM _*TABBAS ASON RAINA LITTAFIN NAN BA ZAI ZARCE FEJI GOMA BAMA KWATA-KWATA😁AMMAN KADDARA YA SAUYA MASA AKALA YA FITA DAGA SAHUN GAJERAN LABARI,KADA KU GAJI😓 AKARA HAKURI DA RASHIN TYPING DINA KAN LOKACI,NA SAN KUNAYI AMMAN AKARA🥰INA SON KU MASOYANA,SON SO❤️*_ _*SADAUKARWA GA YAN GROUP DINA SAI NA AURI MARUBUCI FANS KUYI YADDA KUKESO DA SHI TARE DA RUWAN SHARHI*_ Tsayawa kallon Wayar tai kawai yayinda messages ke shigowa,idonta ba inda yake illa kan Sunan Ruwan Ranta *NAFSEEN* Amman har messeges sun kusa gama shigowa har yanzu ba alamar nasa, Hawayene ya fara zubowa daga fuskarta,ta San cewa tana da bukatar ganin sakonsa "Amman to miye dalilin hawayen? Tamkar wadda akace ya mutu?, Ah'ah bai mutu ba,me zai Sa ya mutu wallahi bai mutu ba." Nan take ta fara share hawayen tare da shiga tana bin hirar rakinsu. Murmushi ne ya fara bayyana afuskarta azuciyarta take fadin, "Lallai kai na mussaman ne kamar yadda rubutun ka yake na mussaman,maza da yawa a media da zaran an fara magana da su ta private burinsu daya suga hoton mutum,Amman ko kadan kai bakada wannan akidar azuciya rayuwarka kake mai cike da annushuwa, tabbas ina sonka kuma SAI NA AURI MARUBUCI (Nafseen), ta cigaba da fadin nikam dai ayanzu duk da ban taba ganinka ba Amman na sanka,kuma ina kara ji araina cewa yadda na siffantaka haka kake babu shakka." Tana karasa maganar ta tashi tare da nufar inda ta saba ajiyar zanen Sahibinta, Kallonsa ta tsayayi na Dan lokaci daga karshe ta shafa fuskarsa tana mai fadin, "INA SONKA, INA SO KASAN DA HAKAN." Ji tai tamkar yana kallonta hakan yasata rufe fuska da hannayenta cikin sauri, tare da nunin jin kunya,a haka har ta bar dakin sannan ta bude fuska. Dakin Mammah ta nufa saida tai alwala sukai sallah tare kan suka fito falo, dai,dai da shigowar Abhi da Sabeer daga masallaci kenan. Da sauri Nafeesa taje gun Abhi ta rungumesa, tana ta sakin murmushi. Dago da ita ya yi yana. "Ammeerna Ya naganki hakane yau sai murmushi ga dukkan alamu yau an faranta miki." Rike mi shi hannu tai tare da janshi suka zauna sannan ta ce, "Ina Sonka Abhi na." Cike da so ya kalli Yartasa, "Tabbas nima ina sonki Ammina farincikina,Allah kara rayamun ke mu sha biki,inga ranar aurenki." Da sauri ta rufe fuska, "Umm Umm nidai bana so." Mammah da Sabeer ko ban da dariya ba abunda suke domin ba yau Nafeesa da Abhi suka saba irin wannan dramar ba,sun shaku matukar gaske. Cikin farinciki,nishadi da walwala sukaci abincin darensu,sai da Abhi ya raka Nafeesa har daki kan ya nufi dakin Mammah. Wa she gari Da sassafe Nafeesa ta shirya domin da safe sukeda lecture, hijabinta tasa har kasa tare da glass, sai jakar makarantarta,ban da kamshi ba abun da ke tashi, ba karamun kyau Nafeesa tai ba. Sallama taiwa Abhi domin yau zai koma aiki,sannan ta nufi skul ita da Sabeer,Mammah kuwa ta tsaya sai taga tafiyan Abhi. Nafeesa na isa dai-dai da lokacin da driven su Maryam ya tsaya. Da gudu Nafeesa zata karasa gun Maryam tayi kicibis da wani duzu zata fadi, da sauri Mutansir ya karaso zai tareta, dagowa tai tare da galla masa wata hamshakiyar harara ta wuce. Binta da kallo kawai yayi azuciyarsa yana kara jin tsantsar so da kaunar ta. Rungume Maryam tai tana, "Oyoyo Habibbty Mie,nayi kewarki aradu." Maryam tai Murmushi , "Umm Habibbty kenan yau fa tin daga nesa nake ganin hakoranki me muka samu ne?" Nafeesa ta kyalkyale da dariya, "har yanzu nima bansan me aka samu ba ko za asamu,Amman ina ji araina cewa abun da Nagani ne jiya,duk da kasancewar ma ya tafi ya barni batare da ya min ko magana ba." Maryam ta ce, "Habibbty kina bani Mamaki,soyayyarki abun karantace mai zaman kanta a makaranta,na saba da ke na jima da ke Amman har yanzu Mamaki kike bani yadda kika dauki so da matsayin da ba kowa zai Iya hakan ba, tabbas kina tare da boyayyen sirri da ya kasa bayyana agaremu Allah ne kadai inyaso zai bayyana mana,bama wannan ba nasan maganar bata wuce na Sahibinki ba to me kika gani?" Nafeesa ta ce, "Yo to wa zan gani bayan shi?.ta karasa maganar tana dariya. Maryam ta galla mata harara, " daman nasani ai, kuma fa ina binki bashin labaran Sirri." Nafeesa ta saki murmushi, "With Time inji bature, muje saura 2minit afara lectures." Rike hanun junansu sukai har sai da suka shiga tare da zama awajensu da suka saba. Karatu ake Amman gabadaya hankalin Mutansir na kan Nafeesa, shi dama ba zaman lectures din yasaba ba,Amman yau Dan ita kawai ya shigo kowa Mamaki yake, in aka lura da yadda yanayinsa ke kan Nafeesa, zaka fahiimci ita kawai yake kallo. Gajiya ya yi abunka da ba sabanba ya tashi zai fita, Lecturern ya ce, "Kai Mutansir Ina zaka yanzu kuma? I think saura 30minit mu kammala ma." Ya karasa maganar yana kallon agogon hanunsa. Mutansir ya ce, "Wallahi Nafeesa....... Sai ya kasa karasa maganar domin bai ma San yadda akayi abun da ke ransa ya fito filiba. Kallon Nafeesan yayi suna hada ido yayi saurin kawar da kai. Daga Lecturern har sauran yan class din dariya kawai suka fara Kunyace ta kama Mutansir ya fita kawai. Zama yayi acikin mota ban da kallon Inda Nafeesa zata fito ba abun da yake yi,ji yake tamkar ya kara komawa domin kuwa tunda ya fito ya rasa nutsuwarsa. Karfe 2 dai,dai Suka fito,Idon Mutansir kuwa Kur akan Nafeesa, cire tsoro yayi tare da tunkararta azuciyarsa yana mai fadin koda marinsa zatayi t dakesa da kanta ba zai fasa bayyana sirrin ransa ba. Haka kuwa akayi Karasa wa yayi yana yi mata magana kamar bazata tsaya ba ji tai ta tsinci kanta da tsayuwar. Mutansir ya durkusa yana fadin, "Dan Allah ki yafemun Nafeesa Sharrin shedanne ki bani dama in nuna miki hakikanin soyayyar da nke miki Dan Allah,ina sonki Nafeesa." Kalmar son da ya furta ya sauya Nafeesa nan take wani irin yana yi ta shiga batare da ko hanunta yayi motsiba Jefar da Mutansir gefe akayi,aka kara dagasa sama kan aka sauke,ban da ihu ba abun da yake. Nafeesa ta........ Urs Xayyeesherth [3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: https://chat.whatsapp.com/GeuRcMbmDGuHPBZu4928K8 _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH https://www.facebook.com/106494781436168/ ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-23 _*JASMINE,RANO ON TOP,MAMAN SHUKRA,MR MUBARAK,AISHATUL-HUMAERAH,MAMAN KHRT,MAMAN IHSAN,NAFEESAT,DAMA SAURAN DANA MANTA🚶‍♀️🤸‍♂️DUK KAN KU YAYA JAMILU (NAFSEEN NA GAIDAKU KYAUTA😂AMMAN FA YACE BAN DA NAFEESA😓ABUN TAUSAYI*_ BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM Tsorata, abun ya bata mamaki kawai jikintane yafara rawa, Maryam ido ya yi zuru-zuru ga dalibai an fito kowa idonshi Kansu. Wata irin kara Nafeesa tai nan take aka ajiye Mutansir gefe, tausayinsane ya kamata nan take,ta karasa gareshi duk jikinsa ya kurkuje. Ganin Nafeesa gabansa maimakon yaji tsoro ko yaji da radadin jikinsa,murmushi ya fara sakewa yana kallonta. Ita kuwa cikin dimuwa take fsdin, "Sannu kaji, nikam dai ban ma komai ba,ka gani ko? Sannu ban San waya Tabaka ba." Kasa magana yayi ban da murmushi ba abun da yake saki. Maryam ce ta karaso tare da rikye hannun Nafeesa tana, "Habibbty mu tafi kinji." Nafeesa ta fara kuka, "Habibbty kin gani fa,ina ni ban masa komai ba." Maryam ta ce , "Eh tashi muje." Dakyar Maryam ta janye Nafeesa daga gun Mutansir ba su ma tsaya lectures din Yamman ba,Maryam ta lura da yanayin Nafeesa hakan yasa kawai suka nufi gida. Mutansir kuwa sai da aka kai shi asibiti. Fatima takaici kamar tayi yaya, kara duban kanta tai,shin wai da me figiggiyar yarnan tafita ne, da har mutansir zaiki ta,tsaki taja azuciyarta tana , "Sai shegen karyar iskanci ga dukkan alamu yarinyarnan matsafiyace, Dan haka nima yanzu aka fara daga ita har Mutansir din sai na basu mamaki wallahi." ****Suna fara tafiya Nafeesa ta mance da abun da ma ya faru gabadaya ta dawo hayyacinta tamkar ba ita ba, dukkansu sunyi shiru sai kallon hanya suke kawai,tsayuwar da mai nafensu yayi ne ya ankarar da su. Kabeer ne ya tsayar da mai nafe din. Maryam na ganinsa taji wani Abu ya tokareta akirji tsaki tayi azahiri sannan ta kawar da kai. Nafeesa ta kalle shi cike da fara'ah , "Ah Yah Kabeer kai ne?" "Eh Wallahi Nafeesa na ga yau kun kammala da wuri gashi nima gida zani mai zai hana in rage maku hanya?" Cewar Kabeer Nafeesa ta ce, "Ayyah Yah Kabeer Karka damu wallahi ai mun kusa gidanma." Kabeer yace, "Eh ai ba Matsala ko Mallam? Nawane kudin in ba da?" Mai nafe yaga alamun za Adan samu cikin Sauri ya ba da amsa, "Eh yallabai." Cikin Fada Maryam ke magana,"kinga Habibbty nifa bazan Iya ba,kai me nafe in zaka kai mu ka kai mu haba, wannan ai wulakancine in baxaka ba mu sauka ai ga wasu nan ma hau.". Maganar take tana kokarin fita a nafen. Nafeesa ta rikota, "Miye haka Habibbty? Ni dai ban sanki da irin wannan halinba,kuma sai mun hau motar Kabeer ko kinki ko kinso in kuma ba za ki hau ba ki ta tafi ni ya kai ni." Ko da wasa Maryam bazata Iya barin ta ba domin tana gudun bacin ran Nafeesa fiye Da nata. Ba yadda ta Iya haka ta shiga,da zata shiga baya Nafeesa ta ce aa, bata da zabi da yafi na Nafeesa hakan yasata shiga Amman fuskarnan amurtuke. Kabeer ya ba mai nafe dubu daya kan ya dawo suka fara tafiya, murmushi ya yi yana kallon Maryam ya ce , "Niko Nafeesa kun San cewa in kuka bata rai ba karamin kyau kuke karawa bane?" Dariya Nafeesa tai, "Lallai Yah Kabeer,yo kaga mukai kyau ma in mun bata ran bare mun sakesa, ina tabbatar maka cewa Habibbtyna ta mussamance, yanzu ma da zatayi murmushi sai ka kusan suma." Saura kiris Dariya ta subucema Maryam Amman ta basar domin ban da kara jin tssnar Kabeer ba abun da take. ********Nafseen ne yafito daga cikin daki cike Da murmushi afuskarsa, wata yar matashiyar Mata ta biyo bayansa tana, "Umm Husband ban fesama turaren ba fa." Kwaikwayon yadda ta shagwabe yayi shima, "Umm Wife kina gani lokaci na kuremun kuma inna biye ki wallahi sai in makara yau fa zamu fara daukan sabon film dinnan So akwai bukatar na isa Kano kan lokaci, kuma na fesa turaren nan fa wai bai isa bane nikam." Murguda masa baki tayi, "ni dai ka daina kwaikwayona,kuma ai naka ka fesa ni baka fesa nawa ba,Allah ba zan Yarda ba." Ta karasa maganar cikin sigar shagwaba. Dawowa yayi kusa da ita, yana magana ahankali, "Fesamun Amman indai yayi yawa kika janyo yau na miki kanwa shikenan ba ruwana." Dariya tayi kan ta ce , "Kanwa! Allah kawota ai a kujera zata zauna ba kaina ba,kowa ya Iya allonsa ya wanke,in yasoma ya sha ruwan." Hade rai yayi, "Wato ma ko irin kishinnan nawa bakya yi ko?" Fara fesa masa turaren tayi tana sakin murmushi, "Ina kishin Mijina fiye da kowa, kishi Mara misaltuwa Amman ban isa in sauya kaddarata ko ince zan musa ikon Allah ba,Ina Sonka Mijina,fiye da numfashina, fatan nasara,Allah Sa afita asa'a adawo lafiya, Zan yi kewarka." Hannunta ya riko suka fito tare, ji yake tamkar kada ya barta domin kuwa yafi kowa Sanin cewa yayi dace da mace ta gari, mai hakuri,hankali da tunani. Kallonta yayi,yana, "Maddala da matar kirki,Amin Amin Na gode, Allah ya miki albarka,byrrbyee." Kamar za ta yi kuka ta ce, "baka fadamun ba." Cikin tsokana ya ce, "Me zan Fada?" Hawayene ke kokarin fito mata, da sauri yadawo tare da rada mata wata magana akunne,murmushi tayi kawai. Ya kara da, "I Love You Wify." "Love you more husband,byeebyee." Hanyar kano suka kama,da yake tafiyar ranane har dare basu isa ba. Kwatsam wata babbar mota tayo kansu,ba damar kaucewa haka ta danne motarsu Innallillahi-wa'inna-ilaihir-raji'un 🤭🤭KUNA SO NAFSEEN YA MUTU???🤸‍♂️🤸‍♂️A TSARE KOMAI YAKE AMMAN YAU ZAN GA MASOYAN YAYANA. Urs Xayyeesherth_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-24 _*SADAUKARWA GA SAI NA AURI MARUBUCIYA FANS GRP😘ARADU SAI NA AURI MARUBUCI FANS GRP2 ZAN YI SHARA🥺KAF XAN CIREKU TUNDA BA SHARHI*_ Banda salati ba abin da ke tashi a motarsu Nafseen duk wani Wanda ke wannan wajen saida hankalinsa ya tashi domin duk Wanda yake cikin motan ba Wanda ake sa rai da zai Rayu. wanine akasamu yayi hankalin kiran yan road safety suka zo da gaggwa aka fara kokarin daga motan da kyar aka samu aka daga motan aka fara fitowa dasu Amma duk basa hankalinsu sannan kuma driver din baya da rai. cikin gaggawa aka wuce dasu asibiti domin ceto rayuwarsu. Muta sir kuwa tunda ya koma gida wani irin ciwon kai da zazzabi ya rufe shi sosai son Nafesa na Neman halaka shi, zuciyar shi tana mashi zafi sosai ko ruwa ya kasa sha bare abinci duk jikin sa rawa yake, ko ido ya rufe ita kadai yake hange, yanzu kuma kaman ita yake kallo tana masa murmushi shima murmushi ya fara hadda kokarin fita a blanket dinsa ya nufi wajenta yana zuwa ya durkusa a gaban ta "Nafesa kema kin fahimci Irin son da nake miki ko? na san za kiji tausayi na dama, plz give me a chance ." Momy ce ta ce, "waye ita?" saiko mutansir ya dago "Momy dama ba Nafesa bane momy plz ki tausaya min zan mutu idan ban same ta ba, wallahi ina sonta." Ya karasa maganar jikin kuka. yau ce rana ta farko da Momy taga mutansir yana kuka da girman sa dago shi tayi taji duk jikinsa ya dauki zafi sosai. ta ce, " son yanzu akan mace Kake wannan abin? Daman na San za arina ai,akwa ranar kin dillanci." "Momy nidai Dan Allah ki taimaka min bakiji yadda xuciyata ke min ba Momy, ji nake tamkar zan Iya rasa raina." Momy ma duk jikin ta ya mutu ban da hawaye ba abin da take, domin ban da dai fita ta Mutansir da ke Sa basa shiri amman tana matukar son 'dannata. Kallonsa tai cikeda tausayi ta ce, " Idan Dady yadawo zamuyi magana,kar ka damu kaji, ka san Dadynka zai iyama abun da yafi wannan ma,bare wannan da nake Sa ran shi zai kara shiryaka." Mutansir ya ce, " Momy plzz kice dady yazo yanzu Dan Allah momy, ni ko yanzu ma a auramun Nafeesa Dan Allah. " Shafa kansa tayi kan ta ce, "yanzu dai kayi wanka kasha magani kayi sallah kaga sakka kara yin addua ko ? Kan Dady ya dawo ai yama kusa." da to ya amsa,sanan ya nufi bangarensa, Momy da kanta ta hada masa ruwa sai da ta tabbata yayi wanka yayi sallah sannan ta bashi abinci duk da ya kasa ci Amma yadanci magani ta bashi tace ya kwanta kafin Daddy ya dawo ba musu ya kwanta shi kadai yasan me yake ji rupe ido yayi Kawai ba Dan yanajin bacci ba Momy data ga ya rufe itama ta fito tana mai jin tausayin Dan nata sosai,tabbas So ba karamun Abu bane kuma zai Iya yin illa ga zuciyar kowa.. **** Sai Dare Nafeesa ta bar gidansu Maryam tunda kabeer ya saukesu tare. Karfi tara bayan tayi karatunta na QUR'ANI ta zauna tare da nufin zata bude data take ko zataga Uncle ya Mata magana. Messegese nata shigowa Amma na shi shiru duk jikinta yayi sanyi ko lafiya kuwa uncle baya online ko dai zan tambaya a group ne can kuma tace hmmm danke kadai ne me baki ko ? to ko na kira shine? Ta ba kanta amsa ehh Bari na kira number dinsa ta duba harzata danna call sai ta ji duk jikin ta na rawa Gaban ta na faduwa numfashinta na fita da karfi wayan ta jeda kan gado itama ta kwanta tafi mintuna ashirin a haka nan da nan ta fara kuka tana cewa "uncle meya sameka kasan inason ka Dan Allah karka min nisa jikina yabani wani Abu ya sameka,Kayi hakuri please." kukanta ne yayi yawa sai da Mamma ta shigo dakin cikin,hanzari ta ce, "meke faruwa ne? Nafeesa kina lafiya kuwa?" Cikin shidewa take fadin "Mamma wani Abu ya same shi wallahi, ba zan Iya....... Kawai sai ta jita shiru ,ta leka ko harta tafi baccin data saba addu a ta mata ta fito, tana gaskiya lamarin Nafeesa ya fara yawa da bukatar fadada Neman magani... A bangaren Nafseen kuwa asibiti aka wuce dasu cikin ikon Allah duk sun dawo hankalinsu sai dai sunji ciwo sosai. doctor ne yazo yana dubasu ana tambayan su daga inda suke sai lokacin ya tunada wayarsa da bai san ina zai ganta ba. tambaya yayi sukace su dae basu samu waya a motan ba. rike Kansa yayi" ohhhh my God." kadda8 ace masa wayan shi ya bata kuma sai wata zuciyar tace masa ka gode ma Allah da abin ya tsaya akan waya azahiri ya ce, "Alhamdu Lillah Allah nagode maka." baa dauki lokaci ba yace a bashi Aron waya Dr din ya bashi , **** Rukayya na zaune ita kadai ban da kuka ba abun da take Kanta har ya fara ciwo ta rasa meke faruwa tunda ya tafi bai kirata ba kuma ita ta Kira shi Amma bata samunsa switch of. wayanta taji ya fara kara da gudu tayi daki a tunanin ta zataga sunan sa Amma sai ta ga number wani haushi ne yakamata har kiran ya katsewani ya kuma shigowa sai da yakusa katsewa ta daga muryansa daya daki kunnenta ne yasata Kara sa wani kuka . yace" haba my rukky meye na kukan kidaina plzz ." Ajiyar zuciyata tana ,"ina kashiga meya faru da kai ka fada min plzz." Murmushi ne ya bayyana afuskarsa kan yace, " ki yi shiru zan dawo gida ina lafiya banson kukanki kema kin sani ko?" tace, " har yanzu hankalina be kwanta ba,ni wallahi." da kyar yasa ta hakura akan zai dawo ta ganshi . " to e Ina wayanka ?" Cewar Rukayya . Nafseen ya ce, " ba caji ne shiyasa na karbo na abokina Dan hankalinki ya kwanta to yi murmushi mana babyna." murmushin tayi tareda Masa sallaama akan yana hanya. Maryam ce zaune itada Ummi suna cin abinci wayan ta ya fara kara number din Kabir ne danta gane number din nan da nan yanayinta ya sanja tayi rejecting kiran Ummi ta ce , "waye yake kira?" " hmm ummi wata course mate dinane kuma shirme zata min shiyasa bazan amsa ba." Ummi murmushi Kawai tayi Wai Maryam ni zata nuna ma wayo kaman banina haifeta ba Allah dai ya shirya min ke Maryam. kiranne ya kuma shigowa take ta kara rejecting wayan tana ta fishi karshe ma abincin dabata Ciba kenan tace bacci take ji dakinta wuce, tana shiga kuwa kiranne ya kara shigowa, cikin fushi ta amsa tare da karawa akunnenta....... Urs Xayyeesherth https://chat.whatsapp.com/GeuRcMbmDGuHPBZu4928K8 _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-25 _*TUKWICI GAREKU YAN team DIN YAYANA🥺DUK DA DAI INA KISHI KUNFI SONSA AKAINA,JASMINE, MRS MUBARAK,RANO ON TOP,AMATULLAH,FATIMA ZAHRA,BELAR MAXARE,XEE XEEN BABA,FATIMA SULAIMAN,UMMU NIHEEL, DA MA SAURAN ,I HEART U OLL🥰*_ 🤔🤔 _*WATO ANGA NA DAGE DA TYPING SHINE ZA AFARAMUN ISKARAN BARANCI🥺TO DAGA WANNAN FEJIN SAI BAYAN SALLAH TUNDA HAKA KUKESO🚶‍♀️*_ ***** Sallama Kabeer ya yi cikin sayayyar murya. Amsawa tai tamkar mai ciwon baki. "Ba zan gaji ba,domin ina Sa ran cewa wataran wannan kiyayyar zata koma so, Ina Miki so tsakanina da Allah Maryam, Ina son nai rayuwa dake rayuwa ta farinciki irin ta masoya,kowa na miki kallo acewa ke Maryam ce kadai Amman anawa bangaren ke tamkar taurarice da ke haskaka sararin samaniyi,aduk lokacin da nai kewarki kallon sama Kadai kan sani nishadi bare kuma ace ke din da kan ki na gani,Dan Allah ki amshi muradin raina ko da sai dayane,tare da sakarmin murmushi komin kankantarsa,duk da kasancewar bama tare Amman hakan ba zai hanani siffata kyakkyawan murmushi da zai bayyana afuskar gimbiyata ba." Maimakon bayyanar murmushi afuskar Maryam wani irin hamshakin takaicine ya turnike mata azuciya, ji take tamkar zaginta yake, kamar yadda ta tssni Kalmar so haka ta tsani kalaman so. Ba ta San lokacin da ta sake wani kasurgumin tsaki ba,Wanda sai da ya ratsa cikin wayar tamkar agaban kabeer tai. Yaji tsakin Amman so da kauna ya hanashi jin haushi ko ganin laifinta illa murmushi da ya sake,domin kuwa yaune rana ta farko da har ta Iya amsa kiransa. Maryam ta ce, "Ka gama?" Jiki asanyaye ya ce, "Ba zan taba gamawaba,Amman ganin cewa baki cika son yin maganar ba yasani dakatawa." Wani tsakin dai ta kara sakewa kan ta ce, "OK Na gode." Batare da ta jira amsar shi ba ta datse wayar. Masalin karfe goma na safiya aka sauke Nafseen Kofar gidansa. Rukayya zaune tai tagumi ban da tunanin Mijinta ba abun da take. Da sallamarsa ya shigo ta karasa gareshi da gudu ,yanayin ta ganshi ne yasa jikinta yin sanyi. Duk jikinsa plaster koba,a fada mata ba ta San wannan hatsarine yayi. wani kuka ta fashe dashi tare da rungumarshi tana da kyar ya lallamata tayi shiru . falo suka shiga ta tayashi ya zauna tana hawaye tace Bari na hada maka ruwan wanka ji take kaman ciwon yadawo kanta. Taimaka masa tayi ya yi wanka,tare da gasa masa jiki,kwanciya yayi ita kuma ta fito cikin hanzari ta hada masa abinci kawo masa tai ta ce, " bari na baka kar kaji zafi ." Murmushi kawai yayi aransa yana kara jin tsantsar so da kaunar matar ta shi,tana bashi tana hawaye kaman ciwon a jikin ta yake. "Yanzu dama abinda yasa meka Kenan kako fada min?"cewar Rukayya Nafseen ya ce, "kiyi hakuri banso hankalinki yatashine, kuma kinga ma ai abun yazo da sauki mussaman yanzu da nai wankannan naji dadi sosai, Mah Yar Lukata." Ya karasa maganar cikin zolaya. Hannu ta kai zata dakeshi, sai kuma ta tsaya tare da murgada baki , "Yasin ni ba yar lukutace ba,kuma zan rama yau Dan baka da lafiyane." Murmushine kawai ya bayyana afuskarsa batare da yace komai ba. Rukayya ta kara da , "yanzu wayarkan fa? Nan ya ce, " Ban gani ba fa tun adaren jiyan, Allah kadai ne yasan meyake nufi da hakan, zanyi amfani da dayar wayar kawai,kinga yanzu ba,a welcome back kan lokaci ga sabgogi sunmin yawa wancan sim card ba kowa yasanni dashi ba zan dai rasa wasa daga contacts Dina." Rukayya ta ce, "Allah Sa hakanne mafi alkairi." Ya amsa da "Ameen." GIDAN SU MUTANSIR Daddy ne yadawo Momy take sanar masa halin da Mutansir ke ciki nan da nan tashin hankali ya bayyana a fuskarsa. Batare da ya ce komai ba,bangaren Mutansir din yayi tare da nufan dakinsa. Ban da rawa ba abun da jikinsa ke yi duk ya fita a hayyacinsa. hankalin Dady ya tashi,matukar gaske. " Son Wai akan Mace ne nake shirin rasa ka? ka fada min ko yar waye bazan bar komai yasameka ba, na maka alkawarin haka son, Dan Allah kacire damuwar komai ka tuna cewa kai waye kuma waye mahaifinka,inka cutar da kanka ba zan yafe ma ba." Kokarin Mikewa Mutansir yake kaman ba abinda ke damunsa, Dady ya yi kokarin tallefa, ya rungumer dadyn ya yi yana "Dady da gaske Dan Allah? Wallahi ina son Nafeesa, na San zaka auramin ita." " In Sha Allah Son, yanzu ka taso mu ci abinci." Haka Dady ya rike shi suka wuce dining Momy ta zaunaddashi,Sannan suka fara cin abinci,Dady kuwa ya kasa ci tunanin yadda zai bullowa lamarin kawai yake. ***Mammah ta gama shirya kayan break tasan tunda taga Nafeesa bata fito ba,to tabbas bata farko awannan barcin nata ba, dakin ta shiga domin dubata. Tana nan dai kamar yadda ta barta, addu'a ta shafa mata cikin yanayin damuwa kan ta fice daga dakin. Haka RANAR Mammah ta zauna agida bataje asibiti tana jiran ko Allah yasa Nafeesa ta farka Amman shiru har Yamma, Maryam ma taje skul gsshi har sun tashi Amman ba Nafeesa, kuma ta kira wayarta akashe hakan yasa ana tashi ta nufi gidan. Isarta kuwa Mammah ta samu zaune tai tagumi afalo. Ta sanar da ita halin da ake ciki,cikin damuwa Maryam ta shige dakin,kuka take tana mai yiwa kawar tata addu'ah,Mammah ce ta kara gyara mata kwanciya tare da kokarin cire mata glass din kar ya dameta,abun Mamaki glass din ko motsawa bai yi yaki fita, ba yadda Mammah ta Iya haka ta bar mata. Maryam ta ce, "Mammah wai me ya farune ma har ya janyo barcinnan nasan dole sai an mata wani Abu." Mammah ta ce, "Hmm nima dai ji nai tana kuka ina zuwa ta ce mun wani Abu ya sameshi daga nan bata kara magana ba." Maryam ta ce, "To shi wa?" Sai kuma ta tuna. Kukan ta kara fashewa da shi. Sallama akayi agidan Maryam ta fito wa zata gani......?? Urs Xayyeesherth[4/7, 9:51 AM] Xayyeesherthul-Sweery: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-26 _*SADAUKARWA GA SAI NA AURI MARUBUCI FANS GROUP 1ND 2😘INA YINKU HAR CIKIN KAUNYEN RUHINA*_ _*FATIMA SULAIMAN MUHAMMAD FATAN ZAKIYI MURMUSHI? TARE DA NMCY NA AMATULLAH😘*_ ********* Mutansir ne tare da mahaifinsa. Maryam na ganin Mutansir sai da gabanta yayi mummunar faduwa,Shi ko Mutansir ban da murmushi ba abunda ke bayyana afuskarsa. Jiki A sanyaye Maryam ta ce, "Ina kwana?" Cike da farinciki Dady ya amsa da "lafiya, ince wannance surukar tawa?" Karaf Mutansir ya ce, "Aa fa wannan kawartace Maryam ita kuma sunanta Nafeesa." Murmushi dadi ya yi, "Ah to Amana sallama da mutan gidan ko?" Maryam ta ce, "To." Sannan ta shiga ciki domin sanar da Mammah sun yi baki,batare da tai bayanin suwaye ba. Cike da Mamaki Mammah ta Sa hijabi sannan ta fito. Rusunawa tai ta gaida Dady,haka ma Mutansir ya gaidata. Mammah ta ce, "Ga shi Mai gidan baya gari,Allah Sa dai lafiya?" Dady ya ce, "Ayyah! Aiko banji dadin hakan ba Sam, zan bukaci number wayarsa domin mu fara tattaunawa kan lamarin nan,zumunci zamu hada, Wanda nake fatan duk zamu karu da juna." Mammah dai bata fahimci mai yake nufi ba,number kawai ta bashi tare da yi masa sallama. Mutansir kuwa ya dage sai lek'e yake ko Allah zai sa ya hangi Nafeesa Amman ina ba alamarta bare ita. Har Mammah zata shige gida, Dady ya mikawa Mutansir wasu makuden kudi, da gudu ya karasa gabanta tare da mika mata. Mammah taki karba fir, Dady ya ce, "Indai ko kika ki karba tamkar kin rainamun arxikine,sannan kuma kin maida hanun kyauta baya." A haka dai da kyar har Mammah ta karba Amman ba da son ranta ba,domin har cikin ranta batajin son mutanen ko kadan yanayinsu bai birgeta ba. Tana shiga ciki kuwa Maryam ta ce , "Mammah Allah Sa dai lafiya? Wannan fa Dan skul din nan namune wanda da yasa Habibbty agaba,ya dawo kuma yanzu yana sonta." Mammah ta numfasa kan ta ce, "Oh Sai Yanzu na fahimta atakaice dai Sunzo siyan Nafeesane ba ma Neman aurenta ba,tunda kiga kudin da suka ban ya fima na sadakin." Ta karasa maganar tana juya kudin da ke hannunta. Maryam ta ce, "Hmm Wallahi Alhajin Mutansir zai Iya abun da ya fi hakama Dan farincikin Dan Sa." Ta shi Mammah ta yi tana, "Koma miye dai ai sai da amincewar Nafeesa za ayi,ayadda take dinnan da ace zataso shi inda gaske yake da nafi kowa jin dadi, Amman indai bata son shi akace za amata dole tabbas zamu Iya rasa Nafeesa,ke kan ki shedace Maryam,ni narasa banbance waye nafseen dinnan SHIN NAFSEEN MUTUM NE KO ALJAN?" Maryam ta ce, "Mammah nima wallahi narasa ganewa kan lamarin Habibbty ga shi dai muna ganin littafai da films din da ya rubuta,Amman ganinshi ya zama wani babban Abu,duk da kasancewar Kwanaki ta fadamun cewa ta fara chatting da shi." Mammah ta ce, "Allah ya kyauta,bara in ajiye wannan kudin mutafi gun mai magani domin ga dukkan alamu wannan barcin na da banbanci da Wanda ta saba." Maryam ta ce, "Hakane kan bara na Kira mana mai Nafe sai muje kawai." Haka kuwa akayi daukan Nafeesa Mammah da Maryam sukai suka sata a nafe har akaje gun mai magani, in kaga fuskar Nafeesa za ka sha mamakin yadda take sheke domin barcinta take bilhakki da gaskiya, ba motsi Amman numfashinta na fita kamar kowa. Mallam Ado,Duk da kasancewar shine mai maganinta,tun tana karama Amman har yau bai daina mamaki ga irin yanayi na kaddarar Nafeesa ba,acewarshi kamar yadda take fada akullum Sirrine Wanda Allah kadai ya San wannan sirrin da kuma ranar bayyanarsa. Adu'o'i ya mata ya shafa mata,sannan ya basu hayaki akarshe ya sanar da Mammah , "In sha Allah zata farka Amman ba kamar sauran ba,wannan barcin ya banbanta kamar yadda kuka gani, zata Iya yin watama ko fi cikinsa,babban abun dai bai huce adage da addu'ah ba Amman nafeesa na cikin lafiya da kwanciyar hankali, ban San miye ba dai Amman sanda abun da takewa barcinnan ya kau zata farka da yardar Allah,domin barcinta ayanzu shine mafita inda ko batai barcinnan ba baxaku taba gane kan ta ba." Mammah ta numfasa kan ta ce, "To Mallam glass dinnan fa tun agida nayi-nayi na kasa cire mata ba zai mata wata illa ba?" Murmushi Yayi , "Hajiya kenan,kin yi kuskuren tabawama da baki taba mata ba domin inda da bukatar hakan da tuni kin tsince shi gefe ko ince ki rasa shi ma, tamkar kariya yake gareta karki damu da hakan ko kadan, ayadda Nafeesa take banjin cewa akwai wani Abu da za a Iya mata na illatawa,abubuwan da ke faruwannanma kisa aranki kawai kaddarane,kuma komai yayi farko zai yi karshe acigaba da addu'ah dai muma muna kan yi." Godiya Mammah ta yi sosai kan suka nufi hanyar dawowa gida. *****bangaren Mutansir da Daddy kuwa suna komawa gida Mutansir ya Sa shi agaba kan cewa sai an kira Abhi. Ringing biyu ya daga kasancewar ya tsaya shan mai amota... 08103080717 ✍️ Xayyeesherthul-humaerath [4/7, 9:51 AM] Xayyeesherthul-Sweery: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-27 _*JASMINE KADA KI CE BAZAKI KARANTA BA🤣SHOLLYNKI KINJI SISYNA*_ **** Number din Abhi Dady ya Kira har ya gama ringing ba ayi picking ba, Dady ya ce, " Wai mutum ba kowa ba sai ji da kai, talaka ba wani abun yi garesa ba da sha mai kai ya kasa amsa waya, gaskiya mutuminnan zai yi jin kai ko da gani ba dan kan Son ba abin da zao Sa in kara kira." Amman ya zai yi Dole ya Kara kira kovdan farin cikin dansa daya tilo a duniya, kara Kira yayi ringing biyu Abhi ya daga Dan dama sanda akayi kiran farkon baya kusa da wayan yana dawowa na biyun na shigowa domin Abhi mutum ne Mai saukin kaj baya da walakanci ko cin zarafi. Bayan ya daga tare da yin sallama Dady ya amsa . Abhi ya ce, "amma ban gane wake magana ba kayi hakuri ." Cikin isa da kasaita Dady ya ce, " eh gaskiya bai zama lallak ka gane ba amma inaga zaka Iya sanin sunana domin ni sannane ne" Batare da ya nuna yanason jin sunan ba ya ce, "ikon Allah to fatan dai lafiya ko?" Dady ya ce, " eh akan zancen yarinyan wajen Kace Nafisa take ko wa?" Nan da Abhi ya tsorata Dan yana ce wani Abu ne ya sami Nafisa. Cikin Sauri ya ce, " to Dan Allah meya faru da ammi na, ka fadamun." Dady yayi murmushi , "ka kwantar da hankalinka alkairi ne yasa na kira ka yarona ke bidar Auren Yarka kuma gaskiya idan bai same ta ba komai zai iya faruwa ya Riga yayi nisa sannan ni kuma a bazan taba Barin Dana yarasa abinda yake nema ba ko meye shi indai ina raye." Abhi ya yi shiru kan ya ce, "to Alhaji idan ita kuma yarinyar bata so fa." Dady ya ce, " kaji zancen banza anan ina maka bayani akan Dana zai iya shiga damuwa kana ce min Wai idan yarinyar na so? ai kai ne zaka sata taso koda bata so,kuma ta aura." Abhi ya ce, "ni bazan taba ma Ammi abin da bata so ba, ai ba kai kadai ke son yaronka ba idan ita ce tace tana so zan iya bata goyon baya tabbas ba dole yadda ba abun ba, ba a ma mahaifiyarta ba itama ba mai mata." Dady ya ce, "what?" Abhi ya kashe wayan dan takaici wato shi mai kudi kullum yabi zabin son ransa koda kai zaka shiga damuwa, Allah ya kyauta mana dai. Dady ya ce, "yanke min kira yayi harni ace da girmana da ikona da kimana ace na kira anyi rejecting lallaima mutuminnan, ga dukkan alamu bai San da wa yake wayarba." Mutansir ya ce, "Dady yadai ?. " son kar ka damu idan ina Raye sai ka auri yarinyannan ko tana so ko bata so zasu nan dani suke zancen wallahi."cewar Dady Mutansir sai sabon hawaye "Dady Dan Allah kayi kokarin ka akak Allah zan iya mutuwa kan soyayyarta wlh ." Dady ya rungumesa Dan har cikin ransa yake jin kukan Son dinsa yana lallashinsa kaman yaro karami Fitowar Momy kenan tace, " Alhaji Ni ko sai naga kaman idan kabi ta haka ba zaka samu ba Dan wlh kudi ba komai yake siya ba ." Tsaki ya sake mata tare da ajiyar wani mumman kallo da ya sata shirun dole batare da ta kara wata magana ba. ******* A bangaren Nafseen kuwa ba Kara min kulawa yake samu ba a wajen Matarsa ko motsi kadan yayi zata fara kuka ita bata so yaji zafi ita shi, har dariya rigimarta ke bashi shi ma kukan ya fara yadda take yake kwaikwayonta, " nima bana son naga hawayenki kinsan tsadarvsu kuwa ?" yayi da Irin yadda take yi dariya tayi ta ce, " kai ba shine kake irin maganata ba ko?" dariya yayi ya ce, " ai nida ke duk daya?" Itam dariya tayi ta ce, "to bari nima nayi irin muryarka ." "aa wallah taf din kiyi muryan maza kinsan dadin muryanki kuwa? wlh kar ma ki fara idan ba haka ba na cire kunnen rashin jin." dariya tayi tace, " sai na rama kuwa nima kaga kowa sai ya zauna ba kunne." dariya suka sa a tare kullum haka rayunwasu take yana, so yaga tana mishadi basa taba zama sai ya bata dariya. ta ce, " bari naje na hada ma ka ruwa ka yi wanka sao muci abincin ko?" tayi ciki shi kuma ya bita da kallo yana kara sonta a cikin xuciyar shi,kasancewar jikinsa na da kyau har ya fara warewa Amman dai tafiyarce bai wani iyawa sai da taimakon Rukayya. ********* Maryam, zaune suke ita da Ummi suna cin abinci Maryam ta ce, "ohhhh Ummi ni kan Dan Allah ki bari na koma gidan su Nafisa Ummi kinga fa har yanzu tana nan ba motsi." Ummi ta ce, " subhanallah Wai dama bata tashi ba? "wlh kuwa Ummi kinga zan taimaka mata sosai itama mamma ta Dan huta wlh har tausayi take bani gata tana da tawwakali duk abinda yasameta zata ce jarabawan rayuwa ne." Ummi tace, " ai idan mutum yasa mu ilmin addini zaiji dadin rayuwar duniya har ma da lahirar kin ga nima bara nayi shiri muje tare sai na barki acan idan Abban ki yadawo zan fada masa kin ga yana son ki da Nafisa shima yana yaba Tarbiyarta tashi ki hada kayanki karki bata lokaci ." Maryam tayi daki Ummi ma ta fara shiri. Mamma ne a dakin Nafisa ta sa mata ido sai kallon ta take a fili ta ce, " kowa da yadda Allah yaso ganinsa Nafesa na in sha Allah wata rana zai zama tarihi kaman ba,ayi ba, ina ji ajikina cewa zakiyi rayuwa mafi inganci anan gaba,tabbas da nasan inda zan sami bawan Allahnnan da na tafi nemansa ko da na second dayane ki gansa arayuwarki." Sabir ne ya shigo yana "Mamma yaushe antyna zata daina baccin ne ta ce zamuyi wasa kuma sai nayi ta kallon ta tana baccinta." Mamma ta zaunar da shi a gabanta ta ce, "antynka takusa tashi sabir kar ka damu ni zan tayaka wasan anji ma kaji ?" Muryan maryam suka ji ta ce, " Dani za ayi wasa dama nice kawarka ko?" Da gudu yaje ya rungume Maryam "Anty na tazo nikan kar ki tapi anty ki zauna muna wasa kin ga Anty me glass taki ta dai na baccin ko?" Hawaye Maryam ta fara kan ta ce, "zata tashi sabir ka dai na damuwa tana hutawa ne nima kaga kayana ko zan rika tayaka wasa da assignment kullum." Mamma sai kallon su take Maryam ta hadu gaskiya irinsu sune kawaye na hakika. "Mamma da Ummi fa muka zo,tana falonki na tsaya muna hira da fine boy Dina." Mamma ta ce, "ai kallon Ku nake Ku gama tukun tun da shi Kika sani, matsa min kig a kin barmin yar uwa a waje ni bari naje." Mamma ta fita suka shigo da Ummi , Ummi tana kallon Nafisa ta fara hawaye. Mamma ta ce, "haba Hajiya meye na kuka ? zata tashi ai addu'ah kawai itace magani." Maryam ganin itama data Iya cigaba da kukan ne yasa taja sabir suka fita . Ummi ta jima tana zubda hawaye kafin ta dai na "to yanzu bayan can ba inda za,aje ne ? Mamma ta ce, "nima nayi wannan tunanin amma kinga shima malamin dayane duba ta gaskiya ya kware wata rana fa sai labari ma , kuma tun tana karama shine dai mai maganin nata, zata dai na ." Ummi ta ce, "Hakane kam,Allah kawo karshen wannan lamarin." Mammah ta amsa da Amen. sun jima suna hira kafin Ummi ta wuce gida tace wa mama ga Maryam nasan zata Dan dibe maku kewa musamman sabir ma. Mamma ta ce, "ban san dawani baki zan gode muku ba kun min komai a rayuwa ko dangina iya abinvda zasu min kenan." Ummi ta ce , "Dan Allah ki dai na maryam da Nafisa duk dayane a wajen mu ." har waje mamma a raka ummi sannan ta dawo Kabir ne a tsaye a kofar su maryam kuma yaga gidan a rupe harya juya zai tafi Dan yasan koya kirata ba dagawa zatayi ba sai ga Ummi har kasa ya gai da ta ta ce, "to amma ban gane ba yaji wani kunya ya kara kasa da kansa dama nazo Neman Maryam ne ." Ummi ta ce, "Amma kuma Dana shine zakazo wajen ta kai tsaye ai ba haka ya kamata ba, ya kamata afara sanarwa agida ko?" " ayi hakuri nayi kuskure insha Allah zan gyara."cewar Kabir " yawwa yaro amma dai yanzu bata nan taje wajen yar uwarta ba lafiya." daga haka ta shige gidan Abin ta sai a lokacn ya Mike shide yasan Maryam bata da yar uwan data kai Nafeesa bari yaje gidan Dan yarinyar nada kirki dole yaje kodan ya duba ta ya dauki mota tare da nufan gidansu nafeesa. Sabir ne yazo da gudu " Anty Maryam kizo Wai ana nemanki waje." " inji wa kuma ?" Mamma ta ce, "kije ki duba mana Maryam ta dauki hijab dinta a fita ba dai ason ranta ba, tana bude kofa suna hada ido kirjinta ya buga da karfi. Adai lokacin Abhi ya kira Mammah awaya. Nafseen kuma................ GASA,,,,GASA,,,GASA _*INADA BUKATAR CIRE GWARZAYEN MASOYAN LITTAFINNAN ABUN ZAI KASANCE YANAYIN SHARHINE,YAWAN SHARHINKI TARE DA NUNA SONKI/KA GA LITTAFIN DUK WA INDA BASA GRP DINA ZA SU IYA YIN SHARHI TARE DA TUROMUN TA NUMBER TA DAKE KASA DAGA YAU ZA AFARA HAR IYAZUWA RANAR DA ZAN KAMMALA LITTAFIN,INA SON MASOYAN LITTAFINNAN SU BAYYANA GARENI ADUK INDA SUKE,KARAMAWA TA MUSSAMAN GAREKU,ABUN SIRRINE BAI FADUWA SAI KUN GANEWA IDANUNKU🥰*_ 08103080717 ✍️ Xayyeesherthul-humaerath_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-27 _*JASMINE KADA KI CE BAZAKI KARANTA BA🤣SHOLLYNKI KINJI SISYNA*_ **** Number din Abhi Dady ya Kira har ya gama ringing ba ayi picking ba, Dady ya ce, " Wai mutum ba kowa ba sai ji da kai, talaka ba wani abun yi garesa ba da sha mai kai ya kasa amsa waya, gaskiya mutuminnan zai yi jin kai ko da gani ba dan kan Son ba abin da zao Sa in kara kira." Amman ya zai yi Dole ya Kara kira kovdan farin cikin dansa daya tilo a duniya, kara Kira yayi ringing biyu Abhi ya daga Dan dama sanda akayi kiran farkon baya kusa da wayan yana dawowa na biyun na shigowa domin Abhi mutum ne Mai saukin kaj baya da walakanci ko cin zarafi. Bayan ya daga tare da yin sallama Dady ya amsa . Abhi ya ce, "amma ban gane wake magana ba kayi hakuri ." Cikin isa da kasaita Dady ya ce, " eh gaskiya bai zama lallak ka gane ba amma inaga zaka Iya sanin sunana domin ni sannane ne" Batare da ya nuna yanason jin sunan ba ya ce, "ikon Allah to fatan dai lafiya ko?" Dady ya ce, " eh akan zancen yarinyan wajen Kace Nafisa take ko wa?" Nan da Abhi ya tsorata Dan yana ce wani Abu ne ya sami Nafisa. Cikin Sauri ya ce, " to Dan Allah meya faru da ammi na, ka fadamun." Dady yayi murmushi , "ka kwantar da hankalinka alkairi ne yasa na kira ka yarona ke bidar Auren Yarka kuma gaskiya idan bai same ta ba komai zai iya faruwa ya Riga yayi nisa sannan ni kuma a bazan taba Barin Dana yarasa abinda yake nema ba ko meye shi indai ina raye." Abhi ya yi shiru kan ya ce, "to Alhaji idan ita kuma yarinyar bata so fa." Dady ya ce, " kaji zancen banza anan ina maka bayani akan Dana zai iya shiga damuwa kana ce min Wai idan yarinyar na so? ai kai ne zaka sata taso koda bata so,kuma ta aura." Abhi ya ce, "ni bazan taba ma Ammi abin da bata so ba, ai ba kai kadai ke son yaronka ba idan ita ce tace tana so zan iya bata goyon baya tabbas ba dole yadda ba abun ba, ba a ma mahaifiyarta ba itama ba mai mata." Dady ya ce, "what?" Abhi ya kashe wayan dan takaici wato shi mai kudi kullum yabi zabin son ransa koda kai zaka shiga damuwa, Allah ya kyauta mana dai. Dady ya ce, "yanke min kira yayi harni ace da girmana da ikona da kimana ace na kira anyi rejecting lallaima mutuminnan, ga dukkan alamu bai San da wa yake wayarba." Mutansir ya ce, "Dady yadai ?. " son kar ka damu idan ina Raye sai ka auri yarinyannan ko tana so ko bata so zasu nan dani suke zancen wallahi."cewar Dady Mutansir sai sabon hawaye "Dady Dan Allah kayi kokarin ka akak Allah zan iya mutuwa kan soyayyarta wlh ." Dady ya rungumesa Dan har cikin ransa yake jin kukan Son dinsa yana lallashinsa kaman yaro karami Fitowar Momy kenan tace, " Alhaji Ni ko sai naga kaman idan kabi ta haka ba zaka samu ba Dan wlh kudi ba komai yake siya ba ." Tsaki ya sake mata tare da ajiyar wani mumman kallo da ya sata shirun dole batare da ta kara wata magana ba. ******* A bangaren Nafseen kuwa ba Kara min kulawa yake samu ba a wajen Matarsa ko motsi kadan yayi zata fara kuka ita bata so yaji zafi ita shi, har dariya rigimarta ke bashi shi ma kukan ya fara yadda take yake kwaikwayonta, " nima bana son naga hawayenki kinsan tsadarvsu kuwa ?" yayi da Irin yadda take yi dariya tayi ta ce, " kai ba shine kake irin maganata ba ko?" dariya yayi ya ce, " ai nida ke duk daya?" Itam dariya tayi ta ce, "to bari nima nayi irin muryarka ." "aa wallah taf din kiyi muryan maza kinsan dadin muryanki kuwa? wlh kar ma ki fara idan ba haka ba na cire kunnen rashin jin." dariya tayi tace, " sai na rama kuwa nima kaga kowa sai ya zauna ba kunne." dariya suka sa a tare kullum haka rayunwasu take yana, so yaga tana mishadi basa taba zama sai ya bata dariya. ta ce, " bari naje na hada ma ka ruwa ka yi wanka sao muci abincin ko?" tayi ciki shi kuma ya bita da kallo yana kara sonta a cikin xuciyar shi,kasancewar jikinsa na da kyau har ya fara warewa Amman dai tafiyarce bai wani iyawa sai da taimakon Rukayya. ********* Maryam, zaune suke ita da Ummi suna cin abinci Maryam ta ce, "ohhhh Ummi ni kan Dan Allah ki bari na koma gidan su Nafisa Ummi kinga fa har yanzu tana nan ba motsi." Ummi ta ce, " subhanallah Wai dama bata tashi ba? "wlh kuwa Ummi kinga zan taimaka mata sosai itama mamma ta Dan huta wlh har tausayi take bani gata tana da tawwakali duk abinda yasameta zata ce jarabawan rayuwa ne." Ummi tace, " ai idan mutum yasa mu ilmin addini zaiji dadin rayuwar duniya har ma da lahirar kin ga nima bara nayi shiri muje tare sai na barki acan idan Abban ki yadawo zan fada masa kin ga yana son ki da Nafisa shima yana yaba Tarbiyarta tashi ki hada kayanki karki bata lokaci ." Maryam tayi daki Ummi ma ta fara shiri. Mamma ne a dakin Nafisa ta sa mata ido sai kallon ta take a fili ta ce, " kowa da yadda Allah yaso ganinsa Nafesa na in sha Allah wata rana zai zama tarihi kaman ba,ayi ba, ina ji ajikina cewa zakiyi rayuwa mafi inganci anan gaba,tabbas da nasan inda zan sami bawan Allahnnan da na tafi nemansa ko da na second dayane ki gansa arayuwarki." Sabir ne ya shigo yana "Mamma yaushe antyna zata daina baccin ne ta ce zamuyi wasa kuma sai nayi ta kallon ta tana baccinta." Mamma ta zaunar da shi a gabanta ta ce, "antynka takusa tashi sabir kar ka damu ni zan tayaka wasan anji ma kaji ?" Muryan maryam suka ji ta ce, " Dani za ayi wasa dama nice kawarka ko?" Da gudu yaje ya rungume Maryam "Anty na tazo nikan kar ki tapi anty ki zauna muna wasa kin ga Anty me glass taki ta dai na baccin ko?" Hawaye Maryam ta fara kan ta ce, "zata tashi sabir ka dai na damuwa tana hutawa ne nima kaga kayana ko zan rika tayaka wasa da assignment kullum." Mamma sai kallon su take Maryam ta hadu gaskiya irinsu sune kawaye na hakika. "Mamma da Ummi fa muka zo,tana falonki na tsaya muna hira da fine boy Dina." Mamma ta ce, "ai kallon Ku nake Ku gama tukun tun da shi Kika sani, matsa min kig a kin barmin yar uwa a waje ni bari naje." Mamma ta fita suka shigo da Ummi , Ummi tana kallon Nafisa ta fara hawaye. Mamma ta ce, "haba Hajiya meye na kuka ? zata tashi ai addu'ah kawai itace magani." Maryam ganin itama data Iya cigaba da kukan ne yasa taja sabir suka fita . Ummi ta jima tana zubda hawaye kafin ta dai na "to yanzu bayan can ba inda za,aje ne ? Mamma ta ce, "nima nayi wannan tunanin amma kinga shima malamin dayane duba ta gaskiya ya kware wata rana fa sai labari ma , kuma tun tana karama shine dai mai maganin nata, zata dai na ." Ummi ta ce, "Hakane kam,Allah kawo karshen wannan lamarin." Mammah ta amsa da Amen. sun jima suna hira kafin Ummi ta wuce gida tace wa mama ga Maryam nasan zata Dan dibe maku kewa musamman sabir ma. Mamma ta ce, "ban san dawani baki zan gode muku ba kun min komai a rayuwa ko dangina iya abinvda zasu min kenan." Ummi ta ce , "Dan Allah ki dai na maryam da Nafisa duk dayane a wajen mu ." har waje mamma a raka ummi sannan ta dawo Kabir ne a tsaye a kofar su maryam kuma yaga gidan a rupe harya juya zai tafi Dan yasan koya kirata ba dagawa zatayi ba sai ga Ummi har kasa ya gai da ta ta ce, "to amma ban gane ba yaji wani kunya ya kara kasa da kansa dama nazo Neman Maryam ne ." Ummi ta ce, "Amma kuma Dana shine zakazo wajen ta kai tsaye ai ba haka ya kamata ba, ya kamata afara sanarwa agida ko?" " ayi hakuri nayi kuskure insha Allah zan gyara."cewar Kabir " yawwa yaro amma dai yanzu bata nan taje wajen yar uwarta ba lafiya." daga haka ta shige gidan Abin ta sai a lokacn ya Mike shide yasan Maryam bata da yar uwan data kai Nafeesa bari yaje gidan Dan yarinyar nada kirki dole yaje kodan ya duba ta ya dauki mota tare da nufan gidansu nafeesa. Sabir ne yazo da gudu " Anty Maryam kizo Wai ana nemanki waje." " inji wa kuma ?" Mamma ta ce, "kije ki duba mana Maryam ta dauki hijab dinta a fita ba dai ason ranta ba, tana bude kofa suna hada ido kirjinta ya buga da karfi. Adai lokacin Abhi ya kira Mammah awaya. Nafseen kuma................ GASA,,,,GASA,,,GASA _*INADA BUKATAR CIRE GWARZAYEN MASOYAN LITTAFINNAN ABUN ZAI KASANCE YANAYIN SHARHINE,YAWAN SHARHINKI TARE DA NUNA SONKI/KA GA LITTAFIN DUK WA INDA BASA GRP DINA ZA SU IYA YIN SHARHI TARE DA TUROMUN TA NUMBER TA DAKE KASA DAGA YAU ZA AFARA HAR IYAZUWA RANAR DA ZAN KAMMALA LITTAFIN,INA SON MASOYAN LITTAFINNAN SU BAYYANA GARENI ADUK INDA SUKE,KARAMAWA TA MUSSAMAN GAREKU,ABUN SIRRINE BAI FADUWA SAI KUN GANEWA IDANUNKU🥰*_ 08103080717 ✍️ Xayyeesherthul-humaerath [4/7, 9:51 AM] Xayyeesherthul-Sweery: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_ _(Nafseen)_ *NOBLE WRITERS ASSOCIATION* °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._ °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° https://www.facebook.com/106494781436168/ NA XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH ✨6STARS INDEED _*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_ PAGE-28/29 *REAL ANTYN BEAUTY🥰GODIYA MAI YAWA TARE DA FATAN ALKAIRI GA REKI DA RAYUWARKI GABADAYA INA FARINCIKI DA LITTAFIN XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH🥰 ALLAH KARA BASIRA* 😉😉 *MY GRP MEMBERS SMILE NA SAN ANSABA MUN UZURI DUK WADDA BATAI SHARHI BA SAI MUN HANATA GANIN YAH JAMEEL😂* *** Kabeer Ya sake Murmushi Tare da yin sallama. Jikinta asanyaye ta amsa kasancewar gani take abun da ta mai aranar ya isa yasa ya barta ta huta amman ina. "Ina hini? "cewar Maryam Murmushin ya kara sakewa tare da fadin, "Lafiya fatan kina lafiya kema?" Shiru tayi batare da ta ba shi amsa ba. Kabeer ya kalleta ga dukkan alamu Maryam tana cikin yanayi na damuwa azuciyarsa yake fadin hakan wanda a zahiri kuma ya ce, "Daman naje gidane Mama ta sanar dani cewa kina nan Nafeesa ba lafiya, Fatan yanzu jikin dai da sauki?" Sabeer ne ya katse Maryam wajen yin maganar tare da cewa , "Anty Wai inji Mammah bakon ya shigo cikin falo." Maryam ta ce, "Bismillah mu shiga ciki." Sun shiga sun tarar da Mammah na waya da Abhi yana sanar da ita yadda suka kaya da Alhajin Mutansir, Mammah ta numfasa, "Lallai ma Mutuminnan wato da kudi yake son siyanmu da ma 'yar tamu shiyasa ko biyar ban taba ba akudin da ya bada.". Abangaren Abhi ya ce, "Yawwa Matar kirki kinga hakan yafi kuma in sha Allah da zaran na shigo gari zan zo na maida masa kayansa,tsaya wai ina Ammiena ne? kwana biyu fa ko waya bama yi kodai karatunne?" Cikin Sauri Mammah ta ce, "Eh,eh dazuma suka fita da Maryam,maganar take hawaye na zuba a idanunta." Jikin Abhi ya yi sanyi yi yana kokarin fahimtar cewa da kwai lamarin da ake boye masa ya ce, "Madam ki fadamun gaskiya,Ammiena tana lafiya ko ya?" Goge hawayen tai cikin dauriya ta sake murmushi wanda sai da sautinsa ya fito ta ce, "Ammien Abhi na lafiya Kasanta da nacin karatu inta dawo in sha Allah zan sa ta kiraka." Shima sakar Murmushin Yayi to, "Ma sha Allah." Daga nan sukayi sallama. Mammah ta dawo da dubanta ga Kabeer da Maryam. "Ah Maryam kin bar bako ba ko ruwan sanyi? maza jeki dibo masa ruwa."Cewar Mammah. Kabeer ya sauka akujerar ya gaida Mammah cikin girmama kan ya zauna tare da fadin, "Mama Ina Nafeesa fatan dai jikin da sauki." Mammah ta ce, "To Alhamdulillah da saukin dai zamuce amman Nafeesa kam gata nan a mutun amman kamar gawa." "Subhnallahi! Mama ko zan iya ganinta." Mammah ta tashi , "bismillah." Kabeer ya jima yana kallon yanayin Nafeesa kan ya duba Mammah tare da fadin, "Wanene wannan da Nafeesa ke mutuwar so?" Sai da Mammah taji wani ras tare da zubawa Kabeer ido. Murmushi Yayi , "Mammah karki damu ban san gaibu ba,amman Allah ya mun baiwar fahimtar matsaloli mussaman wadda ta shafi irinta Nafeesa,kuma in sha Allah Nayi alkawarin nema ma Nafeesa mafita,In ba matsala muje falo mu tattauna." Mammah ta ce, "Ok ba komai muje." Ko da sukaje falo Mammah ta bukaci Maryam da tayiwa Kabeer bayanin komai domin ita ce tafi kowa kusanci da Nafeesa dan haka tafi kowa sanin komai. Maryam ta masa bayanin komai, akarshe ta kara da, "A kullum inna bukaci Nafeesa da ta fadsmun wani abu game da Nafseen ta kan cemun Sirrine bata taba fadamun, kuma aduk lokacin da wani mummunan abu ke shirin faruwa da ita yanayinta na chanjawa ko da batai komai ba alokacin wanda ya mata abun ko ya bata mata rai sai wani abu ya sameshi nan take, akwai lokacin da nazo na kwana Mammah batasan daliliba wannan barcin Nafeesa tayi bata farka ba har sai da na yarda zanenta akuskure zanen da tasabayi akullum tana fadin cewa shine NAFSEEN dinta. Kabeer ya gyara zama tare da fadin , "inba matsala ko zan iya ganin zanen?" Mammah ta ce, "Me zai hana? Maryam tashi ki dauko." Haka kuma akayi Maryam ta dauko zanen tare da mikawa Kabeer. Sai da Kabeer yayi suman zaune na wasu sa'anni "Abun Mamaki baya karewa tabbas wanda ke jikin zanen sunanshine Jameel Nafseen kamar yadda Nafeesa ta saba fada maku kuma abokinane mazaunin garin kaduna,zanen ba inda ya banbanta da Nafseen tambayata anan duk da nasan bakwa da amsarta shin Nafeesa ta taba ganin Nafseen ne? abun da matukar mamaki wannan wace irin sarkakiyace mai cike da boyayyen sirri." Mammah ta ce, "Kwarai a kullum mai maganinta kan fada mana cewa akwai boyayyen sirri kuma itama hakan take fadi,Amman yanzu wani taimako zaka iya mana tunda abokinkane, ba damuwata ace ta auren shi ba Aa ya bayyana ko ma huta da wannan lamarun." Murmushi Kabeer yayi, ga duk alamu tunani yake ya diba dan lokaci kan ya ce" In sha Allah komai ya zo karshe yanzu bara in gwada wani abu Ko Allah zai sa adace,Mintuna kadan zan dawo." Har yaje kofar fita ya dawo yana, "Watakil ba arasa ba,kuna da daya daga cikin wa innan turarukan Tempot smart,Blackberry,koMemory?" Da sauri Maryam ta amsa da , "Eh wa innan sune turaren Da Nafeesa ke amfani da su ai kuma duk da kwai adakinta." Alamun Mamaki ya bayyana fal azuciyar Kabeer yana son yi magana sai kuma ya tuna abun da ke gabansa na farfadowar Nafeesa Kallon Maryam ya yi kan ya ce, "Muje ki bani?" Abun mamakin anan shine dukka turarukannan da Kabeer ya jero sune wa inda Nafseen ke amfani da su kuma ga Nafeesa ma da su,shin wannan wace irin soyayyace? kada ku manta Nafseen bai ma san Nafeesa ba bare ya san wacece ita. Suna shiga kuwa gasunan duka ukun ajere kan dress mirrow dinta,Maryam ce ta karasa tare da dibo masa ,tempot smart ya karba tare da budewa kan ya yi kokarin fesawa Nafeesa ta bude ido,wani irin numfashi take tare da shekar kamshin. Dan Mamaki kowa ya rasa tacewa. Kokarin motsi take amman ba dama jikinta kamar adaddaure,Bude bakima tai magana ta kasa harshenta ya rike. Duk abun nan da take ba mai gani, illa hawaye da ya fara kwarara daga idanunta,Subhannallah cewar Kabeer, Maryam da Sabeer kuwa sai Kuka, Mammah ko ta rasa abun yi. Ruwa Kabeer ya bukata Mammah ta kawo yayima Nafeesa addu'o'i tare da shafa mata ihu ta fara tana, "Wallahi sai mun kasheta bazata taba auren shi b mu zamu auresa." Kabeer ne ya masu tsawa tare da fadin, "Shi wa?" "Shi,shi din." cewar su Tsawa tare da ruwan addu'ar ya kara yarfa masu, "Na ce ku fadsmin shi wa?" ya karasa maganar yana feshe masu turaren hannunsa "Shi MUTANSIR din." Kabeer ya ce, "Waye kuma MUTANSIR? nunu Maryam suke suna, "ita ta san shi kuma tasan komai." Nan da nan jikin Maryam ya fara rawa ta kasa magana sai Mammah ce ta ma Kabeer bayani atakaice tun da itama ba ta gama sanin komai ba. Dawowa yayi ga shedanun ya na , "Waya turo ku? ku fada mun ko kuma in cigaba da azabtar da turaren nan." Kukan Wahala suke suna fadin, "Amina,Amina budurwar Mutansir ta turomu mu kasheta,mun zo tana barci ba dama muyi abun da mukaso aikatawa masu tsaronta sun fi karfinmu hakan yasa mukai nisa da barcin nata ya zarce wanda ta saba, sun hanamu mata komai mu kuma bazamu barta ba har sai ta rabu da Mutansir." Kabeer ya yi ajiyar zuciya, "Wai shin ku wasu irin Shedanune? me ta tare maku? na ga shi Mutansir din ke son ta ba ita ke son shi ba,ina mai tabbatar maku da cewa ku fita ku bar ta ko in cigaba da azbtar da ku." Haka dai Kabeer yata fama da azzalumai da kyar suka tafi,suna tafiya kuwa Nafeesa ta samu barci. Cikin damuwa Mammah ke fadin, "Fatan dai ba komawa tai ba?" Kabeer ya ce, "Aa ba matsala wannan normal barcine nan da anjima ko cikin dare zata farka." Mammah,Sabeer da Maryam suke hamdala Godiya sosai Mammah tayi Kabeer tare da sa albarka,Maryam kuwa sai da ta rakashi har wajen motarshi. Godiyar ita ma ta fara mai,cikin fara'a yake fadin, "Ki dai na godiyarnnan ban so,an kusa kiran Sallah ki koma gida,sannan in da hali kima NAFEESA alwala kan ta farka,In sha Allah gobe na tashi daga aiki zan zo mu karasa yadda za a abullowa lamarin." nan sukayi sallama. ***********Misalin karfe shabiyu na dare Nafeesa ta fara kiran sunan Nafseen," Uncle Dan Allah karka mutu, in ka mutu nima ba zan.......... *HAR YANZU DAI MUNA CIKIN GASAR NAN😉LAMARIN NA MUSSAMANNE AKWAI WANI ABU DA BAN BAYYANAR DA SHI BA CIKIN FEJINNEN KO WACECE ZATA IYA FADAMUN? NAFEESA TA FARFADO LOKACIN DA TAJI KAMSHIN TURAREN SAHIBINTA,KAN DAGA BISANI SHEDANU SUKA BIYO BAYA🤔KU TUNA LOKACIN DA NAFEESA TAI WANNAN BARCIN MEYA FARU ALOKACIN? SANNAN BAYAN WANNAN ABUN YA FARU ME YA KARA FARUWA DA YASA BARCINTA NISA😉A BAYYANE ABUN YAKE AMMAN BA KOWA ZAI FAHIMTA BA😉FATAN ALKAIRI MASOYANA🥰* DOMIN TURO SHARHI KO AMSA 08103080717 Urs Xayyeesherth ✍️ Xayyeesherthul-humaerath