20/10/2021, 20:37 - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more. 20/10/2021, 20:38 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _Jazakillah bilkhair for taking your time to check out my book,I promise you'll never be disappointed. Well..this isn't your usual stories,And I'm loving it more and more with each passing second of my life._ _I'm very thankful to all my fans for their constant love and support I am what i am because of their unconditional love!_ Habibaties barakallahu fikuuuuuu a kakkaɓe zani so You can share and share and share to all groups fisabilillahi! ```Special greeting to ELEGANT ONLINE WTITERS ina ƙaunar ku😍``` EPISODE1️⃣-2️⃣ MAIDUGURI/ BARNO My first word on my story is SAMBISA Forest, The Sambisa Forest is a forest in Borno State, northeast Nigeria. It is in the southwestern part of Chad Basin National Park, about 60 kilometres (37 mi) southeast of Maiduguri, the capital of Borno State. Baƙin daji ne mai girma da tsayin gaske, anyi noticing babu wani daji daya kaisa girma da both faɗi tsayi,ga wasu manyan bishiyoyi da kwazazzabe, duhun dake cikin dajin yafi gaban kwatance, kai tsaye bazan iya siffanta muku duhun sa ba, but yaya kake imagine ace ka rufe idanunka wanne kalan duhu zaka gani? To zan iya haɗa hudun cikin idanun mutum da kuma duhun dake ciki dajin SAMBISA, mugwayen dabbobi babu kalan da babu har wacce ba kayi tunanin ganinta a wajan ba zaka sameta, lokuta da dama ko da bamu da masaniya a kan dajin Sambisa but muna jin labarinsa a cikin kafar yaɗa labarai, irin su Redio,T.v, Media, uwa uba idan ka je BBC Hausa news, ko kuma ka kunna tashar aljazira, wasu da dama basu san dajin Sambisa ba, amma faruwar annoba ta farko wata BOKO HARAM, wanda kowa yasan cewa BOKO HARAM ya fara a 2002 zuwa 2009. (BOKO HARAM Home Politics, Law & Government Law, Crime & Punishment Crime, Terrorism & Counterterrorism Boko Haram Nigerian Islamic group BY The Editors of Encyclopaedia Britannica View Edit History FULL ARTICLE Boko Haram, (Hausa: “Westernization Is Sacrilege”) byname of Jamāʿat Ahl al-Sunnah li-l-Daʿawah wa al-Jihād (Arabic: “People Committed to the Prophet’s Teachings for Propagation and Jihad”), from 2015 also called Islamic State in West Africa (ISWA) or Islamic State’s West African Province (ISWAP), Islamic sectarian movement, founded in 2002 by Muhammed Yusuf in northeastern Nigeria, that since 2009 has carried out assassinations and large-scale acts of violence in that country. The group’s initial proclaimed intent was to uproot the corruption and injustice in Nigeria, which it blamed on Western influences, and to impose Sharīʿah, or Islamic law. Later the group vowed to avenge the deaths of Yusuf and other group members, who were killed by security forces in 2009. In 2015 the group pledged allegiance to the Islamic State in Iraq and the Levant (ISIL) and took the name Islamic State (or State’s) West African Province (ISWAP; also known as Islamic State in West Africa, or ISWA). The next year the group split, with one faction retaining that name and the other reverting back to the original appellation). Wata tafkekiyar bishiya ce,wacce take ɗauke da manyan kogona wajan goma a cikinta , ko wane kogo idan ka shiga zaka samu hanyar ɓullewa a cikin sa, banda kukan dabbobi kala daban-daban babu abinda yake tashi a cikin kogonan. can cikin baccinsa ya ji kamar ana ƙwalla kiran sunansa, kasancewarsa ba mai nauyin bacci ba, yasa ya buɗe dara daran fararen idanunsa wanda suka janye tare da yin jaa sbd tsabar baccin da yake cikin sa, har wani ciwo-ciwo ya ji kansa nayi masa, shiru yay domin yana son ya ƙara tabbatar da abinda kunnuwansa suka jiyo masa a cikin baccinsa, jin shirun yay yawa yasa yay baya kaɗan tare da sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya,kana ya juya zuwa ɓangaren hagunsa, sannan ya karanta addu'ar neman tsari, ya lumshe idanunsa tare da ƙanƙame pillow dake faffaɗan ƙirjinsa,yana rufe idanunsa ya ji an ƙara kiran sunansa, tamkar mai kiran yana cikin ɗakin nasa, da sauri ya ƙara buɗe idanunsa ya shiga dube-dube amma babu abinda ya gani, lubalun dake saƙale jikin ƙofar bedroom ɗinsa ne ya fara kaɗawa sannu a hankali, harya gama kaɗawa idanunsa na kan labulan, waro manyan idanunsa yay waje saboda baƙar matashiyar buduwar mai masifar kyau da ta bayyana a gabansa, ko kaɗan bai ji tsoron ganin wannan halittar ba,sai dai yanayin baƙin fatar ta da kuma dugun baƙin gashinta wanda yake jan ƙasa kaɗai ya isa ya sanya zuciyar mutum rabewa gida biyu, abinda ya bashi mamaki yadda idanunta ya kasance baƙi sosai kamar yadda fatar jikinta take, sai dai eyes balls ɗinta blue ne sosai, ga eyes lashes ɗinta zara-zara, har taɓa girarta yake, abu mafi ɗaukar hankali a jikinta shine jajayen laɓɓanta masu kauri sosai wanda suka kasance ƙarama ye marasa faɗi, tana sanye da fararen kaya har ƙasa wanda suka rufe kofaton dake jikin ƙafarta, tattausan murmushi ta sakar masa, wanda yasa ya ƙara ware manyan idanunsa a kanta, da ace yana mugayen mafarkai kai tsaye zai iya cewa mafarkin yake, but isn't dream is real, a zahiri yake ganin komai a cikin ɗakinsa kuma a gabansa, ƙara sakar masa Murmushi tayi kafin a hankali ta miƙa masa hannunta, cikin wata murya very cool and slowly tace "zo mu je" juya mata ƙwayar idanunsa yay kana yay mata nuni da shanyayyun ƙafafuwansa, kallon ƙafar tayi sai kuma ta marairaice fuska, kafin a hankali ta taka zuwa gare sa, tana zuwa tasa zanƙalelen hannunta ta dafa ƙafaɗarsa, nan take wata guguwa mai ƙarfin gaske ta lulluɓe su, bai tashi ganinsa ba sai a cikin wannan kogon dake cikin bishiya na dajin Sambisa. A gigice yake juya idanunshi yana ƙarewa cikin kogon kallo, shigarsu cikin kogan kuma yasa yay haske sosai, kai tsaye wajan wata haɗaɗiyar kujera mai kyau da kuma tsarin gaske ta zaunar da shi, sai a lokacin ya fahimci ashe a hannunta yake riƙe, ba tare kuma da tayi masa magana ba ta juya ta shige cikin wata ƙaramar hanyar, har 5mins yana zauna yana ƙarewa wajan kallo, a iya tarihin rayuwarsa zai iya cewa bai taɓa ganin waje mai haɗarin gaske irin cikin kogon nan ba, ko a Indian series film dake yake kallo anytime bai taɓa ganin haka ba, ko da a cikin horo Film ne, sai gashi yanzu a zahirance yake ganin komai a idanunsa, bawai a bashi labari ko ya gani a Film ba, a'a all this yana faruwa dashi ne a karan kansa, tambayar da yakewa kansa why bai ji tsoran ta ko kuma ya shiga firgici da ganin ta ba??, Ko dai yana cikin replaction ko nightmare ne?? Fresh skin ɗinsa ya kalla a hankali kuma ya miƙa hannunsa tare da mintsinar saman fatar sa, zafin da yaji yasa yay saurin faɗin "Auchhhhhi!!" Daga can masan kansa yaji ance "what happened to you Bil'adama??" Fararan idanunsa ya ware cikin ransa yace ashe suna iya English? Ita kam tana barin wajan cikin wani makaken kogo ta shige a nan ta samu dandazon Jinnu ƴan uwanta kala daban-daban, wata tsuhuwa ce wacce ta fito a siffar mutane ta kalli buduwar tace "Duk kin tashi hankalinki! Muma kin tashi namu,wai meke faruwa dake ne Airah??" Wasu hot hawaye ne suka kawo cikin idanun Airah, sai kuma ta zube a ƙasa tace "Kiyi min afuwa Kakata, nasan kaf cikin zuri'arki nice na fara karya dokar ki ta shiga jikin Bil'adam, amma babu yadda na iya dole tasa nai haka, kince zamu iya taimakawa mutum a lokacin da mu kaga yana buƙatar taimako, kin hanemu da shiga jikin Bil'adam bisa raddin kanmu" shiru tayi sbd tsawar da Tijama tayi mata, wannan shine karan farko da kakarta ta tayi mata tsawa, cikin ɓacin rai da kuma tashin hankali TIJAMA tace "you're mad Airah,Yajjju da baihakkk Airah ,Bisaka wadayikiii bil Adam Airah?" Cikin kuka Airah tace "Laa! Kaka,but ina son taimaka masa ne,am going to help him Tijama" cikin tsawa Tijama tace "me ne?? Ki rasa wa zaki taimakawa sai shi?? Kin san wanene shi kuwa Airah? Mu kanmu muna buƙatar taimakonsa bare mu mutaimakesa, you're so selfish Airah" Wani Saurayi ne ya kalli Tijama yace "Amma Tijama yana da kyau mu ji dalilin daya sa take son taimkon Bil'adam kamar wanann mutumin wanda idan yaso a lokaci ɗaya zai iya kaimu lahira gaba ɗayan mu kuma...," Shiru yay saboda hannu da Tijama ta ɗaga masa tace "stop interrupt Tuɓe ,babu abinda Airah zata faɗa wanda ban san da shi ba,komai ana barwa lokaci ne, domin shi ke sawa a bayyana komai , Airah tayi mana gaggawa ta ɓata mana komai, ko da za muyi nasara akan taimakon nasa amma yanzu bamu da damar yi, saboda Airah ta ɓata komai tayi abinda sai nan da shekaru wajan biyar ya dace ace munyi shi, babu wanda baya son mutumin nan,hadda mu Jinnu muna ƙaunarsa, mu musulmai ne kuma Turawa ne, haka kuma ALLAH! Yayo mu a cikin halittun da ba kowa yake ganin su ba, sai dai mu kalli abinda mu kai niyya, Airah kina da girman kai sosai, baki jin magana, baki san girman kai yasa Ubangiji ya sakko da Iblis daga Sama ba zuwa duniya ba?? Ko so kike ki zama ƴar uwarsa Airah ??" Da sauri Airah ta girgiza kanta tace "Auzubillahi! bana fatan hakan Kakata, ni dai alfarma nake nema wajanki Kakata ki daure kiyi min ita dan Allah!", murmushin baƙin ciki Tijama tayi, domin tasan jikar tata abu ne mai wahalar gaske ta fahimci abinda take son fahimtar da ita, kuma bata son gaya mata muhimman abubuwan da suke tare da wannan bawan Allan,tana son ta bari lokacin komai yazo ya wuce, da zarar lokaci yazo komai zai bayyana kansa ba tare da sun bayyana shi ba, shiru ne ya biyo baya kowa da abinda yake saƙawa a cikin ransa, ita Airah tana son faɗawa Kakar tata wani abu amma tana tsoro, kamar daga sama taji muryar Tijama tana faɗin "me kike ɓoyewa a ranki Airah ! Feel free to ask" girgiza kai Airah tayi tace "No! Tijama idan lokacin yayi zaki sani amma wannan *SIRRIN MU* ne", Murmushi kawai Tijama tayi kafin tace "me kike so yanzu ai masa?" Da sauri Airah tace "Ina son na bashi muƙami" kafin Tijama tayi magana Tuɓe yace "Muƙami a cikin Jinnu Airah? How can that be possible?" Kallon Yayan nata Airah tayi kafin tace "Is very simple ai, shi kansa bazai san an bashi muƙamin ba, but every night zanna dauƙo sa zuwa zaman fada, zan mantar da shi komai", Dariya Tijama tayi tace "Shirme dai sai yaro, Bil'adam zai zama jagoran Jinnu kenan Wow!" kamar Airah zatai kuka tace "please Tijama" jinjina kai Tijama tayi kana tace "je ki bashi Allah ya ba shi ikon Mulkan rundunar Jinnu bisa gaskiya da Amana", tana faɗin hakan tai girgiza ta ɓace daga wajan, shima Tuɓe bayan ta yabi ya ɓace. Yana zaune yana lumshe idanunsa time to time ya kan buɗe su,wani sanyi yaji a saman ƙafaɗarsa ga wani abu mai tsayin gaske daya fara yawo a saman wuyansa , da sauri ya ɗaga kansa nan idanunsa ya sauka saman wata ƙatuwar mesar dake bin jikinsa tana naɗesa, kasa motsi yay, kuma har zuwa lokacin babu wani tsoro daya shige sa, shi ji yake ma ina ma ya dauwama a wajan har ƙarshen rayuwarsa, domin da rayuwar da yake a cikin mutane gwamma wannan sau dubu da waccan, sai da Mesar ta kama naɗesa tsaf sannan ta ɗaga fuskarta zuwa dai-dai fuskarsa ta shiga ƙare masa kallo, can kuma tai girgiza sai gashi ta rikiɗe ta dawo Airah ,tai kwance jikin sa, motsi yay kaɗan da idanunsa ta kalli bakinsa sai kuma ta kalli idanunsa, shi ma kallonta yake ko ƙiftawa babu, a hankali Airah ta miƙe daga jikinsa kafin cikin ɗaga murya tace "Congratulations! Now you're the king of Jinnu, yanzu kai sarkin ALJANU ne SHEIKH IMAM HAMDAN!!...... SHARE fisabilillahi dan ALLAH 20/10/2021, 20:38 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ EPISODE3️⃣-4️⃣ With much surprise wanda aka kira da Sheikh Imam hamdan ɗin yake kallon fuskar Airah, har kawo lokacin kuma ya kasa cewa komai he is just watching at her face like he is try to remember something fast, but he can't, dukkan abinda Airah take he couldn't understand her, shi dai yana nan a yadda ta ɗauko sa kuma ta ajjiye sa, murmushi tai masa kafin cikin nutsuwa tace "i knew baka san wacece ni ba, so don't mind me, kawai ka saurari me zance maka ya shugabana" fararen idanunsa wanda suke ɗaukan hankali mata harda maza ya juya mata irin kallon am with you ɗin, nan ya baza all ears ɗinsa kawai yana jiran ya ji menene za tace masa, dariya Airah tayi tace "You know what? Sheikh Imam Hamdan! " kamar soko haka ya girgiza mata kansa, hannunsa ta kama a hankali ta shiga murza soft fresh skin ɗin tafin hannunsa, kamar mai shafa masa mai, wani wahalallan numfashi ya sauke mai ƙarfin gaske, lokaci guda kuma yaji kansa ya sara masa, da sauri ya runtsa idanunsa wanda one time jijiyoyin kansa suka fito a saman forehead ɗinsa sukai raɗa-raɗa kamar an zana su, da sauri da sauri ya shiga sauke ajjiyar zuciya yana jin wani sanyi na ratsa cikin farar fatarsa zuwa cikin nama jikinsa haɗi da ɓargon dake sarrafa cikin ƙashinsa, wanda hakan ya haddasa masa afkuwar wani zazzafan zazzaɓi mai ƙonar da jinin Mutum, duk abinda yake tana kallonsa, kuma tana fahimtar komai dake faruwa dashi, abu ɗaya da ta gagara yi shi ne ta haɗa ido da shi, she can't, yana da wasu sexy and killer eye balls, wanda anytime suke a lumshe kamar mai jin bacci ko wanda yake shaye-shaye, wanda bai san shi ba idan ya kalle sa zai ɗauka he's always sleeping ne, but ba haha bane, kawai dai he's strong Man, cikin ƙasa da murya tace "Kai mutum ne, ni kuma Aljanna ce, amma mene yasa nake jin ina da relation da kai?, Ina jin kamar na sanka tun da kamar na taɓa rayuwa da kai, tambayar shi ne where? mene yasa nake jin feelings a kanka?, my grandma told me bil'adam suna da son kansu da yawa, basu da tausayi ko imani, basu tausayawa na ƙasa dasu, kowa hope and wish ɗinsa a kansa yake ƙarewa, sometimes nake ɓadda kama zuwa Bil'adam just to watch the people, but seriously they're all many different types of people in your society, kamar dai kai you have a good heart, baka da damuwar kowa burinka kowa ya amfana daga baiwar ka, amma idanun jama'a na kanka mai yasa mutane duniyarku ke son cutar da rayuwarka ne SHEIKH IMAM HAMDAN?", duk maganar da take idanunsa a lumshe suke yana jin yadda take ta zuba ita kaɗai kamar parrot, wato a Aljanu ma akwai masu shegen surutu kenan?? Ware idanunsa yayi a kanta sosai a hankali kuma ya fara ƙoƙari Motsa jajayen laɓɓansa, runtsa idanunsa yayi a hankali kuma yayi taking deep breath, cikin harshen larabci yace "Wacece ke?" Ƙasa Airah tayi da kanta, saboda yadda zazzaƙar muryarsa ta daki dodon kunanta, ba abin mamaki bane dan ta ji muryar so sweet and cool saboda tasan muryarsa cikin baccinta, amma Wannan ya sha banbam da wacce, wannan is real not dream shi ne a gabanta yake magana da harshen da kowa yake fata da muradin ace ya samesa,domin yazo turanci ya zama ruwan dare, kasa bashi amsa tayi sai ƙasa da tayi da kanta, ganin tai masa shiru yasa Sheik Imam Hamdan saka tafin hannunsa zuwa saman fuskarta ya tallafo haɓarta su kai facing juna sosai kamar mai kunyar magana yace "Answer my question who are you?" Hannunta ta ɗura saman bakinsa tace "shiiiiiit!!" sai kuma ta janye hannunta tace "You asked me at the right time ya shugabana" ganin yadda taƙi yarda su haɗa ido kamar dai wata mara gaskiya yasa Sheikh gyara zamansa a hankali kuma ya kai dubansa zuwa ƙafafuwan ta wanda basu gama komawa na mutum domin ga jelar mesa nan yana gani, ɗauke idanunsa yay yace "Look at me, look into my eyes, akwai wani tarayya daman tsakin mutum da Aljan bani da labari?" girgiza masa kai tayi idanunta na kawo ruwa domin sosai ta ji ta fara shakkar Sheikh saboda jarumtarsa da kuma ƙarfin addininsa, kamar zatai kuka tace "sunana Airah is long story please just keep it on your mind one day I'll tell you everything" kafaɗa ya ware irin "I don't care"ɗin nan, numfashi ya sauke yace "first tell me miyasa kika kawo ni nan?" wani ƙawataccen murmushi tayi sai kuma tace "Yanzu Allah ya nufa ka ganni but every time, every second, every minute you're in my heart,kullum da kai nake kwana" "Uhm" yace kawai yana ƙara ware rikitattun idanunsa a kanta sannan tace "what i mean kullum tare muke kwana a bed ɗinka, bana samun cikakken bacci mai nutsuwa da kwanciyar hankali indai ba'a jikinka nai bacci ba, duk sanda kayi nisa dani ina jin kamar ƙarshen rayuwata yazo ne, ɗomin jikinka kawai ke sawa na samu nutsuwa da kwanciyar hankali, na so faɗawa Tijama sai kuma na fasa saboda wannan SIRRIN MU ne, ni da kai, i thought it was a play ashe ya wuce haka, I'm in love with you Sheikh Imam Hamdan ,i love You too much dear, i love You till the rest of my life Imam ,na ɗauka bani da hankali ko kuma shirme, why Aljana za ta so jinsin mutane, mutum kamar Imam, to muma ai Ubangiji ya halicce mu kuma ya sanya mana zuciya kamar yadda kuke da ita, kaga ba abin mamaki bane dan zuciyata ta kamu da sonka Imam, please accept me as your wife Imam, zan zame maka komai babu wanda zan bari yasan cewa ni Aljana ce, zan ta baiyana gareka da kuma danginka a matsayin mutum just like you're, bawai haka ne kaɗai burina ba, ina son baka kariya akan kariyar da Ubangiji yake baka, ba lallai kasan abubuwan da suke ɓoye ba amma ni nasan komai naka, dan Allah accept, kada ka juyan baya, kamar yadda Mamana da Abbana sukai min,Tijama da Juɓe sune kaɗai suke supporting nawa" ta ƙare maganar tana saka masa kuka tamkar ba Aljanna ba, sosai zuciyarta da kuma hurinta haɗi da gangar jikinta suke ƙaunar Sheik Imam,tun tana zanin goyo wata rana ta ji Iyayen ta na magana akan haƙurinsa da kuma jarumtar sa da taimakon da ya kewa talakawa , tun a sannan ta kamu da soyayyarsa mai wahalar gaske, bata da magana sai ta Sheik, wata rana tayi suffa irinta Bil'adam ta shiga cikin gari, tashin farko gidansa ta nufa tai rashin sa'a lokacin ya je sauke farali a ƙasa mai tsarki, bata tsaya ɓata lokaci ta nufi makkah a nan tai arba da shi a cikin harami gaban ka'aba yana sanye da fararen kaya masu ɗaukar ido, surar jikinsa a bayyana ga six packs ɗinsa abin birgewa, fari ne jajirr kamar ka taɓa shi jini yay tsartuwa haka yake, ko ina na jikinsa gargasa ce kwance sai sheƙi take gwanin sha'awa, is too young domin bazai wuce 23 zuwa 25 ba,t a ɗauka babba ne sosai, amma yanayin hutu da kuma cima mai kyau yasa ya zama cikakken Namiji mai jini a jika da kuma lafiya, yana da faɗin ƙirji wanda duk rabin ƙirjin sa gashi ne kwance lub-lub, kana ganinsa kasan yana gyming yana da wasu kalar fresh pich lips wanda suke very soft and shinny he's behaving like king of Saudi Arabia, eye lashes sunyi zara-zara har saman girarsa, babu abinda ya bawa Airah mamaki sai ganin sa da tayi saman wheelchair da alama yana da nakasa bashi da ƙafa, tun a lokacin taji tausayinsa ya kamata sosai, gashi dai babban mutum yana da komai na rayuwa kuɗi, ilimi both boko da Arabic yama fi ƙarfi ga Arabic domin a nan Saudi'a yay karatunsa, maganar kuɗi kam ba'a magana, bai rasa komai na rayuwarsa ba, babu abinda ya nema ya rasa, amma ya rasa farin cikin sa uwa uba babu ƙafar taka wa, a nan ta gama kallonsa ta koma cikin dajin da suke da zama, tun daga ranar ta ɗaura lalurar duniya a kansa sonsa take sosai, taɓa ta da yayi yasa ta sauke ajjiyar zuciya mai ƙarfin gaske, kafin ta ɗaga jajayen idanunta ta kalle shi, saurin ɗauke kanta tayi saboda ba zata jure kallon cikin idanunsa ba, maganarsa ta dawo da ita hayyacinta inda yake faɗin "Ashe baki da tausayi ke mai son kanki ce ban sani ba? tayaya zan iya soyayya da Aljana what kind of rubbish ?" Cikin hasala itama tace "You can Sheikh Imam Hamdan ,sau nawa kana tarayya dani a Matsayin mata" da sauri ya kalleta Murmushi tayi tace "Yeah! I'm pregnant with your unborn child Sheikh, bana da niyyar cutar da kai ko kuma cin zarafin ka, bana son na haifa maka ɗan Haram domin dani da kai duk Halartattun ƴa ƴa ne, sai da aka yi Aure aka haife mu, mai yasa ni kuma zan zaɓi haifar ɗan zina? Ko kayi accepted ɗina as your wife ko kar kayi kasan ina da ƙarfin ikon da zan zauna da kai na saka kayi tarayya dani, ask me why banyi haka ba? kasan dalili shi ne ina sonka Imam, so mai ƙarfi da kuma girman gaske, tunda na bar iyaye na ai ya kamata ka karɓe ni, ka zame min gurbin dana rasa, nima na baka farin cikin daka rasa na shekara da shekaru, ina sonka saboda Allah! Burina bai huce na kula da lafiyarka ba, zuwa yanzu kasan baka da kowa sama dani saboda nice matarka!" Ta ƙare maganar cikin ɗaga murya, murmushi kawai ya saki kafin yace "Na ji mai dani gida" kuka ta saka masa tare da zubewa ƙasa ta riƙe ƙafafuwansa tace "dan Allah dan girma ALLAH! Ka so ni kwatankwacin yadda nake sonka, wallahi zan iya mutuwa idan baka amince dani ba, kuma ɗanka dake ciki na ba" wani bala'in tausayinta ne ya kama shi, ace wai Aljana ita take sonsa har tayi tarayya dashi ya sanya mata ƙwansa a cikin ta, yaya zai yi da rayuwarsa yanzu shi?ta yaya zai iya rayuwa da ita a cikin gidan su? Yadda take masa kuka sosai da kuma yadda take begen nasa akan ya so ta yasa bai san lokacin da yace "Okey! Imam hamdan accepted you as his wife" cikin farin ciki da Murna Airah ta ƙwala wani uban ihu tace "Didn't i told you Tijama, bana gaya maki cewa my Imam has a good heart ba" kallan yadda take tsalle da murna haɗi da ihun yasa cikin ƙasa da Murya yace "Don't scared your Husband" tsayawa tayi da rawar tana jin wani farin ciki na ratsa jikinta, cikin tsananin farin ciki tace "Thank you so much Sheik, thanks once again i can't stop loving you you're my everything" lumshe idanunsa yana jin abinda ya aikata kamar ba dai-dai ba ne,amma yaya zai yi da ita? Ba zata taɓa barinsa ba indai ba amincewa yayi ba, shi yasan bazai taɓa yin tarayya da ita ba, shiru yay kawai yana sauraren bugun zuciyarsa, ganin tai masa shiru yasa ya buɗe idanunsa da sauri ta ɗauke idanunta wanda tun ɗazo ta ɗaura su a kansa, kamar zai kuka yace "gida Please" wajansa ta ƙarasa tare da durƙusawa a dai-dai ƙafafuwansa ,kana ta saka hannunta ta ɗura saman laps ɗinsa tace "Why are you so worried ?" Shiru Imam yayi mata yana tsareta da fararen idanunsa, Murmushi tayi tace "don't worry, yanzu za'ai mana bikin" ware idanunsa yay sai kuma yay calming yace "Owk" miƙewa tayi kana ta haɗe hannayenta waje guda ta shiga tafa hannayenta, cikin ƙaramin lokaci Tijama da Tuɓe suka bai yana, dariya Tijama tayi tace "Congratulations Airah, congratulations Sheikh Imam Hamdan " bai ce komai ba sai hannunsa daya miƙawa Airah kamar yadda ta buƙata,wani ƙaramin ring wanda yayi dai-dai da yatsansa, kana ganin zoben kasan cewa an kashe kuɗi wajan yin sa, banda haske da ƙyalli babu abinda yake, a saman Ring ɗin a rubuta I&A, fuskarta cike da farin ciki ta sanya masa zoben, kallonsa tayi tace "Now is your turn" jikinsa ya shiga lalubawa yaji babu komai sai wani sirin sarƙar gold, cirota yay a jikinsa kana ya nuna mata sirin sarƙar,wajan sa ta ƙarasa tare da durƙosawa dai-dai ƙafafuwansa tai masa nuni da wuyanta, A hankali ya sanya mata sarƙar, tafi Tijama da Tuɓe su kai tare da faɗin "Congratulations Airah and Imam Masha Allah!" Haka nan dai yaji ya samu kansa cikin farin ciki shima, kallon Airah yayi suka haɗa ido ganin yadda idanunta ya cika da hawaye yasa a hankali ya ware mata hannayensa da sauri ta zo wajansa tare da faɗawa jikinsa , a tare suka sauke ajjiyar zuciya, shiru Sheikh yayi yana duban agogon hannunsa yasan yanzu Subhi ya kusa yana buƙatar komawa gida, ƙasa yayi da murya dai-dai fuskarta yace "Can i go?" Fuska ta marairaice tace "babu wani gift?am your wife Sheikh" taɓe baki yay yace "me zan maki?" Dariya tai tace "ok lemme give you a special kiss Rayuwata" zaro ido waje yayu tace "Yes! Sabon sunanka ke nan a gareni RAYUWATA" lumshe idanunsa yayi kafin ya saki jishi tare da faɗin "Uhm" Sumar kansa Airah ta shafa a hankali kuma ta sanya bakinta cikin nasa da niyyar bashi hot kiss..... 20/10/2021, 20:38 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _This book is for sale it's #500 via 0116886423 Sulaiman Naima s union bank, evidence of payment 08119237616, ga mutan NIGER sai suyi mgn a wannan number 84506476_ EPISODE5️⃣-6️⃣ Da sauri Sheikh Imam Hamdan ya zare bakinsa, bai son abin da take shirin yi masa,kuma bai son ya ɓata mata rai saboda ya tabbatar da ingancin son da Airah take masa,shima garesa yana son ya kwatanta yi mata nasa kalar halaccin ko da ba zan so ta ba,ta guji iyayenta a kansa to namiji yay haka ai yana tare da fushin Allah bare kuma ace mace,dan dai bai son kalar nasu abun ba, tunda suɗin ba wai kamarsa suke ba, Shiru Airah tayi tana jin babu daɗi a cikin ranta kuma bata son takura masa saboda ta ga kamar bai gama yarda da ita ba,ita kuma burinta bai huce ya yarda da ita su saba su zama tamkar Aminan ƙwarai wanda dukkan abin da ya samu ɗaya sai ɗayan ya ji a jikinsa,ganin yadda duk ta sauya fuska kamar dai za tai kuka yasa ya tallafo haɓarta yana lumshe idanunsa kamar bai shirin yin bacci a wajan,cikin ƙasa da Murya wannan karan da larabci ya ce "Ma'aa sa bakiii?" Girgiza masa kai ta yi tana Murmushi ta ce "it's time to go home" taɓe bakinsa yay tare da fesar da numfashi cikin nutsuwa da fitllatanci ya ce "You look so worry" Idanunta a saman fuskarsa tana kallan ƙwantaccen beard ɗinsa da ke Shinny gwanin sha'awa, hannunta ta miƙa ta shafa sajen nasa ta ce "Yeah!am worry" ba tare daya kalleta ba ya ce "Why?" Sosai Airah ta matsu kusa dashi tare da ɗura kanta a saman cinyarsa ta fara kuka kamar ƙaramar yarinya,sai da ta gaji dan kanta Sannan ta tsaya da kukan tana sakin ajjiyar zuciya kafin a hankali ta ce "I Missed you Soo much i missed a lot Rayuwata,kasan lokacin da na ɗauka ina fama da iyaye na akan ka,na rabu da su yanzu saboda ina tunanin zan samu farin ciki a wajan ka,ashe nayi kuskure su Aljanu ba halittar Ubangiji ba ne? Bama da Zuciyar daza mu so dukkan abin da mu kaji muna sonsa ashe? Na daɗe ban yi bacci mai daɗi ba kasan mene yasa? Ba na son taku raka kona matsa maka,a kullum baka da lokacin kanka sai na Mutanan gari dana wa'azi a matsallatai da ba wa mutane darasi,baka samun nutsuwa cikin dare idan kuma nace a wannan daran zanzo inda kake bazan barka kayi bacci ba,zakai ta mafarkai kala daban-daban ƙarshe ka tashi da ciwon kai,ni kuma bana Fatan hakan ya kasance da kai,shiyasa na zaɓi nai nisa dakai ina buƙatar ka Imam,ina sonka kai ne Rayuwata kai ne farin ciki na dan Allah don't ever betray me,kada ka samu wata a jinsin ku kace zaka manta dani" hannunsa ta kama ta ɗura saman cikinsa tace "I'm pregnant with your unborn child Rayuwata me and your unborn child need you please don't ever trying to betray me" kasa magana Sheikh yayi saboda wani tausayinta daya ratsa zuciyarsa ware mata hannayensa yay da sauri ta shige jikinsa tana sakin wani sabon kukan covering yay mata da faffaɗan ƙirjinsa "it's okay AIRAH!!" Turo bakinta tayi gaba tare da dukan ƙirjinsa tace "stop calling my name Rayuwata just give me a beautiful and special name" wani lafiyayyan murmushi yay mata ya ce "just look at you, you're crying like a baby" kanta ta ɗaga lokacin na farko kenan data sanya idanunta cikin nasa, slowly ta dinga nufar bakinta zuwa ga nasa, copping face ɗinsu tayi waje guda Sannan ta buɗe masa bakinsa da hannunta da sauri kuma ta sanya bakinta saman nasa zatai kissing nasa. A firgice Sheikh Imam hamdan ya farka daga nauyayyan baccin daya ɗauke sa mai cike da tarin mafarkai na abun mamaki, ba tare daya buɗe idanunsa ba ya shiga karato addu'ar da addini ya kuya mana idan mun shiga cikin irin Wannan bad dream ɗin kamar haka: _اعوذ بكلمات الله التامات من غضبه وقابه،وشرعباده ومن ه‍مزات الشياطين وأن يحضرون._ _(Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga fushinsa,da uƙubarsa,da sharrin bayinsa,da kuma wasuwasin shaiɗanu,da kuma kada su zo mini (acikin Al'amurana)._ Bayan ya kammala addu'ar ya ware manyan idanunsa sannu a hankali kuma komai na mafarkin ya fara dawowa cikin brain ɗinsa,murza hanunsa yay yaji wani sabon ring wanda bai san dashi a hanunsa ba, kallonsa yakai zuwa ga zararan yatsun hannunsa wanda suke dugwaye masu kyau, wani farin zobe ya gani wanda akai masa rubutu da I&A shafa zoben yay ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa, idanunsa yaja ya rufe a hankali sosai yake son tuna sunanta amma ya kasa, Yun ƙura wa yay daga kwancan da yake ya jingina bayansa da jikin fuskar gadon,a godon da yake manne jikin bangon ƙawataccen bedroom ɗin nasa ya duba,juya idanunsa yay ya ga lokaci har ya fara jaa domin tuni akai kiran fari, yana ta zaune shiru babu abin da yay kuma babu wanda ya shigo cikin flat ɗin nasa,ga lokaci yana ta tafiya, hankali yaga iska na kaɗa labulan dake maƙala jikin window, With much surprise ya fara bin window'n da kallo,domin ya tabbatar bai kwanta bacci ba sai da Granny ta gyara masa komai ta rufe ko ina,amma ya ya akai window'n ya buɗe shi ɗaya? Ganin bashi da amsa babu kuma wanda zai tambaya yasa ya ja bakinsa yay shiru ya bi window'n da kallo,ganin iskar tai tawa yasa ya lumshe idanunsa yana jin sanyi da wata nutsuwa na ratsa jikinsa, seriously Imam he's more handsome guy he's innocent and smart,jin ana shafa sumar kansa yasa ya buɗe ido ganin Granny tsaye a kansa ya sanya ya sakar mata tattausan Murmushi "Sorry sweetheart I'll keep you waiting am sorry for that,na makara ne" jinjina kai yay ya ce "Uhm" Wheelchair Granny ta jawo tare da buɗe ta,sai da tazo daf dashi sannan tace "Get down sweetheart" jan jikinsa yay sosai zuwa gefen gadon da taimakon Granny ya samu ya zauna a saman Wheelchair ɗin cikin nutsuwa ta turasa zuwa cikin Bathroom ɗin sa,Wow wow! Very beautiful komai na cikin bedroom ɗin white color ne, shower, Sink, mirror, Jakuzzie, towels, Bathrobe anything is white color, hatta bathroom slippers ɗinsa fari ne tass, tana kaisa bathroom ɗin ta taimaka masa ya sauya kujera daga wacce yake kai zuwa wacce take gaban shower wacce always a cikin bathroom ɗin take sbd wanka, fita Granny tayi tare Wheelchair ɗin kana taja masa ƙofa, kasancewar farar Singlet ce jikinsa yasa bai sha wahalar zare ta ba,haka nan three gaiter na jikinsa zuwa pad ɗinsa gaba ɗaya yay naked, sexcy eyes ɗinsa ya sauke saman laps ɗinsa wacce take fara tass sai Shinny take ga wasu gashi da yay kwance saman cinyoyinsa abin birgewa,ikon Allah! Kenan duk ƙyansa da da iliminsa both sides arabi da boko uwa uba dukiya ta abin mamaki amma hakan bai hana Ubangiji ya tausyesa da wata lalurar ba,sai Allah ya saka yana ɗaya daga cikin jerin guragun duniya,lallai kuɗi zasu iya yi maka maganin komai amma banda lalura,abu biyu zuwa uku ne kuɗi ba zai iya sama baka so ba, na farko Lafiya,na biyu Soyayya,na uku kwanciyar hankali tabbas kuɗi ba zasu taɓa sama maka ɗaya daga cikin waɗan nan ukun ba,duk isarka ko mulkinka ko tarin Dukiyar ka kuɗi baza su taɓa sama maka soyayyar mace ba,haka kuɗin ka bazai taɓa sama maka Lafiya ba,yau ina shugaban mu Umar Musa ƴar addu'a? Da kuɗi na bada lafiya da tuni yana raye yana yawo ko ina cike da kuzari da kuma ishasshiyar lafiyarsa, haka nan duk mai kuɗi bashi da kwanciyar hankali kullum cikin tunani haɗi da zullumin rayuwa yake, Ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke bayan ya gama tunani a ransa,ganin ba wani kashi yake ji ba yasa yana daga inda yake tsaye ya kama Manhoon ɗinsa zuwa cikin toilet ɗin yay fitsari kana ya wanke sama da ƙasa zuwa tsakanin cinyoyinsa na Monhoon ɗin, Wheelchair ɗin yaja zuwa wajan shower ya sakarwa kansa ruwa lumshe idanunsa yay yana jin yadda ruwan yake dukan saman fatarsa, yana kammala wankan yay brush kana yay alwala, hannunsa ya miƙa ya ɗauki long towel ya ɗaura saman waist ɗinsa,ya zamana iya faffaɗan ƙirjinsa ne a waje wanda yake ɗauke da kwantaccen gashi da kuma manyan brest, duguwar ƙafarsa yasa ya bubbuga ƙofar bathroom ɗin,babu jimawa Granny ta shigo fuskarta ɗauke da Murmushi tace "ka kusa yin late a Masque ɗin Rayuwata" saurin kallanta yay saboda jin sunan data faɗa and he try to remembered inda ya taɓa jin sunan Rayuwata, Murmushi kawai yay ba tare da yay magana ba,domin yawan surutu baya cikin tsarinsa,idan kaga yay magana to Granny ce ko kuma best friend ɗinsa Arjun, sauya masa Wheelchair ɗin tayi kana ta jingine ta cikin bathroom ɗin ba gefe guda, a gurguje ta shafa masa wani lotion mai ƙamshi da kuma kama jiki sbd yau taga an tashi da sauyin weather, wata farar Jallabiya mai ƙyan gaske ta bashi ya saka bayan ya saka pad ɗinsa da boxer sai kuma singlet,ta san bai son kayan nauyi yana iya cirewa a ko ina, hiraminsa ta ɗauko ta saka masa a saman sumar kansa kana ta ɗura masa ta wani baƙin igiya na saman hiramin ta ɗauki casbawa ta bashi,wani simple slippers ta bashi mai kyau da tsada,kana ta fesa masa parfumes Difference, dry tai masa tace "Kai Sweetheart kayi kyau kamar a sata a gudu" a karo na farko ya saki Murmushi cikin ƙasa da murya yace "Jazakillah bilkhair Granny" "no need dear it's my pleasure" ana haka Alhaji Hamdan ya shigo shima cikin maroon ɗin jallabiya ya ce "shira bata tashi kullum sai za'a Mosque" Murmushi kawai Granny tayi ta ce "Sai kun dawo ka kula da shi" Barrister ya ce "Ohh Wow! Ni ba'a ta tawa ko?" Harara tai masa ta ce "wa yake batun babba ga ƙaramin yaro" dry shima yay ya ce "wane yaron Mother? Kullum ke kike maida Imam ƙarami,shiyasa baya ɓoye taɓararsa a gaban kowa" Granny tace "Yau na ga abin da ya dameni ni Faɗimatu,to banda Allah ya baka ɗa mai hankali da nutsuwa da tarin hankali uwa uba ilimi banda haka Imam ɗin guda nawa yake? Duudu bai huce 23 zuwa 25years ba fa" ganin sunata surutu yasa Imam yin gyaran murya ya ce "we getting late Abba" Barrister ya ce "Sorry my son da sauran time ai" yana faɗin hakan ya tura Wheelchair a hankali suka nufi Mosque ɗin dake wajan gidan Barrister Hamdan Balarabe,Granny na ganin fitarsu tai Murmushi jin daɗi a hankali kuma tai hamma tare dayin wata jijjiga sai gashi ta rikiɗe ta koma AIRAH. Bayan Sheikhnyaja ɗarorowan mutane sallah ya tsaya yana azkar,har wajan 7 bakwai na safe yana cikin masallacin,sai da ya kammala sannan ya kalli babban abokinsa kuma Amininsa Arjun wanda ya shigo masallacin yanzu "bacci na keji Arjun" miƙewa Arjun yay domin yasan indai Sheikh bai Wannan baccin daga bakwai zuwa sha ɗaya na safe ba to bazai bar kowa ya huta ba, karɓar Kur'anin hannunsa yay ya ajjiye inda ake ajjiye littafan matsallatan,cikin nutsuwa Arjun ya fara tura Wheelchair ɗin suna tafe Arjun na masa Shira Aliyah sabuwar budurwar da yay a nan garin, Murmushi kawai Sheikh yay yace "Allah yasa albarka" tsaki Arjun yay yace "Buddy a condition ɗinka yaci ace ka ajjiye matar da zata kula dakai,wacce babu hijabi tsakanin ku zata iya yi maka komai ba tare da jin wani nauyi ba, Granny kullum shekarunta ƙara jaa yake,wata rana ba zata iya kula da kai ba,kai ka bathroom dawo dakai cikin bedroom, shiryaka,kana ganin hatta mai ita take shafa maka,kaga dole ba zata shafa maka a inda bai dace ace ta gani ba,amma idan matar kace komai zata iya yi maka ba tare da taji nauyinka ba" kamar Imam ba zai magana ba sai kuma ya ce "kai ma ka fara gajiya da taimakon da kake min ne Buddy?" Girgiza kai Arjun yay ya ce "No! At all,kawai da ina ganin abinda yake dai-dai ne, Ni abinda nake maka gaba ɗaya nawa yake? Tsakani na dakai na kaika gidan redio kana gama program ɗinka na zo na ɗauke ka, sai zuwa shopping ko saloon wani lokacin ma baka bari akai ka,sai kuma zuwa Aikin hajji idan lokaci yayi ko Umara" lumshe idanunsa Sheikh yay kafin ya sauke numfashi ya ce "to menene da matanne? Ni bana da interested akan any women wlh,koda ina dashi wa kake ganin zata zauna dani?? Bana da fellings akan wasu mata wallahi gaba ɗaya shirmammu ne,basa da tausayi?" "Au haba??" Cewar Arjun domin ba ƙaramin haushi Sheikh ya bashi ba, Sheikh na sakin Murmushi domin yana son ya ga Arjun na gaya masa gsky shi kuma ya nuna baya ganewa gaba ɗaya, Arjun ya ce "Buddy ko dai baka da lafiya ne?? A Wannan zamanin da muke ciki ai kamar da sha'awa ake haifar mutum wallahi,kai sheda ne kana ganin mata kala-kala,dan ƙarya kake kace baka taɓa ganin macen da kaji kana sha'awarta ba,indai kaga Manhoon ɗinka bata mutsa to wlh baka da lafiya" tsaki Sheikh yay ya ce "zamani ya lalace tunda Arjun yasan daɗin mata" waro ido Arjun yay yace "kai Allah ya sauwaƙe dai,ina tare da babban Malam Alaramma kuma Sheikh Imam Hamdan Balarabe kake tunanin zan san mace indai ba aure nayi ba,kawai dai nasan ina buƙatar mace kusa dani,domin kullum da ciwon ciki nake kwana wani lokacin sai nayi taɓa Arjun ɗina nake jin daɗi" suna gaf da shiga Babban parlour'n daya raba manyan sides ɗin Sheikh yace "meye Arjun ɗina kuma?" Kai tsaye Arjun ya ce "mtwsss! Hajiya ta nake magana be ma'ana Manhoon" taɓe baki Sheikh yay yace "Iskanci kawai,ka daina ba kyau is better kai aure idan shi ne salama a gareka" Arjun ya ce "Soon ma kowa ma baka ƴarta ka aura" Sheikh bai ƙara magana ba,kallo guda yaywa Mami wacce take shirin fita bank dake aikin banki take, Murmushi tayi ta ce "Wlcm my dear" Arjun ya ce "Mrng Mami" wajansu ta ƙarasa tace "Yaya kake Arjun fatan kana kula min da my dear" Murmushi Arjun yay yace "Mami ɗan naki ai ɗan rigima ne" bata ƙara kallon Arjun ba ta kalli Sheikh tare da durƙosawa dai-dai fuskarsa ta shafa sajensa tace "Me kuma Mother taiwa son ɗinta ba ko gaisuwa?" Idanunsa a rufe ya ce "Sabahul khairai" Murmushi tai masa ta ce "how're you and how are feeling now?" Ya ce "Allahamdulillah!" Kallon Arjun tayi ta ce "kada ka barshi yay bacci yanzu sai yayi breakfast" Arjun ya ce "In sha Allah Mami" idanunta akan Sheikh tai masa peak a forehead ɗinsa kana tai ƙasa da bakinta ta ɗura saman nasa ta sucking lips ɗinsa na ƙasa saurin runtsa idanunsa yay,tana gamawa tai waje tana faɗin "bye sweetie" da idanu Arjun ya bita harta fice daga parlour'n..... 20/10/2021, 20:39 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _This book is for sale it's #500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616, ga mutan NIGER sai suyi mgn a wannan number 84506476_ 🆓P EPISODE7️⃣-8️⃣ Mami na barin parlourn Arjun ya sauke numfashi, tare da tura Wheelchair suka nufi cikin parlourn. Granny ce kwance saman bed tayi ɗai-ɗai sai bacci take abinta hankali kwance, da sauri Arjun ya juya ya nufi inda Sheikh yake yana shan coffee a parlour, with much shock Arjun yace "Buddy i don't understand what's going on?" A hankali Sheikh ya zame bakinsa daga kan glass cup ɗin ya ajjiye saman center table ɗin dake gabansa kafin yace "Meke nan?", Arjun yace "na je flat ɗinka na ga Granny ciki tana mopping, har muka gaisa yanzu kuma kace na ɗauko maka zuma a fridge ɗin Granny nai sallama bata amsa, hakan yasa na shiga cikin bedroom nayi expected wahala take, abun mamaki sai na sameta saman gado tana bacci da alama ko sallah asuba ba tayi ba", ya kai maganar yana kallo reaction ɗin Sheikh, sai bai ga komai ba sai ma murmushin da ya ga yanayi "Ohh!! Ni ka maida wawa ko?" da blue eye balls ɗinsa ya kalli Arjun yace "Oh! come on dear me zance maka" Arjun yace "More explanation about two of them" ware ido Sheikh yay yace "Laa adaari" cikin fusata Arjun yace "what the you mean by that?,bayan kana gidan kuma Granny ita take maka komai" taɓe baki Sheikh yay idanunsa a kan cenema yana kallon labarai a Aljazeera yace "La takaffafuu" kai tsaye Arjun yace "wallahi sai ka faɗa min", a ɗan fusace Sheikh ya kalli Arjun domin ya fara kai shi Ƙarshe bai son mita, da kuma nanata magana, calming yay yace "dole ne nasan komai? Ko zaka saka nai bincike akan abinda bana da iko dashi ne? Wallahi Arjun ka kiyayi kanka ka cigaba da shiga sabgar da babu ruwanka, ni nan ƙarya nai maka or what???" SHI ma Arjun yace "Ashe ba zakai hankali ba Imam? Baka tunanin lafiyar ka, ko ka manta situation ɗin da muke ciki, kullum kai ne zaman gida da tsaron Soldiers saboda gudun abinda zai cuce ka da kuma wanda zai sanya ai maka wani abun, amma kake ganin laifi na, wlh if i find out the truth you'll regret my dear" yana faɗin hakan ya nufi flat ɗin Granny da ido kawai Sheikh ya bisa harya ɓace wa ganinsa, Arjun na tafiya ya ci karo da wata farar mage mai kyau gwanin sha'awa ɗauke kansa yay daga kallon magen yaci gaba da tafiya, wayarsa ce ta fara ringing hakan yasa ya tsaya da tafiya kana yay answering call ɗin, yana tsaye magen ta huce da sauri ta nufi flat ɗin Granny, lokacin Granny ta farka tana ta sallami tana faɗin "A'a da mutanan gidan nan Arna za ai, babu tsoran Allah a ransu ace nai ta bacci kamar matacciya babu wanda ya kula da sabgata, kamar dai mara gata? To Allah dai yaga zuciyata ba ina sane naƙi sallar safe ba makara nayi wallahi tallahi, daman ita wacce ba'a gama sanin a wanne ɓangare take ba tuni na sallama ta, shi ma Barista dake gantalalle ne sai ya rabu dani ko na mutu ko nai rai duk uwar ubansu ɗaya, kai Allah gani gareka ni Faɗimatu da miji da mata duk babu na gari gwamma shi ƙarya yake rabtawa, ita kuma kuɗin jama'a take kwashewa tun da dai naji a banki take aiki, kai amma dai anyi gantalallun mutane wlh" tana faɗin hakan tai cikin bathroom, "ni dai wallahi cikina kamar anyi min sata, babu komai sai hanji wannan da shayarwa ne ma sai naji labari", tana shiga bathroom farar magen na shigowa cikin bedroom ɗin Granny, da ido magen tabi Granny da shi, kafin a hankali magen tai girgiza sai gashi ta koma siffar Granny tatasss babu abinda ya siffanta ta, Arjun ne ya shigo yana faɗin "Mrng Granny" kyaɓe Granny tayi tace "bana son gulma da fi'ili meye kuma Munin Ranjun? Kana gani ba'a mai dani komai a gidan nan ba,ai wlh Imamu da babu ni daya shiga uku, bashi da kowa da komai sai ni,Allah gatansan ni ce gatansa bawan Allah kenan", murmushi Arjun yay yace "haka ne fa Granny, kamar yanzu kika tashi ko makara kikai ne??" Wani kallo Granny tayi masa sai kuma tace "Yaushe ka arnantar dani Ranjun? Ka dai dinga jin tsoron Allah wallahj, babu ruwana sharrin da kai min ma ya ishe ka, yoo sharri mana da hankali na da komai shekara wajan 85 ai ba wasa kawai sai na zauna na makara a sallah, ai ni nan lokacin walaha nake jira kawai", jinjina kai kawai yay yace "bari na shige sai anjima na zo kai Buddy gidan Redio", "to to Allah ya kaimu ka gaida Sadiya" yace "za ta ji" yana faɗin hakan ya fice daga cikin bedroom ɗin, da ido ta bisa yana fita ta rikiɗe ta zama magen kamar yadda ta shigo parlon. Dawowa parlon Arjun yayi ya samu Sheikh yana shan ƴa ƴan inibi masu sanyi yace "am going Buddy sai zuwa anjima" plate ɗin hannunsa ya ajjiye yace "ok mai dani falt ɗina" ba musu Arjun ya kama Wheelchair ɗin suka nufi flat ɗin Sheikh, wanda yafi ko wanne flat kyau da kuma tsaruwa a cikin gidan, idan kaga abubuwan da suke flat ɗin Sheikh saika ɗauka shi ɗin wani lafiyayye ne, har cikin bedroom ɗinsa ya shigar dashi komai tsaf Granny da gyara amma a yadda suke tunani, da taimakon Arjun Sheikh ya kwanta saman makeken gadon sa, har Arjun ya juya sai kuma ya dawo,da ɗan sauri yasa hannu ya zarewa Sheikh jallabiyar jikinsa sannan ya cire masa singlet ɗin,fresh white skin ɗinsa ya bayyana ga santala-santalan ƙafafuwansa da cinyoyinsa da suka bayyana duk a waje, Arjun na gamawa yace "bye" idanunsa Sheikh a rufe yace "Jazakallah bilkhair" yana fita waje yana faɗin "it's my pleasure" Shiru Sheikh Imam yayi domin duk sonsa da bacci a lokacin kasawa yay, sai a yanzu mafarkin da yay ya shiga dawowa cikin brain ɗinsa, idan ya fahimta wacce ta kai shi bathroom da asuba ba Granny bace, domin ya daɗa fahimtar wani abu ɗazu,hakan magen data zo kusa dashi ba asalin magensa bace Wannan AIRAH ce, kenan mafarkin da yayi gsky ne yake ganin abun a mafarki ko yaya? Maganar Airah ce dawo masa cikin ransa inda take faɗin "Am pregnant with your unborn child Sheikh" ta yaya? Yaushe yayi tarayya da ita da har zata samu cikinsa, yasan cewa koda wasa babu wata halitta ko a jinsin Aljanu da ta taɓa ganin Manhood ɗinsa, Lumshe idanunsa yayi yana jin yadda kansa ke masa ciwo ga wani nauyi da yay masa, ji yay gidan yay masa girma dama yace Arjun ya tafi dashi gidansu, ko dai waya zai sanya Abbansa ya sai masa? Idan ya riƙe waya yayi me da ita, babu abokai family kuma iya Abba da Mami da Granny Fareeq Buhaiyya ya sani sai kuma Arjun daya zame masa komai, mirginawa yayi tare kifa cikinsa ya rungume pillow, iska ya ji tana kaɗa gashin kansa can kuma ya ji an dafa fresh back skin ɗinsa, bai Motsa ba saboda yayi tunanin Granny ce domin ya san Mami sai 6 zata dawo Abba kuma sai dare, Murmushi Airah tayi saboda farincikin yau zata kasance da mijinta kuma abin alfahari gareta, zama tayi bakin bed ɗin dai-dai kansa, bai tai kuskuren magana ba sai kansa data kama a hankali ta ɗaura saman cinyarta, ajjiyar zuciya ya sauke yana ɓata fuska yace "Granny!!" Yatsun hannunta ta tura a cikin sumar kansa ta shiga shafa masa sumar tana ɗan wargatsa ta, sosai Sheikh ya ji daɗi saboda daman kan ciwo yake masa, ƙara matsawa yayi jikinta ko zai samu yay baccin gadon da bai samu ya ɗauke sa ba, kasa yin shiru Airah tayi tace "why kake tsoran faɗawa Arjun kana da mata" da sauri ya ɗaga kansa zuwa fuskarta kasa ɗauke kansa yay saboda wata ƙyakkyawar halitta daya gani, zai iya cewa bai taɓa ganin mace me kyau da kuma tsarin halitta irin ta ba, ba fara bace ba baƙa bace za'a iya bata Chocolate tana da dugun gashi wanda ta ɗaura masa siririn veil, duk inda kake neman mace first class Airah ta kai sai yake ganinta kamar ba mutum ba, bakinsa yana rawa "who are you?" Kansa ta mayar saman cinyarta tace "why are you worried Rayuwata?" ji yayi zuciyarta ta buga da ƙarfi amma sam bai nuna a fili ba yace "Uhm" hannunta ta cire a cikin sumarsa tace "So daga juya zuwa yau harka manta dani ko?" Girgiza mata kai yayi yace "No! Kawai am trying to remember you" kallonsa Airah tayi tace "Lemme help you to, Am Airah your wife,Nasan abin zai zo maka kamar a mafarki but is not a dream is reality , tabbas na ɗauke ka da hannuna har zuwa dajin Sambisa an ɗaura mana aure Tijama da Tuɓe da kuma necklaces ɗin daka bani sune shaida" shiru yay mata ya shiga murza zoben hanunsa wanda tun ɗazo baya gajiya da kallonsa can kuma yace "what again now?" Tace "na kasa jurewa tun bayan na dawo dakai gida da Asuba,sai ya zamana na kasa bacci, hakan yasa nazo gare ka a suffar Granny bayan na sanya Granny bacci mai nauyi, sannan duk abinda kuka faɗa kai da Arjun ina jin ku, hakan yasa na zama mage domin bana son ya fahimci wani abu kamar yadda kai ma baka so, ina zuwa falt ɗin Granny na samu ta shiga bathroom sai na koma siffar ta da Arjun yazo ban sha wata wahala ba" shiru tayi sai kuma tace "Amma mai yasa kace?" Yunƙurawa yayi, ya miƙe zaune yana ɗan yamutsa, ƙafarsa ta kalla da sauri tasa hannayenta ta gyara masa ƙafafuwansa, fuskarta ya kalla yace "Tun Asuba nasan ba Granny bace, duk wanda yasan aljani farin sani ya ganki yasan ke ɗin ba mutum bace, na ƙara tabbatar da haka ne ta cikin mirror'n dake maƙala a cikin bathroom ɗina, kuma Granny bata iya English ba" jinjina kai tayi tace "Ko mugwaye Aljanu ai basu isa su ɓoye maka ba, bare ni da nake shirin taimaka maka" hannunta ya zame daga nasa kana ya koma ya kwanta can ya ƙara cewa "i don't have any feelings about women, balle aljana tayaya kike tunanin zan iya rayuwa dake matsayin mata a gare ni? Ta yaya kike tunanin zan baki kulawar daya dace ko wanne namiji ya bawa matarsa? I can't bana son kowa kamar yadda babu mai sona" kamar zatai kuka Airah tace "stop saying that Rayuwata,i promise u, I'll make you happy, ka bani 1week idan har a lokacin kaji baka sona nai baka al'ƙawarin zan rabu dakai", hanunsa yasa yaja sajensa yace "sure?" Kai tsaye tace "Yeah" zamewa yayi ya kwanta duk yadda yasu yay baccin daya saba kasawa yayi, har 11 tayi lokacin tashinsa a bacci kallon Airah yayi wacce har yanzu tana zauna tana shafa masa sumar kansa yace "zanyi Sallah" miƙewa tayi tare da jawo Wheelchair tana son ta kaisa da kanta amma bata son tai abinda zai firgita da ita, bayan yay alwala yay Sallah ya koma ya kwanta kallonsa tayi tace "Breakfast fa?" Girgiza kai yay yace "No i want to sleep" Yana faɗin hakan yana jan duvet ya rufe jikinsa, hawa bed ɗin tayi tace "i want to sleep with you" bai kulata ba yaja idanunsa ya lumshe yana jin yadda ta ja duvet ɗin ta shiga ta yadda ta ware hannayensa daya rungome a ƙirjinsa kana ta shige jikinsa tana Murmushin jin daɗi sosai take farin cikin kasancewa da shi, tsakani da Allah take son Imam bada wata manufa ba, rungomesa tayi sosai ta shiga shafa kansa tana masa waƙa mai daɗi a haka har bacci ya ɗauke sa wanda ya daɗe bai mai daɗinsa ba, ganin yay bacci yasa Airah miƙewa ta cire kayanta kana ta koma wajan Sheikh da yake kwance ta rungume sa sosai tare kissing bakinsa....... 20/10/2021, 20:40 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _Ina ganin masu cewa ko yaya zaman Sheikh Imam hamdan Balarabe da Aljarsa Airah zai kasance??? To kada ko damu you'll be surprised Habibaties kawai a hanzarta payment free pages dai babu yawa😍👌🏾share And share and share_ Pay #500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger sai su nemi wannan number 84506476 🆓P EPISODE9️⃣-1️⃣0️⃣ Sheikh Imam bacci yake mai cike da nutsuwa da kwanciyar hankali, da zarar yay mutsi zai ji an ƙara shigewa jikinsa ga wani ɗumi dake ratsa jikinsa seriously zai ce ya daɗe bai yi bacci mai daɗi irinsa ba, bai tashi daga bacci ba sai da yaji muryar Granny saman kansa tana faɗin "Yau na ga abin da yafi ƙarfina ni Faɗimatu, wanne gantalallan bacci ne wannan Fisabilillahi? anayi ana nishi kamar bai zazzaɓin masharshara?" Buɗe idanunsa yay da ƙyar yana ɗan dafe kansa da yaji yana masa ciwo kallo ɗaya yay wa Granny yay saurin ɗauke kansa tare da juyawa side ɗinsa,ganin babu kowa a gefensa yasa ya kalli Granny ya ce "Granny where is she?" Keɓe baki tayi ta ce "meye kuma Shaa? Kaga Imamu babu ruwana da wannan Ingilishin naka maza tashi ka shirya Ranjun yace min yana hanya,yanzu ya kira a sailolar dake palo" shiru yay kawai yana sauke tagwayen ajiyar zuciya ji yay ransa duk babu daɗi saboda da rashin ganinta da bai ba, yana da tabbacin tafiya tayi bayan ta sashi ya yi bacci, Granny ta taimakamasa yay wanka tare da ɗaura alwala, yana gaban dressing mirror Granny na shafawa fatara versiline "haka kurum baka san darajar fata ba kace a shafa maka wani losha,meye ma wani losha fisabilillahi" Shidai bai ce komai ba domin a karo na farko kenan yaji bai ji daɗin yadda Granny ke shafa masa mai ba,ji yay gaba ɗaya yana da bambanci da wanda Airah ta shafa masa da Asuba, comp ta ɗauka ta taje masa sumar kansa ta kwanta sosai har saman goshinsa,kana tai hanyar wardrobe tana faɗin "Uhm kai kaji wani zance Imamu" idanunsu akan madubi yana kallon yadda jikinsa ya ƙara buɗewa sosai kamar wanda yake yin risilin, jin yay shiru bai magana ba yasa Granny ta ce "Idan bakai miskilanci ba ai sai Allah ya ka maka wlh, domin Ubanka Did...," Sai kuma tai shiru ta cikin madubin ya kalleta ya ce "Speak up Granny,meye Did...?" Girgiza kai tayi tace "A'a babu ruwana da gulma haramun ne wlh,daman wani zance nake som tsegun ta maka da naji Barista ya faɗa" gaba ɗaya attention ɗinsa ya bata yana faɗin "Uhm" wani tissue ɗin yadi mai masifar kyau ta ɗauko masa mai manyan zane gashi shara shara domin komai na jikinsa ana iya gani,wajansa ta ƙarasa tare da sunkuyawa ta bashi boxer ya saka sbd daga shi sai pad,tun yana yaro haka ya tasu kakarsa ke masa komai, shiyasa ba yajin akwai abinda zai iya ɓoye mata a jikinsa sai dai tsaraicinsa, farar singlet ta bashi ya zura a jikinsa bakinsa ɗauke da addu'ar sanya kaya,sai kuma wandon yadin shima yasa rigar mai ɗinkin Jamper ta bashi ya saka, sannan ta miƙa masa babbar rigar kayan, girgiza mata kai yay ya ce "No! Granny ban so" Juyawa babbar rigar tayi tace "Wallahi baka isa ba,ba zan wahalar banza ba ka ga yadda kai kyau kamar dai ɗan firazdat ko ɗan sarki? Kai ma sha Allah" Murmushi yay mata yana ɗaga hanunsa saboda parfume ɗin da take saka masa, lokacin ɗaya ƙamshin Arabian Ohud ya cika cikin bedroom ɗin nasa, harami ta ɗauko masa ya ce "bari sai Friday bani jar darata" wata hula ta bashi mai kyau tana ɗauke da gashi,a saman sumar kansa ya ɗura kana ya sanya farin bluetooth da farin glass ɗinsa yay wani kyau he look like king of Saudi Arabia, baƙin covert shoe ta saka masa a farar ƙafarsa, sai da ta gama masa komai sannan ya kalleta ya ce "Jazakillah bilkhair Granny" zama tayi ta ce "Ni dai amana zan gaya maka wlh,idan kaci kai da Allah babu ruwana da shiga hurumin Ubangiji" lumshe idanunsa yay ya ce "Uhm feel free what's is the matter?" Tagumi tai sai kuma ta ce "Barista ya kitsa abu babu shawara fa, wai Gwamna ya nemi a baka auran ƴarsa,kullum tana jin zantukan ƙaryar da kuke a redio,sai ta kamu da sonka hankalinta duk ya tashi hakan yasa Gwamna ya ce ta gaya masa tace ai Sheikh Imam hamdan take so, to ashe ma ya san Ubanka Barista shine fa ya ce da Barista yana neman sa a govmat house,to Ubanka dai ya yarda ni da waccan ɓarauniyar kuma bamu amince ba" Kallonta kawai Sheikh yake sam bai mamaki ba domin Arjun ya faɗa masa cewa ana yawan kiransa ace Imam ake nema kuma macace,wani lokacin messages harta email ɗin Arjun,to babu mamaki yarinyar ce, Granny tace "banda gantalewa ta yaran zamani yaushe mace take cewa tana son Namiji? To wlh zamanin mu sai an kaika ɗakin mijin kake sanin wa kake aura,kaga ina da shekara 9 akai min aure hatta nono wannan a ɗakin Mijin na samesa" wani ƙawataccen Murmushi Sheikh yay yace "Am hungry" Granny tace "Me kace?" Idanunsa ya mayar bakin ƙofa ya ce "yanzu 12 past 23 yunwa fa" miƙewa tayi bayan ta gama gyara wajan kana ta tura Wheelchair ɗin zuwa tsakiyar haɗaɗɗan parlour'n gidan, har gaban dinning ta ajjiyesa kana ta shiga zuba masa abin breakfast ɗin, Arish ne da meat shawarma sai tea da yaji kayan ƙamshi da na'a na'a tai tashin ƙamshi yake, bisimillah yay yasa yatsun hanunsa guda huɗu ya fara cin meat shawarma bayan ya gama cin abincinsa Granny ta kawo karamin bowl ya wanke hanunsa ya goge da tissue kana yay hamada. Bayan Sheikh yana mutane sallar zuhur Arjun ya koma cikin gidan su ya ɗauko ɗaya daga cikin sabbin motocin Sheik wata ƙarama mai ash color sabuwa dal, Arjun na mazaunin driver Sheikh na ɗaya side ɗin idanunsa akan littafin Zajid zaujain, sosai Arjun ke gudu da motar sbd yasan Sheikh bai son tafiya a hankali "Buddy wallahi aure nake sonyi na gaji a matse nake,Am tried pls daga nan mu huce gida ka tayani roƙan Ummi ta barni nai auran tunda ina so" lumshe idanunsa Sheikh yay lokacin ɗaya yaji tunanin Airah ya faɗo masa, Where is she? Shine tambayar da yaywa kansa, one day kenan yaya kenan idan ya kasance da ita na adadin sati guda kamar yadda ta ce? A haka suka shiga cikin gidan redio'n Arjun yay parking kana ya fita daga inda yake zaune,a back side ya ɗauko wheelchair ɗin Sheikh kana ya taimaka masa ya zauna, har cikin reception ɗin gidan redio'n suka shiga,kowa ya ga Sheikh sai ya tsuguna ya gaishesa,hatta ga wanda suka girmi Sheikh babu a abin da ya siya masa mutunci face Iliminsa sa hqrinsa haɗi da taimako da kyautatawa talakawa, da sauri ya fara gabatar da program ɗinsa na LAFIYAR MU, Mutane da yawa sun buƙaci ya buɗe masu wata ƙungiya ko kuma gruop wanda zai iya yi masu wani bayanin idan yana free,wasu kuma sukace ya basu number wayarsa, Shi dai murmushi yay kawai domin yasan a redio kawai suke jin zazzaƙar muryarsa,amma shi gaba ɗaya bai san yadda zai iya using da wata waya ba,ya wake dashi? Bashi da wanda zai nemasa a waya,a haka suka gama program ɗin shida Arjun kana suka ɗauki hanyar gidansu Arjun. Ummi ta ce "Haba Imam i don't think is nacessary,idan Arjun yay aure bazai samu lokacin kula da komai naka ba" wani abu mai ɗaci Sheikh ya haɗiye idanunsa akan Ummi mahaifiyar Arjun yace "No! Ummi i trust Arjun zai iya komai nawa,yin aurensa bashi ke nuna zai ƙi kula dani ba" Murmushi kawai Ummi tayi tace "Imam ka manta da shirman Arjun fa,and think yourself mana,kalli condition ɗinka,babu wanda ya dace da yay Aure sama dakai,yana da kyau ace kafin wani yay maka wannan mgnar kayiwa kanka" idanunsa ya lumshe kafin ya sauke numfashi yace "Try to understand us Ummi, the way mutum yace zai aure to let him do" Arjun yace "please Ummi i lover so much i need her i want marry her wlh ina sonta" harara Ummi ta watsa masa tace "kai dai Arjun anyi mara kunya,akan na hanaka shi ne ka ɗauko bawan Allah yana cikin hutawarsa,wlh baka da kunya ka kiyaye ni Arjun" Murmushi kawai Sheikh keyi,shi ina ma yana da uwar da zata hanashi abu aida yaji daɗi,he need mother new mother yana son yaji ɗumin uwa mahaifiya,yana son yaji uwa ta rungomesa inda zai samu yayta kukan saman ƙafaɗarta,baya da wannan ƴan cin bashi da uwar daza taji damuwarsa bare harta bashi shawara mai kyau,babu uwar da zata kwantar dashi zaman ƙafaɗarta tasa yay kuka mai yawa ko yaji sauƙin zuciyarsa, tagwayen ajjiyar zuciya ya sauke kallon Ummi yay inda take faɗin "Shikenan yaje yay aure Allah ya sanya albarka,Amma Imam kai ka nemu matar Aure" zoben hanunsa ya kalla ya ɗan murza kaɗan yace "bana da interested Ummi" ganin yanayinsa ya sauya yasa ta rabu dashi, farin ciki sosai Arjun ya shiga rungome Ummi yay yana faɗin "thank you so much Ummi" murmushi tai tana shafa kansa tace "kuje daining ga lunch na jera maku" girgiza kai Sheikh yay idanunsa a ƙasa yace "Am full Ummi" Ummi ta ce "daman koda yaushe you're full" dariya Arjun yay ya ce "Rabu dashi Ummi,ko a gida yake baya cin abinci iyanzu sai dakakkiyar fura" miƙewa Ummi tayi tace "ta kwana gidan sauƙi ai,ina da fura wlh" kwaɓe fuska Sheikh yay bai ce komai ba "Ummi ko kin dama bai zai sha ba indai ba Granny tayi ba" yana faɗin hakan ya nufi hanyar fita daga parlour'n yana tura Sheikh dake zaune saman kujera "To ai shikenan Allah ya baka lafiya Imam Ubangiji ya kawo ƙarshen wahalar" da Ameen ya amsa har suka fice daga parlour'n Ummi na zabga masa addu'a. Da daddare Barrister ne zaune shida Mami da Granny wacce take yankawa Sheikh apple a plate, Sheikh na zaune yana farcing mahaifin nasa yana kallon yadda suke cin abincin su hankali kwance,idanunsa ya mayar kan Granny wacce tace "Fisabilillahi ace ƴar ƴan itatuwa sune abinci? Gsky wannan ba halin zama ba ne Babana" Mami ce ta ajiye spoon ɗin hannunta ta ce "Granny ai wannan sun fi sanya jiki lafiya" "au haba? To Allah ya taimaka nikam wannan sakalcin ba dani ba" shiru sukai mata harta gama surutun da jan plate ɗin Sheikh yay tare da sanya fork ya caki apple,amma ya kasa kaiwa cikin bakinsa sai juya Apple ɗin yake, Barrister ne yace "Yadai son?" Kallon Mahaifin nasa yay ba tare da yay magana ba ya ɗauke kansa a hankali kuma ya tura Apple ɗin cikin bakinsa,duk son sa da Apple yau jiyaye batai masa daɗi ba, he's lost his appetite gefe guda kuma tunanin Airah ne fal a zuciyarsa tun safe rabonsa da ita he's worried, bisa dole ya ci gaba da shan Apple ɗin dan bai son kwana da yunwa yasha rabi ya ture plate ɗin gefe yana hamdala, kallonsa kawai Mami take can kuma ta ce "Sorry my soul kana fushi dani ko? Kasan yanayin aikin nawa" bai ce komai ba ya danna wani abu a gefen Wheelchair ɗin a hankali ta fara tafiya sai da yaje parlour sannan ya tsaya, BBC news yakai ya fara kallon labarai, gaba ɗaya suma suka dawo parlour'n Barrister yace "My son" ko kallansa Sheikh bai ba idanunsa akan cenema ya ce "Uhm" Barrister ya ce "be ready you getting marry soon" ba Sheikh har Mami sai da ta kalli Barrister kasa daurewa tayi ta ce "what wrong with you Barrister? Yaya kake magana ɗaya tun safe? Wanne irin Aure wai ana zaune lfya gaba ɗaya Imam nawa yake ne?" Bai kulata ba yace "kana ji na ai?" Jinjina kai Sheikh yay still idanunsa na kan cenema, Barrister ya ce "Governor da kansa yake neman alfarma gareni akan haɗin Auren daya keso muyi,ƴarsa Nana tana sonka sosai" nan ma shiru Sheikh yay sai murza zoben hanunsa yake yana jin zuciyarsa nayi masa zafi, miƙewa Barrister yay ya ce "ka shirya Nidai na amince" kai tsaye Sheikh ya ce "Ni kuma ban so" da sauri Barrister ya ce "meye baka so ɗin?" Kwallon Granny Imam yay ya ce "Granny bacci zanyi" miƙewa tayi tana faɗin "to Babana yau Ubanka ina ga ƙaryarsa zai gwada a kanka" tana faɗin haka ta tura Wheelchair ɗin zuwa flat ɗin Sheikh,wani Murmushi Mami tayi ta ce "Ina raye Imam yay aure?.over my died body" tana faɗin hakan itama ta nufi flat ɗinta,a tsaye ta samu Barrister ya gama shirin bacci hucesa tayi ta nufi bathroom tai wanka ta shirya cikin kayan bacci, a parlour ta samu Barrister ta ce "Gud night" da mmki ya kalleta ya ce "what the you mean by that? Kisan ke nake jira wai meke damunki ne? Rabuna dake yau wajan sati biyu kenan ko an gaya maki dutse ne ni?" Kallonsa tayi tace "kayi hqr Barrister ban jin zan ƙara baka jikina babu abinda kake tsinana min ko 30mins da ƙyar kakeyi a jikina no test gaba ɗaya salam kake i can't waist my time akan wanann" tana faɗin hakan ta nufi bedroom ɗin ta, Juyi kawai Imam yake ya kasa runtsawa shi kasansa bai san dalili ba a karo na farko ya kejin wani a zababban fellings a tare da shi mararsa har wani kumbura tayi tana ɗagawa, jin bai taɓa jin abu makamancin haka ba yasa ya tashi zaune tare da dafe kansa ya shiga fesar da numfashi,ji yay an dafa shi da sauri ya ɗaga kansa idanunsa ne ya sauka akan Airah wacce take tsaye tana masa Murmushi, fuska ya kwaɓe mata ganin haka yasa ta zaune kusa dashi tana faɗin "Am sorry my life na barka da kewata ko?" Kasa mata magana yay sai hanunsa daya sanya ya jawota jikinsa ya rungome ƙamƙam kamar wani zai kwance masa ita... 20/10/2021, 20:41 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _It's #500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger suyi mgn a nan 84506476_ 🆓P EPISODE1️⃣1️⃣-1️⃣2️⃣ Idanunsa ne suka kaɗa tare da yin jaa,bai san ya ya ake samun farin ciki a wajan mace ba, haka nan bai san yaya ake jin son wata ɗiya mace a duniya ba, hasali ma duk matanan duniya kallon mugwaye yake masu,ba tare daya san dalilin da yake masu wannan kallo ba. Sai gashi yanzu a karan farko yaji yana son kasan cewa da mace,yana son jin ɗumin jikin mace wanda ya rabonsa dashi tun sanda mahaifiyarsa ta kawosa duniya, bai san daɗin zama da uwa ba, Uban ma bai san daɗin zama dashi ba, Granny ya sani sai kuma Arjun ɗinsa wanda ya zame masa komai. Yau shi Imam yake jin kewa mace na damunsa kewar ma ta ALJANA,daga jiya zuwa yau yaji komai ya sauya masa lokaci kaɗan ne wanda zai zo ya huce wanda zaiji bai yi tunaninta,ko kuma bai murza zoben dake maƙale a hanunsa ba. Kallonsa Airah tayi ta ce "Bakai bacci ba?" Kai ya ɗaga mata kamar ƙaramin yaro kafin kuma ta ce "Ka san me?" Nan ma ya girgiza mata kasance yay alamar a'a, ta ce "I want to sleep with you, ina son yin bacci a shoulder ka, i want make you happy zan baka farin cikin duk daka rasa a rayuwarka" idanunsa a lumshe yake ya ce "sure?" Da sauri ta ce "Of cos my life" zareta yay a jikinsa yana fesar da numfashi ya ce "Tell me something Air..aah!!" Yadda yay pronouncing sunanta a ɗan rarrabe yasa ta lumshe idanunta, ta ce "Ina jinka" kallonta yay ido cikin ido da sauri ta ɗauke nata idanun domin bata iya jure kallonsa, ajjiyar zuciya ya sauke kafin yace "Da gaske Uwa na barin ɗan ta riƙo a hannun ex-husband ɗinta? What i mean duk Uwar da take da tausayi da kuma jin ƙai,bai dace ace dan sun samu Matsala da mijinta ta ce zata ajjiye ɗan da gaba ɗaya ko 1week bai cika da haihu ba,hakan shi zai sanya mijinta ya dawo da ita ko kuma ya fahimci cewa abinda yake ba dai-dai ba ne? She leave me ta rabu dani tun ina cikin zanin goyo ban san daɗin nonon uwa ba,ban san daɗin jikin Uwa ba,ban san farin cikin da ake samu idan ana tare da Uwa ba,mene laifi na? Me yasa zata ɗauki laifin mahaifina ta ɗura min, bata san cewa ɗan ta na buƙatar ta bane? Bata san cewa am nothing without her ba? Ba ta san cewa ta haifi nakashasshe wanda bashi da gata bashi da mai kula da shi ba, i want to my Mother ina buƙatar ta, i missed her a lot". Airah tsayawa tai tana kallonsa kafin ta ce "No at all, baka san dalilin rabuwa kai da tayi ba,baka san irin zafin da taji a lokacin da zata rabu da kai ba, sannan baka san damuwar da take shiga idan ta tuna ka ba,zata iya yiwuwa duk abinda ta aikata she's not her fault, koda tana sani babu wanda baya kuskure a rayuwarsa, nasan one day she most come back to her son definitely, so you don't have to worry about that My life". Ajiyar zuciya ya shiga saukewa yana rungome pillow hannunsa a ƙirjinsa da gaske yana buƙatar kulawar Uwa,yana son Uwa ta rungome sa,yana son yaji mahaiyarsa na lallashinsa, yana son ya faɗa mata yadda yay missed nata da kuma abinda yake damunsa, amma bashi da wannan freedom ɗin dole ya samawa kansa salama ya amshi rayuwa a yadda tazo masa. Zare pillow dake ƙirjinsa tayi tace "Why are you hurting your self like this? Come on! Hug your wife not pillow,hug me you'll feel better". A karo na biyu kenan a iya kacin rayuwarsa daya rungome mace, koda yake bazai iya sanya Airah matsayin mutum ba,amma yadda take tsaye gabansa babu wanda zai ce mata ta haɗa jinsi da Aljanu bare kuma kayi tunanin Aljanar ce.. Rungome ta yay sosai yana sakin ajjiyar zuciya, a yadda ya rungome ta kaɗai zai tabbatar bai taɓa riƙe hannun mace ba bare ya rungome ta,ya nayin komai a ɗan tsorace amma tsoransa iya kan mace ya tsaya da dukkan alamu mata sunyi masa tabo a zuciya. Kallonsa tayi taga ya rufe idanunsa kamar mai bacci, jajayen laɓɓansa ta shafa tana jin wani difference feelings na ratsa jikinta tana son Sheikh fiye da sosai,domin a kansa ta karya al'adar su ta shiga jikin Bil'adam bare har su tare a inda suke,amma yaya zatai? Sonsa ya ja mata komai ba iya sonsa ba tana son kasancewa da shi ne domin bashi kariya tana son lokacin da Tijama ta ɗauka ya cika a ranar Sheikh zai san komai game dashi. Gashin dake ƙwance saman ƙirjinsa ta shafa tace "Ina son zame maka Uwa, ina son zame maka Aboki,ƙawa Sannan ina ka amince dani matsayin matarka, ba zan taɓa cutarka ba, zan baka dukkan farin cikin daka rasa ka yarda dani Please" Ƙara lumshe idanunsa yay still kuma yana riƙe da ita a jikinsa yace "Your request accepted my fairy". Miƙewa tayi ta kashe all light ɗin dake ɗakin ta window'n baya ta leƙa taga yadda garin yay duhu ga wata iska mai daɗi da take kaɗawa,sai walƙiya da ake da alama a koda yaushe ruwa na iya sauka "Uhm what are you looking for?" Kai tsaye tace "the weather,garin yay daɗi musamman sky abin sha'awa" bai ƙara magana ba yaja ba kinsa ya rufe,wajansa ta ƙarasu tace "ko kana son fita ne?" Ware manyan idanunsa yay yace "kai No!!" Kusa dashi ta kwanta tare da ɗura kanta saman damtsen hanunsa idanunta akan lips ɗinsa tace "Sheikh!" kasa amsa ta yay sbd gudun da zuciyarsa take masa bai taɓa very close da mace irin yau ba,hakan yasa ya kejinsa duk wani iri. Yatsarta tasa ta fara zagaye lips ɗinsa da ita da sauri ya riƙe hannunta sbd tsigar jikinsa data tashi muryarsa na sharking ya ce "Stop" da sauri ita ma ta ce "No i can't, don't Stop me Sheikh I'll do it just for you, i promise to make you happy,so leave hakanne kaɗai zai sanya ka manta da damuwar zuciyarka, bedside am your wife banga abin damuwa ba" tana faɗin hakan tai saurin haɗe bakinsu waje guda bata bashi damar faɗin komai ba. Lubb yay a jikinta yana fesar da numfashi jikinsa har ɗan rawa yake tunda uwarsa ta haifesa bai taɓa shiga yanayin daya shiga ba, sai yanzu yasan dalilin Arjun na son yin aure tabbas dole ya kiɗi me yaƙi kwantar da hankali sa,shima kansa da bai san daɗin mace ba mai san yaya ake zama da mace aji daɗin ta ba,amma yau yana jin daɗin zama da Aljanarsa kawai a fuska ne baya nuna mata,amma indai ya ganta ko ta raɓu dashi yana jin wani sanyi na ratsa jikinsa, ya yarda Airah zata iya bashi farin cikin daya rasa kuma zata iya zama gurbin mahaifiyarsa,Amma tayaya zai iya zama da Aljana?. Lumshe idanunsa yana ƙara tura fuskarsa tsakanin wuyanta, slowly Airah take sarrafa bakinsa dake cikin nata, bata san lokacin da yay bacci ba sai saukar numfashinsa da taji a saman wuyanta. Murmushi jin daɗi tayi domin daman abin da take buƙata kenan ta ga yay bacci,tasan bazai taɓa barinta tayi abin da take buƙata ba, a hankali ta zare boxer dake jikinsa kafin ƙifta ido ta dawo kamanin ta na Aljana Airah, ƙafarsa ta miƙar sosai ta shiga shafa masa wani abu a saman laps ɗinsa zuwa tafin ƙafarsa, tana jin yadda yake sauke ajjiyar zuciya yana ƙara miƙar da ƙafarsa har ƙara yake,duk da cikin bacci yake amma abun da Airah take shafa masa mai kama da magani yana jin daɗinsa sosai har cikin ransa,tana gamawa ta ƙarayin girgiza ta koma kamarta ta mutane. Idanunta da suke cike da soyayyarsa ta zuba masa tana jin kamar tabi abinda zuciyarta take gaya mata,amma bata son sanya shi cikin damuwa amma yadda zuciyarta take cike da ƙaunarsa yasa ta kejin ba zata iya hqr da abinda take ji game dashi ba, ba tare data bari zuciyarta ta sake gaya mata wani abu ba tayi saurin sanya hannunta ta kama Sheikh ɗinsa take kwance yana bacci like yadda Imam ke yin bacci ta sanya cikin bakinta,wata zabura Sheikh Imam yay lokaci ɗaya kuma gargasar jikinsa ta mimmiƙe ba tare daya buɗe ido ba ya saki wata ƴar ƙaramar ƙara yana faɗin "Auchhhhhi" ganin yana ƙoƙarin tashi zaune tai saurin kaɗa masa hannunta da sauri ya koma ya kwanta saboda iskar data ƙara ratsa sa yana jin wani sabon yanayi game dashi. Washe gari da safe ya kama Monday, Sheikh na zaune saman duguwar sofa daga shi sai 3gauther idanunsa na saman plasma yana kallon Sunna t.v, wa'azin da yay na Ramadan a shekarar data huce suke ƙara maimai tashi sbd Sheikh ya faɗakar da al'umma a wannan lokacin mutane da yawa sai da sukai kuka,hatta shi da yake wa'azin sai da idanunsa suka fidda hawaye. Granny ce ta ƙarasu wajansa ta zauna tana faɗin "Imamu kai ka amince da auren ƴar gidan Gumma na ɗin?Nidai nasan babu abinda uban ƴar zai nunawa Barrister na kuɗi,sai dai kawai ya nuna masa ɗaukaka,Ni mana son a dinga yi maka kallon mai son zuciya da kuma ƙwaɗayi, mutane da yawa suna kawo yaransu ka aura amma kaƙi, hatta sarkin kano ya baka Auren ƴarsa kaƙi,sai kuma rana tsaka aji an ɗaura maka Aure da ƴar gidan Gumna? A'a wlh Wannan abun kunyar ba dani ba,bazan zama sallamammiya kamar Ubanka ba" duk maganar da take yana jinta amma yay mata shiru sbd bai san abin da zai ce mata ba, shi kansa yasan tsofa ya gama cin Granny ɗin sa, ƙoƙari kawai take wajan ganin ta bashi farin ciki. "Meye haka? Mutum ana magana amma yana jinka a iska ko dai kaima ka zama gantalalle bana da labari? a'a wlh wannan ba halin zama cikin Mutane ba ne" ware fararan idanunsa yay yace "Uhm, Granny I'm not interested Aure soyayya friendship duk bana da ra'ayi, i only want my mother babu wanda kemin mgnarta i missed her a lot,idan farin ciki kuke son nayi kuyi mgnar Ammi na where is she?". Barrister dake shigowa cikin parlour'n sbd yau Friday daga shi har Mami basu daɗewa wajan aiki yace "Uhm Your Mother? You'll find everything soon or later" yana faɗin hakan ya shige flat ɗinsa, da kallo Sheikh ya bisa wai wannan shine mahaifinsa? Baya damuwa dashi damuwarsa ɗaya shine aikinsa,tayaya kuma yake tunanin wata rana zaizo da buƙata a matsayinsa na mahaifinsa ya biya masa? Ajiyar zuciya Sheikh ya sauke yana ƙara nutsewa cikin kujerar, miƙewa Granny tayi tace "A'a kadai kai bacci a nan,kamar dai wani mara gata?" Girgiza mata kai yay yace "No! Granny am not sleeping ina jiran Arjun lokacin Mosque ya kusa". "Ohh to Allah ya kasuwa lafiya Ranjun yaron kirki wlh". Misalin 12:30 Mami ta shigo cikin parlour'n hannunta riƙe da hand bag ɗinta ɗayan kuma wayarta ce, jingina jikinta tayi da jikin door maganganun da sukai da ƙawarta suna dawo mata cikin kunanta,gaba ɗaya kanta ya ɗaure tayaya zata iya Wannan abun,gwamma kawai ta samu wata hanyar ba wannan ba, harɗe hannayen ta tayi tana ƙara ware idanunta saman fuskarsa zuwa jajayen laɓɓansa da suka ƙarayin jaa sunyi fresh sai Shinny suke, numfashi ta sauke tana taune bakinta, for the frist time taji ta amince da shawarar Aminiyar ta ta.. A gefen ƙafafuwansa ta zauna tana ƙara ƙarewa babban yatsarsa kallo, imagine tayi idan har babban yatsarsa zai kasance haka,to yaya abinda take tunani girmansa zai kasance? Hannunta ta miƙa kamar zata gyara masa ƙafafuwansa sai kuma ta nufi wajan waist ɗinsa,da sauri ya riƙe hannunta idanunta ya sauke cikin nasa tana wani lumshewa idanunta, cikin ƙarfin hali yace "Mamii" zame hannunta tayi a nasa tana sakar masa Murmushi tare da shafa beard ɗinsa tace "My dear how are you?" Ba tare daya kalleta ba ya ce "Allahamdulillah!" Gira ta ɗaga masa tace "Why kake kallo na haka? Am your mother kona sauya maka kama ne" Girgiza mata kai yay tace "how long kake kai ɗaya a nan? Ya kamata yau muje shopping dakai my dear bana son ganinka cikin damuwa" da sauri ya ce "Oh really?" "Of cos my dear" tashi zaune yay yana naɗe ƙafafuwan sa wanda bai taɓa tanƙwashe su ba sai yau da mmki Mami tace "Oh Wow! Sweet at lest wani ci gaba ya samu yau" ɗan taune bakinsa yay da sauri Mami tace "stop hurting your self dear why kake punishing lips ɗinsa haka?" Ta ƙarasa faɗin maganar tana ɗura hannunta saman leɓansa tare da murzawa, bakinta takai ta shiga hura masa masa isa sbd kula da jan da wajan yay "Kana abu like a baby? Ni zaka hukunta tunda ni na tafi na barka kai ɗaya nasa haushin hakan yasa kake yiwa kanta hukunci,am so sorry I never ever leave you again sorry sweet". Kasa magana yay sbd ganin yadda Mami take basa hqr with all her heart, shi kansa yasan yana jin haushinta sbd barinsa da suke a gida,hawaye ne ya kawo idanunsa muryarsa na rawa yace "Why? Me yasa Mami?". Kansa ta shafa tace "sorry bari na duba maka bakin ba kaji ciwo ba ko?" Girgiza kai yay yace "No! at all kawai i wanted to you to come back" yana faɗin hakan ya shige jikinta yana sauke ajjiyar zuciya idanunsa cike da hawaye, tamkar uwa mahaifiya haka ya ɗauki step mother ɗin tasa, daɗi ne ya cika zuciyar Mami, sannu a hankali zata sanya Sheikh ya sake da ita, yadda duk abinda tai masa bazai zargi wani abu a tare da ita ba, ƙara matse sa tayi a jikinta tana jin yadda jikinsa ya fara rawa. Misalin 1:30 Sheikh ya gama shiryawa cikin bayan kayansa mai babbar riga da Jamper sai wando,ya sanya black half covert shoe mai kyau, shaddarsa fara ƙal sai ɗaukan ido takeyi ya sanya hirami a sama ya ɗura wata half ɗin hula hula mai kyau,sai tashin ƙamshi yake,but kana kallonsa kasan babu farin ciki saman fuskarsa he look worried a sanyaye yake bin Granny da duk abinda tace,babu abin da yaja hakan sai rashin ganin Aljanarsa da bai ba, rabonsa da ita tunda ya kwanta bacci cikin dare,yana dubawa ya ga babu ita. Har cikin mota Granny ta rakasa zai zabga masa addu'a take, hannunta ya kama tare da sumbata yace "Jazakillah bilkhair Granny Allah ya bani abinda zan saka maki dashi" hararar wasa ta cilla masa tace "ɗan nema" Arjun kam cewa yay "just pray Buddy" Sheikh yace "In sha Allah" Granny ta kalli Arjun ta ce "Ranjun ka tafi dashi a hankali" dry Arjun yay yace "Granny ai ya ce shi zai driving da kansa fa" Harara Sheikh ya watsa masa tare dayi masa wani kallo wanda yake nuni da "Munafiki" bai jira me Granny za ta ce ba yayi saurin rufe motar bakinsa ɗauke da addu'a yaywa motar reverse kana ya jata da gudu suka nufi Mosque sbd shine liman ɗin da zai ja dubban jama'a sallar Juma'a, suna tafiya Sheikh ya lumshe idanunsa yana jin me Arjun yake cewa da "Uhm" kawai yake binsa "I love her so much Buddy ina son Aliyah sosai, can't stop loving her wlh Please ka rakani wajanta yau nai missed nata sosai" Sheikh a cikin ransa ya ce "i also missed my Airah too i missed my wife" da sauri Arjun ya kalli Sheikh ya ce "What! Your wife? Uhm who is Airah?... 20/10/2021, 20:42 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _it's #500 via 0116886423_ _Sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger suyi mgn ta nan 84506476_ 🆓 P EPISODE1️⃣3️⃣-1️⃣4️⃣ "Haaa ur wife?" Yaushe ka samu mata ba na da labari? Wait when ka fara soyayya ma?" Haɗe fuska Sheikh yay ba tare kuma daya tanka Arjun da yake masa magana ba, cikin damuwa Arjun ya ce "I kon Allah! Ashe nine sakarai da nake faɗa maka sirri na, banda haka tayaya zaka samu matar aure bana da labari" Murmushi kawai Sheikh yake yana jin yadda Arjun ke ruwan masifa kamar zai ari baki, ajjiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Ohh Shut up my friend" da sauri Arjun ya ce "Why should i?" Taɓe baki Sheikh yay yana karya kwanar da zai kai shi Mosque ɗin,kamar ba zai magana sai kuma yaja gemunsa ya ce "You don't have any reason to talk about it, And wacce macan kake tunanin zata zauna da disabled like me Arjun, wallahi isn't necessary bedside ba na da wani feelings akan mace,ko dai kuje Allah ya taimaka" Sosai Arjun yay dry kafin ya ce "Eh babu komai zamu bauta wa mace,za kace na gaya maka wata rana sai kayi kuka dalilin mace, Uhm soyayya akwai daɗi akwai wahala, kuma duk cikakken Namiji mai jini a jika da lafiya zai so kasancewa da mace, nasan wata rana da kanka zaka gaya min yadda kake son wacce tai nasarar samunka matsayin miji" da sauri Sheikh ya ce "God forbid! Ni na so mace har na aureta?" Murmushi Arjun yay yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa saboda soyayyar Aliyah ya ce "Of cos, ɗan sunna ai mazai ƙi sunna ba, rashin san auren ne yasa Granny ta ce taje tashinka da asuba taji kana ta nishi tare gurnani?" Shiru Sheikh yay bai ƙara kulasa ba har suka ƙarasa harabar masallacin, wasu manyan securities ne suka zagaye motar Sheikh Imam hamdan kafin Arjun ya fito da sauri tare da ɗaukan Wheelchair ɗin Sheikh, bayan Sheikh ya zauna Arjun ya fara tura Wheelchair har zuwa cikin masallacin securities na biye dasu. Bayan an idar da sallar Sheikh ya juya tare da fuskantar Mutanan da ke cikin masallacin,cikin nutsuwa ya gyara zaman babbar rigar sa tare gyara zaman farin glass ɗinsa, Muryarsa ya saita kaɗan Sannan ya fara Bisimillah cikin nutsuwa da kamala ya fara huɗu bar Juma'a,gaba ɗaya ƴan jarida suka saita speaker nasu aka fara ɗaukar recording gidan t.v kuma suka fara ɗaukan vedio'n direct wanda ya kasance live Bayan ya kammala Mutane suka shiga yi masa tambayoyi nan ya fara ba su amsa cike da ƙwarewa, Wane ne ya kalli Sheikh ka na ya matsa kusa dashi da alama dai shima babban Malami ne, cikin ƙasa da Murya yace "Sheikh wata ta turo tambaya ta cikin lambobin da muke badawa, na ga kuma tambayar na da muhimmanci ya kamata a amsa mata duk da cewa lokaci ya tafi" shiru yay Sheikh yay kamar mai nazartar wani abu can kuma ya numfasa ya ce "Faɗi tambayar, Allah ya bani ikon faɗin dai-dai" mutumin ya ce "Ameen" wayarsa ya fara dubawa can kuma ya ɗaga kai ya kalli jama'ar dake cikin masallacin, bakinsa ya saita a speaker ya fara faɗin; _Assalamu alaikum,ina yiwa Sheikh Imam hamdan fatan alkairi Allah ya tsare sa ya kuma karesa daga sharrin mutum da aljan, Tambayata a nan shine (Shin zai iya yiyuwa a samu alaƙa tsakanin mutum da Aljan? Shin zai yiwu Ɗan Adam ya yi alaƙa da Aljanu? Idan har zai yiwu yaya hukuncin yin hakan yake? Tambaya daga baiwar Allah zuwa bawan Allah ka sani ina tsananin sonka da ƙaunar ka,dan Allah ka amsamin tambayoyi na)_. Fesar da numfashi yay nan take yaji wata zufa ta shiga karyo masa, lumshe idanunsa yay tunanin His Fairy kawai yake a wannan lokacin, Wannan amsar mai sauƙi ce garesa sbd ga babban misali a garesa,duk da kasancewar sa babban Malami amma hakan bai hana Aljana shiga jikinsa harta aurensa ba, fesar da iska yay kana ya gyara zamansa sosai cikin nutsuwa tare ƙarfin guiwa da kuzari ya manna idanunsa a saitin camera cikin zazzaƙar muryarsa ya ce. "Amsa a Dunkule Kur'ani mai girma ya tabbatar da samuwar aljani kuma ga wasu daga cikin bayanai kan aljani. 1- Aljani halittace da aka yi shi da wuta sa ɓanin mutum shi da kasa aka halicce shi. 2- Yana da ilimi da idraki da tantance Karya daga gaskiya, yana iya yin magana kuma yana kafa dalili. 3- An wajabta masa ayyuka (na ibada da dss) da kuma nauyaye nauyaye. 4- Wasu daga cikin su muminai ne salihai wasu kuma kafirai. 5- Za a tashe su ranar alƙiyama kuma za a yi musu hisabi. 6-Suna iya keta sararin samaniya su sato ji amma daga baya an hana su. 7- Suna kulla alaka da wasu daga cikin mutane kuma suna yin amfani da masaniyar da suke da ita na wasu Ɓoyayyaun sirrika su halakar da mutane. 8-A cikin su akwai wa Danda suke da karfin da iko na gaske kamar yadda ake samu a cikin mutane. Numfashi Sheikh ya fesar tare da sanya hannunsa yaja dugun sajensa wanda yake kwance luff,ya daɗe bai mgna mai yawan ta yau ba,kula da hakan wani securities ya tsiyaya masa ruwa mai sanyi a glass cup ya miƙa masa, amsa yay tare faɗin "Barakallahu fikaaa" bayan yasha ruwan ya sauke ajjiyar zuciya,cikin nutsuwa yaci gaba da faɗin. 9-Suna da ikon yin wasu ayyuka da mutane ke bukatuwa zuwa gare su. 10-Su aka fara halitta a doron kasa kafin a halicci mutane. 11-A cikin Kissar Annabi sulaiman (as) lokacin da Ifritu daga cikin aljanu ya yi da’awar cewa zai iya kawo gadon BilKisu wajen Annabi Sulaiman (as) kafin ya tashi daga mazauninsa,Annabi Sulaiman (as) bai Karyata shi ba duk da cewa wannan maganar ba ta zo a cikin Kur'ani ba cewa ya kawo gadon ba, Daga cikin abin da aka amabata a cikin a yoyin da muka kawo zamu fahimci cewa aljanni ba halitta ce irin ta tatsuniya da labarai ba, shi halitta ne samamme a haKiKa, mai jiki wanda za a iya yin alaƙa da shi, kuma wasu daga cikin mutane sun yi alaƙa da shi, duk da cewa a zamanin da an fadi wasu nau’o’i na alaka daban daban tsakanin mutane da aljani, amma mu zamu takaitu da irin wacce muka samu a cikin Kur'ani da hadisi, da ita zamu isu don wannan kawai muka yarda da shi. A nan za mu yi nuni zuwa ga yanayin alaƙar da muka samu a cikin Kur'ani da ruwayoyi da kuma maganganun da aka nakalto daga wasu makiya: A.Neman tsarin Allah daga aljanai; ya zo a Kur'ani mai girma cewa: {haƙiƙa wasu mazaje daga mutane sun kasance suna neman tsari wajen wasu mazaje daga aljanu sai suka kara jefa su cikin bala’i da “wahala”}[13]. Al’adar larabawa ta kasance duk lokacin da suka shiga daji mai ban tsoro (misali mai duhuwa) suna neman tsari daga aljanun wannan kwazazzabon, kuma musulunci bai hana yin haka ba kuma ya yi umarni da a nemi tsari daga shaiɗanun mutane da na aljan[14]. B.Tasarrufi da aljani; yin tasarrufi da aljani da yin amfani da su wajen yin hidima duk da cewa abu ne mai yiyuwa, sai dai malamai sun yi bahasi kan cewa shi ya halatta ko kuwa? Gwargwadon abin da suka yarda da shi, shi ne lalle ne kar wannan aikin ya zama ta hanyar da shari’a ta haramta, ko kuma ya zama sanadin cutuwar aljanu,Kuma lalle ne ya zama aikin da suke yi ba wanda shari’a ta haramta ba ne. kuma lalle yin aikin da shari’a ba ta yarda da shi ba ya haramta dai-dai ne da wasida ko babu wasida.[15] An tambayi Marja’I Mai girma Sayyid Ali (as) Khamna’i kan hukuncin zuwa wajen mutanen da ke tasarrufi da rauhanai da aljanu wajen yi wa mutane magani tare da la’akari da cewa bisa yaƙini su aikin alkhairi kawai suke yi, sai ya bada amsa da cewa: wannan aikin ba shi da mushkila a kan kansa da sharaɗin cewa ya zama yana yin aiki ta hanyar da shari’a ta halarta. Duba da Wannan misalan da aka samar a cikin Alkur'ani da kuma hadisai zamu iya cewa mutum na iya mu'amala da Aljanu,domin wasu Aljanun har Auren mutum suke, za'a ga mutum baya sha'awar aure ko kuma bashi da sha'awa gaba ɗaya,abinda nake nufi da sha'awa shine; ko yaga wani shashe na jikin mace ba zai taɓa ji mazantakarsa ta mutsa ba, bare har yay tunanin kasancewa da mace, zamu kawo misalan yadda ake gane Aljani ya auri Mutum ko kuma yana jikin mutum a haɗu bar mu ta gaba. Ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke mai ƙarfin gaske,kafin yaja baya kaɗan shi kaɗai ya shiga sauke tattausan Murmushi ya nayi yana jan ƙwantaccen bear ɗinsa, cikin ƙasa da Muryar kamar mai raɗa idanunsa akan camera yace "Baiwar Allah fatan kinji amsar tambayar ki kuma kin gamsu? Allah ya kyauta ya kuma tsare mu daga sharin kafiran Aljanu". Gaba ɗaya cikin Masjeed ɗin suka amsa da Ameen. Suna cikin mota Sheikh yana driving cikin ƙwarewa ba tare daya saurar abinda Arjun yake magana akai ba, ganin Sheikh ya ɗauki hanyar zuwa gida yasa Arjun marai-raice fuska yace "Haba Buddy bana ce zaka rakani zance wajan Aliyah ba?" Ɓata fuska Sheikh yay yace "Nifa ba za'a kai ni wajan da za'a dinga zabga ƙarya ba" dry Arjun yay yace "Au ƙarya ake a zancen? Malam just wait and see za kaji yadda ake faɗar kalamar soyayya" shiru Imam yay Arjun ya ce "fara kai ni gida na ɗauko mata gift ɗinta" kallonsa Sheikh yay kamar zai magana sai kawai ya karya gwana, a compound ɗin gidansu Arjun yay parking Arjun ya ce "ba zaka shiga wajan Ummi ba?" Girgiza kai Sheikh yay yace "kace ina gaisheta,nasan za ta ce sai na ci abinci ni kuma am full" kafin Arjun yay magana Ummi dake bayansa ta ce "Daman always you're full,kawai kace furar Granny za kasha" Murmushi kawai yay mata kafin ya lumshe idanunsa yace "Evening Ummi" "how are you?" Ya ce "Allahamdulillah!" Daga nan ta shige cikin gidan, Arjun yabi bayanta yana riƙe da hannunta, da kallon sha'awa Sheikh ya biso yana ji inama mahaifiyarsa ce Ummi. Bayan sun isa gidan su Aliyah Arjun yay mata waya daga can ɓangaren ta sauke ajjiyar zuciya kafin ta ce "fatan mijina ya sauka lfy?" Murmushi yay mata har cikin zuciyarsa yake jin ƙaunar Aliyah yana mutuwar sonta kamar ransa "Surprised?" Ware ido tayi ta ce "What a good news?" Cikin jin daɗi ya ce "Tare muke da Buddy" saurin faɗin "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" tayi sbd yadda taji gabanta ya faɗi,cikin ƙarfin hali tace "Sure?" Da sauri ya ce "I mean my words Matata" miƙewa tayi tsaye tana gyara zaman rigar jikinta wacce ta amshi jikinta sosai, Aliyah fara ce sosai tana da ɗan tsayi ba sosai Mahaifinta shine senator na lokacal government ɗin su, ita kaɗai ce wajansa,sun haɗu da Arjun taje shopping shi kuma yaje siyowa Sheikh sabbin jalabiyoyi, a nan sukai exchange na number "come in" daga can ɓangaren Arjun ya ce "No muna sauri lokacin shan furar Buddy yayi" ok kawai tace masa kana ta kashe wayar, parfume tasa masu ƙamshi ta gyara zaman veil ɗinta, but ƙasan zuciyarta taoroy da far gaba ne, tun daga nesa Arjun yake kallonta yana jin kamar yaje ya rungome ta sbd yadda ya kejin ƙaunarta a ransa, fuskarta ɗauke da Murmushi tai masu sallama, Amsawa Arjun yay yace "Ma sha Allah tawan kinyi kyau fiye da ko yaushe" cikin ƙasa da Murya tace "Fatan kana lfy kamar yadda zuciyata ta sanar dani?" Kallon Sheikh yay dake cikin mota ya lafe jikin kujera idanunsa a rufe sai ƙirjinsa dake ɗagawa da sauri yace "Wow ashe haka zuciyarki take da faɗin gsky?" Shira suka taɓa kafin yace "Ga Buddy ko gaisa zamu huce" kallon cikin motar tayi a zuciyarta tana faɗin Tubarkallah ma sha Allah barakallahu ahhasanal kaliƙin Ubangiji yay halitta a nan, da sauri Aliyah ta ɗauke idanunta ta ce "kamar bacci yake" dry Arjun yay yace "haka yake fa, ƙilan zaman ya damesa" cikin motar ya leƙa tare da bubbuga murfin motar yace "Buddy! Buddy!" Ware firgitattun idanunsa yay "What again?" Arjun ya ce "Ruhina ke gaidaka" kallon bayan Arjun yay kallo guda yay mata yay saurin janye idanunsa tare murza zoben hanunsa ka ɗan yace "Ykk?" A fili tace "tab" Arjun ya kalleta ya ce "me" girgiza kai tayi tace "Ina lfy ya jiki?" Ware fararan idanunsa yay kafin yace "Lafiya" Wannan idan bai ji dakai da kuma miskilanci ba ai sai Allah ya tambaye sa da sauri Sheikh yace "me kika ce?" Rufe bakinta tayi tace "No ba dakai nake ba" a zuciyarsa yace "Ƴar ficika kawai" bayan sun gaisa Arjun ya bata tarkacan chocolate daya siyo mata, Sheikh yace ya gaji dole suka sauya waje Arjun yay driving nasu zuwa gida. Misalin 10:30 na dare Sheikh na zaune a parlour'n sa daga shi sai 3gauther fresh skin ɗinsa sai Shinny take ga yadda 6packs ɗinsa suka ƙara buɗewa ƙwantaccen gashin ƙirjinsa yana ta gyalli hanunsa riƙe da mug yana shan coffee, idanunsa ba kan cenema yana Kallon Tafsir a Sunna t.v, bayan an gama tafsir ɗin ya sauya channel zuwa zee world, samu yay ana film ɗin johda &Akbar bai taɓa tsayawa yayi kallo ba,amma ganin film ɗin na musulmai kuma na sarauta sai abun ya birgesa, lumshe idanunsa yay lokacin da yaga Akbar yay kissed ɗin Johda, cikin ransa yake faɗin ko meye abin daɗi a nan ohhhu? Yana nan zaune yana shan coffee kamar bai so amma gaba ɗaya tunaninsa yana kan Airah shi kaɗai yasan yadda yake a zabtuwa da rashinta a ɗan wannan lokacin da yay sabo da ita, tana ɗebe masa kewa fiye da tunanin mutum yana samu kwanciyar hankali da ita, at least ya samu wacce za tana rarrasbinsa zata rungomesa idan yay kewar Amininsa,tana ƙoƙarin bashi farin ciki shiyasa ya yarda da ita sosai ya bata dukkan yar darsa, ta riga ta samu gurbi a zuciyarsa baya jin akwai halin da zai shiga bai tuna da Aljanarsa ba, Aljana ta fi masa sauran mutane da yawa, Aljanarsa ta fi masa Amminsa ta fiye masa Abbansa, tayaya zai iya mantawa da ita, lumshe idanunsa yay yana jin ɗaci a ransa yaushe zai samu freedom ne kamar yadda kowa yake dashi? Yaushe zai zama cikakken Namiji mai lfy? Yaushe zaiji feelings akan mace kamar yadda Arjun yake gaya masa a kullum, cije lips ɗinsa yay tare da fesar da numfashi, hanunsa ya shiga miƙawa wajan table yana son ajjiye cup ɗin hannunsa cikin rashin Sa'a ƙafarsa ta zame daga jikin Wheelchair, ƙara ya ɗan saki saboda tsoratar da yayi kafin ya ƙarasa ƙasa Airah tayi saurin taresa ya faɗa jikinta..... 20/10/2021, 20:42 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _it's #500 via 0116886423 Sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger suyi mgn ta nan 84506476_ 🆓P EPISODE1️⃣5️⃣-1️⃣6️⃣ Murmushi Airah tayi tace "Meyasa kake punishing kanka?" banza yay mata shi a dole yayi fushi da ita why zata tafi ta barsa a lokacin daya saba da ita? Ganin yadda ya marai-raice fuska yasa ta shafi fuskarsa cikin lallashi tace "Am sorry ban ƙarawa ka ji" kai ya ɗaga mata kafin ya zame a hankali ya ɗaura kansa saman cinyarta tare da lumshe idanunsa wanda suka sauya launi, yana jin kansa cikin farin ciki a duk sanda ya kasance da ita, amma mai yasa baya jin feelings ɗin da Arjun ke faɗa masa? Ko dai da gaske bashi da lfy ne luff yayi a jikinta kamar ƙaramin yaro, duk da cewa yana da shekaru Amma Imam shagwaɓaɓɓe ne na bugawa a jarida, yana da haƙuri, juriya, da wahala kaga damuwarsa yana da ɗaga ƙafa akan laifukan da mutum zai masa, Amma idan haƙirinsa ya gaza sam bai iya fushi ba, kaifi ɗaya ne idan yace Yes! babu wanda ya isa ya sauya masa ra'ayin da zai sa shi faɗin No!, Kaifi ɗaya ne yana tsayawa akan Dukkan abinda ya keso baya nuna gazawar sa ko kaɗan, yana da taurin kai idan yace yana son abu baya taɓa haƙuri dashi sai ya same sa, shi kansa sometimes yana mamakin halinsa ya ci ace yadda yake Malami ba komai zai zama halinsa ba, amma idan ya duba yaga hali ba kai kake samawa kanka Allah ke yo mutum a haka, sai ya ji sauƙi a ransa."yau ka gaji da yawa ko?" Hannunta ya kama ya riƙe cikin nasa yana ɗan murzawa yace "Yeah! Na raka Arjun zance" kansa ta shafa tace "I knew, hope da sauƙi jikin naka" juya idanunsa yay yana kallonta yace "Wane yace bana da lafiya ?" "Au sai wani ya gayan bazan iya sani ba? Nasan cewa yau ɗin ba daɗinta ka ke ji ba kawai dauriya ce irinta ta jaruman maza kuma sadaukai", miƙewa yay zaune yace "tell me something, Arjun yace duk sanda ka kasance da mace kana jin feelings da sha'awarta, har yanayinka ya sauya Manhood ɗinka ta fara harbawa" shiru tai sai kuma tace "Of course ,hakan na nuna cewa Mutum nada cikakkiyar lafiya ai, ko a mata haka ne bawai iya maza ba" marai-raice fuska yayi yace "kenan bani da lafiya?" Itama tace "who tell you that?" Komawa yayi saman cinyarta ita kuma ta cigaba da massaging kansa yace "na fahimta ne, saboda jikina baya bani abubuwan nan idan na kasance da mace" gemunsa taja tace "au har mata kake kasancewa dasu?" Kai tsaye yace "You're the first person and last dana taɓa sani har na amince da ita" Airah ta kallesa tace "Kai cikakken mai lafiya ne fiye da sauran mazan da suke da lfy, you have a beautiful and big dick, kana da lafiya kai lafiyayye ne Rayuwata I don't know how to explain saboda SIRRIN MU ne wannan but wata rana zaka ce na faɗa maka" kamar zai mata kuka yace "i don't have any feelings a kanki" dariya tayi tace "it's complicated ka ji fellings akai ne" buɗe baki yay zai mgn tai saurin rufe masa baki tace "You need to rest now" miƙewa yayi zaune ita ma ta miƙe tsaye gyara masa bedroom ɗin tayi in few seconds bama minutes ba abinka da aikin aljanu, bayan ta gama ta haɗa masa warm water a cikin jakuzzie, ta taimaka masa tai wajan zuwa bathroom ɗin, Lokaci da ruwan zafin ya ratsa jikinsa lumshe idanunsa yay yana ƙara nutsewa cikin jakuzzie, yana ta zaune kamar bazai wankan ba sai kuma ya fara yanayi yana fesar da numfashi, bayan ya kammala ya haɗe cinyoyinsa sosai ta yadda babu mai ganin jikinsa kana ya ɗan fara buga gefen bango, babu jimawa ta shigo tare da miƙa masa towel kana ta buɗe Wheelchair ta taimaka masa ya zauna dariya tayi masa tace "Why are you hidding your naked body for me?" Banza yay mata tare da ɗaukan brush ya wanke bakinsa kana ya ɗaura alwala duk akan idanunta, daya ɗaga kai ya kalli mirror sai ya ɗauke kansa saboda ganin Airah da yake ta cikin mirror'n rabi Mutum rabi jikin maciji, abu ne mai wahala madubi ya ɓoye asalin halittar su ko yaya ne sai yayi showing. Shirin kwanciya yayi bayan ya gyara jikinsa ta shafa masa mai just like Granny use to do, gaba ɗaya jikinsa ƙamshi yake lungu da saƙo, Imam yana mutuwar son parfume ko shopping ya je abinda yake ɗauka kenan, sai glass, boxer ta bashi ya saka kana ya maida komai wajan sa, wasu fararan night wears ta ɗauko masa "No! am not interested bana sa kaya idan zanyi bacci, am okey a hakan" ya faɗa yana karanta addu'ar bacci yana gamawa ya shafa ta ko ina. Kwanciya yayi ya lumshe idanunsa ya shiga sauke ajjiyar zuciya jikinsa ta shige bai trying na hanata ba cos yana buƙatar ɗumin jikin mace na sawa ya ƙara samun nutsuwa, Murmushi Airah tayi saboda yadda ya shige jikinta a hakan ma wai baya jin komai game da mace duk sanda ya fara jin daɗin mace sai Allah a haka bacci ya ɗauke sa yana maƙale jikin Airah yana jin yadda take shafa lips ɗinsa..... Washe gari da safe Mami ce zaune da ƙawarta mai suna Fariha suna hira akan bank nasu, numfashi Mami ta sauke tace "Wlh ina cikin damuwa, i don't know how to explain , bana samun nutsuwa da mijina gaba ɗaya" Fariha tace "kamar ya kenan?" Mami tace "rabon dana kwanta da Barrister na manta, kamar yadda bana zama shima baya zama, daga Granny sai Sweet Imam, amma end of this month Su Fareeq da Bahaiyya zasu dawo holiday", tsaki Fariha tayi tace "ke fa baki da fahimta wallahi, bari ki ji yanzu kai ya buɗe idan zaki fuskanci mijinki ki gaya masa bakya gamsuwa da shi to, wallahi kina kallo zaki cuci kanki, ƙilan shi garesa zam yake jikinki amma ai ke baza kiso ki zauna haka ba tunda ba dutse ba ce ke, so go and meet your husband ya je Islamic chemist ya amshi magani ƙilan kuma infection ne yasa haka", wani wawan tsaki Mami ta ja tace "God forbid! Ni na je wajan Barrister nace masa ya nemi magani? Sorry Am classy woman I can't do that", "kenan haka zaki zauna? Ko dai baki da lafiya ne?" Ware ido tai tace "kul ki ƙara faɗa lafiya lau nake wallahi , kullum sai na gyara kaina da sabbin magunguna ina matse kaina yadda babu wanda zai raina ni, ke ni fa ko tsufa nai banga abinda zan sauya ba, domin gyara daɗi gare sa" jinjina kai Fariha tayi tace "ikon Allah kowa da abinda ya dame sa ni Abban Taufiq kullum cikin ƙorafi yake a kaina, ban san mene yasa ba amma kamar baya gamsuwa da ni" riƙe baki Mami tayi tace "Allah dai ya kyauta kema kina gyara, baki son gyara kanki, namiji kuma duk tsufansa da kika gani yasan daɗi, yanzu dai goben za ki zo ko yaya?" Miƙewa su kai a tare Fariha tace "By the grace of God" dry Mami tai tace "kizo akwai magana".... A zaune ta samu Sheikh shida Arjun suna hira ƙasa ƙasa da alama hirar cigaban da Company Sheikh yayi suke, shi dai Sheikh hankalinsa na ga zane da yake a jikin white paper Sheikh na son zane tun yana yaro ya iya zane, domin har zanan gida makaranta, masallatai yana fiddawa, yanzu tunda suka fara magana ya fara zane da pencil ga wasu different colors da yake using dasu "A week ɗin nan mun samu ƙaruwar kuɗi more than 5.1m nai mamaki sosai fa, amma ganin manager bana wasa ba ne yasan aikinsa yasa ban tsayawa wani bincike ba" shiru Sheikh yat domin idan ka tambayesa mai Arjun yake cewa shi kansa bai sani ba, kula da hakan yasa Arjun leƙa paper wata budurwa mai matukar kyau da tsari yake zanawa, ga gashi da ido farare tass, ga shape mai tsari, murmushi Arjun yayi yace "Wannan alama ce take nuna Buddy ya faɗa soyayya", manyan idanunsa ya ɗaga bayan ya kammala zana Airah babu abinda ya bambanta tsakanin Airah fairy da zanen, lumshe idanunsa yayi kana ya buɗe a kan, taune lips ɗinsa yayi kaɗan tare da tsotsa "you're very beautiful Airah,i never see a beautiful lady like you, you make me happy, wlh billahi am proud of you Aljanata i love You more than anything, your love and care mean a lot to me, I love you My Aljana" farin ciki ne ya cika zuciyar Arjun da sauri ya kama hannun Sheikh yace "Who is that Airah da kaketa magana a kanta time to time" haɗe fuska Sheikh yay yace "kamar ya? Wace wata Airah kuma?" Kallonka rainawa kanka hankali Arjun yay masa yace "kada ka mai dani wani sakarai mana, yanzu ka fara mgn kana Airah waye-waye kace wai wace ce Airah, idan ka fara son mace ni nafi kowa farin ciki saboda ko babu komai zaka samu farin cikin daka daɗe kana nema wajan mace" taɓe baki Sheikh yay yace "Duniya ta lalace tunda su Arjun aka fara wa'azi", "ohh da kai kaɗai ka iya wa'azi?" Idanun Sheikh a saman zanensa yace "A'a fa" fushi Arjun yayi yace "ok fine sai anjima" da sauri Sheikh ya riƙe hannun Arjun yace "Sit" zama yay yace "zagina zakai yanzu kuma?" Ware idanunsa yay yace "Laaa! Bana son ka matsa kanka wajan sanin abinda ba hurumin ka ba ne Buddy, kowa yana da private life ɗinsa, nasan ka cancanci kasan komai nawa amma bana da ikon faɗa maka SIRRIN MU but time will tell us everything" miƙewa tsaye Arjun yay kafin yay mgn Granny ta ƙarasu tana faɗin "Haka fa! ya gaya maka meke damunsa? To dai Ranjun abun kullum lalacewa yake kamar wanda iska ta aura, jiya fa ban faɗa maka ba naje tashinsa da asuba na samesa yana ihu da surutai, nidai babu ruwana idan ya jawa kansa masifa ina dalili ina mafari fisabilillahi?" Girgiza kai kawai Arjun yayi yace "something is fishy" yana faɗin hakan ya fice abunsa daga cikin gidan... Mami dake tsaye ta saki wani sound da sauri Granny ta juya tana faɗin "Mahammadur Rasulullah ashe kema gantalalliya ce? Wannan ɗaukan zunubi har ina fisabilillahi? Sai kace ana yaƙi kawai zaki faɗo kamar dai a sabon gari, daman kwana biyu duk a tsorace nake, gaskiya idan baki nemi yafiya ta ba sai Ubangiji ya kamaki babu ruwana wallahi, kawai dai sbd son jin zance sai ai tsaye akan mutane kamar wata ƴar dama??" Murmushi Mami tayi tare da ƙarasa shigowa parlourn ta zauna saman kujera idanunta na kan Sheikh tace "Afuwa Granny nai sallama ba ki ji ba kina ta faɗa" a fusace Granny tace "yaushe na zama sallamammiya da zanyi faɗa, da Imamu zanyi faɗa ko da Arjun? Yau naga lukutar masifa" Mami tace "kiyi haƙuri Granny", Granny tana keɓe baki tace "shiya kashe Jaki" zaro ido Sheikh yayi still idanunsa na kan zanen da yay "Yooo an loda masa kaya yau, gobe an loda masa babu ruwa bare abinci duk wahalar daya sha babu mai gani, ba dole haƙurinsa ya gaza ba dan Allah?" Mami tace "haka ne fa" miƙewa Granny tayi tace "bari na dama masa wannan furar ta gado yaro kamar wanda yasha nonon Fulani, towa kake da shi wanda zai kula da kai? , ai sai ni daya dana zame maka dole, wannan yana wajan gilla ƙarya, waccen na wajan sata" haka tai shige cikin flat ɗinta tana sababi, matsawa Mami tayi wajansa tana leƙa zanan fuskarta ta ɗan sauya tace "who is she?" Da mamaki yace "ban san ta ba" "kuma ka zauna har ka zana kamarta and you don't know her Bravo!" Baya yayi tare kwanciya saman Sofa yana jan ƙwantaccen beard ɗinsa, lumshe idanunta Mami tai tana jin wani Irin da sauri ta kalli derection ɗin Manhood ɗinsa, ƙara runtse ido tayi kafin ta fesar da wani huci mai zafin gaske, ganin ya lumshe idanunsa yasa ta shafi pech soft lips ɗinsa tace "Sweet me kake shafawa lips ɗinka?" Ba tare daya buɗe ido ba yace "Noting " ƙasa ɗauke hannunta ta shiga ƙoƙarin zura masa yatsarta a baki da sauri ya ware idanunsa mamakin yadda idanunta ya sauya lokaci ɗaya yay, hannunta ya riƙe yace "Mami" da sauri ta miƙe tsaye tare da shige flat ɗinta tana dafe bango, mamaki kenan meya samu mahaifiyar tasa kuma yau oho... Abu kamar wasa soyayya mai ƙarfin gaske ta shiga tsakanin Sheikh da Airah takai ta kawo koda rana sai ta zama siffar Arjun ta shigo gidan, Sheikh ya samu nutsuwa da farin ciki,komai sai yace Airah aka rasa wacece Airah, baya taɓa iya bacci idan bai ji sa a jikinta ba,komai nasa ya zama ita take masa, ɓangaren Airah kam sannu a hankali ciwonta ya fara tashi kullum cikin ciwo take bata iya bacci sbd zafin da zuciyarta ke mata, tun tana yarinya Ubangiji ya ɗura mata ciwon zuciya, ciwon ya ƙara zafi lokacin data fara son Sheikh, ko da wasa bata taɓa gaya masa ba domin wani lokacin haka za tazo wajansa very weak babu fara'a a fuskarta, hankalin Sheikh idan yayi dubu ya tashi baya samun nutsuwa sai ta sake ta dawo normal , cikin dare zata tashi tai ta kallon jikinsa wani lokacin tana jin kamar ta aiwatar da burinta a kansa amma dole ta jira kamar yadda Tijama tasha faɗa mata. MAIDUGURI/BARNO Garin Maiduguri dai ita ce babban birnin jihar Borno dake arewa maso gabacin Nijeriya. Maiduguri ita ce birnin da tafi kowane birni wajen girma da yawan jama'a a arewa maso gabas din Nijeriya. A'kalla birnin tana da jama'a fiye da miliyan daya. Birnin Maiduguri da sabon birni ne kuma an kafa ta ne a shekara ta alif da dari tara da bakwai (wato 1907). Maiduguri ta 'kunshi unguwar Yerwa (Yerwa yana nufin alheri a harshen kanuri) ta yamma da kuma tsohuwar Maiduguri da take ta bangaren gabas. Kowa yasan Barno gari ne na kanuri The Kanuri people (Kanouri, Kanowri, also Yerwa, Bare Bari and several subgroup names) are an African ethnic group living largely in the lands of the former Kanem and Borno Empires in Niger, Nigeria, Sudan, Libya and Cameroon.. KANURI ako ina suna girmama al'adunsu basu yadda da wulaƙanci ba sam-sam, kowa ya sansu da tsayawa akan ra'ayinsu musamman akan abinda suke so, bari mu leƙa Unguwar *Shehuri North area*. Wata yarinya ce wacce a ƙalla ba zata haura 17yrs ba amma girman jikinta shi zai sanya ka ɗauka wata babbar macace, tana sanye da wata black ɗin Lafaya wuyanta yasha murjani ga wata saƙar azurfa data sanya a ƙafarta ta sosai ta sanya bangles wanda a yaran kanuri ana Kiransa da (Mukarram) hannunta yasha red henna na salatif kasancewar ƙafar da hannun farare yasa suka ƙara fito da zanan lallan, duk yadda ta yane a bayar hakan bai hana sumar kanta wacce take kwance luff bayyana ba, cikin nutsuwa take tafiya ga faffaɗan waist ɗinta dake juya ta cikin lafayar shafaffan cikinta shine ya ƙara taimakawa wajan bayyanar tsayayyun brest ɗin da kuma manyan bombom ɗinta, she's sexy girl ko a kallonta sai ta firgita mutum sam magana baya daga cikin tsarin halittar ta, kunanta maƙale da airpies wanda ya zame mata jiki ba komai take saurara ba sai amso shin tambayar da tayiwa Sheik Imam hamdan, lumshe idanunta tayi a hankali ta rasa mai yasa Baba Baa'na baya son ajjiye masu t.v a gida, da ko babu komai sau ɗaya dai ta kalli wannan shararran malamin bayan baiwar ilimin da Ubangiji ya ba shi, kuma taga baiwar kyansa bata taɓa ganinsa ba sai dai ta ji muryarsa tai messages sau nawa babu reply amma yau ta samu an bata amsar tambayarta. Horn taji daga bayanta hakan yasa ta ɗan tsaya kaɗan tana son ta ga waye domin ta kusa kaiwa gida, wani magidancin mutumi ta gani zaune cikin mota wanda a ƙalla zai haifeta sau biyu sbd yawan shekarunsa, juyawa tayi taci gaba da tafiya a hankali shima fitowa daga cikin motar tare da biyo bayanta, jerawa yayi da ita da sauri ta tsaya tana ɗan haɗe rai ganin ya tsaya yasa taci gaba da tafiya shima yabi bayanta cikin zafin nama tace "Are you mad? And who are you?" Calmly Mutumin yayi yana ƙara bin surar jikinta da kallo Tabbas ya samu auranta zai mure da ƙuruciyarta bai damu da shakarunta ba indai za'a ɗaura masa aure da ita tabbas zai ji daɗi wannan shi ake kira da uban wasu yayi wuff da wata murmushi yay yace "Am Barrister Hamdan Balarabe...... An kusa kammala free pages Habibaties😍🤕 Kuyi share ɗinsa please fisabilillahi whatsapp ɗina yay min left daga cikin grps ɗin da nake. 20/10/2021, 20:43 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ _it's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger suyi mgn ta nan 84506476_ 🆓P EPISODE 1️⃣7️⃣-1️⃣8️⃣ Da sauri yarinyar ta dakatar da shi ta hanyar faɗin "Yumba rukuna" (Am so tired), murmushinsu na manya Barrister yayi mata yana ƙarewa ƙyakkyawar fuskarta kallo wacce ta ƙara tafiya da zuciyarsa bai taɓa tunanin zan samu kansa da zazzafar soyayyar ƙaramar yarinyar like her ba, sai gashi in one time dukkan ƙofofin zuciyarsa sun kamu da son yarinyar. Shafa fuskarsa yayi kafin yace "let me introduce myself to u" Shiru yayi sbd ganin idanunta ya cicciko da ƙwalla ta marai-raice fuska kamar zatai kuka, a nan ya fahimci zallar shagwaɓar yarinyar ɗaurawa yayi da faɗin "My name is Barrister Hamdan Balarabe, but abokan aiki da kuma ƴan uwa na faɗa min Barrister, am the second born of my parents, ina da big bro but he's passed away shekaru masu yawa kenan, Mahaifina sunansa Balarabe Mumtah ya daɗe da rasuwa shi ma ina tare da mamana , we call her Granny, seriously i love her soo much more than anything, bayan ita sai first son ɗina yafi komai muhimmanci a gare ni, yara uku gare ni da babban ɗana Sheikh sai Fareeq mai bin Sheikh sai Auta Bahaiyya but duk suna school soon zasu dawo after holiday, ina da mata her name is Saudat but we call her Mami, nayi karatu mai yawa akan Shari'a, now am working with Sharia Court Of Appeal, sannan ina manyan contract da masu ƙasar Nigeria am the richer old man, Zaki yi farin ciki sosai zan shagwaɓa ki da kalar soyayyar manyan mutane" zuwa lokacin tuni idanunta sun kawo ruwa wanda ya sauka saman kuncinta, ware idanunsa yayi yace "Ohh my God, what exactly make you cry beauty?" Kamar zatai kuka tace "Dan Allah am going za'a min faɗa" Jinjina kai yayi yace "Ok you can go amma kimin mgn da mahaifinki please" bata ce komai ba tai gaba abinta, bayanta yabi har zuwa ƙofar gidansu tana zuwa ta shige gida, a parlour ta samu Yakura (yayar Mama) zaune tana cin abinci brabisko da miyan yakuwa wanda ya ji nama manya-manya, zama tayi saman kujera tana lumshe idanunta a hankali kuma ta zare airpies ɗin kunanta, ɗan tsaki taja kaɗan tana zamewa akan kujerar idanunta cike da hawaye wanda ita kanta bata san na menene ba, Yakura ce tace "Wushe(sannu)" buɗe ido tayi kafin ta miƙe tsaye tana jin zuciyarta duk ba daɗi tace "ina su Yaya Falta da Yana?" Kai tsaye Yakura tace "suna cikin ɗaki" hanyar cikin ɗakin tayi da ido kawai Yakura ta bita saboda yanayin ta da ta ga ya sauya, bata da tambaya sosai shiyasa ta ja bakinta tai shiru. A cikin ɗaki ta samu Yana da Yaya Falta suna turara kayansu da wani tureren ice mai ƙamshi AL'AJABU, ƙarasa shiga ciki tayi da sauri Yana tace "kin daɗe da yawa" murmushi kawai tayi masu tace "Kunyi kyau" tashi Ya Falta tayi tace "duk ƙyan mu ai bamu kama ƙafar ƙaramar ƙanwar mu Fannah ba" kwaɓe fuska tayi tace "ni duk isa ta kuke da wani kyau? Ƙyan da bashi da wani amfani" dafa shoulder ta Ya Falta tayi tace "babu wanda bai san cewa kaf family kinfi kowa kyau ba ke dai kawai wani dalili naki ya hana bawa wanda suke sonki da Aure damar masu dama ba" Yana ce tace "Abinda kike so is complicated Fannah, kowa nada tasa ƙaddarar amma haƙuri da juriyar mutum ke sawa, ƙaddarar ta zama mai sauƙi, look dani da Ya Falta mun isa good example to you, we're your sisters Ya Falta babba then me sai ke duk muna gida zaune Allah bai kawo mana mijin Aure ba, dukkan sa'aninmu suna ɗakin mazajansu, do u think we're happy?? No! Muna fatan wata rana ace muma muna ɗakin mazajan mu, amma ai bamu nuna wata alama ta damuwa ba, takura damuwa bata taɓa sawa Ubangiji ya bamu Mijin Aure" Ya Falta tace "Muna farin ciki kin samu masu sonki zamu ragu a gaban iyayen mu amma kina wasa da damar ki? Wallahi kina cutar kanki zuciyarki na yaudarar ki, how wannan mutum zai san da zamanki? Uhm ki ɗauka ya sanki amma bazai taɓa ko love dake ba bare Aure abeg my friend do what is right is not is easy" kuka Fanna tasa tace "Wallahi zuciyata ba zata taɓa Yaudara ta a kansa ba, kuma insha Allah zai na samu farin ciki na da kuma muradin zuciya ta just watch and see" da kallo kawai suke bin ta domin da alama ƙanwar tasu tayi nisa bata jin kira.. A can waje kuwa Barrister ne da mahaifin Fannah mai suna Baa'na, Murmushi Baba Baa'na yayi yace "To Barrister bazan hanaka auren Fannah domin basan kalan nata ƙaddarar ba, a wannan karan kuma bazan nemi shawararta ba, domin na gaji da banzar ɗabi'arta" ƙasa Barrister yayi sa kansa yace "Ayya! Abba kasan yaran yanzu sai addu'a ai mata a hankali", "wake bin yara yanzu? Ba damar da ake basu yasa suke iskancin dasu ka ga dama ba?" Barrister yace "haka ne Abba nagode sosai da fahimtar da kayi har ka yarda ka bani Auren Fannah, zaka iya yin bincike a kaina domin ka samu full information ɗin da kake buƙata a kaina", Murmushi Baba Baa'na yayi yace "Kada ka damu wannan abinda ya zama dole ne, ka je zuwa gobe, in Allah yadda zaka ji mu" Barrister ya shafa kansa yace "Abba zan iya magana da ita?" Kallonsa Baba Baa'na yay yace "No ka je goben sai ka dawo, Autar tawa rigimarta yayi mata yawa" Sallama sukai Barrister ya ɗauki kuɗi masu yawa ya bawa Baba Baa'na yace "A'a sam-sam kada ka fara ka bari muga kamun ludayin", "to shikenan Abba na gode da karamci" Sheikh ne kwance saman makaken gadonsa yana juyi tare da rungume pillow, yana ɗan sakin murmushi, idanunsa ya ɗaga zuwa Jamus jikin bango Ya kalli zanan Airah da yayi she looks so beautiful, musamman daya zanata tana murmushi, zuwa yanzu ƙaunarta ta kama ratsa dukkan jikinsa, murmushi yayi yana ƙanƙame pillow shi ɗaya cikin ƙasa da murya very slowly yace " I only want you, is only you i want to spent my life with" ajjiyar zuciya ya sauke kafin yasa soft hands ɗinsa ya shafi fuskarsa zuwa gemunsa yace "the you know what Aljanata? Don't ever try to leave me, i cant spend my life without you, you make Sheikh Imam hamdan, happy Yeah you make me happy, just like you says, but why is my heart telling me one day you pass away from me?? No i can't leave you, please Airah my Aljana promise you always be by my side, you're mine Airah.." ya ƙarasa maganar yana jan wani wahalallan numfashi tun bayan dawowarsa daga wajan aiki babu wanda yazo ya dubasa bare a ji yana buƙatar wani abu, he missed his Airah bai san mene yasa gaba ɗaya yau bata neme sa ba, lumshe idanunsa yayi sbd fitsarin daya cika masa mara, a hankali kuma idanunsa ya fara sauya kala sbd zafin da zuciyarsa ta farayi masa, ƙofar da aka turo yasa ya ware idanunsa a hankali ya kai kallonsa zuwa ga ƙofar haɗa ido sukai da Mami tana sanye cikin wata Orange ɗin atamfa ɗinkin fitted gown, ta ɗaura head har gaban goshi sai ƙamshi take kayan sun zauna a jikinta dukkan shape ɗinta sun bai yana, murmushi tai masa Sheikh kam tuni ya janye idanunsa daga Kallonta, "So sorry sweet, Granny bata jin daɗi ni kuma nai baƙuwa shiyasa ka ji shiru, na kira Arjun he's on his way", ta ƙarasa maganar tana zama kusa da shi tare ƙare masa kallo can tace "the you need something?" Muryarsa a can maƙoshinsa yace "Yeah! I do" idanunta ta sauke saman ƙirjinsa da sauri kuma ta lumshe idanunta tace "what?" Kai tsaye yace "I want to ease myself" miƙewa tai tana kama hannunsa tace "Ohh sorry my darling" Wheelchair ta ɗauka zuwa inda yake kafin ta fara ƙoƙarin taimaka masa wajan hawa Wheelchair hannunta ya sauka saman mararsa gaba ɗaya jikinta ya ɗauki rawa musamman da taji tudun mararsa, kasa ɗauke hannunta tayi sai ma ƙara kwantar dashi da tayi, Sheikh kam ko a jikinsa hanunsa kawai yasa ya zare nata hannun, bayan ya hau Wheelchair ya fara murzata zuwa bathroom sosai ya ke jin fitsari kamar zai fasa mararsa ya fito, Mami ficewa tai daga bedroom ɗin idanunta na sauya kala, yana shiga daga zaunan ya zare Manhood zuwa cikin toilet kana yay tsarki, ki fa kansa yayi saman sink yana fesar da numfashi zuciyarsa fal da tausayin kansa gefe guda kuma ga rashin Aljanarsa, ji yayi an shafa sumar kansa wata sassanyar ajjiyar zuciya ya sauke kafin ya ƙara rufe idanunsa rufe, Murmushi Airah tayi kafin ta murza Wheelchair ɗin zuwa cikin bedroom, gyara masa komai tayi sannan ta zauna kusa dashi tana danna masa ƙafarsa tace "Kayi haƙuri kaji, ban ƙarawa nayi ƙoƙarin zuwa gare ka amma na kasa am so sorry Rayuwata" ƙin kallonta yayi sai ma ƙasa daya ƙarayi da kansa yana sauke tagwayen ajjiyar zuciya, leƙa fuskarsa tayi a karo na farko taga hawaye masu zafi suna sauka daga cikin idanunsa zuwa tafin hannunsa, jikinta har rawa yake ta shiga faɗin "What..What.. are you cry? Ka yafe min please" kasa magana yayi sai jawota jikinsa da yayi tare da fashewa da kuka. Da yamma Arjun ya shigo gidan fuskarsa babu yabo babu fallasa Granny ce tace "Ya haka kuma? Kamar dai wanda aka cewa Sadiya ta mutu? To Allah dai ya kyauta, ko ita Aliliyan tace bata sonka??" Kallonta kawai yake kafin yace "a'a Granny ba ko ɗaya daga ciki, hasali ma yau Papa ya je gidansu shida Abba Barrister" haɓa Granny ta riƙe tace "shi Barrister dama yana nan ne? Yace min zai tafiya zuwa Barno sai jibi zai dawo Abuja _( a farkon labari na ambaci Maiduguri wannan duk cikin mafarki ne,amma garin dasu Imam suke shine Abuja)._ Arjun yace "Ni dai na ganshi" tace "to Allah ya kyauta yayi mana maganin abinda ya dame mu, na ji ance gata su Hayya zasu dawo" Arjun na zama yace "haka na. ji Mami ta ce" bata ƙara magana ba ta cigaba da damawa Sheikh fura wacce ta ji Zuma ga wata dakakkiyar fura da aka zuba akai, kindirmon yay sanyi sosai, ba shi tayi tace "sai ka sakamar min mara nai fitsari" kyakƙyawan murmushinsa ya saki wanda yake ƙara masa kyau yace "da riƙe maki nai ko?" Granny tace "Allah dai ya kawo mai maka abinda nake maka", cikin ransa yace "already i have it" "magana kake?" Shiru yayi tare da yin bisimillah ya fara shan furar, daɗi da kuma garɗinta yasa yayi baya kaɗan yana Lumshe idanunsa, girgiza kai Arjun yay yace "Am Engaged " Sheikh na Murmushi yace "congratulations hankali ya kwanta,what ever, am happy too saboda farin cikin ka is my happiness" da sauri Arjun yace "Ohh really??" bai kulasa ba ya cigaba da shan furarsa, domin yasan maganar da take damun Arjun, miƙewa Arjun yace "akwai sabon contract na makaranta zaka zana ana buƙata nan da kwana biyu sun bada kuɗin da komai na zuba kuɗin cikin account ɗinka" Idanunsa a lumshe yace "why me? Ka ɗauka duk kayi hidimar biki" kallon baka da hankali Arjun yayi masa kuɗi masu shegen yawa zai ce ya ɗauka "Next two months bikin", "Allah ya nuna mana, babu wata bidi'a da Za'ai kama shirya" daga nan sallama su kai Arjun yabar gidan ya nufi gida Fitowa tayi daga bathroom sanye da kayan bacci komai na jikinta a bayyane, da kallo Barrister dake gefen gadon ya bi ta har ta shige ta nufi gaban dressing mirror ta shiga shafa humura masu ƙamshi sosai, miƙewa Barrister yayi tare da ƙarasawa wajan ta yana ƙoƙarin riƙe tace "Kada ka fara, banga me zaka amfana min ba, banda gayyar siya mutum jiki duk infection ya kashe sa" cikin ɓacin rai Barrister yace "look ba ihu nace kimin ba domin har yanzu My son Yana parloo shida Granny, just nazo KI ban haƙƙi na" cikin fuskata tace "na ƙarfi ne haƙƙin ka zo ka ƙwata" Kallonta yayi yace "kin san zan iya,vamma bazan hakan ba kawai ina baki shawara ki sauke nauyin dake kanki Saudat", "ok ka jira next but now am not in the mood" kallonta yayi yace "kamar ya you are not in the mood Saudat, look how erect i am" Ya nuna Manhood ɗinsa daya mik'e da cikin sleeping dress yace "Saudat wacce irin mata ce ke??", Cikin ɗaga Murya tace "kai ma wanne irin miji ne?nafa san komai a kanka Barrister kar ka mai dani sakarai" jinjina kai yayi yace "Ok get ready am getting marriage soon", ware kafaɗa tayi tace "dana fi kowa farin ciki" cikin zafin nama Barrister ya nufi inda take tsaye hana zuwa yasa hannu ya fincike rigar dake jikinta."Ni kikewa wulaƙanci akan ina buƙatar haƙƙi na dake a kanki? Baki tsoran fushin Mala'iku?" Mami ta kallesa tace "ni fa bawai so ne ba nayi ba kai ne bana sha'awarka kwata bana jin wani feelings a kan ka" , cikin ɓacin rai yace "ko ki so ko kada kiso wallahi sai na amshi haƙƙina yanzun nan" yana faɗin hakan ya cilla ta saman gado.... *Topic gareku mata* Rashin sha'awar jima'i na yin tasiri a rayuwar mata da miji Mata sun fi yiwuwar rashin son jima'i ninki biyu idan aka kwatanta su da abokan zamansu maza, in ji wani rahoto kan yadda ake jima'i a Birtaniya. Rahoton ya gano cewa a yayin da mata da miji ke nuna rashin sha'awar yin jima'i a lokacin da suke kara manyanta, ita macen takan ji ba ta sha'awar yin jima'in saboda dadewar da aka yi tare. A takaice, rashin isasshiyar lafiya da shauki tsakanin mata da miji yana yin tasiri wurin sha'awarsu ta yin jima'i. *ABUBUWAN DA SUKE KAWO SAB'ANI WURIN JIMA'I TSAKANIN MATA DA MIJI* mazaje su ne kawai suke yin jima'i domin jin dadi amma abin ba haka yake ba, a wurin mata ba wai ana nufin cewa mata ba sa jin dadi wurin jima'i bane. Abin da ake nufi, shine ita mace bayan ta ji dadin jima'i akwai kuma abin da zai iya biyo baya wato shi ne daukar ciki da wahalahlunsa, saboda haka, kafin namiji ya iya buɗe kafofin sha'awar mace sai ya sami karbuwa a zuciyarta tukunna, rashin yin la'akari da wannan shi ke kawo rashin cin nasarar mijin wurin jawo hankalin matarsa, kafin miji wurin jawo hankalin matarsa, kafin miji ya fara kokarin ta da sha'awar mace, ya kamata ya fara kokarin samun shiga zuciyarta tukunna ta hanyar yin amfani da maganaganu na soyayya masu sa zuciya nutsuwa. bayan wannan akwai wasu abubuwan da su ke kawo sab'ani wurin jima'i, tsakanin mata da miji wadannan kuwa su ne: Remain 1 page🤕 Share do Allah Fisabilillahi 20/10/2021, 20:44 - 🤔🤔: *SIRRIN MU* *BY* _✍🏾 NIMCYLUV_ Dan Allah kuyi SUBSCRIBE na youtube channel ɗina mai suna *Nimcyluv T.V* https://youtube.com/channel/UClywbagpRx5qlVyOy0ZPPDA Last 🆓P EPISODE 1️⃣9️⃣-2️⃣0️⃣ "Ni ne mijin ba ke ba,so ina da right ɗin da zan karɓi hakƙi na a duk sanda naga dama,and you know what? Wlh kinyi kaɗan kice za kiyiwa Hamdan Balarabe fariya da jikinki, lemme repeat myself aure zan ƙara zan aure sabuwar harka mai jini a jika wacce ta fiki komai, zan auri farin cikin rai na zan zauna da macen da zuciyar Barrister Hamdan Balarabe ta aminta da ita, abun farin cikin kuma Kanuri ce inda zaki tabbatar tai maki zarrah, ta fiki komai ko zama kayi inda take sai ka tafi da dadɗan ƙamshin ta, zan nuna maki bani da kirki tunda haka kike buƙata daga gareni,ina ɗaga maki ƙafa nai maki zuro na sanya maki idanuwa na amma ke baki gani zuro ko??? Weldon Saudat..." Ya ƙare mgnar yana cilli da ita saman gado tare da pouting ɗinta da yatsarsa ya ce "Badai akan haƙƙi na kike wannan shirmen ba? To kije ba'a so akai kasuwa,kuma na gaya maki muna nan dake za kizo inda Barrister Hamdan Balarabe yake a lokacin zan nuna maki true color ɗina" Yana faɗin hakan ya fice daga cikin ɗakin yana dafe kansa tare da fesar da iska, miƙewa Mami tayi tana wani kalan murmushi mai nuni da dani kake zan can, hannunta gaba ɗaya ta tura saman waist ɗinta ta shiga girgiza wa wai kamar ita za'a ce wata mace ta fita komai? Lallai Barrister zai sha Mamaki, wacce kalar lukutar masifa yake son jawowa kansa? Murmushi tai tana shafa tsayayyun brest ɗin ta Mami macece ƴar gayun gaske bata yarda da raini da wulaƙanci ba, tana daji da kanta irin matan nanne da kallo mutum bai ishesu ba, ga kallon raini daya zama ɗabi'arta tana son ado da gayu sam bata yarda da ƙazanta ba tana jin kanta kamar ƴar shekara sha biyar, kallon kanta tayi ta cikin mirror cikin sexcy voice ta ce "Weldon da sweetheart kayi aiki mai kyau,zan baka mamaki tabbas zaka gane ni ba irin matan da kake tunani bace,ina matar ba shike nuni daka isa dani ba, zan maka illa a zuciya Yes! Iove you so much darling but ba na da feelings a kanka since i was have my on children, ban san mene yasa ba amma dole zan nemawa kai na mafita kamar yadda kaima ka zaɓi yin aure, let's see my time talk us everything tana faɗin hakan ta ɗauki wayarta tare da kunna data ta hau network, best group ɗinta ta shiga wanda take samu zafaffan littafai masu shegen daɗi, ganin writer ɗin MOON tai mgn a grp yasa Mami faɗin "Hi my best writer" cikin few minutes Marubuciya Nimcyluv ta bata feedback,har mamakin writer ɗin take sam bata da jin kai na sauran writers ɗin Musamman yadda take zama cikin members ɗinta suna hira. "Mrs Hamdan how are you?" Nimcyluv tai bata reply da haka, Mami na Murmushi tace "Allhamdulillah,ya hqr da jama'a? Naga kinyi mgn a grp akan sabon littafinki wanda zaki cikin dabuwar shekara how much? I want to pay the money" Wata marubuciya ce mai suna Real Smasher ta ce "A'a kaga manyan tun kafin time weldone ƴan ajin tubarkallah!" Dry sosai Mami tayi domin tana son taga tafi kowa, jin shiru yay yawa yasa "Anty Nimcyluv am waiting wlh idan ina karanta books ɗinki ji nake kamar realty abin ke faruwa can You imagine halin dana shiga da akace Deen ya mutu,Wow! ga littafin UNCLE NE ba'a magana thank you so much my best writer" Nimcyluv ce ta fara typing cikin ƙaramin lokacin tai reply da "Oh! Yeah that's what i want, Ina magana akan book ɗin WASIYYA ne but ba yanzu zai fita ba" Da sauri Mami ta ce "Anytime your welcome dear, ai ba jira cos i like your story and you too nasan akwai lukutar masifa a book ɗin WASIYYA" daga nan sukai sallama Mami tai mata transfer na 50k tana ƙara mata gdy... washe gari da safe misalin 10:30 mutan gidan suna zaune saman daining suna breakfast kasancewar weekend ne, Sheikh na zaune da wani tissue ɗin yadi fari ƙal sai sheƙi yake ya sanya hula jar dara mai gashi-gashi tai bala'in yi masa kyau, baka jin komai sai ƙarar spoon,fork,and knives gabansa chips and chicken ne sai ƙamshi suke, ga Arish with cup of coffee sai tiriri yake, Lumshe idanunsa yay yana jin zuciyarsa na masa zafi tunda yazo wajan ya gaidasu an garara samun wanda zaice Sheikh yaka kwana ko yaya jikinka? Bai samu wannan damar ba, tagwayen ajjiyar zuciya ya shiga saukewa tare da fesar da iska daga cikin bakinsa, he missed his Airah a lot "the you like the girl?" Shiru Sheikh domin bai ma san me ake cewa ba bare yasan cewa dashi ake,Mami ta ajjiye cup ɗin hannunta tare da kallon Sheikh ganin yadda ya lumshe idanunsa yana jan ƙwantaccen beared ɗinsa yasa ta ɗan ja idanunta itama ta lumshe kamar mai shirin yin bacci Barrister yace "My son" ya faɗa buga daining wata wahalalliyar ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke yana ɗan zare fararan idanunsa masu ɗaukan ido kallon Mahaifin nasa yay ba tare da yace komai ba,ganin haka yasa Barrister faɗin "You look so worry Son meke damunka?,what exactly making you sad?" Gently ya ɗago kansa yana ƙara fuskar mahaifinsa juyawa yay suka haɗa ido da Mami tattausan Murmushi ta sauke masa, numfasawa yay yace "Me kace Abba?" Barrister ya goge bakinsa yace "Ina magana akan Nana wacce na keso na haɗaka Aure da ita" ɓata fuska Sheikh yay tare da danna abun jikin Wheelchair a hankali ta fara tafiya mmki sosai ya bai yana fuskar Barrister ganin duk son Sheikh da coffee ko kaɗan bai sha ba, bare kuma yaci sauran abinci Parlour Sheikh ya koma da zama har wajan daya ajjiye kayan art ɗinsa cikin nutsuwa ya ɗauki blue ɗin color ya fara yiwa zanan coloring. Miƙewa Barrister yay shima yabi bayan ɗan nada sbd yau yaga da sarauta ya tashi Mami dai murmushi kawai take saki ita kaɗai tasan abinda take shiryawa, zama Barrister yay a gefen Sheikh kafin yace "Wow who is she?? Zanan yay kyau" wani killer smile Sheikh ya saki sbd yabon Airah ɗinsa da akai, idanunsa a kanta yace "i have no idea why nake zanata,but she's very special to me Abba" Barrister photon Airah kawai yabi da ido kafin yaja numfashi yace "Ok let's talk dear za'a kai kuɗin gaisuwar iyaye, sannan zaka shirya kai da Arjun kuje wajan yarinyar kafin nan Fareeq ya dawo sai kuje gaba ɗaya" slowly ya janye idanunsa a kan Airah kana ya ɗura a kan fuskar Barrister ya ce "Why dole sai ni za tasu? Abba kuda koka haifan ma baku da cikakken lokaci na bare wacce kuke shirin ƙaƙabamin? Ban san daɗin iyaye ko daɗin shira dasu ba, kullum sai dai naga Arjun da Ummi suna Shira tana masa faɗa idan yay ba dai-dai ba,sannan ta jashi jikinta ta rungome, meyasa ni ban samu wannan damar a wajanku ba?ko dan kasancewata nakashasshe Abba, idan aiki yake saka haka Abba dan Allah ka hqr da wannan aikin ina da kuɗin da masu isa mu cinyesu komai yawan mu,ina buƙatar iyaye domin sune jigo a rayuwar ko wanne yaro,ban san tayaya zan gane idan nai abu kuskure ba ne,Granny kawai ke ƙoƙarin fahimtar dani, Granny a kullum shakarunta shigewa suke kenan wata rana zan iya rasa ta,i need your love and care ka bani lokacinka nai Shira dakai kaji damuwata ka rungume ni jikinka koda sau ɗaya ne" ya faɗa idanunsa na cika da ruwan hawaye,Mami ce ta miƙe tare da ƙarasawa inda yake ta zauna bata jira komai ba tasa hannu ta jawosa jikinta ajjiyar zuciya ya sauke yace "Mami..." Sai kuma hawaye ƙara rungomesa tayi tace "it's okay sweet,ya isa kaga condition naka bayan halin da kake ciki ga lalurarka kayi shiru haka,i promise ban ƙara barinka indai aiki ne zan ajjiye nawa" da sauri ya ɗaga kai ya kalleta kamar bazai magana ba sai kuma yace "Really?" Tana wani ƙayataccen murmushi tace "sure.." Lumshe idanunsa yay tare da zare jikinsa ya kwanta jikin kujerar kamar yadda Sheikh yake kallon zanan haka Barrister yake kallon zanan. "Look son kasan bazan maka abinda zai cutar da kai ba,hasali ma inayi ne domin ganinka cikin farin ciki kamar kowa,ina son dawo maka da farin cikin daka rasa ka aminci ka auri Nana,dani dakai zamu ƙara hutawa manyan contract zasu ƙara shigo mana ba tare da wani shamaki ba,kuma yarinyar nan ita tace tana sonka kaga babu maganar cutar dakai sai dai ta sanya ka farin ciki ma" shiru Sheikh yaywa Abban nasa ya shiga fesar da iska daga cikin bakinsa a hankali kuma ya saki Murmushi tare da shafa fuskarsa ya ɗaga gira guda ɗaya,gaba ɗaya Barrister da Mami suka saki baki suna kallonsa Musamman dasu kaga ashe duk abinda yake mage yakewa, miƙewa tsaye Barrister yay sbd a yau ya keson zuwa Barno ya dawo, idanunsa akan Sheikh yace "Am going nan da 1week Baffanka zasuje ai mgnar aurenka da Nana,yadda nai al'ƙawari dole na cika ba zaka sa na zama mutumin banza ba" Granny ce ta shigo parlour'n tana faɗin "A'a ya haka? Kamar dai dole? Me kake masa na rayuwa da zaka ishi yaro da mgnar aure? Tunda yace baya buƙata basai a rabo dashi ba fisabilillahi,kaifa barista ga daɗe da zama sallamamme banda haka ina ruwanka da takura yaro akan wata Nana,Nano nace Nano bazai aureta ba,ban dama zamani yaushe na taɓa jin mace tace tana son Namiji banda lukutar masifa da rashin kunya da tai yawa a wannan zamanin,to wlh kul kadama ka fara bana son shirman banza". Mami dake zaune ta kaɗa ƙafa tace "Ah to ƙilan tunda kece zaiji maganarki,amma ni na gaya masa ya rabu da sweet yaƙi shiyasa nai shiru". Granny ta ce "idan ta ƙamarka ka haifesa kana da iko dashi to Allahamdulillah kaima ba daga sama ka faɗo ba ninai ciwon maƙudarka kwanana goma a asibiti kamar bazan rai ba,ledar jinin nan haka na shanye goma sha biyar kamar dai mayya,kai nasha baƙar wahala kaga ni nake da ikon yi maka dole bakai ba". Barrister kallon Granny kawai yake kafin ya ce "Amma Mama haka za'a bar sa fisabilillahi? Kina Arjun an gama komai na bikinsa" cikin kumfar baki ta ce "Maye kuma Ranjun? Nace uban waye Ranjun? To maza ɓace daga gaba kafin na baka mamaki". Ransa babu daɗi ya fice daga cikin gidan gaba ɗaya zuwa airport. Miƙewa Mami tayi ta nufi kitchen tsaye ta samu mai aikinsu Asma'u tace "Asma'u kiyi mana tuwan shinkafa da miyar wake With cow meat" Asma'u ta rusuna ta ce "an gama Hajiya" tasu zama a parlour'n amma ganin Granny yasa kawai ta shige flat ɗinta. Gyara zama Sheikh yay yana ƙara sakin lallausan murmushi a hankali magen dake gabansa tai girgiza ta zama kamar Granny, kusa dashi ta zauna jikinta a sanyaye ta kalli Sheikh tace "me yasa kaƙi amincewa da maganar Abba?" Ka faɗa ya ɗaga sai kuma ya ɗan haɗe rai yace "sbd ke" hanunsa ta riƙe cikin nata da sauri ya riƙe hannunta sbd zafin da yaji ya shiga kallonta yana son ya tambayeta bata da lfy ne ko me?? Amma ya kasa ƙasa Airah tai da murya tace "so the you love me right?" Idanunsa a lumshe ya shiga tauna lips ɗinsa wanda ya zame masa jiki can kuma yace "Yes! I do Honeybee" Murmushi tai masa tace "don't ever betray me Rayuwata,ina shan wahala a kanka but you can understand, kada kaso wata bayan ni zuciyata da kuma Ruhina ba zasu taɓa yafe maka ba idan har ka ci amanata ina son ka da yawa" Lumshe idanunsa yay sbd daɗi da farin cikin da yaji yana ratsa dukkan jikinsa, kasa magana yay sai hanunsa daya sanya ya jawota zuwa jikinsa, rungome juna sukai kowa ya shiga sauke numfashi, Airah kam tunanin mgnar da Tijama tai mata take tabbas tana buƙatar ƙarin haske akai,tana son tasan Ɓoyayyan Sirrin da Tijama take ɓoyewa... Granny ce ta fito daga cikin kitchen hannunta riƙe da mug na fresh milk saurin sakin mug ɗin tayi jikinta ya hau rawa, kallon kanta tayi sannan ta kalli wacce take jikin Sheikh wacce ya rungome kamar zai mai data jikinsa,tabbas mai kama da ita ce babu ko bambancin hatta kayan dake jikinta shine jikin Airah wacce tai siffar Granny tsaɓar tsoran daya shigeta bata son lokacin data sanya ƙara ba,firgigit Sheikh ya dawo daga cikin hayyacinta Airah kam tuni tayi girgiza ta koma siffar Arjun sanye da milk ɗin shadda, Mami da sauri ta fito tana faɗin "Mama lfy?" Juya idanu Granny ta fara kafin ta sauke idanunta akan Arjun tace "Fisabilillahi Ranjun ba kaga wata mai kama dani a jikin Imamu ba?" Juya idanu Airah wacce sukewa kallon Arjun tace "kawai dai kice mutananki sun kawo maki ziyara,amma wa za'a gani mai kama dake wanda ya huce ke ɗin" zare gefen zaninta tayi ta shiga matsar hawaye tace "Amma wlh mutum nagani sak mai kama dani,babu abinda ya raba" Mami danne dryar ta tayi tace "Ikon Allah,tsorata kawai kikai" Face majina Granny tayi tace "Amma fisabilillahi kuma wacece basai ta tsaya ba inji yadda akai muke kama,koba gsky ba" Sheikh dake sakin murmushi shi ɗaya idanunsa akan Arjun ko kace Airah yace "Ƙilan kuma tana jinki ai,kinga cikin dare sai tazo ko gaisa" da sauri Granny tai flat ɗinta har tana tuntuɓe.Mami ciki ta koma tana jirin zuwa ƙawarta Fariha, Mami na barin wajan Airah ta miƙe tsaye jiki kuma a sanyaye bata jira abinda Sheikh zai ce ba kama Wheelchair ɗin har cikin falt ɗin Sheikh, a gyara yake komai tsaf sai ƙamshi yake ga ƙarar a.c daya haɗu dana airfreshner mai ƙamshin strawberry, a saman wata lafiyayyiyar kujera dake jikin gadon ta ajjiye Wheelchair shi kuma ya zame daga saman wheelchair zuwa kan kujera,ganin zata juya yay saurin riƙe hannunta idanunta ta runtse kafin tace "zan duba abu" sakin ta yay kana ya koma ya kwanta da sauri Airah ta shige toilet tana shiga ta nufi wajan Sink ta shiga yin Aman jini duk ta fita a hayyacinta, baki ta wake kana ta kalli cikin madubin sai kawai ta fashe da kuka ta shiga faɗin "Am sorry Sheikh Imam hamdan Balarabe, i can't life without you amma dole zan barka, nasu ƙarasa rayuwata dakai amma bazan iya ba, nasu baka kariyar da nake faɗa maka a koda yaushe cewa zan baka amma bazan iya ba,ko bana nan tabbas zanyi faɗa da dukkan wanda yace zai cutar da rayuwarka, zan tabbatar baka zauna da wata macen ba sai ni zakai ta rayuwa kai ɗaya ba tare da kasan daɗin mace ba bare ka fara son mace,zan dauwamar dakai da soyayya ta, tabbas hakan shine kawai mafitar daya rage min" tana faɗin hakan ta fice daga cikin bathroom ɗin,samunsa tayi tuni yay bacci rungume da pillow,maganar Tijama ta faɗu mata da take cewa; "Ki tabbatar kin shiga jikinsa na kwana biyu,ki bashi farin ciki, ki fara sabar masa da jikinki tun kafin wani kuskure ya faru ki lalata mana aikin mu"cikin baccinsa yaji kamar ana riƙe masa Manhoon ɗinsa ƙara ware ƙafarsa yay ya ɗan saki wani sound kaɗan, lokacin da Airah ta ɗora bakinta a kan Sheikh ɗinsa yay saurin ƙanƙame pillow jikinsa, da sauri ya fara sauke ajjiyar zuciya kansa ya fara sara masa wata zufa ta fara wanke masa jiki duk da sanyin A.c dake ɗakin, Arjun dake tsaye saman kansa ya harɗe hannayensa yana kallon ikon Allah, yana zuwa gidan Granny tace masa "sannu Ranjun kai dai Allah yay maka albarka,yanzu ka tafi amma harka dawo" da kallon mmki ya kalli Granny sbd yasan rabonsa da gidan tun jiya "Ni kuma Granny?" Ta washe baki tace "kaji ɗan nema to uban waye Ranjun idan ba kai ba?" Idanunsa ya ɗauke zuciyarsa cike da tunani kana yace "Ina Buddy?" "Yana ciki kaga har lokacin Zhur yayi" bai ƙara mgn ba ya shige flat ɗin Sheikh shine fa tun daga bakin ƙofa ya fara jiyo sounds ɗin Sheikh yana sakin wani irin nishi, tsaki Arjun sbd labarin Sheikh ya fara bashi tsoro hanunsa yasa ya fara bubbuga jikin kujerar a hankali Sheikh ya taune bakinsa tare buɗe nauyayyun idanunsa da sukai masa nauyi, jajayen idanunsa ya sanya a cikin idon Arjun, gaban Arjun ne ya faɗi domin this is the first time on his life da yaga idanunsa Sheikh a haka, Sheikh kam janye idanunsa yay tare da haɗe cinyoyinsa daya kejin kamar danshi a jikinsa bai yarda Arjun yaga komai ba, Allah ya taimakesa Wheelchair na kusa dashi ya taimaka da ƙyar yaja jikinsa zuwa kan kujerar, hanunsa dafe da forehead ɗinsa wanda ya kejin kamar zai rabe gida biyu sbd azabar ciwon da yake masa, tsaye Arjun yay ya kasa koda mutsi Sheikh na shiga bathroom Arjun yaje wajan wadrp ya ɗauko masa wata tsadaddiyar shadda ƴar gske ruwan ƙwai anyi masa ɗinkin half body hatta hannun rigar half ne,kana ya ɗauko masa wata milk ɗin hula tangaran sai milk ɗin takalmi Kubta mai ƙyau, sai agogon warist company Gucci, kana farin glass ɗinsa mai ƙyau ya ajjiye masa parfumes ɗinsa duk gefe guda, Sheikh tsayawa yay yana kallon ikon Allah kamar a mafarki haka yake ganin abun abinda bai taɓa gani ba wai Sheikh ɗinsa ce take halbawa harda dripping take, sai kuma tunanin Airah ya faɗo masa lallausan murmushi ya saki kana ya saukarwa kansa shower, ba'a ɗauki lokaci ba, ya gama wanka tare da ɗura towel ya ɗan bugga bathroom ɗin, Arjun ne ya shigo kana ya fito dashi. Duk abinda yake bai yarda ya kalli Arjun ba kuma fuskarsa a haɗe a haka ya gama shiryawa yay masifar kyau kamar dai wani ango, sai zabga ƙamshi yake sosai Sheikh yake babba mai girman gaske domin iya ƙafaɗarsa kaɗai abar kallo ce, daga nan masjid suka nufa domin yin sallar zhur then su huce gidan Redio....Mami ce zaune da ƙawarta Fariha ajjiye cup ɗin hannunta tayi tace "baki da kirki Saudat basan rashin imanin ki ya kai haka ba wlh" dry Mami tayi tace "baki da hankali solution nake nemawa kai na,kuma i alrdy make my decision babu wanda zai sauyan tunani" Fariha tace "nidai damuwata yadda Abban Taufiq yake share ni yake banza da lamari ne, i believe him baya kula wata ƴar mace bare zuciyata ta zarge sa akan mata yake mu'amala dasu har yake min wannan wulaƙancin, kullum naje masa da buƙata ta nunawa yake bashi da lokaci na, na fara gazawa wlh i can't handle it" Taɓe baki Mami tayi tace bazan san mene zance maki ba, amma zan baki number writer ɗin The new emir sai ki gaya mata damuwarki ƙilan zaki samu mafita, da sauri Fariha ta amshi number, network ta hau tare da yiwa NIMCY mgn tai mata bayanin yadda mijinta yake banza da ita koda takai masa kanta, babu jimawa Nimcy tai mata reply da; _Matsalolin suna da yawa Malama Fariha, bansan tayaya matsalarki da mijinki ya fara ba,zan baki wasu baya nai saiki duba yanzu i don't have much time to talk about this,but we'll talk my tomorrow morning in sha Allah,Allah ya dai-dai ta tsakani_ Murmushi Fariha tayi tare da reply da heart emojin kana tace _"Thank you so much Anty Nimcyluv Allah ya ƙara fikiri😍"_ Nimcy: _Thnks lemme send it to you_ Babu daɗe wa ta fara rubutu kamar haka: Dukkan mace matar aure ko budurwa data samu kanta a yanayi na rashin sha awar namiji to gaskiya ta hadu da kalubale a bangaren zaman aure Zata fuskanci rashin kulawa a wajen mijinta musamman idan ya fahimci batajin dadin saduwa dashi ballantana ace tanada kishiya shiyasa mata masu dabara basa nunawa namiji suna cikin wannan halin kokarinsu su gamsar dashi da abinda yakeso Hakika wasu matan tun suna yan mata suke kashe kansu da shan wasu magunguna marasa inganci da sunan ya rage musu sha awa wasu har jar kanwa suke jikawa da lemon tsami sunasha don ya rage musu sha awarsu kuma wannan duk kuskurene idan har bazaki iya azumiba to ki ajiye burin rayuwa kiyi aure domin ita Sha awa ajikin mace ko namiji ba cuta bace amma rashinta kuma cutace bazaki gane hakanba saita faru dake koda yake namiji be cika damuwa don bashida sha awar maceba amma kuma matarsa zata rasa kulawa To idan akace rashin sha awa ga mace ko rashin jin dadin jima i to ya hada abubuwa da yawa amma masana sirrin jima i suna takkaita bayanin gida uku kamar haka. (1) akwai wacce tana sha awar namiji hasalima ko zancen jima i tayi da namiji koda a wayane ko a chat zataji jikinta ya jike alamun sha awa zata bayyana a fuskarta zataji sha war namiji ya sadu da ita amma da zaran na miji ya saka jikinsa a nata saita rasa ina dadin yake ita wannan tana bukatar kyakyawar kulawar soyayya a wajen mijinta ya kamata mijinki yasan hanyoyin Wato sarrafa mace da sanin wurarenda mace takeso namiji ya taba ajikinta musamman lokacin jima i kuma soyayya itama tanada muhimmanci awannan lokacin wato tana saka mace jindadin jima'i. (2) sannan akwai wacce ita kuma kwata kwata bata sha awa ita ko za ayi wata daya ko biyu ba a tabataba batada matsala idan kin samu kanki acikin wannan halin akwai tambaya akanki kina mafarkin namiji? kinada jinnu ma ana suna tashi? idan duk babu daya to kici gaba da shan maganin karin sha awa amma wanda zaki hada da kanki wannan duk muna bayaninsu a grp to idan kuma kina mafarki ko kinada jinnu suma suna daukewa mace sha awa ta zahiri saboda surinƙa saduwa da ita amafarki sannan zasu iya barin mijinki ya rinka jin dadinki idan sunga dama shima su hanashi saiya rinƙa jinki salam kamar ba maceba ko kuma su hanaki ni ima lokacin saduwa saiki bushe sai anyi da karfi ta shiga gaskkiya wannan matsalace kuma wani lokacin sihiri akeyiwa mace hakan take faruwa kiyi kokari ayi miki ruƙiyya wacce ta dace da sunna kema kici gaba da addu a kuma kina kwaciya da alwaa idan zaki kwanta ki karanta wasu ayoyi daga cikin qur ani sannan kina share shimfida kafin kwanciya kuma keda mai gida ku rinka addu a kafin ku fara jima i insha Allahu zakiyi mamaki (3) haka kuma akwai mace wacce tana sha awar namiji amma ta fiso ya saka mata yatsa a jikinta tafi jindadi idan ya saka mata jikinsa sai taji daɗin ya ragu kuma irinsu zaka samesu da bushewar jiki to irin wannan itamma tana buƙatar kulawa ta musamman daga wajen mijinta sannan kada kiyi. wasa da gyaran jiki da kuma tsaftar HQ to amma inaso ki gane shifa jin dadin jima i ya danganta dagake wato ina nufin yaya sha awarki take yawan sha awarki shine yawan jin daɗinki yana iya kasancewa haka Allah ya haliccceki dama sha awarki gajeriyace ba iirin ta sauran mata ba sai kiji ƙawarki tana baki labari jin daɗin da takeyi a wajen jima i to zai iya kasancewa dama ta fiki sha awa ko kuma tafiki samun kulawa a wajen mijinta kinga kada kice dole sai kinji dadi irin nata Malama Fariha na barki lfy" Shiru Fariha tayi ta fara tunanin maganar NIMCY, kafin ta sauke ajjiyar zuciya ta kalli Mami tace "yanzu mene plan ɗinkin? Barrister dai Aure zaiyi babu fashi" dry Mami tayi sosai tana kaɗa ƙafa tace "Tabbas naji zafin abun kuma ina kishi da dukkan wacce zai aure,amma ba zai tafi a banza ba sai nai masa tabo kamar yadda yay min zan nuna masa mata guba ne" da mmki Fariha tace "what will you going to do" miƙewa tsaye Mami tayi tana kaɗa jikinta kafin ta riƙe waist ɗinta tace "Ɗan sa Imam shi nake so ya muri jikina ya muri abinda Ubansa ya kasa murewa, Zan maida Imam mijina Wannan zai zama Sirrin mu nida shi tabbas sai Imam ya kusanci matar Ubansa.... *END OF MY FREE PAGES HABIBATIES, TAMABAYAR A NAN A JIKIN WA SIRRIN YAKE??? GA MAMI,GA ALJANA AIRAH,GA KUMA FANNA AMAYAR BARRISTER?? ME ZAI FARO GABA? MAMI ZATA SAMU DAMAR SAMUN CIKAR BURINTA KO YAYA?? WANENE WANDA FANNA TAKE SO?? ME YASA AIRAH TA KASANCE A JIKIN SHEIKH IMAM HAMDAN BALARABE??? WANNE SIRRIN TIJAMA TAKE ƁOYEWA AIRAH???......* *HABIBATIES TAFIYA CE MAI TSAYIN GASKE KADA KI BARI SAI AN SATO AN BAKI ZAKI KARANTA KI ZAMA MACE MAI AJI WACCE TA HUCE KAYAN SATA,BANA ALLAH YA ISA A BOOK ƊINA BUT DUK WANDA YA KARANTA FREE YASAN INA DA HAƘƘI A KANSA HAKA NE KO??? CIKIN FARASHI MAI SAUƘI ZAKI KARANTA LITTAFIN NGD SOSAI DA SOYAYYARKU DOMIN DAKU NAKE TAƘAMA MASOYA NA,NASAN KUNA SON DUKKAN ABINDA NA BAKU DAN HAKA KO NUNA MIN ƘAUNA A WANNAN KARAN KU SIYI LITTAFI NA, AKAN FARASHI ME SAUƘI.* BOOK 1&2 AMOUNT #500 ACCOUNT NO: 0116886423 ACCT NAME: SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 Ga NIGER SAI SUYIWA WANNAN NUMBER MGN 84506476 Love and romantic story ba'a fara komai ba💃🏽🤙🏽 SARAUTA 👑 20/10/2021, 20:44 - 🤔🤔: &&&&&&&&&&& 2️⃣1️⃣-2️⃣2️⃣ "He made a very big mistake,wlh wlh billahi sai na sa masa dafin da zai gwamma ce bai aikata haka gareni ba,Ina da tabbacin bai san cewa nasan komai game dashi ba, shiyasa yake abinda yaga dama idan naso lokaci ɗaya zan iya wargatsa duk rayuwarsu but bana da ra'ayin hakan, Imam he's mine, he always be my side" Kallonta kawai Fariha tayi domin ta riga tasan wacece Saudat dukkan abinda tace zatai babu wanda ya isa ya hanata,idan harta sama ranta son abu babu shakka bata hqr dashi sai ta cimma buƙatar ta, bare ta daɗe da sanin cewa Saudat na ƙaunar ɗan nata "Tayaya zaki iya mu'amala da Uba da kuma Ɗa?". zama Mami tayi tare da ɗaukan yan kakkiyar Apple ɗin dake saman plate tace "kai! kema dai ban san cewa daƙiƙiyar ƙwaƙwalwa ce take ba sai yau,sam bakya jaa kamar bai brain ɗin kifi,kinfa san wacece Saudat kin san abinda zan iya da wanda bazan iya ba right? to ki daina mmki domin kaɗan daga cikin aikina kenan". jinjina kai Fariha tayi tace "Ba dai haka akaso ba wai ƙanin miji yafi miji kyau" Mami tace "A nan kuma Ɗan miji ne yafi miji kyau da kuma tsari ina son Imam so mai yawa bana iya control kai na idan ina kusa dashi,dat why ban fiya zama inda yake ba,amma abu guda keban mmki da Sheikh". idanun Fariha a kan wayarta tana ƙara duba bayanan da NIMCY ta tura mata tace "what?" Mami tai shiru kana kuma taja numfashi tace "kamar baya da lfy, za kiga sometimes nakan rungome sa da gayya amma baya nuna wani feelings a kaina" wata muguwar dry Fariha tayi tace "Ayi dai mugani idan tosa zata hura wuta". tsaki Mami taja domin taga sam Fariha bata ɗauki abin da muhimmanci ba, miƙewa Fariha tai tace. "i think am going now, Abban Taufiq ya kusa dawowa" Mami na taɓe baki tace "iska dai na wahalar da kayan ƙara,kiyi ta rawar jiki akan mutumin da bai damu da damuwarki ba". Murmushi Fariha tayi tace "To Mrs Hamdan zance? ko Mrs Imam zance ne? zan tafi sai mun haɗu wajan aiki" fari Mami tai tace "duk wanda kika kirani dashi is okey to me" daga nan sukai sallama da juna Fariha ta koma gidanta.. Numfashi ya kuma saukewa a karo na wajan uku kenan, Arjun dake driving kamar zai tashi sama ya juya ya kalli Sheikh yace "Buddy akwai abinda ke damunka,ban san mene matsayina da ba saka iya sharing all your feelings with me ba, ina da tabbacin bazan taɓa cutar dakai ba" tattausan Murmushi ya saki tare dayin baya ya ƙara shigewa jikin kujerar motar, slowly yaja fararen idanunsa mai ɗauke da blue eye balls ba tare kuma da yace wa Arjun komai ba yaja ba kinsa yay Shiru, haɗe fuska Arjun yay tare da dukan staring motar yace "Damn it, you're mad Arjun" idanunsa ya buɗe ya saukesu saman fuskar Arjun kana yasa hanunsa zuwa saman innocent face ɗinsa ya shafi sajensa,cikin ƙasa da murya kamar mai raɗa yace " Arjun the know what? Lot's of folks confuse bad management with destiny. Destiny is no matter of chance, it's a matter of choices, it's not a thing to be waiting for, it's a thing to be achieved. Our destiny changes with our thought, we shall become what we wish to become, do what we wish to do when our habitual thought corresponds with our desire. Be someone recognized for havinga beautiful heart so when you leave that memory of you lingers, Arjun soon or later you know everything da nake hading nasa, ka ɗauka abunda nake ɓoye maka wata sabuwar ƙaddarar Sheikh Imam hamdan Balarabe ne, i knew everything will be ok!" Ya ƙarasa mgnar yana taune leɓansa tare sauke ajjiyar zuciya mai ɗan ƙarfi, tunda ya fara mgn Arjun yake kallonsa wani murmushin takaici Arjun yay baice komai ba ya karya kan motar zuwa wani titin daban,kamar yadda Arjun bai mgn ba haka shima Sheikh bai mgn ba sai ma lumshe idanunsa yay a hankali ya fara Mutsa bakinsa ya shiga rera karatun Alkur'ani. Tunda suka shiga cikin Asibitin har suka zauna gaban likitan Sheikh bai ɗago kansa ba, Baƙin ciki da takaicin abinda Arjun yay masa ya hanashi ƙwaƙƙwaran mutsi, idanunsa sun kaɗa sunyi jaaa sbd damuwa, Dr ɗin ne yace "kun zauna a gabana babu wanda yay mgn" idanu Arjun ya ɗaga yasan da Dr yasan waye Sheikh ɗin da tuni ya nuna masa girmamawa,amma Sheikh bai damu sam daga ganshi ba,hasali ko hotonsa ya haramtawa media sawa, duk wanda ya san Sheikh sai dai ya sanshi ta zazzaƙar muryarsa, bayan ya gama wannan tunanin yace "Dr kai masa medical check-up" kallon Sheikh Dr yay yaga kansa a ƙasa mutum fari lafiyayye mai jiki ga kwarjini shi za'a ce za'ai wa medical check-up, koda yake daman masu kuɗin nan haka suke babu dama suji wani ciwo sai su tafi ganin likita,shi dai ko kaɗan bai ga alamun ciwo ga mutumin da ake mgn ba, gyara zaman glass ɗin sa yay yace "meke damunsa da Za'ai masa medical check-up?" Arjun kai tsaye yace "kawai muna buƙatar hakan,sbd rashin cikakkiyar lfy da rashin guzari da kwana biyu baya dasu" jinjina kai Dr yay yace "wannan bashi yake nuna bashi da lfy ba" kallon Dr Arjun yay yace "za kayi ne ko muje wani wajan?" Murmushi Dr yay yace "No! Zanyi as your wish" miƙewa Dr yay tare da danna wata belet cikin ƙaramin lokaci wasu likitocin guda biyu suka shigo, shima Arjun ya miƙe yace "bari na kaisa room ɗin" kafin Arjun yakai hanunsa Sheikh yay saurin faɗin "don't touch me Arjun Maleek Alhassan" gaban Arjun ne ya faɗi domin indai Sheikh ya kirasa da full name ɗinsa yasan ba ƙaramin bacin rai ya shiga ba, da sauri Arjun yace "why? Idan zaka iya jure ganin kanka a haka mu ba zamu iya ba,ya kamata kasan me kake kai ba yaro ba ne"shiru Sheikh yay sai huci kawai da yake fesarwa idanunsa ya jaa sosai duk jijiyoyin kansa sun fito saman goshinsa kamar zasu tsaga fatar jikinsa su fito,hannu Arjun ya ƙara kaiwa zai tura Wheelchair ɗin cikin ƙaraji da tsawa Sheikh yace "don't ever trying to touch me, hhhhh badai da lfy ta da komai kake son cin mutuncin na ba? Ba wani abu ba ne idan kace ka gaji da ɗawainiya dani,sam ba zanji haushinka ba bazan ɗauke matsayin mai laifi ba,domin iyayen da suka haifan ma sun gaji da kula dani bare kai da kake aboki na, just go leave me Arjun leave me alone,na gode da ƙaunarka thank you so much, ciwo ne bani na ɗorawa kai na ba kuma bani na zaɓi yadda za'a haifan ba" yana faɗin hakan ya danna abun dake jikin Wheelchair da sauri ya murza Wheelchair yana ƙara mata gudu, Dr ɗin ne ya kalli Arjun yace "Daman ba da saninsa za'ai masa ba?" Kasa mgn Arjun yay sai dafe kansa kawai da yay,mai taɓa ganin ɓacin ran Sheikh Irin haka ba,abinda ya ɗauka daban abinda shi kuma yake nufi daban, Dr ɗin ne ya ƙara faɗin "idan haka ne kayi kuskure,domin duk wanda akaiwa haka sai yay tunanin kamar ana zarginsa da wasu manyan cututtuka shiyasa aka kawosa nan domin a dubasa" waje Arjun ya fita Dr yay sauriju riƙe sa yace "kada ka bisa ya riga yay fushi da better ka rabu dashi a yanzu" hannun Dr Arjun ya zame yace "Dr please" yana faɗin hakan yay waje da gudu tsayawa yay a compound ɗin hospital ɗin ganin babu Sheikh babu labarinsa sosai tashin hankali ya bai yana akan fuskar Arjun da sauri kuma ya shiga mota yay mata reverse da wani irin speed yaja motar yabar cikin hospital ɗin... Barrister ya kalli ya kalli kawon Fannah da kuma mahaifin Baba Baa'na yace "Daman amincewar ku kawai nake jira na turo Magabata" kawo Modu yace "Wannan ba abin damuwa ba ne,mun gama bincike a kanka kamar yadda ka bada izini kuma mun yarda da dukkan nagartar ka, daga yanzu zuwa ko wanne lokaci sai ka turo iyayenka" Murmushin jin daɗi Barrister yay yace "Ngd Sosai Kawo Allah ya ƙara suttura" kawo yace "ba damuwa Allahu yasa Albarka a wannan haɗin" Barrister da Baba Baa'na sukace Ameen,daga nan Kawo ya miƙe tsaye sukai Sallama ya shiga gidansa dake gefen gidansu Fannah, Baba Baa'na miƙewa yay yace "bari na turo maka sai ana hqr,kasan ance ka haifi yaro baka haifi halinsa ba" Barrister baice domin yasan ko Fannah zata zagi uwarsa da ubansa babu abinda zai sanya ya janye mgnar aurenta,bare ƙiyayyar mace bata tasiri, Baba Baa'na kai tsaye cikin gidan ya shige a Parlour ya samu Mama kolo mahaifiyarsu Fannah ita da Yana zaune suna gyara ganyan ugun wanda zasuyi miya dashi,zama yay yana kallonsu Yana yace "Sannu Baba" yace "yawwa kiramin Faɗimatu" ajjiye zogalan tayi tare da shigewa cikin ɗakin su, a kwance ta samu Fannah tana sanye da wani farin lace mai kyau gashin kanta har wuyanta sai ƙamshi take ƙafafuwan ta har yanzu yana nan da jan lallen da baya barin fatarsu, idanunta a lumshe ta rungome pillow kunanta sanye da airpies tana sauraran tafsir wanda baya shigeta, kallo ɗaya Yana tayi mata ta ɗauke kai kafin tace "Kije Baba na kira" shiru Fannah tayi domin bata ta san me take cewa ba, cikin fushi Yana ta fisge wayar hannunta tace "Wlh kina wahalar da ganki a banza da wufi,wlh tallahi shima Mutumin nan bashi da aikin yi daya nace maki" Kallonta Fannah tayi kana ta ɗauke kanta wata light blue ɗin lafaya ta ɗauka kana ta ɗaura saman lace ɗin, cikin nutsuwa ta sanya flat shoe ta fito,a gaban iyayen nata ta zauna kamar ba zatai mgn ba sai kuma tace "Gani Baba" Kallonta Baba Baa'na yay yace "Sannu Faɗimatu, Allah yay maki albarka" kasa amsa masa tayi sai Mama kolo sa tace "Ameen" Baba Baa'na yace "maza jeki ana kiranki waje,biyayyar da kikai min kaɗai ta isa ki samu abinda kikeso a nan duniya da kuma lahira" tuni idanunta sun cika da hawaye domin harga Allah bata ƙaunar wannan mutumin ace mutum sa'an ubanta tsabar rashin tsoran Allah da kuma budurwar zuciyar da yake da ita yace zai auri ƴar cikinsa which can of selfish, bata iya ɗaga kai ta kalli mahaifin nata ba sbd zafi da raɗaɗin da zuciyarta take mata, runtsa idanunta tayi da ƙarfi ta shiga jan ajjiyar zuciya, sai da Mama kolo tace "kin bar Mutum a waje" gently ta miƙe tsaye tare dayin waje, a zaune ta samesa saman kujerar da aka kai masa, tsayawa tayi tare da ɗauke kai gefe guda, miƙewa tsaye yay yace "Haba Fatymerh babu ko gaisuwa??" Taɓe baki tayi tace "baka cancanci gaisuwar ba ai,kai fisabilillahi ko kunya bakajin ace ka auri ƴar cikinka" ta ƙare mgnar tana Jinjina kanta, kafin yay mgna wayarsa ya fara ringing, answering call ɗin yay,daga can ɓangaren Arjun yace "Abba ka dawo gida yanzu" da mmki Barrister yace "akan wane dalili mene ya faru Arjun" cikin damuwa Arjun yace "Abba! Sheikh missed bamu gansa ba" da ƙarfi Barrister yace "Sheikh!!" Calmly yay yace "kaga Arjun i knew you can handle it, ina abu very important so bazan iya dawowa ba" kasa mgn Arjun yay kawai ya kashe wayar, Fannah samun kanta tayi da kallon Barrister sbd sunan Sheikh da taji a ambata.. Arjun kasa komawa gida yay ga Granny harta fara kiransa a waya akan ina suka tsaya,ya gama zagaye amma ko alamar Sheikh bai gani ba,tashin hankalinsa guda Sheikh ba ƙafa ce dashi ba bare yace gida zai koma, rashin samun mafita yasa ya kira Abba, amma gashi yay burus da lamarin kamar bashi ne ya haifi ɗan a cikinsa ba, cikin ɓacin rai yaci gaba da driving motar... Sheikh na fita daga cikin ward ɗin kai tsaye can bayan Asibitin ya fara tafiya duk da cewa ba sanin kan Asibitin yay ba amma haka yaci gaba da tafiya sai da yace wajan mutuware inda yake da duhun jeji sosai sannan ya tsaya, lumshe idanunsa yay tare da fesar da wata zazzafar iska daga cikin bakinsa, a hankali kuma ya ɗura kansa saman cinyarsa,sosai zuciyarsa take masa zafi,mai Arjun ya ɗauke sa? Bashi da hankali ko kuma bai son ciwon kansa ba ne? Abinda yay masa kyautatawa ne ko kuma cin zarafi? Da lafiyarsa da komai zai kawo shi ai masa wani medical check-up,ko dan yaga bashi da ƙafar da zai taka yabar masa Asibitin shiyasa ya zaɓi kawosa ba tare da yay shawara dashi ba? Yasan Arjun mai son sa da kuma kaunar sa ne,amma mene yasa yay masa haka? Ko da gaske gajiya yay dashi shine yasa yay masa wannan wulaƙancin,ji yay wani zazzafan zazzaɓi ya fara rufesa a hankali jikinsa ya ɗauki rawa tare da ɓari ya shiga haɗe fararan haƙoransa, iska mai sanyin yaji ta fara kaɗawa hakan yasa ya ƙara lumshe idanunsa yana jin zuciyarsa duk babu daɗi, dafa shoulders akai yanayin zafin hannunta yasa ya fahimci itace,kasa ɗagowa yay sbd jin kansa yake kamar zai rabe gida biyu, zagayawa tayi cikin nutsuwa kana ta durƙoshe dai-dai wajan ƙafafuwansa hannunta tasa ta ɗago kansa, wata sassanyar ajjiyar zuciya ya sauke da jajayen idanunsa ya shiga Kallonta idanunta ta janye sbd yanayin da tagansa ya ƙara tabbatar mata da cewa zuciyarsa sam babu daɗi,can ƙasa dai-dai kunnansa tace "Arjun..?" Kasa bata amsa yay sai jawota da yay kusa dashi ya ɗura kansa a saman wuyanta,shafa sumar kansa tayi tace "me yasa to?shi dole sai ya san abinda bashi da iko akai? Why Arjun yake maka haka?ina ɗaga masa ƙafa dalilinka amma baya fahimta, wlh idan akan ka ne zan iya yiwa kowa rashin kirki,babu wanda ya damu dakai sai dai kai ka damu da wani, what is this? Idan yana taƙamar yana taimaka ne ,sai ya basshi zan iya maka dukkan abinda yake maka" Girgiza mata kai yay tare da fashewa da kuka bakinsa har rawa yake ya shiga faɗin "No! Kada ki masa komai, Arjun he's my Best friend,Kada kiyi masa wani abu just let him go" ya ƙarasa mgnar yana rungome ta sosai a jikinsa ya shiga fesar da numfashi,abinda bai taɓa yi ba kenan a hankali ya ɗaga kansa tare da tallafo haɓarta slowly ya ɗura soft lips ɗinsa saman nata Muryarsa can ƙasa yace "Sorry!" Yana faɗin hakan ya datse bakinsa a cikin nata, lokacin da yay trying na kissing nata sai yaji kansa ya tsara da sauri ya zare bakinsa ya shiga faɗin dukkan addu'ar da yazo bakinsa, idanunsa na zubar da hawayen baƙin ciki yace "ki ɗauke ni, ki tafi dani Please Ai..rahh,go with me Airah hhh.. *SIRRIN MU na kuɗi ne, if you need my book just it's v #500 via👉🏾0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger kuma sai suyi mgn ta wannan number 84506476* NIMCYLUV✍🏾 20/10/2021, 20:44 - 🤔🤔: SUBSCRIBE MY YOUTUBE CHANNEL *Nimcyluv T.V* https://youtube.com/channel/UClywbagpRx5qlVyOy0ZPPDA ########## 2️⃣3️⃣-2️⃣4️⃣ Ya ƙare maganar yana langwaɓar da kansa a saman wuyanta,ganin yadda duk ya shagwaɓe yasa ta saki murmushin jin daɗi domin farin ciki ƙarara ya bai yana a saman fuskarta. Zame kansa tayi daga wuyanta tana faɗin "take it easy, nasan Arjun bai maka haka dan yaci zarafin ka ba right? Then kafi kowa sanin soyayyyar da Arjun yake maka all this ya nayi ne domin lafiyar ka" Lumshe idanunsa yay yana ɗan matsa hannunta, kasa ce mata komai yay duk da cewa ya fahimci so take yay mgn but he can't say anything sam baya jin daɗin zuciyarsa. Zame hannunta tayi tace "da alama dai Sheikh ya manta harin da aka kawo masa last year a mosque ranar idin babbar sallah, da alama Rayuwata ya manta tuggun da aka haɗa masa na sace masa tayar mota, da alamar farin cikina ya manta maid ɗin data sanya masa poison a cikin abincin ka, gaba ɗaya wannan bai isa ka gane cewa Arjun domin lafiyarka yake wannan abun ba?". Da Mmki yake sauraran dukkan abinda take faɗa masa,idanunsa a rufe amma bai hana ta gane cewa yana mmkin maganganun data faɗa masa ba, tayaya tasan wannan abubuwan da yake ɓoyewa? Yes! Yasan maid ta sanya masa poison a abinci amma ko Abbansa bai san da wannan mgnar ba daga shi sai Arjun suka sani kuma suka ɓoye mgnar,kawai yaywa Abbansa bayani akan yana son zuwa waje ya huta! shine shida Arjun suka bar ƙasar gaba ɗaya a can yay jinyar poison ɗin daya sha. Numfashi ya sauke yana tuna abubuwan da suka faro a baya wanda suke dawo masa cikin kansa kamar yanzu komai ke faruwa. Ganin yadda take ta surutu ko tsayawa ba tayi yasa shi saurin kama hannunta yace "Enough please okay!" Gira ta ɗaga masa tace "should I go with you or gida zaka?" Ɓata fuska yay yana ɗan taune bakinsa yace "just go with me... Fannah dake tsaye kan Barrister kamar an dasa ta ko zama ta gagarayi sbd ɗacin da zuciyarta take mata, ji take inama tai ta zabga ihu ko hakan zai sanya iyayenta su fahimci halin da yake ciki,wlh da Auren wannan suger Dad ɗin ita kam gwamma mutuwar ta. Miƙewa Barrister yay yana sakin lallausan murmushi yace "zan tafi amma zan dawo zuwa dare before na koma Abuja" banza tai masa ko ajikinsa bai wani damu ba saima wani kallo da yake binta da shi na zagi gane baki da wayo, hannu ya miƙa zai kama nata hannun da sauri ta juya tare da shigewa cikin gida,da Murmushi kawai ya bita kana ya juya zuwa inda yay parking motarsa slowly ya dinga tafiya kai kace wani saurayi ne wanda bazai huce shekara 30 ɗin nan ba, da haka ya shiga mota zuwa hotel ɗin da ya sauka. Fannah baƙin ciki da kuma takaicin tsayawa da Barrister yasa tun daga ƙofar shiga parlon nasu ta saki kuka bai taɓa zuciya bata taɓa tunanin auren sa'an ubanta zai zama ƙaddarar ta ba, sanin cewa idan tai kuka mai yawa kanta zai iya yi mata ciwo kuma iyayenta zasu fahimci bata aminci da zaɓin da sukai mata ba yasa ta share hawayen ta,banda sakin ajjiyar zuciya babu abinda take, a sanyaye kuma ta ɗaga labulan parlon bakinta ɗauke da sallama Murya kuma can ƙasa, Falta da Mama kolo mahaifiyarsu ne kawai zaune a parlon suna duba wasu new designer furniture a wayar Falta, kallo ɗaya Mama kolo taiwa Autar ta ta, Falta kam da ido ta bita har zuwa cikin uwar ɗaki, miƙewa tsaye tayi tace "Mama am coming" ko Kallonta Mama kolo ba tayi ba taci gaba da duba abinda take nema, kwance ta samu Fannah sai sakin ajjiyar zuciya take kana ganinta kasan bata cikin nutsuwarta dauriya kawai take, zama tayi gefen gadon tace. "Aiye ye" (Yadai) Shiru Fannah tai mata Murmushi kawai Falta tayi domin tasan halin ƙanwar tasu bata fiya son takura ba, ita kanta bata son wannan Auren,amma wanene ya san abinda gaba zata haifar? Allah kaɗai yasan abinda wannan auren yake nufi da kuma abinda yake ɓoye a cikinsa,banda haka tayaya wannan ƙaton mutumin zai kalli Fannah yace ita ya keso?? Bayan gasu duk a gidan babu auren koda yake ance komai lokaci ne, shi kuma aure kamar layin malkaɗe ne idan ka kai ko kana wajan ko baka wajan tabbas zai zo kanka, ajjiyar zuciya ta sauke tace. "Chi'ne" (Tashi). A sanyaye Fannah ta miƙe tana kallon yayar ta, Falta tace "Ayi wazo" (Mene ya faru) girgiza mata kai kawai Fannah tayi idanunta na ƙara kawo ruwa sbd bata san mene za tace a yanzu ba,bata da ikon da zata buɗe baki tace bata son auren ko kuma tace Barrister bai mata ba,tunda ta riga ta aminci da magnar Baba Baa'na tun farko kawonta ma daya tambayeta ta tace masa ta amince so dan haka dole ta auro jarumta nutsuwa ta sanyawa zuciyarta. Hannunta Falta ta kama tare da faɗin "look! dear kin san iyayenmu baza su taɓa zaɓa maki abinda zai Cutar dake da hankalinsu da komai ba ko?" Ɗaga kai kawai Fannah tayi tana jan numfashi "so You don't have to be worry about that, Aure ai ibada ce ko wanda ka aura kana so sai kiga kun samu saɓani dashi ya dinga nuna maki rashin daraja kala-kala, wanda kuma ka aura baka so ya wanci anfi samun kwanciyar hankali da su,so kiyi addu'a neman zaɓin Allah tare istikaara, nasan zaki samu sauƙi a ranki". A hankali Fannah tace "Nagode Yaa Falta" kanta ta shafa tace "it's my pleasure ƴar ƙanwata,keda kikaci sa'a kowa yana sonki a dangi ma,babu wanda zai bari aci uwarki yay shiru dan haka ki sake ki daina sanya damuwa a ranki domin bata magani just pray". ɗaga kai Fannah tayi itama Ya Falta miƙewa tayi tana faɗin "kije kiyi wanka kici abinci zamu gidan Anty Yakura,daga nan zamu huce gidan kawo Modu" tana faɗin hakan ta fita a ɗakin itama Fannah ta miƙe tsaye tare da fara cire kayan ta, a gaban mirror ta tsaya tana kallon surar jikinta wai ace duk wannan baiwar da Ubangiji yay mata tsuhu ne zai mureta? Ita kam an gama da ita wlh, hawaye taji ya kawo idanunta da sauri ta share hawayen ta domin ta ɗauki niyyar auren kuma ko dawa yake tafe ba zata taɓa amincewa dashi ba.... Zaune yake a gefen wata ƙorama dake guda na, time to time ya kan lumshe idanunsa shi kansa bazai ce ga inda yake ba, waje ne kamar jeji amma bashi da duhu sosai ga wata daddaɗar iska dake kaɗa ƙwantaccen gashin ƙirjinsa wanda ya bai yana sakamakon rigar jikinsa da Airah ta cire masa. Gajiyayyun idanunsa wanda suke a ɗan lumshe ya sauke a kanta tana cikin ruwan tana wanka sai dry take masa tare da watsa masa ruwan, ya kanɗan murmusa bakinsa sbd sha'awar data bashi, sai ta ƙara zama ƙaramar yarinya a idanunsa, Ta ɗaure ƙirjinta da wani farin yadi haka ma waist ɗinta, ajjiyar zuciya ya sauke ya shiga shafa ƙirjinsa zuwa wajan red nipples ɗinsa wanda suke da ɗan tsini sakamakon brest ɗinsa da yake da girma, Murza Wheelchair ɗin ya fara har zuwa gaɓar ƙoramar cikin nutsuwa ya zura dugwaye fararen ƙafafuwan sa cikin ruwan, sanyi da kuma daɗin ruwan da yaji yasa ya ɗan saki wani sound mai daɗi, kallonsa Airah tayi tace "the you like it?" Juya idanu yay kamar bazai magana ba can ƙasa a taushashe yace "Yeah! Wajan very beautiful" "Olright get down" ta faɗa tana kama hannunsa tare da jawosa jikinta a hankali ta zamesa daga saman wheelchair zuwa ƙasa gefen ruwan gaba ɗaya ruwan ya kawo masa sama har wajan waist ɗinsa, haɗa ido sukai ya kwaɓe fuska yana ɗan lumshe idanunsa cikin ƙasa da murya yace "kayana" da ido tai masa mgna "meye samesu?" Shima da ido yay mata nuni da jiƙewar da wandon jikinsa yay, dry tai masa sbd ta lura yana da ƙyanƙyami bai son abu mai danshi, hannunsa ta kama ta ɗura a kanta ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa ta fara zame masa wandon jikinsa, tana gamawa ta miƙe tare da nufar wajan data ajjiye nata kayan ta shanya masa su, ƙafafuwansa ya fara wasa dasu a ruwan yana jin wani farin ciki yana lulluɓe sa, gaba ɗaya damuwar dake zuciyarsa wacce Arjun ya sanya masa ta kau, wasai ya kejin zuciyarsa,yana ta zaune babu Airah hakan yasa ya juya yana kallon wajan da yaji kamar tafiyar abu, ƙatuwar mesa ya gani zabgegiyar gske sai juyi take a saman ciyayin wajan,ware idanunsa yay domin ya tabbatar da cewa Airah ce wannan mesar ganin yadda mesar ke juyi tana cikurkuɗewa waje guda yasa ya zare ƙafafuwansa daga cikin ruwan kamar yaro mai rarrafe haka ya dinga jan jikinsa zuwa wajan mesar, yana zuwa mesar tayo kansa tare da nan naɗesa ciff ta kwantar da kanta a saitin ƙirjinsa tai lamo sai fasa kai take, Sheikh samun kansa yay da Mutsa ba kinsa ya shiga yin addu'a cikin nutsuwa yana tofa mata a kanta zuwa jikinta, well yana shafa kanta da hannayensa, almost 5minutes suna haka kafin jikin mesar ya ɗauki rawa iska ta fara kaɗawa lumshe idanunsa Sheikh yay bayan iskar ta lafa ya ware manyan idanunsa yaga tuni mesar ta koma AIRAH tana kwance jikinsa sai rawar sanyi take, ga jikinta daya ɗauki zafi a rikice ya kalleta yana ɗago kanta daga jikinsa muryarsa bata fita sosai yace "Fairy..na! what..what wrong with you?" Girgiza masa kai tayi tace "babu komai kawai sanyi na keji" kanta ya shafa yace "okey! Just hug me nothing will happen in sha Allah!" Ya faɗa yana rufe ta da faffaɗan ƙirjinsa tare da ɗura kansa a saman wuyanta, riƙesa tayi sosai sbd wani sihirtaccen ƙamshi haɗi da ɗumi dake ratsa jikinta. Ringing ɗin farko Arjun yay answering call ɗin da Granny take masa yana mannawa a saman kunnen sa tace "Haba Ranjun? Haka ake rayuwa fisabilillahi? To nidai babu ruwana ka daina ganin kai abokin sa ne ko ubansa bai isa ya taɓa Imamu na zuba masa ido sasakai yay abinda yaga dama ba, haƙƙi nama kaɗai ya isheka bare na yaron da baiji ba bai gani ba,ka ɗauke sa kuyita gantali a titi babu tsaro ba komai wannan lokaci na ƴan kidnama da ƴan dama,yaro ko furar da yake sha ta yamma bai shafa ba ina nan nai tsoru kamar dai wata nunafa,alhalin babu wanda naiwa munafurci,rabuna dashi tun ina yarinya". Shiru Arjun yay yama rasa ta ina zai fara yiwa Granny bayani jin yay shiru yasa ta fara matsar ƙwalla tana share hanci tace "Nidai ka gayamin gsky kada kaji komai ai tsautsayi ne ko ba hk ba?". Sauke numfashi Arjun yay kafin ya share zufar dake karyo masa yace "No! Granny baki fahimta ba" cikin fusata tace "wlh kuma bazan fahimta ba, rabona da ganewa tun a makarantar allo, nidai kawai ka dawo min da jikana idan ba haka yasin polis zan kai ka". Daga can ɓangaren Arjun ya kalli wajan da yake yace "Look! Granny he's fine fa, muna tare da shi wajan Ummi but yanzu zamu dawo gida ai". Tace "Ah to! Haka dai yafi daman na san ba inda zaka kai shi ai, to yaya Sadia?" Yana shafa kansa yace "tana lfy,tana ma gaisheki" yana faɗin hakan ya kashe wayar bai tsaya yaji mene za tace masa ba. Abun kamar wasa zazzaɓi mai zafi ya rufe AIRAH jikinta sai rawa yake Sheikh kam bai taɓa ganin ciwon aljanu ba sai yay ta Mmki daman Aljanu na cuta,gaba ɗaya ya manta shi malami ne bare ya samu amsar tambayarsa a cikin karatun da yake na yau da gobe, suna nan zaune saman ciyayi ta ƙanƙame sa shima gaba ɗaya yay covering ɗinta da ƙirjinsa bai san ta ina zai fara ba, bai san tayaya zai taimake ta, idanunsa da yake a lumshe ya buɗe yana ƙarewa ƙyakkyawar fuskarta kallo a hankali kuma ya sanya hannunsa ya shafi fuskarta idanunta ta buɗe da ƙyar ta kallesa cikin dauriya kuma ta sakar masa Murmushi, fuska ya kwaɓe bakinsa dai-dai kunanta yace "how do you feel now?" Shiru tai masa sbd ita kaɗai tasan zafi da ciwo da kuma raɗaɗin da zuciyarta take mata, hannunta na rawa ta kama hannunsa tare da ɗurawa a saitin zuciyarta wacce take bugawa da ƙarfi, runtsa idanunsa yay sbd tudun brest ɗinta da yaji,a hankali kuma ya haɗe hannayensa ba tare da tunanin wani abun ba, ƴar ƙara kaɗan ta saki sai lokacin ya lura ashe brest ɗin nata ya matse, kamar mai shirin taɓa wuta haka yake ƙoƙarin zame hannunsa ita kuma tana ƙara matse hannayensa, muryarta na rawa tace "please just for your love" kasa ce mata komai yay sai cikin idanunta daya ke kallo wanda ya ɗan sauya launi kana kallo kasan eyes ball ɗin ta ba nrml yake irin na mutane ba,sai a lokacin ya shiga ƙare mata kallo ya shiga haddace surar jikinta, wannan surar a zahirance haka take? Ko kuma kawai ta samawa kanta surar mutane ne bawai ai hana yin ta ta bace? AIRAH jin ya tsaya yasa ta yun ƙura a hankali, tare da fakar idanunsa tasa dukkan hannayenta ta hankaɗa sa baya tabi bayansa ta kwanta saman fresh skin ɗinsa wacce take a bai ya ne daga shi sai boxers domin hatta farar singlet ɗin dake jikinsa ta cireta,kasa mutsawa Sheikh yay sbd sassanyar isakar dake kaɗawa a wajan ga wani hadari daya haɗu lokaci guda duk sai ya firgici, domin babu abinda yake tsoro sama da ruwan sama musamman idan yaji ana tsayawa, yanzu ma da yaga anyi wata walƙiya yay saurin tura kansa tsakanin wuyanta yana sauke numfashi... Yana ce ta kalli Fannah tace "tunda muka dawo ki tarar da Mutumin nan yana jiranki amma kike zaune ko?" Kamar Fannah zatai kuka cikin sangarta irin tasu da Auta ƙarshen haihuwa tace "Nifa Tafsir na keji kuma kina kallon ruwan za'ai,ni tsoran ruwan sama nake" Mama kolo dake zaune tana turara kayan baccinta tace "Auta kada ki sake na ƙara yi maki mgna, kije ko gaisawa kuyi saiki dawo tunda naga garin kamar ruwa za'ai" miƙewa Fannah tayi tana turo baki gaba dan dai kawai bata taɓa yiwa mahaifiyarta musu ba ne da wlh babu inda zata, babban hijab ta ɗauka ta zura ya sauka har ƙasa, zaune ta samesa a cikin motarsa da waya a hannu yana operating nata, tun kafin ta iso wajan jikinsa ya sanar masa da zuwanta, wata Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke fuskarsa ɗauke da Murmushi yace "Wlcm Beauty" ɓata fuska tayi a hankali tace "Ina wuni" faɗaɗa fuskarsa yay yace "Allahamdulillah kin wuni lfy?" Shiru tayi bata bashi amsa ba sbd haushin da yake bata yace "gobe za'a kawo kayan na gani ina so" gabanta ne ya faɗi har sai da ta runtse ido, idanunta data rufe ya bashi damar kallon innocent face ɗinta, kansa ya ɗauke yace "So the you love me?" Cikin sanyin murya Fannah tace. "Nyiro dolero lorosande kadanine gulg3n ba, amma awodone gyiye rama asu wallahi soro fandumba saide chuntun rumin, knum adu karu`u jiliyi Allahyi nyiroci nong3yi. Amma nonedea lurusande de namgam kaddaru yelan kara wa nyande soro, Tawadu fannummo gakin su kamummen amma wllh k3jiram lurusa adeya fanumba" da Hausa kuma shine; (Bazan maka dole akan cewa ka hqr da aure ne ba,amma abinda kake so kuma kake muradi wallahi Allah sai dai ka gani daga nesa,ban san wacce irin Zuciya Allah ya baka ba, Amma ka ɗauka Auren na da zakai dani dakai duka zai zama ƙaddarar mu,gidanka zan shiga tabbas matsayin matarka amma wlh baza ka taɓa jin daɗin Wannan Auren ba"). Tana faɗin hakan ta shige cikin gida idanunta cike da hawaye, ka faɗa Barrister ya ɗaga irin i don't care ɗin nan kafin ya shige motarsa ya koma hotel dan ya ɗauki niyyar bazai bar garin ba sai an kai kayan na gani ina so yana komawa kuma zai je wajan Uncle ɗin Sheikh su kai masa kayan sa rana. Granny ce ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da yankakkun fruits, Mami dake parlo ta ɗura ƙafa ɗaya kan ɗaya tace "Wai son lfy kuwa?" Sarai Granny ta gane da ita take ta ɗauke kai da Mami tace "Mama!" Tsayawa tayi tace "Magana kike?" Danne zuciyarta ta tayi tana sakin murmushi tace "Daman Sheikh naji shiru tunda na dawo ban gansa ba" Granny na taɓe baki tace "to wacce uwar zaki basa Saudala? Fisabilillahi nifa wannan abun son zuciya ne wlh babu ruwana da neman mgna irin taki, Yaushe kika damu da Imamu har kike tambayarsa?" Shiru Mami tayi bata ƙara magana ba ta maida kallonta zuwa ga film da take kallo a zee world mai suna This is fate. Granny na tafe tana sababin Faɗa ita ɗaya a haka harta isa flat ɗin Sheikh, a fridge ɗinsa ta sanya masa tana faɗin "ko zuwa dare koka dawo ka sha nidai bacci na keji, shima Ranjun Bana da labarin sanda ya zama gantalalle ta ban bari ya tafi min da jika ba,kuma zan nemi Sadia naji yaushe ta sallama Ranjun bana da labari?" Bayan ta ajjiye plate ɗin fruits ɗin a cikin fridge harta yi waje sai ta dawo baya tana faɗin "bari dai na duba cikin ɗakin idan da inda za'a kakkaɓe to" tana buɗe ƙofar bedroom ɗin tai saurin sakin labulan jikinta ya ɗauki rawa kafin wani lokaci sai ga fitsari yana bin ƙafar Granny... Sirrin mu isn't free,you read for free🤷🏾‍♀️.. It's #500 via... 0116886423 sulaiman Na'ima s union bank evidence ga Niger 84506476.. Show evidence via WhatsApp 08119237616.... 20/10/2021, 20:44 - 🤔🤔: $$$$$2️⃣5️⃣-2️⃣6️⃣ Kwance ta samu Sheikh Imam hamdan Balarabe yana bacci a saman gadonsa, ga wata ƙatuwar mesa dake gefen sa ta naɗe sa ciff sai ɗaga kai take sama,ganin hakan da tayi yasa ta saki ihu ta tsorata ainun. Da sauri kuma Sheikh ya buɗe idanunsa yana sauke ajjiyar zuciya, juyawa yay gefensa yaga babu Airah babu dalilinta idanunsa yaja ya rufe tunawa da ko sallar magrib bai ba yasa ya yunƙura kaɗan tare da jingina da frame ɗin gadon. Mami dake Parlo ta miƙe da sauri ta nufi flat ɗin Sheikh inda yake jiyo ihun Granny, a tsaye ta sameta jikinta duk rawa yake ga fitsarin daya ƙwace mata yana zarya a tsakanin cinyoyinta. Da Mmki Mami ke binta kafin tace "lafiya dai?" Kuka Granny tasa tace "inafa lfy fisabilillahi!? Wacce lukutar masifa Imam ke shirin jawowa kansa ne ni Faɗimatu" Mami tace "Kamarya Mama ni ban gane ba" Granny tace "ba yanzu na gama gantali a gidan nan ina igiyar sa ba, lungu da saƙo babu inda ban laluba sbd rayuwar babu gsky kana zaune da mutum amma baka san zuciyarsa ba, to dai duk gantalalin da nake ashe yana ɗakinsa yana bacci,kuma...kuma" sai tai shiru ta kasa ƙarasa faɗar abinda tayi niyyar faɗa sbd tsoron daya gama cika zuciyarta. Mami bata ƙara magana ba tabi gefen Granny inda take tsaye a doorway tana sharce majina, zaune ta samesa ya lumshe idanunsa yana shafa sumar kansa,zama tayi a hankali tace "Sweet" slowly ya buɗe fararen idanunsa masu kyau da ɗaukar hankali ya sauke a kanta, murmushi ta sakar masa tana kama hannunsa tace "ka tayar mana da hankali, tun ɗazo ashe kana ɗaki abinka, at least ko fitowa Parlo kayi ko?". Ajjiyar zuciya ya sauke kafin yace "Mami,Granny fa?" Kansa ta shafa tace "what the you what?" Kwaɓe fuska yay yace "i wanted to taken a shower" miƙewa tace "ok lemme help you sweet" ta faɗi hakan tana shigewa cikin bathroom ɗin nasa warm water ta haɗa masa a cikin jacuzzi tare da ajjiye masa dukkan abinda zai buƙata, fitowa tayi lokacin tuni ya cire troser dake jikinsa daga shi sai boxers zaune ta samesa akan Wheelchair yana jiran fitowar ta, not too long ta fito fuskarta ɗauke da Murmushi tana girgiza jiki, ɗauke kai yana duban agogon ɗakin nasa. Saukar hannunta a saman ƙirjinsa yasa yay saurin kallonta ido ta lumshe hannunta ya zame daga ƙirjinsa da take shafa ƙwantaccen gashin sa, kasa ce masa komai tayi kamar yadda ya ɗauke kansa yana tunanin sabon halin da step mother ɗin tasa ta sauya. Da sauri ta turasa zuwa cikin bathroom ɗin har gefen jacuzzie inda ta tabbatar zai iya sauka da kansa da sauri ta fice daga cikin bedroom tana haɗa hanya, a Parlo ta samu Granny tai jigum kamar mai takaba. Tana zuwa flat ɗinta bathroom ta shige tare da zame kayan jikinta har zuwa pad ɗin jikinta ta zare cije baki tayi sbd ruwan data gani kwance saman wandon, sai yanzu ta ƙara tabbatar da ƙarfin so da kuma sha'awar data kewa Sheikh yaya zatai yanzu? Me zatai ta mallakesa tana jin ta kusa yin abun kunya soon, domin ba zata jure zama inda Sheikh yake ba,ko raɓarsa tayi sai taji ƙasanta na rawa komai ya kunce mata dole kota halin yaya ta mallaki Sheikh ya zama nata ita ɗaya bata jin zata iya hqr dashi, wanka tayi tare gyara kanta ta sauya kaya zuwa wasu blue nightwear masu kyau, tana sane da cewa Barrister baya nan sarai amma hakan bazai hana ta fasa abinda tayi niyya ba, miƙewa tayi ta nufi gaban dressing mirror ɗinta ta shiga fesawa jikinta parfumes masu ƙamshi, sweet tasa a bakinta ta shiga tsotsa tana imagine yadda zataiwa hjyar Sheikh, da sauri kuma ta sanya hijab tai waje a Parlo ta samu Granny ita da Sheikh da kuma Arjun suna Shira ƙasa², Sheikh yana sanye da fararen kayan bacci masu kyau rigar half ce wadon kuma ina laps ɗinsa ya tsaya fararen cinyoyinsa suka bai yana wanda suke ɗauke da gargasa sunyi kwance lubb saman fatarsa, hannunsa riƙe da plate ɗin Apple yana sha a hankali gaba ɗaya tunaninsa yana ga Airah su yake yasan halin da take ciki amma no way, Arjun duk yadda yasu su haɗa ido da Sheikh kasawa yay da sun haɗa ido sai yaji nauyi da kuma kwarjin Sheikh sun cika masa ido bisa dole yaja bakinsa yay shiru ba tare daya tambayesa inda yaje ba, Granny ba tunani ne fal ranta jin abinda Arjun yace sun dawo tana bacci shiyasa hata san da dawowarsu ba yasa taji hankalinta ya ɗan kwanta ba kamar da ba, miƙewa Arjun yay yace "Granny sai da safe" Granny tana kallonsa tace "To Allah dai ya tashe mu lfy,amma kada ko ƙara nisa da gida" yace "In sha Allah! Gobe ma za'a kai lefe nasan zaki ko?" Haɓa ta riƙe tace "Yanzu da gske dai auren zakai ashe? Nifa na ɗauka ƙarya ce kawai to Allah yasa Imamu a dan shinka" yace "Ameen Granny sai kizo da safe kiga lefan kafin akai gidansu Aliyah domin maza ne zasu kai" baki ta taɓe tace "Allah dai yay wadaran wanda suka tsiro da wannan iya shegen, mutane dai duk sun zubar da al'adar su ace wai lefen maza ne zasu kai? To wlh ada a kwalla ake kai lefen atamfa guda ɗaya zuwa biyu aka cilla sun isa,sai kaga mata hamsin sunje kai lefe,amma yanzu sake zamani ne sai ace wai ƙauyen ci ne" Murmushi kawai yay yace "sai dai kinzo" ya faɗa idanunsa akan Sheikh yace "Gud night buddy" idanunsa ya ɗaga ya kalli Arjun ya ɗan sakar masa Murmushi yace "Olright Tasbahii alaa khaaiir" yana faɗin hakan ya sunkuyar da kansa yaci gaba da shan fruits ɗinsa, wajan fridge Mami ta nufa ta ɗauki malt mai sanyi tasha, hamma Granny tayi tace "to nidai kada a shiga haƙƙin idanu bacci na keji" miƙa mata plate ɗin hannunsa yay yace "You can go" ta ware ido tace "me kace?" Shafa kai yay yace "nace ruwa zan sha" tace "Au to" fridge taje ta ɗauko masa gorar ruwa mai sanyi ta ɓalle murfin ta bashi tace "muje na kai ka nikam na kaji da wannan sallamar ace sai sha biyu mutum zai bacci kai ba aure ba komai ba" hannunta ya riƙe yana ɗan sakin sound yace "No! Zanje da kai na" "ka tabbatar?" Yace "sure" Duk da bata san mene yace ba amma tana da tabbacin amsa ya bata, kansa ta shafa tare da ɗura tafin hannunta a saman kansa ta shiga yi masa addu'ar data saba shi kuma yana Lumshe idanunsa, tana gamawa ta shafa masa har fuskarsa tace "ka kula" yana sumbatar hanuntu yace "in sha Allah, jazakillah bilkhair Masoyiya" baccin da take ji yasa bata ƙara yin mgna ba tai flat ɗinta. Lumshe idanunsa tare da miƙar da ƙafafuwansa a saman Sofa bacci yaji yana fisgarsa yana ta tunanin why Airah bata zo ba? Ganin yadda yake rufe ido yasa miƙewa tace "sweet bacci ko?" Kai ya ɗaga mata kamar ƙaramin yaro yace "Yeah!" Wheelchair ɗin ta ɗauko tare da gyara ta zata taɓa sa yay saurin cewa "No! Thank you" da kansa ya hau kujerar ita kuma ta tura masa zuwa cikin flat ɗinsa kwanciya yay bayan yayi addu'a yaja duvet zuwa waist ɗinsa,kallon Mami dake zaune gefensa yay yace "Mami what wrong?" Marai-raice fuska tayi tace "Sweet ban san yadda zan faɗa maka ba,amma Mahaifinka baya kyauta min" gaba ɗaya attention ɗinsa ya bata yana ƙara ware idanunsa yace "ban gane ba,me Abba yay?" Hawaye ta goge tace "kaga yana kwana a gidan nan yanzu" girgiza mata kai yay yace "A'a" tace "good to Aure zai ƙara soon" manyan idanunsa ya buɗe sosai a kanta tace "Zai ƙara Aure ban san dalilinsa na yin hakan ba, nace idan akan kula dakai ne na hqr da aikina zan zauna dakai,nasan a baya nayi kuskure rashin ko in kula da nake baka, amma yanzu na gane baka da uwar sata huce ni koda ba haka bane a gareka,Ni step mother ɗinka ce,ina maka kallon Ɗa kuma abaki na tunda zanyi sharing all my feelings to you, dole zan gaya maka abinda yake faruwa Rabon da Abbanka yay tarayya dani na manta, baya damuwa da damuwata bare yay min maganinta,ina da lafiya ni lafiyayya ce a koda yaushe zan iya buƙatar mijina,nasan kai ba yaro bane Sheikh kasan irin wannan problems wasu ma kana solving nasu, me Barrister yake nema dani? So yake naje na nemi maza ko kuma so yake na dunga biyawa kai na buƙata da kai na? Am tied na gaji am sorry but na gaji da halin mahaifinka" ta ƙare maganar tana sakin kukan munafurci. Shiru Sheikh yay yama rasa mene zai ce tabbas hqrin mace iya wata huɗu ne ko Namiji zai tafiya ba'a son ya huce wannan watannin amma shi Abba meye dalilinsa na yin aure? Ko kuma danshi zai auren da sauri yace "i need to talk to Abba right now" tana sakin ajjiyar zcy tace "bazai picking call ɗin ba wani time ɗin ma wayar a kashe za kaji ta, wlh sweet na gaji ina buƙatar mijina na gaji ko kuma na tafi gidanmu" ta ƙare mgnar tana kifa kanta a ƙirjinsa ta shiga rera kuka kai ka ɗauka kukan har zuci take yinsa, shiru yay yana ɗan buga bayan ta domin she's like mother to him koda bata kula da shi amma hakan bazai hana ya bari aci zarafinta ba, ajjiyar zuciya ta sauke tace "Ina sonka Sheikh dalilinka kawai nake zaune a gidan nan banda haka ta tuni nabarsa" ta faɗa tana rungomesa a jikinta ko kusa bai kawo wani abu a ransa ba hakan yasa shima ya rungome ta sosai a jikinsa tana faɗin "it's okay everything will be fine" lumshe idanunta tayi sbd farin ciki data ke ciki, cikin sauƙi zata mallaki Sheikh ya zama nata har abada zata nunawa Barrister kalan nata barikin tunda hakan ya zaɓa. _Habibaties littafin kuɗi ne ki biya kafin ki karanta_ Kanta ta ɗaga da sauri taga ya lumshe idanunsa cikin ranta take faɗin Am sorry Sheikh, ruwan da kasha ɗazo akwai maganin bacci ciki dana sanya a cikin allura na zuba a ruwa nasan ruwanka ne kuma tabbas zaka sha sbd babu wanda yake shan kalar ruwan a gidan sai kai, ganin sosai bacci ya ɗauke sa yasa ta ɗan bubbuga shoulders ɗinsa tana faɗin "Sweet! Sweet!" Ko mutsi bai yi ba da sauri ta miƙe tare da sanyawa Ƙofar key ta kashe hasken ɗakin ta dawo inda yake kwance, da sauri jikinta yana rawa ta cire hijab ɗin jikinta tare da zame rigar jikinta manyan booms ɗinta suka baiyana, gefensa ta samu ta kwanta tare da kama hannunsa ta ɗura saman booms ɗinta a hankali tace "Suck them Imam,ka taɓa su, suck my nippy it's all yours,na ka ne bana Ubanka ba, matse su Sweet" ta ƙare mgnar tana haɗe hannayensa a saman booms ɗinsa dukkan abinda take bai sani ba bacci kawai yake hankali kwance, ganin tana wasting time ɗinta yasa da sauri ta miƙa hannunta ta zame boxers ɗinsa kusan suman zaune tayi a kuɗi me tace "Ohhh..oh my goodness, dukkan wannan abun a jikanka sweet? Can you imagine ace a jikina take" gaba ɗaya Mami ta rikice tama rasa mene za tace girma da tsayin Sheikh ɗin ya gama firgitar da ita jikinta na rawa ta kama tare da tura ta gaba ɗaya a cikin bakinta... Sirrin mu isn't free, you read for free🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️ It's 500 via...0116886423 sulaiman Naima s union bank, ga ƴan Niger 84506476 Show evidence via WhatsApp 08119237616 Ban yafe ba🤕 20/10/2021, 20:45 - 🤔🤔: 2️⃣7️⃣-2️⃣8️⃣ Isn't free book Contact to subscribe 08119237616 niger 84506476 Lumshe idanunta tayi lokacin da taji yadda Sheikh ɗinsa ta cika mata baki, bata taɓa ganin halitta mai ɗaukan hankali kamar wannan ba, tana lumshe idanunta tana ƙara turata cikin bakinta Tamkar tana shan lolipop, Sheikh mutsawa yayi a hankali yana haɗe laps ɗinsa bawai dan yana jin feelings abun da take masa a'a,kawai yana jin kamar ana ja basa abarsa ne tamkar wacce za'a cire kanta hakan yasa ya fara mutsawa a hankali, duk yadda yasu buɗe idanunsa da kuma miƙewa ya garara bisa dole ya maida kansa ya kwanta, ganin tana neman zaucewa yasa da sauri ta nufi bakinsa tare da buɗewa ta zura masa nippy ɗinta tace "Suck it my sweet Imam is yours bana kowa ba ne" ta faɗa tana shafa kansa tare da hura masa iskar bakinta,datse bakinsa yay duk da cewa bai san me take ba, yaƙi bata damar aikata abinda take so, ganin bazai mata ba yasa ta saki marayan kuka tana faɗin "help me please Imam wlh mutuwa zanyi idan baka kusance ni ba, ka taimake ki Maminka Sweet" sosai take kuka sbd azabar data keji ta sha maganin ba kaɗan ba hakan yasa take jinta a sama ga wani kumburi da mararta tai mata, cikin zafin nama kuma miƙe tare da ƙoƙarin shigar da Sheikh ɗinsa jikinta bata ankara ba taji an ɗaga ta sama tare da haɗata da jikin bangon ɗakin. Wata gigitacciyyar ƙarar a zaba ta sanya tana dafe goshinta da taji lokaci ɗaya ya kumbura ga jini na zuba a wajan, cikin wata iriyar murya taji ana faɗin "Tabbas kina son sanya kanki cikin halaka, zanyi maganinki tunda kikai kuskuren taɓa abinda yake halaliyata, zan nakasa abinda kike taƙama dashi, lallai bil'adama baku da kunya kuyi mu'amala da Uba Kunyi da ɗa,sai dai kinyi kuskuren taɓa mijina kinyi kuskuren taɓa abinda ba naki ba" cikin kuka Mami ta shiga juya kanta tana neman inda ake mgnar gaba ɗaya jikinta rawa yake, tuni ta fara gani dishi dishi sbd jinin dake zuba a kanta "Dan Allah kuyi hqr wlh bazan ƙara ba, na daina" wata dry aka sanya wacce ta cika ɗakin gaba ɗaya akace "Jiiii kuuujibaaa jituu Saudat" shiru akai sai kuma akace "Kina ƙwaɗayin Imam ba sonsa kike ba, kina tare da Uban Imam ba dan kina sonsa ba,duk abinda kike ɓoyewa mun sani, burinki ki haɗa zuri'a da Imam yadda zaki mallake dukkan wasu dukiya daya mallaka haka ne??" Shiru Mami tayi ta kasa cewa komai sai fitsari daya ƙwace mata ta shiga yin sa, tsawa mai ƙarfi aka daka mata akace "Ko ba haka bane?" Da sauri Mami tace "Haka ne" dry aka kuma yi akace "tashi ki ɓace daga nan kinci Sa'a bana cutar da ɗan Adam da kinsha Mmki yau,kema bawai barinki nai ba ina son naga iyakar iya warki ne,kuma duk sanda kikai ƙoƙarin taɓa wani abu a jikin Sheikh babu shakka zan bayar da gabanki irin na maza" kuka Mami tasa tace "wlh bazan ƙara ba,dan Allah kuyi hqr" wani mari taji an waka mata da sauri ta dafe fuskarta sbd zafin da taji, tsoro yasa Mami ko riga bata ɗauka ba tai waje da gudu nono yana up and down a cikinta. Washegari da safe Sheikh na zaune a saman Wheelchair yana sauraren abinda Granny take cewa, shi dai jinta kawai yake a hankali yake shan coffee ɗin dake hannunsa, yana sanye da black ɗin yadi wanda akai masa ado da red ɗin zare yay masifar yi masa kyau, ya ɗura jar dara a saman sumarsa, idan kaga Sheikh a lokacin zaka ɗauka yay irin 35yrs ɗin nan a duniya sbd girmansa da kuma buɗewar jikinsa, bayan ya gaba shan coffee ɗin ya lumshe idanunsa, yana jin bacci na fisgarsa "To dai Ubanka yakai Toshi" idanunsa a rufe yace "meye hakan?" Tace "au kasan kanuri ya ɗauko ko barebari zance maka ne? To a yaransu ne suke cewa TOSHI kuɗin na gani ina so, nidai babu ruwana nace Allah ya sanya alkairi yasa muna raye za'ai,kaga aini ma haifesa bazan masa baki ba domin idan ya lalace ni ya lalacewa,to ba gwamma kawai nai masa addu'a ba" Murmushi Sheikh yay shidai baya baƙin ciki da auren at least ko Granny bata nan akwai wacce zaiji mutsinta a gidan, dan haka yabi Auren da addu'a yace "Allah yasa albarka" Granny tace Ameen dai,Ni da kai ya zaɓawa matar auren ba,amma Fisabilillahi guɗe guɗe dashi yace aure zaiyi" Murmushi kawai Sheikh yake yana shafa sajensa yace "Granny zani airport" taɓe baki tayi tace "meye eyapass kuma?" Yana wata ƙasaitacciyar dry mai ɗaukan hankali yace "yau su Fareeq da Bahaiyya zasu dawo jirginsu na gaf da sauka ma" ta washe baki tace "Laa! Kace yau zamu samu manyan baƙi daga Turai, to sun gama bastas ɗin ne?" Yana taune lips ɗinsa yace "In sha Allah!" Tace "To Allahamdulillah" tace "Au ban baka labari ba Barista har kuɗin K3re sart2ye (kayan sa Rana) aka kai masa, wai ana son yin bikin da gaggawa, babu ruwana nidai nace gaggawa aikin sheɗanne, kuma Ankul ɗinka yazo baka nan yace kaje ka samesa" da to kawai ya amsa mata. Yana zaune har Arjun ya shigo da addu'a Granny ta bisu har zuwa wajan mota Arjun yaja motar suka bar gidan, shirun da yay yawa yasa Granny faɗin "Ita kuma wannan lfy yau ko aikin bata fita? Badai kurarta akai ba" ta ƙare maganar ta nufar flat ɗin Mami a parlor ta samu Mami zaune,da sauri Mami taja gefen veil ɗinta ta rufe rabin fuskarta, haɓa Granny ta riƙe tace "yau naga abinda ya daman ni Faɗimatu,ya haka Saudala?" Mami tai ƙasa da Murya tace "Kin tashi lfy?" Granny tace "Kamarya? Nace Kamarya ganina kaɗai ya isa ya baki amsa, keda baki da lfy ba gashi nazo dubaki ba" Calmly Mami tayi domin bata son duguwar magana tace "A'a Mama lfy nake,kawai ina hutawa ne shiyasa" Granny tace "naga alama kam, kisan abun dace ne wai Auren mace da ciki, Allah ya ƙara lfy" tana faɗin haka tai waje tana ɓoye dryarta domin sarai taga kumburin dake fuskar Mami, Mami kam tun sanda abun ya faru cikin dare kasa bacci tayi data kwanta zata tashi a firgice hatta sallah sai da gari ya hawaye tayi ta, Granny na fita Mami ta ɗauki wayarta tare da kiran Fariha kiran farko ta ɗaga cikin kuka Mami tace "na shiga uku Fariha yaya zanyi da cikar muradina,kince nai hqr da batun Sheikh wlh ji nake ko Aljanun zasu kashe ni bazan zama iya hqr da Sheikh ba sai na cikar muradin zuciya ta a kansa" Fariha ta sauke ajjiyar zuciya tace "yanzu me kikeso ayi a kai? Ni gsky ban goyi bayan kije wajan wani boka ba,domin suma da Aljanu suke aiki to kuma wanda za kiyiwa yana da Aljanun, amma akwai shawara ina ganin idan kika bita za'a dace" da sauri Mami tace "wacce shawarar faɗi ina jinki" Fariha tace "a fara raba Sheikh da aljanar data aure sa" share hawayen ta Mami tayi tas tana sakin murmushi tace "Tayaya? Wa kike ganin zan faɗawa maganar Aljanun nan har su yarda da magana ta?" Fariha tace "Uncle ɗin Sheikh mana" Mami tai shiru tana na zarin maganar kafin tace "Kina ganin hakan babu matsala Uncle ɗin zai amince?" Fariha tayi dry tace "Why not? Ke matsalar idan kina son abu idanunki rufewa yake billahi, babu wanda Sheikh yake jin maganarsa kamar Uncle ɗin sa, kinga da zarar kinje masa da magnar kuma kikai masa bayanin komai zan yarda kuma zai nemi Sheikh ɗin" tsalle Mami tayi tace "Good idea gaba ɗaya kana ya toshe i don't know how to do, sai yanzu bari kiga na kirasa a waya domin ance da sanyin safe ake kama fara" Fariha tai saurin faɗin "Wait Hajiyata zuwa ya kamata kiyi idan kin ɗauki abun da muhimmanci, kinga ni jiya harna rasa yadda zanyi idan naji damuwarki sai naji ba komai bace a kan tawa" shiru Mami tayi tace "kamar ya?" Fariha ta share shawayen daya zubu mata tace "Saudat what should I do? Abban Taufiq ya mai dani sakarya a cikin gidansa,ina tsoran haƙƙi na ya kamashi wlh,bazan iya bin maza ba domin da ina budurwa banyi yanzu da nake da yara bazan iya ba,amma na kasa jurewa rabuna dana haɗa shimfiɗa da Abban Taufiq good 2yrs kenan,Nima fa mutum ce juya nai kuka harna gode Allah sai dai fa nayi azumi, wlh jiya da abin yaymin yawa da kaina na biyawa kai na buƙata" da sauri Mami tace "What da kanki fa?" Kuka Fariha tasa tace "Yaya kike so nayi Saudat abin yay min yawa zuciyata ga take da bugawa wlh" Calmly Mami tayi tace "it's okay! Kiyi hqr komai zaizo ƙarshe nasa ke ba irina bace dasai na faɗa maki wani abu,amma akwai number wani likita da zan baki kiyi masa bayani idan ba wata matsalar ce daga gareki saiki faɗa masa,ko kuma kikai ƙararsa idan ma auren za'a raba sai a raba mene a ciki?" Da sauri Fariha tace "A'a banda raba aure Saudat wlh ina son mijina, yana kyautata min babu abinda na nema na rasa sai haƙƙina na kwanciyar Aure" tsaki Mami tayi tace "kinga ina da abinyi idan fuskata ta sace nazo wajan aiki mayi magana" daga nan suka katse kiran da sauri Mami ta shirya zuwa gidan Uncle tana gama shiryawa ta sanya liƙab, fita tayi taga ba taga driver, mai kula da Flowers ta samu tace "Isa driver fa?" Kansa ya sunkuyar yace "Hajiya ai ya fita tare da Granny" baki ta taɓe ba tare kuma da tayi magana ba ta shiga motar ta mai ƙirar Mahindra XUV7000 black color taja da gudu tabar gidan. Yana zaune a saman kujera ya maƙala abun ɗaukan sauti a kunansa kamar yadda ma'aikatan gidan Redio suke yayin program, lumshe idanunsa yay yana kallon yadda Arjun ke operating system cikin ƙwarewa gefe guda kuma yana sauraran tambayar da wata take masa akan muhimmanci lemon tsami,shin da gaske yana rage sha'awa? Ko baya ragewa? Juyawa idanunsa yay domin idan da samu ya saba da irin wannan tambayoyin,shiyasa mutane da yawa suke masa kallon magidancin mai aure wanda ya tara iyalai da yawa. Zama ya gyara shima Arjun yabar abinda yake ya shiga kallon Sheikh domin shima yana buƙatar jin wannan amsar, sautari yakan yanka lemon tsami with black tea ya shafa domin kwantar da sha'awarsa, dan haka yanzu a shirye yake domin jin full impormation akan lemon tsamin, Sheikh yay domin yama rasa ta ina zai fara a karo na farko kenan yaji tambayar tai masa nauyin jin yay shiru yasa Arjun sanya waƙar larabci a tashar, kallonsa Sheikh yay da ido yay masa alamar mene yasa ka kashe? Dry Arjun yay yace "naga baka shirya ba, da alama lemon tsami yana da matuƙar tasiri ga hajiyarmu" ya faɗa yana shafa wandonsa tsaki Sheikh yay kamar bazai mgna ba sai kuma ya sauke numfashi tare da fesar da iska yace "Banza ɗan iska" dry Arjun yay yace "ba zaka gane ba sai ranar daka rakani ɗakin Amayarta zaka tabbatar da cewa niɗin cikakken ɗan iska ne" da sauri Sheikh ya saita speaker gabansa tare dayin stop na waƙar cikin ƙasa da muryar yana Lumshe idanunsa yace. "Muhimmancin lemon tsami ga lafiyar maniyi Lemon tsami yana gyara maniyi Lemon tsami yana cikin muhimman ƴaƴan itace da likitoci suka ce suna da muhimmanci a jikin ɗan Adam saboda sinadaran da ke ƙunshe a cikinsa. Akwai nau'in lemon tsami daban-daban a sassan duniya amma wanda aka fi sani shi ne ƙarami mai tsami musamman a Afirka da yankin Asiya. Mujallar lafiya ta Healthline a wani cikakken bayani da ta wallafa game da lemon tsami da amfaninsa ta ce lemon tsami yana ɗauke da sinadarin Vitamin C sosai, kusan yana samar da kashi 20 na buƙatar mutum. Yana kuma ƙunshe da sinadarai na iron da calcium da vitamin B da Potassium da magnesium" shiru yay yana maida numfashi da sauri Arjun ya ɗauki gorar ruwan sa daya tawo masa dashi ya tsiyaya masa a cup ya bashi a sanyaye ya karɓa tare da kafawa a bakinsa sai da ya shanye ruwan tas,sannan yaja kujerarsa baya ya shiga maida numfashi, gaba ɗaya matan gidan redio'n da mazan tsayawa sukai da abinda suke suna sauraran abinda zai ce,bayan ya maida numfashi ya ɗura da faɗin. Sannan lemon tsami yana kunshe da sinadaran da ke hanawa ko rage lalacewar kwayoyin halitta a jikin dan adam da ake kira antioxidants a Ingilishi. Binciken ya bayyana cewa ci ko shan lemun tsami yana ƙara ƙarfafa garkuwan jiki, yana kuma rage barazanar kamuwa da ciwon zuciya da kansa da ciwon koda da kuma inganta lafiyar fata" lumshe idanunsa yay yana shafa sajensa wanda yake a ƙwance yace "Muhimmiyar tambayar Shin Lemon tsami na tsinka maniyi?" Zaro ido Arjun yay yana ɗan danne dryarsa gudun kada Sheikh yaji, kallon kai ɗan iska ne Sheikh yaywa Arjun kafin ya ɗura da faɗin. "Wasu mutane sun dade suna ganin cewa shan lemon tsami yana illa ga rayuwarsu ta aure, tsakanin al'umma ko kuma a al'adance ake bayyana cewa lemon tsami yana tsinka maniyin namiji. Wani lokaci ma akan faɗa wa mutum cewa shan lemon tsami yana rage ƙarfin sha'awa ga maza da mata da kuma rage ƙarfin mazakuta. Sai dai Hajiya Jummai Hassan ƙwararriyar likita kan abinci da ke asibitin Wuce a Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya, ta shaida wa BBC cewa, baya ga amfanin lemon tsami a hanyoyi daban-daban na lafiya yana kuma ƙara inganci da gyara maniyin mutum. Ta ce lemon tsami yana da amfani da yawa ana - amfani da shi ta hanyoyi daban-daban wurin sha da kuma abinci. "Yadda mutane suka ɗauka cewa lemun tsami yana da matsala ga ma'aurata ba haka ba ne domin yana da amfani a jiki sosai. Domin wani bincike ya nuna cewa idan ana shan sa ba da yawa ba yana gyarawa da inganta maniyi." "Ɗan ruwan lemun tsamin da ake matsawa a ruwa ko a shayi a sha bai kai yawan da zai tsinka maniyi ba- sai dai ya gyara da inganta shi." "Nasan duk yadda ake shan lemun tsami ba a matsa shi har rabin kofi zallarsa a sha - amma ɗan matsawa kadan ba shi da wata matsala ga lafiya ko tsinka maniyi kamar yadda ake cewa," inji kwararriyar likitar abincin. Sai dai kuma ƙwararriyar likitar ta ce shan lemun tsami da yawa a lokaci ɗaya yana iya tsinka maniyi musamman ga masu son ƙayyade iyali kamar waɗanda ba su son haihuwa. Ta ce akwai bincike da aka yi a Australia wanda ya nuna cewa yawan shan Lemun tsami adadi mai yawa a lokaci guda yana iya tsinka maniyi. "Idan an yi amfani da shi a jiki kafin jima'i ko kuma a matsa ruwansa sosai a sha zai iya tsunka maniyi." Shan sa ne da yawa lokaci daya ne ba a so- Kuma duk abin da ya yi yawa yana da matsala amma baya da wata matsala ga ma'aurata. Yana gama faɗin hakan yay saurin katse shirin ta hanyar sanya tallah, kallonsa Arjun yay yace "Malam ya haka bayan baka gama ba,Nima ina da tambaya" banza yay masa yaci gaba da duba takardun gabansa, Arjun yace "Ya kamata gsky kai min lecture ta musamman yadda san sumar da My Aliyah kaga in one time ta ɗauki cikina yadda zan samu damar haihuwa da wuri na baka abinda na haifa" wani duka Sheikh ya kaiwa Arjun yana kwaɓe fuska yace "stop buddy ban so, kasan komai lokaci ne fa dan haka bana fidda ran wata rana zan shiga duniyar da kake ƙwaɗayin shigarta, kawai dan ban san tayaya ƙaddara zata zomin da abun ba" Shiru Arjun yay sai kuma yace "kaga tunda ka katse mana shiri tashi muje ka rakani wajan my Aliyah ina son naji abinda take so" "God forbid dani za'a shirya bidi'a? Kasan Allah ka rage rawar kai babu abinda za'ai daga walima sai ɗaurin auren walimar ma sai anyi ɗaurin auren" ɓata fuska Arjun yay yace "Haba buddy nidai gsky ka shiga haƙƙina" shafa ƙirjinsa yay yana sakin Murmushi mai sauti yace "to wannan zamanin mata da aljanu sukai masu yawa ana fara kiɗa kaga ƴar ƴan mutane suna zubewa a ƙasa kamar wasu tattabaru, nikam bana so" tura Wheelchair Arjun yay yace "ok nama fasa zuwa muje kawai gidan Uncle kaji kiran da yake maka" jama'ar gidan redio'n suka dinga gaisar da Sheikh suna masa gdy da ido kawai yake kallonsu domin bai fiya sakewa da mutane ba,daga Arjun sai yaran gidansu. Bayan sun hau kan titi Sheikh yay ƙasa da murya yace "mu huce airport after y maje gidan Uncle" murmushi Arjun yay yace "Duk yadda kace haka za'ai Sheikh Imam hamdan Balarabe. Sosai Fannah tasa Barrister a gaba tana kuka tare da begen ɗinsa akan ya janye maganar auren, murmushi yay mata yace "mene yasa baki so?" Kai tsaye tana sauke ajjiyar y tace "Nifa bana sonka" har ransa yaji ɗacin maganarta dan haka ya miƙe tsaye yace "But ni ina so ina ƙaunar Auren yay za'ai?" Kuka ta ƙara sawa kamar ƙaramar yarinya tace "wlh bana so ran kuwa zai ɓaci da wannan auren, ka ɗauka sabur ƙaddarar muce zata fara dani dakai, badai kace sati biyu kakeso ba" yana ƙare mata kallo yace "eh haka ne,amma yaymin tsayi wlh naso ace 1week ne amma yana iya dole zan hqr, kinga ana auren zan ɗauke ki zuwa honeymoon" idanunta ta share tas tace "Shikenan zanyi Auren amma ka sani auren nan na nufi abubuwa da yawa, wlh wlh idan har aure akai aka haifan baza ka taba samun abinda kake muradi ba kana ji kana gani wani zai amfana dani kuma da auren ka a kaina..... *SARAUTA 👑* 20/10/2021, 20:46 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 2️⃣9️⃣-3️⃣0️⃣ "Badai budurwar zuciyarka ta dake Ƴar cikanka take so ba? Ok fine idan ni kake so tabbas zaka saman idan kuma gangar jikina kake muradi zaka mutu da wannan muradin domin baza ka taɓa samun sa ba, wlh ni bana sonka dan Allah try to understand my feelings,zuciyata akwai wanda take ƙauna da muradin kasancewa dashi tun kafin na san menene so da kuma daɗin sa,ina jin kamar zan kasance dashi amma ƙaddarar aurenka na shirin wargatsa min all my plans" with much surprised yake bin bakinta da kallo gaba ɗaya bata huce good 17yrs a duniya ba amma har soyayya tai mata wannan mugun kamun? Tabbas ya shirya faɗa da dukkan wanda zai kawo masa cikas a zaman aurensa da Fatimansa,ya shirya ƙalubatanar ko uban waye wanda take so da kuma ƙauna kuma a shirye yake da shafe babinsa a duniyar baki ɗaya, juyawa tai da sauri zata bar wajan yay saurin riƙe gefen hijab ɗinta yana faɗin "Wait Fatima.." tsayawa tai ba tare data kallesa ba sai ajjiyar zuciya kawai take saukewa, from head to toe ɗinta yake ƙare mata kallo sai yanzu ya kula da zallar ƙuruciyarta domin ko a fuska ka kalleta kasan yarinya ce ɗaya sharaf. Kamar daga sama yaji muryar ta tana faɗin "kima ɗauke rayuwa take, Soyayya kuma bada rayuwa take" Murmushi ya sakar mata yace "of course my dear,idan kin shiga ciki ki cema Abba gobe Uncle zaizo" ko ƙara kallonsa ba tai ba ta shige cikin gida tana share shawayen da suka taro a cikin idanunta, juyawa yay zuwa cikin motarsa mai ƙirar Audi RS5 mai blue black, kai tsaye hanya ya ɗauka domin a yau yake son komawa Abuja. Nnamdi Azikiwe International Airport Nnamdi Azikiwe International Airport is the prime international airport of the capital city of Nigeria, Abuja. Situated, shine airport ɗin dasu Sheikh suke jiran zuwan su Fareeq da Bahaiyya, cikin nutsuwa passengers suka fara sauka daga cikin jirgin wanda ya sauka a filin tashi da saukar jirgi na Nnamdi Azikiwe International Airport, kusan sune na ƙarshen fitowa kowa ka gani yana cike da farin ciki da murna, kusan rabin mutanan cikin jirgin students ne wanda suka samu hutu sakamakon kammala exam ɗin 3rd semister da sukai, kowa yana ɗauke da jakar matafiya, wata farar yarinya ce wacce ba zata huce age mate ɗin Fannah ta fara ce tass ta fara sauka daga stairs ɗin jirgin fuskarta ɗauke da zallar murmushi, tana sanye da duguwar milk wacce akaiwa ado da red ɗin stones rigar ta tsage daga gaba kana hango dugun crazy jeans data sanya,tai rolling kanta da red ɗin veil, hannunta riƙe da trolly ɗin ta, fuskarta ta cika da farin ciki gaba ɗayan ta ba zata huce 17 to 18 yrs ba, daga bayanta kuma wani chocolate ɗin sarauyi ne bashi da tsayi sosai but he's handsome guy yana kyau mai tasiri a zuciyar mace, da sauri shima yake sauka daga stairs ɗin jirgin bazai huce 20yrs zuwa 22 ba amma gaba ɗaya suna da girman jiki wanda hutu da jin daɗi da kuma kwanciyar hankali sune sukai tasiri a jikin nasu har ya haddasa masu girman jikin, kasa jurewa sukai a kusan tare suka kwaso da gudu suna faɗin "Yayahhhh Sheikh, Yayahhhh Sheikh" faɗaɗa fuskarsa yay da Murmushi tare da gyara zamansa da kyau a saman kujerar da yake domin yasan suna iya ka dashi wajan kokawar hawa jikinsa, rige rige zuwa wajan sukai da sauri kuma Fareeq ya ture Bahaiyya ya faɗa jikin Sheikh yana faɗin "Yayahhhh Sheikh we missed you a lot missed wlh,kamar nai fiffike na dawo Naija haka nake jina" lumshe idanunsa yay tare da bawa ɗan uwan nasa side hug yace "Wlcm back Fareeq Hamdan Balarabe wlcm Bahaiyya Hamdan Balarabe" Bahaiyya kuka tasa tana turo baki gaba, da sauri Sheikh ya ture Fareeq daya shige jikinsa yace "Ƙaton banza" dry Fareeq yay yana kallon Arjun yace "Yaah Arjun mun sameku lafiya?" Arjun ya ɗauke kai yace "A'a ban sani ba tunda ni ba za'a rungome ni ba" da sauri Fareeq ya rungome Arjun yana faɗin "double sorry Yayana" kansa ya shafa yace "Ohh Fareeq an zama manyan samari ma sha Allah" dry Fareeq yay yace "kai Yaah Arjun" Kallonta yay yace "Sorry Habibty" tana ƙara matsu hawayen idanunta tace "Ba Yaah Fareeq ba ne kuma na riga shi zuwa wajanka shine ya ture ni" Murmushin da baya barin fuskarsa a ƴan kwanakin nan yay yace "yanzu baya baki wajan ba?" Kai ta gyaɗa masa yana sauke ajjiyar zuciya yace "Barakallahu fikiii how was your study?" Tace "Yaah ba sauƙi wlh" Murmusawa yay kaɗan ba tare da yay mgna ba yaja idanunsa ya rufe ruf kamar mai shirin yin bacci. Wayar Arjun ce ta fara ringing da sauri yay answering call ɗin sbd ganin sunan Uncle Sham yana kira, cikin ladabi yace "Ina yini Uncle" daga can ɓangaren Uncle ya gyara zama idanunsa akan Mami yace "kai da Imam kuzo yanzu" Arjun yace "Uncle bamu kaɗai bane munje ɗauko su Fareeq ne" jinjina Uncle Sham yay yace "ok ki fara drng nasu a gida then zai kuzo nan is that clear?" Arjun yace "Yeah" daga nan gaba ɗaya suka nufi gida bayan sun sauke su Fareeq suka juya zuwa gidan Uncle Sham, haka nan Sheikh ya samu kansa da faɗuwar gaba amma sai bai nuna a saman fuskarsa ba, yana zaune ya lumshe idanunsa yana yana sauraran bugun zcyarsa wacce bata fita sai da tunanin Aljanarsa. A zaune suka samu Uncle a saman kujera idanunsa sanye cikin farin glass, ga laptop a gabansa yana operating akan aikin da yake wanda ya wancin dukiyar da yake kula da ita bata kowa bace face Sheikh, kusan fiye da rabi na Dukiyar Sheikh tana hannun Uncle Sham yana kula da ita, sam Sheikh bai kula da Mami dake gefe ɗaya zaune a saman kujera ba,sai matar Uncle Sham mai suna Aunty Amina, Arjun ne ya zauna saman carpet bayan ya gaida Uncle da Aunt Amina, sbd shima bai kula da Mami wacce take ta rufe gefen fuskarta wanda ya haye lokaci ɗaya ba. A sanyaye cikin kasalar data saukar masa yana ɗan fidda numfashi a hankali ya ɗaga kansa tare da duban Uncle da zararan gashin idanunsa,ya sauke ajjiyar zuciya tafi a irga kafin ya samu damar buɗe baki cikin ƙasa kuma da murya yace "Evening Uncle" Murmushin Uncle Sham yay zuciyarsa fass da ganin Sheikh cikin nutsuwa ba kamar sauran shekaru da watannin da kuma satittikan zuwa kwanakin daya ɗi ba bashi da walwala. "Imam my son kana lafiya?" Ƙasa Sheikh yay da gansa sbd sarawar da yaji yay masa yana sauke ajjiyar zcy yace "Allahamdulillah!" Ya ƙare maganar yana jan manyan idanunsa wanda suke cike da bacci ya rufe, gyara zama Uncle Sham yay yace "Me kake shiryawa rayuwarka Didat?" Da sauri Mami ta kalli Uncle Sham sbd sunan da taji ya amsa na Didat sai kawai ta ɗauke kai tana tunani kala², shiru Sheikh yay domin bashi da amsar tambayar da Uncle ɗin ke masa, up ɗin laptop ɗin yay yace "what i mean mene hujjarka taƙin am Amincewa Auren yarinyar da Barrister yake faɗa maka?" Ɗan haɗe fuska Sheikh yay ba tare kuma da yay magana ba sai kuma ya sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya wacce ta cika ɗakin, Uncle Sham yace "it's okay! Na fahimta, amma kasan zama haka a gareka bamai yiwuwa ba ne ko? Idan taƙamar ka Mama na kula da kai wata rana dole zata gaza yayinda tsufa ya gama cinta,ko yanzu dauriya kawai take amma responsibilities ɗinka ya kusa fin ƙarfinta" shiru kowa yay yana sauraran abinda Uncle Sham ke faɗa kana yace "me yasa baka son Auren ita Nanan?" Runtsa idanunsa yay da ƙarfi ya shiga sauke ajjiyar zuciya dan seriously baya ƙaunar ai masa mgnar wata ƴar idan ba Aljanarsa ba, Uncle Sham ne ya ƙara maimaita masa tambayar kansa a ƙasa idanunsa a lumshe yana yatsuna fuskarsa cikin ƙasa da Murya very slow yace "ban so ne Uncle" jinjina kai kawai Uncle yay cike da gamsuwa yace "ko kana so ba lallai ya yiwu ba" Anut Amina tace "why?" Yace "I don't think a Governor will give him his daughter hands in marriage, Duk dukiyar daya tara, cos shi kansa baya da labarin auren shima Young brother ɗinsa wanda suke uba ɗaya ne yake son abun sbd lura da yadda yaga yarinyar tana ƙaunar Sheikh, dan haka ka manta da wannan mgnar, just forgot the past kawai ka fuskanci ƙalulaban dake gabanka ko zai sameka" cikin rashin fahimta suka kallesa gaba ɗaya kafaɗa ya ɗaga yana maida idanunsa kan jaridar darly trust dake gabansa. Tun daga bakin ƙofa Granny ta sanya kuka tare da cire gefen mahaifinta tana faɗin "Assha, Assha Allah dai ya shiga tsakanin na gari da bugu" idannunsu suka bayar zuwa bakin ƙofar harta shigo ta nemi waje ta zauna tana matsar ƙwalla, Aunt Amina ce tace "Mama lfy dai ko?" Ƙara matsu hawayen tayi tana share hanci tace "inafa lfy Aminatou?" Uncle Sham ya ɗaga kansa ya kalli Granny wacce take matsayin yayar mahaifiyarsa yace "Mama wanine ya mutu ne?" Kamar wacce aka faɗawa wani abu ta ƙara rushewa da kuka tana matsar ƙwalla tace "Inafa Shansu, wani abun alamara na gani a talabijin wai wani ƙaton mutum fisabilillahi ya ɗaga uwar ƙafar sa ya danne mutum ana ji ana gani babu wanda yay mgn saima ihu suke,amma ai dai babu kyau cin zali na gaya maka gsky wancan har baki aka fasa masa nikam ina zan zauna gidan Sadia ina ganin wannan lukutar masifar fisabilillahi? Itama dai Sadia zama kawai ake da ita ba'a gama sanin ƙarfin imaninta ba wlh, nidai na bar mata gidanta babu ruwana" kusan rabin parlon sai da suka murmusa Uncle Sham yace "Hajiata kodai Resling film Kika kallah ne?" Da sauri Granny tace "Yawwa ɗan albarka sisilin amma dai ko gantalallu wlh ita kuma Sadia badai na bar mata gidanta ba?" Jinjina kai Uncle Sham yay yace "haka ne" Arjun dai na zaune yana jin yadda ake gantalar da uwarsa murmushi kawai yake, Gyara zama Uncle Sham yay yace "Allahamdulillah daman su nake kowa ya taro nasu kiran Baffanka a waya to baya ƙasar baki ɗaya,ina son na sani da gaske abinda Saudat ta faɗa gsky ne ko menene?" Tun zuwan Granny sai yanzu ya ɗaga kansa ya kalli Uncle Sham ba tare kuma da yace komai ba yaja idanunsa ya rufe. Granny dake kuka tai tsit tana son taji abinda Uncle Sham zai faɗa "Saudat tace akwai mutanan ɓoye a jikinka haka ne" da sauri ya ɗaga kai ya kalli Uncle ɗin nasa kasa mgna yay sai ajjiyar zcy da yake saukewa, Granny ce ta muskuta tace "Wace Saudat kuma? Wacce gayyar ce?" Uncle Sham yace "gata nan gabanki ai Mama ita ta faɗa gama ciwon da suka ji mata nan, kuma tace kema an taɓa tsorata ki da mai kamarki" shiru Granny tai tana kallon Mami shima Sheikh sai lokacin ya juya ya kalli Mami suna haɗa ido ta janye nata idon tace "Eh Uncle gsky ne, shima kansa Sweet yasan da hakan kuma ina da tabbacin sune suka hanashi Aure domin a mgnarsu ta jiya sun tabbatar min da haka" kafin kowa yay mgna Granny ta fashe da kuka tana faɗin "kiji tsoran Allah Saudala kema uwa ce ki rasa sharrin da zakiwa jikana sai na Aljanun fisabilillahi? Kuma dai wlh Nima ina zargin haka sanin cewa Imamu malami ne yasa ban taɓa kawo tunanin wannan ba, to tayaya zanyi wannan tunanin do Allah? Tunda sai babu kyau zargi kuma wutar mai zargi daban take, amma nasha zuwa nemansa sai naga baya nan sai na koma ɗakinsa na ganshi shida Ranjun yace wai fita sukai,wani lokacin ma harda Barista nake ganinsa,naita Mmki sbd nasan Barista ba zama yake ba, nasha zuwa ina samunsa yana bacci yana surutai shi ɗaya yayta ɗaga ƙafa kamar dai wanda akaiwa kaciya, to haka nan naje ɗakinsa a ranar da nake gaya maka ya yini baya gida to wlh ina zuwa naga ƙatuwar macijiya a jikinsa, ina dalili ina mafari zaka jawa kanka masifa tunda kana da hanyar rabuwa dasu" Sheikh ji yay ransa ya ɓaci haka nan jikinsa ya ɗauki rawa jijiyoyin kansa suka fito a saman goshinsa lokaci ɗaya duk gargasar jikinsa suka mimmiƙe tsaye, ya shiga fesar da numfashi yana jan ajjiyar zcy, sosai Uncle Sham ya kaɗo da jin zancan Granny idanunsa akan Sheikh yace "is that true?" Shiru Sheikh yay idanunsa na sauya launi Granny tuni tai bayan kujera ganin abinda Sheikh yake, cikin tsawa Uncle Sham yace "dakai nake Imam haka ne? Gsky ne abinda Mama take faɗa ko mene? Da gaske ne akwai Aljana jikinka" idanun Sheikh akan Mami yaja ajjiyar zuciya ba tare daya kalli Uncle Sham ba yace "haka ne, kuma ina sane da ita a jikina rayuwa da ita ya fimin rayuwa da Iyayena tunda ta fisu ƙauna ta,bana jin kuma akwai abinda zai rabani da ita sai dai wata sabuwar ƙaddarar" kasa mgna Uncle Sham yay sai kallon Sheikh kawai da yake, Arjun ma with much surprised yake bin Sheikh da kallo, sai yanzu abubuwa da dama suka fara dawowa kansa, wato Airahn da yake yawan faɗa ba kowa bace face Aljanar dake jikinsa, zanan da yay ba kowa bace a jiki face Aljanarsa, da yawan lokuta yana ganin Granny a jikin Sheikh ashe ba kowa bace face Aljanar dake jikin Sheikh, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wanne irin abu ne haka? Ta maza Uncle Sham yay yace "ita aljanar da ita zaka zauna har ƙarshen rayuwarka kenan?" Kai tsaye Sheikh ya bashi amsa da "Eh" Jinjina kai Uncle Sham yay ba tare da yay mgna ba ya ɗauki wayarsa ya shiga latsawa harya fice daga parlon not too long time ya dawo ya zauna ba tare kuma da yace komai ba, cikin ɓacin rai Sheikh ya kalli Mami ya jinjina kansa ita dai ko a jikinta tasan sai an cire Aljanar jikinsa sannan zata samu damar kasancewa da sweet Imam ɗinta. Ƙara miƙewa Uncle yay babu jimawa ya dawo da wani babban Malami wanda yake ɗauke da babbar jaka da kuma Kur'ani a hannunsa, zama Uncle yay fuskarsa a sake ya kalli malamin yace "Sit Malam" Zama Malamin yay kamar yadda Uncle Sham ya buƙata kallon tsaf yaywa Sheikh ya ganu gskyar lamarin, Sheikh wanda ya durƙosar da kansa ya kalli Arjun yace "let's go" kafin Arjun yay mgna Granny dake bayan sofa tace "me kace?" "Malam ina son a cire Mutanan dake jikinsa yanzun nan" zama Malam ya gyara yana kallon Sheikh wanda yake zaune ko mutsi ba yayi sai sakin ajjiyar zuciya da yake. A can cikin jeji kam Airah ce kwance tana fitar da numfashi sai Tijama dake gefenta tare da Tuɓe, cikin mawuyacin hali ta kalli Tijama tace "Nasan bazan tashi ba, na san kin fini sanin suwaye suke farautar rayuwar Sheikh da kuma abinda suke so game dashi, Nakasar Sheikh ba daga Ubangiji take ba magauta ne suka samar da ita tun yana Ƙarami,sannan ba Saudat ce kaɗai take buƙatar wani abu game dashi ba,bayan ita akwai wasu, Ya kakata ina son ƙaddarar Imam yazo masa da sauƙi, bazai iya ɗauka ba naso na kasance dashi amma nima bani nake da kai na ba,akwai wanda ya halicci ne wanda a koda yaushe zai iya ɗaukan rai na,amma ina son kimin wata alfarma Yake Kakata" Tijama da jikin Airah ya fara bata tsoro kuma ta tabbatar wannan karan ba zata tashi ba ta daɗe da sanin Airah ba zai duguwar rayuwa kamar yadda ake faɗa sauran aljanu nayi,rashin Airah a jikin Sheikh ba ƙaramar tawaya bace amma dole tasan abin yi, kallon Airah tayi tace "Me kikeso ya jikanyata?" Sauke ajjiyar zuciya tayi idanunta na janye wa tace "kalli Tijama yadda Rayuwata yake baƙin cikin rabuwa da ni? Basu san ko basu rabani dashi ba Ubangijin daya haɗamu yana gaf da rabamu ba, Tijama ina son Sheikh Imam hamdan Balarabe yay farin ciki a rayuwarsa bana son yay kuka akan rashina kiyi abinda zaki akan cikar muradina, kiyi ƙoƙarin ɗaukan fansar da nace zanyi akan wanda ya lalata Rayuwar Sheikh Imam hamdan Balarabe, Tijama a koda yaushe numfashi na iya tsawaya ina son ki gayamin abinda kike ɓoyewa game da Sheikh wanda kikace SIRRIN MU ne ina son sani yanzu" shafa kanta Tijama tayi tace "Tabbas nakasar Sheikh ba lalura bace samar da ita akai ta hanayar a siri tun yana cikin mahaifiyarsa abu guda ne zai dawo masa da ƙafafuwansa har ya fara tafiya kamar sauran mutane" Airah na jan numfashi idanunta na tsiyayar da hawayen baƙin ciki da kuma takaicin rabuwa da Mijinta tace "Menene shi Yake Kakata?" Tijama ta kalli Tuɓe tace "Sheikh bazai taɓa taka ƙafafuwansa da zumar tafiya ba har sai ya kusanci mace.... 🤕Hello nace idan an fitar da wannan sai a nemi sanitizer a wanke hannu asa face mars aci gaba da zaman jira SIRRIN MU isn't free book Contact to subscribe 08119237616 ga Niger 84506476 20/10/2021, 20:47 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 3️⃣1️⃣-3️⃣2️⃣ Zare ido Airah tayi tana ƙara kallon kakarta ta "Tabbas sai ya kusanci mace yay tarayya ta auratayya da ita sannan ƙafafuwansa zasu warke ya fara tafiya kamar sauran mutane,haka tsarin karyewar asirin yake, komu bamu da ikon da zamu karya wannan sihirin sai dai mu taimaka masa wajan samun macen da zata bashi wannan damar" kuka Airah tasa tace "Mene yasa sai an sama min kishiya kafin Rayuwata ya samu lfyarsa? Bazan iya jurar ganinsa da wata ba koda babu raina please Tijama do something" riƙeta Tijama tayi sosai sbd rawar da jikinta ya fara cikin ƙaramin lokaci ta fara kokawa da numfashinta, riƙe hannun Tijama tayi da kyau tace " please i need your help Tijama" shafa kanta tayi tare da danne mata ƙirji tace "zan maki komai zan ƙarasa cika maki muradin ki ko bayan babu ranki, amma dole ki rabu da Imam a dai-dai wannan lokacin domin hakan shima wata damace a garemu, ki fita a jikin Sheikh yanzun nan Airah" kuka Airah tasa tare da juya idanunsa zuwa gefe guda tana hango Sheikh dage gaban Uncle Sham kansa a ƙasa, girgiza kai tayi tace "i can't Tijama dan ki rabu dani na mutu a jikinsa ko zan samu sauƙin abinda na keji a raina, ki barshi yaga mutuwa dan Allah Tijama" tsawa Tijama ta buga mata mai ƙarfin gaske tace "idan baki fita a jikinsa ba yanzu tayaya zan samu damar kawo maki shi nan? Ya zama dole ki hqr da jikin Imam tunda ba tare Ubangiji ya kawo ku duniyar ba, idan kuma taimakon nasa da gaske kike sonyi dole ne ki ɗauki taki ƙaddarar kamar yadda shima sabuwar ƙaddara zata riskeshi a tasa rayuwar, rabuwa da Sheikh Imam hamdan Balarabe ya zama dole domin hakan kaɗai zai sanya mubawa matar Ubansa kunya a gaban muta nan da suka amince mata,kinga ko gaba ta kai wani zancen ba zasu yarda da ita ba" ƙanƙame jikinta tayi tana karkarwa tare da danne ƙirjinta dake mata ciwo tace "shikenan zan rabu dashi Tijama amma kimin al'ƙawarin babu wata ƴar macen da zai raɓa soyayyata ce kawai zatai ta tasiri a zuciyarsa, da soyayyata zai dauwama ita zata zamu abokin shirarsa, zata zame masa mata ɗa Aboki, dan Allah kada ki bari wani abu ya raba tsakani na da Rayuwa ta" tsaki Tijama taja duk tana tausayin jikar ta amma hakan bazai sanya ai mata abinda take so ba,ita da zata bar duniyar ta yaya zata bar Mutum kamar mara lfy bayan tafi kowa sanin ingantacciyar lfyar da Sheikh yake da ita, clamly tayi tace "Look! Airah do what is right not what is easy, kada kiyi amfani da damar ki ki cuci bawan Allan da baiji ba bai gani ba, kinsan cewa da bakya jikin Sheikh da bazai taɓa kawo iyanzu ba tare da mace ba, yana da ƙarfin sha'awa irin mazan nan ne da basa iya jure abinda suke ji game da mace, Sheikh kaifi ɗaya ne tayaya kike tunanin duk wannan lafiyar da Ubangiji ya ba shi mu kuma mu zama masu son kanmu wajan daƙoshe sa, wanda suke lalata rayuwar Sheikh kima suke nema ke kuma naki soyayya ce, Kima ɗauke rayuwa take Soyayya kuma bada rayuwa take,kinga hakan na nufin zaki iya sadaukar da dukkan farin cikin ki akan Imam, to ki ƙarfafa zuciyarki kiyi supporting ɗina akan raguwar aikin da baki ƙarasa ba, na shaida kema kin shaida kaima Tuɓe ka shaida Airah ba zata tashi ba, to why are you wasting your time akan abinda kinsan ba mai yiwuwa ba ne" zuwa lokacin Airah bata fahimtar abinda Tijama take faɗa idan Idanunta na kan Sheikh tana tuna yadda zai iya rayuwa babu ita, tana tuna tarin ƙalubale da kuma manyan ƙaddarori da zasu hau kansa? Bazai iya ba Sheikh ɗinta bashi da hayaniya bazai iya ɗaukan tension ɗin da zai hau kanshi ba, yaya zatai tabi magnar Tijama ko kuma ta shareta, Ajjiyar zuciya mai ƙarfin gaske ta sauke tana ƙara dunƙule wa waje guda yayinda wani jini ya fara biyo bakinta, da ƙarfi kuma ta sanya ihu da kuka, Tuɓe ne ya riƙeta yana faɗin "Airah kiyi hqr dole ki hqr da Sheikh idan soyayyarki gsky ce ya zama dole ki bamu damar da zamu taimakawa rayuwarsa ya samu lfy sannan mu hska masa baƙi yansa" cikin fitar hayyaci da ɗaukewar numfashi tace "What should I do?" Kai tsaye Airah tace "ki sakar masa mazantakarsa frist, sannan ki dawo masu da nutsuwarsa ya fara gani mata a matansu ba kamar yadda yake masu kallon maza ba,ki dawo masa da asalin faɗan sa domin wannan shiru shirun da yake dashi duk kece sili duk masifar ABU MALEEK da DEEN Sheikh ya fiso so dole kibar hakan ya faru" cikin kuka tace "idan nayi hakan kina da tabbacin zai samu farin cikin da nake masa burin samu a rayuwarsa?" "Why not? Zai samu farin ciki kafin samuwar farin ciki amma dole sai zuƙata sun ɓaci, kin san idan kana son abu ƙalu bale baya hana kaso abu sai dai ka ƙara kusanta kanka dashi, zaki mmkin Sheikh zai zama Garkuwa ga jama'ar gari, zai zama zaki wanda babu wanda ya isa ya taka shi, zai zama zakara wanda kukan sa kaɗai zai tashi al'umma" rungome Tijama tayi a jikinta bata ƙaunar rabuwa da Sheikh ɗinta amma ya zama dole ta rabu dashi tunda hakan ne kaɗai zai sama masa farin ciki, wani gigitaccen ihu da ƙara ta sanya sai kuma cak numfashinta ya tsaya. Jikinsa rawa kawai yake tunda Malamin ya bashi ruwan rubutu yasha kana ya fara yi masa karatu ko ɗaga kai baiyi bare su sanya ran aljanar dake cikin sa zatai magana kuma ta fadi dalilin daya sanya ta shiga jikinsa, gumi kawai yake haɗawa jikinsa sai rawa yake idanunsa a lumshe ya sanya dukkan hannayensa ya rungome ƙirjinsa dasu sbd dukan da zuciyarsa take masa, Arjun na can gefe guda a zaune idanunsa ya kaɗa yay jaa sbd ɓacin rai harga Allah abinda Mami tai baiji daɗinsa ba, yasan cewa Sheikh yana da matsala sbd shi kansa yasha kamasa yana wasu abubuwa na almara amma bai taɓa kawowa kansa akwai wasu mutanan ɓoye a jikin Sheikh ɗin ba, kullum yana masa addu'ar Ubangiji ya yaye masa damuwa da kuma ƙunci dake cikin zuciyarsa,Malamin ne ya sauke numfashi yana mai ƙara ƙarewa Sheikh kallo da idanunsa, kafin yaja numfashi yace "Sheikh Imam hamdan Balarabe kalleni" banza Sheikh yay masa domin shima ya fara fita daga nutsuwarsa ji yake kamar yana shirin rasa wani abu mai matuƙar muhimmanci a rayuwarsa, Uncle Sham ya kalli Malamin yace "Ya dai Malam?" Jinjina kai Malamin yay yana ƙara kallon Sheikh kana ya kalli Mami yace "Hajia kin tabbatar da abinda kika faɗa gsky ne?" Kai tsaye Mami tace "haka ne Malam" bai ƙara mgna ba ya ƙara buɗe shafin Alkur'ani yaci gaba da karatu sai dai yay karatu mai yawa amma ko mutsi Sheikh bai ba, gajiya yay yace "gsky ko baƙin Aljani ko Aljana ce a jikinsa wannan karatun ya isa yasa ya ƙone bama yay mgna ba" cike da gamsuwa Uncle Sham yace "Malam kenan babu batun mutanan ɓoyen ko?" Kai ya jinjina yace "gsky babu sai dai akwai abu a jikinsa amma bana da ikon aiki a kansa sbd ba huru mina bane" miƙewa Uncle Sham yay yace "Ngd Sosai Malam Allah ya ƙara girma" Malam yace "Kai haba yiwa kaine fa kuma ai aikin mu ne ai so no need to thanks" rakasa yay har waje yana fita Granny ta fashe da kuka tana faɗin "Ni daman nasan sharri ne kawai irin na Saudala,banda haka yaya za'ai Alaramma kamar Imamu ace wai Aljana ta auresa fisabilillahi? Aiko makaho ya sha yasan wani zancan bana ɗauka bane,hankalinki ya kwanta kinci zarafin Imam to wlh keda Allah haƙƙina kaɗai bazai barki ba bare na Imam,babu ruwana ai Allah gafurur rahimu ne sai kiga Ubangiji ya yafe maki idan kiga nemi ya fiyar mu,amma wlh ba wasa ba kinci mutuncinsa aljani fa ba wasa ba" daga baƙin ƙofa Uncle Sham ya tsaya yace "Yaya haka Mama? Meye abin kuka a nan kuma,ai hamdala zaki tunda dai Allah ya ƙaresa" ƙara rushewa da kuka tai tana faɗin "babu ruwana ka barni nai kukan ko zanji daɗi kaima Imamu yi abunka za nemu maka ruwan wake fuska" Jinjina kai kawai Uncle Sham yay tare da faɗin "Toke Saudat kinji me Malam yace dan haka ki sake jikinki babu komai in sha Allah! Allah zai kiyaye" Anut Amina tace "Ameen" Arjun ma ya amsa, Mami kam kasa samun nutsuwa tayi sbd ta tabbatar da Aljanun Sheikh sbd ga shaidar a fuskarta nan, Tayaya za'a ce yanzu kuma babu su? Gsky akwai wani abu akwai dalilin rashin bai yanar su amma ne shi? Shine abinda bata sani amma dole ta bincika, tashin hankali Sheikh ya shiga hankalinsa yaƙi kwanciya da rashin bai yanar Aljanarsa shi zafi kowa farin ciki ba bayyanar ta domin zai samu ƴan cin rayuwa da ita ba tare dasa ido ko kuma wani abu ba,yasan kuma dukkan aljanu suna bai yana yayinda ake masu ruƙiyya where is my fairy? Tana ina? Ina ta ɓoye, nan da nan idanunsa ya ƙara birkicewa lura da hakan kuma yasa Uncle Sham cewa Arjun "kuje gida Allah ya tsare" miƙewa Arjun yay tare da tura Wheelchair har zuwa compound na gidan kai tsaye kuma ya taimakawa Sheikh ya shiga cikin motar kana ya naɗe Wheelchair shi kuma ya zauna seat ɗin driver yaja motar da gudu zuwa gida, suna fita Granny ta miƙe itama ta nufi waje driver yaja ta zuwa gida, ajjiyar zuciya Mami ta sauke kafin ta miƙe tsaye tace "Hjy Amina bari naje nima" da Murmushi a fuskar Anut Amina tace "kai haba dai ga lunch ina shirin shirya maki ai ba za'ai haka ba" Murmushin dole Mami tayi tace "kada kiji komai wlh am full Ngd sosai" Sallama sukai Mami ta shiga motar taja ta gudu kai tsaye gidan Fariha ta nufa. "Ni kam kamar akwai abinda Saudat take ɓoyewa naga gaba ɗaya taƙi sakin harta" Uncle dake juyawa white rice ɗin gabansa with vegetables source wacce taji cow meat sai ƙamshi take, yace "Wutar mai zargi daban take ki kiyayi kanki Mmn Huda" spoon ɗin hanunsa ta amsa ta fara basa abincin yana lumshe ido tace "Allah ba wasa ba Uncle na daɗe da zargin matar nan akan Sheikh, kana kallo a ranar da Mahaiyarsa ta haifesa a ranar kuma Abban Sheikh ya saketa" spoon ɗin ya amsa yana faɗin "kina samun ladar ci da miji kuma kina zobe ladan ta hanyar gulma ko?" Dry tai masa tace "kai dai kawai kace cikinka bai cika ba sai nafi gane karatun" ka faɗa ya ɗaga mata yace "whatever". Tunda suka ɗauki hanya ya kifa kansa a a tsakanin cinyoyinsa ya shiga fesar da numfashi da sauri² ko Arjun yana iya jiyo yadda Numfashinsa ke fita, kamar wanda zazzaɓin ma sharshara yake shirin kamawa tsoransa ɗaya kada ciwonsa ya mutsa domin yasan Wannan ajjiyar ziyara da yake ba haka kurum ba ne, yasu shigewa dashi hospital amma yadda yake ganin yanayinsa da kuma abinda ya faru last time yasa yaci gaba da driving a zuciyarsa yana nemawa Sheikh ɗin sauƙin abinda yake damunsa. Bayan yayi parking motar ya shiga ƙoƙarin zaro Wheelchair ɗin daya santa a back seat, da sauri Sheikh cikin zafin nama ya durƙosa tare da ɗura soft fresh hands ɗinsa a ƙasan tarazon gidan, cikin tashin hankali Arjun yace "Buddy mene haka what are trying to do? Idan rai ya ɓaci nutsuwa ke samu sa" ko inda yake bai kula ba yaci gaba da tafiya kamar yadda guragu suke cikin ƙaramin lokaci guwwar wandonsa tai baƙiƙƙir sosai yake jin zafi da kuma raɗaɗin da hannayensa zuwa ƙafafuwansa suke masa sbd bai taɓa gwada irin wannan tafiyar ba tunda ya samu kansa a cikin wannan lalurar, ya gwammace ya azabtar da kansa da wani ya azabtar da shi, he need his wife yana buƙatar Aljanarsa ita kawai zai samu yaji daɗi a ransa, ɗumin jikinta da kuma soft lips ɗinta sune kaɗai za suyi tasiri a cikin zuciyarsa har ya samu nutsuwa, shock ɗin da Arjun ya shiga yasa ya kasa koda mutsi, tausayi da ƙaunar Sheikh suka ƙara ratsa zuciyarsa. A haka ya ƙarasa har babban parlon gidan ya samu Sa'a babu kowa kai tsaye ya nufi flat ɗinsa yana jan guwwar sa zuwa lokacin har shaddar dake jikinsa ta fara yagewa, yana shiga ya buga ƙofar da ƙarfi tare da danna mata key, ya saba yiwa Granny kuka amma bai yarda wani wanda ba Granny ko Airah ba yaga zubar hawayensa, yana da rauni amma rauninsa aka abinda yake so ne, ke nan Airah itace weakness nasa, shiru yana sauraran bugun zcyarsa duk yadda idanunsa kuma suka zo zuba da ruwan hawaye ya tauye masu haƙƙin su ta hanyar hana faruwar hakan rashin Airah a yanzu shine kaɗai zai sanya a zubda hawaye, da fasa yaji an sanyin hannunta kaɗai ya tabbatar masa da cewa itace da wani mugun saurin ya ɗaga kansa,tana tsaye a kansa hannunta dafe da saitin zcyarta sai fitar da numfashin wahala take, bai tsaya jiran komai ba yasa hanunsa ya fisgota zuwa jikinsa tare da manna ta a faffaɗan ƙirjinsa ya ƙanƙame ta yace "My Airah my Aljana my Fairy Rayuwar Sheikh Imam hamdan Balarabe where are you hiding? Why are you leaving me? You broke my heart, don't ever trying to leave me i knew you're mine forever and ever and ever always" ya ƙare maganar yana ƙanƙame ta tare da sakin wani marayan kuka jin, tsaye Arjun yay bakin doorway shida Fareeq suna faman babbuga ƙofar, Granny ce tazo wajan hannunta riƙe ƙatuwar gora tana faɗin "wlh bazan lamunta Aljanun wanne kala ne bamu gani ba? Nace wacce kalar Aljana ce bamu gani ba yau suma ba gantalallun ba ne?" Kasa mgna Arjun yay abin duniyar yay masa zafi, shigar da ita ya kumayi ƙirjinsa yana shafa bayanta yace "No! Airah nothing will happen to you indai ina raye, I'll stay with you to the rest of my life" jin tai shiru jikinta ya saki yasa slowly ya ɗaga kan kamar mai tsoran Kallonta, wata gigitacciyyar ƙara ya sanya sbd jinin da yaga yana fita ta hanci da bakinta ga numfashinta daya saki, hannunsa ya sanya a saman ƙirjinsa for the frist time yaji baya ko harbawa da mugun sauri ya ɗaga fuskarta tare da covering face ɗinsu rada abinyi yay kawai sai ya haɗe bakinsu a kuma dai-dai lokacin ya saki wani kukan.... SIRRIN MU isn't free book Contact to subscribe 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 20/10/2021, 20:47 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 3️⃣3️⃣-3️⃣4️⃣ He's cry like a baby tare da jijjigata cikin dukkan muryarsa mai taushi da kuma daɗin sauraro wacce zuwa yanzu ta fara sauyawa sakamakon tension da yake ciki yake faɗin "Wake Up Wify! Wake up my Fairy, please don't do this to me Airaaa..hhh!" Yaja sunan da ƙarfi tare da wani emotional sound, ƙara rungome ta yay a jikinsa tamkar zai tsaga ƙirjinsa ya maida ta ciki haka nan yake jin zuciyarsa, lumshe idanunsa yay yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi cikin muyarsa mai taushi ya ƙara faɗin "No!! Noting will happen to you in sha Allah! Everything will be am telling you zaki ce na faɗa ohyyyah! Open your eyes Aljanata just look at into my eyes and tell me you're fine" haka ya wanzu yana surutai Airah kam babu abinda take ganewa ta daɗe da komawa ga mahaukacin ta wanda kowa garesa yake kuma garesa zamu koma, shi ya halaccin mutum da aljan kuma shike da ikon ɗaukan numfashinsu a lokacin da yasu kuma a lokacin daya ga dama, shiyasa ake cewa dukkan mai rai da buri yake mutuwa, Just like Airah Ubangiji ya ɗauki ranta da muradai masu yawa gske wanda kusan rabin muradanta akan yadda zata dawowa da Sheikh Imam hamdan Balarabe farin cikinsa da kuma yadda zata dashi da mahaifiyarsa, yanzu babu muradi babu ita mene makomar Sheikh?. Uncle Sham ne yay sallama tare da shigowa cikin parlon idannunsa kan side ɗin Imam inda yake jiyo kukan Granny, domin ita kaɗai ta cika gidan da kuka sai Buhaiyya wacce ta mara mata baya, Granny na ganin Uncle Sham tace "Shikenan nan wlh hankalinsu ya kwanta sunwa Imam fyaɗe nasa wannan ihun da yake bana lfy bane,Ni kam yaya zanyi da haƙƙin marayyan Allah!?" Da mmki Uncle Sham ya kalleta yace "Mama Maraya kuma?" Cikin kumfar baki tace "Nayi ƙarya ne? Nace ƙarya dana saba nayi ko?" Sai kuma ta rushe da sabon kuka tace "maraya mana yanzu Fisabilillahi banda ni ɗin wa Imamu yake dashi a wannan gidan duniyar? Banda lukutar masifa ma ina wata tarayya tsakanin mutum da aljan dan Manzon Allah?" Kai tsaye Uncle Sham yace "ƙaddara" ya faɗi hakan yana ƙarasawa wajan ƙofar Arjun yace "Uncle i try all my best wajan ganin ƙofar ya buɗe but i can't ya datse ta ciki" Jinjina kai Uncle Sham yay zuciyarsa cike da tunani yace "Ok! Just leave it soon or later zan buɗe he most open the door" shiru Arjun yay dan bazai iya musu da Uncle Sham amma sam hankalinsa yaƙi kwanciya domin zuciyarsa na gaya masa something bad gonna happen, Juyawa Uncle Sham yay yana kallon Bahaiyya wacce ta rungomesa tana kukan yayan nata, hannunta ya kama zuwa cikin parlo yana faɗin "Ina Mamin?" Cikin kuka tace "Uncle muma bamu dawo mun sameta ba kuma till now bata dawo ba" Murmushi kawai yay yace "ok yaya karatu ya makaranta hope kina jin daɗinta?" Kaita ɗaga masa tace "eh Uncle amma na gaji wlh,ina son zama tare da Yaah Sheikh" kanta ya shafa yace "just pray for him shine kawai" tace "I'll inama kanyi" yace "Good gal". Abu dai kamar wasa Sheikh yaƙi buɗe ƙofa Arjun kuma bai fasa buga ƙofar ba, har zuwa magrib lokacin Barrister ya dawo yake faɗin ko lfy? Cikin kuka Granny take gaya masa sharrin da Mami tai masa da kuma halin da yake ciki da kukan da yake yana kiran Airah, Jinjina kai kawai ba tare kuma da yay mgna ba ya nufi flat ɗin Sheikh a tsaye ya samu Arjun idanunsa yay jajirrr kamar wanda yay kuka yana zuwa yace "broke the door" kamar wanda yake jira ya ɗauki wata ƙaramar knife ya shiga kunce ƙososhin jikin ƙofar ya nayi yana sauke numfashi not too long ya kunce ƙofar kamar zai tashi sama haka ya faɗa ɗakin,abinda ya gani yasa yay saurin tsayawa zuciyarsa na bugawa sbd tsabar firgici da kuma damuwa haɗi da zallar tausayin buddy, ba Arjun ba hatta Barrister sai daya shiga shock da ganin halinda Sheikh yake ciki kusan a tare suka nufi wajansa yana kwance Dadduma ya ƙanƙame pillow yan gefe kuma ga casbawar dake riƙe a hannunsa farar jallabiya dake jikinsa gaba ɗaya ta ɓaci da jini, cikin kiɗima da kuma tashin hankali Arjun yake jijjagasa tare da kiran sunansa, zare ido Arjun yay lokacin da yayi arba da jinin dake fita daga bakinsa zuwa hancinsa, cikin wani sabon tashin hankali, Juyawa Barrister yay tare da nufar flat ɗinsa babu jimawa ya fita kunansa maƙale da waya yay waje da sauri ya nufi wajan driver yace "get the car" yana faɗin hakan ya koma ciki sosai ya samu nutsuwa ganin Granny na flat ɗinta da taimakon Arjun Barrister ya ɗaga Sheikh zuwa jikinsa sbd nauyin da yay ga jikinsa daya saki, kai tsaye cikin mota suka nufa Fareeq na biye dasu wanda shigowar sa kenan daga Mosque, Barrister na gaba Arjun na baya shida Fareeq sun sanya Sheikh a tsakiya gaba ɗayansu hankalinsu a tashe yake musamman Arjun. Kai tsaye a The Peake Specialist Hospital suka sauka suna zuwa manyan likitoci suka ƙarasu wajan tare da kama Sheikh suka ɗurasa akan gado har zuwa emergency room su kuma suka zauna a reception kowa da tunanin da yake, babu jimawa Uncle Sham ya ƙarasu shida Anut Amina domin tun a hanya Barrister ya kira su ya faɗa masu abinda ke faruwa, yadda Uncle Sham ya kasa zama haka Arjun ya kasa zama yana jin yadda Aliyah ke kiransa amma sam bashi da confidence ɗin answering call ɗinta, suna ta zaune wajan 1hr amma ko likita ɗaya bai fito ba,ganin hakan yasa Uncle Sham kallon Arjun yace "Muhd ya kama kaje gida haka kuma ka gabatar da sallah" girgiza kai Arjun yay yace "Bana jin zan iya barin buddy a wannan halin da yake ciki,ko na tafi bazan samu nutsuwa ba" "Olright i understand your feelings, yanzu kaje kai sallah sai kazo kaci abinci" kansa ya shafa yace "bari nai sallar am full" yana faɗin hakan ya nufi Mosque ɗin dake cikin hospital ɗin. Bayan tafiyar Arjun wani Dr ya buɗe ƙofa ya fito yana fitowa sauran suka fito ɗauke da gadon da Sheikh yake yana kwance samɓal kamar ma tacce hannunsa manne da drip lokaci ɗaya ya faɗa sai fari daya ƙarayi, kai tsaye wani special room aka nufa dashi Dr ya kalli Barrister yace "ina buƙatar magana dakai" sunkuyar da kai Barrister yay yace "Ok ga Uncle ɗinsa ma ni dashi duk ɗaya" kafin Dr yay mgna tuni Uncle Sham ya miƙe ya barawa Dr baya, jinjina da jikin bango yay zuciyarsa fal da tunani gefe guda yana tunanin Sheikh ɗinsa wani gefen na zuciyarsa na tunanin Fatimansa, wayarsa ya ɗauka tare da dailing number busy yaji wayar alamar an danna masa rejecting, sau wajan biyar yana kira babu response hakan yasa ya hqr da kiran a zuciyarsa kuma yana ƙara niya da kuma ɗaukan ƙudirin auren Fannah koda zai ƙarar da dukkan abinda ya mallaka Fannah kimarsa ce ta kuma mutuncinsa dan haka dole ya mallaketa a matsayin mata. Dr ya kalli Uncle Sham yace "he's critical condition I don't know how to explain you but Imam na cikin muhuyacin hali, akwai abinda zuciyarsa ke muradi da kuma fatan samu tun yana yaro ƙarami, nasan ba abun mmki bane idan nace baku san cewa yana da hawan jini da kuma ciwon zuciya ba, ciwon baiyi tsamari ba sbd kwanciyar hankalin daya samu a kwanakin nan, ciwon nasa yay tsamari daga jiya zuwa yau wanda harya sanya zuciyarsa ta kumbura" share zufar data keto masa yay yana ƙara nanata innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wacce kalar lukutar masifa ce wannan mutum kamar Sheikh yana da kuɗi yana da lfy yana da iyaye wanne irin abu yasa a zuciyarsa har zuciyarsa ta kumbura, kodai Nakasar dake jikinsa kai! Ina Sheikh yana da yarda da ƙaddarar a duk sanda tazo masa yasan da wahala ace lalurarsa ke damunsa harya sanya abun a zuciyarsa wanda yay affecting zuciyarsa, ajjiyar zuciya ya sauke yace "Dr mene yaja ciwon yanzu, muna da kuɗin da zamu samawa Sheikh dukkan abinda yake so kuma yake ƙauna idan har kuɗi na maganin abu tabbas a yau Sheikh zai samu lfy" Murmushi kawai Dr yay yace "Anya kowa? Idan kuɗi na mganin lalura ai da tuni ya daɗe da samun ƙafafuwan sa, yanzu magana ake ta ABINDA ZUCIYA KE MURADI, Tabbas akwai abinda zuciyar ke so kuma take muradi ban sanshi ba kaima ina da tabbacin baka sanshi ba, Allan daya halacce sa ne kaɗai dashi suka san komai amma samuwar abun ga Sheikh shine samun daidaito a cikin zuciyarsa, namu bashi taimako amma ba zamu iya cire masa damuwar dake ransa ba" tunanin abubuwan da suka faru shekaru masu yawa Uncle Sham ya fara har kawo yau da safe da kuma mgnar Aljanar Sheikh kai tsaye kuma zanan da Sheikh yay a jikin white paper ya faɗo masa, miƙewa yay tare da bawa Dr hannu yace "zan iya ganinsa yanzu ai?" "Bana jin hakan sbd yanayin yadda zuciyarsa take a kumbure abu kaɗan zai iya haddasa matsala,da zan maku shawara da kawai kun fita dashi waje ya samu cikakken hutu zuciyarsa ta samu sauƙi da sukunin ƙuntarar da take ciki" Uncle Sham yace "Ok I'll think about that Ngd Dr" Dr yace "your wlcm" yana fitowa ya samu Arjun da Anut Amina sai Fareeq da Mami wacce zuwanta kenan idanunta ya kumbura sbd kukan munafurci idan har Sheikh ya mutu ita kam ta tashi a tutar babu shiyasa take kuka kamar ranta zai fita, Granny kam duk yadda tayi masifar a tawo da ita taga jiƙanta ƙi Fareeq yay domin yasan saita cika masu asibitin da jama'a, Barrister ya kalli Uncle Sham yace "Yaya me Dr yace, wlh I'm scared shiyasa nace kaje bazan iya jure ganin Yarona a haka ba i luv him a lot" kallon gefe Uncle Sham yay masa yace "zai samu lfy in sha Allah just pray for him" jim sukai kafin Barrister yace "maganar Abban Fannah fa?" Idanunsa akan matarsa yace "zuwa gobe sani nima i want to talk to him" Barrister yace "Okey! Allah ya nuna mana" "Ameen" Uncle Sham ya faɗa yana yin gaba, babu wanda ya samu damar ganin Sheikh sbd ya under kulawar Dr Ilyas. Washe gari da yamma Arjun ya dawo Shida Aliyah sai ɓoye fuskarta take sbd kunyar dake cikinta Musamman da taga Umma a wajan, haka nan suka Karachi zamansu babu wanda ya samu damar ganinsa. Tijama ta kalli Tuɓe tace "yanzu aiki yana gareka domin kai ne zaka maye gurbin Airah kai ne takubin da zai sanya mu cika mata muradin data mutu dashi" shiru yay kana yace "Tijama mene nawa? Me zanyi wanda ƴar uwata zatai alfahari dani?" Murmushi tayi tace "zan faɗa maka komai da zarar lokaci yayi ina faɗa maka ne ka shirya domin a yanzu babu gudu babu jada da baya". Kwanaki suna tafiya kamar fitar numfashin Mutum yau kusan satin Sheikh biyu a cikin asibiti ya dawo hayyacinsa amma ko mgn ba yayi sai dai kallon da ido wani lokacin kuma zai fara masifar da ba'a sanshi da ita ba haka zai ce kowa ya fice ya bashi waje, ji yake zuciyarsa kamar zata fashe yasan yay rashi rashin da kafin ya samu wanda zai maye masa gurbinsa zai sha wahalar gaske ji yake ƙasar ma gaba ɗaya ta ishesa dan haka ya ƙudirci niyyar barin ƙasar da zarar an kammala bikin Abbansa da Arjun ɗinsa. Ƙofar baka buɗe tare da shigowa dake dare ne Yana sanye cikin sleep wears na parda white colour, idanunsa farare tass har wani fitta ruwa suke sbd fari, ga faffaɗan ƙirjinsa daya ƙara buɗewa sbd yanayin zaman da yay a saman bed ɗin, sumar kansa sai Shinny take sbd gyaran da Arjun ke mata, Arjun ne ya shigo tare da Aliyah wacce take biye a bayansa ta haske sosai sbd gyaran amarci da aka farayi mata sbd gaba ɗaya bikin bai huce 1week ba, kallo guda Sheikh yay mata ya janye idanunsa ya rufe sbd shi bai ƙaunar ganin mace ma wlh, duk da sauyin da yake jin a jikinsa amma hakan bai hana yaji sha'awar mace ba, kujera Arjun yaja mata ta zauna shi kuma ya koma kusa da Sheikh ya zauna a bakin bed ɗin, kallonsa yay yana Murmushi yace "Allahamdulillah! Nafi kowa jin daɗin samun sauƙin ka" shiru yay masa Arjun yace "kaga stop all this nazo mgnar biki ne tunda kace babu wani event shiyasa nazo ka tsara mana abinda kakeso ayi" ware idanunsa yay sosai akan Arjun kafin ya sauke numfashi ya shiga murza zoben hanunsa, Aliyah ce tace "Ina wuni buddy?" Shiru yay mata sanin halinsa yasa sam bata damu ba ta ƙara faɗin "Yaya jikin?" Kai tsaye tace mata "Allahamdulillah" yana faɗin hakan ya juya idanunsa ya kalli Arjun yace "mayan mace mai data gida saika dawo anjima" dry Arjun yay yace "Rai dai wlh zan rama duk abinda kai min" cije ba kinsa yay domin bai hango ranar da Arjun yake mgna akanta ba, rungomesa Arjun yay yace "I'll be back, Allah ya ƙara maka lfy Buddy na" da ido kawai ya bisu yana mmkin yadda Arjun yake rawar jiki akan mace. A ranar aka sallami Sheikh da daddare an gyara masa komai na ɗakin domin nan da 5days zasu koma sabun gidan da aka gama gyarawa. Ɓangaren su Fannah Barrister yakai kuɗin turaren huta da kayan gyaran jiki suka fara biki sam bata farin ciki da bikin amma ko a fuskarta baza kaga alama ba, Barrister ya haɗa lefe na amarya da iyayen amarya da ƙanwar uwa,da ƙanan uban amarya da uwar ɗakin amarya ko wanne sai da aka sanya gold a ciki, kaya na gani na faɗa iya Amarya wajan set uku akai mata,Sannan Uncle Sham ya ƙara da key ɗin mota. Yau ta kama ranar (WUSHE WUSHE) Amarya Fannah tasa kwailliya anyi mata kitso na gaba, wanda ya sauka har wuyanta sbd tsayin da gashinta yake dashi, anyi mata jan lalle tana sanye da Ghana kauwa da gyalen mindil na kanuri, ƙawayen Amarya sunsha ado kusan rabin ƴan uwa ne sbd bata da wasu ƙawaye na kuzo mu gani, bayan nan washe gari sukai KUNO wankin kan Amarya wanda ƙanin ango dana amarya suke mata, kasancewar Barrister yanzu bashi da wani ƙani sai kawai ya tura Arjun yin Duniya Arjun yay su tafi da Sheikh yace Allah ya sauwaƙe a bari ya zama ɗan daudo saiya fara zuwa biki tukun, dry kawai Uncle Sham yay domin ya basa dry wai ɗan daudo kenan duk mazan da suke zuwa biki ƴan daudo ne bana da labari, shidai shiru kawai yay yana spending tea ɗin dake gabansa, yana kallon Arjun ya tafi, domin shi Arjun ba wani event daya haɗa sai an ɗaura auren tukun za'ai walimar da Sheikh ya haɗa masu shida Barrister, haka dangin Fannah sukai bikinsu Ranar asabar aka fara ɗaura Auren Arjun suka ɗauki Hanyar zuwa Barno wajan ɗaurin auren Barrister Hamdan Balarabe da Fatima Baa'na. Gyara zamansa yay a cikin motar yana lumshe idanunsa yana sanye cikin wata dakakkiyar shadda white colour mai ɗinkin riga jamfer da wando sai babbar riga, ya sanya hula mai zanna bukar, hannunsa sanye bada Rolex Balancpain, yana kishin giɗe a bayan motar Arjun na gama yana driving ya gama mitar driver da Sheikh ya mai dasa shidai yana jinsa yay masa banza sbd lugudan da zuciyarsa ke masa, saurin buɗe ido yay tare da dafe ƙirjinsa a kuma dai-dai lokacin Arjun ya karya kwana tun daga bakin kwanar suka fara ganin taron jama'a wanda suka halarci ɗaurin auren Barrister, Sheikh ji yay kamar zuciyarsa zata fito sbd harbawar da take masa, runtsa idanunsa yay da ƙarfi ya runtsa idanunsa ƙara buɗe idannunsu yay kai tsaye idonsa ya sauka akan wasu ƴan da suke riƙe da wata ƙaramar yarinya an lulluɓe ta lafaya yarinya zai ce dan gaba ɗaya bata huce age ɗin Bahaiyya ba, da sauri ya cewa Arjun "Reverse the car" kallonsa Arjun yay ta cikin motar yace "why?" Da ƙarfi yace "ka juya motar Arjun.... SIRRIN MU isn't free book contact to subscribe 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 *Nimcyluv* 20/10/2021, 20:47 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 3️⃣5️⃣-3️⃣6️⃣ Da wani irin speed Arjun ya juya kan motar zuwa wani lungu nada ban wanda ya ɓulle har babban titi, ganin sun bar area'n yasa Sheikh ya saki wata wahalalliyar ajjiyar zcy yana dafe saitin zcyarsa, haka nan fargaba ta riskesa ba tare daya san dalilin faruwar ta ba, baya yay tare da lumshe idanunsa a ransa yana ambaton Allah, sai da Arjun yay tafiya mai tsayi sannan ya samu gefen titi tare da parking motar, ta cikin madubi motar yake kallon Sheikh yaga ko a jikinsa jin kuma shirun yay yawa yasa Sheikh fesar da numfashi tare da ware narkakkun idanunsa wanda suka ɗan janye kaɗan sbd baccin safe da bai samu yayi ba,tsaki Arjun yaja hakan yasa Sheikh kallon madubin motar suka haɗa ido kallon da Arjun yake aika masa kaɗai yasa ya fahimci yana son yaji dalilin daya sanya yace su juya, ɗauke idanunsa yay dan bashi da amsar da zai bawa Arjun, a karo na biyu Arjun ya ƙara sakin tsaki hakan yasa Sheikh ya ɗan ware laɓɓansa da ƙyar ya samu damar faɗin "wlh ka ƙara zaka fita,idan bani da ƙafa kasan ina da hannu i know how to drive" ta cikin madubin ya kallesa yasa yace "Ohhh! Really" yana fito da fararen idanunsa waje yace "sure" juyawa yay gaba ɗaya zuwa back seat ɗin da Sheikh ɗin yake a kishin giɗe yace "why?" Shoulders ɗinsa ya ɗaga yace "haka nan Buddy kawai hankali nane bai kwanta da zuwan ba" Murmushi Arjun yay da kallon ka rainawa kanka hankali arjun ya miƙawa Sheikh yace "Why are you acting like a child Sheikh? Kasan me kayi? Why tun farko kazo kasan hankalinka bai kwanta ba?" Banza yay masa dan yasan abune mai wahala Arjun ya fahimci halin da yake ciki. Koda wasa Uncle Sham bai san cewa su Arjun sun juya ba har suka isa ƙofar gidansu Fannah time ɗin ango kawai ake jira da kuma danginsa, bayan sun yi parking Uncle Sham ya kalli Barrister yace "shall we go?" Ajjiyar zcy Barrister ya sauke yace "why not Uncle?" Buɗe ƙofa Uncle Sham yay ya fito daga cikin motar shima Barrister ya fito daga cikin motar idanunsa a rufe sbd jirin dake ɗibansa, har wani duhu yake gani yana sanya da light blue ɗin gezner yay kyau sosai kana ganinsa ba sai anyi mgn ba kasan cewa shine angon. Yanayin yadda ya kejin kansa wani iri ya sanya ya fara taka ƙafafuwan sa a hankali cike kuma da nutsuwa but bottom of his heart fargaba ce zallah ga kuma wani Irin bad Mood daya samu kansa ciki a daddafe yaci gama da tafiya shida Uncle Sham sai kuma wasu manyan abokansa, cikin jama'ar suka shiga nan aka fara miƙa hannu ana gaisuwa, lokacin da suke gaf da isa tsakiyar rumfar da Za'ai ɗaurin auren wani jiri ya kwashi Barrister yay Baya luuu zai faɗi da sauri Uncle Sham da wani Sha'aban suka tare Barrister tare da faɗin "Subuhanallah!" Da kyau Uncle Sham ya riƙe Barrister yace "be careful" ya faɗa yana miƙar dashi ganin idanun jama'a na son dawowa garesu yasa Uncle Sham faɗin "ka shiga mota ka zauna you will feel better" Kawo Madu ne yace "A'a muje cikin gida dashi akwai special room sai ya huta a can" bai musu wani gardama ya amince har cikin gidan Kawo Madu aka shigar da Barrister cikin parlo mai kyau da kuma tsari ga t.v.da fridge da kuma a.c dake faman bada iska, bayan ya zauna Kawo Madu ya ɗauko masa gorar ruwa mai sanyi tare da glass cup ya ajjiye masa saman table yana faɗin "Bari naje lokaci na hucewa kuma munfi son baka matarka ka huce da ita domin ko ɗan rakiya baza mu baku sbd tafiyar nesa ce" da ƙyar Barrister yace "Ngd da karamci" waje Kawo Madu yay yana faɗin "haba an zama ɗaya kai kuma Allah ya jisshe mu alkairi" wajan taron jama'a ya koma yana fita Barrister yaji wani sanyi ya fara ratsa jikinsa sai ya kejin kansa fresh ba kamar ɗazo daya samu kansa a jiri ba, harya miƙe zai fita wajan ɗaurin auren sai yaji sanarwar har an ɗaura Auren akan sadaki dubu 100k with sisin gold. Ajjiyar zuciya ya sauke a taƙaice wani rabi daga cikin burinsa ya fara cika cikin ƙaramin lokaci kuma yaji so da ƙaunar Fannah na ƙara shiga cikin zuciyarsa. Sheikh ne yace "The you have any problem with that?" Taɓe baki Arjun yay yace "kaga canta matse maka shegen iyayinka yay maka yawa, nidai dan Allah muyi mu koma kai wa'azin a kaimin matana am anger to see my wife wlh" banza Sheikh yay masa sanin halin Sheikh ba irin mgnar nan yake so ba yasa Arjun ƙara faɗin "Finally zan kwana a jikin matata yau Wow akwai bacci mai daɗi" a cikin ran Sheikh yaja tsaki yana faɗin "Meye ajikin matar har kake rawar jiki Allah yasa ba yarinya bace masu kwararaton tsiya" wata dry Arjun yay yace "ehyeee har kasan mace nada raki? Idan yarinyar ce ni bani naji na gani ba? Ka jimu da mutum kai da ka tare da Aljana fa" haɗe rai tamau Sheikh yay Arjun na shirin yin mgna wayarsa ya fara ringing ganin sunan Uncle Sham yasa Arjun faɗin "ka nemi amsar bayarwa" kana yay picking call ɗin Uncle Sham na zaune a parlo shida wasu mutane sai kuma Barrister wanda yay garau sai wurga ido yake yaga ta inda matarsa zata fito "Mohd kuna ina ne haka?" Shiru Arjun yay kafin yace "Uncle ba ruwana Buddy ne yace mu juya" jim Uncle Sham yay kana yace "Ok bashi wayar" wayar ya miƙawa Sheikh kamar wanda ba dashi ake ba ya ɗauke kai yana kallon can sama ta cikin motar, sbd yanayin gari daya fara sauyawa hadiri ya shiga haɗuwa hakan yasa Sheikh ya fara tsorata sam bai son ruwa haka nan Allah yayi sa, calmly yay yace "sata speaker" sai lokacin ya tuna Sheikh bai taɓa riƙe waya ba hakan yasa cikin sauri yasa a handsfree muryar Uncle Sham ta cika motar yana faɗin "Why Imam?" Shiru Sheikh yay yana bin wayar da kallo sai da Uncle Sham yace "Speak up" sannan ya sauke numfashi Murya bata fita sosai yace "Uncle kawai naji bana son zuwa" Uncle Sham yace "akwai wani abu ne?" A taƙaice Sheikh yace "A'a" sanin halin Sheikh baya ƙarya yasa Uncle ya yarda da abinda yace kana yace "Ok ya kamata kuzo ko ruwa kusha kuma ko gaida Kawon Fatima" taɓe baki Sheikh yay yace "Who is she?" Murmushi Uncle Sham yay yace "Your Mother i mean your stepmother" lumshe idanunsa yay ba tare kuma da yace komai wai mother to Allah yasa ta zame masa uwar da yake fatan samu a kullum, Amma gani yake sam itama ba lallai ta bashi kulawar da yake buƙata ba komansa ya wargatse he missed his Airah ya rasa matarsa shiyasa ya kejin sa kamar ba mutum mai ƴan ci ba, ya rasa farin cikin sa a lokacin da zcy da kuma gangar jikin ta amince da ita, ya ɗauki hakan a matsayin wata ƙaddara amma meyasa tasa ƙaddarar zata zo masa a haka? Mai yasa a duk sanda yayi sake ya samu abu sai ya tafi ya barsa? Wanne laifi ya aikata haka? Da sauri yay astagafirullah a zcyarsa kana ya ɗaga kansa tare da sauke ganinsa akan Arjun yace "What again?" Arjun yace "burinka ya cika sai mu ɗauki hanyar Abuja ko?" Fesar da huci yay daga cikin bakinsa kafin yaja numfashi yace "Olright bari nai driving" da sauri Arjun yace "ka rufan asiri da Granny" ko kallonsa bai ba yaja jikinsa har zuwa gaban motar ganin hakan yasa Arjun fita shi kuma ya koma mazaunin driver Arjun ya nufi seat ɗin mai zaman banza, bakinsa ya mutsa kaɗan tare dayin bisimillah key yaywa motar kana yay reverse da gudu ya har bata kan titi bakinsa ɗauke da addu'a. Sosai Fannah take kuka kana ganinta kasan shagwaɓa ya zauna mata ta maƙale mahaifinta tana faɗin "Abba ni bana son auren wlh, ko an kaini sai na gudu ni bana so dan Allah kabar ni na zauna daku" ya lura da gaske bata son Auren amma kuma harda shagwaɓarta ta Auta ƙarshen haihuwa, banda abin Fannah duk wannan jikin nata wazai mata kallon yarinya da har za tace ko an kaita saita gudu rarrashinta ya shigayi yana faɗin "Sorry Mamana ai kullum ƴan uwanki zasu dinga zuwa Ya Falta ga Yana ke ai ƴar gata ce" cikin kuka tace "Abba ni ba wanda na sani kuma ina zan dinga samun tea da daddare?" Murmushi yay mata yace "Shirme dai sai yaro banda abinki ai gidan mijin ki ne ko? So duk abinda kike so shi za kiyi" kuka ta ƙara sawa tace "Abba to muje dakai" bashi ba duk Mutanan wajan sai da suka buɗe ido Ya Falta tace "A can fa akwai t.v kullum za kina ganin Tafsir" da sauri tace "Zanga Malami na da nake jin muryarsa?" Ya Falta tace "Eh Mai zai hana" nan dai aka dinga rarrashinta harta daina kukan sai ajjiyar zuciya kawai take saukewa, Ƙanan Mama kolo ne suka yiwa Fannah wanka da Humrah kana suka shiryata cikin wani blue ɗin lace mai kyau wanda akaiwa ado da touch ɗin Flowers, kana aka ɗaura mata farar lafaya mai kyau da kuma tsada sai ƙamshi take turare ya gama ratsa jikinta sbd tun ana saura sati biyu ta fara tsugunawa akan dorot ga gyaran jiki babu kalan da ba'ai mata ba, ga wata azurfa da aka sanya mata mai tsada da kuma bangles da aka saka mata a ƙafa (Mukarram). Kitson dake gaban goshinta ya sauka har wuya zallar ƙuruciyarta ya bai yana, har bakin motar Barrister aka sanyata sai a lokacin wani sabon kukan ya ƙwace mata tana tirjewa tana ba zata ba, da ƙyar dai aka samu ta shiga ta haɗe kai da gwiwa sai sakin ajjiyar zuciya take, addu'a sosai Kawo Madu yay masu tare da nasiha kana ya jaddawa Uncle Sham dole yau ango zai tare da Amaryarsa sbd al'adar su ce haka, Uncle Sham yana Murmushi yace "In sha Allah" da haka yaja motar suka fara tafiya, Barrister ji yake kamar yasa hannu ya jawota jikinsa ya tsotse bakin kukan haka ya keji ga sihirtaccen ƙamshin ta dake sauya masa lissafi dole ya rabu da ita sbd Uncle Sham da abokinsa Sha'aban dake gaban motar. Ganin Sheikh ya ɗauki hanyar gidan Uncle Sham yasa Arjun ya kallesa yace "Ya haka?" Bai kulasa ba har sai da suka isa gate ɗin gidan yay horn mai gadi ya buɗe masa, bayan yayi parking a harabar gidan cikin ƙasa da murya yace "Allahamdulillah" kallon Arjun yay yace "Malam ɗan kawomin ƙafata" wani kallon ka rainawa kanka hankali Arjun yay masa kafin yace "me kake nufi da haka buddy? Bayan kasan abunda yake gabanmu" idanunsa akan ƙofar da zata kaisu cikin parlon Anut Amina yace "me akai?" Haushin ne ya kama Arjun yace "tambaya kake ko neman sani? Malam kada ka rainawa kanka hankali mana me kake nufi da zuwanmu gidan Uncle bayan kansa shima ta can gida zai sauka sbd walimar" Ba tare da shakka ko wani abu Sheikh yace "Bana jin daɗi Arjun i need to rest" hannu Arjun ya miƙa zuwa wuyan Sheikh yaji da gaske fever ke son kama Sheikh yasa yace "Allah ya sauwaƙe" yana faɗin hakan ya fita zuwa Boot ya ɗauki Wheelchair tare da taimakawa Sheikh ya hau har cikin parlon Anut Amina ya shigar dashi Huda suka samu tana shan tea da sauri ta tashi tana faɗin "Ayyyyah sheik" Lallausan murmushi ya sakar mata domin yana ƙaunar yarinyar yana son yara a rayuwarsa, "how are you my Cutie?" Tana jan gemunsa tace "Fine" yana dry kaɗan yace "And where is your Mom?" Da hannu ta nuna masa kitchen bai ƙara mgna ba sai hannunta daya riƙe, Anut Amina ce ta fito tana faɗin "A'a angwaye ne har suka dawo" sunkuyar da kai Arjun yay Yana faɗin "Evening Anut Amina" tace "ya hanya da kuma Amarya?" cike da kunya yace "Allahamdulillah" tace "To Allah yasa albarka Aure dai sai hqr abinda kake so bashi kake samu ba yau fari gobe baƙi ai ta hqr" ya jinjina kai yace "In sha Allah Ngd Anut Amina bari na huce" tace "A'a bari kuyi lunch mana" yace "Sheikh na nan ni zani na dawo" tace "to Allah ya kiyaye" Sallama yay masu yace "sai anjima Buddy" Sheikh idanunsa a lumshe yace "Take care" yace "I'll" daga nan ya fice zcyarsa cike da tausayin Sheikh dan ya lura dauriya kawai yake amma da gske baya jin daɗi" kallon Anut Amina tayi tace "Zan kwanta Anut Amina" tace "sallah fa?" Yace "nayi" tace "abinci fa?" Yace "zanwa Arjun mgn yaywa Granny mgna ta dama min fura" tana turasa zuwa wani bedroom mai kyau tace "ai kam sai kaci wani abu kafin ka kwanta" jinta kawai yake har suka isa bedroom ɗin da ganta ta kwantar dashi tare da zare masa babbar rigar da Jamper zuwa singlet ya rage daga shi sai boxer fresh skin ɗinsa sai Shinny take luff yay akan bed yana sauke numfashi ganinsa a kwance yasa Huda faɗin "Ayyyah Sheik zan ancci" ware mata hannayensa yay da sauri ta shige jikinsa kamar yadda Uncle Sham yake mata babu jimawa bacci ya ɗauke su. Granny na zaune a parlo ita da Buhaiyya sai Mami wacce ta caɓa ado tana jiran zuwan Amarya babu wanda zaka gani kace ya nuna zallar farin cikinsa da auran Barrister Fareeq kam yana can cikin flat ɗinsa yana buga game kasancewar sabun gidan da suka koma kowa da part ɗinsa ko iya upstairs akwai flat wajan 4 dan haka wanda kakeso kawai zaka ɗauka, Amma Amarya Fannah can sama Barrister ya zaɓa mata an zuba mata kaya masu kyau da tsada hatta sutturar sawa wasu daga waje Barrister yazo dasu,hak nan Mami ma ya bata set ɗin akwati guda biyu Granny ɗaya. Wayar Granny ce ta fara ringing da sauri ta amsa tana faɗin "Aloo Ranjun" yana tsaka da driving yace "Granny anyini lfy?" Washe baki tayi tace "lfy lou tass ma kowa ina Imamun? Yana jiku shiru ne?" Gefensa ya kalla suka haɗa da ido da Aliyah da sauri ta ɗauke kanta yace "Mun daɗe da dawowa yanzu haka wajan walima zamu huce alrdy su Abba ta can suka sauka" tace "To ma sha Allah! Allah dai ya nuna min na Imamu haka" yace "Ameen daman shine yace na kiraki wai ki dama masa fura kisa zuma sosai idan ya dawo zuwa dare zai sha" miƙewa Granny tayi tace "kamar dai ka shiga raina yanzu nake cewa bari na samu ladan sa na dama masa domin nasan dole zai buƙata, to Ranjun wa yake dashi wanda zai masa? Ai saini ɗin dana zame masa dole ko?" Tunda Granny ta ambaci fura Mami ta maida hankalinta tana ganin wannan kaɗai itace damar da zatai amfani dashi wajan cimma buƙatar ta a kamar yadda Barrister yake taƙamar zai angwance yau itama wlh billahi da namiji zata kwana namijin ma ɗan cikinsa, hakan yasa ta miƙe tsaye tare da shigewa falt ɗin ta wayarta ta ɗauka ta kira Fariha tana ɗagawa tace "Uwar gida ran gida ykk?" Tsaki Mami taja tace "kina da matsala yasin how many times zan gaya maki ki daina bana so? Ina baƙin cikin Auren nan sosai ba zaki gane dalili ba sai nan gaba" Fariha tace "yanzu Meyesa kika kira?" Ajjiyar zuciya Mami ta sauke tace "Maganin dana amsa a islamic kin tabbatar yana sanya mahaukacin feelings in few minutes?" Dry Fariha tayi tace "you're mad Saudat just leave it idan baki yarda ba, amma wlh i trust him he never lied to me ko ubanwa kika sakawa Maganin nan sai sha'awarsa ta mutsa bare sabon shiga irin Sheikh ai sai yadda kikai dashi,kawai dai ki shirya domin naga ɗan naki Tubarkallah he's hot" Mami tace "Yeah he's! He's" lumshe idanunta tayi tana jin tsigar jikinta na tashi tun bata haɗa jikinta da tattausan jikinsa ba da sauri ta kashe kiran sbd ƙarar motocin da suka cika gidan, ta window'n ɗakinta ta leƙa taga motar Barrister sai ta Uncle Sham da alama har sun gama walimar, dubawa tayi taga babu sweet Imam ɗinta hakan yasa taji wani iri. Nasiha sosai Uncle Sham yaywa su Mami wacce ta hakimce tana nuna ko a jikinta kishiya ai ƴar uwa ce balle wannan wacce bata fi ƴar cikin ta ba, ita dai Fannah zuwa lokacin ta gaji da kuka sai ajjiyar zuciya take saukewa musamman yadda ta samu kanta na faɗuwar gaba, flat ɗinta a sama yake amma sai Granny ta kaita wani daban a donw stairs tace zuwa da safe sai ta koma nata flat ɗin. Sheikh kam yana gidan Anut Amina shida Huda mai tayasa shira Anut Amina har mmkin yadda yake mgna da yarinyar yake wanda idan babba ne sai yayi niyya zai kulasa, da ƙyar ta samu yasha inibi amma sam yaƙi cin abinci sbd bai saba cin abincin kowa ba sai na Granny ɗinsa, wankaya sauya Anut Amina ta bashi farar Jallabiya mai kyau da santsi ya saka, 10 dai-dai Uncle Sham ya shigo sosai yay mmkin ganin Imam yace "Badai kana nan tun ɗazo ba" idanunsa akan Huda dake bacci yace "Eh Uncle" yace "sai ka shirya kwana kam dan dai dare yayi" "No! Gida zani ni gsky ka kira min buddy" wani Uncle Sham yay masa "To ina da hankali ni mutum da sabuwar Amarya ƙarfe 10 kace a kirasa idan zuwa gidan ya zama lalle muje na kaika nima dai duk a gajiya nake" wajan 10:30 Uncle Sham yakai Imam har cikin parlo sannan yay masa gud night ya fita babu kowa a parlo shiru kawai yana bin ko ina da kallo, ji yay kamar an sauya turaren da ake sawa a parlon lumshe idanunsa yay sam baya jin bacci sbd daɗewa da yay yana bacci amma kuma yana buƙatar hutawa koya samu yin tunani mai kyau, Granny ta daɗe dayin bacci yana ta zaune can kuma sai Mami ta fito tana faɗin "my sweet kai dawa haka kasa ina ta tunani" ta ƙare maganar tana tura masa Wheelchair zuwa flat ɗinsa, Barrister duban furar yay sosai yaga ta basa sha'awa hakan yasa ya sha fiye da rabi kana ya ajjiye yasan da idanun Granny biyu bai isa ya sha furar ba,yazo yi mata sai da safe ya sameta ta daɗe dayin bacci miƙewa yay ya nufi flat ɗin Mami domin yana buƙatar yay mgna da ita kafin ya shige ɗakin Amaryarsa. Da taimakon Mami ya sanya kayan bacci masu taushi sbd sayin dake busawa a garin ya gama shan furar ya kwanta sai lumshe idanunsa yake Murmushin jin daɗi Mami tayi kana ta kashe masa light ɗin ɗakin tabar masa wani light blue ɗin haske,kana ta fita luff yay saman bed ɗin ya cukukuye jikinsa da duvet a zabar data fara samunsa a lokacin yasa idanunsa sauyawa sai matse ƙafa yake jikinsa duk rawa ya shiga kiran sunan Allah, babu abinda yake tayar masa da hankali sai ciwon da mararsa take masa ga yadda Sheikh ɗinsa ke halbawa ita ɗaya bai taɓa jin masifa irinta yau ba, ga Mami ta bar masa ƙofa a buɗe ga yanayin garin da ake ta walƙiya da alama koda yaushe ruwa na iya sauka, sai tsoro ya ƙara shigarsa da abin ya ishesa sai kawai ya miƙe zaune tare da jin gina da frame ɗin gadon ya shiga fesar da numfashi lokaci ɗaya kuma jikinsa ya fara ɗaukan zafi. Can cikin baccinta ta fara jin saukar ruwan sama sbd window'n dake ɗakin ba'a rufe da sauri ta miƙe jikinta duk rawa yake daga ita sai wata ƴar ficikar rigar bacci iya laps ɗinta gashi kayan sunyi mata masifar kyau, wata tsawa da taji anyi yasa tai waje da gudu sbd ganin ƙofar a buɗe, rasa inda zata shiga tayi hakan yasa ta saki kuka jikinta ya shiga rawa sam bata ƙaunar ruwan sama Allah yaga zcyarta, kamar ance ta ɗaga kanta ta hangi wani bedroom a buɗe a jikin wani flat da sauri tayi hanyar tana addu'a Allah yasa tsuhuwar ɗazo tana ciki. Yana zaune ya cure waje guda tare da toshe kunansa zuwa lokacin ya fara fita daga hayyacinsa sbd masifar data haɗe masa wacce bai san dalilin hakan ba sai abun ya zame masa sabun shiga kamar wacce aka cillo haka ta faɗo ɗakin Sheikh a dai-dai lokacin kuma aka tsaki wata gigitacciyyar tsawa lokaci ɗaya da ita dashi suka sanya kuka, tsoran daya shigeta yasa tai kansa da gudu tana neman wajan tsira idanunsa a lumshe yaji an ƙanƙamesa ana sakin kuka.... SIRRIN MU isn't free if you read for free🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️ It's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank. Show your evedance via WhatsApp.... 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 21/10/2021, 07:23 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 3️⃣7️⃣-3️⃣8️⃣ Kusan a tare suka saki ajjiyar zcy wacce su kansu basu san suyi ta ba, jin mutum kusa dashi shima yasa ya riƙeta gam a jikinsa yana ƙara sakin kuka kamar yaro seriously ruwa har sumar dashi yake sbd tsoro tun yana yaro, hakan yasa da Sheikh da Fannah suka maƙale junansu kowa yana sakin ajjiyar zcy, sunje can ƙarshen gado sun cure waje guda, sabon ƙamshin daya fara dukan hancinsa da kuma ɗumin daya fara ratsa masa jiki wanda ya rasa daga ina ƙamshin da ɗumin suke tawowa, Fannah kam zafin jikinsa Sheikh ya sanya ta ƙara maƙalewa jikinsa sbd sanyin data keji, ga yadda take jin jikinsa da wani taushi da laushi da tsantsi yasa duk ta shagala ta kumayiwa kanta masauki a jikin nasa ba tare da wani tunani ko wane abu ba, lumshe idanunsa yay a karo na barkatai ya ƙara jin tsigar jikinsa na tashi fiye da sauran lokotan, da sauri da sauri kuma ya fesar da numfashi yana jin kumburin da mararsa take masa yana ƙaruwa, tsawarce ta lafa ya zamana sai saukar ruwan kawai hakan yasa suka ɗan fara samu tsoron ya sakesu sai a lokacin kuma kowannan su yake son yasan a jikinwa yake, ita ta fara ɗago kanta a hankali tun daga kan yatsun ƙafarsa ta fara Kallonsa har zuwa manyan santala santalan cinyoyinsa wanda suke farare ga gargasar datai masu ƙawanya, kai tsaye idanunta ya samu damar sauka akan West ɗinsa da sauri da runtsa idanunta ƙirjinta ya shiga dukun uku³ gabanta kuma ya shiga faɗuwa all her life bata taɓa ganin mai girman jiki kyau da kuma tsari kamarsa ba, is he her husband? Shine tambayar data shiga yiwa kanta kenane,Amma wannan kamar yafi mijinta ƙyan fata da kuma tsarin halitta ga kuma hasken fata, ko dan bata taɓa ganin jikinsa bane,kamar mai tsoran ganinsa ta shiga buɗe idanunta ta ƙara saukesu akan west ɗinsa abinda ta gani yasa tai sauri yin sama da idanunta kai tsaye Idanunta kuma ya samu gurbin sauka a ƙirjinsa wanda yake da daɗi ya buɗe sosai ga wasu kwantattun gashi baƙi siɗik sai sheƙi suke kasa ɗauke idanunta tayi duk da lugudan da zcyarta take mata, idanunta ta juya ta kalli yadda brest ɗinsa suke manya kamar na mace ga wani six packs dake jikin kasa kallon fuskar mutumin tayi domin bata san abinda idanunta zasu gani ba,a jikinsa yaji cewa ana kallonsa amma tsoran abinda zai gani yasa yaƙi yarda ya buɗe idanunsa, so yake ya shiga bathroom ya watsa ruwa koza samu sauƙi abinda ya keji domin raɓarsa da tayi sai ya zamana kamar ta watsa mata tsotsotsi haka ya keji wani abu na binsa kamar ki yashi ga yadda Manhoon ɗinsa ke ɗagawa samanta nayi masa wani ƙaiƙayi bai taɓa samun kansa cikin wannan masifar ba sai yau.Duk da cewa bai taɓa jin tsoran wani abu makamancin wannan ba amma haka yay shahada slowly ya fara ɗaga zara zaran eyes lashes ɗin idanunsa tashin farko idanunsa a sauya a ƙirjinta dake cikin rigar bacci data sanya domin komai ana ganinsa a sarari hatta hasken dake fita daga jikin farar fatar ta, da wani sauri ya janye idanunsa sbd arba da yay da lafiyayyun kuma tsayayyun brest ɗinta wanda suke tsaye cirrr ta jikin rigar Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un ya shiga faɗa a ransa yana faɗa tana duguwa daga cikin bakinsa, kasa ƙarasa kallon fuskarta yayi hakan yasa ya zame jikinsa daga nata tare da kifa kansa a cinyarsa ya shiga sauke ajjiyar zuciya mai ƙarfi, jikinsa kuma yaci gaba da rawa ga wani zazzafan zazzaɓi daya saukar masa a lokaci guda jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa banda rawa da karkarwa babu abinda yake. Lokacin da Barrister ya shiga bedroom ɗin Mami ya tarar bata har zai fita sai kuma yaji yana buƙatar mgna da ita hakan yasa ya nemi gefen bed ya zauna tare da ciro wayarsa ya fara operating wayarsa almost 10mins yana zaune kafin yaji shigowar ta, kallo guda tayi masa ta ɗauke kanta tare da shigewa cikin bathroom, kashe wayar yay ya ɗan lumshe idanunsa sbd yanayinsa da yaji ya fara sauyawa ga wani mahaukacin feelings daya saukar masa wanda bai taɓa jin irinsa ba duk iya tsayin rayuwarsa, jin abin yay masa yawa yasa ya miƙe ya shiga sama da marwa a cikin ɗakin so yake yaje ga Fatimansa amma yana buƙatar mgna da Mami very important kuma hakan yasa yaci gaba da zagaye a cikin ɗakin, a hankali abin ya fara yi masa yawa hakan yasa ya fara rungome hanunsa a ƙirjinsa daga ƙarshe kuma sai yaji Barrister ɗinsa na mutsawa ita ɗaya tana masa wani yawo a cikin wando, cikin ƙaramin lokaci idanunsa kuma suka fara sauya launi, da sauri yay hanyar fita daga cikin ɗakin kafin ya fita yaji Mami ta fito daga cikin bathroom sanye da ƙaramin towel kallo ɗaya yay mata yaji hjyarsa tayi tsalle tare da miƙa wa a cikin jallabiyar daya sanya ɗauke kansa yay tare da sanyawa a shiga ƙoƙarin dai-dai ta nutsuwarsa yace "me kike haka ne?" Ba tare data kallesa ba tace "ai daka shigo ka duba kaga idanunta yaga komai" ka faɗa ya ɗaga tare da watsa hannayensa irin i don't care ɗin nan kafin yaja baya ya koma ciki yace "Ina son mgn dake Saudat" cikin sauri tace "Yaya akai kuma?" Ta ƙarasa mgna tana murje jikinta da wata humura ƙamshin humura ya sanya kamar tana ƙara masa hutar sha'awar dake damunsa, idanunsa daya gama rinewa ya ɗaga ya kalleta yace "Naga kinga Amarya kuma naji daɗin amsarta da kika a matsayin ƴar uwa bawai kishiya ba really appreciate" shiru tai masa sai kuma tace "naji wannan saura abu na gaba" kasa mgna yay sbd yadda yaga west ɗinta na juya hakan yasa ya miƙe a hankali zuwa inda take ko kallon arziƙi ba tayi masa shi kuma yana sauke ajjiyar zuciya yace "Ina son kija girmanki yadda Fatymerh zata ji daɗin yi maki biyayya, nasan ba zata taɓa maki kallon kishiya ba bare har wani saɓani ya shiga tsakaninku" cikin fusata ya juya ya fuskance ita burinta bai huce ya barta ta nufi wajan Sweet Imam ɗinta ba,amma ya kansa fahimtar komai cikin damuwa tace "Congratulations! Barrister, May God bless your life as beautiful as this day and you both enjoy every day of your journey ahead by sharing your love with one another. Wish You Very Happy Married Life! Hamdan Balarabe, Ahhha that's what you want to hear to me ko? To na faɗa you can leave now" Duk surutun da take babu abu guda ɗaya daya fahimta domin wutar kansa ta daɗe da ɗaukewa, gaba ɗaya ya dai nai mata kallon Saudat gani yake kamar Fatimansa ce a gabansa take masa rausayawa da ƙyakkyawan jikinta, idanunsa akan ƙirjinta yace "Ohh my Fatymerh you look so beautiful" wani kallon baka da hankali Mami tai masa tace "Heeee! Are you out of your right sense? How is Fatymerh koma uwar Fatima ce ba Fatymerh Malam get lost" Barrister ji yake kamar Mami na faɗin "I love you more than words can say. Loving you has been a beautiful dream I never want to wake from. You are a rare, beautiful soul. I love you so much. You sowed seeds of love in my heart, quickly, before I realized, and now love has taken root, flowering for you. My Barrister torch my brest suck them, my Barrister you're best sexcy man" tunanin haka a garesa daya ɗauka duk maganganun Mami abinda take faɗa kenan yasa ya ƙara sukurku cewa jikinsa ya shiga rawa tamkar ana kaɗa masa mazari, a duk sanya ya ɗaga kai ya kalli Mami sai yaga gaba ɗaya ta zame masa Fannah hakan yay saurin sanya hannu ba tare da tayi tunanin haka ba ya jawota zuwa jikinsa ya rungome ta sosai yana sauke numfashi yace "My Sweet and honey I knew you loved me too, so please allow me to enjoy your body it make me feel like I'm not old man, zan mai daki shalele na zan nunawa Saudat jikinta baya gaban Imam ke ɗaya ce a ido na, wlh ina sonki nasan wannan manyan abinda kikeso dasu duk mallakin Hamdan ne" ya faɗa yana tura hanunsa cikin wuyanta tare da fincike towel ɗin jikinta, Mami ganin abin nasa ba sauƙi idan tayi sake duk zai wargatsa mata shirin da tayi akan Imam yasa ta shiga kokawa dashi yana "Barrister am not that Stupid gril da kake magana akai buɗe idanunta nice Saudat ba Fatymerh please bakai na shiryawa kai na ba" yayi nisa baya jin kira sai da yaga ya samu nasarar hankaɗa kan bed Sannan yasa ƙafa ya danne ƙafarta gudun kada ta tashi da sauri kuma ya zame jallabiyar dake jikinsa, bai tsaya bata wani lokaci ba ya shiga faɗin "Ina son cika al'ƙawarin da Uncle Sham ya ɗaukawa Kawonki akan yana son na mai daki cikakkiyar mace and i promise to him" ya ƙare maganar yana ƙara shigewa jikinta dokansa kawa Mami take tana faɗin "You're mad Barrister kada ka sake ka shiga ba wajanka bane bakai na gyarawa ba wlh billahi sai kayi dana sani mara iyaka idan ka sake ka aikata hakan,sai na wargatsa dukkan shirin ka" bai iya bata amsa ba sai faɗin "you're so sweet and honey my Fatymerh". Da wani irin sauri Fannah ta ɗaga kanta zuwa fuskarsa sbd hucin numfashi sa da yake dukan fuskarta, kusan suman zaune tayi sbd ƙyakkyawar fuskar da tayi arba da ita kasa ɗauke idanunta tayi tana tunanin wanene shi? Yaya akai tazo garesa, sai a lokacin ta fara tuna komai cikin sauri koma ta shiga ƙoƙarin miƙewa rawar da ƙafarta take mata yasa cikin rashin Sa'a ta zame tare da faɗawa kansa, jikinta ya samu karɓuwa a cinyarsa ya zamana fuskarta tana kallon tasa sbd sunkuyar da kan da yay, duk abinda ke faruwa Sheikh na jinta sai yanzu ya samu damar buɗe idanunsa sbd nauyi da sukai masa daɗin da ɗawa yana tsoran kallon wacce take jikinsa, slowly kamar makaho ya shiga buɗe idanunsa da sauri ya ƙara ware su bakinsa har rawa yake wajan faɗin "My fairy" jin Muryar wanda ko a mafarki bata taɓa tunanin jinta ba bare ido biyu yasa tayi saurin buɗe idanunta tana shiga kallonsa yayinda shima ita yake kallo, da dukkan hannayensa ya ɗaga ta daga kwanciyar da tayi, kallon nasan baza ki mutu ki tafi ki barni yay mata, yayinda ita kuma take masa kallon ina son na ƙara jin muryarka, kamar ta shiga ransa cikin sassanyar Muryar mai daɗi da kuma saurare wacce ta saba jinta a gidan Redio taji yace "Kin dawo gareni Fairy,kin dawo a lokacin da zcy da gangar jiki suke muradin kasance dake, please don't ever trying to leave me again,i can't spend my life without you Aljanata, dan Allah ko zaki tafi ki tafi dani kada ki sake barina" ya ƙare maganar yana mannata a ƙirjinsa. Me zatai farin ciki kome? Ga ƙoshi ga kuma kwanan yunwa ta farin cikinta da muradinta a kusa da ita amma yazo mata a lokacin daya haramta a gareta, yaya akai ya kasance a gidan ko kuma shine Sheikh ɗin da taji Barrister ya taɓa, kenan hakan na nufin shi ɗan sa ne? Batai aune ba taji ya tura hanunsa cikin wuyanta yana shafa ƙasan gashinta, ji tayi tsigar jikinta ya tashi guda tana mmkin yadda akai ta kasa hanashi abinda yake, ko sbd ƙauna da kuma soyayyyar da zcyarta data daɗe tana masa ne? Sheikh yay sha'awar daya keji ta dawo masa sabuwa bai kuma taɓa jin daɗin jikin ta kamar wannan time ɗin ba, duk a tunaninsa Airahnsa ce ta dawo rayuwarsa, sbd zallar kamar da suke da kuma tsarin halittar su da yazo ɗaya domin babu abinda ya bambanta su, bakinta na rawa lokacin daya mirgina ta zuwa saman bed ɗin shi kuma yay mata rumfa da Physique chest ɗinsa, fuskarsa ya samman a saman ƙirjinta ya shiga sauke mata numfashi Murya can ƙasa bata fita sosai sbd yanayin daya shiga yace "My Airah Fairy ta, i missed you a lot missed Aljanata, i think i fall in love with you MA'UL HAYAT" Fannah ƙara firgi cewa tayi sbd abinda yake mata gashi yadda yake mata mgna kamar ya sanya ya taɓa rayuwa da ita ne, bakinta na rawa tace Leave me! Ni ni ba AIRAH ba...," Kafin ta ƙarasa mgnar taji saukar soft and sweet lips ɗinsa a matar wuyanta saurin runtsa idanunta tayi still jikinta bai bar rawa ba, Sheikh kam tuni ya fara manta abinda yake da kuma Duniyar baki ɗaya rashi sabo da abune yasa yanzu da yaji ƙwaɗayin abun sai ya kejin babu abu mai daɗi sama da jikin mace da kuma kasancewa da ita musamman his Airah, ba kinsa har rawa yake Wajan faɗin "I want you i need your body and you know what i think i have a feeling for you, ohhh yaaa my Airah hug me and kiss me it will be better for me" zuwa time ɗin ta farayiwa Sheikh kallon mara hankali ko dai zautacce bankin na ɓari tace "Am your father's wif.." kafin ta ƙarasa maganar yay saurin sanya bakinsa cikin nata... SIRRIN MU isn't free it's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 NIMCYLUV 21/10/2021, 07:24 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 3️⃣9️⃣-4️⃣0️⃣ Fito da ido waje Fannah tayi sbd jin abinda bata taɓa jiba a all her life he kissed her like a snowflake and tenderly, yadda yake sarrafa tongue ɗinsa cikin bakinta kaɗai zai tabbatar maka bai taɓa aikata irin wannan abun ba sai a kanta, ya bata dukkan tsuhuwarsa iyawarsa dama rayuwarsa baki ɗaya, yana kissed nata well idanunsa na zubda ƙwalla wacce shi kansa bai san ta mecece ba,duk da irin tsoran da take cikin zcyarta bai hana ta lumshe idanunta ba sbd abinda yake mata yana ratsa dukkan jikinta ko ina lungu da saƙo amsar saƙon Sheikh yake,kallon abin take kamar a mafarki idan har ba tunaninta ne ya bata ba dai-dai ba Sheikh ɗane a wajan mutumin da aka aura mata,amma mene ya sanya rayuwa za tazo masu a haka? Da wanne ido kuma zata kalli Ubangijin ta? Meza tace masa rana gobe ƙiyama da wanne harshe zata fara bayanin abinda ta aikata ga ɗan mijinta,wasu hot tears ne suka fara sauka daga cikin idanunta zuwa saman fuskar Sheikh,so that why Arjun yake mutuwar so da ƙaunar aure? Wannan dalilin ya sanya Arjun ya tukura kansa, a ƙasan ransa yake faɗin "Nima zanji daɗin da kake ji a yanzu, zan kasance da Airah fairy na" yanayin yadda hawayensu ya haɗe waje guda yasa fuskarsu har wani tsantsi² take, a wahalarce ya zare bakinsa daga nata a lokacin kuma ji yake kamar ana ƙara masa wutar sha'awarta, kallonsa yakai zuga ƙirjinta da sauri ya kifa kansa a ƙirjinta ya shiga sauke numfashi bai san meke damunsa ba a yau shi yau yana jin kansa a cikakken namiji mai ishasshiyar lafiya da kuma kuzari, yau yana jin abinda bai taɓa ji ba game da mace, jikinsa har rawa yake sbd sanyin dake ratsa jikinsa ga a.c dake ƙara banda wani sanyin banda sanyin gari dake busawa, matse laps ɗinsa yay sbd harbawar da yaji abar ciki take masa,hanunsa na rawa ya shiga turawa ta ƙasan rigar ta zuwa saman ƙirjinta, lokacin Fannah ta gama tsorata sai daɗin abin dake ratsa ta hakan yasa duk tayi weak jikinta ya saki, wata wahalalliyar ajjiyar zuciya suka sake lokaci da soft hands ɗinsa mai ɗumi ya sauka saman brest ɗinta ji yay wutar kansa ta tsaya sai kuma yaji kamar ana juna masa lantarki a jiki tsayawa yay ya zama kamar wani soko ya shiga ƙarewar innocent face ɗinta kallo well hanunsa na saman booms ɗinta, saukar zazzafan hawayensa a saman fuskarta yasa ta dawo hayyacinta tana jan numfashi tai saurin faɗin "stop this" cikin idanunta da bakinta yay hakan yasa ta fahimci ƙarayin bayani yake nema daga gare ta cikin jarumta tana lumshe idanunta tare da ƙara manna hanunsa a ƙirjinta wanda ita kanta bata san tayi hakan ba tace "Ni.. ni ba Airah bace sunana Fannah" kallon kin haukace yay mata still kuma bai ce komai so yake yace "You're lie, you're my Fairy my Aljanata" amma ya gangara furta komai tunawa da magnar Uncle Sham da yake faɗin "suzo su gaisa da Kawon Fatima" yasa ya ƙara ware idanunsa a kanta, yanayin daya keji game da ita yasa ya kasa ɗauke hanunsa daga kan nippy ɗinta, wani zafi² taji suna mata da kuma ƙarfi tace "Ka daina nifa matar babanka ce" ji yay kasan ya tsara da mugun ƙarfi hawayen idanunsa kuma suka ƙara samun damar fita daga ciki idonsa, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un shine abinda ya shiga maimaita wa a ransa wacce kalan masiface keson faɗa masa why matar Ubansa zatai masa kama da Airah, wlh Airahnsa ce the face the face voice komai nasu ɗaya hatta surar jiki meye kuma zata ce masa matar Ubansa ce,Abban nasa ya rasa wa zai aura sai ƴar cikinsa, matse nippy nata yay da ɗan ƙarfi tare da sakin wani numfashi, saurin rufe idanunta tayi tare da ɓangare masa murya na rawa tace "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Malamina ban san shi da wannan halin ba, kaji tsora ka tuna ayoyin Ubangiji, kada ka aita abinda zai zame mana tabo wlh tallahi nice wacce Barrister ya aura dan Allah ka rabu dani am scared kada mu faɗa komar Ubangiji" tunda ta fara mgna yaja idanunsa ya rufe yana sauraran muryarta wacce bata da wata maraba data Aljanarsa, kamar mai kuyan magana yace "Out!!" Ya faɗa yana ƙara matse ƙirjinta ƙanƙamesa tayi domin ta kasa mutsawa sbd wani sabon abinda ya risketa, wani shauƙi abinda yake mata ta keji su duka biyun kuka suke da idanunsa yana ƙara shigewa jikinta yace "fita nace..!!" Ya faɗa yana shafa cikinta tare da sakar mata jishi, kallon ikon Allah kawai Fannah keyi yace ta tashi amma yana ƙara shige mata idanunsa na zubar da ƙwalla well yana ƙara shafa jikinta muryarsa na rawa cikin tsawa kuma yace "Get out!! Fita nace tashi" jikinta na rawa da ɓari ta ƙwace jikinta da ƙarfi bata tsaya jiran wani abu ba tai waje da gudu tana kuka, tana fita shima ya faɗa saman bed ɗin tare da fashewa da kuka, kamar ƙaramin yaro wacce irin rayuwa shi Imam yake ciki ne? Meyasa rayuwa take juyasa ne kamar ƙwallo?meke damunsa ne tayaya his Airah zata zama matar Ubansa,ko shakka babu yasan wannan Airahnsa ce bawai wata Fannah ba, kifa kansa a cikin pillow ya shiga sauke ajjiyar zcy, me zai gayawa Ubangijin sa? Tayaya zai taɓa wani sashe na jikin matar mahaifinsa da sauri kuma ya girgiza kansa yana faɗin "No she's never be my stepmom, never matata ce Airah my wife please come back to me nine Rayuwarki ba wani ba" ya ƙare maganar yana dafe saitin zcyarsa wacce ya keji dan zafi kamar zata faso ƙirjinsa ta fito, ya daɗe kwance yana ta surutai jin danshi a tsakanin cinyoyinsa yasa ya ɗan mirgina tare da shafo wajan ware manyan idanunsa yay abinda bai tsammaci gani ba ya gani spram zai ce ko mene, jin tsallan da Sheikh ɗinsa ke masa yasa ya riƙeta da kyau har wani hucin azaba take da kuma neman ɗauki, har lokacin kuma bata bar dripping ba, meya akaita shi sam bai ga abinda yay ba, banda sweet bakin Airahnsa daya shafa mai yayi sai brest ɗin ta daya taɓa don ko a zahirance bai gansu ba, ɗan wannan abun har ya kai yaji wani abu ko wani abu ya fita daga jikinsa, yaya zai yi yanzu shi haƙƙin Ubangiji kawai yake tunawa amma yasan bashi da wani laifi tunda jikin Airahnsa matarsa masoyiyyar sa ya taɓa ba wata ba, kuma idan banda ita babu wata ƴar mace daya kejin wani abu a kanta, itama Aljanarsa yau ne abin yay girmama, Lumshe idanunsa yay tayaya zai wanka kafin wayewar gari? Bazai iya kwana sam da najasa a jiki ba. Ɓangaren Barrister bai taɓa jinsa a cikakken namiji mai kuzari ba sai yau Mami tun tana gane karatun da yake bata wanda ba'a son ransa ba harta kasa gane komai, dauriya kawai take bata son ta nuna masa gazawar ta bare raini ya shiga tsakaninsu amma ta ɗauki alwashin rama abinda yay mata zata nuna masa iya kar iskancin sa, ganin yana ta Abu gudu yasa ya zame jikinsa a hankali tare da mirginawa gefe yana sauke numfashi yabarta ne kawai sbd yasan ita yarinya ce ba zata iya ɗaukan dukkan wata buƙatarsa, kallon fuskarta yay wacce har yanzu ya kewa kallon fuskar Fatimansa a kan ta Mami yace "Am sorry my Teemah, you make this day very special to me thank you so much" haushi da baƙin ciki ne suka cika Mami hakan yasa cikin damuwa tace "Malam get out tunda ka gama" mgnarta yasa yaji kamar tana faɗa masa wasu romantic words hanunsa yasa zai riƙeta tayi saurin sauka daga gadon tana wale legs ta faɗa bathroom, shidai kamar wanda yasha giya haka ya kejinsa domin baya gane fari ballantana baƙi jallabiyar sa ya sanya kana yay waje tare da nufar flat ɗinsa, sai da yaje kusan flat ɗin ƙarshe har zai shige sai kuma ya tsaya tare da tura kansa ciki shiru bathroom ɗin babu kowa hakan yasa ya ƙara tura kansa tare da neman wajan zama ya zauna, jin ƙarar ruwa kuma a bathroom ya tabbatar masa da tana ciki sai yake ganin daman ai sanda zai fito bathroom ta shiga kenan ɗakin ya dawo. Lokacin da Fannah tabar flat ɗin Sheikh ta dawo inda take gado ta faɗa jikinta na rawa da ɓari domin har yanzu ji take kamar hannunsa na yawo a saman ƙirjinta, rasa abinyi yasa ta fashe da kuka tana maƙale jikinta a waje guda mai yasa tasa kalan soyayyar zata zo masa a HARAMTACCIYAR SOYAYYA, mai yasa wannan abinda yazo mata a JUYAYI ne? Tasan tana ƙaunar Sheikh da muradin samunsa wannan shine mafarkin zcyarta amma mene yasa abun zaizo mata a haka ne? Mai yasa bata tashi ganin Sheikh ba saida ta riga ta zama matar mahaifinsa? Yanzu yaya sunan abinda ta akaita tana da iliminta tasan me take duk da ƙarancin shekarunta amma tasan haƙƙin Aure tasan haƙƙin miji a kan matarsa ta karanta Zaadiz zaujen ta gani ta karanta Umdatul ahhkam ta gani, Malaminta yasha faɗa masu sannan ga babban malamin ta dake ƙara nusur da ita rayuwa wanda kullum take ji da sauran Muryarsa a redio shima yana faɗa,amma mene yasa yau da kansa zai aikata wannan babban kuskuren, ganin bata da wata ma dafa kuma Allah ya taimaketa ba'ai mai gaba ɗaya ba yasa ta Miƙe sbd wani iri data keji a jikinta ta nufi bathroom tare da zame rigar jikinta, ta sakarwa kanta ruwan sanyi dan ba zata iya jira ta haɗa na zafi ba. Yana ta zaune kafin yaji ta buɗe ƙofa ta fito kanta a ƙasa ta fito domin ko kula da shi ba tayi ba, inda aka ajjiye mata wasu ƙananun kayanta ta buɗe ta ɗauki wasu Sleep wears na prada dark brown masu kyau, idanunsa a kanta tana ƙoƙarin zame towel taji yay tari shima kansa bai san lokacin da tarin ya kwace masa ba, da sauri jikinta na rawa tai bathroom da gudu tana haƙƙi tare da dafe ƙirjinta, dry kawai yay kana ya kwanta saman bed ɗin domin yasan kota fito babu abinda zai mata shi tausayinta ma ya keji, Fannah kam bayan ta sanya kayan da sukai mata wani bala'in kyau kasa fitowa tayi sai da taji alamar ya fita, Sannan ta fito kai tsaye kwanciya tayi ta rufe idanunta cikin sauri ta buɗe su sbd Sheikh daya faɗo mata da kuma kukan da yake sai taji gaba ɗaya jikinta yay sanyi menene dalin daya sanya yake kuka? Kodan ta hanashi taɓa jikinta a yadda take jin son sa ƙaunar sa ko rayuwarta zata iya bayar indai zai farin ciki da wannan tunanin bacci ɓarawo ya ɗauke ta. Mami ruwan zafi sosai ta shiga zafi da kuma raɗaɗin bata keji yasa ta shafa versiline ita da sweet Imam ɗinta ne bata da wata matsala sai daɗin abinda daza taji amma Barrister ya wargatsa mata dukkan shirinta kuma wlh saita rama. Sheikh yadda yaga rana haka yaga dare sam ko runtsawa bai ba, da ƙyar ya nemi duvet ya rufe jikinsa. Da asuba Granny ta tura ƙofar sosai tai mmkin ganinta a buɗe tunda ta shigo yake binta da kallo harta ƙarasu gadon tabi da kallo tace "Yaya haka Imamu? Meye duk ka hargitsa gadon fisabilillahi kamar dai wanda ya samu filin sukuwa?" Bai tankata ba abinda ya keji a zcyarsa bazai taɓa barinsa yay mgn, ji a matuƙar sanyaye ya zuro ƙafafuwan sa ƙasan bed ɗin tare da zura wasu Slippers ɗin Berluti masu tsada sosai da kuma rashin nauyi, Warm water yasa Granny ta haɗa masa a cikin jakuzzie kana ta fita Lumshe idanunsa yay lokacin da ruwan ya ratsa cikin jikinsa ya shiga sauke numfashi wahala, har zuwa lokacin kuma hjyar nan inda take sai da ya sakar mata ruwan zafi sosai sannan ta dai-dai ta amma har yanzu mararsa ciwo take masa, daɗin ruwan zafin yasa wani bacci ya fara fisgarsa da ƙyar ya lallaɓa ya hau saman wheelchair dake bathroom ɗin ya ƙarasa wajan shower ya ɗaure raye jikinsa kana yay ɗaura alwala tare dayin brush, bathrobe ya saka a sanyaye ya shiga buga ƙofar Granny nice ta shigo ganin yanayinsa na yau yasa bata ƙara yin mgna ba sai duk ta firgita tunaninta ya shiga bata ko Aljanar ce ta dawo, a gurguje ta gama shafa masa wani versiline mai ƙamshi a saman fatarsa kana ta ɗauko kayansa ta bashi, abun yay mmki ya bata ganin bai yasa cire kayansa ba sai da ya juya mata baya Mmki duk ya cika Granny, bayan yasa Maroon ɗin jallabiyar ta fesa masa parfumes ɗinsa mai ƙamshi, sosai ya ƙara kyau ya fito a Sheikh ɗinsa har Parlo Granny ta kaisa tana jiran fitowar Barrister can kuma Fareeq ya fito shima sanye da Jallabiya kallonsa Granny tayi tace "To ina Uban naku kuma?" Fareeq yace "bai fito ba" haɓa ta riƙe tace "Yau naga abinda yafi ƙarfina ni Faɗimatu wacce rashin kunya ce wannan yaushe ya zama gantalalle bani da labari? Sbd yana tare da matarsa shine yaƙi fitowa" da sauri Sheikh ya kalleta sbd ambaton matar da yaji tayi ƙasan zcyarsa ya shiga bugawa, gyaran murya yay hakan yasa Fareeq ya tura Wheelchair ɗin zuwa waje. Sai wajan 6 na safe sannan Fannah ta shiga buɗe idanunta jinta kuma a jikinta mutum yasa ta hantsila da sauri jikinta na rawa tana tashi shima ya fara yana mata wani shu'umin murmushi da sauri tai bathroom shima waje yay yana jin kansa yau a fresh haba Saudat daman babu abinda take dashi take masa iyaye yanzu ya kejin ya sauke dukkan abinda ya tara a mararsa, da wannan tunanin ya haura saman upstairs ya nufi flat ɗinsa yana mmkin yadda gari har yay haske ba tare kuma daya sani ba, wanka yay kana ya shirya ya gabatar da Sallah yana gamawa ya fita zuwa downstairs, Mai aikinsu ya gani tana ta shirya breakfast, gaishesa tayi shi kuma ya nufi bedroom ɗin da Fannah take,samunta yay har tayi Sallah ta koma bacci kayan daya kawo mata ya ajjiye kana ya shafa kanta yana jin soyayyyar ta na ƙara ratsa masa zcy. Arjun kam ji yake kamar bai taɓa jin daɗin rayuwa dama duniyar baki ɗaya, sam bai bacci ba sbd kukan da Aliyah ta kwana ta nayi masa, sai wajan 9 na ya tashi ya shiga shiryawa domin buddy ya tsaya masa a rai yana son yaje yaga yaya ya kwana kafin ta farka daga bacci. Mami tun 7 tabar gidan zuwa wajan aiki shima Barrister ya fita sbd wani meeting da yake da shi. Tsaye take gaban dressing mirror tana kallon yadda idanunta ya kumbura sbd kukan da tayi, tana sanye da wata pitatte gwon ɗin atamfa Holand Orange color wacce taji ɗinkin fatan a sanya mata masu stones masu kyau, ga shape ɗinta daya baiyana ta cikin rigar hips ɗinta sun samu damar zama, bata saba sanya ɗan kwali ba hakan yasa ta ɗauki veil ɗinta daya kasance milk kai Orange ɗin Flowers ta ɗura saman kanta kitson dake gaban goshinta ya ƙara fidda kyanta, yunwa ta keji sosai hakan yasa ta fito daga cikin bedroom ɗin tana fidda wani ƙamshi na abin mmki,babban parlon babu kowa gidan shiru rasa inda zatai tayi su take ko tea ta sami tasha ko taji dai-dai, kanta ta ɗaga taga wajan 12 na safe, abin abinda zcyarta ke gaya mata tayi hakan yasa tabi wata ƙofa wacce take tunanin kitchen ne, tana shiga ta sauke ajjiyar zuciya sbd ganin da gaske kitchen ɗin ne, ƙarasa shiga tayi ta fara duba flast ɗin dake ajjiye saman stool ɗin kitchen ɗin, cikin Sa'a ta samu ruwan zafi ta ɗauki mug ta zuba ta fara haɗa tea mai kauri sbd kayan tea ɗin data gani, bayan ta zuba komai ta ɗauki spoon ta fara juyawa, cikinta har wani ihu yake, ɗauka tayi tare da jin gina da kantar kitchen ɗin idanunta a rufe ta fara shan tea ɗin tana hurawa sbd zafi, ƙamshin da taji kuma ta tabbatar ba jikinta yake ba, bata kawo komai ba ta buɗe idanunta kai tsaye Idanunta ya sauka cikin nasa wanda da alama ya daɗe yana Kallonta, yana zaune saman wheelchair saika ɗauka wani ɗan sarki ne sbd yake da wani kwarjini da cika ido yana sanye da wata shadda white colour anyi masa ɗinkin half body sumar kansa a kwance luff domin ko hula bai saba, hanunsa riƙe da cup of tea yana juya a hankali tuni ya ɗauke idanunsa daga kanta yay kamar bai ganta ba, sbd tsorata da kyansa da kuma kwarjininsa da kuma tuna abinda ya faru jiya yasa wani tari ya kawo mata ziyara tea ɗin bakinta yay feshi ya sauka a saman fuskarsa.... SIRRIN MU isn't free via WhatsApp number 08119237616 for more information ga ƴan Niger 84506476 NIMCYLUV 21/10/2021, 07:24 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 4️⃣1️⃣-4️⃣2️⃣ Bayan tea ɗin data fesa masa a fuska tsoran daya gama kamata yasa ta saki cup ɗin a ƙasa, gaba ɗaya bata tsammaci ganinsa ba hakan yasa da tai arba da shi gaba ɗaya ta gigice still kuma idanunta na kansa, Sheikh ko mutsawa bai ba kansa a ƙasa tamkar bai ganta ba haka yay pretending yaci gaba da shan tea ɗin cike da nutsuwa da kamala, a zahiri kuma idanunsa ne kawai baya gareta amma idon zcyarsa gaba ɗaya ya karkata ne gareta shi har kusan bashi dry tayi sbd yanayin da yaga tsoro ya shigeta kamar wacce taga dodo, ganin ko takan ta baibi ba yasa ta sunkuya tare da ɗaukan cup ɗin ta ajjiye, shi kam tuni yaja Wheelchair ɗin sa yay waje yana sauke numfashi domin baya jin zai iya ƙara some minutes a wajan, babban parlo ya koma tare da zamewa ya zauna saman duguwar sofa ya lumshe idanunsa yana sauke ajjiyar zuciya ganin zai faɗa wani tunani daban ya ɗauki remote ya sauya channel zuwa Aljazeera ya fara kallo duk da cewa ba wani fahimta yake ba,amma dole ya sabarwa kansa dasu sbd ragewa kansa damuwa da kuma wani banzan tunani, yana kallon amma rabin tunaninsa yana ga kitchen ɗin musamman da har yanzu hancinsa yake jiyo masa daɗaɗan turarenta kai ƙamshi da kuma sanyaya zcy. Yana fita ta dafe ƙirjinta tare sauke wata wahalalliyar ajjiyar, kasa aikata komai tayi sbd tuna yanayin da suka shiga shida ita a daren jiya, jikinta ne yay sanyi tana jin yadda zcyarta tayi mata nauyi har yanzu tana ganin girman abun da kuma muninsa,ko wacce mace burinta ta kai mutuncinta gidan mijinta ita gashi yanzu tayi auren duk da ba ƙaunar Barrister take ba kuma bata niyar dugun zama dashi,amma ganin Sheikh sai ya kure mata dukkan wani damuwar da take ciki Sheikh ya taɓa abinda Ubansa bai taɓa ba iya wannan kawai ya tabbatar so da kuma ƙaunarsa sun riga sunyi nisa a zcyarta,amma abu guda ke bata mmki mai yasa a aikata haka? daga ganin mace banda wani dalili ai ba zaka faɗa mata ba haka nan, wacece Airah? Tsaki taja kaɗan sbd sunan Airah data tuna, da kyar ta lallaɓa tasha ruwan tea ɗin ko madara bata iya sanyawa ba. Barrister ne zaune a cikin office ɗinsa yana operating system ɗinsa wayarsa ta fara ƙara alamar kira ya shigo tsayawa yay da abinda yake ganin sunan Uncle Sham yasa yay answering call ɗin yana faɗin "Evening Uncle" gyara zama Uncle Sham yay shima yana cikin office ɗin nasa yace "Barrister ykk ya kwanan amarya?" Murmushi jin daɗi Barrister yay yace "Wlh Allahamdulillah" Uncle Sham yace "Ma sha kasan dalilin kiran ai ko?" Girgiza kai Barrister yay kamar Uncle na kallonsa yace "A'a saika faɗa" shiru Uncle Sham yay yana nazarin abinda zai faɗa can dai yace "Bisa al'adar kanuri dole idan miji ya kwanta da matarsa a sani sbd tabbatar da mutuncinta, hakan tasa kawonta yay min mgn ni kuma nai maka abinda kace shi zan faɗa masa" baya Barrister yay sbd tuna yanayinsa na juya shida Fatimansa duk sai yaji kasala ta saukar masa idanunsa a rufe yace "haka fa, na kwanta da matata kamar yadda al'adar su saukesu,banda abinsu ma waye zai samu kamar dai Fatima kuma yay burus da ita ai sai mara lfy" jinsa kawai Uncle Sham yake amma ba komai ya fahimta ba sauke numfashi yay kafin yace "Ok! Allah ya kyauta" yana faɗin hakan ya kashe kira idanunsa akan laptop ɗin sa yana duba ayyukansa can wayarsa tayi ƙarar Kawon Fannah ya gani kamar dai bazai ɗauka ba sai kuma ya ɗaga yana faɗin "Assalamu alaika" da sauri Kawo Madu yace "wasalamu alaika Shamsudeen yaya ake ciki?" Miƙewa Uncle Sham yay gaba ɗaya tare da ɗaukan key ɗin motarsa ya fita daga office ɗin gaba ɗaya yana tafe yana faɗin "Congratulations Allah ya sanya albarka a auren" Uncle Sham ya faɗa yana shiga cikin motarsa, daga can ɓangaren Kawo Madu yace "Ma sha Allah! Allahamdulillah! Allah dai yay mata albarka dashi Hamdan ɗin gaba ɗaya" da Ameen Uncle ya amsa bai tsaya ya ƙara jin wani abu ba ya kashe kiran gaba ɗaya tare da yiwa motarsa key ya fita daga hospital ɗin. Kawo Madu ne ya kalli matarsa mai suna Yagana yace "Ma sha Allah! Yarinya ta riƙe mana mutuncinta" Yagana tana dry tace "kai amma dai nai farin ciki wlh,daman yarinyar badai hankali da nutsuwa ba" Jinjina kai Kawo Madu yay yace "Haka fa, kinga sunyi nisa damu dole za'a a hqr da farin gyalle a zummar shaida,tunda mijinta ya faɗi hakan shkknan sai kiji wajan Maman Fannah ki gaya mata" da sauri ta miƙe tana ɗaukan Lafayar ta ta ɗaura tace "Ai babu zama wai an saci zanin mahaukaciya yanzu zani na shaida mata" yace "To Allah ya kiyaye" tace "haba dai kamar wacce zatai nisa" ware idanunsa yay waje yana faɗin "Kai amma dai a gaisheki idan Allah ya nufa sai kiga ko waje baki ƙarasa ba Ubangiji ya ɗauki ranki amma ana Allah ya kiyaye wai ba nisa zaki ba" kallonsa tayi tace "Kayi hqr bari naje ma dawo ta ngd da addu'a" tana faɗin haka tai waje. Mama kolo na zaune da Ya Falta sai Yana dukkansu suna parlo suna cin abinci brabisko da miyan yakuwa wacce taji nama manya² masu yawa Yagana tai sallama, gaba ɗaya suka amsa mata Mama kolo na faɗin "sannu da zuwa kece da rana haka?" Yagana ta zauna tana faɗin "Wlh Kawonsu ya tasu ni yanzu haka" Mama kolo tace "to Allah yasa dai lfy?" Murmushi kawai Yagana tayi ta fito da kwalin sabulo da ashana ta ajjiye gaban Mama kolo tare da rangaɗa buɗe, farin ciki da kuma jin daɗi yada Mama kolo sakin kuka daman tana da tabbacin tarbiyyar da tayiwa yaranta ba zasu tashi a banza ba, kusan al'adar su ce haka idan an samu yarinya a matakin budurwa dangin miji zasu bada kwalin sabulo da ashana matsayin tukuci idan kuma ba'a samu ba za'a dangwarar da kwalin sabulo a gabanki empty babu komai a ciki haka kuma shine shaidar ƴar ki bata tare da mutuncinta, tun a titi tayi gantali dashi Yagana tace "Kawonsu ne ya fanshi dangin Mijin tunda basu kusa shine ya bayar a bada kyautar Fannah" sun ɗan jima suna Shira tare da sawa Fannah albarka kana suka ƙara yiwa su Ya Falta faɗa sosai daga nan tai masu sallama ta koma gida. Ƙyakkyawar fuskarsa ta zubawa idanu tun bayan fitowar ta daga kitchen ta samesa yana bacci ya rungome pillow a ƙirjinsa,kasa tafiya tayi tai tsaye nesa dashi tana ƙara jinjina kyawon halittar da Allah ya bawa Sheikh, kallon agogo tayi taga lokacin sallar Zhur ya kusa gashi har yanzu bacci yake, a jikinsa yaji ana kallonsa kuma ya tabbatar da itace domin babu kowa a gidan tun safe Granny ta tisa driver a gaba zuwa a asibiti dubiya, zuwan Arjun ne ma ya taimaka masa har yay wanka ya sauya kaya shine da zai tafi yace ya kawosa cikin kitchen ɗin, sam ba bacci yake ba yay hakanne kawai domin ya bata damar ƙare masa kallo kamar yadda take so, slowly ta janye idanunta tana mmki kujerar guragun data gani kusa dashi, bashi da ƙafa ne kome? Zara-zaran yatsun ƙafarsa ta kalla babu wata alama da zata nuna bashi da ƙafa, tana nan tsaye taji alamar buɗe ƙofar babban parlo cikin nutsuwa ta juya idanunta ya sauka a cikin na Mami gabanta ne ya faɗi da sauri kuma ta janye nata idanun, Kallonta Mami tayi from head to toe sai yanzu tasan dalilin auren ƴar cikinsa da yayi, wato yaga manyan bombom da kuma shafaffan ciki wanda ya bawa ƙirjinta damar bai yana sosai,ga farin da take dashi domin da ita da sweet Imam bata san wanda yafi wani jar fata ba, rufe ƙofar tayi tana takun ƙasaita ta ƙarasa shigowa cikin parlon,kamar yadda bata ƙara kallon Fannah ba itama Fannah bata sake kallonta ba, fuskarta ɗauke da Murmushi tace "Ohh my sweet darling Imam bacci a parlo kai da gidan Ubanka" ta faɗi haka tana ɗauke kansa tare da zama a gefensa,kansa ta ɗura saman cinyarta da sauri shi kuma ya tashi zaune idanunsa a lumshe, fuskarsa ta shafa tana shafo jajayen laɓɓansa tace "am sorry an barka kai ɗaya ba mutane a gidan ko?" Da sauri Fannah ta kalli Mami lallai ma matar nan tana nufin ita ba mutum bace, sai kuma wata zcyar tace kika sani ko Mamansa ce, girgiza kai tayi ita ɗaya ganin babu wata kama da suke da juna, a ganiye ya buɗe ido mai makon ya sauke ganinsa akan Mami sai kawai ya sauke a fararen hannunta wanda suka sha jan lalle mai kyau da tsari, idanunsa ya janye da baya jin zai jure kallon hannunta "Yaya jikin naka,i mean yaka kwana?" Da Mmki yake kallonta tayaya tasan ya kwana da wani abu? Ba tare daya kalleta ba Muryar very slow sbd kasalar data saukar masa yace "Allahamdulillah!" Miƙewa tayi tace "ya kamata kaje ka shirya time ɗin sallah ya kusa nima bana jin daɗi that is why bar wajan aikin na dawo gida da wuri" ta faɗi hakan tana jawo masa Wheelchair zuwa gabansa, zcyar Fannah ce ta buga da ƙarfi kardai tunaninta ya zama gsky tataya ƙyakƙyawan mutum zai zama gurgu saurin astagafirullah tayi a zcyrta, idanunta kuma ya cicciko da ƙwallar tausayinsa ga kuma soyayyyar sa data ƙara shiga zcyarta, ɗaga idanunsa yay suka haɗa ido zaro mata nasa idon yay tsoran da taji yasa ta saki ƙara da sauri kuma tai flat ɗin data kwana tana kuka, wani ƙawataccen Murmushi ya saki yana jan gemunsa tsaki Mami tayi tace "An kawo mana mahaukaciya dai" nan take launin fuskarsa ya sauya hanunsa yasa ya zame mata hannun daga Wheelchair da take ƙoƙarin turawa, gabansa ta dawo ta sanya dukkan tafin hannunta ta tallafo fuskarsa tace "My Sweet Imam me Maminka tayi maka kuma?" Banza yay mata yana zame fuskarsa zata ƙara taɓa sa yace "Stop please" ya faɗi hakan yana danna abinda ke jikin Wheelchair kai tsaye ya nufi flat ɗinsa. A dai-dai inda sautin kuka yake fitowa ya tsaya cikin ƙaramin lokaci kuma ya gane muryar mai kukan domin baya tunanin akwai abinda zai manta wanda ya shafe ta, runtsa idanunsa yay kana ya ƙarasa cikin bedroom ɗinsa. Bayan asar Arjun ne ke driving sai Sheikh dake gefensa yasha wata shadda wagambari amy color sai wula zanna yay kyau sosai, dawowarsu kenan daga gidan redio Arjun yace Sheikh dole sai yaje gidansa sannan zai kai shi gida, buɗe ido Sheikh yay sosai jin abinda Arjun yake cewa, sai da Arjun ya ƙara faɗin "kai mata duniya ne,akwai sanya mutum nishaɗi wlh,jiya ai ban san a wacce duniyar nake ba, yawo kawai nake saman gaji mare" taɓe baki Sheikh yay kafin ya kalli Arjun yace "Eh kam kusan abinda ka faɗa haka ne,amma ka kuji sharrin kace am telling you one day za kace na faɗa maka,am dan Allah enough ni bance ina son naji komai infact ban tambayeka daranka na jiya ba" dry Arjun yay sosai har yana kifawa kan staring motar yace "wlh that's what i wanted kuma finally naji" calmly Arjun yay yace "buddy ban san meyasa kake tunanin banza akan mace ba,amma na sha faɗa maka akwai wata rana daza tazo ka kasa gane kanka sbd mace" baya Sheikh yay tare da rufe idanunsa tunanin wacce ya gani matsayin Airahnsa ta faɗo masa, a hankali ya fara tuna ko wanne moment nasu na daran jiya yana loosing control ɗinsa idan har ya sanya idanunsa a kanta, shiyasa ya zaɓi barin gidan kamar daga sama yaji Arjun yace "Ya Mom ɗinka?" Da ido Sheikh ya tambayesa "Wa?" Kai tsaye yace masa "your stepmom Fatima" shiru Sheikh yay yana karatu nanata sunan "Fatima! Fatima! Fatima!" A ransa kasa amsa yay kawai ya ɗauke kansa cikin serious talking Arjun yace "she's very nice tana da hankali kuma zatai hqr tunda sa'ar Buhaiyya ce so kaga zata baka duk kulawar da kakeso,tunda ba wani waje za tana zuwa ba kaga ita da Granny sun isheka komai har zuwa sanda matarka zata amshe su" still shiru Sheikh yay zcyarsa ta lula tunanin wacce akace Fatima kuma itace matsayin matar mahaifinsa, fesar da iska yay tare da faɗin "impossible" idanun Arjun akan titi yace "meke nan? Har Shira za kunayi ku zama friends" da jajayen idanunsa ya kalli Arjun cikin kaushashiyar Murya mai amo yace "wlh ka sake min mgnar wata a nan ko a haka sai naje gida" ya faɗa yana nuna masa ƙafarsa shiru Arjun yay domin mgnar Sheikh ba ƙaramin dukan sa tayi ba,har suka ƙarasa gidan Arjun wanda yake ɓangaren Hjy Sadia mahaifiyar Arjun, har Parlo Arjun ya shigar da Sheikh zuwa lokacin duk baƙin da suka zo sun tafi tana kitchen taji yana kiranta "honey am back" ajjiye abinda takeyi tayi ta fito, kallon yadda take tafiya yay yana dry yace "honey da alama na maki aiki" marai-raice fuska tayi tana nuna masa Sheikh, Sheikh kam ko a jikinsa sun daɗe basu aikata wani abuba, bai kulata ba yasa ya jawota yace "uhm i missed you a lot missed wify" ya faɗa yana kissing goshinta tsaki Sheikh yayi hakan yasa Arjun zame ta daga jikinsa yace "jeki kawo mana lunch" juyawa tayi Sheikh ya kalli Arjun yace "bani key ɗin motar" yace "for what reason?". Washe gari da safe Mami na tare da Fariha tace suna mgn tace "wlh Fariha Barrister ƙaramin ɗan iska ne zan nuna masa bani da kirki wlh wlh sai na wargatsa dukkan shirin sa badai nasan dalilin daya sanya yake haka ba?" Fariha tace "mene kuma ya faru?" "Am storage woman bazan masa kuka ba,amma wlh sai na rama" Fariha ta fita daga cikin littafin da take karantawa na SAI NA AURETA tace "nifa ban gane maki ba mekike nufi?" Cije baki tayi tace "Barrister ya ƙara maimaita abinda yay min shekaranjiya ya kwanta dani out of ya kwanta da matarsa wacce giyar hauka yasa ya aureta" dry Fariha tasa harda tafawa tace "to meye abin damuwar? Ƙilan rabo ke kira, niba har addu'a nake Ubangiji ya karkato da hankali Abban Taufiq kai na ba,ke kuma kin samu kina wulaƙanci" girgiza kai tayi tace "ba haka na tsara ba, ba kuma haka nkeso ba, dukkan plans ɗina akan ɗan sa yake bashi ba" "to mene zaki i mean what a you going to do?" Mami tace "shiyasa nai maki mgn ai Shawara nake so kiban" ajjiyar zcy Fariha ta sauke tace "Haba Saudat idan kura na maganin zawo tayiwa kanta mana?" Cikin ɓacin rai Mami ta miƙe tsaye tace "ok zanje inda zan samu mafita kuma zakiyi mamaki wlh you'll be surprised" tana faɗin hakan ta fice tunda time ɗin tashinsu kasancewar Friday ce. Gaba ɗaya suna zaune a saman danning table Fareeq Bahaiyya Mami Barrister Fannah sai Granny wacce fitowar ta kenan daga falt ɗin Sheikh, Kallonta Barrister yay yace "Ina son ɗin?" Zama tayi tace "A'a nan kuma ɗaya ina ruwanka dashi Fisabilillahi? Badai ka zama gantalalle ba wanda bai damu da damuwar yaransa ba,koda yake ai Sheikh ɗin kawai kake ma haka ban san zcyarka ba,nidai ba ruwana kaji da iya haƙƙinsa kada kace zaka ɗurawa kanka sabo,kuma yace ba zai zo ba da ƙyar na lallaɓa sa nace yanzu zai aika takwarata Faɗimatu takai masa" zcyarta ce ta buga da ƙarfi hakan yasa ta ɗaga kai a hankali ta kalli Granny sai kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa, Barrister yace "ga Saudat takai masa mana" da sauri Granny tace "Wace kuma Sandal? Wani abune haka? To bazan bayar ba banyi jiya ba idan kuma rashin ɗa'a zaka koyawa yarinya daga zuwanta bisimillah" shiru yay kawai ba tare da yace komai ba Bahaiyya da Fareeq dinner ɗinsu kawai suke ce idan da sabo sun saba da halin kakar tasu. SPAGHETTI WITH BEEF STEW ta fara zuba masa sai PLANTAIN PORRIDGE. With cup of coffee ta jera saman tray tace "tashi maza ƴar albarka irin alkairi jeki kai masa ki tabbar yaci dan shima naga ya zama sallamamme bai damu da lfyarsa ba" dan dole ta miƙe jiki a sanyaye hijab ɗinta har ƙasa ta amshi tray ɗin Granny tace "ai kin san pilat ɗin nasa ko? Yoo keda gidanki ma ai dole ki sani jeki Allah ya tsara ya kuma tsune idon a sara" yana zaune gaban dressing mirror cikin nutsuwa yake bin jikinsa da wani lotion mai ƙamshi daga shi sai farin towel gama shafawa yay ya ɗauki parfume ya fesa a jikinsa,yana shirin zame towel ɗin jikinsa yaji an turo ƙofar bedroom ɗinsa yasan itace tun tuni zcyarsa ta gama gaya masa zuwanta sbd harbawar da take masa, tsaye tayi bakin ƙofar jikinta ya shiga rawa haka take samun kanta cikin wani hali. *_Dan Allah dan Annabi kada ki karanta ba tare da kin biya, da ki karanta ban sani ba come and explain to me cewa baki da halin biya idan nai niya na baki idan banyi ba nabar abuna, it's 500 ba yawa akwai wanda suka bada 300 amma kin zaɓi ki karanta abinda ba naki ba why sister? Tell me why? SIRRIN MU isn't free if you read for free🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️ it's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 for Niger people 84506476_* Kasa ƙarasawa ciki Fannah tayi tsoransa da abinda ya faru tsakaninsu jiya ya shiga dawo mata,amma yaya zatai dole ta miƙa masa abinda ke damunta dole wai sai ta tsaya yaci tukunna zata fito, tayaya zata jure zama kusa da wannan ƙaton mai kwarjini da cika ido haka, fasa zame towel ɗin yay ya shiga taje sumar kansa da handrayer, shahada tayi gently ta fara taƙa ƙafarta zuwa tsakiyar bedroom ɗin a saman wani table ta ajjiye masa ƙamshin sa duk ya gama cika mata hanci har tana jin kamar zata zube masa a wajan ne, ina ba zata jure zama kusa dashi ba da sauri ta ajjiye ta juya zata fita kamar daga sama taji yace "Zahraaah... NIMCYLUV 21/10/2021, 07:24 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 4️⃣3️⃣-4️⃣4️⃣ Tsayawa tai cak tare da runtsa idanunta sbd sunan daya kirata dashi har tsakiyar kanta ta jishi, kasa juyawa tayi bare da amsa kiran da yay mata haka nan kuma taji ta kamu da ƙaunar sunan a ranta, a zcyarta take ƙara maimaita sunan "Zahraaah!!" Very nice name dole tai accepted wannan sunan domin yay mata daɗi a kunne dama zcyrta, shi kansa bai san sanda sunan ya fita daga bakinsa ba, kawai ya samu kansa da furtawa amma yasan ba aibu bane da hakan tunda sunanta ne, idanunsa akan mirror yana kallon faffaɗan ƙirjinsa wanda yake ɗauke da chest beard wanda yake kwance sai sheƙi yake,gaba ɗaya bedroom ɗin ya cika da ƙamshin turarensa wanda kai tsaye zaka ɗauka Arabia Ohud ne zallah,amma idan ka tsai da hankali ka za kaji ƙamshin Maison francis, baya yay ya kwanta akan Wheelchair da yake kai idanunsa a rufe amma yana sane da ruɗewa da tayi shi kuma yana farin cikin yaga da shiga ruɗu idan ta ganshi yana son yaji dalilin hakan, hakan yasa yay calmly muyarsa very slow ga wani sanyi data ƙara sbd kasalan data saukar masa kamar mai raɗa ya ƙara faɗin "Zah..raaah" ya faɗa a ɗan rarrabe kamar wanda bai iya magana ba. Kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta cikin rawar murya tace "ba haka sunana ba ai" ware idanunsa yay waje kafin ya taɓe baki bai kuma cewa komai ba taci gaba da tsaiwa a wajan, sai da ya gaji dan kansa sannan ya kalli cikin mirror ya hangeta tsaye kanta a ƙasa, lumshe idanunsa yay yana sauke numfashi da ajjiyar zuciya ji yake kamar ya dauwama yana Kallonta, babu bambanci tsakaninta da Aljanarsa shiyasa baya jin zai iya yi mata kallon matar mahaifinsa kamar yadda akace, ji yay bakinsa ya buɗe har bai san lokacin daya furta "Can you help me?" Sassanyar Muryar mai daɗi ta daki dodon kunanta,ji tayi saman ba zata iya yi masa musu ba sbd kwarjinin da yay mata gaba ɗaya ya cika mata ido cikar haibarsa, jikinta a matuƙar mace walking slowly ta ƙarasa inda yake zaune ba tare kuma da tace komai ba, shareta yay kamar bashi ne ya kirata ba, yana ta zaune yana Kallonta ta cikin madubi da yaga zata ɗaga Idanunta sai ya janye nasa idon, almost 5mts tana tsaye sai da ta gaji a hankali tace "Gani" ba tare daya kalleta ba cike da nutsuwa yace "Mene?" Turo baki tayi cike da kuma shagwaɓar tasa sabayi a gida tace "To bakai ka kirani ba" cikin son ya jata da hira yace "sure?" Wani juya Idanunta da tayi ya sashi juyawa gareta baki ɗaya ba tare daya shirya ba, hannayensa ya harɗe saman faffaɗan ƙirjinsa ya ɗura mata firgitattun idanunsa wanda suke saukar mata kasala, a wannan time ɗin kallon his wife yake mata matarsa Airahnsa slowly ya miƙa tattausan hannunsa zai riƙe nata sai kuma ya zame hannunsa yana sauke numfashi, idanunsa ya ɗauke baki ɗaya a kasalance Sheikh ya fesar da iska daga cikin bakinsa kafin ya sauke numfashi yace "Sit, let's talk" zamewa tayi a ƙasan ƙafafuwan sa ta zauna tana wasa da hannunta, janye ƙafarsa yay sbd tsigar jikinsa ta fara tashi, kamar wanda ka takura ya fara magana cike da nutsuwa yace "What's your name?" Bakinta na ɗan rawa tace "Fannah" taɓe nasa bakin yay idanunsa akan red henna ɗinta yace "Fannah isn't a real name..," sai kuma yay shiru kafin ya ɗura da faɗin "i think is Faɗimatu, nasan ko a gida ba'a danne rago ance anya domin suna Fannerh ba" saurin kallonsa tayi komai nasa yana da bambanci wato har Fannah ɗin ma nasan dana banne bata ankara ba taji bakinta yace "To ai haka naji ana faɗa" ta ƙare maganar tana ɗan kwaɓe fuska, janye idanunsa yay daga kanta yana ɗan dunƙule hannunsa,kasa mgn yay sbd shagwaɓar ta ba ƙaramin tafiya tayi dashi ba, a hankali yace "Meye ma'anar sunan Fannerh or what?" Watsa hannayenta tayi irin i don't know ɗin nan jinjina kai yay kafin ya rufe idanunsa yace "Imam Ali (AS) yace Manzon Allah (SA) yace: “An kirata da suna FATIMAH ne, domin Allah mai girma da ɗaukaka ya ƴantata kuma ya ƴanta duk mai ƙaunarta daga wuta.” a wahalarce ya ƙarasa maganar duk da cewa baya jin zai gaji da mgn idan akanta ne, yace "Dan haka sunayen ki suna da yawa kamar yadda Imam Hussain(AS) da Imam Jafarus-Sadiq (AS)suka lissafa sunayen a cikin hadisi" nan ma shiru yay yana maida numfashi da sauri ita kuma tace "To Malam yaya sunayen suke" Kallonta yay ta gefen ido sbd sunan da yaji ta kirasa dashi yasu Murmusawa sai kawai ya share yace "Fatima tana da sunaye guda tara ko wanne kuma yana nasa muhimmanci akwai SIDDIQA, MUBARAKA, ƊAHIRA,ZAKIYYA, RADIYA,MARADIYYA,AZ-ZAHRAH,FATIMA" shiru yana kallon wayar hannunta dake haske ganin sunan dake kan wayar yasa ya taɓe baki, itama kallon wayar tayi taga sunan Barrister na yawo harta gama ringing batai picking ba. Granny ce ta kalli Fareeq take tura abinci da sauri tace "Yaya haka kuma kamar dai ana yunwa,ai idan taro naje sai kasa a zagen, gsky ba kyau Ƙarif ka sauya hali" Kallonta yay yana dry yace "Wlh Granny yunwa na keji tun safe banci abinci ba" baki ta kwaɓe tace "Ita Aminan bata baku bane ko me?" Bahaiyya ce tace "Granny tuwon shinkafa tayi miyar wake with cow meat, shi kuma bro baya cin tuwo,kuma wlh ba kiji daɗi ba" tura ɗan kwali tayi gaba tana riƙe haɓa tace "Muhammadur Rasulullah! Au ɗan gidan uban waye kai? Nace Ubanka waye a Nijeriya fisabilillahi? To wlh tayi zcyar musulunci ma data baku abincin gantalalliyar uwarku ta zauna tayi mana, to wlh idan baka nemi yafiyar Amina ba babu ruwana domin kasata wahala" haɗe fuska yay yace "To ba sis ɗina taci ba, kinga anyi 50% kenan, kuma Ubana ai yafi ƙarfin kuɗin tuwo wlh" tana taɓe tace "Ai haba?" Yace "Yeah! Ke baga shi nan kullum nama kike ci ba, ko kina cin tuwon ne?" Bakin zani ta zare ta fara matsalar hawaye tace "A'a wlh babu ruwana uwarka Sandala kake zagi bani ba,kuma ma ai Dacta yace na daina cin tuwo" dry Buhaiyya tayi sosai ba tace komai ba, Barrister dai na zaune rabin hankalinsa yana ga Amaryarsa, Mami ma hankalinta nakan Sheikh ta kalli Bahaiyya tace "Go and call your Anut" Daɗi Barrister yaji sosai kamar Saudat ta shiga ransa, miƙewa Bahaiyya tayi Granny tace "Wazai cinye maki abincin?" Tace "Granny Mami tace na kira Anut Fatima" kujera ta nuna mata tace "Zauna nan, gulmammiya shine aka juya baki sbd an san munafurci ne,yau ɗaya bayan huta ba dg cewa ta kaiwa Imamu abinci shine za'a saka mata ido kamar dai zai cinyeta,ina itama uwace a wajansa ko badan ta kula da Imamun ka aureta ba bani da labari?" Barrister na miƙewa tsaye yace "Haka ne Mama" yana faɗin haka ya haura upstairs yana dailing number ta. Haushi da baƙin ciki ya ishi Mami itama ta miƙe tare da aikawa Granny wata muguwar harara "Ato ba sai dai kuci kanku ba" Fannah take zube a ƙasan ƙafafuwan Sheikh tace "naji guda takwas kuma tara kace" baya yay fuskarsa na fidda annuri domin yaji daɗin yadda ta sake dashi lokaci ɗaya yace "Ki ajjiye ɗayan a gefe soon or later Zaki sani" ɗaga masa kai tayi ya haɗe rai kamar bashi ke murmushi ba yazu yace "Ban so" juya ido tayi wanda yake ƙara narkar da zcyar Sheikh tace "What?" Banza yay mata kafin yay mata nuni da kayan baccinsa, miƙewa tayi ta ɗauko masa da sauri ta juya masa baya sbd bata son ƙara kallon naked body ɗinsa musamman his chest, ganin duk jikinta na rawa sbd bata taɓa ganin mutum haka ba ta nufi ƙofa da sauri zata fita yace "Ohhh Hello!" Tsayawa tayi cak tana rarraba idanu sai da ya gama sanya sleepwear white colour Comfort Apparel, sunyi masa kyau sosai,wasu milk ɗin high Res stock ɗin bedroom slippers ya sanya a ƙafarsa, yana jan ƙwantaccen beard ɗinsa yace "What about my food?" Zaro ido tayi domin tama manta data kawo masa wani abinci tace "To ba gashi nan na ajjiye ba.." wani kallo ya wasa mata wanda yasa tai saurin mgnar yace "wane ya baki ki kawo?" Kai tsaye tace "Granny ce" jinjina kai yay yana lumshe idanunsa yace "And daga nan me tace?" Tana marai-raice fuska tace "tace ne na tsaya har kaci kuma.." sai tayi ta kasa ƙarasa faɗar abinda tayi niyya yace "Uhm speak up" hawayen Idanunta na sakko harga Allah bata skny zama kusa dashi sbd yana cika mata ido tace "wai kona baka kaci" yana fidda tattausan Murmushi yace "Then come back and feed me" baki ta buɗe zatai mgn yace "You're like mother to me, uwa kuma babu abinda ba tayiwa yaronta,If she's still a live" ji tayi mgnarsa ta tsaya mata a rai wai babarsa ƴar itace zata haifi wannan ƙaton how comes? Bata an ƙara ba taji hawaye nabin fuskarta ita sam ba wannan mgnar take son ji ba, me yasa bazai bata wani matsayin nada ban ba ko Sister ko friend ko dai wani matsayin amma kalmar uwa babbace tai mata girma kuma ba zata taɓa zama uwarsa ba, mutsinsa taji kusa da ita da sauri ta juya zata fita yay saurin riƙe hannunta da tattausan hannunsa wanda har wani gumi² yake fiddawa, shiru sukai gaba ɗaya da ƙyar yasa ɗaya hannunsa ya juyo da ita gabansa, ya zamana tai masa tsayi sbd tsayi Muryarsa a ƙasa yace "Zahraaah!!" Kasa amsa shi tayi sbd tension ɗin data shiga yace "Sheikh Imam hamdan Balarabe bai san daɗin uwa ba, bai san yaya ake ji idan ana tare da uwa mahaifiya ba, bansan kalan jikin mahaifiyata ba bare naji ɗumin jikinta, kullum ina tunanin mene yasa tai nisa dani, amma bana da amsa na rasa dukkan wata kulawa ta uwa daya dace ta bawa yaronta ba" shiru yay yana fidda numfashi kafin yaja numfashi a kasalance yace "Zahraaah, you'll be my mother,my sister my friend, i want sharing all my feelings to you" ƙafafuwanta ne suka kasa ɗaukan rawar da jikinta yake mata hakan yasa ta zube a gabansa tana sakin kuka ita harga baya son kalma uwa da yake faɗa mata, kukanta ya keji har ƙasan zcyarsa cikin rarrashi abinda bai taɓa ba yace "Enough! Stop cry friend" a karon farko tun shigowar ta ta ɗaga ido ta kallesa tace "Why Mother? Ni ban haifeka ba kuma bazan haifeka" duk da halin da yake ciki sai da ya ɗan saki Murmushi yace "Yasubuhanallah! Nida man nace kin haifeni ne? And guda nawa kike ma da zance haka,kinsa inta surutu" kwaɓe fuska tayi cike da ƙuruciya tace "tace to bakai kace na zama Mamanka ba" ɗauke idanunsa yay yace "A'a ba ruwan Imam,kawai nace ki zama part of me" da rashin fahimta tace "Sorry! I didn't get you" hannunta ya kama yana murza tafin hannunta sbd laushin da yaji kafin a hankali ya ɗura saman shafaffan cikinsa yace "May be you'll understand" zame hannunta tayi tace "Sorry!" Ta faɗa tare da tashi ta ɗauki tray ɗin tazo har gabansa ta ajjiye saman carpet, bai kulata ba ya zame kaɗan tare da zama a ƙasan carpet ɗin buɗe komai tayi ganin ya rufe ido tabi haɗaɗɗiyar fuskarsa da kallo, idan kyau ne an sallama masa yana da wani irin sihirtaccen kyau wanda kai tsaye ba zaka iya gane da wanne ƙabila yake kama ba kamar dai shi ɗin ruwa biyu ne (Half -caste) ga wasu zara-zaran gashin ido da yake dasu (Eye's lashes) sai wani dugun hancinsa wanda ya tsaya dai-dai ma dai-dai cin bakinsa wanda yake da wasu laɓɓa masu kauri wanda suka kasance jajaye kamar wanda yake shafawa jambaki, sai sajensa wanda yaywa gefen fuskarsa ƙawanya, ji tayi yace "Idan kin gama kallon feed me" cike da kunya ta ɗauke kanta tana ɗan ɓoye fuskarta a cinyarta, buɗe ido yay yace "Am your son ring? So kina da damar kallo na ai" turo baki tayi tare da shura ƙafa zatai birgima yay saurin riƙe hannunta yana bin lallan da kallo yace "meye wannan?" Tace "We called it henna" taɓe baki yay yace "ki daina ba kyau" tace "to" spoon ta ɗauka zata ɗebo abincin yace "bana ci da spoon" kallon ban gane ba tayi masa yace "Alrdy night yanzu ki ban ki tafi ki kwanta" bisa dole tasa hannun dan ba zata iya da gardamarsa ba laumar farko ya riƙe yatsunta a bakinsa ita kuma ta kasa mgn sbd faɗuwar gaban daya sameta tasan abinda take ya huce ƙa'ida amma bata san lokacin da zcya da kuma ƙaunarsa suke rinjayarta ba, yatsun hannunta ya fara bi da kallo kafin ya lumshe idanunsa ba tare kuma saya sani ba ya tura yatsun duk a bakinsa ya shiga tsotsa, jikinta ne ya ɗauki rawa sam ba zata iya da kalar nasa salon ba da sauri ta zare hannunta tai waje da gudu, da gajiyayyun idanunsa ya bita dasu a zcyarsa yana aiyana ƙuruciyarta, lumshe idanunsa yay daman ba wata yunwa ya keji ba. Tana fita ta nufi bedroom ɗinta tare da faɗawa kai ta saki wani kuka wanda ita kanta bata san dalilin yinsa ba, sai da tayi kuka mai yawa kafin bacci ya ɗauke ta,Mami kam baƙin cikin Granny yasa ko fitowa bata sakeyi ba, shima Barrister gudun mgnar Granny yasa ya kwanta yana juyi a gadonsa yasu ya kwanta tare da Fatimansa amma dole sai hqr yana ga dole ya shirya masu wata tafiyar yabar garin da ita kawai zaifi masa. Washe gari ƙin fitowa tayi sbd bata son haɗuwa da Sheikh da kuma baban Sheikh, Bahaiyya da kanta takai mata breakfast Mami tun safe ta tafi gidan wata Aminiyarta Kubra. Sheikh ne da Arjun zaune a babban Parlo a hankali Sheikh yake mgn "Arjun try to understand me, ina son fara zuwa Company ne badan ka gaza ba,kawai zaman gidan" jinjina kai Arjun yay yace "I understood, when zaka fara zuwa?" Idanunsa a rufe yace "I think this week in sha Allah!" Murmushi Arjun yay yace "Buddy naga ka fara sauyawa ba miskilanci ba haɗe fuska meye labari? Nasan duk sanda kayi haka akwai wani abu" banza yay masa kana yay signing akan file ɗin da Arjun ya basa "Ina Mom ɗin taka?" Kamar bai gane abinda yake faɗa ba yace "Wa kke mgn?" Yace "Anut Fatima mana" taɓe baki bai ce komai ba. Mami ta kalli Kubra tace "Wlh zcyta gaf take da fashewa ina son sweet Imam fiye da yadda baki tunani, ina sonsa bana jin zan bari ko wacce mace ta raɓesa" dry Kubra tayi tace "Ke kam Saudat kina da son zcyarki kiso ɗa kuma kiso Uba" Mami tace "Ba zaki gane ba, Ina kishin Barrister ne sbd wani Babban dalilin bana son ya ƙara samun wata zuri'a bayan wacce yake da ita,kisan rabin kuɗin Barrister na Sheikh ne, da zarar kuma na samu ciki da Sheikh kinga da kuɗin Uban dana Ɗan duk mallakina ne" Kubra tace "meye damuwar to?" Shiru Mami tayi sai kuma tace "Granny ne itace matsalar" miƙewa Kubra tayi tace "I have an idea". Wajan 11 na dare tana kwance sanye da kayan bacci sai ƙamshi take taji an turo ƙofar ɗaga ido tayi taga Barrister cikin kayan bacci da sauri ta rufe idanunta yana dry yace "Wake Up Wify nasan idonki biyu" ya faɗa yana zama kan bed ɗin tare da zame duvet ɗin data rufe jikinta dashi, Kallonta ya farayi nan da nan yaji yanayinsa ya sauya ita kuma da sauri ta miƙe tsaye tare da sauka ƙasa, tashi yay har zuwa wajanta yace "nayi kewarki nayi rashin jikinki two days My Sweet" baya ta farayi tana faɗin "pls don't touch me" har inda take ya tsaya kafin yasa hannu ya jawota jikinsa da sauri ta ƙwace jikinta ya hau rawa idanunta suka firfito waje, yana matsuwa wajanti tana ja baya sbd ganin ya zama wata siffa mai ban tsoro ga wani manyan harshe da idanunsa da suke lililo a waje, ya zame mata kamar dodo ko Aljani wata razananniyyar ƙara ta saki tare dayin waje da gudu, tsoran data bashi yasa ya nufi wajan ƙofa ya rufe da key jikinsa na bashi aljanu gareta, tsakiyar Parlo ta tsaya jikinta ya ɗauki rawa ta hau surutai ga parlon duhu babu kowa, baya tayi zata faɗi yay saurin miƙa hanunsa ya fisgota zuwa jikinsa tana sauke jikinsa numfashinta ya tsaya, runtsa idanunsa yay da ƙarfi kafin ya mannata a ƙirjinsa... Dan Allah kiji tsoran Allah ki biya kafin ki karanta via WhatsApp number for impormation 08119237616 ga ƴan Niger 84506476 NIMCYLUV 21/10/2021, 07:26 - 🤔🤔: *_NLUV💞_* 4️⃣5️⃣-4️⃣6️⃣ Fisgewa take ƙoƙarin yi sbd rawar da jikinta yake, ƙara shigar da ita jikinsa yay sbd lura da yay kamar bata hayyacinta, sai da ya tabbatar ya matseta a jikinsa no way da zai bata damar guduwa, rufe idanunsa yay yana mmkin ƙarfin ta sai kuma yay shiru yana nazarin wani abu, surutun data keyi ƙasa² yasa ya tsaida hankalinsa waje guda, slowly kuma ya ɗura kunansa a saman bakinta sai a lokacin yaji abinda take faɗa "Bana so, kada ka taɓa Ni,Ni bana sonka wlh ka taɓa ni sai na kasheka,ni bakai nake so ba Malamina shine rayuwata kuma shine farin ciki na, kuma dashi zan rayu" a sanyaye ya cire kunnansa kafin yaja idanunsa ya rufe ya shiga nazarin mgnarta,wane bata so? Waye kuma Malaminta, ji yay kalmar Malamin ta ɓata masa rai, yana riƙe da ita har jikinta ya fara saki gyara zamansa yay yana jin yadda take shigewa jikinsa, a taushashe muryarsa very slowly yace "Zah..raaaah!!" Ya kira sunan a ɗan rarrabe kamar mai jin tsoran faɗa, Shiru tai masa yana kallon yadda take zare ido ta raguwar hasken dake parlon, hannu yasa zai zameta a jikinsa tai sauri riƙesa tana maƙale sa duk ta wani marai-raice fuska, ɗan Murmushin gefen baki yay domin sai yanzu ya fahimta, haɗe rai shima yay yasa dukkan hannunsa ya zameta a jikinsa idanunsa a saman fuskarta, a kasar ce ya kuma cewa "Zahraaah!!" Ƙin amsawa tayi sai da ya sanya tafin hannunsa ya ɗan bugi tsakiyar kanta da sauri tace "Auchhhhhi" cikin dakakkiyar murya yace "Ke dallah" kwaɓe fuska tayi tace "Ba ita bace" kai tsaye yace "ita wa?" Zare ido tayi shima ya zare mata nasa fararen idon yace "Uhm wace?" Ɗauke kai tayi tace "Kawai ba ita bace,ni kuma basai kaji sunana ba,dan Allah ni ka sakeni bana son zama kusa dakai" baya yay ya kwanta jikin kujerar still hanunsa na riƙe da fuskarta yace "Why?" Shiru tai masa yatsarsa yasa ya daki goshinta saurin riƙe hannunsa tayi tana faɗin "Wayooo!ka daina dan Allah ni kawai taimako nake" shima ya riƙe nata hannun yace "Why are you helping her?" Tace "It's our secret" taɓe baki yay cikin serious talking yace "Let's talk wace ke ɗin? tunda kince ba Zahraaah bace" kamar zatai kuka tace "is not your business Sheikh Imam hamdan Balarabe, ina jin kunyarka da nauyinka yasa nake amsa maka dukkan tambayar ka,amma kayi hqr zan bar jikinta yanzu sai lokacin da zan ƙara kawo mata ziyara yayi" da sauri yace "No!! Wait please, ko kin tafi kin san zan iya kiranki ko?" Da sauri ta ɗaga kai tace "Na sani wlh hakan yasa banyi maka wata gardama ba,amma bana jin zanci gaba da musu dakai shiyasa zan tafi na baka waje, kai ɗin babban mutum ne kada kima da kuma daraja a dukkan idanun Bil Adam dama Jinnu,nasan ko yanzu kai niyyar ganin bayana zaka iya sbd ƙarfin ilimin da kuma sanin addinin da abinda Allah ya sharaɗanta" yana cije bakinsa kamar bazai mgn ba sai kuma yace "Ke kuma baki sani ba ko?" Shiru tai masa tsawa ya daka mata yana fito da idanunsa waje yace "Look at into my eyes and tell me who are you?And meyasa kike a jikinta?" Jikinta na rawa tace "Nifa Musulmace kawai taimako sanyi,nasan me nake bazan taɓa zama mai cutarwa a gareta ba believe me" Calmly yay dan ya fahimci taurin kai ne da Aljanar yace "Ok! Wacece ke?" Ƙin mgn tayi hannunsa ya ɗaga zai kuma dukanta tayi saurin yin atishawa sai kuma jikin Fannah ya saki ta faɗa jikinsa tana fidda numfashin wahala. Lumshe idanunsa yay ya shiga sauke ajjiyar zuciya kafin ya buɗe idon ya sauke kallonsa a saman fuskarta bin ƙyakkyawar fuskarta yay da kallo sai yanzu ya ƙara ganin zallar ƙuruciyarta da kuma tarin kamanin da suke da Aljanarsa, wani sassanyan murmushi ya sauke a hankali kuma yace "Zahraaah mai gayyar aljanu". Barrister tsoro ne ya cikasa sam baya ƙaunar aljanu hakan tasa ya gagara yin ƙyakƙyawan mutsi, yana ta tsaye kamar wanda aka dasa, jin baiji mutsin komai ba yasa ya buɗe ƙofar a hankali yana tura kansa wayam yaga parlon da sauri ya haura upstairs yana sauke numfashi, lokacin daya shiga bedroom ɗinsa ya fara tunanin mafita bazai jure zama da ita haka ba,idan kuma akace tafiyarsu zata zama a hakane duk sanda ya nemi kasancewa da ita sai tayi aljanu Tabbas da matsala, shiru yay kafin yaja y a bai yane yace "What should I do?" Ya faɗa yana kallon saman ɗakin nasa Murmushi kawai yay a haka bacci ya ɗauke sa. Cikin tare ta fara mutsawa jin wani sassanyan ƙamshi ya daki hancinta wanda ya haifar mata da mutuwar jiki, ƙoƙarin zare jikinta tayi hannunta ya sauka a ƙirjinsa wanda yake ɗauke da gashi da sauri ta ɗauke hannunta sbd tsigar jikinta data tashi cikin ranta take faɗin "Astagafirullah!" Ba ƙaramin mmki tayi ba Lokacin data ganta a jikin Sheikh, mene ya kawota wajansa yaya akai sukai bacci tare? Ganin bata da amsa yasa da sauri ta Miƙe tare da shigewa falt ɗin ta, tana barin parlon ya mirgina tare da jawo pillow ya maye gurbin ta dashi,domin dama ba bacci yake ba bai kuma san yadda zai bacci tana jikinsa ba, da yana da ƙafafuwan takawa dama da tuni ya barta a wajan ya shige part ɗinsa, kasancewa da ita a yanzu ba ƙaramin da gula masa lissafi yay ba, duk yadda yasu ya samawa kansa nutsuwa ya kuma cire tunaninta daga ransa abin faskara yay, gefe guda kuma idan ya tuna matsayinta a garesa sai yaji duk ya sare baya jin kuma zai jure ganinta a haka, me zai yi? Ina zai sanya kansa? Mai yasa zcyarsa ke ƙwaɗaita masa ita bayan ita ɗin ta haramta a garesa wacce irin HARAMTACCIYAR SOYAYYA ce wannan? Ga ƙoshi kuma ga kwanan yunwa, hannunsa yasa ya dafe ƙirjinsa dake masa zafi yana jin kamar ciwonsa na neman tashi kodai ya samawa zcyarsa abinda take muradi kodai ya nemi mafita,yasan illar son matar wani amma shi tasa ƙaddarar itace MATAR BABANSA, har aka kiran farko na Subhi idanunsa biyu ana idar da sallah ko samun zaman karatu da azkar bai ba sbd baccin dake cin Idanunsa haka ya bawa basu jiransa karatu hqr yana kwanciya kuma wani wahalallan bacci ya ɗauke sa cike da tunaninta. Washe gari da safe duk yadda Barrister yasu ganin Fannah ƙin fitowa tayi da yay tunanin zuwa wajanta sai ya fasa sbd tsoran abinda zai faru, misalin 10 bayan ya gama shiryawa zuwa unguwar da zashi tunda Weekend ne ba zuwa wajan aiki, ganin babu kowa a parlo yasa ya nufi bedroom ɗin da take ciki na flat ɗin da aka bata, walking slowly ya ƙarasa bakin ƙofar sosai yay mmkin jin ƙofar a buɗe kamar mai jin tsoran wani abu ya tura ƙofar, tun daga baƙin ƙofar yaji dadɗan ƙamshin airfreshner da kuma wani turaren AL'AJABU daya gama cika ɗakin tana kwance saman bed ta rufe jikinta da duvet sai sharara bacci take cike da nutsuwa time to time kuma tana sakin ajjiyar zcy da kwaɓe fuska kamar zatai kuka, zama Barrister yayi a bakin bed ɗin yana ƙarewa fuskarta kallo wacce ta ƙara kyau da haske ga kitson da akai mata duk ya barbazo a saman fuskarta hanunsa ya miƙa zai shafi fuskarta sai kawai ya fasa, fita yay not too long ya dawo ɗauke da jotter da biro a hanunsa zama yay akan stool ya fara rubutu kamar haka: *_Dan Allah masu karanta littafina free ko tausayawa Ni'eemerh ko ji tausayin Nimcyluv,Ni daka karanta ban sani gwamma kazo ka faɗan ba tsada via WhatsApp number 08119237616 for more information_* _♥You need to get out of my thoughts and into my arms where you belong. Please come back! And you know what My Sweet Fatima i missed your sweet lips and tongue wlh i can't imagine how happy am i lokaci da nake jikinki nayi rashin dadɗan jikinki, Hey you.._ _I really wish you were here next to me in bed..._ _Just thought you should know you're my favorite dirty thought! Uhm Fatima Too bad you’re not here right now… oh, wow, I better stop thinking about this, or I’ll never get to sleep get ready ki shirya kiyi ado mai kyau zan dawo na kasance dake a cikin wannan ranar bye miss you!"_ Yana gama rubutawa ya ajjiye mata a ƙasan pillow yana sakin Murmushi shi kaɗai yasan abinda ke rasa game da ita, bakinsa yay kaɗan wajan kwantanta yadda ya kejin sonta da ƙaunarta duk yadda zai faɗi soyayyarta a zcyarsa wlh yay ƙarya, shafa ɗan tumbinsa yay kana yaja shekararrun ƙafafuwansa ya fice daga cikin ɗakin, kai tsaye ya fice daga cikin gidan zuwa babban compound ɗin wajan motarsa ya nufa Honda Amaze wacce ta kasance ash colour da gudu yaja motar zuwa wajan gate tun kafin ya ƙarasu gate keeper ya buɗe masa gate ɗin da wani irin gudu ya harba motar zuwa kan titi. Kallon mutumin dake gabansa yay cike da damuwa yace "Alhj Kamal kafi kowa sanin wanene Hamdan tun kafin yanzo,then babu wanda yasan sirrina fiye da kai kusan dukkan abinda nake yi ba nayi sai da sanin ka wani abun ma shawararka tafi yawa, kace na ƙara aure Finally na ƙara amma ina ganin kamar matsala na shirin faruwa" Murmushi Alhj Kamal yay kafin ya kalli Barrister yace "Wai ina basirarka Barrister? Ina tunaninka tun kafin na iya shirya wani abu ka rigani iyawa sbd kai Barrister ne kasan hanyar da zaka sauya abu kuma cikin sauƙi ya tafi yadda kake so,abu nawa kakeyi wanda kaga ci gabansa sai wannan zai baka matsala?" Ya ƙare maganar yana kallon idon Barrister fesar da iska Barrister yay yace "Ba zaka gane ba, ina buƙatar samun iyali masu yawan gaske,amma tunda na fahimci Saudat tana da nata manufar a kaina naji bana ƙaunar haɗa zuri'a da ita" Murmushi Alhj Kamal yay kafin yace "Yanzu yaranka nawa Barrister?" Kallon ban gane nufinka Barrister yaywa Alhj Kamal, dry Alhj Kamal yay yace "No! Is simple question ai answer me" kai tsaye Barrister yace "Guda uku Imam, then Fareeq then Bahaiyya why are you asked?" Baya Alhj Kamal yay kafin yace "Kana yaudarar kanka" "dame fa?" Ka faɗa ya ɗaga kafin yace "Kawai na baka assignment go and searching ƙilan ka fahimta, amma dole ka ɗauki ma taki akan Granny" miƙewa Barrister yay yana faɗin "Mahaifiyar tawa kake tunanin zan iya yi mata wani abu to ko Sheikh dana Haifa bazan iya yi masa wani abu ba bare uwar data haifan" dry Alhj Kamal yay yace "I see" yana faɗin haka Barrister ya mara masa baya. *Lebanon/Beirut* Beirut Rafic Hariri international airport! A nan jirgin yay saukar ungulo da sauri² wasu manyan securities with soldiers suka fara sakkowa daga jikin private jet ɗin daya sauka a cikin airport ɗin, daga baya kuma wasu manyan mutane irin ƴan Majalisso da zuwa manyan sakarori na ƙasar, gaba ɗaya tsayawa sukai a gefen stairs ɗin jirgin suna jiran sakkowarsa, yana zaune a saman kujerar wacce ya maƙala belt a jikinsa, daily trust ɗin hanunsa a ajjiye a gefe kafin zame belt ɗin a jikinsa cike da nutsuwa ya miƙe tsaye yana taka ƙafafuwansa, zuwa wajan jirgin, gaba ɗaya securities ɗin suka game tare da saita bindigoginsu sbd tsaro, magidancin mutumi ne wanda a ƙallah zai ya ɗaukan shekaru wajan 75 a duniya yana sanye da farar shadda white colour ƙal a jikinsa mai santsi wacce ake kira (London King) yay kyau sosai He's dark-skinned yet handsome, *GOVERNOR DEEDAT* kenan sauka ya fara cike da nutsuwa Lumshe idanunsa yay lokacin daya shaƙi daddaɗar iskar ƙasar sa, kafin ya fito tuni wata ƙaramar mota mai ƙyan gaske tai parking gabansa ba tare daya kalli kowa ba ya shige back seat ya zauna yana mai duban agogon hannunsa Iwc Schaffhausen, kewar iyalansa ita tafi damunsa a yanzu, kai tsaye suka nufi Government House, bai daɗe a taron ba ya ƙara shiga mota ya nufi gidansa dake *Hamra Street* unguwar manyan masu kuɗi da kuma tarin ilimi wani tangamemen gida motocin suka fara tsayawa da gudu wani babban soldier ya buɗe gate ɗin gaba ɗaya motocin suka fara shiga cikin babban compound ɗin, bai tsaya jira an buɗe masa ya buɗe murfin motar ba ya buɗe da sassarfa ya nufi wani gate wanda yana dosar gate ɗin ya buɗe da kansa, cikin babban parlon ya shiga babu kowa ciki sai ƙarar A.c wajan sides biyar ne a tsakiyar parlon upstairs ƙaramin parlo'n dake upstairs ya tsaya fuskarsa cike da farin ciki yace "Your Dad is back my lovely daughters" da gudu Anushka da Aditya suka miƙe daga jikin mahaifiyarsu suka nufi wajan DEEDAT suna faɗin "yeee Dad Oyoyo" durƙosawa yay tare da rungome yaran nasa a jikinsa yana sakin Murmushi, kallon wacce take tsaye kasan yay ya miƙe tsaye yana sakar mata lallausan murmushi yace "Madam come closer" tana dry tace "Wlcm back Ur Excellence" jawota yay ya haɗa da twins ɗinsa ya rungome yana jin farin ciki na ratsa zcyarsa. Granny ta kalli Fannah dake zaune gabanta tace "to banda ke ɗin wazai kulamin dashi dan Allah? Nidai Barista ya gaman komai daya kawoki gidan nan, gashi sai na kwanta na runtsa sbd kina kula da Imamu,bawai gulma ba wlh Sausaz take ko Sandala banda sata da yawo babu abinda ta iya, kinga ke na faɗawa balle ace gulma nayi" ita dai Fannah jinta kawai take domin tunda ta farka ba taji mutsin Malaminta ba,kamar Granny ta shiga ranta tace "Yooo shima baya zama gantalalle ba, ya tsiri zuwa ofis kamar dayi yake,ina dalili Ni Faɗimatu salan yaja min zagi ace na sallama ɗa a duniya, kuma...," Saurin yin shiru tayi sbd haɗa ido da sukai da Sheikh wanda yake murza Wheelchair ɗin sa, miƙewa tayi tana faɗin "Lalle marhabin da Imamu,yanzu nake faɗin shiru duk hankalina ya tashi" Murmushi kawai ya sakar mata ba tare da yace komai ba, ta gefen ido ya kalli Fannah dake zaune kanta a ƙasa, marai-raice fuska yay yace "Granny Am hungry ina jin yunwa sosai" tura Wheelchair tayi tace "Yoo ba dole ba, ace tun safe bakaci komai ba gashi kai baza kaci abincin kowa ba,sai yanzu dana samu kake cin na wannan ƴar albarkar shiyasa tun ɗazo nace ta shirya maka akan tire, muje ka watsa ruwa saita miƙa abincin ni zan leƙa gida Amina naji ance Huda ba lfy" ita kaɗai take mgnarta babu wanda ya tankata har suka isa cikin flat ɗinsa, a gurguje ya watsa ruwa Granny ta bashi Three gauthier ko singlet bai samu damar sawa ba, ya dawo ƙaramin parlonsa da zama wanda yake mai kyau da tsari, yana zaune saman carpet ya miƙar da ƙafafuwansa yana jin daɗin iskar dake kaɗasa har wani bacci² ne ya fara ɗibansa, tun kafin ta ƙarasa shigowa turarenta ya sanar masa da zuwanta, bakinta ɗauke da sallama kanta a ƙasa ta shigo, can ƙasa ya amsa ba tare daya kalleta ba, har gabansa ta tsaya kana ta ajjiye masa tray ɗin a gabansa dan ta lura yafi jin daɗin cin abinci a ƙasa, bata san lokacin da bakinta yace "Sannu da zuwa" ba sai jin Muryarsa tayi a kunnanta yana faɗin "thank you" buɗe ido yay ya sauke a kanta ganinta zata fita yace "Mummyna" turo baki tayi nan da nan Idanunta ya ciko da hawaye ta fara ɗaga ƙafa tana saukewa wacce ita kanta bata san tayi ba cike da shagwaɓa tace "Nifa bana so" muryarta ya kwaikwaya yace "Ni kuma ina so" zama tayi a wajan tare da saka masa kuka saurin danne dryarsa yay yace "Am sorry" tace "to bakai bane" waro idanunsa yay tace "Wayyoooo" ɗan haɗe fuska yay yace "what" turo baki tayi tace "ba kaine ka zaron ido ba" lumshe idanunsa yana jin kasala na saukar masa yace "kefa uwace a gareni why are you acting like child?" Tace "Nima ban sani ba amma ni ban haifeka ba" yana ɗan jan sajen fuskarsa yace "Uhm Zahraaah" shiru tai masa gaba ɗaya attention ɗinsa ya mayar kanta yace "Zahraaah!!" Ya kira sunanta a hankali kasa amsawa tayi yace "I think i fall in love" da sauri ta kallesa ya ɗaga mata kira Shiru tai masa yace "Amma ina jin tsoran ban iya soyayya ba ban sani ba ko zata soni" ji tayi zuciyarta na bada sauti ƙoƙarin daidaita nutsuwarta tayi tace "to" yana sauke numfashi yace "Ki ɗauka kece budurwa da nake so, zan gwada yin soyayya dake idan kince na iya then sai na faɗa mata" kanta a ƙasa tace "Tayaya ni bangane ba kuma mene haɗi na da budurwaka?" Murmushi yay yace "Akwai kefa uwace gareni sannan ita kuma sirikarki, kawai ki ɗauka ni saurayin ki ne ba ɗan ki ba, nima zan ɗauke ki matsayin budurwata ba uwa ba" tace "kana ganin ba matsala?" Yace "Yeah! Just 2week idan kikace na iya soyayyyar shkknan zanje na gayawa Rayuwar Sheikh Imam hamdan Balarabe" hawaye ne ya taro Idanunta tace "Your request accepted" yana rufe ido yace "انت جميلة وانت عقيلة الله يدومك في السرور كما تكون دائما في السرور في حياة "الشيخ إمام حمدا بلاربي" Kallonsa tayi tace "me kace" ba tare daya kalleta ba yace _"Kina da kyau da hankali, Allah ya dauwamar dake cikin farin ciki,kamar dai kika zama farin ciki a rayuwar SHEIKH IMAM HAMDAN BALARABE"_ ji tayi soyayyarsa ta ƙara nunkuwa a zcyarta anya zata iya wannan game ɗin, ba tare data ankara taji yasa hannu ya jawota jikinsa yana faɗin "Come closer my Kurratul aini.... It's 500 via 0116886423 Sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 SIRRIN MU isn't free book..if you read for free🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️ Ai hutun ƙarshen mako lfy🌚🤕 22/10/2021, 10:30 - 🤔🤔: *SM💞* Da sauri Fannah ta zare jikinta daga cikin nasa tana sauke numfashi tare da sunkuyar da kanta ƙasa tana jin yadda zcyarta ke harbawa da sauri, ta rasa wanne irin so da ƙauna ta kewa Sheikh,mgn yake amma gaba ɗaya hankalinta baya tare da ita, sosai take jin zafi da baƙin cikin zancan budurwar da yay mata, bata jin zata iya wannan game ɗin sam ba zata iya abinda zai iya zama illah ga zcyarta ba, sunkuyar da kanta tayi ƙasa tana ƙara jan numfashi ji take kamar ta fashe masa da kuka ko hakan zai sanya ya janye batun budurwar,ko dai za tace masa yay hqr da budurwar ne? Amma mene hujjarta? Akan wanne dalili zata hanasa? ko dai ta faɗa masa abinda yake zcyrta game dashi, kai ina bazai yiwu ba ita ɗin ta haramta sam a garesa matsayin matar uba take a wajansa, ba tare data sani ba tace zube a ƙasan carpet ɗin ta shiga rera kuka kamar yarinyar goye, dukkan abinda take yana jinta kuma yana sauraran yadda take kukan, shi mmkin yadda kuka bai mata wahala yake ganin yadda take kukan da gaske yada yaji sam bazai iya jurewa ba idan yace zai jure jin kukanta to tabbatas zcyarsa zata iya bugawa, calmly yay yace "Zahraaah!!" Ƙin amsawa tayi sai shassheƙar kuka da take, yana kallon yadda ƙirjinta ke up and down alamar kukan yaci ƙarfinta,cikin ƙasa da Murya yace "What i have done to you?" Ya faɗa Sounding emotionally worried, girgiza masa kai tayi tana kuka shiru shima yay mata ba tare daya ƙara ce mata komai ba, almost 30scnds tana kuka kafin ta gaji dan kanta tai shiru ta shiga sauke ajjiyar zuciya, Kallonta ya ƙarayi, He don't actually know the meaning of the feelings Amma yasan cewa yanzu yasan komai yana jin zai iya jajircewa akan abinda ya keji game da ita,Amma yasan it deeply hurts some hidden parts da ke ƙarƙashin zcyarsa, ciki yanayi na sarewa yace "Idan mgnar game ɗin mu ne ke saki kuka, I'll cancelled it" girgiza masa kai tayi kuka na son ƙwace mata tace "No at all" "then why are cry?" Ya tambaya ba tare daya kalleta ba,kanta a ƙasa tace "Kawai ina jin tsoro ne, i think dani dakai kamar zamu tafka babban kuskure ne" ya gane me take nufi sarai sai ya share ba tare daya tanka waccen mgnar ba yace "You can go" kamar zatai kuka ta kallesa tace "Abincin fa?" Yana ya mutsa fuska yace "Ni! Am okey zaki iya tafiya dashi" share hawaye suka ƙara sakko mata tana sharewa tace "Amma ai ba kaci komai bafa" tashi yay ya zauna sosai ya kalli cikin Idanunta yace "Ai bakiso naci ba" girgiza masa kai tayi wani kukan na shirin ƙwace mata yay sauri cewa "Don't ever trying" haɗiye kukan tayi ta shiga sauke ajjiyar zuciya, ba zata gane ba da zata gane da batai wannan kukan ba domin ji yake kamar zcyarsa zata tarwatse sbd yadda kukanta yake taɓasa, Lumshe idanunsa yay kana ya ƙara buɗe su akanta cikin ƙasa da murya alamar rarrashi yace "Kin gama kukan?" Kamar wacce yace tai kuka haka ta ƙara fashewa da kuka numfashinta har wani maƙalewa yake, hannunsa yasa a hankali ya matsu da ita kusa dashi tare da ɗura kanta a saman shoulder sa yace "Cry! Cry! Yi kuka idan hakan zai sa kiji daɗi" hannu tasa ta riƙesa sosai ta shiga rera kuka kamar ranta zai fita, yadda take kukan sauka rantse da Allah cewa wani nata ne ya mutu, bai kulata ba bai kuma hanata kukan ba sai bayan ta kawai da yake bubbugawa kamar ƙaramar yarinya, Shiru tayi ta shiga sauke ajjiyar zcy tana jan numfashi, ɗago kanta yay yaga inda hawaye suka ɓata mata fuska, a sanyaye yasa tattausan hannunsa ya shiga share mata hawaye yace "Kin gama? I mean kin gamsu da kukan da kikai?" Kaita gyaɗa masa yace "Sure?" Ta ƙara gyaɗa masa kanta, bai ƙara magana ba ya goge mata fuskarta tass,kana yay baya ya kwanta jikin kujerar yana fidda numfashi tana jan numfashi tace "kaci abinci" a hankali ya buɗe gajiyayyun idanunsa wanda suka sauya kala yace "Kina so naci ne?" Da sauri ta ɗaga masa kanta yace "Ok Promise me?" Tace "Me?" Yana kallon fuskarta yadda ta ƙara yin jaaa sbd kukan da tayi yace "Har abada har gaban abada ba zaki ƙara yin kuka ba,har sanda Ubangiji zai ɗauki ranki baza ki ƙara zubar da hawayenki ba, Promise me Zahraaah!" Kallonsa kawai takeyi domin bata tsammaci abinda zai faɗa kenan ba, hanunsa taji a cikin tafin hannunta ya ƙara cewa "Promise me Zahraaah baza ki ƙara kuka ba? hawayenki bazai ƙara zuba komai daɗi komai wahala, You're not my Mom anymore you're my girlfriend,dan haka kimin al'ƙawari" bata san meke bin fuskarta ta ba ita dai kawai taji zafi da ɗumin abu na bin fuskarta hawayen daya goge ta ƙara tabbatarwa kanta cewa wani kukan take "Cry again" ya faɗa cikin damuwa da ƙonar rai me take nufi dashi ne? Ko kuma so take ta kashesa da kukanta sbd data san baya ƙaunar jin kukan nata, iska ya fesar Fannah kam ji tayi zcyarta ta tsinke har bata sanin sanda hawayen ke zuba daga cikin idanunta data tuna mgnar budurwar da yay sai taji hankalinta ya tashi Tabbas ita ɗin mai raunice a kansa tana masa son da baki bai isa ya faɗesa ba, Muryarsa taji yana faɗin "Ok Game ɗin ne baki so? To an fasa zanje da kaina na gayawa farin ciki na cewa ina sonta, be happy" kai ta fara girgizawa tana jaa baya sai kuma ta tashi da gudu tai waje tana toshe bakinta sbd sabon kukan da yazo mata, binta yay da ido yana jin babu daɗi a ransa yay zai da sabuwar ƙaddarar da taiwa rayuwarsa kotse ne? Mai yasa zcyarsa take son abinda bai dace dashi ba,mai yasa so da ƙaunar matar mahaifinsa nasa suke barazana da lfyar jikinsa ne, sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya yay tare dasa hannu ya ture tray ɗin abincin, kwanciya yay flat saman carpet tare da rufe idanunsa da tafin hanunsa sosai yake son yayi tunani akan sabon abin daya shifa'u rayuwarsa har yake son wargatsa masa dukkan wani jin daɗinsa. Fannah na fita ta shige bedroom ɗinta jikinta duk rawa yake a ranar kuka babu kalar wanda ba tayi ba, tunanin ya toshe ta gagara samawa kanta mafita bare ta samawa Malaminta mafita,zata iya tayashi neman abinda yake so indai zai farin ciki amma ita a wanne matsayi take haka zata ƙare Rayuwata bata wani ƴanci, shikenan ba zata taɓa samun abinda zcyarta keso ba?. Washe gari tun 7Am Arjun yazo suka nufi Company yana zaune akan kujera yana duba wasu files hannu yasa kana ya miƙawa wani P.A baya yay tare da kallon Arjun yace "Mene?" Shima Arjun yace "Naga har wajan 6 baka da niyyar tafiya shiyasa nazu naga ko lfy?" Taɓe baki yay baice komai ba dan bashi da abin cewa Arjun yace "Wannan halin naka shike ban haushi kai idan bakai kayi niyyar mgn babu wanda ya isa kai masa" idanunsa a rufe yace "idan sauri kake ajjiye min key ɗin" da rashin fahimta Arjun yace "As how? Bangane ba zaman me zakai a nan?" Banza yay masa yaci gaba da duba tarin files da suke gabansa cike da damuwa da kuma tuhuma Arjun yace "Akwai matsala ne a gidan?" Nan ma shiru yaywa Arjun tsaki Arjun yaja tare da miƙewa fuuuu ya fice daga office ɗin yana mai jin haushin halin Sheikh, kamar yadda Sheikh bai tafi gida ba haka Arjun ya kasa tafiya nasa gidan yana kallon wayarsa na ringing cikin sanyin jiki ya ɗauka daga can ɓangaren Aliyah tace "Me ajjiye min mijina a waje haka?" Murmushi yay mata kamar tana gabansa cikin son danne abinda ke ransa yace "My! Kinyi kewata ne?" Haɗe fuska tayi tace "faɗa ma ɓata baki ne now tell me mene ya tsayar dakai?" Ajjiyar zuciya ya sauke yace "Wlh buddy ne na kasa gane kansa,kallo ɗaya nai masa nasan cewa yana cikin damuwa,abinda yafi damuna yadda yaƙi tfy gida,bana son barinsa ban san mene zai iya faruwa dashi ba" jinjina kai Aliyah tayi tace "Ban san wanne irin haline da Sheikh ba,mutum sarai yana da damuwa amma ya ajjiye ta a cikinsa bai san cewa damuwa bata mgni ba?" Cikin damuwa Arjun yace "haka yake tun muna yara,yana tunanin zai iya handle dukkan abinda yake damunsa,na rabu dashi nasan idan abun yafi ƙarfin sa da kansa zai faɗa min" wahalallan numfashi Aliyah ta sauke tace "Allah sarki! Allah yaye masa abinda ke damunsa ya kawo masa sauƙi" cikin jin daɗi Arjun yace "Ameen² thank you My!" Tana dry tace "It's my pleasure abinda mijina keso shi nake so" "I love you so much you're the best ki shirya kimin wanka da kwalliya mai kyau" tace "I'll take care" kai tsaye yace "In sha Allah" da haka sukai sallama tare da katse kiran. Sai bayan Isshā Sannan Sheikh ya ajjiye komai ya murza Wheelchair ɗinsa zuwa waje a reception ya samu Arjun zaune yana shan Cork sai p.a miƙewa tsaye Arjun yayi tare da kama Wheelchair yana faɗin "Yap! Muna da aiki gobe sosai,dan haka ka fito da wuri zamu fidda sabbin designers na necklaces da ring da sauransu" cikin girmamawa p.a yace "In sha Allah before 7:30 ina nan" Arjun yace "Allah ya nuna mana goben" sanin halin Sheikh ko p.a yay mgn ba lallai ya amsa kawai yace "Sheikh na barka lfy" kamar yadda yay tsammani hakane ya kasance ko kallonsa bai ba bare ya sanya ran zai amsashi,a haka suka nufi motar Sheikh wacce Arjun keja, sai dai sukayi tafiya mai nisa a hankali Sheikh kamar bai son mgn yace "muje shopping" kallonsa kai yay ya ɗauke kai kana ya juya kan motar ya nufi Jabi Lake Mall, a harabar mall ɗin Arjun yay parking ya fito, kana ya buɗewa Sheikh ƙofa zai ɗauko wheelchair ɗin Sheikh yace "No! Bazai naje ba go and buy new phone for me" da mmki Arjun yace "Phone?" Kai tsaye Sheikh yace "haka nace" jinjina kai yay yace "Dame kuma?" Shiru yay alamar tunani sai kuma yace "With ice cream and Chocolate sai shortbread" Murmushi kawai Arjun yay yace "Zance zaka ne?" Banza yay masa yana dry yace "Something is fishing" ya faɗa yana yin cikin mall ɗin, lubb yay a jikin kujerar yana maida numfashin wahala yay ɗaya ya azabton da rashin ganinta anya zcyarsa zata jure rashinta? Zai iya hqr da ita kamar yadda ya tsara? A bai yane yace "Ni bazan iya ba, Airah is mine Always be mine forever and ever, ta zama jinin jikina rashinta a gareni babban illa ne,dole ya sauke wannan fushin da yake yaje ya ganta" ya faɗa yana jan ƙwantaccen beared ɗinsa. Arjun na shiga ya nufi side ɗin manyan wayoyi na zamani tashin farko ya zaɓar masa wata white ɗin Iphone 12 max pro, bayan ya ɗauka ya nufi wajan tarkacan chocolate ya lodar masa manya colours daban daban sai da ya cika basket Sannan ya nufi wajan biyan kuɗi, A.t.m ya baiyar suka sanya jikin pos suka ɗauki a dadin kuɗin su kana suka bashi receipt, kayan ya ɗauka zuwa mota yana zuwa Sheikh ya kallesa yace "Hauka dai? Wannan kayan fa?" Ajiye su yay a back seat kana ya nufi wajan zamansa yana yiwa mota key yana faɗin "kaita sha har sai ka gaji,kaga zasu ɗauke maka kewa tunda ka zaɓarwa kana ajjiye damuwa" jinjina kai kawai Sheikh yay kafin ya numfasa yace "me kake buƙatar ji SIRRIN ZUCIYATA? Ida hkne ka nemawa kanka sauƙi wajan hqr daji" Arjun cikin ɓacin rai yace "Daman nasan baka ɗauke ni a bakin komai ba,tunda haka ka zaɓa kowa yaje yay sabgar gabansa" ganin yadda Arjun duk ya sauya yasa Sheikh yay ƙasa da Murya yace "Idan abinda ke damun Sheikh za kaji to tabbatas kana gab dayimin kallon mahaukaci ko kuma zautacce,munin abin yasa na zaɓi barinsa a zcyta dan haka kaima ka hqr daji badan baka isa na faɗa maka ba" yana faɗin haka yay baya ya kwanta jikin kujerar yana sauke numfashi, a hankali kuma yasa hannu ya dafe ƙirjinsa dake bugawa da ƙarfi cikin dauriya ya fara faɗin "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" sai kuma ya fara tari, cikin kiɗima Arjun yasa hannu ya riƙesa yana faɗin "Lfyarka kowa? Sheikh are you ok?" Cak tari ya tsaya ya shiga maida numfashin wahala tayaya zai zama lfy? Tayaya zcyarsa taza samu nutsuwa idan har bai samu abinda yake so ba, zcyarsa yasan gab take da bugawa sbd abubuwan cikinta yawa gare su, a haka yana sauke numfashi Arjun yay parking a harabar gidan ba tare daya sani ba, "Buddy! Sheikh! Imam!" Haka Arjun ya jeru masa sunayensa amma babu ɗayan da yaji yana can ya lulaaa duniyar tunani, cikin damuwa Arjun yasa hannu ya shiga jijjiga Sheikh yana ƙara kiran sunansa, firgigit ya buɗe jajayen idanunsa akan Arjun, ganin sun zo gida yasa ya fidda wani emotional sound a hankali ya sakko da fararan ƙafarsa ya zauna saman wheelchair, cikin sauri Arjun ya shige cikin babban parlon sbd yayyafin da aka fara, a zaune suka samu Uncle Sham shida Barrister, yana ajjiye Sheikh ya juya ya nufi waje not too long ya dawo hanunsa riƙe da siyayyar da sukai, Uncle Sham ne yace "Imam lfy kowa?" Shiru yay sai numfashin dake fitarwa da sauri², ganin yay masa shiru yasa ya kalli Arjun yace "Mohd mene ya faru?" Kallon Sheikh yay suka haɗa ido ya janye nasa idon yace "Kawai gajiya ce sai yunwar dake damunsa" cike da gamsuwa Uncle Sham yace "ayyyaa! Ga Granny ɗin taka ba lfy" Idanunsa a ƙasa yace "Arjun let's go" turasa yay har ciki Uncle Sham kam yana lura da kallon da Fannah kewa Sheikh sai bayan sun shige ta sauke ajjiyar zuciya mai ƙarfin tana share hawayen da yazo mata, cikin ƙasa da Murya kuma tace "An shirya dinner ɗin" Murmushi Barrister yay yana miƙewa tsaye yace "thank you dear" tuni tabar wajan ta nufi wajan dinning ɗin inda Fareeq da Bahaiyya suke zaune sai Mami wacce take sauri ta gama domin yau ranar ta ce tana son jin ɗumin jikin sweet Imam ɗinta, gashi tana sa Enough time ta zama dashi tunda Granny ba fitowa zatai ba, Barrister yace "Uncle bisimillah" miƙewa Uncle Sham yay yace "Allahamdulillah bari naga Imam" yana faɗin haka ya nufi flat ɗin Sheikh a hanya suka haɗu da Arjun yay masa sai da safe, a zaune ya samu Sheikh a saman bed yana ƙarasa shan malt ɗin hanunsa yana sanye da kayan bacci farare ƙal, da alama har yayi wanka, zama Uncle Sham yay tare da tattaro nutsuwarsa zuwa ga Sheikh yace "meke damunka Imam?" Kwallon Uncle Sham yay yana maida numfashi tare da ɗauke kansa baice komai ba, Uncle Sham yace "Don't worry everything will be fine ok! Kaci abinci ko?" Sai a lokacin ya kalli Uncle Sham yace "Am full" cike da tausayawa Uncle Sham yace "sure?" Ya ɗaga masa kai ba tare da yace komai "Imam ka kula da Lfyarka nasan har yanzu baka da wasu shekaru a duniya amma yanayin rayuwa zai sanya ka zama babba kasan mene kake, ada kace Mami bata kula da kai right? Yanzu ga matar mahaifinka nan Fatima" saurin runtsa ido yay yana jin gudun zcyarsa na ƙaruwa wai matar Mahaifinsa wannan kalmar kaɗai bata sanya ya rasa ransa ba Uncle Sham ne yaci gaba da faɗin "Ita yarinya ce ba kamar Saudat ba, dole kasan mu'amalar da zakai da ita,idan ita macace kai namiji ne,matar mahaifinka ce matar mahaifinka kuma mahaifiyarka ce fatan ka gane?" Shiru kawai Sheikh yay a zahiri kallon Uncle yake amma hankalinsa sam baya ga abinda yake cewa, tunanin makomar zcyarsa yake, sam jaririyar zcyarsa bata kyauta masa ba ta sanya ya shiga son abinda bazai taɓa samunsa ba a rayuwa,tabbas idan yaci gaba da zama yana Kallonta a gidan nan sai dai a wayi gari a ɗauki gawarsa dole ne yabar ƙasar cikin satin nan ma kowa, miƙewa Uncle Sham yay yace "Bari naje zuwa gobe zan kawo Anut Amina da Huda" kasa yi masa mgn yay, ya rufe idanunsa ruf, ganin haka yasa Uncle Sham tunanin ko bacci yay, gyara masa kwanciya yay tare daja masa duvet,ganin yadda yake ta haɗa gumine yasa ya ƙaro masa gudun a.c kana yaja masa ƙofar ya fita. Fannah kasa daurewa tayi da Idanunta ya kawo ruwa zatai kuka sai tayi saurin goge Idanunta ta hana kanta kuka sai ajjiyar zuciya da take faman saukewa akai², tana zaune sanye da kayan bacci Lingerie Suit Pajamas - White, ta ɗura baby hijab a saman kanta taji an turo ƙofar an shigo, ƙamshin turarensa kawai ya sanar mata cewa shine zcyarta na bugawa tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasa, murmushi Barrister ya saki yace "My dear" ya faɗa yana ƙarasa zama kusa da ita saurin jaa baya tayi tace "A..a'a ni bacci zanyi" kallon fararen fuskarta yayi yace "The what?" Tace "Shkknan" yace "Kin tabbatar?" Tayi saurin cewa "Eh" haurawa yay saman bed ɗin yana faɗin "To zo mu kwanta am your husband ai" girgiza masa kanta tayi jikinta na rawa ta shiga jaaa baya cikin damuwa yace "Dear na kin san yadda nake ji kowa? Kisan azabar da nake kwana nake tashi da ita akan ki? Ina son jin ɗumin jikinki, Baby look" ya faɗa yana sanya hannunsa da niyar nuna mata Hjyarsa zare ido yay jin abu lagwaf aya mutse gaba ɗaya ko tsayin ƙaramin hanunsa bata kai ba,cikin tashin hankali yace "What wlh ƙarya ne abata tafi haka wlh hjyta babbace kuma lfy yayiyya" da sauri ya diro daga kan gadon ya nufi wajan mirror tashin hankali ya ƙara bai yana a saman fuskarsa a cikin mirror lfya lou take amma a zahiri a shafe mararsa take,bai tsaya bin takan Fannah ba yay waje cike da tashin hankali. Tsoran dake zcyar Fannah yasa sam taƙi yarda ta zauna a ɗakin ba tare data duba kayan dake jikinta ba ta nufi flat ɗin Sheikh lokacin ruwa ake sosai kamar da bakin ƙwarya, turawa tayi a hankali tare da maida ƙofar ta rufe rufe idanunta tayi sbd wani ƙamshin mai daɗi daya daki hancinta ji tayi gaba ɗaya ƙafafuwanta sun fara rawa da ƙyar yaja ƙafarta zuwa inda yake kwance ya rungome pillow a ƙirjin sa, durƙoshe tayi a gabansa bakinta ya shiga faɗin "Why mene yasa? Meyesa zaka idanuwa na zubda ƙwalla bayan sune sukafi dacewa dani? Mene yasa zaka ɗauki abinda nake so ka bawa wata? Tana da komai Ni kuma kaine komai ɗina dan Allah Malamina ka taimakeni ka taimaki jaririyar zcyta wlh idan kace zaka so wata kabarni mutuwa zanyi" ganin ko mutsi bai ba yasa ta tabbatar bacci yake cikin jan numfashi tace "Minty karuye (sweetheart)" shiru tayi tana kallon ƙyakkyawar fuskar sa tace "Nyi gyiya dinan kam rak3na ba nyibaa karuye rassi dainba Martine wande wadunnde nammimi" ( Ba wanda nakeso sama dakai aduniyar nan, dan ALLAH karka karya al'ƙawari) wlh Malamina kai nakeso ba babanka dan Allah karka bari wani abu ya rabamu zcyta ba zata ɗauka ba, kukan data daɗe ba tayi bane ya kwance mata cikin kuka tace "Kuru jiriman wande kwallim andea yanssayi" (Iya wuya karka bari arabamu). Kuka ne ya kwace mata ta shiga jijjiga hannunsa tana faɗin "Please Malamina you're my everything my favorite dan ALLAH ka rabu da waccen yarinyar, mutsi yay da hannunsa da sauri ta ɗaga kai Idanunta cike da hawaye suka haɗa ido kafin tai mgn yasa dukkan ƙarfinsa ya fisgota jikinsa, ta samu gurbi a faffaɗan ƙirjinsa Idanunta ta shiga zarewa domin ba tayi tunanin idanunsa biyu ba, tana ƙoƙarin yin mgn yay saurin ɗura mata yatsarsa a baki...... Littafina na kuɗi ne kada ka karta ba tare daka biya ba kaji tsoron Allah...... If you read for free🤷🏾‍♀️🤷🏾‍♀️ It's 500 via 0116886426 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 NIMCYLUV 22/10/2021, 10:30 - 🤔🤔: *SM💞* ```Kuci gaba dayi min gantali dashi😒 maci amana kawai, a to! wanda yaci amana, amana taci shi fisabilillahi sbd an maidani gantalalliya aita fidda book ɗina waje what have i done to ```you``` ??```. Unexpected abun yazo min domin seriously ban san cewa idanunsa biyu ba, shi kowa Sheikh daban ba bacci yake ba yaywa Uncle Sham pretending like he's sleeping, amma yana kwance luff yana fama da zcyarsa dake masa matsanancin ciwo,da ƙyar yake iya fidda numfashi sbd yadda Numfashinsa ke sarkewa ga tarin daya fara damunsa, kallon cikin idanunta yay yaga yadda ta rufesu ruff ga yadda ƙirjinta ke wani Irin ɗagawa, gwauron numfashi ya sauke wanda fita da wani zazzafan huci, slowly ya janye idanunsa daga kanta yana fidda numfashi wahala kafin ya mirgina ta can gefe ya juya mata baya, Tashin hankalin tsantsa ya bai yana saman fuskarta she never expected why zai juya mata baya? What exactly did to him? Kallonsa kawai take ko ƙiftawa babu, kafin a hankali taji wani abu mai zafi da kuma ɗumi na bin saman innocent face ɗinta wanda ta tabbatar hawaye ne,kamar yadda ya buƙata haka tai masa al'ƙawarin ta daina kuka, amma she's can't hide it, sun mata zuwan ba zata komanta yana neman lalacewa, Idanunta ta rufe fuskarsa take gani, cikin wayarta Sheikh take gani hatta plate ɗin abincin ta Sheikh take gani,wanne wacce Irin jarrabawa ce? Fatan ta ɗaya ace baiji abinda take faɗa game dashi ba,but tasan abune mai wahalar gaske ya kasa ji, koda baiji ba Idanunta ba zasu taɓa ɓoye shekararriyar soyayyarsa a ranta ba. Ko mgn wani yay mata zazzaƙar muryarsa ita take dukan kunansa seriousness. Duk yadda taso hana kanta kuka kasawa tayi bata san lokacin da kukan yay fitar gurmi ya fasallasa kansa ba. Narkakkun idanunsa ya buɗe da ƙyar wanda suka gamayin jaa sbd condition ɗin da yake ciki, yaga kuma Tabbas idan bai magance wannan matsalar a yanzu ba za'a iya wayar gari aga gawarsa, gently yaja jikinsa ya jingina da frame ɗin gadon yana sauraren heart breathing ɗinsa, Wheel yana jin yadda kukanta ke ƙara dagula masa lissafi, cikin daƙushashiyar Muryarsa yaja numfashi da ƙyar yana dafe ƙirjinsa yace "Zahraaah!!" Ina Muryarsa kaɗai na narkar da zcyrta balle a tafi wani abun daban, Sheikh wani Irin mutum ne mai cikar zati, ga wani ƙwantaccen kyau wanda kai tsaye ba zaka iya dangantasa da wata ƙabilar ba, yana da hankali da kamewa sam babu alamun wasu Exceptional qualities a tattare dashi, inama yake zuwa banda Mosque sai umara da hajji idan lokaci yayi, sai yanzu da tsiri fita company na designer, mai suna *I.M.H designers shoes and galleries* sai kuma wani wanda ake iya zallar zanan necklaces da ring sai zanan gida makarantu masallatai da sauransu. Shiru tayi ta kasa amsa kiran da yay mata domin har tsakiyar kanta taji sautin lafiyayyiyar muryarsa mai tsananin taushi. Cike da son samawa kansa nutsuwa da abinda ya keji ya ɗura softness hands ɗinsa akan nata wata ajjiyar zuciya ta sauke cikin jarumtar daya samawa kansa ya ɗura hannunta a saman ƙirjinsa dai-dai inda zcyarsa ke bugawa, cije baki yayi yana fesar da iska mai zafi cikin serious talking yace "Zahraaah zaki kashe Imam da ransa, dan Allah ki barni naji da soyayyar budurwata please, I'm going to die Zahraaah!" Zare ido tayi tana mai janye hannunta sbd sam ba zata iya jure jin yadda zcyarsa ke beating it hurts her heart, Idanunta tane ya ƙanƙance taji zcyarta ta bushe ya ɗauki niyyar dukkan abinda zai faru ya daɗe bai faru,daban tace bata son Auren akace sai anyi to Finally ga abinda Auren dole yaja nan,kuma tasan harga bata wani laifi zcyrta yaja komai ita tai forcing ɗinta zuga Internal love (Haramtacciyar soyayya) . Hannunsa ta riƙe gam cikin nasa tace "Malamina.." sai kuma tai shiru tana jan wani wahalallan numfashi kafin cikin wata raunatacciyar Murya tace "Malamina i love You since before! I can't imagine tun yau shine hakan, but i love You with all my heart! _You are the only thing that gets me going nuts. My heart and my mind can’t think of anything else aside from you. I’m_ _addicted to you because I can’t stop myself from daydreaming about you. I am your baby forever._ _It’s self-evident that I’ve got to be with you_ _because I can’t let you go. You should know that my heart beats for you, and all I hear in my head all day round is your_ _name. How am I going survive this torment of being so into you?_ _I can tell that my heart belongs to you. Even if it_ _beats inside of me, it still beats on your_ _command. You are my everything, and I can’t live without you. I can’t stop myself from loving you._ _It’s as if I’m under your spell._ _I love you, baby, and I can’t exist without you! Love so...so..much Malamina"_ Kallonta kawai without blending, wannan mgnar nata yafi kama dana wanda ka daɗe ana so, ko mu'amalar auratayya. It is something which goes far beyond mere explanation,but extent reality, mmkinta bai gama kashesa ba sai da yaji shassheƙar kukanta tana faɗin _”Nya Raakna”_ (I love You) kanuri, _”Mo nifẹẹ rẹ”_ Yaruba. _”Nopp na la”_ Wolof _Nakupenda/Begg naa la_ Swahili. _”Ana uħibbuk”_ Arabic. _”Mi Yidi ma”_ Fulani. Shassheƙar kukan da take ya hanata ƙarasa faɗin Asirin zcyrta,ya hanta faɗin gayawa Malaminta irin zallar so da ƙaunar da take masa,so Bara algus, muskutawa yay kaɗan a kasalance yace _“Are you crying Zahraaah!?”_ shiru sbd tarin daya kawo masa ziyara hakan yasa ya kifa fuskarsa a tafin hannunsa yana jin kamar yasa hannu ya ciro zcyarsa ya huta, shin kotai shima ya fallasa mata nata asirin zcyar? Saurin girgiza kai yay yana faɗin _Isn't nacessary, i can't say it, it's my own secret between me and my heart_ tattausan Muryarsa yay yace "C'mon dai na kukan haka, Wow you did a great job Zahraaah, what a beautiful game?" Kallon baka da lfy tai masa wato duk wannan maganganun a matsayin game take gaya masa, kenan shine player ɗin ita kuma ball ɗin sai yadda ya juyata,kasa mgna tayi kamar yadda ta kasa tsaida hawayenta, Muryarsa a ƙasa yace "firstly dai na wannan sai muyi mgn ok!" Da sauri tai shiru ta goge fuskarta sai ajjiyar zuciya kawai take saukewa "Zah...raaah!" Ya kira sunanta a rarrabe kanta a ƙasa tace "Na'am" fesar da numfashi yay kafin ya sanya softness hands ɗinsa ya tallafo fuskarta gaba ɗaya yana kallon yadda taƙi yarda ta buɗe ido yace _“Open Your eyes! And look at into my eyes”_ ji tayi sam ba zata iya Kallonsa ba bare cikin idanunsa ita kam ba zata iya wannan rashin kunyar ba, yana wasu irin kifiyo a cikin idanunsa wanda ko namiji ya kalla dasu zaiji yana shakkarsa bare ita mace, macen ba wacce take da rauni a kansa, cikin son gane abinda ya keson ganewa yace "Tashi kije to" girgiza masa kai tayi shima ya girgiza kansa yace "Ok, buɗe idonki ki kalle ni Zahraaah" slowly ta shiga buɗe kumburarrun idanunta ta sauke saman red lips ɗinsa dan ba zata iya kallon idanunsa ba,shiru sukai na wani lokaci kafin yace "Mummyna! A haka zaki taimaki ɗan naki?" Ya faɗa yana fiddo idanunsa waje a ransa kuma yana Astagafirullah, domin haramci ne kwantata macen da kakeso da Uwa, kwaɓe fuska tayi tana cizon hanunsa daya riƙe mata fuska dasu yace "Don't worry zan rama, just buɗe idanunki ki kalli wanda kikeso indai da gske ne ba sharri ba" tana marai-raice fuska ta buɗe idanunta akan ƙyakkyawar fuskarsa mai cike da haiba ga hasken ɗakin ya ƙara masa kyau, wutar kansu ce gaba ɗaya ta ɗauke na wani lokaci sbd haɗuwar idannunsu waje guda, a hankali Sheikh ya fara karantar dukkan wasu feelings wanda suke cikin idanunta, Fannah jikinta na ya ɗauki rawa sbd ba zata iya kallon Ƙwayar idonsa ba,abin yay mata girma ba zata jure ba, ƙasa ta fara yi da Idanunta da sauri yace "Don't ever trying it" bisa dole ta ƙara haɗa ido dashi rashin sabo yasa jikinta saki wata kasala ta saukar mata gaba ɗaya ta faɗa jikinsa tana sauke numfashi jikinta duk rawa yake, matsuguni ya sama mata a Physique ƙirjinsa, ita nata ne ya fito fili shi kuma tashi a zabar a cikin zcyarsa ya keji yasan dole yay jinya, yanawa Zahraaah mahaukacin so da ƙauna, ada ya ɗauka Aljanarsa ce,ya ɗauka Airahnsa ce daga baya fahimci zallar kama kawai suke kuma ya tabbatar bawai kamarta da Airahnsa yasa yaji yana sonta ba, shidai ya samu kansa dumu² a masifaffiyar soyayyarta, numfashi yaja da ƙarfi yace "Me kike so ayi zah..raaah! _Am in love since before_" west ɗinsa ta riƙe sosai ta shiga jijjiga sa tana kuka tare da faɗin "Dan Allah kasoni nima wlh idan kace a'a mutuwa zanyi,idan na mutu kuma kai ne sila you're the reason behind everything tun ban san kaina ba nake sonka kai ne kaɗai Namijin dake cikin zcyar Fannah, Malamina ina sonka da dukkan zcyta" ta ƙare mgnar cikin emotional sound yadda take kukan yasa ya rungome ta a jikinsa tsam suka shiga fitar da numfashi atare, banda kada taga rauninsa da babu abinda zai hanasa fitar da nasa hawayen kozai ji daɗi da sauƙin abinda ke damunsa, tagwayen ajjiyar zuciya ya kuma saukewa kafin yace "Me kike so ayi Zahraaah?, And kisan tarayyata dake haramun ne ko? Kin san matsayinki kowa? Kefa matar mahaifina ce kada kiyi amfani da son zcyarki kika mu'ikata abinda zai zo yana damun mu" da sauri tace "In dai akan soyayyarka ne bazan taɓa ladama ba, _believe me_ Malamina" Numfashi ya sauke yace "Uhm to ki amshi game ɗin da nayi maki tayi ƙilan na fasa son waccen ɗin idan naga kin iya soyayya, just accepted my request Zahraaah" runtsa idanunta tayi bata ƙaunar jin Wannan budurwar gaba ɗaya danne zcyarta tayi tace "Wacece ita budurwar ya sunanta" wani ƙawataccen Murmushi Sheikh yay kafin yasa hannunsa ya zareta daga jikinsa yana jan ƙwantaccen beard ɗinsa yace "her name is *Muhaddaserh* a very nice name" kasa magana tayi sai kuma tace "to idan kuma ban iya soyayyar ba fa? Shkknan ni baza ka soni ba?" Mmkin shirmanta yake ta kasa fahimtar komai yace "Am not sure seriously, amma ki zama mace mai ƙarfin gwiwa, mai jajircewa akan da take so ki samawa kanki jarumta hqr salama,babban abu kuma ki gayawa Allah damuwarki idan abun ya kasance alkairi a gareki sai kiga komai ya sauya babu abinda lokaci baya sauyashi" kai ta jinjina masa yace "tashi kije" kwaɓe fuska tayi tace "Nifa tsoro ake ban wlh" idanunsa akan wani wajan yace "Uhm" lura tayi ya fara gajiya da mgnar akwai abinda ke damunsa sbd yadda yake ta riƙe ƙirjinsa tace "Eh wlh tsoro na keji kawai na kwana a nan" bai kulata ba ya kama kanta sosai ya shiga karanta mata addu'a kana ya ɗura laɓɓansa a goshinta nan ma ya karanta mata addu'a tare da sauke mata wata lafiyayyiyar sumbata a wajan yace "Jeki nothing happen in sha ALLAH" miƙewa tayi tana jin kamar idan ta tafi wani abu zai samesa a dolenta ta miƙe tsaye ta nufi wajan ƙofa harta buɗe zata fita taji yace "Zahraaah" da sauri ta juya taga ya ware mata hannayensa da sassarfa ta nufi wajansa suka rungome juna, Sheikh riƙeta yay sosai lokacin tuni jikinsa ya gama ɗaukan zafi cikin Muryar mara lfy yace. _لا شك أن حبك في قلبي كمثل نفس الذي يخرج من أنفي،_ _الذي كان إدفاعة كان أن يكون كالموت_ _إذا كان كذالك كيف تري أخرجه في قلبي،_ _إلي أحبك ياصاحبة الحسن والنسب.💘💘_ Kallonsa tayi tace "me kace?" Girgiza kai yay yace "basai kinji ba Allah yay maki albarka jeki kwanta" juyawa tayi bisa uamarninsa tana tafe tana waigensa harta fice daga cikin bedroom ɗin, tana fita sauke ajjiyar zuciya "nayi amfani da harshen da bakya ji nace _Haƙiƙa sonki acikin zuciyata tamakar numfashin da yake fita daga hancina wanda tsayar da shi dai-dai yake da mutuwa_" baya yaja ya kwanta amma tarin da yazo masa yace sam bai isa ya kwanta ba cikin fitar hayyaci ya fara tari wanda daman tun ɗazo yake riƙesa, yana tsaka da tarin yaji wani wani ƙaton jini yay tsaruwa daga cikin bakinsa, fitar jinin yasa ya samu relief, sanyin ɗaya keji yasa yaja duvet ya rufe jikinsa. Can cikin dare yaji ana turo ƙofarsa ko mutsi bai ba bai kuma san mai shigowar ba, yaji dai ana buɗe inda yake ajjiye muhimman abubuwa, can kuma yaji ƙarar papers not too long akai waje da ɗan sassarfa, numfashi kawai ya sauke abinda ya keji bazai taɓa barinsa ya buɗe ido ba,idan yaga ko waye ta ina zai iya kamasa shi ba ƙafa garesa ba. Washe gari Sheikh da azumi ya tashi sbd Alhamis ce, gefen Fannah ma da nata azumin ta tashi, Barrister na zaune a cikin bedroom ɗinsa yana duba ayyukansa yaji an buɗe ƙofar an shigo, Mami ce sanye da wata Holand ɗin atamfa mai kyau tayi fess da ita sai zabga ƙamshi take, fuskarta ɗauke da Murmushi tace "Mrng dear" with much surprise ya kalleta kafin yace "Mrng" zama tayi tace "Yau ba zaka fita bane?" Kai ya ɗaga mata yana faɗin "Am not sure dai,amma jikin Son na bani tsoro yaƙi yarda a kaisa asibiti,ga kurar da yaywa Arjun da kuka Arjun yabar gidan nan,so ina jiran Uncle ɗinsa yazo" jinjina kai tayi tace "Daman fita biki ya kamani shi ne nace i can't anywhere without your permission" miƙewa yay tsaye yace "Oh really?" Tana tashi tsaye zuwa wajansa tace "Sure! I'm sorry Barrister _for the past Weird experiences with are all regretful._" yana duba wayarsa yace "What the you want" kai tsaye tace "Your permission allow to go" yace "where?" Matsuwa wajansa ta sakewa zata riƙesa yace "Ohhh Hello, don't trying it" baya taja tana fidda wani kalar murmushi tace "Zani Sakoto ne" waje yay yace "ok" da ido ta bisa tana jan wani lalataccen tsaki "You're mad Barrister Hamdan Balarabe". Sheikh ko Company ban je ba sai yanzu daya fita zuwa Mosque sallar asar ya daɗe zaune yana yiwa Mutane karatun bulugur mara, sai wajan 5 yaja Wheelchair sa ya dawo, a Parlo ya samu Granny tana faɗin "To duk basai suci kansu ba,ina dalili fisabilillahi? To wlh babu abinda yaymin zafi ni ba gantalalliya bace yanzu zan haɗa kaya na, na tafi inda Allah ya kaini" Uncle Sham yace "ba takai ga haka ba,tunda yaƙi faɗin abinda yake damunsa sai a rabu dashi ai asirin ciki sai hanji" share ƙwalla ta fara tace "In dai da halarci baici Imamu yaymin haka ba, yaro abun tausayi rayuwarsa duk a gantale,ban sani wa yake dashi? To sai wannan yarinyar mai taimako na" Uncle Sham kallon fannah yay wacce take sanye da wata light blue ɗin laffaya wacce tai mata kyau sosai,tana tsaye wajan dinning area tana shirya dinner "Ah to babu ruwana idan hawan jini na ya tashi idan na mutu wana macewa wane yake da asara?" Shi dai Sheikh na zaune idanunsa rufe yana jin dukkan abinda Granny take faɗa "ɗauko min Mantina nasha ko zanji dai-dai" jiki a sanyaye Fannah ta nufi fridge ta ɗauko mata tana zuwa dai-dai inda yake zaune suka sauke ajjiyar zcy a tare slowly kuma ya buɗe idanunsa wanda ya samu sauka a cikin nasa, jikinta ne ya ɗauki rawa ƙafafuwanta suka ƙasa ɗaukan jikinta gaba ɗaya tayi kansa zata faɗi da sauri ya rufe idanunsa yana tura Wheelchair baya, Granny ta riƙeta tana faɗin "Ya! Ya! Ya! Haka kamar wata mai shafar aljanu, Auzubillahi sharrr walaƙuuwata!" Ta faɗa tana riƙeta girgiza kai kawai Uncle Sham yay yana tura Wheelchair Sheikh yace "Mohd jeka gobe kazo i want talk to you" miƙewa Arjun yay yace "In sha Allah Uncle" Granny tace "Ranjun kaga gida ya kusa zama na Maraya ko? Yooo idan na mace Imamu kaɗai yay asara amma dai in sha Allah mutuwa ba yanzu" murmushi kawai yay mata yace "We hope so.." Uncle Sham yace "Imam bazan takuraka aka ka faɗa min abinda ke damunka ba,Amma ka sani damuwa bata mganin komai, kasan komai tunda kana da ilimi amma ina gargaɗinka kasan me kake Fatima matar Ubanka ce" calmly yay yace "bana nufin wani abu amma ka iya takunka da ita za'a iya haɗa baki da ita a cutar dakai" sai lokacin ya ɗaga idonsa ya kalli Uncle Sham yace " i want freshen up" Uncle Sham yace "ok bari na turo maka Granny, ka tabbatar kaci abinci mai yawa tunda azumi kayi" bai ƙara kallon Uncle Sham ba sai ma idanunsa da yaja ya rufe yasan har abada Zahraaah ba zata taɓa cutar da rayuwarsa. Bayan Isshā Barrister na zaune a parlon sama yana waya da Alhj Kamal yace "Na kasa gane maganganun ka, nayi searching harna gani dan Allah ka fahimtar dani" Murmushi Alhj Kamal yay yace "Na daɗe da danin baka da ƙwaƙwalwa Hamdan let's go to the point a cikin yaranka guda Uku, ka kwana da sanin cewa guda biyu bakai ka haifesu ba, i mean bakai ne real father ɗinsu ba... Allahamdulillah end of book 1🌚🌝. Dan Allah dan Annabi Anty ki daina karanta littafina ba tare da kinbiya ba kiji tsoran Allah,ki sani ina da haƙƙi a kanki bazan maki Allah ya isa ba,amma kisan haƙƙin wani akan wani Ubangiji baya taɓa yafesa. SIRRIN MU isn't free book..if you read for free..🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️. It's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank. Show your evedance via WhatsApp 08119237616 NIMCYLUV 22/10/2021, 10:31 - 🤔🤔: 51-52 [9/22, 6:46 PM] Nimcyluv✍🏾: Da rashin fahimta Barrister yace "What the you mean by that Alhj Kamal?" Wani Murmushin gefen baki Alhj Kamal ya sauke wanda ta cikin wayar Barrister yaji sautin fitarsa yace "I mean my words Barrister, acikin yaranka guda Uku biyu ba kai ne real father ɗinsu, wlh bakai ne Ubansu na gsky ba" wata zufa Barrister ya share yana son ya tuna abu amma sam ƙwaƙwalwarsa ta gaza ɗaukan komai, cikin ƙarfin hali yace "Am on mah way Alhj Kamal" zaro ido Alhj Kamal yay yace "Aini ka ganni gaf da shiga jirgi bana jin zan dawo Nigeria sai nan da 3yra to above" ƙitt Barrister ya kashe wayar ba tsaya ya gama jin zan can ba. Zagaye ya shigayi a parlo'n zcyarsa cike da tunani kala² daban², yaransa har guda uku wanda yake alfahari dasu ace guda biyu bashi ne ya haifesa ba, kenan guda ɗaya ne nasa to idan haka ne tsakanin Sheikh,Fareeq, Bahaiyya wanne ɗan sa? Da ƙarfi yace "Impossible, wlh babu wanda zaiji Wannan zan can, koda Alhj Kamal ɗin ne yace zai faɗa Tabbas zai iya ganin bayansa akan wannan muhimmin abun ya fita cikin mutane, yasan Alhj Kamal sarai tunda ya faɗi wannan maganar da gske haka ne babu ko tantama, dan haka dole ya nemi wata mafitar, dole ya samu wata sabuwar zuri'ar daga wajan Fatimansa ya shirya komai, dan haka ba a haifi wanda zai ruguza masa plans ɗinsa wanda ya tasu dashi ba, a gobe ko suma Fannah zatai sai ya kasance da ita" Yana zaune sanye da nightwear Pajamas Kimono Smooth Comfy Soft Bathrobe, a dalilinsa na son ɗauke damuwar dake ransa yasa tun safe Arjun ya kawo masa system, hanunsa saman system ɗin yana operating ɗinta, skin ɗinsa tai fresh sai Shinny take fuskarsa mai cike da haiba da kwarjini ta faɗa kaɗan idanunsa ya ƙara shigewa ciki, sai ya ƙarayin kyau fiye da lokotan baya. Yanayin yadda gabansa ya faɗi da zcyarta data buga yasan cewa Zuciyoyinsu sun yi kusa da juna, a hankali kuma ƙamshin turarenta ya fara kawowa hancinsa ziyara, ko ɗan baiyi ƙoƙarin ɗago kansa ba sai ma ƙara himma da yayi wajan latsa system sai ka ɗauka tun asali ya iyata. A hankali take kata ƙafafuwanta da sukai mata wani nauyi at the same time kuma itama taji zcyarta ta buga har sai data runtse idanunta, tana sanye cikin wata nightgown Amazon ta ɗura hijab a jikinta, ta rame itama sbd rashin ishasshan abinci a cikinta, har inda yake ta ƙarasa cike da nutsuwa ta ajjiye masa tray ɗin dinner mai ɗauke da Ingredient Shrimp Stir Fry, chicken and vegetables stir- fry, sai coffee da kunun gyaɗa, shiru ne ya biyo baya kuma ta kasa tashi a wajan sai ma zamewa da tayi ta zauna ƙasan ƙafafuwansa, few seconds ya ɗaga jajayen idanunsa ya sauke a kanta kamar wanda bai son magana yace "Have you eaten?" Shiru tai masa idan har gsky zata faɗa to rabunta da abinci tun jiya,dan ko datai azumi batai wani shur ba, a hankali ya sauke numfashi tare da ajjiye system ɗin can gefe guda, zamuwa yay tare da zama a inda take zaune kallon yadda tai wani zururu yay fuska ya haɗe sosai kafin ya sanya tattausan hannunsa a saman fuskarta ya tallafo haɓarta yace "What Is this?" Kwaɓe fuska tayi tare da sauke ƙwayar idanunta ƙasa tace "Me nayi to?" Ta faɗa a shagwaɓe, tsayawa kawai yay yana Kallonta yadda take abu kamar yarinyar goye, sakinta yay yaja baya kaɗan yace "Ci abinci" marai-raice masa tayi tace "To ai kaima ba kaci ba" ba tare daya kalleta ba yace "Uhm" banda tasan idan hawayenta ya zuba tamkar ta rusa al'ƙawarin da tai masa da babu abinda zai hana tai kuka kota samu yaci abinci, idanunsa a lumshe ya lulaa duniyar tunani yana jin sanda ta buɗe warmers ɗin ta shiga zuba masa abincin a plate, bai ji zuwanta ba sai jinta yay gaba ɗaya a kusan rabin jikinsa ta riƙe fuskarsa da kyau, da ɗan sauri ya buɗe ita kana ya buɗe baki da niyar faɗin "Move" sai kawai yaji ta tura masa laumar abinci ba kinsa, rufe idanunsa yay sosai sbd ɗacin da abincin yay masa a baki ya kasa kota taunasa, cikin ƙasa da mai ɗauke da lallashi tace "Babu ruwan ciki da damuwa, yanzu zai haifar maka da wata cutar ta daban, ita na rasaka ka sani rayuwan Zahraaanka na cikin wani hali, babu abinda nake buƙata a yanzu sama dakai Malamina, please kaci sabo da soyayyar da nake maka,ban shirya rasa Malamina farin cikin zcyta ba" ba tare daya kalleta ba ya fara tauna naman data saka masa a hankali cike da nutsuwa da ƙyar ta samu ya taune naman ya tafi, tana ganin haka ta ƙara ɗebuwa still idanunsa a rufe ta buɗe madaidaicin bakinsa ta saka masa, taunawar farko yay saurin dafe ƙirjinsa yana shirin fito da naman daga bakinsa ta saurin sanya nata baki naman ya faɗa ciki, da ɗan sauri ya janye bakinsa, Fannah kam kasa hqr tayi tasan da gaske duk su biyun suna buƙatar taimako amma a yanzu yafi buƙatar taimako fiye da ita, a sanyaye ta lallausan hannunta ta shiga murza masa ƙirjin haɗe da shafa bayansa, cak tarin ya tsaya sai numfashi da yake saukewa, cikin rawar murya yace "Leave Zahraaah" girgiza kai tayi tace "Why?, Kana buƙatar taimakona Malamina! A shirye nake da baka koda rayuwata ce" ta ƙare maganar tana ɗura masa mug ɗin kunun gyaɗar a baki, sha ya farayi a hankali² harya sha fiye da rabi while Hannunta na bayansa, Sheikh ji yake kamar tana zuba masa wuta a jikinsa haka ya keji dauriya kawai yake ya tsani kusancin da suke samun kansu a kullum,zcy sam ba tai masu halarci ba hanunsa yasa ya riƙe nata kana ya buɗe idanunsa tare da Kallonta, matsuwa jikinta ya fara a hankali ita kuma tana zaune kamar statue sbd buguh da ƙirjinta ke mata ya hanta ko ƙwaƙƙwaran mutsi ne, fuskarsa ya kifa a shoulder nata ya fara sakin ajjiyar zcy yana jan numfashi, a hankali kuma yasa hanunsa a bakinsa tare da tufar da yawo,mai makon yaga yawon kamar yadda yay expected sai yaga wani gudun jini a tsakiyar farin hannun nasa, wani murmushi takaice kawai yay ya ɗauki handkerchief ya goge jinin dake hanunsa kana fesar da iska daga cikin bakinsa kafin ya sauke numfashi yace "Don't leave me alone Zahraaah!" Bakinta na rawa tace " I won't, always be your side forever and ever you're the only one i pray for" hanunsa yasa ya rungome ta sosai a hankali yaji idanunsa na lumshewa wa cikin ƙaramin lokaci taji Numfashinsa na fita da zafi, Cikin rawar jiki tasa hannunta a kwantacciyar sumar kansa tace "Malamina... Sheikh na Are you okey!?" Gaba ɗaya nauyinsa ya sauke mata, da ƙyar ta zamesa a jikinta taga ashe bacci ya ɗauke sa, wata ƙwallar tausayinsa ta kawo idanunta da sauri ta goge Idanunta ta raɓa kusa dashi a ƙasan carpet ɗin ta kwanta ta daɗe tana kallonsa kafin bacci ya ɗauke ta a kusa dashi numfashinsu na haɗewa. Misalin ƙarfe 1 na dare Mami zaune ita da ƙawart Kubra suna jira layi yazo kansu, wannan shi ne first time da Mami ta ziyarci wajan boka,domin ta aminta da shawarar ƙawarta suna ta zaune har wajan 1:30 sannan layi yazo kansu Kubra a gama Mami biye da ita a baya sbd tsoran daya shige ta, a zaune suka samu wani ƙaton baƙin Mutum mara fasali da kayan asiri birjik a gabansa, yana ganin su ya fasa dry yace "Sannunku da zuwa gantalallu wanda suka yarda da shirka fiye dasu roƙi Ubangijinsu" kallon juna sukai ita da Kubra kafin su nemi waje su zauna, Kubra ce ta buɗe baki zatai mgn yace "To muguwa mai mugun nufi, taki bata fissheki ba sai ta salammiyya ƙawarki,maza duba nan" ya faɗa yana dukan ƙwaryar dake gabansa, zare ido Mami tayi haɗe da dafe ƙirjinta sbd ganin Sheikh da tayi kwance a ƙasan carpet gefensa kuma fannah ce ta zagaye hannayenta a wuyansa suna bacci cike da nutsuwa, tashin hankali ƙarara ya bai yana saman fuskar Mami jikinta na rawa tace "Na shiga uku ni Saudat me nake Shirin gani, Imam da matar Ubansa,wlh sai naga ƙarshen ki munafukai" dry bokan ya ƙyalƙyal kana ya haɗe fuska yace "Gana almura mai baƙar aniyya abinda kike ƙwaɗayi itama take ƙwaɗayi" cikin Kuka Mami tace "Ka taimakamin ka raba tsakanin wannan mutanan, wlh zcyta ba zata sami sassauci Ba indai ban mallaki Sheikh ba" Dry ya kumayi wannan karan har wani hayaƙi ke fita daga cikin bakinsa yace "Rabuwar su na nufin faruwar wasu sabbin alamura,haka haɗuwar su na nufin sabon abu, ko wanne da muhimmanci sa" kai tsaye tace "A'a ban damu da dukkan abinda zai faru ba,kawai ka rabasu dukkan abinda kake so zan maka" yana zana abu yace "Kaga kinibau, a fuska Musa a baki fir'auna" shiru gaba ɗaya sukai kafin yana numfashi yace "Akwai hatsari a aikin duba da yadda suke matuƙar so da ƙaunar junansu, sannan duk abinda za'ai bana jin aikin zai tasiri jikin namiji,ko aljani bai isa ya cutar da shi bare mutum" Kubra tace "Kawai kayi Abinda Ya dace kayi ka rabasu" jinjina kai yay yace "Kun aminci da dukkan sharaɗin dana faɗa?" Da sauri Mami tace "Shegiya mai baƙar aniyya, ai dole ki aminci sbd mugun nufinki na gab da cika" Mami tace "I mean my words ko akan yarinyar ne kayi aikinka burina kawai su rabu na mallaki Sheikh Mallaka ta har abada" kai tsaye bokan yace "Duk abinda kike so za ki samu, amma bazan taɓa gaya maki sharaɗin ba sai bayan na gama aikin, sannan duk abinda nace kiyi ya zama dole tunda kin manta lahira kinzo neman duniya" ba tare da shakka ko tunanin komai ba tace "Na amince" "Uhm ta yaro kyau take bata ƙarko" tashi yay ya nufi wani ɗaki ya daɗe ciki kafin ya fito ɗauke da wasu garin maganin yace "Amshi wannan, ki zubawa ita yarinyar a abinci" wani ya ɗauka ya bata yace "Wannan kuma sanda zaki kwanta dashi tsarkakakken yaron saiki saka a cikin jikinki yana kwanciya dakai zaiji baya ƙaunar ko wacce mace saike duk abinda kikace jiki na rawa zai aikata" karɓa tayi tace "To ka gano rabon yara a tare dani dashi?" Dry yay yace "Yara dai? Tabbas akwai rabon yara masu matuƙar yawa da kuma kyau uwa uba addini, sai dai ban san a ina ya samu rabon ba domin yaran a wajansa na gansu" farin ciki ya kama Mami tasan Sheikh bazai taɓa samun wasu yara ba indai bana ta ba. Bayan ya gama komai tace "Nawa ne kuɗi" tsawa ya daka mata yace "Kul! Ba kuɗi muke nema ba abu ɗaya kawai zaki shkknan kin gama aikin ki" jiki na rawa tace "Mene?" Yace "Zaki kwanta tare da kare na" zare ido tayi lokacin data kalli karen wani jibgege sai zaro harshe waje yake kamar zai ci babu ga yadda wutsiyyarsa ta miƙe sosai, dafe ƙirjinta tayi tace "Haba kamar dai wata dabba zanyi tarayya da Kare? Ka faɗi wani abun dai" dry yay mata yace "Ai ban maki dole ba da amincewar ki, idan kika ƙi ki yadda karen nan yake to haka zaki koma mu'amala da kar nuka, wutsiyyarsu ita zata zama ruwanki shanki, abincinki,dan haka bani da matsala akai wannan kadan ne da sauran bala'in da zasu sameki" kuka tasa tace "Na shiga uku kwanciya da kare Ni Saudat?" Kubra tace "Look! Saudat akan biyan buƙata rai ba abakin komai yake ba,bayan abun iya yau ne kawai ba dauwama zaki akai ba? Kina da burika dalilin haka kuma ki Auri Barrister da kika fahimci gskyar komai a kansa ba shine yanzu kike son kasancewa da ɗan sa ba,to aike ba mahaukaciya bace dole ki amince idan kinƙi yanzu ki fara haushin kare" shiru Saudat tayi can tace "Shkknan na amince" dry boka yay yace "Annamimiya taji zuƙar ƙawa" wani ɗaki ya nuna mata yace ta shiga, miƙewa tayi tana shiga karan ya biyo ta, tattare zanin jikinta tayi zuwa sama ta yaye manyan bombom ɗinta kana gani kasan akwai taimakon magani, wani gurnani karen ya fara ya shiga ɗaga wutsiyyarsa sama, kai tsaye ya nufi bakinta bisa dole ta buɗe da sauri ya zura mata a baki ya shiga kaɗa jela, sai tasha sosai har wani rawa jikin karen yake kana ya zare lokacin daya zura a jikinta wani gigitaccen ihu ta sanya sbd tsananin azaba, har can cikin ƙarshen jikinta wutsiyyarsa ke taɓowa, bata taɓa tunanin azaba irin na lokacin ba, cikin sauri ya dinga shiga jikinta banda ihun azaba babu abinda take. A hankali Fannah ta shiga buɗe idanunta wanda suke cike da bacci, farar fuskarsa mai ɗaukan hankali ta kalla kana ta sauke ajjiyar zcy mai ƙarfi, a hankali takai dubanta zuwa ga hannunsa taga gaba ya shige jikinta ya maƙaleta sai fidda numfashi mai zafi yake daga cikin hancinsa, sai lokacin ta samu yi masa kallon tsaf ita kam Ubangiji ya bata wannan as husband ya gama yi mata komai na rayuwa, tashin hankalinta ɗaya ne ace zata rabu da Malaminta to tabbatas sai dai a ɗauki gawarta, kwantar da kanta tayi a ƙirjinsa tana sakin murmushi cikin ranta take cewa _“Ya ALLAH! For give us_, ka yafe mana bayin kanmu bane mu duka ƙaddara ta faɗa mana, nasan Malamina na sona kamar yadda nake mutuwar sonsa, Ubangiji kada kayi amfani da kuskuren mu ka hukunta mu ta hanyar raba Zuciyoyinmu, baza mu iya ba zuƙatanmu ba zasu ɗauka ba, _Ya ALLAH!_ ka hukunta mu da komai banda rabuwa da JUNANMU” ta ƙare maganar idanunta na zubar da hawaye, mutsawa taji yayi tai saurin rufe idanunta sbd bata son ya ganta a jikinsa,wata wawiyyar Ajjiyar zuciya ta sauke,cike da so da ƙaunarsa tai copping face ɗinsu waje guda bakinta na rawa tace _“ Everytime i see You! My eyes wet with tears..My hearts.. Addicted to You! Don't ever.. Betray me I am Used to You.. It's not My fault.. Without You it's impossible to live_ Ina sonka da dukkan zcyta” ta ƙare maganar tana sanya bakinta cikin nasa da a lokacin wata giyar soyayyarsa ce ta taso mata har tana jin ko idanunsa biyu ba zata fasa abinda tayi jiya. (Wanda hakan shine faruwar komai tsakanin Sheikh da Fannah! Nimcy). *KIJI TSORAN ALLAH KADA KI KARANTA ABINDA BA HAƘƘIN KI BA, SIRRIN MU NA KUƊI IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616* Cikin wani sabon feelings ta ƙara tura bakinta cikin nasa tana sakin wani Emotional and sexcy sounds, wani ƙamshi mai daɗi taji yana fita daga bakin nasa ga wani yawo mai daɗi dake kwance a cikin bakinsa, tongue ɗinta ta zura ta shiga tattaro yawon ta haɗeye tass a bakinta, hannunta a saman ƙirjinsa tana shafa sumarsa zuwa nippy ɗinsa wanda sukai tsini ga wani ƙyakƙyawan gsky daya kewaye nippy ɗin yay jajirrr dashi. Ajjiyar zuciya ya sauke domin duk abinda take ba bacci yake ba domin a 2days ɗin nan baya iya wani bacci, kallon yadda ta lumshe hannunta yay, da sauri kuma yaja nasa idanun ya rufe sbd wani fitinan nan feelings daya kawo masa ziyara in one time, numfashi ya shiga fitarwa da sauri da sauri kansa ya shiga sarawa cikin zafin nama ya mirginata ƙasansa cikin wata wahalalliyar murya yace “Uhm! _Lemme give you a welcome kiss Zahraaah, My life, My happiness, My bestie, Mother of my children's, The one i love most after Granny”_ ya faɗa cikin ƙasa Muryarsa da bata fita sosai, idanunsa yay jajirrr sbd a zabar daya keji a mararsa, wata miƙa yay wacce bai son lokacin daya samu damar yinta ba, zare ido Fannah tayi sbd sandan da taji yana sukarta a mara, fuskarsa ya ɗura a Tata _"Help me Zahraaah!_ ki taimaki Malaminki _I'm going to die"_ ya faɗa ya kama hannunta tare da ɗurawa a jikin sandan da taji yana sukarta, zatai mgn yay sauri sanya softness lips ɗinsa a cikin nata.... Mu haɗe jibi🌚😂 [9/22, 6:46 PM] Nimcyluv✍🏾: 51-52 22/10/2021, 10:31 - 🤔🤔: 53-54 _Why Are doing this?_ zucyarsa ta shiga ta tambayarsa wata zcyar tace _You're mad Sheikh_ ta yaya zaka iya barin ƙyakkyawar halittar? Mene amfanin so da kuma ƙaunar da kake mata? _You have to me good and great man_ Sheikh Imam hamdan Balarabe _Show her true love_ bai tsaya tunanin wani abu dana ban ba yafi abinda zcyarsa ke gaya masa kuma yaga shine dai-dai, cike da nutsuwa jikinsa na ɗan rawa ya ƙara manna bakinsa a nata, gaba ɗaya suka sauke ajjiyar zuciya su duka zuciyoyinsu da gangar jikinsu na buƙatar abokin tarayya, ko wacce Zuciya na buƙatar Zuciyar ɗan uwanta Sheikh kamar mai tsoran aikata abinda yake haka ya ɗura bakinsa cikin nata ya gagara aikata komai sbd tsoran ALLAH daya shigesa, gaba ɗaya ya manta da last time lokacin daya fara ganinta ya manta kiss ɗin daya shiga tsakaninsu a lokacin sbd time he's not on his right mood so he's can't remember, yanzu ne ya kejin zai bata a hot and sweetness kiss, zcyarsa na son fahimtar dashi amma gangar jikinsa ƙara ingiza shi take zuwa gareta, a karo na biyu ya ƙara sakin wata wahalalliyar ajjiyar zuciya, slowly ya cafki dwon lips ɗinta ya saka cikin nasa ya ɗan zafafa ya shiga bata wani hot kiss mai tsayawa a rai da kuma tafiya da zcyar duk macen da akaiwa. It was kind of gentle romance Sheikh malamin addini ya karanta komai cikin hadisi fiqhuu, Umdatul ahhkam, Zadiz zaujen so yasan dukkan wasu launin kan soyayya da kuma hanyar da zaka bi da mace ta faɗa komarka,tundakakan yatsun ƙafarta har zuwa tsakiyar kanta taji wani azabban daɗi na ratsa ta , yanda yake shan lips dinta jitai in her holl life bata taɓa jin makaman cin abinda take ji ayanzu ba, gaba ɗaya jikin Sheikh rawa yake all what he need right now is Zahraaah ,cikin wani wahalallan numfashi yazare bakinsa a hankali ya sauko da kanshi neck dinta slowly yadinga shaƙar abinda yaji yana ƙara sashi zaucewa ƙamshi dake fita a skin dinta iyashi ya isa ya ƙara ingiza shi ,da sauri ya ƙara manna hancinsa dan jiyayi there is something killing him a skin dinta ,ganin yadda jikinta ke rawa ya tabbatar she is in need of him ,jiyayi komamene he want to feel Zahraaah he want her in any case yanda yake ganin jikinta cikin night wearing dress besan lokacin da ya juyo da face ɗin taba yawani haɗe bakinsu irin sex kiss ɗinnan kamar zai ciri mata lips and ko fargaba babu ta biye mishi out of control suka cigaba da baiwa juna sexy and hot feeling kiss dawannan damar yafara ƙoƙarin removing dress dinta but unexpected yaji wani abu ya ziyarci zuciyarsa and his brain too besan time ɗin daya tureta gefen saba hankali ya zauna trying to control his self ,all abubuwan dake faruwa between him and Zahraaah suka shiga dawo masa head besan lokacin da yace _“out Zahraaah! out of my side Zahraaah!! Out of my room!!”_ Yayi maganan _Sounding angry_ jiyayi a zaba tai masa yawa ya shiga juyi akan carpet ɗin kamar zai haɗiye zuciya haka ya keji idanunsa jajir ya buɗe tare da saukesu akanta, da sauri ya rufe idanunsa yana jin yadda tsigar jikinsa ke tashi bai yanar saman brest ɗinta bai taɓa ganin su a zahirance sai yau ba duk da cewa iya samansu kawai ya gani banda ainayin abinda zai nuna cewa Tabbas kaga full na brest wato nipples, Kuka Fannah ta sanya sbd yadda ta keji a jikinta shima jin kukanta yake har tsakiyar kansa da ƙarfi ya kuma cewa _“Get Out!! Zah..raaah!”_ ya faɗa bakinsa na rawa alamar a koda yaushe kuka zai iya kwace masa, tsawar da yay mata ta tabbatar cewa eh wannan Sheikh ɗin gsky ne bawai wanda ta sani a yanzu ba, miƙewa tayi tare da sanya hijab ɗin ta jiki na rawar tai waje tana sanya wani sabon kukan. Tana fita ya jawo pillow ya danne ƙirjinsa tashi a bai yane yace "Why Imam? Meka aikata? Me yasa kabi ruɗin zcy dana sheɗan?" Yanzu mene makomarsa ya tafka babban kuskure a rayuwarsa ya kasance da matar Ubansa wacce take matsayin uwa a garesa, _Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!_ Da ƙarfi kuma ya shiga buga kansa a ƙasan carpet ɗin yana sakin wani kukan baƙin ciki da kuma ladama, a hankali kuma tari ya fara maye gurbin kuka da ƙarfi ya danne saitin zcyarsa wacce take masa zafi da kuma raɗaɗi, bai samu sauƙin tarin ba sai da yay aman jini dole ya nemi taimakon wani amma wa zai faɗawa damuwarsa shi ya faɗawa Uncle Sham ne? Ko kuma ya faɗawa Arjun ne? Haka ya kasance cikin tunani har Subhi tayi. Washe gari tun 7:30 yabar gidan zuwa office tunda yaje ya kasa aiwata komai kana ganinsa kasan something is feshin jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa idanunsa yay jajur, fesar da iska yay ya shiga juya kujerar da yake kai yanzu ko buɗe ido baya iya yi sbd duhun da yake cikin idanunsa, a hankali aka turo ƙofar office kana aka mayar tare da rufewa, kallon tsaf Arjun yaywa Sheikh yaji ransa ya ɓaci kujera yaja ya zauna kana ga ajjiye masa cup of coffee wanda yake ta ƙamshi da tiririn zafi, Arjun yace "Sheikh ban taɓa damuwa da halin da kake irin yau ba, wlh wlh idan har a yau baka gayamin damuwarka to wlh zan barka rabuwa da har abada tunda kallon ɗan iska kakemin, tarayya ta dakai bata da wani amfani tunda za zamu iya sharing all feelings ɗinmu ga juna ba, ina ƙara tambayarka wacce itace tambaya ta ƙarshe da zan maka _What's your problem_" ba tare daya buɗe ido ba ya sauke Ajjiyar zuciya dan ko ya buɗe idanunsa bashi da tabbacin zai iya ganin Arjun sosai, ƙasa yay da muyarsa very slow yace "Pls Arjun forget about me Dan Allah" Murmushin takaici Arjun yay kana ya miƙe tsaye yace "Saduwar alkairi" ya nufi ƙofa zucyarsa cike da tausayin Sheikh yana ƙoƙarin buɗe ƙofa yaji Sheikh yace _"I Am in love Buddy"_ da sauri Arjun ya dawo ya zauna zcyarsa cike da farin ciki har baya iya ɓoyewa yace _"What a beautiful new?_ Wacece? Wa kakeso _Buddy just tell i promise you_ ko wacece sai ka sameta" maida idanunsa yay ya rufe yana ɓoye tarin da yazo masa yace _"Sure?"_ da sauri Arjun yace "Da gaske ba wasa, did i telling you? Bana faɗa maka da bakinka zaka faɗa min wacce kakeso da irin son da kake mata ba? Na faɗa maka babu ruwan so aduk sanda yaso yake faɗawa mutum _just go to the point who is she?"_ idanunsa ya buɗe tare da saukesu akan Arjun yana kallonsa dishi dishi Wani lafiyayyan murmushi wanda ya daɗe bai irinsa ba indai ba a gaban _Zahraaah_ bane yace "I love Zahraaah with all my heart, And i can't live without her Zahraaah itace komai na Arjun ban san yaushe ne hakan ta faru ba, Amma na samu kaina a soyayyar Zahraaah dumu², nace mata basu iya komai ba mata shashashu ne, but My Zahraaah tana da bambancin da sauran mata she's a darling ita bar so ce a kullum a zuciyarsa Sheikh Imam hamdan Balarabe, Buddy _I Ioves Zahraaah! I love her to the rest of My life_.Murmushi fal fuskar Arjun yace _"Who is that Zahraaah!?_ , Wacece ita gsky na tayata murna da samun ingantaccen Namiji wanda ko wacce mace za tasu zamunsa, Buddy kana da right na faɗa mata cewa kana sonta _Yeahh! U have a right And confidence_ ka shirya faɗa mata Sirrin zcyarka _I'll support you_ kayi amfani da damar ka kafin wani tsautsayi ya gifta Loves her care of her protect her Support her Buddy, mace na son soyayya kulawa ina da tabbacin Zahraaah zata soka" Murmushi Sheikh yay yana shafa ƙirjinsa wanda a zahirance danna zcyarsa yake bai son Arjun ya gane, gently ya miƙa hannunsa ya ɗauki mug ɗin da coffee ke ciki ya ɗura saman bakinsa rufe idanunsa yay sosai sbd ɗacin da yaji yana son coffee amma a yanzu sam baya sha'awarsa he can't remembered last day da yaci abinci. Mug ɗin ya ajjiye kafin ya sauke tagwayen ajjiyar zuciya yace "I love her, And she loves me to! But Soyayyar is _FORBIDDEN LOVE_ (Haramtacciyar soyayya)." Da rashin fahimta Arjun yace "SORRY! I na kasa fahimta kana sonta tana sonka And what's the problem?" Pouting lips ɗinsa Sheikh yay kafin yay wani irin tari da ƙarfi yace "She's My Mom i mean my Stepmom _FANNERH_" wani zaro ido Arjun yay yace "What Anut Fannah? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" gaba ɗaya office ɗin yay Shiru sai ƙarar A.c cikin wata mata Sheikh yace "What should I do Buddy? Kada kaga laifin zcyta Zahraaah is like My Airah Fairy, suna kama da Aljanata, na ɗauka kamar tasa nake sonta, daga baya na fahimci Kawai Ubangiji ya ɗura min sonta, Zahraaah tana da dukkan QUALITIES ɗin da nakeso daga wajan mace, Ina jin nai ba dai-dai ba Amma Arjun Trust me Alh inawa Zahraaah mahaukacin so" kallonsa kawai Arjun keyi yama rasa mene zaice masa sbd tashin hankali daya shiga. Fannah na kwance a saman bed ta rufe idanunta _Yesterday night will forever remain fresh in her memory_ Sheikh na musamman ne har yanzu tana jin ƙamshi da kuma ɗanɗanon Saliva ɗinsa da taushin laɓɓansa, tun fitowar safe da tayi ta kasa kallon Sheikh sbd kunya _The Images of yesterday night, The glimse of the occurances, The gentle love love making! The caresses of the mid-night, under the dim-light_ tana son Sheikh so na har abada Sallama taji kamar a mafarki da sauri ta diro daga kan bed ɗin tana dafe ƙirjinta. Tare da faɗin "Ya Falta" sai kuma tasa kuka tana rungome yayarta, sun daɗe suna hira Fannah ji tayi kamar ta faɗawa Ya Falta abinda yake damunta sai kuma taga it's our secret no need ta faɗa tunda tasan ba abune mai kyau ba. Tasu kuma ya Falta ta kwana amma taƙi wasu magunguna ta bawa Fannah tace inji Mama kolo, wasu manyan perfumes ta bawa ya Fatla da tare Kayan make up, har kuka tayi lokacin da zasu rabu. Mami tun safe suka tasu Amma mota tai masu tsiya suna tsakiyar titi tare da mai gyara ji tayi kamar tayi fiffike sbd fargabar dake ranta. DEEDAT ne zaune a babban parlonsa yana kallon wani breaking news a t.v kallon twins ɗinsa yay yace "You guy's where is your Mom?" Da sauri Aditya tace "Papi Ammi she's not feeling well tana ta kuka fa" da sauri yace "What ina big bro ɗin naku ina Aslam yake?" Anuska ta watsa hannu tace "I have no idea" kama hannun su yay zuwa part ɗin Ammi Tun a bakin ƙofa ya fara jiyo nishinta da sauri ya saki hannun twins ɗinsa ya buɗe ƙofar da sauri kwance ya sameta jikin jini.... 🤕karku ce komai ysin ALLAH yayi zanyi posting sai 5 na fara typing It's paid book 08119237616. 22/10/2021, 10:32 - 🤔🤔: 55-56 _*SIRRIN MU* RAYUWAR *SHEIKH* DA *FANNAH* RAYUWACE WACCE ZA'A CE BASU TAƁA TUNANIN ZASU SAMU KANSU A CIKI BA, ZATA IYA YIWUWA ACE ƘADDARA HAƊUWA DA *SHEIKH* YASA *BARRISTER* YA AURI *FANNAH* AMMA KU SANIN DUKKAN ABINDA ZA KUJI KUMA KU KARANTA ALRDY A HAKA TSARIN LABARIN YAKE SINCE BEFORE! BABU KUMA WANDA ISA YA KUJEWA TASA ƘADDARAR SAI DAI ƘADDARAR ABACE MARA TABBAS! KUMA ZATA IYA YIWUWA *SHEIKH* SAI YA KASANCE DA *ZAHRAAAH* SANNAN ZAI SAMU LAFIYARSA YA FARA TAKAWA KAMAR SAURAN MUTANE! *SHEIKH* MALAMINE AMMA BABU RUWAN ƘADDARA DA MATALANTAKAR MUTUM SO THINK BEFORE YOU TALK *NIMCYLUV* Da sauri Deedat ya ƙarasa inda take kwance cikin jini yana zuwa ya tsuguna ba tare da tunanin komai ya ɗauke ta zuwa wani part wanda da alama shi ne part ɗinsa, ganin jini yasa Anushka sakin kuka tana riƙe hannun Aditya, kasancewar Aditya tafi Anushka wayo yasa ta kama hannunta tare da nufar Parlo,har lokacin kuma Anushka bata daina kuka tana kiran sunan Ammi ba, ruwa Aditya ta ɗauko ta bata tana sha tana faɗin _"Uhm! Ammi,Ammi ce"_ shafa kanta Aditya tayi tace _"Sorry baby!, Ammi ce?"_ kai ta ɗaga mata ita kuma ta rungome ta tana rarrashinta. kwantar da ita Deedat yay saman wani bed madaidaici bayan ya samu jinin ya tsaya, dubawar farko da yay mata ya fahimci ƙaramin cikin dake cikinta ne ya fita, yaji ba daɗi da kuma kewar ɗan gudan jinin nasa amma lafiyar matarsa yanzu tafi masa komai dan haka ya tattara komai ya ajjiye dan baya buƙatar abinda zai samu matarsa _She's in critical condition_ domin jikinta yay mugun hawa ya rasa wacce kalar damuwa ta sanya ranta dama zuciyarta, _Sharp Sharp_ ya ɗaura mata drip ya ƙara mata gudun a.c kana yaja ƙofa ya rufe yana zuwa Parlo ya tarar da twins har sun yi bacci suna rungome da junansu, murmushi yay masu tare danna ball ba jimawa Nanny ɗinsu ta shigo Deedat tuni ya juya da sassarfa ya shige nasa part. Da Yamma yana zaune a Parlo ya kasa fita duk da aikin dake gabansa amma shi ɗin Mutum ne mai mutuwar son iyalansa yana kashe dukkan abinda yake ya bawa iyalansa time ɗinsu _He just make them happy_ dan rayuwa babu farin ciki kawai damuwa. Kallon Aslam yay yace _"Your Mom Need You son_ so stay with us nayi cancelled aikin nan baka rasa komai na rayuwa ba" Aslam yace "Papi na ajjiye _as your wish_ aikin ban kuma zuwa office ɗin" shafa kansa Deedat yay yace "Allah yay maka albarka, _i have a meeting_ so ka kula da mahaifiyarka da ƴan uwanka" jinjina kai Aslam yay yace "In sha Allah ur Excellencea Allah ya ƙara baka yawan rai Papina" cike da so da ƙauna Deedat ya rungome ɗan nasa yana jin wani iri a zcyarsa sakinsa yay yace "Ka Kula son ka tabbatar Ammi taci abinci" Aslam yace "Papi! Ammi tana da damuwa amma taƙi faɗa kullum tana cikin ciwo" murmushi Deedat yay yace _"Don't worry_ akwai lokacin da basai ka tambaya zata faɗa maka damuwar dake ranta ok!" Yana faɗin haka ya shige part ɗinsa _not too long_ ya fito sanye da wata dakakkiyar shadda sky blue sai zanna bukar yay kyau sosai haiba da kwarjininsa sun ƙara fitowa. Tana zaune ta rufe Idanunta taji ƙamshin turarensa ware idanunta tayi tana ɗan saikin Murmushin ƙarfin hali kafin ta miƙe tsaye tace _”Ur Excellence”_ Murmushi ya sakar mata tare da haɗata da jikinsa yace _"Finally my wife is back, so how the you feel now Madam AYSHART"?_ maƙalesa tayi tana ɗan sakin murmushi tace "Feeling better ur Excellence" peak ya bata a goshinta tare da riƙe hannunta zuwa Parlo yace "Allahamdulillah! Matata ta samu kin kusa Governor Deedat da ransa" dry tayi domin tana ƙoƙarin danne damuwarta a gabansa tace "Uhm wai ma And ina zaka?" Yace "Zan fita nema kina zauna ne?" Kaita girgiza masa tace "Ni AYSHART bance ba, ina zaka kai nauyin mutanan daka ɗauka kullum addu'a nake Allah ya baka ikon sauke nauyin dake kanka" hannunta ya matse yace _"I hope so.._ Amma mulki ba sauƙi" rungomesa tayi tace "Ina maka addu'a in sha Allah komai zai dai-dai" Aditya na ganin Ammi ta tashi da sauri tare da ajjiye Apple ɗin da take sha Anushka ma ta miƙe suna zuwa Ammi ta rungomesu, tana shafa kansu Deedat kuma ya kalli Aslam dake zaune sanye da Armless da 3gauther yace "Kai ka yafe rungomar?" Miƙewa yay yana sakin dry yace "Papi idan da twins bazan samu komai wajan Ammi ba" yana zuwa shima ta rungomesa Deedat kuma ya haɗa ya rungomesu baki ɗaya yace "Kune farin cikin Deedat ƙaunar ku tada nai nisa da abubuwa masu matuƙar muhimmanci a rayuwata, Allah yay maku albarka". Yana zaune saman Wheelchair yana yana operating system kusan dukkan abinda yake yi kawai yake amma hankalinsa na kanta yana lura da yadda walwalarta ta rago a kwana biyu, ga aiyukan cikin gida sun mata yawa har yanzu Mami bata dawo ba Granny ƙarfi ya fara janye wa Buhaiyya bata iya komai ba, Numfashi ya sauke lokacin da tazo ta gabansa ta shige cike da nutsuwa tana sanye cikin wata farar Laffaya mai kyau tai sharr da ita sai ramar dake fuskarta da kuma damuwa dan kana ganinta kasan cewa tana cikin y saɓanin shi dake ƙoƙarin danne damuwar dake fuskarsa, ta gama setting daining ɗin ta dawo kanta a ƙasa zata shige kitchen domin ɗauko masa furar da yake sha, yay saurin sanya ƙafarsa tare da taɗeta gaba ɗaya tayi baya zata faɗi ya ƙara sanya ɗaya ƙafar tasa ya tarota cikin rashin Sa'a ƙafar tasa ta goce abinka da mara lfy tayo kansa gaba ɗaya cikin sauri ya janye system ɗinsa ta faɗa jikinsa tana sauke numfashi tare da dafe ƙirjinta sosai ta tsoranta dan ta gaba bawa kanta sai taje ƙasa sai kuma taji ta sauka akan tattausan jikinsa dake fidda wani sihirtaccen ƙamshi, kasa kallonsa tayi kunyar abinda ya shiga tsakaninsu jiya yasa ta kasa sakewa yanzu haka ji take kamar ta nutse sbd kunya amma ta lura shi ko a jikinsa, shikansa idan ya tuna moment ɗinsu na jiya yana jin wani iri tsigar jikinsa duk ta miƙe ga wani sabon fellings dake ƙara yawa a tare dashi, Wasu scenes ne da suka kasa ɓacewa a idanu da zcyar Sheikh da Fannah, _Everything happened majestically in a dignified And inspiring way._ iya jiya ya gama gane weakness na jikin Fannah _and he wish ace everytime, every second Every minutes_ ya tare da Zahraaah ɗumin jikinta kaɗai na sawa yaji nutsuwa da ƙarfi a jikinsa ya ƙara tabbatar _Physical relationship_ na ƙara sanya so da ƙaunar juna. Fesar da numfashin yay kana ya buɗe idanunsa tare da saukesu a kanta bayan na kashe system ɗin, ganin yadda ta shige jikinsa ya dashi faɗin _"Hello Mummyna"_ turo baki tayi gaba bata yarda ta kallesa tana ɗan kaɗa jiki tafe "Uhm ni ka daina" taɓe baki yay yana sassauta Muryarsa yace "Baki damu dani ba ko Uhm?" Da sauri ta girgiza kai tace "Uhm ni yaushe nace haka? Kawai ina.." sai kuma tai Shiru cije lips ɗinsa yay clamly yay yace "Kina jin kunyar Malaminki right?" Mmkin yadda ya fahimci abinda yake ranta tayi kamar ya ƙara shiga zuciyarta yace "Ki daina Mmki, ina fahimtar komai na zcyar _Muhaddaserh_ shiyasa nake saurin gane naki tunda yanzu matsayinta kike har sai mun gama game ɗin mu" zcyarta ce ta buga da ƙarfi domin harga Allah ta manta da wata game ta riga ta sakankance, kallonsa kawai take ta kasa cewa komai yace _"I love her so much har ban iya faɗin yadda zcyata take sonta, She's beautiful more beautiful ma, her lip's UHMMM sweetness and honey kenan"_ kamar zatai masa kuka tace "Itama kayi kissed nata _just like you did to me"_ ware manyan jajayen idanunsa yay waje yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi cikin dauriya yace "Kiss? Ke kuma? When?" Ji tayi ranta ya ƙara ɓace tace "Eh! Juya mana a bedroom ɗinka" wani ƙawataccen Murmushi ya saki yana jan ƙwantaccen beard ɗinsa yace "You're dreaming Mmyna, ƙilan nai mafarkin ina shan sweet bakin _My Muhaddaserh_ ne" Idanunta cike da hawaye tace _"You mean u don't have any feelings for me"_ Yana lumshe idanunsa yace "Ni dai nace game And idan kikai winning why not na ɗan cillaki a zuciyar Malaminki" bata san ya akai ba sai jin ɗumin wani abu taji a saman fuskarta tattausan hannunsa a saman fuskarta ya tabbatar mata da hawaye take ba tare daya ƙara cewa komai ba ya ƙara jawota very close to him tare da copping face ɗinsu waje guda Murya na ɗan rawa yace "Are you cry because of me Zahraaah?" Sai kuma yay Shiru yana Kallon yadda take shassheƙar kuka rufe idanunsa yay yana fesa mata numfashi slowly ya fito da tongue ɗinsa waje tare da ɗurawa a saman fuskarta ya shiga share Dukkan hawayen daya fita daga cikin idanunta har lumshe idanunsa yake sbd wani ɗumin hawayen da yaji saida ya shanye hawayen tasss sannan ya tsaya yana riƙe hannunta yace _"May we live together in prosperity And blessings, Die together in love and Affection, blessings upon you blessings!.. May Allah's Rahma cover us forever"_ sam bra yadda Sheikh baya sonta kawai buga game ɗin sa yake bada ita as he said bakin ta tura gaba tace "To kace kana sona" Murmushin ƙarfin hali yay yace "Noo! Meyasa zaki sani abinda ban shirya yin sa ba? Na faɗa maki akwai lokaci to ki bari lokaci ya bai yana komai da kansa" hannunta ya ɗura a saitin zcyarsa wacce take bugawa da ƙarfi yace _"This is your humble ba"_ kaita gyaɗa masa yace "Just pray" And he start kissing her tun daga Ƙasan zcyarsa sautin sumbar ke fita tsut-tsut banda fitar da numfashi babu abinda suke sosai yake kissing bakinta da dukkan zcyarsa a wannan lokacin ƙasa controlling kansa yay zcyarsa ta gama ƙwaɗaituwa da ita banda wutar so da kuma ƙaunarta babu abinda ke cin zcyar Sheikh Soyayyar da Malamin Zahraaah yake mata ta musamman ce yayinda ita kuma ta kasa fahimtar sunan MUHADDASERH shine cikon sunan FATIMA a cikin guda tara daya gaya mata. (Wannan shine sabin babun soyayyyar SHEIKH da FANNAH). Mami taja tsaki tana faɗin "Wlh kayan nasara ko asarar kuɗi,Ni nan zcyata har wani numfashi take sbd damuwa ji nake kamar nai fiffike wlh" Kubra tai dry tace "Me kike ci na baka na zuba haka Saudat? Da kin koma gida fa shkknan yanzu dai dole mu ƙara kwana domin motar ga zatai aiki yanzu ba" cikin damuwa Mami tace "Ba zaki gane ba ji nake kamar wani abu sai shiga tsakanin sweet Imam da waccen shigar yarinyar wlh sai naga bayanta ƴar matsiyata kawai" Dry Kubra ta sakeyi tace "Ai ɗan naki ne wlh yayi daga gani kuma nasan zai kawo wuta" Murmushi Mami tayi tace "Yeah! He's honey ba'a mgn amma wlh inajin sai anyi min ɗinki har yanzu zafi na keji wannan shegen karan kamar Mutum ko Barrister ban taɓa ji abarsa ta shige can ciki ba sai wannan dabbar" Kubra tace "Hhhhh ai ina jiyo ihun ki fa, ai dai-dai dake kika samu tunda kin raina Barrister" Mami tace "Allah ina jin mutum ne ba kare ba abun is too much fa" a haka suka ƙara hotel ɗin dake kusa da inda suka sauka. Granny ce ta fito riƙe da hand-bag tana kallon Fannah tace "To ni zan tafi sai na dawo" Fannah ta marai-raice fuska tace "Ayya! Granny nima zani fa,tunga naga Buhaiyya zaku" Granny na ɗan kakkaɓe jikinta tace "A'a bana son sallama wannan ai gantali ne daga ganinki anga mai ciki bazan fita dake waje baki ya kamaki na shiga wajan Barista ba" Fannah jin kalmar tai wani iri wai ciki kasa magana tayi Granny tace "To zamu huce Nida su wancan yaran to mutane ne su dinga sanya sunaye ba daɗi bare dadaɗawa, ke yama sunansa?" Ta tambaya tana kallon Buhaiyya tace "Fareeq" Granny tace "Yawwa! Shi fa yar kirki to ba gwaramin shi akan wajan gantallan diriban ba dan Allah? Tunda ai ba gama sanin tuƙin nasa nai ba" Fannah tace "haka ne, Allah ya tsare ya kiyaye" Granny tace "To ko dai na tawo baki da taura da magarraya ne naga ganki kamar kazar da ƙwai ya fashewa" miƙewa Fannah tayi tana sunkuyar da kanta ƙasa tace "Sai kun dawo Granny" Buhaiyya tace "Anut Fatima sai mun dawo" Murmushin ƙarfin hali tayi tace "Uhm Allah ya kiyaye" daga haka tai part ɗinta Hanne mai aiki kuma ta fara shirya dinner. *DAN ALLAH DAN ANNABI KIJI TSORAN ALLAH KADA KI KARANTA ABINDA BA HAƘƘIN KI BANE DAN ALLAH, LITTAFIN SIRRIN MU NA KUƊI NE AKAN 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616* Bayan Isshā Barrister yana ta sauri ya ƙara so gida dan yau burinsa ya kasance da Fatimansa kamar zai tashi sama haka yake jinsa, yawarsa ce ta fara ƙara yana ɗagawa Alhj Kamal yace "Duk abinda kake ka bari kazo yanzu na dawo ba bisa son rai na ba Oga yana buƙatar ganinmu kuma.." bai tsaya jin abinda zai ce ya kashe wayar tare da juya kan motar yana jin ransa babu daɗi. Parking Arjun yay yana kallon Sheikh yace "Buddy kaci gaba da addu'a kuma ka kiyaye duk abinda zai haɗaka da Anut Fatima, ita haramunce a gareka yanzu kalli inda ka rame ka sanya damuwa a ranka ga jininka da yay mugun yawa ga ciwon Zcyarka kai ɗaya abun yay yawa" banza Sheikh yay masa Arjun yace "Bari na shigar da kai wlh nai missed My Aliyah" sai lokacin Sheikh ya buɗe ido yace "Banza ɗan iska" dry Arjun yay yace "Naji ba komai rai dai" daga ya fito da Sheikh suka nufi cikin gida Fannah ce kaɗai a Parlo tana watching TV tana sanye cikin wata gwon mai kyau roba-roba ta tufke sumar kanta wacce ta tsaya tai kamar alkaki, tana jin sallamarsu tai saurin ɗaukan veil ta rufe jikinta wata Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke daman fargabarsa kada Arjun ya ganta a haka, ɗauke kai Sheikh yay Irin bai ma san da zamanta a wajan ba Murya a sanyaye tace "Sannunku da zuwa" Arjun ne ya saki Murmushi yace "Yawwa Anut Fatima yau aikin lada nai na raka buddy zance" da sauri ta kalli Sheikh taga ko inda take bai kala ba kasa cewa komai tayi gudun koma kada ta bada kanta yasa tai saurin barin wajan. Har bedroom ya kaisa bai bar gidan ba sai da Sheikh yay wanka ya sanya kayan bacci kana yay masa sallama. Yana zaune a haɗaɗɗan parlonsa yana rufe idanunsa jin wata daddaɗar Murya a t.v yasa ya buɗe ido news ake ana haska wani Governor dake ziyartar maƙabarto da asibitoci, idanunsa ƙurrr akan fuskar Mutumin kafin kuma ya sauya akalar kallonsa zuwa kan twins ɗin da suke riƙe a hannunsa sunnan Governor ya duba yaga ansa _THE GOVERNOR OF LEBANON GOVERNOR DEEDAT_ samun kansa yay da ƙara kallon Mutumin haka nan yaji so da ƙaunar mutumin a ransa yana sone yaga Mutum mai kyautatawa talakawa. Kashe kallon yay sbd abubuwan da zcyarsa take raya masa turo ƙofa tayi a hankali ta shigo kana ta maida ƙofar ta rufe hannunta riƙe da tray ɗin abinci ta ajjiye a gabansa sbd yana zaune saman carpet ya tanƙwashe ƙafafuwansa baza ka taɓa cewa gurgu bane, tana ajjiyewa ta juya zata fita yay saurin riƙe ta tare da zaunar da ita yace "Kee!" Turo baki tayi tace "Ni ka sakeni" yace "If not kuma fa,zaki daken?" Girgiza kai tayi ba tare da tayi mgn ba yace "zauna" ƙin zama tayi tace "Bacci ina ji" yana Murmushi domin ya gama gane fushin da take na zancan yaje wajan wata da Arjun yay mata yace "ki daina gani na haka, wlh zaki mmki gwamna ki zauna" ka faɗa ta noƙe tace "Ni dai a'a" batai aune ba taji ya fincikota jikinsa tare da ture tray ɗin abincin ajjiyar zuciya suka sauke a tare botten ɗin rigar sa ya buɗe ƙwantaccen gashin ƙirjinsa ya bai yana kana ya sanya hannunsa ya zare baby hijab ɗin jikinta ya ƙara mannata da ƙirjinsa yace "zaki kashe ni da soyayyarki Zahraaah" jin jikinsa zafi rauu yasa ta zare ido tace "Meya samu Malamina?" Yana shafa sumar kanta yace "Kina son sani?" Kai ta ɗaga tana kwaɓe masa fuska yace "Kada ki damu" yana faɗin haka ya kwantar da ita tare haɗe bakinsu waje guda ya shiga bata wani gigitaccen kiss mai tsayawa a zuciya a wannan lokacin shi kasan Sheikh bai taɓa sanin cewa zucyarsa da kuma gangar jikinsa na buƙata kasancewa a duniyar mace ba sai yau, idanunsa har wani zubda ƙwalla yake yana sauke numfashi tare sauke ajjiyar, cikin ƙaramin lokaci suka zama naked wanda basu taɓa sanya ran haka aikin rayuwarsu ba. Lokacin Sheikh baya gane fari balle baƙi a lokacin kuma Fannah tana tuna Yadda JALILERH ta kasance tare da MUHAMMAD JALAL BOBO(Uncle ne) ne, kafin tunaninta ya koma kan azabar da ZARINA TA SUMEWA SAIF( the new emir) idan kuma ta tuna azabar da M.K ya ganawa ANUSHA (Raino ne sila) sai taji zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske Idanunta ne ya fito waje ta shiga tura Sheikh tana kuka tace "Kada ka aita abinda zai wargatsa farin cikin mu dama duniyar mu baki ɗaya kada mu biye zucyarmu da ruɗin sheɗan mu aikata ba dai-dai ba Malamina ka tuna ayoyin Ubangiji akan aikata zina dan Allah..." Bata ƙarasa maganar ba sbd wani azababban zafi da kuma raɗaɗi daya shigeta, Sheikh kuka ya saki zcyarsa cike da tsanar abinda yake aikatawa amma gangar jikinsa takii bashi haɗin kai ƙara ingiza sa take zuwa ga Zahraaah! Bakinsa ya zare daga saman nippy ɗinta ya shiga faɗin _"Yasubuhanallah!"_ ya kuma ya ƙara danna jikinsa a jikinta da wani irin ƙarfi da yazo masa gaba ɗayansu suka saki kuka bakinsa na rawa ya shiga addu'ar kasancewa da iyali, kafin a karo na biyu ya ƙara danna jikinsa nan take ji da ganinta sukai ƙaura daga gare ta Sheikh kuka ya saki Yayinda da kuma jijiyoyin ƙafafuwansa suka shiga mutsawa tare da saki yana jin yadda ƴan yatsun ƙafarsa suke ƙara kamar wanda aka ƙarawa ƙarfi haka ya shiga ratsa jikin Zahraaah... Ai weekend lfy🌚 NIMCYLUV 22/10/2021, 10:33 - 🤔🤔: 5️⃣7️⃣-5️⃣8️⃣ _SUBSCRIBE MY YOUTUBE CHANNEL_ Nimcyluv T.V https://youtube.com/channel/UClywbagpRx5qlVyOy0ZPPDA Da sukkan ƙarfinsa yake ƙarasa ratsa jikin Fanan, a zabar dake ratsa jikin Fannah yafi a zabar da LAMRAT taji wacce YISHAM ya gama mata, duk shigarsa jikinta numfashinta ya ɗauke shi kansa bai taɓa sanin yake da girman halitta ba sai yanzu, tun farko da yay try na shiga jikinta yasan cewa shi ɗin na musamman ne, kuma irinsu Sheikh daban suke a cikin maza, sun san takan mace shawo kan mace bayayi masu wahala, cikin zafi² da kuzari haɗi da jarumta yaci gama da lulaawa duniyar daɗin ta, duk Yadda yaso kiran sunan Allah a wannan lokacin kasawa yay babu abinda ya keji yake gani sai _Zahraaah!_ ɗumin jikinta ƙara zautar dashi yake yana jin kamar ba'a duniya yake, Yana ratsa jikinta har ya samu nasarar basa tantanin budurcinta, gaba ɗaya suka saki gigitaccen ihu. Fannah na ihun na azabar daya farkar da ita daga ɗan ƙaramin suman da tayi, yayinda Sheikh yake ihun zamansa cikakken namiji da kuma wani daɗi mara misaltuwa daya shigesa, a lokacin ji yay duk nauyin da kansa yake mata ya sauka rabin ciwonsa na zuciyarsa. zcyar Sheikh banda zafi da raɗaɗi babu abinda take masa, cike yake da tsanar rayuwarsa baki ɗaya yana mai lamadar zuwansa duniya a halin yanzu, bai taɓa jin ya tsani rayuwarsa irin yau ba. A Yadda ya kejin kanshi a yanzu bai ƙi ya dauwama a jikin _Zahraaah_ ba Bai ƙi yaci gaba da jin daɗin jikinta a wajan nan ba, he will have this gril a nan tsakar carpet ɗin parlo'n sa ba, which is not nice, shi kansa bai taɓa sanin haka akeji idan an taɓa mace ba sai yau, _He's crazy about Zahraaah Omg!_ Tuni Fannah ta ƙara ficewa a hankalinta baya sanin me yake sbd shigarta yake da dukkan ƙarfinsa da lafiyarsa, samatakarsa, yadda Sheikh yake juya Fannah baza ka taɓa cewa shi ɗin Nakashasshe ba ne. Daɗin da yaywa Sheikh yay yawa yasa ya saki kuka cikin shassheƙar kuka yace _"Yasubuhanallah! You Make me so horny Zahraaah I feel like a wild animal right now! Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! You're my world Zahraaah"_ sai kuma ya ƙara sakin kuka while jikinsa na jikinta yana ratsa lungu da saƙo na cikin hole ɗinta. Sheikh Imam hamdan Balarabe kenan a wata Ta daban wacce bai taɓa tunanin samun kansa a ciki ba, zucyarsa ta shiga fallasa abinda yake ransa wanda bai shirya faɗin su ba, ba kinsa na rawa idanunsa a saman farar ƙyakkyawar fuskarta wacce tai faca-faca da hawayen azaba fuskar tai jajurr yace _"You're the only girl that I'm ever going to need Zahraaah! I love you scatter, I can't handle a minute not touching you Idan kusa dani, My hands want to feel every in of you, Innalillahi!_ Zan mutu da baƙin cikin abinda na aikata zcyata da gangar jikina sunci amanar addini..," sai kuma yay shiru yana manna lips ɗin a nipples ɗinta da sukai jajirr ya shiga fesar da numfashi da sauri yana jin yadda mararsa tai wasai ba ciwo ba kumburi, hawayen dake fita daga cikin idanunsa ya sauka saman fuskarsa yasa taja wahalallan numfashi tare da buɗe baki zata fasa wani sabon ihun da sauri ya sanya bakinsa cikin nata ya rungome ta tsam a jikinsa yadda jikinta ke rawa haka nata, kanta kawai yake shafawa, duk abinda suke still jikinsa na cikin nata ya kasa fita sbd har yanzu bai samu nutsuwarsa da yake son samu ba, jin tai Shiru ta fidda wani wahalallan numfashi da ajjiyar zuciya yasa ya cire bakinsa, Muryarsa na rawa yace _"Please lemme play with you or I will cry for you"_ yana mgn yana ƙara shigewa jikinta yana bata wani hot kiss a fatar wuyanta, Murya can ƙasa yace _"Don't leave me alone ZAHRAAAH_, Zan mutu wlh ki ɗauki wannan matsayin sabuwar ƙaddarar Sheikh da kuma Zahraaah, zan fifitaki zan rayu dake cikin aminci da kula" yana faɗin hakan ya sakar mata wani finannen sexcy cry a kunanta. Kuka itama ta saki hadda shassheƙa burinta ya cire jikinta ko ta zamu sassaucin azabar data keji a jikinta, wajan 50mins Kafin Sheikh ya samu nutsuwa ya mirgina kefenta yana saikin Ajjiyar zuciya mai makon yaji daɗi sai ya samu zcyarsa cike da baƙin ciki da kuma ƙonar rai yana jin kamar an saya masa dutse a ƙirjinsa a danne zcyarsa sbd nauyin da tayi masa, cikin ƙaramin lokaci kuma wani zazzafan zazzaɓi da ciwon kai ya saukar masa a jikinsa teeths ɗin sa har wani haɗuwa yake cikin dauriya da jarumta ya juya tare da kallon Fannah dake fita da hawaye ta rufe jikinta da rigar baccinta wacce yay wurgi da ita, ba fushinta bane damuwarsa a yanzu fushin Ubangiji shi ne damuwarsa yay zaiyi da rayuwarsa ne ina zai sanya kansa yaji daɗi mene amfanin Iliminsa , mai yasa rayuwa take juyasa kamar ball ne, kansa ne ya sara yay saurin dafe kansa yana kiran sunan Allah. Cikin rawar murya yace "Am so sorry Zahraaah! Please for give me ki yafewa Malaminki mana" kuka ta ƙara sawa wanda ya ƙara firgitar da Sheikh da sauri yana jikinsa zuwa gare ta ya miƙa hannunsa gaba ɗaya ya jawota jikinsa tare da rungome ta sosai yace "Wlh nayi ladama na tafka babban kuskure, sai yanzu nasan ƙaddara bata shallake kan kowa, Zahraaah ilimina bai tseratar dani daga aikata zina ba, Zahraaah karatuna ya tashi a banza bai min rana ba, ji nake kamar na mutu na....," Da sauri ta toshe maki tana ƙara sakin wani sabon kukan, idanunsa na zubar da hawaye yace _"Cry as you can, i got you okay, you'll not die and nothing will happen to okay Za.....raaaah!"_ he could feel yadda hawayenta ke jiƙa masa gashin ƙirjinsa, kuka take sosai ta kasa dainawa har wani ihu take irin kukan nan na kamar an maka mutuwa tai bala'in bashi tausayi,yadda take kukan da ace da Mutane a gidan Tabbas za'a jita, And baice mata uffan ba banda patting bayanta da yake. Dan kanta tai shiru kana ta sakesa daga mugun riƙon da tayi masa gently ya zareta daga jikinsa looking at her face wacce ta cika da hawaye a hankali yasa tattausan hannunsa ya goge hawayen yace "Ki yafe min Zahraaah, kafin na nemi yafiyar Ubangiji na maki laifi" Ajjiyar zuciya ta sauke kafin ta kalli fuskarsa wacce har wani Shinny ta ƙara tace "Damuwata bata abinda kaimin mace, ban san meyasa ka aikata haka gareni ba bayan ba sona kake ba, mai yasa why Malamina? Ni ban cancanci ka soni bane ko me?" Sai kuka ta hau dukansa gyara zama yay yana ƙara buɗe mata jikinsa yadda zata ji daɗin dokansa Idanunsa a kanta yace _"SHEIKH IMAM HAMDAN BALARABE LOVES YOU_ I LOVE YOU ZAHRAAAH YEAH! INA SONKI BAN SHIRYA FAƊAR KALMAR BANE, YOU'RE MY MUHADDASERH, MY EVERYTHING" baki ta saki ga wasu sabbin hawaye da suka fara saukar mata, saukar mgnar taji kamar ruwan sama Murmushin takaice yay idanunsa na fidda hawaye yace _I promise to protect you you till my last breath Fatima Zahraaah! I promise to stand by you harsai inda ƙarfina ya gaza, stop cry Jewel_ daɗin da magnar tai mata yasa taja jikinta da sauri zata rungomesa yay saurin jaa baya yana girgiza mata kai yace. وكون ذلك سيكون إثبات فرحي، في قلبي، مرادي كل يوم أن ترض بأني أحبك. "Ki yadda Sheikh Imam hamdan Balarabe yana sonki dan Allah kada ki bari abinda na aikata gareki ya zama sillar da zaki amfani da ita wajan wulaƙanta ni bayan kin san all abinda ya faru bayin kai na bane, ANAAA UHIBBIKI ZAHRAAAH har abada" yana faɗin hakan ya fara ƙoƙarin jan ƙafarsa ya shiga cikin bedroom ga mmkinsa sai yaji ƙafarsa ta miƙe ba kamar Yadda ya saba jin jijiyoyin ta a riƙe ba, da mmki ya fara ƙoƙarin tashi wata ƙyakkyawar ajjiyar zuciya ya sauke yana mai ƙanƙame jikinsa yana kasa mutsawa sbd tsananin mmki daya kusa kashesa, babu ƙasar da ba'a je ba akan wannan ƙafar babu roƙan Allah da bai ba a ɗakin Allah akan samun lafiyar ƙafarsa sai ganshi yau shine ya Miƙe da ƙafafuwansa, wasu hawayen farin ciki ne suka fara sauka daga cikin idanunsa zuwa saman fuskarsa, fannah zallar mmki yasa ta kasa mutsi daman tuni kalaman sa sun narkar mata da zcy sai gashi yanzu wani abu mai kama da almara yana faruwa, Yasubuhanallah lallai Sheikh nada banne yana tsaye akan ƙafafuwansa daman duk wannan abun rigar jikinsa bata zame ba, yana da tsayi domin yafi Arjun tsayi ga wani faɗi da yake dashi siffarsa mai kyau da tsari ta ƙara bai yana, tashi take ƙoƙarin yi amma zafin da taji yasa ta saki ƙara da sauri ya juya ganin abinda take yasa ya nufi inda take Kallonsa kawai take tsahun watanni biyar kenan tana tare da Sheikh amma yau shine yake taka ƙafafuwansa Al-hakkamu kenan mai yin yadda yasu a lokacin da yasu, gaba ɗaya ya durƙosa gabanta yama kasa cewa komai sai kawai ya ɗura fuskarsa a shoulder ɗinta ya saki kuka yace "Kinga ko Zahraaah? Bamu san Abinda Ubangiji ya ɓoye a tsakanin mu ba, na aikata ba dai-dai a lokacin kuma na samu lafiyar ƙafafuwana wanne Ɓoyayyan al'amari ne wannan, look Zahraaah dukkan abinda ya faru it's our secret kada ki bari kowa ya sani, Jewel kalli nima zan fara tafiya kamar kowa, bana faɗawa Granny komai lokaci bane Thank you God! Thank you for everything Allah ka ƙara samin tsoranka a zcyata Ubangiji ka kiyaye min imani na" wani irin tauyinsa ne ya kamata zatai kuka saurin rufe mata baki ba tare daya ƙara mgn ya dubi jinin dake jikinta bai tsaya tunanin komai ba dan bashi da wani lokaci ɗaukan ta yay cak kamar baby ya nufi cikin bedroom ɗinsa da ita. Yana zuwa ya nufi cikin bathroom ɗin sa da ita tana riƙe a jikinsa ya haɗa warm water ya sanyata ciki, ƙara ta saki sbd zafi da raɗaɗin daya shigeta, Kallonta yay a hankali yace "Sorry! Kiyi hqr ko" bata kallesa ba tace "da zafi ruwan fa, kuma ni wajan ciwo yake min" lumshe idanunsa yay kafin ya ɗan ja numfashi cikin ƙasa da murya yace "Ina kenan?" Tana turo baki gaba tace "Me?" Ba tare daya kalleta ba yace "Ni! Ba komai" ruwan ya huce ya zubar ya ƙara haɗa wani a wannan saurin riƙesa tayi tana sakin kuka tace "Wayyoooo bapiii" girgiza mata kai yay ba tare da yayi mgn ba ya juya tare da ficewa daga cikin bathroom ɗin, yana fita ta sauke ajjiyar zuciya tana ƙara ware ƙafarta ko taji daɗi, wani murmushi ta saki tana shigewa cikin ruwa ita kaɗai tasan yadda take jin so da kuma ƙaunar Sheikh a ranta, Sheikh nada banne kamar yadda soyayyarsa tada bance a ranta, ba zata taɓa haɗa soyayyarsa data wani a ranta ba Cikin jin daɗi tace "Love You so much My Malamina kai ɗin daban kake" ta faɗa tana shafa brest ɗinta dake mata zafi² sbd wahalar da suka sha a wajan Sheikh. Yana fita kai tsaye Parlo ya koma cikin nutsuwa ya fara mopping wajan yana gamawa ya fesa airfreshner ya ƙaro gudun a.c zubewa yay saman sofa yana maida numfashi lallai mace sai ta zautar da mutum shiyasa wasu suke cewa mace ƙanwar sheɗan bai san ya ake aiki sbd bai taɓa yi ba sai gashi yanzu shine dayin mopping da sauran aiki duk a sanadin mace, agogon parlo'n ya duba yaga wajan 9:30 sam bashi da wani sukuni sbd kunyar Ubangiji daya keji amma wacce hanya zaibi har Allah ya yafe masa wannan lukutin laifi, ko dai zai kai court ne domin a cire haƙƙin Ubangiji a jikinsa? Miƙewa yay ya shiga zagaye Parlon tunani fal ransa ya kasa yankewa kansa hukunci, abin duniya yay masa yawa gently ya nufi ƙofar bedroom ɗinsa yana zuwa yaga bata fito daga cikin bathroom ɗin ba, a hankali ya bubbuga ƙofar amma shiru cikin nutsuwa ya tura ƙirjinsa na buga yana shiga yay saurin janye idanunsa sbd shaf ya manta naked take, tana kwance cikin ruwan tuni bacci wahala yay gaba da ita sai Ajjiyar zuciya ta saukewa, wani wani long white ɗin towel ya ɗauka idanunsa a ƙasa yana zuwa ya cilla mata ya samu ya ɗan rufe cikinta kafin ya sanya tattausan hannunsa ya fara taɓa kumatunta firgita tayi ta buɗe baki zata saki ihu yay saurin rufe mata baki, miƙewa yay ya nufi ƙofa yana faɗin "get down before I coming back". Baki ta turo tana mur guɗa maki yana shafa sumar kansa yace "It's your time Mmyna" ruwa ta ɗebo zata watsa masa yay saurin fita yana rufo Kofar, Sharp² ya nufi part ɗin Fannah har lokacin su Granny basu dawo ba walking slowly ya shiga bathroom ɗinta cikin nutsuwa ya saukarwa kansa shower yana fesar da numfashi kallonsa yakai zuwa ga Sheikh ɗinsa yaga har lokacin halbawa take tana dripping, bayan yay wanka ya ɗura da wankan tsarki, bathrobe ya saka kansa na ɗigar ruwa ya fito, wasu sabbin kayan bacci ya ɗaukar mata kana ya fice daga cikin part cike da nutsuwa. Lokacin daya nufi part ɗinsa yaji ƙarar mota da sauri ya ƙarasa shigewa yana zuwa ya sameta zaune a saman bed kanta a ƙasa Kallonta ya shigayi yana jin wani iri a ransa. *_DAN ALLAH DAN ANNABI KADA KI KARANTA HAƘƘIN DABA NAKI BA PLEASE, LITTAFIN SIRRIN MU NA KUƊI IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616_* Saurin janye idanunsa yay daga gareta tare da ajjiye mata kayan a kefenta yace "Wear it now" turo baki tayi tana kwaɓe fuska zatai kuka wanda yasa ya kalleta ba shiri yace "What again?" Tana mirginawa saman bed zata kwanta yay saurin ƙarasawa wajan ya riƙeta yace "Keee!" Idanunta a lumshe tace "bacci na keji" ware idanunsa yay waje kamar mara guzari yace "Baki da kai ashe?" Tace "Uhm whatever nidai bacci na keji kuma yunwa na keji" jin footsteps yasashi jawota kusa dashi idanunsa a rufe ya ware towel ɗin jikinta ya fara ƙoƙarin sanya mata farar night gown. Idanunta ta buɗe sosai a saman laɓɓansa wakanda sukai jajirr hannunta na rawa ta ɗura saman bakinsa wani iri yaji wanda yasa yay saurin rufe idanunsa gaba ɗaya ta saukar masa da kasala a jiki baya yay itama kamar an janyo ta tayo kansa gaba ɗaya suka zube a saman Parlo, ƙoƙarin tashi yake amma gaba ɗaya ta saukar masa da kasala a jikinsa, Fannah kowa wani sabon so da ƙaunar Sheikh ne ya ƙara ratsa mata zcy lokaci guda taji shauƙinsa na fisgarta, jan numfashi yay cikin damuwa yace "Please Zahraaah tashi" girgiza masa kai tayi tace "Please ka barni nai bacci a jikinka daman nayi missed jikin Mamana" kai ya ɗaga yace "Ok ɗa gani to sai mu hau bed ko?" Marai-raice fuska tayi tace "wayo dai" Ya iyali wannan ba zata gane ba. Granny ta zube saman kujera tace "Kai yau naga abin almara a gidan bikin nan" Murmushi Buhaiyya tayi tace "Ya gidan shiru ina Anut Fatima?" Kwaɓe fuska tayi tace "A'a babu ruwanki Hayayya, kin san me ciki da son bacci balle yanzu dare yayi" Buhaiyya tace "Mene kuma Hayayya Granny?" Turo ɗauri Granny tai gaba tace "Waya sani kuma? Haka naji ganlalliyar uwarki na faɗa Yooo meye laifina kuma a nan?" Fareeq yay hamma kafin ya miƙe yace "Gud night Sis and Granny" da sauri Granny tace "A'a ina zaka kuma kamar yaƙi fisabilillahi? Maza ungu kaiwa Imamu kilishin nan, Bazan iya cinye abu ban sammasa ba" karɓa Fareeq yay yace "Allah yasa bai bacci ba" tace "A'a gsky bai zama sallamme ba tukunna, nasan yana duba ƙawa'idi" bai ƙara mgn ba ya nufi part ɗin Sheikh. Kuka ta sanya masa tace "Pls bakai ka fara ba mene laifina yanzu danna buƙata" dafe kansa dake sara masa yay yana fesar da numfashi cikin sauri kasa ce mata komai ba sbd bai san kuma mene zaice mata ba, kukanta har ransa ya keji mai yasa ba zata fahimci abinda suka aikata haramun bane, bayanta ya bubbuga murya a shaƙe yace "Ok" da sauri ta saki Murmushi tana ɗura fuskarta a tashi tace "Love You so much" "Uhm" kawai yace yana rufe idanunsa turo baki tayi tace "To kace kana so na" ware idanunsa yay waje yana juyasu ya fahimci yanzu kawai rigimar take ji dashi a hankali yace "To nace" girgiza kai tayi tace "Ni dai ba haka ba" cikin tsawa da damuwa yace "Wai what's this Zahraaah?" Tsoran daya bata yasa tai saurin ƙanƙamesa tana sakin kuka Rungome ta yay sbd tausayin data bashi Calmly yay kafin yace "Ok _I love you Fatima Zahraaah_ yi abinda kikeso" ajjiyar zcy ta sauke dan ba zata iya fushi da Sheikh ba a hankali ta ɗura bakinta saman nasa ajjiyar zcy suka sauke da sauri kuma ya runtsa idanunsa yana jin yadda take ƙoƙarin kama lips ɗinsa ko kiss ɗin da take ƙulafucin yi bata iya ba, bakinsu ya haɗu cikin na juna sosai tana ƙoƙarin fara kissing ɗinsa suka ji ƙarar abu a saman su. BONOS PAGE YOU CAN SHARE IT IF YOU LIKE. YADDA NA TSARA LABARI NA A HAKA ZAN TAFI, DUKKAN ABINDA YA SAMU SHEIKH DA FANNAH ƘADDARA CE WACCE TA RIGA FATA. *TALLA! TALLAH!! TALLAH!!!* HALACCIN MAZA BIYU! *Duk da ta kasance goyon kaka hakan bai gurb'ata tarbiyyar ta ba, sai dai ta wayi gari da rashin makusantan da sune adon duniyarta, a lokacin da ta samu shiga aljannar duniya sakamakon had'uwa da shi, a yayin ne wata guguwar k'addara ta kawo sauyi* Shin wane sauyi ne...? *Sihirin bai sauka kansa ba sai kan uwar da ta kawo shi duniya, wanda ya sababba tarwatsewar rayuwarsa a kan furucinta na cewar...* Wane furuci ne...? *Ta zab'i rabuwa da d'an da ta haifa ta shiga duniya, dalilin fuskar jaririn tana fama mata wani tabo da ya mamaye zuciyar da ke k'irjinta...* Wane tabo ne...? *A lokacin da ta yanke k'auna ga rayuwa, sai tayi gamo da Halacci na biyu...* Shin wane halacci ne? Kuma wanne ne halaccin farko? Na san kuma kuna yi wa kanku wad'annan tambayoyin, kuma za ku samu amsarsu kad'ai ne cikin gawurtaccen labarinnan mai suna *HALACCIN MAZA BIYU* wanda marubuciya *REAL LADINGO* ta rubuta. Babbar tambayar ma shin ya HALLACIN MAZA biyu yake ga mace? marubuciyar ce kad'ai ke da wannan amsar, kuma za ku same ta ta hanyar sayan labarin a kan 300 kacal👌Kar ku sake a yi babu ku domin wannan tafiyar ta daban ce🥰 Za ku iya tuntub'arta a kan wannan number +22796515805 domin sayan labarin. 22/10/2021, 10:34 - 🤔🤔: 5️⃣9️⃣-6️⃣0️⃣ Gajiyayyun idanunsa wanda sukai jaa sbd yanayin damuwa da kuma a zabar da ya keji ya shiga buɗe idanunsa yaga abinda yay wannan ƙarar, Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke lokacin da idanunsa ya sauka akan kwalbar parfume ɗin data faɗo daga saman dressing mirror, idanunsa ya mayar kan Fannah yaga duk abinda take ta kasa kissing bakinsa a hankali ya sanya tattausan hannunsa ya shafa sumar kanta kana gently ya zare laɓɓansa wanda suka jiƙe da yawon bakinta, sai a lokacin ya fahimci bacci ya fara ɗaukan ta a hankali ya miƙe tsaye da ita yana tunanin yadda zai kai ta bedroom ɗinta ba tare da wani a gansa ba, walking slowly ya nufi royal bed ɗinsa da ita yana zuwa ya shimfiɗeta ya juya kenan zai shiga bathroom yaji ta tare riƙe tafin hannunsa gam, lumshasshun idanunsa ya saukar a saman fuskarta yana nazarin abinda zai akan wannan lukutin abin daya tunkaro rayuwarsa, Yana son Fannah so bana wasa son da bakinsa yay kaɗan ya faɗesa, a hankali ya zare hanunsa daga cikin nata, cikin nutsuwa da kuma kamala ya fara tafiya yana gaf da shiga bathroom yaji ana buga ƙofarsa,cak ya tsaya ya shiga juya fararen idanunsa. Daga can waje kuma Fareeq ne tsaye yana Shirin buga ƙofar yaji ƙarar abu tsayawa yay domin a tunaninsa wani ne a cikin bedroom ɗin, jin shiru kuma yasa ya fara tunanin buga ƙofar sai kuma ga Granny ta ƙarasu wajan tana faɗin "Muna fikin Allah! Ni zaka munafurta rimi² na yarda dakai kilishin nan badan bana so ba bayar ka bawa Imamu shine ka tsaya zaka cinye? A'a wlh sam wannan ba rayuwa bace idan yau kaci Mama gobe kaci jibi kuma idan baka ci ba ai sai ka farar tunanin yagar fatar mutum, bawai cin mutuncin ba amma dai wannan kalan maita ce, bar iyayanka da gantali amma babu maye" Kallonta Fareeq yay kana ya haɗe rai yace "Ai sharri kuma Granny? Kinga kilishin amma tunda kince haka wlh sai na cinye kinga jibin sai na fara yagar fatar jikinki" zare ido tayi sai kuma ta zare bakin zani ta shiga matsar ƙwalla tace "Muhammadur Rasulullah! (S.A.W) Yanzu daga faɗin gsky sai zagi? Wlh Ni bada wata manufa na faɗa ba kawai idanunka na gani kamar na mayo" dry Fareeq yay yace "Keta shafa kinga kam dana fara maitar sai dai wata bake ba" kuka ta ƙara fashewa dashi tace "Yanzu mai sunan indiyawa koza kaci naman mutum ai banda na tsofaffi" yana tafiya yana faɗin "baki da labarin irin naku yafi daɗi musamman kai masa gashi mai kyau" majina ta face tace "To wlh sai dai kaci gantalalliya uwarka Amma kurwata kurr" tana faɗin haka ta nufi bedroom ɗinta daman Buhaiyya tuni ta shige part ɗinta sbd baccin data keji, Granny na zuwa bedroom ɗin ta ɗauko wata tsohuwar akwati ba jimawa ta zaƙolo wata farar leda tace "Aini na manta da wannan mganin barbaɗa kare mangul wlh yau zanga ƙarshen maita daman ai babu gama sanin halinka ba". Taɓe baki Sheikh yay bayan ya gama jin surutun Granny da Fareeq yay kamar ya fita sai kuma ya fasa, yana ta tsaye domin tsaiwar daɗi take masa abinka da ba'a saba ba, cikin lafiya da kuzari ya ƙara matsawa jikin ƙofar a hankali ya ɗura hannunsa a saman handle ɗin kana ya murza ka ɗan ƙofar ta buɗe, fararen idanunsa ya shiga juyawa ganin babu kowa a parlo yasa ya juya ya koma nasa bedroom tana kwance sai sakin ajjiyar zuciya take ta ƙwaƙome pillow sosai ya shiga ƙare mata kallo sbd wani kyau data ƙara a cikin idanunsa, ganin babu wani time yasa yaja ƙafafuwansa zuwa jikin gadon cak ya ɗauke ta yaji kamar wata baby babu nauyi, walking slowly gudan kada ta tashi taƙi yarda tabar ɗakin. Bai tsaya ko ina ba sai cikin bedroom ɗin ta, wani dadɗan ƙamshi ne ya dakesa wanda ya saukar masa da kasala yana jin yanayinsa na sauyawa da ɗan sauri ya kwantar da ita, ya juya zai fita yaji ta saka masa kuka a zcyarsa yake faɗin _Ya ilahi yau Sheikh ka haɗu da aiki_ sai kuma ɗan zaro ido waje a bai yana cikin tattausan Muryarsa irinta Malamai yace _"It's my responsibility"_ a hankali ya zauna gefen gadon da sauru kuma ya janye idanunsa sbd ganin saman ƙirjinta a bai yane, wata wahalalliyar ajjiyar zuciya ya sauke kana ya fara Musa bakinsa a hankali ya shiga karanta mata addu'a har ya gama ya shafa mata a fuska da jikinta sassanyar Ajjiyar zuciya ta sauke lokacin da ɗumin hannunsa ya sauka a fuskar ta, duvet yaja ya rufe mata jiki kana yabar ɗakin da sauri, kai tsaye kitchen ya nufa sbd cikinsa da yaji ba komai mug ya ɗauka ya tea mai kauri kurba ɗaya yay ya ajjiye sbd ɗacin da yaji, jingina yay da jikin sink zcyarsa fal tunani ya dace ace ya samu sauƙi da kuma raɗaɗin daya keji amma zucyarsa kamar an ɗauki ƙaton dutse an ɗura masa haka yake jinta, hannunsa ya zuba cikin aljihu ya nufi bedroom ɗinsa kulle ƙofa yay kana ya zame kayan jikinsa ya rage daga shi zai troser sam bai son kaya a rayuwarsa, gudun a.c ya ƙara abun mamaki daya rufe idanunsa surar jikinta ke masa gizo damuwa ta fara yiwa Sheikh yawa domin yau ɗaya kawai ƙwaƙwalwarsa na neman zautar dashi. Sharp-Sharp ya ɗaura alwala ya fara lafila yana roƙan Ubangiji ya fiya da kuma neman zaɓi mafi alkairi. Zaune yake da wata farar Jallabiya mai kyau da santsi haɗi da taushi ya ɗura harami a kansa idanunsa cikin farin glass ya ƙara kyau da girma haiba da kwarjininsa sun ƙara bai yana kansu ga wata ilhama data ƙara fidda asalin nutsuwar Sheikh Imam hamdan Balarabe, Murmushi mai sauti ya saki kana ya juya ya kalli Fararan yaran da suke nesa dashi kaɗan, idanunsa ya sauka akan ta farkon kana ganin su kasan cewa twins ne. Littatin hannunsa ya ajjiye gefe kana ya miƙe cikin kamala ya nufi inda suke zaune suna wasa da teedy, ta farko ta kallesa cikin murna ta Washe bakinta tace "Abbi!" Sunkuyawa yay tare dasa hannunsa gaba ɗaya biyun ya ɗauke ta yana faɗin _"Mamana"_ gemunsa taja tace _"Abbi Ana uhubbka"_ sumbatar ta yay a saman goshinta yace _"Your Abba is always loving you Twin na_ " turo baki tayi tace "Abbi Ummi bata son mu" juya idanunsa yay yace _"Who tell you that?"_ fuska ta marai-raice tace "To bata goyamu ai" Murmushi mai ɗan sauti yay yace "Mamana baki girma goyo ba?" Cike da yarinta ta ɗaga masa Kai, bai tsaya jiran komai ba yace "Yau Abbi ya fanshi Ummi ki daina mita kinji Mamana" tana daga bayansa ta rungomesa tace "Jazakallah bilkhair Abbi" yana kallon ɗaya yarinyar yace "Barakallahu fikiii" miƙawa yarinyar yay wacce take ta kallonsa ta miƙe tana shirin zuwa wajansa taji an riƙe ta, kallon matar data riƙeta tayi ba tare da yay mgn tai masa kallon saura kwata tace "Wai sai yaushe zaka fahimta? Bana ce ban ƙaunarka bana son ƙara ganin wannan mummunar fuskar taka ba, wlh wlh duk sanda ka sake bari naga fuskar ka sai na kashe kai na" tsaiwa ya gyara yana ƙara kwantar da yarinyar da take bayansa gudun kada ta faɗo tunda ba goyan ya iya ba, cikin ƙasa da Murya yace "Ƙarya kike _Zahraaah_ babu abinda kikeso duniya sama dani" cike da masifa tace "Sbd kaga Ubana ko? Wlh idan kaci gaba da tsaiwa a nan zai na tafka maka rashin mutunci zaka gane shayi ba ruwa bane, ka ɗauki gantalallun shegun yaranka ka ɓace min da gani" idanunsa ne yay jajir sbd ɓacin rai wai Zahraaah ke zagar masa yara har tana dan gan tasu da kalmar shegu? Kuka yarinyar bayansa ta fara, ɗayar ma ta saka kuka tana miƙawa Mahaifin nata hannu ya ɗauke ta, wajanta ya nufa zai ɗauke ta Da Dukkan ƙarfinta tasa hannu ta hankaɗa sa baya banda yay jarumta ya riƙe kujera ta tuni ya faɗi a wajan, tsoro yasa yarinyar bayansa shiɗewa daman ga Athmar dake damunta tuni da sume a bayansa jikinta ya saki, cikin ɓacin rai ya kalleta yace "Zahraaah baki da hankali kisa zaki? Ƴar da kika haifa zaki kashe?" Cikin tsawa tace "Kai ne babban mahaukaci sakarai kuma shasha" jikin sane ya fara rawa ya ɗaga hannu ya zabga mata mari tace "Kan Uba Imam ni ka mara" kai tsaye yace "Yes! Ko zaki ram...," Kaifin ya gama faɗin abinda yay niyya ta ɗaga hannu ta zabga masa mari..... A gigice Sheikh ya farka daga baccin daya ɗauke sa jikinsa duk ya jiƙe da gumi hannunsa ya miƙa ya shafi fuskarsa wajan data maresa, Innalillahi kawai yake faɗa wanne Irin mafarki ne wannan Meke shirin faruwa tsakaninsa da Zahraaah, wannan yaran guda biyu yaran wanene? Kan sane ya shiga juyawa wani zazzaɓi ya kawo masa ziyara jin kansa yake kamar zai fashe wannan mafarkin ba ƙaramin tayar masa da hankali yay ba, idan akwai abinda zai tayar da hankali bai wuce rabuwa da Fannah, fesar da numfashi yay yana mai sauke ajjiyar zcy bala'i goma da ashirin ga ciwon da zcyarsa da take masa ga mafarkin da yay uwa uba wani fitanan abu daya fara kawo masa zira a karo na biyu yana mai ƙara son jin ɗumin mace a kusa dashi, jin kiran Sallah yasa ya fahimci Subhi tayi har lokacin ya fara jaa, miƙewa yay cikin nutsuwa yana mai ƙarfafa jikinsa sam baya son damuwar zcyarsa tayi ta siri a jikinsa, bathroom ya shiga ya sakarwa kansa shower ruwa ya fara saukar masa sosai yake jin daɗin ruwan yana ratsa shi, yana gamawa yay brush tare da ɗaura alwala, wani ma dai-dai cin towel ya ɗaura, bai tsaya busar da kansa ba ya shiga goge ruwan jikinsa wata Maroon ɗin jallabiya ya ɗauka sai farin hirami ya ɗaura saman kansa, yana gamawa ya buɗe ƙofa ya fita zuwa parlo zaune ya samu Fareeq da mmkin ganin yayan nasa da ƙafarsa tsaye kuma a gabansa ya kusa sumar dashi sai kawai ya saki baki yana kallonsa, Sheikh kallo ɗaya yaywa Fareeq ya ɗauke kansa, ganin kallon kuma yay yawa yasa ya ɗan fara tafiya raguwar ruwan kansa ya sauka wuyansa, Cikin raguwar sautin lafiyayyiyar muryarsa yace _"Uhm stop looking"_ Murmushi fal fuskar Fareeq yace "Yahhya! When? How gsky I'm so much happy" Sheikh bai kalli Fareeq sbd rawar da naman jikinsa yake masa, waje yay bakinsa ɗauke da addu'a yana dafe ƙirjinsa da kansa, a compound sukaci karo da Barrister yay parking da motarsa da alama ba'a gidan ya kwana ba, ƙirjin Barrister ne ya buga da ƙarfi kasa koda mutsi yay yabi Sheikh da kallo wanda yake tafiya kamar wani ZAKI a wannan karan sai yaga gaba ɗaya Sheikh ya riki ɗe masa, da sauri ya janye idanunsa tashin hankali tsantsa ya bai yana saman fuskar Barrister, Sheikh kam sarai yaga Barrister amma ganin time na tafiya yasa kai tsaye ya nufi Mosque, Jama'a sai taya Sheikh murnar samun ƙafarsa suke suna ƙara yi masa addu'ar samun lfy, Bayan yay Azakar yay Mutane karatu, Zama yay yana nazarin rayuwarsa da kuma yadda zai ɓullowa al'amarin. Sai wajan 8 yabar cikin Mosque ɗin a compound ya samu motar Arjun ɗauke kai yay yaci gaba da tafiya get keeper yace "Ƙaramin Alhaji Allah ya ƙara maka lfy, ya kare gabanka da bayanka sharrin mutum da aljan ya kare, SHEIKH Allah ya ƙara ilimi da wata" kan Sheikh a ƙasa yana tafe yana bada faɗi cikin da jarumta, ta gefen ta ido Sheikh ya kalli mai gadin jinjina kai kawai yay harya shige cikin gidan, A babban parlo Ya samu Arjun da Granny sai Fareeq Arjun na ganin Sheikh da wani farin ciki mara misaltuwa idanunsa har ƙwalla ce ta taro yana zuwa ya rungome Sheikh yana faɗin _"Allahamdulillah! Allahamdulillah! Allahamdulillah!_ Allah abin gdy yau buddy kai ne da ƙafafuwanka kake tafiya? Kaine ka samu lafiyarka?" Sai kuma ya sanya kuka idanunsa a lumshe ya ɗan rungome Arjun kana kuma ya zare jikinsa tare da buɗe idanunsa yana son yaga ta inda zata ɓullo yaga yanayin jikinta amma ko mai kama da ita bai gani ba, cikin nutsuwa ya shige part ɗinsa sbd zazzafan zazzaɓi daya kawo masa ziyara a lokacin, yana shigewa Granny ta fashe da kuka tace "Idan dai duniya da gsky ai Imamu ba zai ƙi kulani ba, to! Wa yake da shi sama dani amma ko inuwata bai kalla ba fisabilillahi! To wani laifi nayi masa ne?" Girgiza kai Arjun yay domin shima ya girgiza da ganin sauyin na Sheikh yace "A'a Granny rashin sabo ne shiyasa". Mami ta sauke ajjiyar zuciya tace "Wlh sai yanzu na samu nutsuwa da muka ƙarasu lfy, lokaci yana neman ƙuremin" Kubra tace "Yanzu tataya zaki fara samun Sheikh harki biya buƙatar ki?" Wani kallon da sauran ki Mami taiwa Kubra tace "Hala kin manta Saudat ko? Zan fara aikina akan Yarinyar idan na gama sannan zan nufi wajan Sheikh, maganin da nai amfani dashi kwanaki yanzu ma shi zanyi amfani dashi,nasan dole ya biye min Musamman idan yaga asalin jikina And abinda ba ƙafa ne dashi babu da zatar yay arba da jikina komai ya ƙare" A bakin gate Mami ta sauka sukai sallama da Kubra kana ta shige cikin gidan ranta fal farin ciki. *A 2week lrt* Abubuwa sun faru da yawa hankalin Barrister ya tashi hakan yasa ya kasa neman Fannah domin baya cikin hayyacinsa, Mami kam ko Fannah bata gani sbd yanzu bata fiya fitowa ba, Sheikh kullum da zazzaɓi yake kwana yake tashi ya rame sosai ya ƙara fari, Arjun yin duniya yay da Sheikh ya faɗa masa damuwarsa yaƙi, dan haka ya hqr ya zuba masa ido, tsahun sati biyun Sheikh da Fannah basu ƙara haɗuwa da juna ba kowa yana can yana fama da ciwon da zcyarsa take masa. Yau sun kai Azumi na goma a cikin watan Ramadan a kuma cikin satin nan Sheikh zai tafi Makkah kamar yadda ya saba, yana gama fidda zakkah. Tunda aka sha ruwa ya dawo daga sallar Ashan har wajan 10 na dare bai ƙara fitowa ba, yau ko coffee da yake sha bai sha ba, Granny ce ta buɗe ƙofar tana faɗin "Wlh da dai-dai ka mutu gwamma ni na mutu wlh yau ko ka faɗan damuwarka kona bar maka gidan, daman....," Maganarta ce ta tsaya sbd ganin Sheikh yashe a ƙasa jini na fita da hanci da bakinsa.... SIRRIN MU na kuɗi ne dan Allah ki biya kan ki karanta dan Allah it's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 Nimcyluv✍🏽 22/10/2021, 10:34 - 🤔🤔: 61-62 Jini ne wanda yake nuni da zcyar Mutum gaf take da bugawa sbd yadda numfashin Sheikh ya tsaya cak, hannunsa dafe da ƙirjinsa da dauri Granny ta ƙarasu tana fasa kuka tare da faɗin "Na shiga uku mene ya samu ɗan maran Allah ni Faɗimatu, wacce kalar gantalewa ce wlh wannan sa hannu ne niyya akai a jefemin shi Allah bai nufa ba" ta ƙare maganar cikin kuka tare da durƙosawa wajansa, rasa abinyi tayi sai kawai ta juya ta nufi waje da gudu a Parlo ta samu Fareeq ta bashi wayarsa tace "Maza kira min Shansu" karɓa yay ringing ɗin farko Uncle Sham yay answering tun kafin yay mgn Granny tace "To gashi nan dai Za'a kashe mana Imamu sai ambaliyyar jini da yake ta baki da hanci, maza kazo domin bashi da kowa sai mu ɗin wlh jefansa akai banda haka mutum lafiyayye kamar Imamu mene nasa nayin aman jini fisabilillahi?" Sosai tashin hankali ya bai yana a saman fuskar Uncle Sham yana ɗaukan key car ɗinsa tare da kallon Anut Amina yace _"On my way Granny"_ Yana faɗin hakan ya kalli matar tasa yace "Koda ban dawo ba sai zuwa safe kada ki damu ki tayasa da addu'a" Jinjina kai tayi tare da ɗaukan Huda zata rakasa waje yace _"Not stay there"_ da addu'a ta rakasa tare da yiwa Sheikh addu'a samun lafiya. Uncle Sham da Arjun tare da matarsa wacce cikinta ya fara fitowa kusan tare suka iso gidan, suna shiga Granny ta miƙe tana share zufar data yanko mata fuskarta tai face² da hawaye. Sheikh duk abinda Granny take yana jinta tsananin azabar daya keji ni yasa ya kasa koda mutsi, ya fison ya rufe idanunsa samu samun nutsuwa da yake a hakan rabon da yaga fuskarta ya manta rufe idanunsa shike bashi damar ganinta ta cikin ƙwayar idanunsa, zcyarsa ta gama azabtuwa da rashinta wani gefe na zcyarsa sosai yaji daɗin hakan wani ɓangaren kuma babu abinda yake so da kuma ƙwaɗayin gani face _Zahraaah_ da ƙyar ya samu damar jan wani wahalallan numfashi wanda ya ƙara haddasa fitar jikin hancinsa, slowly ya fara ɗaga zara-zaran lashes ɗin idanunsa kafin jajayen ƙwayar idanunsa ta bai yana,Makeken zanan Airah ya tsorawa idanunsa so yake ya furta _So this is your love And care ɗin? Why are you doing this to me Fairy na? Kece silar komai you're the reason behind_ ki koyan yadda zan soki na kasance dake naji ɗumin jikinki, _What i have done to you?_ Da kika zaɓi barin Sheikh ɗinki ki tafi wata duniya tada ban? Why!! Why!!? _My Aljana I missed you a lot missed_ ban huta da rashin ki ba sai gashi wata ta ƙara shigowa rayuwar Sheikh ɗinki, me yasa kuke min haka ne? _I'm scared Dan Allah My Fairy come back to me!_ ko zan samu sauƙi da sukunin ƙuntarar da zyta take ciki, Yeah! Kin gayan ni namiji ne mai ishasshiyar lafiya amma lafiyata wake kaɗai take aiki meyasa kika bari tayi aiki a kanta? _What should I do Airah you leave me_ bani da kowa wacce nake tunanin komai daga gare ta is not my Halal ta haramta a gareni zcyta zafi, Zan bar ƙasar gaba ɗaya ko zan samu sauƙi _i love her to the rest of my life without her Means my life is ended I love Zahraaah!!!"_ Uncle Sham dake tsaye a kansa ya harɗe hannayensa a saman ƙirjinsa yace _"Who is that Zahraaah?"_ haɗe fuska Sheikh tare fisgar numfashinsa yay baya ya ɗan kwanta Arjun ne yay saurin cewa "Uncle wata ce i think kamar saɓani suka samu?" Kallon idanun Arjun Uncle Sham yay kafin yace "Saɓani? So he still loves her?" Kai Arjun ya ɗaga Uncle Sham yace "Sure!" "Yeah?" Barrister dake tsaye idanunsa akan Sheikh yace "Akan Soyayya zaka kashe kanka kaimin asara Son? Kasan tashin hankalin daka sani? Dame zanji ga matata Fatima ba lfy ga ɗan da nafi so fiye da komai ba lfy" sai lokacin Sheikh ya ɗaga jajayen idanunsa ya kalli mahaifin nasa a taushashe Sheikh cikin zallar damuwar daya kasa danneta a ranta yace _"Zahraaah!!? MY ZAHRAAAH!"_ sai yanzu ya fahimci dalilin cewan nasa wato rayuwarsa ba lfy shine yasa shima ba lfy? Ganin Sheikh na neman kauce layi yace "Buddy Your Zahraaah is fine kuma zata dawo gareka i promise to you" yan faɗin haka ya fice daga bedroom wayar Uncle Sham ta ɗauki vibration a hankali ya ɗauka yace "Ok Dr ina zuwa" yana faɗin haka ya fice daga cikin ɗakin, Barrister kasa ɗauke idanunsa yay daga kan Sheikh mmkin samun lafiyarsa wajan sati biyu kenan yaƙi sakinsa, meke shirin faruwa ne? Hakan na nufin aikin shekara da shekaru ya ruguje?? Ina bazai yiwu ba, ya faɗa afili duk abinda yake Sheikh na jinsa ko kallansa bai ba yana jira yaga ta inda Arjun zai kawo masa Zahraaah. Arjun na fita kai tsaye ya tsaya a Parlo idanunsa akan Aliyah yace "muje ki gaida Anut Fatima" miƙewa tayi tana sakar masa lallausan murmushi taɓe baki Mami tayi ta ɗauki niyyar daga yau zuwa gobe zata gabatar da aikinta, Fareeq da Bahaiyya kam suna zaune amma kallo guda za kaiwa Fareeq kasan cewa yana cikin damuwa da ciwon ɗan uwan nasa, Granny banda fatar majina babu abinda take. Aliyah na gaba yana binta a baya har suka isa ƙyakƙyawan part ɗin Fannah, cikin nutsuwa Aliyah ta tura ƙofar taji shiru hakan yasa ta nufi ƙofar da take tunanin itace ta bedroom tana shiga ta sameta kwance akan bed daga ita sai riga wata half body mara nauyi, fatar jikinta ta ƙara wani fari har yellow take fiddawa, cinyoyinta sunyi manya sai Shinny suke jikinta ya murje, amma kallo ɗaya za kaiwa innocent face ɗinta kasan tana cikin halin ciwo wanda a zahiri zaka ɗauka zafin ciwon ya sata rama sbd ramewar da tayi ga idanunta da suka faɗa, amma a ranta ba haka abin yake ba rashin ganin Malaminta shine silar damuwarta, saurin rufe idanunta tayi a tunaninta Barrister Muryar mace kuma da taji yasa ta fahimci Wacece, juyawa tayi tana ƙaƙalo murmushi wanda iya kacinsa laɓɓanta, murmushi itama Aliyah tayi tare da ƙarasawa inda fannah take kwance, hannunta ta riƙe tace "Ashe ba kiji daɗi ba? Ya jikin Allah yasa kaffara ne" ɗaga mata kai kawai Fannah tayi ta kasa amsawa, miƙewa ta nufi fridge ta ɗauko mata ruwa mai sanyi girgiza kai tayi tace "Akwai juice na lemon shi zaki ban" mayarwa tayi ta ɗauko mata yay sanyi sosai, sai data shanye tass kana ta ajjiye robar sannu a hankali ta fara sauke tagwayen ajjiyar zuciya, gyaran murya Arjun wanda yasa Aliyah ɗau kan hijab ta sanyawa Fannh kana ya shigo yana daga tsaye yace "Fatima baki san meke damun zcyarki ba? Wannan lokacin bana keɓewa bane dake da Buddy junanku kuke buƙata, babu wanda Sheikh yake son gani sai ke,gaba ɗaya hqr za kuyi ku amshi ƙaddarar data zo maku, na sani kin sani Sheikh ya sani wannan Soyayyar is forbidden love, Haramtacciyar soyayya (Babyluv) ce, mene yasa gaba ɗaya kuke son sanya kanku a DAMUWA (Autar manya) wlh tallahi duk damuwar da zaku shiga bai kai na ABU MALEEK (Nimcyluv) ba shi da yabar danginsa da sarautarsa, da al'ummar da suke so ya mullesu ya bar matayensa har guda biyu yay badda kama ya zama mahaukaci ƙarfi da yaji sbd kawai yaje wata ƙasar nemawa OBA OF LEGOS Maganin cutarsa, ashe silar wata yarinya ya kaisa ƙasar.." shiru yay yace "bawai ina ƙaunar abinda kuke da Sheikh bane a'a ina son ke taimaki Sheikh ki bada kulawa wlh Sheikh ya rasaki to tabbas za'a iya rasashi gaba ɗaya a duniyar" wasu zafaffan hawaye ne ya fara sintiri a fuskarta Aliyah ta riƙe hannunta tace "Look! Sis BIN ABINDA ZUCIYA KESO (m.shakur) shi ne dai-dai ki tashi tsaye ki san mene kike bawa Sheikh farin ciki bawai yana nufin bashi mutuncin ki ba wanda muma Bama fatan haka" kuka Fannah ta sanya ta riƙe Aliyah tace "What should I do? Zcyta zafi ta kemin?" Rungometa sosai Aliyah tayi Arjun na juya yace "Ku fito ta dubasa yanzu" yana faɗin hakan ya fice daga cikin bedroom ɗin, babban hijab Aliyah ta ɗauko mata bayan ta saka ta kama hannunta sukai waje. Granny na ganin su ta miƙe tsaye tace "Ya! Ya! Haka Ilina? Yarinya na fama da laulayi zaki fito da ita?" Ware ido Aliyah tayi tace "Granny ciki gareta ne?" Washe bakinta tayi tace "Ai ko yarana ina naki cikin sai dana faɗa kukaje asibiti kuma akace ciki ne? To billahil lazi yanzu ma Faɗimatu ciki gareta kalli idanunta" Fannah ji tayi gabanta ya faɗi da sauri ta sunkuyar dakai sbd yasan ba wani ciki daga abu ɗaya sai kuma ciki ya shiga? Jinjina kai kawai Aliyah tayi tace "Allah ya inganta" daga haka suka nufi part ɗin Sheikh. Mami jine an ambaci ciki sai hankalinta ya tashi tama rasa mene zatai. Lumshe idanunsa Sheikh yay yana kallon Dr shima Dr bai ce komai sbd kallon da Sheikh ke aika masa wanda yake nuni da warning, bayan ya gama Uncle Sham yace "Dr Meke damunsa?" Murmushi Dr yay yace "kawai zafin zazzaɓin masassara ne, in sha Allah zaiji sauƙi" "Uhm what about the blood dke fita hanci da baki?" Shiru Dr yay yace "Shima zai daina" daga haka ya sanya Sheikh drip duk da yace bai so amma dole Uncle Sham yace a sanya masa, daga Uncle da Barrister suka fita daga ɗakin, Barrister kallon Fannah yay yace "Kinga na manta Dr ya duba ki?" Kallonta Dr yay yace "Wannan ai ci..?" Da sauri Aliyah tace "Cikin zazzaɓi take amma taji sauƙi ni nace tazo ta rakani na duba Sheikh ko taji daɗin jikinta" Wani ƙawataccen Murmushi Barrister yay Uncle Sham kallo ɗaya yaywa Fannah yay gaba abinsa. Yana kwance daga shi sai 3gauther idanunsa a lumshe ga ƙwantaccen gashin ƙirjinsa da yake ɗigar ruwa sbd ruwan daya watsa, A parlo Arjun da Aliyah suka tsaya bayan fannah ta shige cikin bedroom ɗin Aliyah tace "My man who kamar ciki gareta" ware idanunsa yay yace "Mace da Mijinta dan ta samu ciki abin damuwa ne?" Tun kafin ta iso yaji bugun zcyarsa ya sauya hakan kuma ya tabbatar masa cewa ita ce, bai Yadda ya buɗe ido ba, a hankali jiki ba ƙwari ta zauna kefen gadon Idanunta na zubar da hawaye cikin ƙasa da murya tace "How are feeling now?" Manyan gajiyayyun idanunsa ya buɗe kallo guda yay mata ya ɗauke idanunsa ba tare da yay mata mgn ba, jin yay shiru yasa ta fara shassheƙar kuka da sauri ya buɗe idanunsa da ya gama yin jaaa jikin zafin nama ya zare drip ɗin hannunsa jini ya fara zuba, ganin yana shirin tashi tai saurin kifa kanta a cinyoyinsa tare da fashewa da kuka, kansa ya dafe wanda yake jin kamar zai rabe gida biyu, cikin zafin nama kuma ya jawota jikinsa tare da matse ta sosai faffaɗan ƙirjinsa suka shiga sauke ajjiyar zuciya laɓɓanta ya mannu a tsakiyar ƙirjinsa a hankali kuma ya fara jan numfashi yana fesar da iska cikin ƙasa da Murya yace "Mene?" Girgiza kanta tayi hakan yasa ta ƙara goga masa laɓɓanta har a tsaitin nipples ɗinsa wanda suke da tsini, gently ya ɗago kanta tare da tallafo haɓarta cikin hannayensa idanunsa ya shiga juyawa a nata kafin ya zare hannunsa ɗaya ya shiga ɗauke hawayen yace "This.." ya faɗa yana nuna mata hawayen daya lakato yace "Wannan shi ne Sheikh baya son gani? Kukanki azabace a gareni Zah..raaah.." ya faɗi sunan bata a rarrabe cikin sauke ajjiyar zuciya tace "Dan Allah karka rabu dani..," kasa mgnar tayi sbd idanunsa da sukai mata kaifi a ido ta zame fuskarta da sauri tana ɓoyewa a ƙirjinsa, shiru yay yana jine yadda zuciyoyinsu ke bugawa a tare cikin rayuwar Murya Sheikh yace "Laaaa!" _إني أفخر بكونك معي،_ _وإني أدعوا أن تكوني أم أولادتي وصاحبة حياتي في الجنة._ (Ina Alfahari dake A rayuwata! Kuma ina fatan ki zamanto uwar ƴar ƴar na! kuma abokiyar rayuwata har a Aljannah!) Da sauri ta rungomesa tana sakin Murmushi mai sauti tace "Ina son ka Malamina" kasa mata magana yay sbd abinda ya tukare masa zcya,a hankali ya zareta daga jikinsa, turo baki tayi gaba fiddo idanunsa waje yay yana juya tace "Na daɗe ban ganka ba nayi kewarka" ta ƙare maganar tana zagaye lips ɗinsa da hannunta, idanunsa a kanta yace "Same Nima haka" ya ƙare maganar yana mutsa bakinsa a hankali sautin "Astagafirullaha wa'atubu ilaik, Astagafirullaha! Astagafirullaha!! Subahanallahi! Walhamdilillah wa lailaha'illalahu Allaahu akbar. Astagafirullaha". Yake fita daga Ƙasan maƙoshinsa, tsayawa yay da tasbihin yana kallon Idanunta yace "jeki kwanta kada ki makara sahur" kwaɓe fuska tayi tace "Ni ina son kwanciya a jininka bana iya bacci kwana biyu" ganin da gaske take yasa yace "Ok come closer" ta sauri ta shiga cikin jikinsa tana sauke ajjiyar zuciya har ranta take jin daɗin turarensa na Ohud Mood, cikin nutsuwa take shafa gashin ƙirjinsa, Sheikh kam ji yake kamar tana watsa masa wuta matseta yay sosai a ƙirjinsa bakinsa a saitin kunanta yaci gaba da faɗin "Astagafirullaha wa'atubu ilaik, Astagafirullaha! Astagafirullaha!! Subahanallahi! Walhamdilillah wa lailaha'illalahu Allaahu akbar. Astagafirullaha". luff tayi jikinsa tana ƙara maƙalesa sbd daɗin zazzaƙar muryarsa dake dukan kunanta tana ratsa dukkan gaɓoɓin jikinta, a hankali Aka turo ƙofar kusan mutuwar tsaye Arjun yay sbd ganin Fannah kwance male male a jikin Sheikh tana shafa gashin ƙirjinsa... An jima za kuji ni🤕 SIRRIN MU 08119237616 22/10/2021, 10:34 - 🤔🤔: 🚶🏾‍♀️ Okey bye &&&&&&&&&& 63-64 Da raguwar ƙarfin ta tayi saurin miƙewa daga jikin Sheikh tana sunkuyar da kanta ƙasa sai raba ido take, Allah ya gani taji kunya sosai, Sheikh juyawa yay tare da basu baya ita da Arjun ɗin, ji tayi sam ba zata iya tsaiwa a wajan ba sbd Arjun dake wajan, a sanyaye kanta a ƙasa tai waje tana mai ɓoye sassanyar Ajjiyar zuciya, da kallo Arjun ya bita tana fita ya kalli Sheikh yace "Meke nan haka Sheikh? What is this? Ina ilimin naka pls?" Banza Sheikh yay masa shi kansa yaji kunyar ganin Arjun kawai daurewa yay sbd jarumtar sa, cikin damuwa Arjun yace "Gsky banji daɗi ba wannan kuma ba dai-dai bane, wani ya dace yay hakan kai masa faɗa hawai kai kayi da kanka ba, a karo na farko ka ɓata min rai kuma indai baka sauya ba wlh zamu samu matsala dakai" jin surutun yana hawa kansa yasa a hankali cikin izza nutsuwa kamala ya miƙe tsaye walking slowly ya nufi ƙofar bathroom, sai da yaje bakin bathroom ya tsaya idanunsa a rufe a taushashe yay Calmly yace "What are you saying? Me kake nufi? Arjun i know what Im doing, Soyayya guba ce tana gaf da kurɓata zcyar Sheikh, ina yawan yi maka kallon shasha akan abinda kakewa soyayyya da bautar da kake mata..," shiru yay tare fisgar numfashinsa yana ɗan shafa ƙirjinsa yace "Ashe nine shasha, domin yanzu ne nasan cewa soyayya halitta ce a zcyar ko wanne bawa, na so Airah sai nai tunanin ko sbd ba jinsu mu ɗaya ba yasa nake sonta? A yau nasan cewa ba mutum ke faɗawa soyayya ba, soyayya ce ke faɗa kansa, Zan iya bada rai akan Zahraaah, i love her, soyayya ta kan bada rai amma muradi..." Sai kuma yay cije bakinsa ba tare daya iya cewa komai ya shiga fesar da numfashi, Arjun ne ya ƙara su gabansa yace "I understand your feeling, amma Sheikh try to control your temper, kayi ƙoƙarin ɓoye abinda ke ranka da Zcyarka, everything will be fine in sha Allah" rungome Arjun yay yace "In sha Allah, just pray for me" shima Arjun hug back ya bashi yace "I'll" Sheikh kam ya rungome Arjun ne sbd kada yaga hawayen dake shirin zuba daga cikin idanunsa, da sauri ya zame jikinsa Arjun yace "Gud night" ba tare daya jiyo ba yana shiga cikin bathroom ɗin yana faɗin "Tasbahii alaa khaaiir" Yana faɗin haka ya shige bathroom ɗin tare da sakarwa kansa ruwa mai sanyi, Alwala ya ɗaura kana fito daga cikin bathroom ɗin sanye da bathrobe jikinsa na ɗigar ruwa, wasu fararan night wears ya sanya Panjams santsi, wandon iya laps ɗinsa, rigar iya west ɗinsa. Parfume ya fesa zafin da cikinsa ke masa yasa ya sanya bedroom sleeper cikin nutsuwa Kamar mai tausayawa ƙasa haka yake tafiya, ba kowa a parlo tuni Uncle Sham ya huce Arjun ma haka, kai tsaye kitchen ya nufa ba tare daya kunna hasken kitchen ɗin ba, a wajan sink ya tsaya ya shiga juyawa Idanunsa yaci Sa'a akwai ruwan zafi a jug ya ɗauki mug ya tsiyaya kana ya sanya laptop guda biyu, ya ɗauki lemon guda huɗu ya matsa ciki, zama yay saman Sink a cikin duhun ya fara shan black tea ɗin a hankali ya nayi yana rufe idanunsa, not too long ya fara hangota tana tafiya kamar wacce ƙwai ya fashewa, ta sanya white ɗin kaya kusan Company ɗaya da nasa ta ɗura baby hijab a kanta, idanunsa ya ɗauke tare da rufe su yaci gaba da shan tea ɗin, A hankali Fannah ta fara duba inda za taga lemon amma babu marai-raice fuska tayi sbd har yawon ta ya gama tsinewa sbd ƙamshin lemon da taji, ga ƙamshin turarensa daya adda beta tana da tabbacin jikinsa data shiga ne yasa taji haka, jingina tayi jikin Sink ɗin tana maida numfashi, a hankali ya ajjiye raguwar tea ɗin hannunsa tare da sakkowa daga saman sink ɗin, mutsin da taji yasa ta fara ƙoƙarin yin baya cikin rashin za'a ta daki wani abu tai baya zata faɗin taji an tare ta faɗa tattausan jiki, jikinta na rawa ta fara ƙoƙarin kwace jikinta, rashin waye kuma yasa duk ta firgita dan a tunaninta ko Barrister ya ƙara zuwa sbd yazo ɗazo ta gudu bathroom har sai daya tafi ta fito, yana jin yadda take sauke ajjiyar zuciya cikin nutsuwa yazo gyara mata tsaiwa hannunsa ya sauka saman mararta, wani iri taji da sauri tace "Wanene, I'm scared ka barni, wayyoooo Malamina ga Aljani" wani tattausan murmushi Sheikh ya saki tare da zame hannunsa haka nan yaji ransa fess daya taɓa mararta, mug ɗin ya ɗauka kana ya ɗura mata a baki jin ƙamshin lemon yasa bata san lokacin data buɗe baki ta fara sha ba, da sauri har riƙe hanunsa take sbd daɗin tea da taji sai data shanye kana ya zame hannunsa tare da ajjiye mug ɗin, tattausan hannunsa wanda yake fidda gumi yasa ya goge mata baki, turo baki tayi tace "To waye kai ne" sakinta yay kana a hankali yay waje da sauri tace "Zan ƙara tea ɗin" gemunsa taja cikin harshen larabci yace "Idan za kici Sheikh Bisimillah" yana faɗin haka yay waje cikin kamala, sandarewa Fannah tayi a wajan wajan domin harga Allah bata san cewa shi ne ba, sai yanzu ta fahimci ƙamshin turarensa da taji lumshe idanunta tayi tana jin Feeling ɗin na sauka ba kamar da ba. Washe gari aka tashi a zumi na 13 Arjun na zaune a office ɗinsa shida p.a suna duba wasu sabbin aiki da aka basu, miƙewa Arjun yay tare da fita yabar office ɗin kai tsaye office ɗin Sheikh ya nufa, tura ƙofar yay a hankali kana ya mayar ya rufe, Sheikh na zaune da wani lallausan voyal milk colour mai manyan zane, ɗin kin riga da wando sai babbar riga, ya ɗura hirami a kansa saman hiramin ya ɗura zanna bukar jaa, a hankali yake mutsa bakinsa yana faɗin _"Astagafirullah wa'atubu ilaik, Astagafirullah! Astagafirullah! Subuhanallah! Walahamdulillah wa La'ilaha illallahu Allahu Akbar, Astagafirullah!"_ Mutsawar bakinsa shi zai nuna maka cewa Tasbahii yake, fararan yatsun hannunsa a saman keyboard ɗin system yana operating system ɗinsa, Zama Arjun yay yace "Mrng Sheikh ya jikin naka?" Shiru yay kamar bazai amsa ba can kuma yace _"Sabahul khair"_ Ya faɗa ba tare daya ɗago kansa ba idanunsa cikin Fararan glass yaci gaba da abinda yake, Arjun yace "Wannan karan Bazan bika zuwa Oumara ba" shiru Sheikh yay ganin bashi da niyyar yin mgn yace "Mun samu sabon contract daga Governor of lebanon" idanun Sheikh saman system yace "Ka maida masa" Arjun yace "Why, mutumin nada kirki sosai kuma abin alfaharin a nan ƙasar yake buƙatar ai ginin makarantar islamiyya" Ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke yace "Wa kace?" Kai tsaye Arjun yace "Governor of lebanon Deedat" cak Sheikh ya tsaya da abinda yake yana son tuna inda yasan sunan amma ya manta, a gajarce yace "Accepted" rufe system ɗin yay bakinsa yana ta mutsawa a hankali yace "Ka faɗawa ko wanne gidan t.v, Redio a duk inda suke idan suna buƙatar ɗau kan tasfir ɗin da za'ai a ranar juma'a wanda yay dai-dai 15 ga watan Ramadan" da mmki Arjun yace "Why? Abinda baka son kowa yasan kai ne Sheikh Imam hamdan Balarabe" miƙewa Sheikh yay a hankali yana fita waje yace "Yanzu Duniya ya kamata tasan wanene Imam hamdan Balarabe" yana faɗin hakan yay waje gaba ɗaya mutanan reception suka miƙe suna gaidashi hannu kawai ya iya ɗaga masu, Wata lafiyayyiyar Farar mota mai tintak ya shiga Arjun yace "Bari nai kaika nima gida zani" sai yanzu Sheikh ya ɗaga idanunsa ya kalli Arjun yace "No thanks" yana faɗin hakan yaja ƙofar ya rufe bakinsa ɗauke ta addu'a yaywa motar key tare barin Company ɗin baki ɗaya kai tsaye wata court ya nufa. *Federal Court of Appeal* shine court ɗin da Sheikh yay parking a harabar cikinta kansa ya ɗura saman string motar Shiru shi kansa bai san mene yake tunani ba ya dai biye umarnin zcyarsa akan yazo court a cire haƙƙin Ubangiji a jikinsa ko ya samu nutsuwa, Ajjiyar zuciya ya sauke ya duba agogon hannunsa babu time juya fararan idanunsa yay kana ya fara ƙoƙarin buɗe motar, after ya fita daga motar a nutse ya fara taka ƙafafuwan sa zuwa cikin court. Ya Falta ce "Finally za muga Malamin Fannah" Yana ta ajjiye firar dangalin da take tana sakin murmushi tace "Dani dake ba'a san wanda tafi wani farin ciki ba, amma wlh Sheikh ya haɗu" Ya Falta tace "To ta ina kika san ya haɗu kuma tunda ba taɓa ganinsa kikai ba?" Yana ta kalli Mama kolo tace "Ai cikar kamalar Muryarsa ita kaɗai ta isa ka fahimci haɗuwar Sheikh Imam" jinjina kai Ya Falta tayi tace "Kuma fa haka ne, amma ina jin kam Balarabe ne wlh" Sai lokacin Baba Baa'na yace "Au sai Balarabe ne yake zama Malami ko ya iya Larabci?" Da sauri Yana tace "Ai Baba wlh Sheikh ɗin ne ba duk mutum ba" miƙewa tsaye yay yace "Kawai dai kunci Sa'a Mijin Mamana ya baku t.v da sai naga inda za ku kallesa" Wayar Mama Kolo ce ta fara ringing Ya Falta ta ɗauka tace "Laa Ya kura ke kira" Mama kolo ta amsa bayan sun gaisa da Yakura Mama kolo tace "Ya baƙo a baki?" Daga can ɓangaren Yakura tace "Gashi ya zama ɗan gari yau muna 13, Daman Indo ta sanar min bayan babbar Sallah za tazo" da Murna Mama kolo tace "Haba dai yau Indo ta tuna mu Allah ya kaimu" daga nan sallama sukai Mama kolo taci gaba da aikin abincin buɗe baki. Kan Sheikh a ƙasa ya gama zayyanawa Alƙali abinda yake tafe dashi, jinjina kai Alƙalin yay tausayin Sheikh ya kama sa yama rasa mene zai ce, Ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke a sanyaye kamar mara lfy yace "Ni ba kowa bane face bawa na Ubangiji, Bazan taɓa samun nutsuwa ba idan ba'a fidda haƙƙin Ubangiji a jikina ba, kada kai duba da wanene ko matsayina sbd matsayin da nake dashi bai hana na fatka babban kuskure ba" shiru yay yana sauke numfashi sbd kwana biyun nan mgn wahala take masa, Alƙalin ya jinjina kai yace "Haka ne, kuma ina da tabbacin da hankalinka da komai ba zaka aikata hakan ba, something is feshin" Kalansa kawai Sheikh yay kana ya janye idanunsa daga kan Alƙalin, jin Sheikh yay Shiru yasa Alƙalin cewa "Kaje bayan ka dawo daga Oumara sai ka dawo before nan na tattauna da manyan Malamai" cak Sheikh ya miƙe yana covering jikinsa da babbar rigar sa sai da yaje bakin ƙofa yace "Ma'assalam" . A can cikin jeji Tijama ce da Tuɓe suna zaune suna tattaunawa akan babban aikin dake gaban su, Tuɓe yace "Yake Kakata ki sani a yanzu bana da hali ko ikon shiga jikin Bil'adam kamar Sheikh Imam hamdan Balarabe, musamman a wannan lokaci na ibada" Kallonsa Tijama tayi tace "Mai yasa kake son yin hani ga abinda yake halartacce?" Kai tsaye Tuɓe yace "Ya kakata, kinsa na shiga jikin Sheikh na tilasta masa yin abinda bai niyya ba, yanzu zucyarsa cike take da ƙunci da kuma damuwa ina zamu kai haƙƙin Wannan bawan Allah?" Sanda Tijama ta buga tace "Sheikh yana ƙudirin zuwa Court domin ai masa hukumcin abinda ya aikata kada ka sake hakan ta faru? Bashi da laifi ko kaɗan idan akwai mai laifi bai huce mu ba, yanzu abu ɗaya gareni kula da gudan jininsa da dake jikin yarinyar, Nima a yanzu bazan iya shiga jikinta ba sai ranar da akai sallar idi, daga yanzu zuwa ko yaushe wani abun na iya faruwa mudai bisu da addu'a" cike da tausayin bayin Allan Tuɓe yace "In sha Allah! Allah na tare dasu Sheikh na iya kare kansa ita yarinyar itace abinji" Sheikh na zaune a Parlonsa domin yanzu ya daina zaman babban Parlo, idanunsa manne a sunayen Allan da suke jikin bangon parlon bakinsa na mutsawa yana faɗin _"YA RAHAMUU! YA RAHIMU! YA AZIZU! YA JABBARU!"_ sune abinda yake ta faɗa cikin ransa, Fareeq ne yace "Yah Sheikh ina son binka Oumara" shiru Sheikh yay masa durƙosawa Fareeq yay dai-dai ƙafafuwansa yace "Dan Allah Yah Sheikh, ina son binka Nima ina da buƙatu wajan Ubangiji" miƙewa Sheikh yay tare da yiwa Fareeq kallo guda ya ɗauke kansa sai da yaje bakin bedroom ɗinsa yace "Mafimushkilah" yana faɗin hakan ya shige bedroom daman alrdy harda Fareeq ɗin ya shirya tafiya da Granny amma yanzu ya janye na Granny sbd wani dalili, Fareeq yace "Nagode sosai Yah Sheikh Allah ya baka abinda kake so duniya da kuma lahira" sarai Sheikh yaji addu'ar Fareeq yanzu a nan duniya buƙatarsa biyu ce Allah ya haɗasa da Amininsa sai kuma farin cikinsa _Zahraaah_ freshen up yay ya sanya Islamic Men Thobes (Jallabiya) Ash colour, jikinsa na fidda ƙamshi mai daɗi ya zauna ba saman kujera dake jikin bed ɗin sa ya shiga duba Azkar. Fitowa tayi daga cikin bathroom tana goge jikinta da towel kallon kanta tayi a mirror tana mmkin yadda skin ɗinta ta ƙara fari ga girman da ƙirjinta ya ƙara, a kasalance ta shafa body lotion kana ta nufi wardrb ta ɗauki wata farar Jallabiya ta mata ta sanya sai Milk ɗin Laffaya mai White stones Laffaya tabi fatar jikinta ta kwanta lubb ta ƙara kyau ƙuruciyarta ga fito sosai, jin ana kiran sallah yasa ta nufi waje karo suka kusanyi da Barrister tai saurin jaa baya kanta a ƙasa bata kallesa ba tace "Ina yini?" Murmushi yay mata ya tafi zai rungome ta tayi saurin yin gaba lallausan murmushi yayi shi kaɗai yasan me yake rayawa a zcyarsa, A parlo ta samu Granny da kuma Mami zama tayi tace "Ina yini Granny?" Washe baki Granny tayi tace "Kinsha ruwa lfy" Murmushi kawai Fannah tayi kafin ta kalli Mami tace "Anut ina yini?" Kallon Shegiya munafuka Mami tai Mata ba tare kuma daya amsata ba ta saki siririn tsaki, Granny tace "To mudai ha ibada muke ba? Ai sai dai Mutum kuma yaci kansa fisabilillahi, kana dai aikin lada kana zobe ladan ka" miƙewa Fannah tayi Granny tace "Ƴar tunda kin miƙe ɗauki tray ɗin can ki kaiwa Imamu nasan bazai ci abinci yanzu ba" gaban Fannah ne ya faɗi ta kasa ɗaukan try ɗin Murmushi Mami tayi tace "Jeki kai masa mana, Nima na haɗa wani dambun mama nasan zai maki daɗi" Granny tace "Allah gamu gareka" Fannah bata sake mgn bata da wani option dole ta ɗauke try ɗin ta nufi part ɗinsa, fitowar sa kenan daga ɗaura alwala yaji sauyin bugawar zcyarsa ɗauke kansa kana ita kuma ta turo ƙofar a hankali ta shigo akan ƙaramin table ta ajjiye masa kamar zata juya sai yaji ta ba zata iya ba kewarsa ta dameta, koda wasa Sheikh bai kuskuren Kallonta ba yaci gaba da fesa parfume ɗinsa cikin nutsuwa ta ƙarasu inda yake tsaye tana zuwa tasa hannu ta amshi turaren ta fara fesa masa idanunsa ya Lumshe a hankali tace "Barka da dare,fatan Malamina ya sha ruwa lfy?" Ware idanunsa yay yana kallon ƙwantaccen gashin gaban goshinta yace _"Lailatan sa Isa (barka da dare)"_ shagwaɓe fuska tayi tana shiga jikinsa tace "Me nai maka? Me yasa kake ɓoye min?" Innalillahi ji yay kamar ta aza masa wutar dake tashi a jikinsa , hannu yasa ya zareta a jikinsa yana ware mata manyan idanunsa kamar mara lfy yace "Uhm Azumi dai ake" idanunta ya cika da hawaye da sauri ya girgiza mata kansa alamar kada ta fara "Why? Meyasa? Bayan ka koyan kasancewa dakai shine yanzu zaka hanani raɓarka ko sbd ka samu abinda kakeso?" Da sauri ya kalleta tace "Ehmn, kada kasa na yarda cewa abinda kake ƙwaɗayi daga gareni kenan shi yasa yanzu ka fara gudu n....," Da sauri yasa hannu ya jawota jikinsa ya rungome ta sosai bakinsa na rawa yace "Ki yafe min dan Allah, wlh Allah Ubangiji shine shidar Imam ban san yaya akai hakan ya faru ba, _believe me Zahraaah_ har gaban abada bazan taɓa gudun ki Anna UHIBBIKI ZAHRAAAH" ya faɗa idanunsa na sauya kala, maƙale masa tayi tace "To ka daina guduna sai na kwana na yini ban ganka ba" Jinjina kai yay tare da zare a jikinsa a hankali ya ɗura jajayen laɓɓansa saman goshinta ya sumbata yace "Idan kika guje ni zan iya rasa rai" Murmushi tai masa tana jan gemunsa tare da nufar bakinsa zata sumbata yay saurin ɗaukan dabinon Ajjuwa ya cilla cikin bakinsa tare da matsar da ita gefe guda ya juya da sauri yabar mata ɗakin.. SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:35 - 🤔🤔: Touching heart //////// 65-66 Sheikh bai dawo gida ba sai da yaja mutane sallar Ashān, ya daɗe cikin Mosque ɗin yana azkar da addu'oi kafin gently ya miƙe tare da nufar ƙofar barijy masallacin, cikin Dattaku yake taka ƙafafuwansa cike da ilham da kuzari yana tafe yana magana ƙasa² tare da gyara zaman farin bluetooth ɗinsa a kunne yana jan ƙwantaccen sajensa yace "Yeah! Mafimushkilah Arjun" shiru yay yana sauke numfashi kafin yaja idanunsa ya rufe cikin taƙaitawa yace "Uhm! Sure?" Daga can ɓangaren Arjun na zaune da matarsa Aliyah tana bashi ƴar ƴan itatuwa yana ci yace "Lemme freshen up, zan zo na maka bayani komai amma duk dukiyar da za'a bada zakkar ta Olrdy an shiryata kai kawai ake jira, then kace a kawo kaji guda dubu uku a ramawa mutane sbd wanda basu dashi, Nan ma nai mgn da gidan gonarka ba zamu iya taɓa kajin can ba sbd suna kanyin ƙwai ne, zan duba wani gidan gonar" fararen idanunsa Sheikh ya juya sbd footsteps ɗin da yaji idanunsa suka sauka kan Barrister dake tafe yana waya "Ok! See you soon Arjun" yana faɗin hakan ya katse kiran dan har yanzu bai wani saba da riƙe waya ba, Barrister ne ya sakar wa Sheikh murmushi yace "Son how are you? Kasha ruwa lfy?" Idanun Sheikh akan Mahaifin nasa kamar bazai amsa ba sai kuma yace "Allahamdulillah, jibi zan tafi Oumara" ya faɗa yana ɗauke idanunsa dai-dai ta tafiyarsa yay data Sheikh yace "Ma sha Allah, nasu zuwa amma abubuwa sun min yawa" jinjina kai Sheikh yay ba tare da yay mgn ba "Ya kamata kaje waje ka huta Sheikh" nan ma shiru Sheikh yay sai kuma yace "Ok zani" ya faɗa yana tura kansa cikin Parlon tare da faɗin _"Assalamu alaikum"_ Granny tace "Mara ba lale, yau kam Imamu ka gajiyar dani wannan jan Sallah Kamar a filin tashin ƙiyama" fiddo idanunsa waje yay kana ya durƙosa dai-dai ƙafafuwanta ya ɗura kansa saman cinyarta ganin haka yasa Granny yin shiru jikinta yay sanyi tace "Imamu kai dawa wane ya taɓa ka? Duk sanda kayi min haka nasan Zcyarka babu daɗi damuwarka taje ƙarshe" Shiru yayi sai riƙe hannayenta da yay cikin nasa cikin nutsuwa Granny ta Fara wargatsa masa sumar kansa ya shiga sauke tagwayen ajjiyar zuciya kamar wanda yake tsaka da jinya, sai da ta tabbatar ya samu nutsuwa tace "Allah ya tsare gabanka da bayanka, yooo ni duk wanda yace zai ci zalinka bashi da Allah ba? Dodo gudanawa kake fisabilillahi? Amma abi an sawa rayuwarka idanu, to! Ta Allah bata mutum ba idan mutum maye ne sai dai yaci kanka" ta faɗa tana tura kallabi gaba tace "Haka Yarinyar kallo guda nai mata nasan ciki gareta, fatana suzo bisa Aminci da kuma ishasshiyar lafiya ba kamar yadda mahaifiyarka ta kasance ba" Sai lokacin ya ɗaga kai ya kalleta kamar bazai magana ba sai kuma yace "Granny AMMI!!" Shafa kansa tayi tace "kayi addu'a wata rana zaka kanta jikina ya fara bani ka kusa ganinta" miƙewa kawai yay ba tare daya sake mgn. Yana shiga Part ɗinsa ya watsa ruwa tare da sauya kaya zuwa ƙanana na shan iska, bayan ya gama wannan karan babban Parlo ya fito. Mami ta riƙe wayar tace "Ai dani suke zan can daga Barrister har ita yarinyar nan badai jibi zai bar ƙasar ba to zasu gane ni Saudat ba kanwar sala bace" Fariha tace "Ke kam kina nan da halinki Ni yanzu Abban Taufiq ai gantalalliya ya mai dani" Mami tace "Mene ya faru kuma yanzu?" Cikin damuwa Fariha tace "Uhm! Wai warin hammata nake kinji masifa" dry Mami tayi harda faɗuwa daga kan bed tace "Kambu, gsky na miji a barshi, dame kike amfani?" Fariha tace "Wlh ni nama manta sunanta" Mami ta tsaya da dry tace "ki nemi alamun ba warin hammata ba ko ubansa kike wlh zaki daina, ke ko gumi fatarki ke riƙewa wlh ta daina, Alimun yana da kyau sosai ki siya ki jiƙa a jarka ko kwalba" cike da gamsuwa Fariha tace "Ok I'll try, Ya Nimcyluv kowa ta Fara ABU MALEEK?" Mami tace "A'a! Tace sai new year but payment is still going zaki y biya, tace kamar dai long story ne, kuma abin daɗi na Sarauta" Fariha tace "Wow! Matar tayi ai, sai kika tuna min da THE NEW EMIR Musamman wajan kilisar nan, kin san a wajan Sarki ya mada umarnin tafiya da Saif zuwa ɗakin duhu sbd ya faɗi a kilisar" Mami tace "Tabbas anyi haka, ai wannan Lil Prince ɗin anyi gantalalle nidai kam Olrdy nai payment har ƙari 10k na mata, domin littafin yafi kuɗin data faɗa" Fariha tace " She's nice person bata da hayaniya, in sha Allah I'll send her my money, zan mata kyauta domin tana da hqr gashi ta iya tsara labarin sarauta" Mami tace "Hkan yayi bari nai wani babban aiki sai da safe" tana faɗin haka ta kashe wayar ta. Fitowa tayi da sauri taga Fannah ta ajjiye plate ɗin abinci saman dinning ita kuma ta shige cikin kitchen da sauri ta nufi abincin ta barbaɗa magani tare da juya,cikin sassarfa tabar wajan. Bottle e Fannah ta ɗauko tare da lemon juice ta dawo wajan dinning ba tare da tunanin komai ba ta ɗauki spoon ta fara juya Abincin, walking slowly Sheikh yake tafiya har ya ƙarasu cikin Parlon yana ƙoƙarin zama yaji mutsu a dinning area Juyawa da sauri kuma ya ɗan miƙe tsaye yana ware idanunsa yana son tabbatar da abinda idanunsa suka gani, plate ɗin abincin da Fannah ta keci yaga yana hayaƙi, ganin haka kuma ya tabbatar masa da rashin ingancin abincin, tana ƙoƙarin sanya wani abincin taku ɗaya biyu yayi yay fatali da spoon idannunsa har ruwa yake, kallonsa tayi tana ƙoƙarin yin magana ya sanya hannunsa tare da ɗaga ta tsaye idanunsa a saman bakinta cikin saurin Murya yace "Kinci abincin?" Kallon ban gane mai kake nufi ba tai masa cikin tsawa yace "nace kin ci abincin?" Kaita ɗaga masa alamar "eh" ta kasa magana sbd sauran abincin dake bakinta matsuwa ya wajanta ita kuma taja baya sbd tsoransa daya shigeta, har sai da suka je bango kana ta tsaya ba tare da yace komai yasa tattausan hannunsa ya tallafo haɓarta kana yay copping face ɗinsu waje guda suka shige sauke numfashi jin kamar wani zaizo yasa ta buɗe baki zatai magana yay saurin sanya lallausan softness lips ɗinsa cikin bakinta runtsa idanunta tayi jikinta ya saki gaba ɗaya ta sakar masa nauyinta cikin nutsuwa Sheikh ya fidda tongue ɗinsa ya fara yawo dashi cikin bakinta yana zaƙolo raguwar abincin bakinta yana mai dawa nasa, sai da ya kwashe tass Sannan ya zare bakinsa yana sauke numfashi, kai tsaye wajan ragowar abincin yaje ya zubar dana bakinsa ciki ba tare daya kalleta ba ya nufi cikin kitchen zcyarsa cike da fargaba. Daskarewa Fannah tayi a wajan sai fidda numfashi take some minutes tana tsaye kafin a hankali taja ƙafafuwanta ta nufi part ɗinta, tana zuwa ta samu wayarta na ringing zama tayi tare da answering call ɗin cikin ƙaramar muryarta tayi sallama da sauri Yana tace "Fannah Albishirinki" ware ido Fannah tayi kafin tace "Goro fari" Yana tace "Gobe Sheikh zai bai yana kansa ka masoyansa" ƴar dry tayi tace "Shi Sheikh ɗin kenan ko?" Da Murna Yana tace "Wlh da gaske fa, Wow ki kunna ko wacce channel kike so zaki samu sbd live ne a bun" dry Fannah tayi tace "To yaya kike tunanin zai kasance?" Yana tai jimm sai kuma tace "Nasan zai kasance kyakkyawa koda fatarsa ta kasance baƙa" kai tsaye Fannah tace "bana jin ma zai zama baƙi, yadda kike tunanin ya huce haka, kwarjininsa kaɗai sai ya zautar dake Yana" "To ke ina kika san haka?" Fannah tace "A'a kin san soyayyya gaske daban take, turawa kuma sukace _true love never end_ Tsaki Yana tai tace "Wlh ba kyau kina gidan wani kina zan can wani daban" Fannah tace "Shkknan na daina Amma wata ranar zaki gane cewa Allah ɗaya ne, Yawwa Bayan Sallah zan zo nai missed gida sosai" haka dai suka ci gaba da hira kafin kuma su kashe wayar, dafe kanta tayi jin yana sara mata a hankali tai baya ta kwanta tana tunanin fal a haka bacci ya ɗauke ta. Sheikh na shiga kitchen ya ƙura wa plate ɗin abincin ido a hankali ya zare fararen idanunsa dan bai son sanyawa zcyarsa zargi, bakinsa ya wanke tass kana ya ɗauki Apple da Malt ya dawo ya zauna saman sofa tare da ɗaukan remote ya ƙaro gudun ac, bai daɗe da zama ba Arjun yay Sallama ya shigo da mita ya fara mgn "Allah sarki ni Mohd abin tausayi, wlh sai ƙarewa nake a tsaye" ko inda yake Sheikh bai kalla ba sai da ya ƙara faɗin "Wlh ko damar kasancewa da matata bana samu, haba nikam na huru kawai ka haɗe min aikin nan waje guda yasin indai akai magrib na daina fitowa" lumshe idanunsa yay a hankali ya dinga tauna Apple yana jine yadda zaƙin ta ke ratsa cikin bakinsa, ɗauka Arjun yay shima yasa a baki yace "Kasan ance kayan kwaɗayi yafi daɗi" cire hannunsa yay tare dayin baya yana hamdala sai da ya ɗan nutsu yace "Uhm, hope ka gama komai?" Arjun yace "As your wish, kai kawai ake jira domin ko wanne gidan t.v da redio a shirye suke tuni an saki breaking news" jinjina kai Sheikh yay yace "Nima jibi jirgin mu zai ɗaga" haɗe fuska Arjun yay yace "Ni dai gasky wannan karan ba zani ba, wanda nai Allah ya bada lada" ta gefen ido Sheikh ya kalli Arjune ba tare da yace komai ba ya miƙe tsaye yace _"Tasbahii alaa khaaiir"_ miƙewa Arjun yay yace "Mace tasa kana neman zaucewa duk ka aro halin daba naka ba ka ɗura kanka" Murmushi kawai Sheikh yay kana ya nufi Masar part ɗinsa haka nan yaji gabansa na faɗuwa. Cikin dare Fannah ta farka da wani a zababban ciwon kai ga nauyin da kanta yay mata haka nan ta samu kanta cikin ɓacin rai da kuma damuwa wacce bata san ta mecece ba. Washe gari ya kama Friday (juma'a) tun wajan ƙarfe 11 Mutane suka cika babban *Abuja National Mosque* mata da maza manya da yara kowa burinsa bai huce yaga SHEIKH IMAM HAMDAN BALARABE ba, gidan Redio banda Sanarwa ba abinda suke t.v tuni sun fara haska cikin Masallacin. Aslam ya kalli Ammi yace "Wlh yau ina cikin farin ciki wlh jiya har mafarki bawan Allan nan nayi" Tattausan Murmushi tayi tana kallon Mijin ta Deedat dake suba wasu files tace "Same to me, Ina son ganinsa a zahirance ba'a t.v, ko wacece ta haifesa babarsa ta iya haihuwa Ma sha Allah" kallonta Deedat yay yace "Da gaske kina son ganinsa?" Kai ta ɗaga tana ƙara kallon cikin t.v yace "Zan nemi Appointment dashi in sha Allah, badai zaije Oumara ba" Aslam yace "Papi nace ba zani Oumara ba amma dalilin Sheikh naji ina son zuwa" Anuska tace "Yaaaah Sheikh" Aslam yace "Kaga ƴar iya har ya zama yaya". Sheikh yana gaban mirror sanye da wata ɗan yar shadda Gezner ɗin kin wando da Jamper sai babbar riga, ya ɗura wata farar riga mai kamar Alƙyabba a saman shaddar, kana ya ɗura farin hirami saman hular kansa, sai ƙamshi ke tashi a jikinsa idan kaga Sheikh a lokacin zaka ɗauka wani babban mutum ne mai bala'in shekaru sbd tsarin halitta da kuma kamewarsa haɗi da cikar kamala, kallon kansa Sheikh a madubi cikin zazzaƙar muryarsa yace _"Ohh! Ya rabbi You look Good Sheikh Imam hamdan Balarabe"_ ya faɗa yana shafa fuskarsa, jim yay tare da kallon wayarsa yaga Arjun ke kiransa yasan Tabbas jiransa yake, katse kiran yayi kana ya faɗa saman kujera yana ɗan lumshe idanunsa a karon farko ya fara danna wayarsa cikin nutsuwa ya sanya lambobin ta wanda ya haddasa ce a kansa, dailing ta fara ringing, tsaki Fannah taja sbd ƙuncin dake ranta tana jin wayarta na ringing tai banza da ita, wayarsa yabi da kallo yana mmkin rashin ɗaga wayarta kuma yana da tabbacin tana da numbersa, ƙara kira a karo na biyu ware Idanunta ta kalli wayarta taga sunan _SHEIKH_ na yawo tsaki yaja kana tai answering call ɗin cikin ɗaga murya tace _"Pls who I'm i speaking with?"_ fiddo idanunsa waje yay sbd yanayin muryarta da yaji ta sauya kamar ba Zahraaansa ba, cikin ƙasa da murya kamar mai lallashi yace "Assalamu alaiki" ya faɗa a tattaushe ji tayi kamar an caka mata mashi a zcy a zuciye tace "Nace waye ne kamar ba'a fahimtar hausa" Dam!! Dam!! Zcyar Sheikh ta buga da mugun ƙarfi ɗauke tunanin komai yay yace "I'm Sheikh Imam hamdan Balarabe" Shiru tayi kafin tace "Mtwsss to meye haɗi na da kuma wani Imam, dan Allah malam Allow me to enjoy ka gane" miƙewa Sheikh yay ya fara zagaye Bedroom idanunsa yay jajirrr cikin damuwa yace _"Wake Up Zahraaah!!"_ miƙewa tayi tsaye tace "Uban Uban wake up ɗin, kai dallacan kai ka san wata Zahraaah ni Fannah nake, kuma kada ka sake kira na idan kuma ka kira wlh..." Sai kuma tai shiru wani Murmushi takaici yay dan baya tunanin wannan Zahraaah ce sai dai mutanan ta suka kawo mata ziyara yace "Or else?" Kai tsaye tace "wlh za kaga rashin mutuncin da tunda uwarka ta haifeka ba'a...," Bai tsaya yaji ƙasashen zan can ba yay saurin cire wayar a kunansa kai tsaye kashe wayar yay gaba ɗaya ya cilla cikin wardrobe, tsaki Fannah taja tace "Mai gemun banza kawai" kansa a ƙasa zcyarsa na mugun bugawa yay waje a Parlo ya samu Fareeq da Arjun suna ganinsa suka miƙe tsaye Mami kam da wani ƙayataccen kallo ta bishi har suka fita. Kai tsaye babban masallacin juma'a suka nufa securities sun fara binsu Sheikh yace baya buƙata, lokacin da suka isa kowa tuni masallacin ya ɗinke da al'ummar Musulmi, a tsaye ya tsaya saman digadigansa speakers babu adadi a saitin bakinsa, gyaran murya yay kaɗan hakan yasa gaba ɗaya hankalin jama'a na masallacin dana gida sukayo kansa, Ya Falta tace "Yasubuhanallah, tsarki ya tabbata ga wannan halittar, amma kamar na taɓa ganin sa, but where? And when?" Yana tace "ƙaryar banza ina za kuga wannan Balaraban?" Kai tsaye Ya Falta tace "Wlh a gidan Fannah na ganshi time ɗin yana Parlo ko inda nake ban kalla ba yabar waje amma kamar a Wheelchair na ganshi". Ammi tunda ta ɗura idanunta akan Sheikh ta kasa ɗaukewa, Fannah kam tashi daga Parlon ta koma cikin bedroom tana jin gidan yay mata zafi ko buɗe ido bata son tayi taga Sheikh ko taji an ambaci sunansa. Gyara tsaiwar sa yayi idanunsa a lumshe kana ya ƙara covering jikinsa da rigar daya ɗura ƙara saita lafiyayyar Muryarsa yay yace. _السلام عليكم يا إخوة المسلمين كما عرفتم أن اسمي الشيخ إمام حمدا (بلا ربي) اليوم يوم الجمعة الذي يواق ١٥ في شهر رمضان سأذكر علي أشياء الذي شغلنا عليهم_ _(Assalamu alaikum ya ikwatul musulimina kamaa araftum anna ismii ashsheik imam hamdan balarabe alyaum yaumul juma'a yawaaqi 15 fi ramadhana sa'uzakkiru alaa ashiya'ul lazi shagalna alaihim)_ gaba ɗaya wajan yay tsiit kowa yana sauraran abinda Sheikh zai ce, numfashi ya sauke kana ya kure damuwar ransa ya fuskanci mutanan gabansa yaga kusan rabi hausawa ne dan haka ya sauya akalar harshen sa zuwa Hausa yace "In sha Allah! Zanyi tuni da abubuwa guda Uku da muke yawan mantawa dasu kana muka gafala akansu.." Shiru da sauri wani securities ya miƙa masa bottle ganin haka Arjun yabar wajan ba jimawa ya dawo ɗauke da ruwan da Sheikh yake sha ya buɗe ya bashi, cikin nutsuwa yasha ruwan kana ya matsar da bakinsa sai tin kunan Arjun yace "kar ka kuskura ka ƙara tashi" ya ƙare maganar yana ɗan sakin murmushi. Gyara tsaiwa yay yace. *ZINA* ﻭَﺻَﻠَﻰ ﺍَﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻰ ﻣَﻦْ ﻵ ﻧَﺒِﻲِّ ﺑَﻌْﺪَﻩُ Tsira da amincin ALLAH sutabbata ga ANNABIN dababu wani bayanshi Salati da tsira da amincin Allah su tabbata bisa Jagoran Annabawa da Manzanni, Shugabanmu Annabi Muhammadu (ﷺ)tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa Maɗukaka. ILoLin zina da kuma Hukuncinta Ya tabbata a cikin hadisi an tambayi Annabi (ﷺ) a kan wane zunubi ne ya fi girma, sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce, “Shirka da Allah alhali Shi ne Ya halicce ka.” Sai aka ce ‘sai wane?’ Sai ya ce, “Sannan kashe ɗanka don kada ya ci tare da kai.” Sai aka ce “sannan sai wane?” Sai ya ce, “Ka yi zina da matar makwabcinka.” (Bukhari). yadda ruwaito Allah Maɗaukakin sarki Ya sanya hukuncin wanda duk ya yi zina kuma ya taɓa aure, a jefe shi, namiji ko mace; idan kuwa bai taɓa aure ba, sai a yi masa bulala ɗari, sannan a baquntar da shi a wani gari daban tsawon shekara guda. Duk wanda ya kalli hukuncin zina, zai ga Allah Ya keɓance shi da wasu abubuwa masu yawa, saboda munin zina. Ga kadan daga cikin abubuwan da hukuncin ya kunsa: 1. Kausasawa wajen ukubar mazinaci, ta hanyar jefewa. Ko kuma bulala da bakuntarwa shekara guda. 2. Hana jin tausayin mazinaci ko mazinaciya yayin da ake musu ukuba. Allah Ya ce : ٱلزَّانِيَةُ وَٱلزَّانِى فَٱجْلِدُوا۟ كُلَّ وَٰحِدٍ مِّنْهُمَا مِا۟ئَةَ جَلْدَةٍ ۖ وَلَا تَأْخُذْكُم بِهِمَا رَأْفَةٌ فِى دِينِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمْ تُؤْمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلْيَوْمِ ٱلْءَاخِرِ ۖ وَلْيَشْهَدْ عَذَابَهُمَا طَآئِفَةٌ مِّنَ ٱلْمُؤْمِنِين “Mazinãciya da mazinãci, to, ku yi bũlãla ga kõwane ɗaya daga gare su, bũlãla ɗari. Kuma kada tausayi ya kãma ku game da su a cikin addinin Allah idan kun kasance kunã yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Kuma wani yankin jama, a daga mũminai, su halarci azãbarsu.” . (Annur : 2). . Yi musu ukuba a gaban mutane, ba a yarda a yi musu a boye ba, Allah Ya ce : Duk waɗannan abubuwa suna nuna mana munin zina da rashin kyanta a Musulunci. Imamul Bukhari ya kawo, a cikin ingantaccen littafinsa, daga Maimun Al-audiy ya ce, “A lokacin jahiliyya na taɓa ganin wani biri da ya yi zina da wata biranya, sai sauran biran suka taru suka jefe su”. Mafi munin zina ita ce wadda mutum zai yi da mahaifiyarsa, sai da muharramarsa, sai wadda zai yi da matar makwabcinsa. Allah Ya kare mu. ILLoLin Zina: Babu shakka duk mai hankali ya san cewa zina tana tattare da illoli masu yawa, waɗanda suke shafar mazinacin ko mazinaciyar, ko su shafi al’umma gaba daya. 1. Zubar da mutunci da jawo wa kai qasqanci: Duk matar da ta yi zina to ta jawo wa kanta da danginta da mijinta ƙasƙanci, ta kuma zubar musu da mutunci a idon duniya. Idan har ta sami ciki ta haihu, sannan ta kashe ɗan, to ta haɗa laifi biyu, laifin zina da laifin kisan kai. In kuma ta bar shi, to kuma ta shigar wa mijinta ko danginta, wanda ba ya cikinsu. Idan kuwa mai zinar namiji ne to ya lalata mace, ya jawo mata lalacewa da taɓewa, wanda hakan lalata duniya ne gaba daya. 2. Zina ta haɗa dukkan sharri gaba ɗaya: Saboda a cikin zina akwai rashin tsoron Allah; rashin kunya; rashin tsantseni; rashin cika alkawari; ƙarya da butulci da sauransu. Duk kuwa waɗannan munanan halaye a Musulunci. Manzon Allah (ﷺ) yace Allah ya la’anci mai sake al’aura da mai kallon al’auran wani. Baihaqi ya ruwaitoshi an karɓo daga muazu ɗan jabal (r.a) ya karɓo daga manzon ALLAH (ﷺ) sai yace ranar alqiyama ranar hasara ce da nadama ALLAH zai ta da al’umma daga ƙabarburansu siffa goma sha biyu (12). Siffa na biyar daga ciki. Za’a tashesu daga cikin ƙabarinsu suna wari kamar dunge Mai kira yayi kira da fuskar ubangiji waɗannan sune masu zina sun mutu batareda sun tuba ba, basuji kunyar Allah maɗaukaki ba wannan shine sakamakonsu makomarsu zuwa ga wuta. Gaba ɗaya wajan yay shiru wasu daga cikin matasa banda kuka babu abinda suke, sunkuyar dakai Sheikh yana jan numfashi a hankali wata zazzafar ƙwalla ta sakko daga cikin idanunsa zuwa saman fuskarsa, yana jin wani ɗaci a ransa ga wani zafi da zcyarsa ke masa, idanunsa a goge tass yana gyara tsaiwarsa, a hankali ya buɗe dararan idanunsa ya sauke saman camera da sauri Fannah ta janye idanunta sbd ganin kamar ita yake kallo tace "Anyi banzan Malami dai, kai har kana da bakin yin magana akan zina? Shiyasa ake cewa ka yarda da faɗar Malam kada kai aiki da abinda yake aikatawa" girgiza kai Sheikh yay kana yace "Ƙaddara!!! Ba abinda bata sanyawa wasu ba halinsu bane ƙaddara ce wasu bata da madafa idan ta hau kan ka sai lokacin lokacin ta yay, kuma ƙaddarar tana da nata lokacin wata rana zai zo kamar ba'ai ba, wasu iyayansu nada sila wajan abinda ɗan su yay, wasu kuma ƴan matan su keda sila haka dai, Bayan zina sai. *ZAKKA* WACE IRIN DUKIYA CE ZAKKA TAKE WAJABA A CIKINTA? Zakka ba ta wajaba a cikin duk abin da Musulmi ya mallaka domin amfanin kansa, kawai, komai tsadarsa kuwa. Misalin wannan shi ne gidan da yake zaune a cikinsa. Ba ta kuma wajaba a cikin motarsa ta hawa komai alfarmarta. Haka nan kuma tufafi da abin ci, da abin shansa. shiru Sheikh yay tare ɗaukan ruwa yasha idanunsa cikin camera yace. Dukiyar da kawai, Allah Maxaukakin Sarki ya wajabta fitar da Zakka daga cikinta, ita ce wadda ta tabbata, ba ta daga cikin abin da yake biyan bukatun mai ita, na yau da kullum, tana kuma kan wata turba ta qaruwa da havaka da bubuta, kama: Zinari da Azurfa: Zakka ba ta wajaba a cikin zinari da azurfa, sai idan sun kai wani matsayi na ywa, wato, nisabi, sa’annan kuma sun cika shekara xaya cif ta shekarar Musulunci, wato kwana xari uku da hamsin da huxu. Nisabin Zakkar Zinari da Azurfa Shi ne Kamar Haka: Ba za a tava Zinari da nufin fitar masa da Zakka ba, sai idan nauyinsa ya tasar wa giram tamanin da biyar “85’’. Ita kuwa Azurfa sai nata nauyin ya tasar wa giram xari biyar da casa’in da bayar “595’’. Dukiya da Kuxaxe: Dukiya da kuxaxe kowaxanne iri ne kuwa, da suke hannun mai su, ko ajiye a cikin bankuna. Yadda Ake Fitar Musu da Zakka: Ana lissafa nisabin dukiya da kuxaxe dabra da kwatankwacinsu na Zinari. Idan qimarsu ta yi daidai da qimar Zinari ta Zakka, ko fiye da haka, wato nauyin kusan giram tamanin da biyar “85’’ xin can da aka ambata a kuma daidai lokacin da Zakkar ta zama wajibi; bayan ta cika shekara xaya ta Musulunci tana qanqashin mallakar mai ita. To, zai fitar da kasha biyu da xigo biyar 2,5% a matsayin Zakka. Ga Misali: Kowa ya san farashin Zinari ba ya da tsayayyar alqibla; canzawa yake yi. To, da za mu qaddara cewa, farashin giram xaya na Zinari a daidai lokacin da fitar masa da Zakka ya wajaba, yana daidai da dalar Amerika ashirin da biyar “25’’. To, a haka nisabin Zakkar dukiyar zai zama kamar haka: 25 “farashin giram xaya na Zinari wanda yake canzawa lokaci-lokaci) x 85 “adadin giram da aka mallaka, wanda ba ya canzawa) = dalar Amerika 2125 “wannan shi ne nisabin dukiyar). Dukiyar Kasuwanci: Abin da ake nufi da dukiyar kasuwanci xin nan, shi ne duk wani abu da mutum ya tanada domin kasuwanci, wanda kuma ba a iya canza wa bagire, kamar filaye da gidaje manya da qanan. Kazálika, da kayan abinci da waxanda ake saye don wani amfani na daban. Yadda Ake Fitar Musu da Zakka: Mutum zai gano tare da lissafa qimar gaba xayan dukiyar nan tasa, ta kasuwanci bayan shekara xaya cikakkiya. Zai kuma yi amfani da farashi mai ci; wanda yake gudana a kasuwa a daidai ranar da ya shirya fitar da Zakkar dukiyar. Idan dukiyar nan ta kai nisabi, to, sai ya fitar da kasha xaya bisa huxu na kasha goma daga cikin xari, wato 2,5%. Abin da Yake Fitowa Daga Cikin Qasa: Tsirrai da ‘Yayn Itace da Hatsi: Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Ya ku waxanda suka yi imani! ku ciyar daga mai kyau abin da kuka sana’anta kuma daga abin da muka fitar saboda ku daga qasa” [Baqara:267]. Sai dai Zakka tana wajaba ne kawai a cikin wasu kevantattun tsirrai; ba gaba xayansu ba. Ko kuma da sharaxin sai sun kai wani adadi kevantacce a idon Shari’ah. A wajen fitar da Zakkar wannan nau’i xin ma, ana la’akari tare da banbancewa tsakanin abin da aka noma ta hanyar ruwan sama, wato noman damana, da wanda aka noma ta hanyar shayarwa, wato, noman lambu. Haka kuma da tsakanin wanda aka shayar ta wasu hanyar amfani da wasu kayan aiki, da aikin kansa. Duk ana la’akari da waxannan abubuwa a cikin qimanta abin da yake wajibi na Zakka. Shari’ah kuma ta yi haka ne saboda kula da mutunta yanayi da halaye da al’adun mutane. Sharuxxan Wajabcin Zakkar Tsirai da ‘Yayan Itace: Cikar Nisábi: Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya riga ya qayyade adadin da wannan Zakka take wajaba a cikinsa; qasa gare shi kuma walá. Ga abin da yake cewa: “Babu Zakka a cikin qasa da buhu biyar na dabino.” [Buhari:1447/Muslim:979]. Wannan miqidari na kilo ne. Sai dai alkama daa shinkafa ana kimanta nauyinsa da kilo giram 580-600. To, duk abin bai kai haka ba, babu Zakka a cikinsa. Tsirrai Xin su Zama Daga Cikin Abubuwan da Zakka ke Wajaba a Cikinsu: Zakka bat a wajaba sai a cikin amfanin gona wanda ake iya ajewa da taskancewa na tsawon lokaci, ba tare da ya lalace ba. Wannan, kamar alkama, da sha’iri, da zabíbí, da dabino, da shinkafa, da dawa. Amma abin da ya shafi ababen marmari, waxanda ba ta yiwuwa a ajiye sun a tsawon lokaci, kamar kankana, da Rumman, tumarur, da matara kama da su, Zakka ba ta wajaba a cikinsu. Kammala Nomewa: Zakka tana wajaba ne kawai a cikin kayan amfanin gona idan an nome an kuma girbe su gaba xaya.Sa’annan kuma zagayowar shekara a kansu, ba sharaxi ba ne. Idan akwai wani amfanin gonad a ake girba sau biyu a shekara. To, ya zama wajibi a fitar masa da Zakka duk lokacin da aka yi girbinsa. Garukkan Dabbobo: Abin ake nufin da Garukkan Dabbobi xin nan, shi ne kevantattun dabbobin da mutum yake amfani da su, da suka haxa da: Raqumma, da Shanu, da Bisashe. Ta tabbata cewa, Allah Maxaukakin Sarki ya halicci waxannan dabbobi ne a matsayin wata ni’ima ga mutane, domin su ci namansu, su sha nononsu, su sarrafa fatunsu su yi tufafi, su kuma riqa xora musu kaya idan za su yi wasu tafiye-tafiye ko qaurace-qaurace. Ga abin da Allah Maxaukakin Sarki yake cewa a kan haka: “Da dabbobin ni’ima, ya halicce su dominku. A cikinsu akwai abin yin ximi da waxansu amfanoni, kuma daga gare su kuke ci. Kuma kuna da kyau a cikinsu a lokacin da suke komawa daga kiwo da marece da lokacin da suke sakuwa. Suna kuma xaukar kayanku masu nauyi zuwa wani gari, ba ku kasance masu isa gare shi ba, face da tsananin wahalar rayuka. Lalle ne Ubangijinka ne, haqiqa, mai tausayi, mai jinqayi” [Nahki:5-7]. Manyan Sharuxxan Zakkar dabbobi: Nisábi: Wajibi ne adadin dabbobin nan ya kai nisabi karvavve a idon shari’ah, saboda Zakkar bat a wajaba sai a kan mawadata. A haka kenan wanda ya mallaki wani xan adadi na dabbobi, wanada biyan wasu bukatum rayuwarsa ya dogara a kansu, ba zai fitar musu da Zakka ba. Nisabin raqumma shi ne raqumi biyar “5’’, na bisashe kuma, tunkiya arba’in “40’’, na shanu kuma, shanuwa talatin. Duk adadin da bai kai wannan ba, babu Zakka a cikinsa. Cikar Shekara: Ba za a tava garken dabbobi da nufin fitar masa da Zakka ba, sai bayan cikar shekara xaya ta kalamdar Musulunci, da mallakarsu. Kiyo: Dabbobin da suke tafiya yawon kiwo, suna ci daga taskar Allah, su ake fitar wa Zakka. Amma, waxanda mai su yake saya wa abin ci a mafi yawan kwanakin shekara, babu Zakka a cikinsu. Húxá: Dabbobin da mai su yake huxa, da hawa, da xaukar kaya da su, ba a fitar musu da Zakka Hannu yasa ya dafe ƙirjinsa da zafi² yace "a nan ni Sheikh nake cewa Ma'assalam Allah ya amshi ibadunmu" yana faɗin hakan ya juya da sauri Fareeq da Arjun suka mara masa baya, Ammi kuka tasa wanda bata san menene dalilin yin hakan ba, mutane da yawa suka dinga sanyawa Sheikh albarka yayinda ya tafi da zuciyoyin ƴan mata da yawan gske. Washe gari asabar jirgin su Sheikh zai ɗaga da misalin karfe 10 na safe, abun Duniya yay masa zafi Fannah yanzu ko waje bata fitowa idan ma ta fito sai bayan baya gidan ya gama shirin sa tsaf amma zcyarsa ba daɗi fuskarsa ba walwala, yana tsaye gaban Granny tace "Mugun ji da mugun gani ya kare Allah ya tsare ya kiyaye ka wuni a ka'aba ka gayawa Allah dukkan buƙata tunka ah! To baya gyan gyaɗi bare bacci shi mai yafiya ne da kuma kyautatawa" Rungome ta yay sosai yace "Granny ko akwai abinda kikeson faɗa min ne?" Kansa ta shafa tace "Ka siyo zam zam da dabino da yawa, da takwarata ta haihu shi za'a na bawa ɗan" gabansa ya faɗi yace "Wace zata Haihu?" Tace "Matar ubanka baka san ciki gareta ba? An to daman meye naka da zaka sani? Ai shirgin mata ne wannan" zare jikinsa yay yace "Ok mun tafi Granny ki kula" yana faɗin hakan yabar ɗakin daman Fareeq da Bahaiyya da Arjun na waje Mami kam tuni tabar gidan dana haɗa wani plan, Barrister ma baya gidan, fitowa SHEIKH yay kamar ance ya ɗaga kansa ya ganta tana ƙoƙarin shiga kitchen da sauri ta juya ta shige kitchen cikin zafin nama shima ya shiga kitchen ɗin tare da rufe ƙofar kai tsaye ya fara takawa zuwa inda take jikinsa har rawa idanunsa yay jajirrr... SIRRIN MU isn't free contact to me to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:35 - 🤔🤔: Heart broke ###### 67-68 Waje Fannah taja ta tsaya idanunta ta akan Sheikh ta haɗe fuska ko alamun fara'a babu, shima Sheikh fuska babu walwala ya ƙarasu inda take yaja ya tsaya, haka nan ta fara jan tsaki shi kam ko mutsi bai ba sai da yaga ta gaji dayin tsaki ya Tattausa harshen sa yace "Are you ok?" Banza tai masa idanunsa ya lumshe ya ƙara matsuwa kusanta kamar zai haɗata ta jikinsa ya leƙa fuskarta yace _"Zahraaah?"_ wani ƙyakƙyawan tsaki tayi kafin ta ɗaga Idanunta tace "Malam wai meye haɗina da kai ne? Kai min abu na rabu dakai ko su kake ka ƙarayin zina dani? Kaje ka fake da ayoyin daka sani ka karyawa mutane zcy? Koda yake ba abin mmki bane daman Malaman nan ka ɗan ne masu tsoran Allah" runtsa idanunsa yay sosai yana jin maganganun ta kamar fitar mashi a ransa, rinannun idanunsa ya sauke a fuskarta ya ƙara matsawa yay jikin kamar zai rungome ta tace "Kaga mana son rainin wayoo da ƙwarewa a iskanci dalla kauce kaban waje, mai gemun banza kawai" da sauri ya ƙara buɗe idanunsa domin yana son ya fahimci inda ta dosa dan haka sai ya ɗan ja baya tare da miƙa fararen hannayensa zai kama nata tai saurin hanka ɗesa tace "Allah ya sauwaƙe ba zaka shafan najasa ba wlh, Allah kaɗai yasan karnukan matan da kake bi" bai son lokacin daya fidda tafin hannunta ya sauke a saman fuskarta ba, jikinsa duk rawa yake, ba ƙaramin shigarta marin yay ba amma sbd taurin kai da kuma nace tace "Goodness! Sai dai ka dake ne amma wlh kayi tsararo ka taɓa jiki na, jikina ba irin na ƙaza mai bane kamar ka" wani marin ya kuma sauke mata zafin marin yasa tai saurin yin baya zata da wani Irin zafin nama yasa hannu ya fisgota jikinsa ya matseta sosai a saman faffaɗan ƙirjinsa ya shiga sauke mata numfashi a fuska, idanunta ta rufe domin da gske bata ƙaunar ganinsa ko kuma taji an ambaci sunansa, jajayen laɓɓansa ya sauke saman nata hancinsa dai-dai nata kana ya sanya tafin hannunsa a saman lafaffan cikinta wanda akace tana da ciki dan sai yanzu mganar ta faɗu masa sai fi kowa farin ciki da samun cikinta, domin Ubangiji kaɗai yasan abinda yake ɓoye tsakaninsa da _Zahraaah_ tarayya ta lokaci ɗaya ace har an samu rabo wannan rabon kam ba ƙaramin rabo bane, murmushi ya sakar mata yace "Oh Wow! Ashe dai ba Sheikh bane kaɗai ɗan iska, tunda lokacin da mukai abun ba dole nai maki ba, then bani na roƙa nace ki so ni" baƙin ne ya kama Fannah tai saurin tattaro rayuwar yawon bakinta ta tofa masa saman farar kamilalliyar fuskar, sosai zyar Sheikh take zafi da raɗaɗi domin har wani duhu yake gani daurewa kawai yake don baya son ta fahimci cewa itace weakness ɗinsa, hannunsa yasa ya shafo yawon kana yace "Ki ƙara tofan yawo kiga banda abinki da hauka meye yawonki zai min?" Da sauri tace "Kai ne mahaukaci wlh bani ba mara tsoran Allah bai min matar Ubansa, aikin kawai mutum a baka Musa a ciki fir'auna, wlh na tsanaeka bana ko son ganin fuskar ka" a wannan lokacin Sheikh ji yay zcyarsa ta tsaya gaba ɗaya da harba tsayawa yawa yay kawai yana Kallonta kamar statue, da ƙyar ya samu ya fisgi Numfashinsa kana yace "U have no idea akan abinda zan maki kika ƙara dan gan tani da wata mummunar kalma, Yeah! I believe it na yarda da zcyta akan cewa ina sonki bazai taɓa daina cewa Ina sonki ba sai dai idan Numfashin Sheikh ne ya tsaya, Uhm matar uba kuma? Shi yasa naga nine wanda ya fara huda tantanin budurcinki Wheel nine kika zo da kuka akan na soki? Mace ai daman ance zuma ce ga ɗan ɗano ga harbi, amma ni ɗan ɗanonta kawai na sani har abada banga abinda zatai min naji harbinta ki sawa ranki cewa ko wuƙa kika ɗauka kika kashe Sheikh ya dawo duniyar nan bazan fasa faɗar abin yake rai na ba, _SHEIKH IMAM HAMDAN BALARABE LOVES you Zahraaah, i love You Zahraaah"_ ya ƙare maganar yana kifa kansa a ƙirjinta ya shiga sauke ajjiyar zuciya tare rungome ta tsaf a jikinsa "Kaga malam a zumi nake wlh Allah zaka sanya nai maka ihun kwarto yanzu nan na tonae asirin da kake ɓoyewa" kallon idanunta yayi kafin a hankali yace "Kada ki sake haɗa ni da kalmar kwarto wlh banda ina jin tsoran Allah da sai na karya azumin da kike mgn akai". Baki ta mur guɗa tace "eh ɗin da mene idan ba kwar...," Bai bari ta ƙarasa faɗa ba yay saurin sanya bakinsa cikin nata, sam baiyi dan jin daɗi ba bare azumin sa ya rau nana, yayi dai dan dakatar da ita, dadɗan ƙamshi bakinsa wanda tafi so fiye da komai amma a wannan karan ji tayi har wani wari yake mata, bakinsa ya zare Muryarsa na rawa yace "I love You so much Zahraaah, dan Allah kada ki zaɓi hukunta zcyata akan abinda nai maki bayin kai na bane, zyata gaf take da fashewa Zahraaah ki tausaya min ko sau ɗaya ne ina ƙaunar ki ina maki sahihiyar ƙauna, _رؤيتي كل حين أن تكوني ملكتي،_ _وأم أولادي والظاهرية كوني في حوار،_ _وسائر كلام فمي._ Ya faɗa yana ƙara rungome ya shiga fidda numfashi da sauri², soyayyarta ta gamayi masa illa a zcyata banda haka da tuni ya manta da babin rayuwarta a yau ɗin nan, amma he never give up yaci gaba da dauriya zai roƙi Ubangiji akan ya yaye masa idan kuma da alkairi Allah ya kawo masa mafita, shamfatar sa tayi ta ɗauki tare yankar hannunsa zafi da raɗaɗin da yaji yasae ya saketa da sauri yana runtsa idanunsa, bai tsaya jira jin wani abu yay waje da sauri yana riƙe da hannunsa, yin duniya Arjun yay masa amma yaƙi kulasa da ƙyar ya bari aka duba hannun kana suka huce airport not too long jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasa mai ƙarfi zucyarsa Sheikh na cikin da azabtuwa da abinda Fannah tai masa amma har abada ko da gaske zata kashesa bazai janye ƙudirinsa yana addu'ar kuma Allah ya sauketa lfy domin hakan ma wata damace ya samu da wannan tunanin jirginsu ya keta sararin samaniya... 🌚daman al'ƙawari nai dan Allah ku sani addu'a😩 zazzaɓin zamani na neman kamani idan ya kwantar dani da matsala wlh pray for me. NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:35 - 🤔🤔: Welcome back 69-70 Sheikh jirginsu ya sauka a ƙasa mai tsarki, Yayinda suka fara ibada baji ba gani, kullum Sheikh yana hanyar ka'aba yana kaiwa Allah kukansa, domin shike da ikon yaye masa dukkan damuwarsa, a kullum ya ɗura goshinsa a ƙasa addu'ar sa ta farko Allah ya sadashi da Amminsa, abu na biyu wannan babban al'amarin daya kunnu masa kai idan da alkairi tsakaninsa da Fannah Allah ya kawo masa komai cikin sauƙi, sannan Allah ya farkar da ita daga nauyayyen baccin da take, dan yana da tabbacin dukkan bala'in da ruwan rashin mutuncin da tayi masa bata cikin hankalinta, a hankalinta koda bata sonsa da gaske yasan ba zata jefesa da wannan munanan kalaman ba. Sosai ya ƙoƙarin wajan ya danne damuwarsa yaci gaba da ibada cikin dauriya da kuma jajircewa, ya barwa Allah komai fatansa ɗaya kafin ya koma 9ja Zahraaansa ta dawo cikin hayyacinta kuma zai ta addu'a bazai gaza ba. Ɓangaren Fannah ta daɗe da mantawa da rayuwar Sheikh rayuwarta take hankali kwance, ko sunansa taji an ambata tashi take tabar wajan, Barrister yin duniya yayi da Fannah akan ya kwanta da ita amma da zarar yay niyyar hakan sai yaga Fannah ta koma masa wata baƙar halitta mai ban tsoro. Mami itama a lokacin ta fahimci shigar ƙaramin ciki a tare da ita dan haka ta shirya yadda zata samu Sheikh cikin ruwan sanyi. Yau sun kai azumi na ashirin da ɗaya da Sheikh na zaune saman kujera sanye da farar Jallabiya hannunsa riƙe da Apple yana gutsira a hankali, Fareeq na zaune shima yana danna wayarsa bell ce ta fara ƙara alamar suna da baƙo kuma shike kaɗa bell ɗin, Fareeq ya miƙe tare da nufar wajan ƙofa bai tsaya jiran wani abuba ya buɗe ƙofar idanunsa suka sauka kan wani saurayi ƙyakƙyawan gaske fuskarsa cike da fara'a ya miƙawa Fareeq hannu sukai musabawa yace "Sunana Aslam Deedat, ina son ganin Sheikh Imam hamdan Balarabe kamar yadda yay min appointment jiya da muka haɗu a ka'aba" Fareeq yace "ok to bari a sanar masa ko" Aslam yace "Ok! No wahala" idanun Sheikh a rufe Fareeq ya ƙarasu yace "Yaah Sheikh kana da baƙo wai Aslam Deedat" buɗe gajiyayyun idanunsa yay tare da saukesu akan Fareeq yana son ya tuna inda yasan sunan amma abubuwan da sukai masa yawa a brain ba zai sanya ya tuna one time ba, jinjina kai yay yace "Ok yazo" juyawa Fareeq yay tare da komawa bakin ƙofar ya cewa Aslam ya shigo, farin sosai a fuskar Aslam ya shiga ciki bakinsa ɗauke da Sallama, kasa zama yay sbd kwarjini da haibar Sheikh. Sheikh kansa a ƙasa dan bai ɗago ba sbd bugun da zcyarsa take masa, sai da yaji shiru kana ya ɗaga kyawawan idanunsa zuwa ga fuskar Aslam, ba tare da yace komai ba ya nuna masa kujerar dake farcing tasa, zama Aslam yay kana yace "Barka da dare" Sheikh ya ɗauki Malt ya kai bakinsa kana ya zame yana ɗan fidda numfashi a hankali ba tare daya amsa Aslam ba ya miƙa masa tattausan hannunsa yace _" Azunnu annaka bikhair"_ shiru Aslam yay dan bai san mene Sheikh yace ba gane haka yasa Sheikh ya ɗan ɗauke kansa gefe yana mai Istigifari a ransa yace "fatan kana lfy?" Murmushi Aslam yay yace "Lfy Allhamdulillah" jinjina kai Sheikh yay yace "Ma sha Allah!" Shiru sukai gaba ɗaya Fareeq kam idan ya juya ya kallo Yayan nasa sai ya juya ya kalli Aslam sosai yake son cewa wani amma sbd abinda ya bashi mmki amma ya shanye ya bisu kawai da ido, sunkuyar da kai Aslam yay yace "Daman alfarma nake nema a wajan ka, a cikin Alfarmar da kakewa mutane" Juyawa Sheikh yay ya kalli Aslam can kuma yace "Allah ya ban iko" kai tsaye Aslam yace "Ammina ke sonka wlh, kullum tana jin tafsir ɗinka, to abun ya ban banta dana da tun sanda taga an haskaka a t.v shkknan muka rasa kanta, abinci ba taci sosai ita dai Sheikh, to mgnar Gsky ba tayi niyyar zuwa Oumara ba amma tunda taji kace zaka Oumara shkknan ta cewar Papi itama zata dan dai kawi tazo ta ganka, dan Allah ɗan uwa Yayana kai mana alfarma ko zuwa ne Ammi tayi ko gaisa" tunda ya fara mgn Sheikh ya lumshe idanunsa yana sauraran mgnar Aslam kafin buɗe ido yace "Kada ka damu, kaban number wayarta zan kirata, yanzu babu wani lokaci amma nai maka al'ƙawarin da zarar ba koma 9ja akwai inda zani so daga nan zanzo har gida na gaisheta" sosai Aslam yay farin ciki yace "Ngd Sosai Allah ya ƙara girma Allah ya baka abinda kake so" miƙewa Sheikh yay yana faɗin "We Are family now kada ka damu" Aslam ya miƙe zai miƙawa Sheikh hannu shi Kuma Sheikh ya jawosa jikinsa tare da rungomesa ya masa gaisuwar larabawa" daga sukai Sallama Aslam ya tafi gida cike da farin ciki. Mama kolo zau ne ita da Ya Falta suna ta aikin miyar idi, Baba Baa'na ya shigo hannunsa riƙe da ledoji manya, da Sauri Yana ta miƙe ta amshi ledar tace "Allah ya saka da alkairi Baba wannan kaji haka" murmushi Baba Baa'na yay yace "wlh wani bawan Allah yaban hadda Zakka fa" Mama kolo tace "Ma sha Allah ya jikin Kawo Madu?" Yace "da sauƙi wlh,daman ina son muyi mgn dake" kallonsa tayi tace "wacce magana ce wannan da baza a barta sai bayan Sallah ba?" girgiza kai Baba Baa'na yay yace "kusan dole ce ji nake kamar akwai wani babban abu da zai faru dani" miƙewa tayi tace "ka sawa ranka nutsuwa kayi hqr zuwa bayan idi hankali ya kwanta sai muyi mgnar" kallanta kawai yay sai bai ce komai ba ya kalli Ya Falta yace "Ga mgani na amso ɗauki ki kaiwa Kawo Madu jikin nasa sai addu'a ciwon ciki Lokaci guda" miƙewa Ya Falta tayi jiki a sanyaye tace "In sha Allah! Allah zai bashi Lfy" ta faɗa tana ficewa daga gidan riƙe da maganin, tana zuwa gidan Kawo Madu ta samu matarsa na kuka sbd yanayin jikin nasa, kasa mgn tayi kawai ta bisa da ido. Granny ce riƙe da magani tace "Maza shaa maganin mugun ji da mugun gani kenan, wannan cikin ƙalau zaki haifawa Barista shi" Ya tsuna fuska Fannah tayi tai wani fresh tai kyau sosai fatar jikinta ta murje ga girman jiki data ƙara ta zama babbar mace, brest da hips ɗinta sun ƙara girma sosai, tana sanye da wata red gwon mai kyau wacce ta haskata, shan ruwan ta kenan tayi sallar Isshā da ashan, girgiza kai tayi tace "Granny nace nifa ba wani ciki gare ni" haɓa Granny ta riƙe tace "Mahammadur Rasulullah (S.A.W) ashe maƙaryaciyya na zama bani da Lfy, to banyi gantalewa da zan faɗi magana ace ba haka ba, ga nonowa nan sunyi saɓa² alamun shayarwa su nuna jikin ki? Maza amshi kisha tun ranki bai ɓaci ba?" Karɓa tayi tana shagwaɓe fuska idanunta ya cika da ƙwalla duk ta zama wata shagwaɓaɓɓiyya, "To basai kici kanki ba? Nidai magani ne dole kisha a to! Wa kike dashi a nan ɗin banda ni kuma?" Badan tasu ba ta amshi maganin ta fara sha, washe baki Granny tayi tace "Hamdalan kasiran ƴar nan ko ke fa, ai shiyasa jiya da nai waya da Imamu nace ya haɗu min kayan baby wlh, shima na lura yana son cikin" wani tiririn baƙin ciki da damuwa ne ya tawowa Fannah ita gaba ɗaya ta manta da wani Sheikh kamar yadda bata yadda da cikin jikinta ba, jug ɗin maganin ta saki tare da miƙe tai part ɗinta zcyarta a cunkoshe, Bahaiyya ce tace "kema Granny da wahalar da kai tunda bata son let her go" miƙewa Granny tai tace "Uwarki ce wahalalliya kaji min fitsararriyar yarinya bari naje wajan uwar taki naji idan ita take daki kimin rashin ɗa'a?" Tana faɗin haka ta nufi part ɗin Mami a gaban dressing mirror ta sameta tana tauna ƙanƙara, baki Granny ta saki tace "Ke kuma masifar data sameki kenan ko? Meye shan ƙanƙara kuma?" Kallonta Mami tayi tace "Granny bake na nunawa Result ɗina cewa ina juna biyu ba? Ƙilan shike sani ci?" "Ayyo! Naga alama shi cikin na Barista ne ashe" da mmki Mami ta kalli Granny sai kawai tai Murmushi tace "Soon za kiji mai shi" taɓe baki Granny kana ta fice daga part ɗin tana sababi. Fannah tsaye take gaban mirror tana ganin yadda cikin ƙaramin lokaci ta zama Babbar mace ta kyau na ban mamaki, hankali kwance take gudanar da rayuwar amma yau tuna mata da sunan Sheikh da akai taji ranta duk a ɓace, tsana mafi muni ta kewa Sheikh wacce bata san dalilin yin hakan ba, a hankali kuma ta sanya hannunta saman lafaffan cikinta tace "Tayaya zan samu ciki daga yin abu sai ɗaya?" Wata zyar tace _"Rabo mana Fannah_" dai kuma ta girgiza kai tace "It's impossible! Wlh dana haifi cikin sheƙe gwamma ban zo duniyar ba baki ɗaya, daman yay amfani kenan dani wajan cimma burinsa zan shayar dashi mmki wlh zai san cewa mace goba ce tunda shi ɗan akuya ne ya saba bin mata, haka kuma banyi mmki ba daya nemi matar Ubansa ƙilan shima ta haka yazo Duniyar" ta faɗa tana sakin kuka wanda bata san dalilin yin nasa ba, tunanin abinda Sheikh yay mata har take jin zafin sa ta duba taga babu kawai ta tsane sa ne, ya ilahi ita inane zata sanya kanta, Tabbas akaci gaba da ambatar sunansa baƙin cikin haka zai iya ajalinta baki ɗaya, saman bed ta faɗa tana sauke numfashi data rufe ido cikakkiyar surarsa mai kyau da tsari ce take bai yana a cikin idanunta, kuka ta ƙara saki tace "i hate him! I hate you Sheikh na tsanaeka wlh" Uncle Sham ne ya kalli Matarsa Anut Amina kana yaci gaba da Rubutun da yake a diary ɗinsa, bayan ya gama ya miƙe tsaye yace "Maman Huda let's talk pls" ɗan kallonsa tayi tace "Abban Huda, bari na bawa Huda magani to" jinjina kai yayi sai kuma ya koma ya zauna, Anut Amina kuma ta shige cikin ɗaki, wayarsa ya ɗaga ya kira Arjun, ba jimawa Arjun ya ɗauka suka gaisa Uncle Sham yace "Mohd yaushe Imame yace maka zai dawo?" Daga can ɓangaren yace "Uncle wlh bai faɗa ba" Uncle Sham yace "Ok naga jibi idi _that's why i am asked you"_ Arjun ya kwantar da kansa a shoulder Aliyah yace "Hkne banyi tunanin zai jima haka ba Nima" miƙewa tsaye Uncle Sham yay sbd baccin daya keji yace "Ok! Ba damuwa Allah ya dawo dashi Lfy" Arjun ya amsa da _Ameen_ kana suka ajjiye kiran. Uncle Sham na shiga bedroom ɗinsa ya huce bathroom ya watsa ruwa kana yay shirin bacci ya zauna ya nata jiran Anut Amina amma shiru, kwanciya yay yana addu'a Allah ya kaimu sayi mgnar. Sheikh na tsaye sanye da farar Jallabiya misalin ƙarfe 12:30 sbd yau shine zai jaa sallar _TAHAJJI_ a babban masallacin makka dake jidda, yay kyau sosai ya rufe kansa da hirami sbd ɗan sanyin dake busawa da alama kuma yau rana ce mai muhimmanci ana sanya ran ganin dare mafi suyiwa wanda kowa yake fata da burin ya gansa wato _DAREN LAILLATUN KHADDRI_ gyara tsaiwarsa yay jin Fareeq shiru bai fito ba yasa walking slowly ya fara takawa zuwa bedroom ɗinsa kwance a samesa yana ta bacci cike da jin daɗi, lumshe idanunsa kana ya nufi wajan fridge ya ɗauki bottle water mai sanyi ya kwarara wa Fareeq, a firgice ya farka ya buɗe baki zai mgn yaga Sheikh tsaye ya haɗe hannayensa a ƙirji ya ɗura masa gajiyayyun idanunsa wanda kullum suke a lumshe, juyawa yay ya fara tafiya tare da faɗin "Get down my friend" yana faɗin haka ya fice, bacci cike idanun Fareeq haka yaje ya watsa ruwa ya ɗaura Alwala kana ya sanya jallabiya irin ta Sheikh, cike da nutsuwa a jere suka nufi masallacin. Sallar raka'a goma sha ɗaya Sheikh yaja bai idar ba sai wajan 3:45 kana ya shiga kwararo addu'a wanda da yawa sai da suka zubar da ƙwalla, addu'a Sheikh Babu kalar wacce bai ba, yay addu'a tsakaninsa da Fannah sau ba adadi yana da tabbacin yadda zucyarsa ke azabtar dashi da soyayyar Zahraaansa abu ne mai wuya ace ita ba alkairi bace a garesa. Bayan an sallame mutane da yawa sun fita shikam tanƙwashe ƙafafuwansa yay tare da buɗe Alkur'ani ganin hakan yasa Fareeq shima ya buɗe. Daga can ɓangaren Governor Deedat ne yake ta sakin ajjiyar zuciya idanunsa akan Sheikh wanda tunda ya shigo masallacin yake kallonsa. miƙewa yay tsaye a hankali ya fara tafiya ya tsaya dai-dai kan Sheikh harya buɗe baki zai mgn sai kawai ya juya da sassarfa sbd sarawar da kansa yay masa. Yau ta kama jajiberin sallah ƙarama tun safe al'ummar gari suke ta kai koma, kowa yana Shirin zuwan ƙaramar sallah,masu amsar ɗinki mayi masu siyo kajin miya nayi wasu kuma suna ta siyan kayan miya. Tun safe Granny ta kira wasu mata da zasu tayasu aikin Sallah dan haka cikin nutsuwa suka fara aiki sbd kada lokaci ya ƙure masu. Bayan ansha ruwa Misalin 10:30 na dare Fannah na ɗakinta daga ita sai 3gauther sai half vest a jikinta ta sanyawa gashin kanta ribbon tana kwance saman bed time to time ya kanji faɗuwar gaba. Barrister ne ya fito daga part ɗinsa waya maƙale a kunnansa yace "Haba Alhaji Kamal kafa san ko waye Barrister, wlh bazan ɓata shekaru na a banza ba, dan haka watch and see what will going to happen" Alhj Kamal yay dry yace "Wlh ina tausaya maka, idan baka tsaya ka fahimci abinda yake gabanka da irin wutar daza ta tashi to zaka kwana ciki" Barrister yace "Uhm kai ka sani ni nasan har gobe babu wanda ya san true colour ɗina" jinjina kai Alhj Kamal yay yace "Ina fatan haka sai goben" daga nan sallama sukai kai tsaye Barrister ya nufi part ɗin Fannah tana kwance ta lumshe idanunta farar fatar ta sai ƙyalli, a hankali ta buɗe idanunta sbd ƙarar Kofar da taji da sauri ta miƙe sbd ganin Barrister tsaye a kanta idanunsa sunyi jajir, kanta ta ɗauke shi kuma ya sakar mata Murmushi tare da ƙarasawa inda take tsaye yana zuwa yakai hannunsa zai riƙeta tayi saurin yin baya, tsayawa yay yana Kallonta cikin damuwa kana ya kalli cikinta inda gudan jinin sa ke ciki yace "Fatima kin san how long na kasance babu ke? Bana son nai maki ba dai-dai sbd jinina dake jikinki, amma ki sani a yau bazan bar ɗakin nan ba sai na samu haƙƙi na" kallonsa tayi zcyarta na bugawa ba tare da tace komai ba, idanunsa a rufe banda wutar sonta babu abinda yake ɗawainiya dashi, da sauri ya ƙara matsawa inda take yace "Nayi kewarki sosai nayi rashin ki rabu na dake tun first night ɗin mu so allow me to enjoy my dear Fatima" ya faɗa yana ƙara riƙota da ƙarfi wata gigitacciyyar ƙara ta saki lokacin da Barrister ya haɗata da jikinsa ya fara ƙoƙarin zame vest ɗin data rufe kyawawan brest ɗinta masu wanda suka ƙara girma gwanin sha'awa, idanun Barrister har wani ruwa yake kawowa baya gani da jin komai sai Fannah dake gabansa, duk yadda tasu kwacewa kasawa tayi sbd ƙarfin Namiji dana mace ba ɗaya bane bai rabu da ita ba sai da ya samu nasarar zame vest ɗin jikinta ta ƙara sakin ƙara tare da sanya duka hannayenta ta rufe ƙirjinta dasu, wani lalataccen murmushi yay lokacin da idanunsa suka sauka akan matasan tsayayyun brest ɗinta, wanda a zahiri wannan shi ne gani na farko da yay masu amma anasa ƙaramin tunanin ya ɗauka ya daɗe da sanin su, jikinsa har rawa yake da dukkan ƙarfinsa yasa hannu ya zare nata hannun tare mannata da jikin bango slowly ya kai bakinsa saitin nippy ɗinta yana gaf da ɗurawa yaji an turo ƙofar da wani irin ƙarfi, da sauri ya ɗaga kansa wanda ya gani ba ƙaramin gigitasa yay ba, amma meye nasa da zai shigo masa ɗakin mata? Fannah najin Barrister ya saketa ga Kuma tsaiwar mutum da taji ko kallan gabanta ba tayi idanunta a rufe da gudu ta ƙara inda mutumin yake tana zuwa ta shige jikinsa tare da rungomesa taki wani gigitaccen kuka jikinta duk rawa yake, da sauri Sheikh ya gyara tsaiwarsa sbd jin kamar zai yadda dashi sbd yadda ta faɗa jikinsa ba zato. Idanunsa da suke lumshe ya ware tare da sauke su akanta da sauri kuma ya ƙara runtsa idanunsa bai san lokacin daya ƙara shigar da ita jikinsa ba yay covering ɗinta da faffaɗan ƙirjinsa, kana ya sauke kallonsa akan Barrister suka shiga kallon kallo! Mmki ya hana Barrister cewa komai dan haka yabi ta gefen Sheikh ya fita a bunsa yana fita ya samu Fareeq tsaye a Parlo yana shan fresh milk. Ganin yadda take kuka sosai tana jijjagasa yasa a hankali ya saki wata wahalalliyar ajjiyar zcy yana mai ɗan taune leɓansa tare fesar da iska daga cikin bakinsa kafin ya daidaita tattausan laɓɓansa a saitin kunnanta cikin zazzaƙar muryarsa yace _"It's okay Fatima Zahraaah, I'm here nothing will happen to you je..wel"_ ya faɗa yana rungome ta a jikinsa, cak ta tsaya da kukan zcyarta na harbawa da ƙarfin gaske sbd Muryarsa daya daki kunnanta da sauri ta ɗaga kanta ta kallesa taci Sa'a idannunsu ya sarke cikin na juna. _Wai mene haka ne😩why labarin yake taja haka ne?? Gashi na kusa kai book 2 amma labarin da ɗan saura idan ya kaini book 3 akwai sabon payment🤕🤫 Ina gdy sosai da addu'oin ku Allah yabar ƙauna jiki gashi da sauƙi_ SIRRIN MU isn't free book is for sale contact to subscribe 08119237616. NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:36 - 🤔🤔: When Destiny Call 71&72 Ƙoƙarin kwace jikinta Fannah tayi sbd wani baƙin ciki daya kamata, da ace tun shigowar sa tasan cewa Sheikh ne babu dalilin da zai sanya taje inda yake bare ta nemi taimako daga wajansa, idan akwai Mutumin da tafi tsana a duniya bai huce Sheikh ba, ta gwamma ce Barrister ya kwanta da ita da ace ta raɓo inda Sheikh yake, _"Goodness"_ ta faɗa a bayyane tare da saurin maƙale jikin Sheikh lokacin da taji saukar lallausan softness hands ɗinsa a ƙasan mararta, tuni jikin Fannah ya ɗauri rawa take ta turesa amma babu dama, cikin ƙasa da murya dai-dai kunanta Sheikh yace _"اللهم رب كما انعمت فزدنا"_ _(Ya uban giji kamar yadda kayimin wannan ni imar kaqaramana)_ ya ƙare maganar yana tattare rigar ta sama a hankali ya dinga shafa cikinta yana jin yadda soyayyar unborn child ɗinsa ke ratsa jinin jikinsa, Kuka ta sanya masa ganin ta kasa kwatar kanta, a hankali ya ware hannayenta data dungole su a ƙirjinta yay saurin haɗata da faffaɗan ƙirjinsa wanda ya ɗan ƙara faɗi da cikar suma, tsaf ya rungome ta yana jin yadda zyrsa tai kewar sahibar tasa, da sauri Fannah ta tura fuskarta tsakiyar ƙirjinta sbd softness lips ɗin Sheikh da taji a ramin cibiyar ta a hankali ya shiga hura mata iska yana lumshe idanunsa, wani ƙyakƙyawan murmushi ya saki wanda ya haddasa lomawar dimples ɗinsa da bayyanar teeths gave ɗinsa siririya mai kyau da tsari, sai da ya tabbatar jikinta ya saki kana ya ware laɓɓansa yay kissing cibiyar ta tare da tsotsa kaɗan, gaba ɗaya jikin Fannah ya saki masifa ce fall ranta wacce tayi niyyar sauke masa amma yadda tai weak tasan ko buɗe baki ba zata iya ba, gaba ɗaya yabi ta suka zube a saman bed yana ɗan fidda numfashi tare da sexcy sounds mara sauti sosai. Cikin daddaɗar muryarsa mai cike da nutsuwa da kamewa yace _"Ya rabbi ka karemin gudan jinina, Ya Ubangiji na ka kulamin dashi domin rayuwarsa a wajanka take, Ya Allah ka sanya masa hqr da tawassali tun yana cikin mahaifiyarsa! Ya Allah ka sanya masa nutsuwa da dangana, Allah ka bashi sa'ar rayuwa, Ya Allah ka sanya yazo duniya bisa Aminci da Lfy! Allah ka kula min da gunan jini na"_ ya ƙare maganar yana kifa fuskarsa gaba ɗaya a cikin nata yana jin yadda zcyarsa ke halbawa, yana sonta yana son jin ɗumin jikinta, Ita yake buƙata gaba ɗaya yana son yay sharing dukkan wani feelings ɗinta gareta, amma sam bai shirya jin maƙaƙen maganganun da zata faɗa masa ba, ba komai zyrsa a yanzu zata ɗauka ba, mutsi ta fara wanda yasa ya sauke Ɓoyayyiyar ajjiyar zcy tare da zare jikinsa daga nata, baya taji zata faɗi sbd jirin daya ɗebe ta yay saurin riƙeta da sauri ta boge hannunsa idanunta fal ƙwalla tace "Azzalumi! macuci! Maha'inci! Butulu! Maci Amana in sha Allah sai Allah ya rama min abinda kayi min me gemun banza kawai" runtse idanunta yay yana jin duk wata mgnarta yadda take dokan ƙahon zcyarsa, rinannun idanunsa ya ɗaga tare sauke su a kanta, fesar da numfashi yay kana yaja ƙwantaccen gashin fuskarsa _(saje/gemu)_ fuskarsa na fidda annuri dan bai bari taga ɓacin ransa ba, cikin kamewa da nutsuwa ya isa gabanta yana ƙare mata kallo from head to toe yace _"Fatima Zahraaah! Ina sonki gaba ɗaya, And i like ur attitude! Ko zaki uwata da ban san inda take ba bazan taɓa cewa bana sonki, And kin san me all abubuwan nan da kike min wlh ko a ƙafar Sheikh da zaki gane da kin ɗauki wata hanyar amma komai naki birgeni yake, kuma duk sanda kika ƙara yimin mgn makamancin wannan baki san me zan maki ba"_ wata harara ta zabga masa tace "An gaya maka gurɓatattun mgnar ka zai sauya ra'ayin Fannah ne? Wlh ba'a haifi wanda ya isa ya sani zama dakai ba, ɗan isa irinka kwarto kamar...," Bata ƙarasa faɗa ba taji yay mata wata cafka tare da haɗata da jikinsa, bada rawa babu Abinda jikinsa keyi ya ƙwaƙwaƙumeta sosai kamar zai ɓalla mata ƙashin baya har sai data saki ƙara, idanunsa yay jajirrr jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa, yasan bazai taɓa iya dokan ta ba amma hakan da yake mata kaɗai yasan purneshiment ne, ƙarar data sake yi ne yasa ya sassauta riƙon sbd gudan jinin sa dake cikinta, ɗago kansa yay kana yay copping face ɗinsu bakin sa na rawa yace "Why? _Why Zahraaah what i have done to you"_ idanunta cikin nasa tace "I hate you Imam hamdan Balarabe na tsaneka Sheikh" ware manyan idanunsa yay waje yace _"Goodness!_ Ni Malaminki kika tsana?" Kai tsaye tace "Malamina Uba na ne?" Murmushin ƙarfin hali yay yace "Na maki al'ƙawarin nan da 1week wannan bakin idan ance ya furta kalmar tsana ga Sheikh bazai iya ba ke da kanki za kiji kunyar abinda kika aikata" murguɗa masa baki tayi ya buɗe baki zatai magana yay saurin sanya mata Tattausan laɓɓansa wanda suke fidda ƙamshi a cikin bakinta a zafafe ya fara bata wani fitananniyar sumbata wacce ita kaɗai zaiwa mutum nuni da yadda Sheikh Imam hamdan Balarabe yay missed Zahraaansa a lot missed mai yawan gaske, har wani cizon tongue ɗinta yake, kaf yawon bakinta sai da ya zuƙesu tass bakinta banda zafi da zugi babu abinda yake ga wani irin abu da yake mata yawo a jiki, ganin yana neman e zaucewa da huce ƙa'ida yay saurin sakinta idanunsa a rufe yana rarraba hanya ya fice daga cikin bedroom ɗin Allah ya taimaketa duk babu kowa a parlo. yana fita Fannah ta faɗa saman bed ta rushe da kuka tana jawa Sheikh Allah ya isa, dan ya tasu mata da wani azababban feelings wanda yake damunta da alama cikin jikinta ya ƙara mata son Namiji, miƙewa tayi tsaye tana goge hawayen fuskarta kana ta nufi bathroom yana duba pad ɗin jikinta taga farin ruwa da sauri ta yar tana ƙara jin tsanar Sheikh na nunkuwa a ranta, da haka tai wanka ta sauya kaya kana ta faɗa gado wani wahalallan bacci yay gaba da ita da alama baya rasa na saba da ɗumin jikin Sheikh da taji. Sheikh kam kasa bacci yay yadda yaga rana haka yaga dare. Washe gari ta kama idin ƙaramar Sallah Sheikh ya shirya cikin wata bugaggiyyar Gezner fara tass sai ƙyalli take, ko ina ya juya ƙamshi ke tashi a jikinsa, bakinsa sai mutsi yake yana faɗin _"Allahu Akbar³! La'ilaha illallahu Allahu Akbar walillahil ham"_ a haka har ya isa Mosque ya ja Sallah raka'a biyu kana yay huɗu ba, daga nan gidan su Arjun ya huce ya gaida Umma, Arjun ya kalli Sheikh yace "Muje muci Abinci Madam ta gama nasan ba babbar Sallah bace bare kace sai kaci kayan ciki" taɓe baki Sheikh yay kamar bazai magana ba sai kuma yace "har wani abincin kirki matar taka ta iya?" Dry Arjun yay yace "Ni bazan ce komai ba, amma yau duk abinka sai ka shiga ciki ai yau daman ranar ziyara ce" kwaɓe fuska Sheikh yay yana lumshe idanunsa ba tare da yace komai, Murmushi kawai Arjun yay tare da kama hannun Sheikh ya fara jansa zuwa part ɗinsa, Aliyah na zaune tasha ado cikin wata atamfa golden mai haske, tana ganin Sheikh yaja vail ta rufe jikinta sbd tasan halin Sheikh yanzu zaiƙi shigowa, Zama yay yana ɗauke idanunsa sbd Arjun daya bawa matarsa side hug yana sakar mata Murmushi yace "Matar Kinyi kyau har ba'a mgn" nuni tayi masa da Sheikh yace "ke ƙyalle wannan ya fini rashin ta ido akan mace" ƙwace jikinta tayi tace "Buddy barka da dawowa daga ƙasa mai tsarki, anyi sallah Lfy?" Ba tare kalleta ba yace _"Taƙƙabbalallahu Minna wahh minkii"_ jinjina girman jan ajin Sheikh tayi wanda ya riƙa ya zama ɗabi'arsa, miƙewa tayi ta nufi kitchen tana shiga wayar Arjun ta ɗauki ƙara ganin sunan Uncle Sham yasa Arjun yace "Wai Buddy ina wayarka meye amfaninta?" "Uhm" kawai Sheikh yace Arjun kuma yada wayar a handsfree Muryar Uncle Sham ta cika wajan inda yake faɗin "Imam ina son ganinka yanzu" shiru Sheikh yay kana ya gyara zamansa yace "In sha Allah! Uncle zan zo" Uncle Sham da yake kallon matarsa data miƙe tsaye yace "Mgna ce mai muhimmanci kada kai wasa" Jinjina kai Sheikh yay yace "In sha Allah Uncle" yana faɗin haka yay Shiru tare da rufe idanunsa, Aliyah ce ta ƙarasu cikin Parlon da babban tray, wanda yake ɗauke da funkaso da miyar agoshi miyar taji naman kaza ga sinasir da masa, sai soyayyan naman kaza da farfesun ƙafar saniyya. Barrister ne tare da Alhj Kamal a parlon baƙin sa suna tattaunawa, a hankali aka Turo ƙofar Mami ce ɗauke da basket ta shirya abinci a ciki satar kallon Alhj Kamal tayi shima ya kalleta sai kuma suka ɗauke kansu, ajjiyewa tayi tare da zama tace "A'a yau Alhj Kamal a gari gsky baka da kirki yaushe rabon dana ganka?" Dry yay yace "Komai kamawa take yanzu ba gashi nazo sanadin Sallah ba?" Tace "Haka ne! Anyi Sallah lfy ya iyali?" Yace "Allahamdulillah" daga haka ta miƙe tana sauke ajjiyar zcy, wayar Barrister ta fara ƙara ya ɗauka tare dayin Sallama, Shiru yay sai kuma yace "Subuhanallah! Yaushe ne?" Shiru yay yana sauraran abinda ake faɗa kana yace "Ok ba matsala zan biyo bayanku" yana faɗin hakan ya kashe wayar tana sakin dry. Uncle sham ya kalli Anut Amina yace "Maman Huda mgn ce dani, kinƙi bani hankali ina jin idan ban sauke nauyin abinda yake kaina ba kamar nayi ba dai-dai ba ne" kallonsa tayi tace "Haba Abban Huda, bari dai nazo naji mgnar nan" ta faɗa tana nufar kitchen shiru Uncle Sham yay abin duniya duk yay masa zafi ga Sheikh har yanzu mai zo ba, wayarsa tai ƙara ya ɗauka ganin sunan Baba Baa'na yasa yay picking yana fidda murmushi Baba Baa'na ya kalli ɗan uwansa dake suma ya tabbatar yau jikin kawu Madu yau sai abinda hali yay yace "Shamsudeen! Jikin Kawo Madu ya tashi sai suma yake gashi yana ta kiran sunan ka" da sauri Uncle Sham ya miƙe tare da ɗaukan key ɗin wayarsa yana faɗin "Subuhanallah! Gani nan zanzo yanzu bari na siyi online ticket yanzu" Anut Amina tace "A'a Lfy dai?" Kasa ce mata komai yay sai rungome ta yay Murya can ƙasa yace "I love You! Ki kula da Huda" bai tsaya jiran me zata ce yay waje yana kiran driver. Sheikh tunda ya samu yaci Funkaso guda biyu wani bacci yay gaba dashi a saman sofa abinda bai taɓa yi ba kenan bacci da Zhur. Sai bayan asar ya tashe bayan sunyi Sallah suka nufi gidan Uncle Sham Anut Amina ta tabbatar masu Uncle Sham ya fita itama gata san inda ya nufa ba. Kai tsaye gida ya nufa yana zuwa ba kowa a Parlo kai tsaye part ɗinsa ya shige yana zuwa ya samu Mami zaune a saman kujera tana sharɓar tana ganinsa ta miƙe tsaye tare da faɗin "My Sweet Imam na shiga uku" ta faɗa tana faɗawa jikinsa. 22/10/2021, 10:36 - 🤔🤔: When All Is Gone 73-74 Da sauri Sheikh ya zare Mami daga jikinsa yana mata kallon baki da hankali, sai kuma ya sauke Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya yana jiran yaji mene kuma zata faɗa masa nan gaba, Mami kuka ta saki tace "My Sweet Imam wlh mahaifinka baya tsoran Allah! Baya kulawa da haƙƙin Aure,Nima mutum ce kamar kowa amma bai damu da halin da nake ciki ba bai damuwa daya zauna dani ya kasance dani ba" sai kuma ta ƙara sanya kuka tana nufarsa ya ƙara ja baya still shanyayyun idanunsa na kanta, tace "Dan Allah My Sweet Imam ka taimaki rayuwata help me, ka taimaki mahaifiyar ji nake kamar zan bar duniyar" jajayen idanunsa ya juya mata wanda ya sanya Mami ta ƙara zaucewa tama rasa mene zatai, Yau Sheikh ya zama na Musamman ƙaunarsa ta musamman ce take yawo a jinin jikinta, musamman yanzu da yake yawo bisa ƙafafuwansa sai cikar halittar sa tafi fitowa tare da bayyana! Kasa mgn Sheikh yay sai Kallonta da yake da ido, Mami ta zube saman e ta riƙe ƙafafuwansa tace "Dan Allah My Sweet Imam ka taimaki Maminka, kai kawai nake dashi a yanzu kai ne kawai zaka iya bani abinda nake buƙata" da ƙyar ya samu ya fisgi Numfashinsa tare da buɗe daradaran idanunsa waje cikin nutsuwa da kamewa yace "Me kike so? Me Abba yay maki?" Ya faɗa yana lumshe idanunsa jine haka yasae Mami Miƙewa tsaye ta tsaya daf da Sheikh idanunta fess cikin nasa cike da soyayyarsa tace "Sweet Mahaifinka na daɗe rabon dana kasance dashi! Ina buƙatar Namiji yau ɗaya ka cikamin burina ka ɗauke min rashin mijina kuma mahaifinka,ka maye min gurbinsa pls Sheyykh" ta faɗa tana ƙara matsawa jikinsa, with much surprise Sheikh ya dinga kallon Mami yana son gasgata zan canta amma maganganun ta sun masa nauyi a kunne dama ƙwaƙwalwa, cikin rashin fahimta yace _"Pardon?"_ Murmushi ta saki tace "Haba sweet na! Kamar ba ɗan zamani ba kaga abinda nake nufi" ta faɗa tana ƙoƙarin rungomesa da sauri yaja baya yana zare idanunsa yace "kai! What? Ni kike tunanin zan aikata hakan God forbid!" Ya faɗa tana taune leɓansa, cikin dakiya tace "Eh! Nasan kaima kana buƙata shekarunka sukai kai tarayya da mace, na maka al'ƙawarin wannan zai zama *SIRRIN MU* our secret bazan taɓa bari kowa ya sani ba yau ɗaya" ta ƙare maganar taja shafa fuskarsa zuwa jajayen laɓɓansa, iska ya fesar kafin ya ɗan buɗe baki yace "Yasubuhanallah! Da matar uban nawa? Zina mafi muni? Da wannan ranar gwamma ba'a haifi Imam ba" soyayyarsa ta rufe mata ido tace "Wlh Sheikh saika kwanta dani, kasan how long dana kasance ina mafarkin samunka? Dan Allah kada kace a'a bazan iya hqr da kai" fiddo idanunsa waje yay yace "To fyaɗe zaki min kenan ko?" Da sauri tace "Wlh indai zaka tsaya" hannunsa ya harɗe yana ɗan sakin murmushi tace "ok go ahead" cikin sauri ta ƙarasu wajansa tana ƙoƙarin rungome yay saurin zare hannunsa ya zabga mata wani ƙyakƙyawan mari wanda ya kusa zata zauce tayi baya zata faɗi ya riƙeta yace "Nasan ne nake, koda ni ɗan iska ne na gwamma ce naje waje na nema da kuɗi dana kwana da matar Ubana, ki ɗauka na taɓa aikata hakan to wannan ƙaddara ce daga mai duka wanda babu wanda ya isa ya kaucewa ƙaddarar sa, dan haka ina jan kunanki tun ina kallonki da raguwar mutunci ki fice ki ban waje" kuka ta saki sbd masifar dake damunta duk abinda Sheikh yake faɗa ba abinda ta gane saima kunnuwanta da suke jiye mata wasu kalamai dana ban, cikin zafin nama ta tashi ta faɗa jikinsa tare da qanqamesa ta shiga ƙoƙarin zura hannunta a wani keɓantaccen shashe da sauri yay ball da ita tare dasa hannu ya jata zuwa bakin ƙofar Parlon sa yana fidda ta yasa key kana ya jingina da jikin ƙofar yana fesar da numfashi tare runtsa idanunsa wanda ya kejin sunyi masa nauyi ga wani zafi da suke masa. A hankali yaja jikinsa zuwa cikin bathroom yana jin wata kasala na shigarsa abubuwa da yawa sun masa yawa yama rasa wanne kalar tunani ya dace yayi, bayan ya watsa ruwa ya sanya Armless da 3gauther kana ya ɗauki ruwan zam², da gayan magarya ya buɗe ruwan tare da kafa bakinsa ciki ya shiga karanta sururin karya sihiri, sai da ya gama kana ya jijjiga tare da ajjiyewa gefe guda yana jiran ya jigo yaje har inda take ya ɗura mata idan taƙi sha. Fannah na kwance ta kasa cin komai sai rarraba idanu take ko mutsin kirki ba tayi ta zama kamar wata statue, wayar tace tayi ƙara sunan Ya Falta taga yana yawo da sauri ta ɗaga tare da mannawa a kunanta, daga can ɓangaren Ya Falta tace "Autar Mama kina lfy" kwaɓe fuska tayi tace "Ya Falta wlh duk a tsorace nake" Shiru Ya Falta tayi sai da Fannah tace "Lfy wai? Meke faruwa gaba ɗaya bni da nutsuwa dan Allah mene?" Kasa magana Ya Falta tayi sai kawai ta kashe wayar tare da riƙe Yana suka shiga rera kuka, baki da hanci Fannah ta saki ta shiga juyawa wayar ta kasa fahimtar komai bare da kirasu, saɓanin hakan ba sai kawai ta kashe wayar baki ɗaya. Uncle Sham na sauka a airport ya ɗauki mai taxci zuwa unguwar su Kawo Madu basu daɗe a hanya ba suka ƙarasa, bai ganin nawa ya bawa mai taxci ɗin ba ya nufi cikin gidan jikinsa na rawa duk da ƙoƙarin danne damuwarsa da yayi, yana shiga a tsakar gidan ya samu Baba Baa'na da Mama kolo sai matar Kawo Madu dake rusar kuka, dubansa yakai wajan Kawo Madu da yake ta faman suma an rasa mai yi masa komai, da damuwa a fuskar Uncle Sham yace "Yaya akai aka barshi a gida bayan yana cikin wannan halin?" Baba Baa'na yana share zufar yace "Wlh yaƙi bari ko taɓa shi ayi bare har akai sa wani asibiti, yace kai kawai yake son gani" Uncle Sham ya miƙe tsaye yace "Yanzu ganie shi kuma bai san inda kansa yake ba" Baba Baa'na yace "meye abinyi to?" Kai tsaye Uncle Sham yace "A samu mai taxci yanzu mu huce asibiti" Baba Baa'na ya miƙe kana ya kalli Mama kolo yace "Muje ina son mgn dake" Uncle Sham yay gyaran yace "Time is not our side, mu fara abinda yake gabanmu i think is better" Baba Baa'na yace "hkne bari naje muga" wayarsa Uncle Sham ya ɗauka ya shiga kiran Number Sheikh wacce Arjun ya tura masa amma baya ɗauka sai ringing take, tsaki Uncle ya sauke kana ya kira ta Arjun ya jita a kashe, Message ya shigayiwa Arjun da sauri kana ya tura yana gamawa ya cire sim ɗin ya sanya a cikin aljihun sa, wayar kuma ya ajjiye saman window. Baba Baa'na yana fita ya nufi Babban titi ya daɗe tsaye kafin ya samu taxci ya shiga suka nufi unguwar da suke da zama, suna tafe amma tunani ne fal ransa, a wannan karan babu wacce take ransa kuma ta tsaya masa irin Mamansa _(FANNAH)_ tunaninta kullum yake damunsa, musamman da yake yawan mafarkinta tana cikin wani hali, dafe kansa yay ya shiga kiran sunan Allah yana jin kansa nayi masa nauyi a haka suka ƙarasa bakin ƙofar gidan, yana shiga suka kana Kawo Madu tare da sanyasa cikin mota, matarsa tace zata sukace a'a ta zauna, juyawa tayi sai kuma ta dawo da sauri tana riƙe hannun Kawo Madu ta saki kuka addu'ar da take son yi masa ta gagara faɗin komai. Uncle Sham a gaba sai Kawo Madu da Baba Baa'na a baya a haka suka ɗauki hanyar zuwa babban prvt hospital. A can cikin jejin Sambisa Tuɓe ne kwance cikin hali na rashin lafiya ko lafcecen hannunsa ya kasa ɗagawa sbd yadda ya kejin zafi da raɗaɗin ciwon na shigarsa, Tijama da jikinta ya fara janye wa ta kalli Tuɓe tace "Yakai jikana, ka sani cewa idan har haka tashi ba ka taimaki wannan ahlin ba, to kamar baka cikawa ƴar uwanka Airah burinta da muradin ranta ba, a yau komai zai iya lalacewa ba, wannan itace ranarka, wannan itace ranar! Ranar da zaka taimaki duban rayuwaka ranar da muke jiran zuwanta ka tashi kaje ka riskesu" ta faɗi mgnar ta riƙe masa hannu, numfashi Tuɓe ya fisga da ƙarfi idanunsa na tsiyayar da ƙwallar baƙin ciki da kuma damuwa da tarin tsanar kansa daya kasa cikawa ƙanwarsa muradinta wanda ta tashi dashi tun tana yarinya, kallon Tijama yay yace "Ya kaka ta! Ki sani a yanzu dani da gawa duk kusan abu ɗaya muke, babu abinda zan iya lokaci kawai nake jira, a yanzu wannan ahlin bamu suke buƙata ba addu'a da taimakon Allah suke nema" Girgiza kai Tijama tayi a karon farko ta shiga zubda ƙwalla tace "Me kake nufi da haka Tuɓe? Kana nufin Mu zuba idanu akan wannan lukutar masifar? Kana nufin Mu zuba idanu a rama zuciyoyi biyun da suka mace a ƙaunar junansu? A yanzu bana damuwa da halin da Fatima take ciki, domin tana tare da Sheikh zai iya magance mata komai da izinin Allah, Amma Sheikh wa yake dashi? Kana tunanin zai iya shallake abubuwan da suke shirin samunsa, abubuwa mafi muni daga wajan wanda bai zato ba bai kuma yi tsammani ba? Haba akwai duba akan wannan lamarin" Murmushin ƙarfin hali Tuɓe yay yace "Haba Kakata, kada ki manta damu dasu duk Abu ɗaya yayi mu, Allah Ubangiji Subuhanahu wata'ala shi ya halarci mu, kuma nayi imanin duk zcyar da take da imani take kusanta kanta ga Allah ba zata taɓa tuzarta ba, al'ƙawari guda nayi maki wanda ko shine ƙarshen taimakon da zanyiwa Sheikh Imam hamdan Balarabe Tabbas zanyi masa" Tijama ta kallesa tana sakin Murmushi tace "Tabbas wannan bawa na Allah bazai taɓa tuzarta ba, Sheikh Imam hamdan Balarabe zakai farin ciki farin ciki na har abada, gudan jinin ka zasu zama abin alfaharin ka, wata rana sai an samu Babban Malami kuma magajin mahaifinsa" Sheikh na kwance yay rigingine idanunsa na saman bedroom ɗinsa, kana kallonsa zaka fahimci kamar tunani yake amma a zahiri ƙwaƙwalwarsa a toshe take ya samu wani irin shock wanda bai taɓa samun kansa a ciki ba, Miƙewa tsaye yay yana gyara zaman 3gauther ɗinsa yana tafiya cike da nutsuwa da kamala, gashi dai yau ranar farin ciki ce wacce ya kamata ace kowa yana farin ciki, sbd shan ruwa da akai _(ƙaramar Sallah)_ cikin nutsuwa da kamewa haɗi da cikar haibarsa ya ƙarasa bakin fridge kana ya durƙosa dai-dai tsayin fridge ɗin ya ɗauki bottle water mai sanyi tare da Apple guda ɗaya, yana gamawa ya nufi babban Parlo, tunda ya ƙara so wajan Fannah taji ranta ya fara ɓaci hakan yasa ta shiga sakin tsaki tare sauke nauyayyiyar ajjiyar zcy Granny dake zaune ta ɗura ƙafa ɗaya kan ɗaya ga plate ɗin farfesun kaza wanda yaji kayan ƙamshi sai tiriri yake akan cinyarta, kallon Fannah tayi tace "A'a Allah ya baki hqri, kyaci kanki yau naga jaraba, daman ance mace da ciki akwai iya neman mgn" Mami dake wajan ta saki wani shu'umin murmushi kana ta maida kallonta ga Sheikh wanda kwarjininsa ya cika mata ido "Yooo duk mai ji da masifar sa basai dai ta ƙare a kansa ba, fisabilillahi?" Ta faɗa tana kallon Bahaiyya da wacce take latsa wayarta da alama ita takewa tambayar, a hankali Sheikh ya ɓalle murfin bottle ɗin tare da kafawa a bakinsa ya fara sha yana lumshe gajiyayyun idanunsa Granny tace "Amina na nan zuwa ita da koɗaɗɗiyar ƴarta" Sheikh ya kalli Granny tana ɗan shafa ƙirjinsa yace "Uhm! Ba kyau fa" ya faɗa yana zama kujerar dake farcing Fannah kana ya maida hankalinsa kan Film ɗin da ake a telemundo na _When All Is Gone_ taɓe baki yay a ransa yana faɗin "Iskanci everywhere" kana ya sauya tashar zuwa CNN, ko inda fannah take bai kalla ba bare tasan cewa ya damu da ita, amma ƙasan zcyarsa wata iriyray azaba yake sha, sbd tafarfasar da take masa akan so da ƙaunar _Zahraaansa_ miƙewa Fannah tayi ta nufi kitchen tana tafe a hankali buɗaɗɗan hips ɗinta na yawo ta cikin Laffaya data sanya golden da ratsin ruwan huda, ƙafarta fara tass domin ta daɗe rabonta da lalle, daman niyyar ta idan taje gida Ya Falta ko Yana wasu suyi mata. Kitchen ta shiga idanunta yay raurau kamare zatai kuka, jingina tayi sbd sarawar da kanta yake mata, mgnar cikin ta faɗo mata, cikin sanyin jiki ta sanya lallausan hannunta a saman cikin tana son gasgata mgnar cikin amma tunaninta da zcyarta sunƙi bata haɗin kai, ganin tana son zaucewa yasa ta shiga haɗa lemon juice domin shine abinda tafi so a yanzu sbd bata wani laulayi. Granny ta kalli Sheikh tace "Shi Campanin zaka rufe? Bisa wanne dalili kenan?" Ta gefen idanunsa ya kalleta kana ya sauke Ɓoyayyiyar ajjiyar yana ɗan saita kansa idanunsa a hanyar kitchen ɗin yace "Kawai fa, ana samun kuɗi sosai amma bana ra'ayi?" Mami ta kalli Granny sai kuma ta sauya yanayi tace "na ɗauka shine Company da Barrister yake kula maka dashi?" Bai ce komai ba ya miƙe tsaye tare da nufar kitchen yana tafe yana faɗin "Granny bari na samu cup of coffee" yana faɗin haka ya shige cikin kitchen ɗin rufe ƙofar yay ganin bata juyawa ba yasa walking slowly ya nufi inda take tsaye, hucin numfashinsa mai fidda wani dadɗan ƙamshin ya fara dokanta idanunta ta runtse, tana jin ɓacin ranta na ƙara yawa, cikin nutsuwa Sheikh ya danya hanunsa a ququnta tare da manno bayansa da nata, a tare suka fidda wani numfashi, Fannah kam ta ɗauki al'ƙawarin ko kala ba zata ce dashi ba, kansa ya ɗura a bayanta yana jin nutsuwa na shigarsa a hankali ya fara ware Laffaya jikinta ya ƙyakƙyawan bayanta ya bai yana rigace half vest a jikinta, slowly ya fara ƙasa da hannunsa zuwa ramin cibiyar ta, bakinsa daf da kunanta yace _"Zahraaah"_ ya faɗa yana fesa mata Numfashinsa a kunne tare da sakar mata fitananniyar sumbata ƙasan kunanta, Wheel hannunsa na yawo bisa cibiyar ta. Arjun yana tsaye a kitchen shida Aliyah tana haɗa masa tea yaji wayarsa tayi ƙara alamar notification ya shigo, sassauta riƙon da yay mata yayi kana ya ɗauki wayarsa yana ƙoƙarin buɗe passward ɗin Aliyah ta saki ihu sbd ruwan zafin daya zubu mata a ƙafa a rikice ya saki wayar ta faɗa jikin jug ɗin shayin take ruwan shayin ya fara shiga cikin wayar. Drip guda uku aka sanyawa Kawo Madu sai manyan injection da akai masa, anso bashi gado amma Kawo Madu yaƙi yarda, ana gama yi masa dukkan retirement ɗin daya dace ai masa aka samu ya farfaɗo yaji Kwari, Sannan suka nemi kai taxci wajan ƙarfe goma na dare suka ɗauki hanya, Kawo Madu ya kalli Uncle Sham kana ya riƙe hannunsa yace "Shamsudeen ka kira min Imam ina buƙatar ganinsa, babu da wani lokaci" jinjina kai Uncle Sham yay yace "In sha Allah ka kwantar da hankalinka" Kawo Madu ya kalli Baba Baa'na dake gaba shida driven taxci ɗin yace "Lokaci yayi da Imam zai san cewa...," Bai ƙarasa maganar ba sbd salatin da Baba Baa'na ya saki shida drive, Uncle Sham ya ɗaga kansa da sauri ya runtse idanunsa yana karatu sunayen Allah da kuma kalamar shahada, wata ƙatuwar tirela ce irinta babban Company tayo kan motar su Uncle Sham nan take kuma taxci ɗin tai ƙarƙashin tirelar, lokacin da taxci ɗin ta shige ƙasan motar ji kake wani ƙuuuuuuuuu tassss kawo nan su Uncle Sham suka fashe gaba ɗaya. Sirrn mu isn't free book contact me to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:37 - 🤔🤔: Emotional 75-76 Not too long mutane suka zagaye titin inda accident ɗin ya faru, tashin Farko Baba Baa'na aka fara cirowa lokacin tuni rai yay halinsa, sbd cikinsa daya fashe ta hanyar tayar motar data taka cikinsa, daga Baba Baa'na sai Kawo Madu shi babu abinda ya same sa amma yana kwance samɓal kana Kallonsa kaga matacce, Uncle Sham ba kowa ya iya tsayawa yaga gawarsa sbd munin da jikinsa yay banda jini dake gudu babu abinda yake yawo, kansa fita yay cif. Haka driven su Uncle Sham shima yaji rauni gaba ɗaya babu wanda ya tsira da ransa kafin kace wani abu an kashe titin gaba ɗaya ana jiran zuwan Ambulance, Ambulance na zuwa aka ɗauki gawar su Uncle Sham, securities kuma suka fara bincikar motar Company abun mmki babu driven babu dalilinsa, motar Company ɗin securities ɗin suka ja zuwa police station. Ambulance na zuwa asibitin aka shigar da gawarwakin zuwa lap domin yin bincike bayan nan aka fara duba daga ina mamatan suka fito domin samun sauƙin Impormation zuwa ga families nasu. Deedat na zaune ya ɗura Aditya a cinyarsa hannunta riƙe da chocolate, idanunsa akan t.v dawowarsa kenan daga Government house, gaba ɗaya yau bashi da wani kuzari fuskarsa walwala ya rasa meke damunsa kwana biyun nan fama yake da wani ciwon kai mai azaba ga rashi bacci daya rufe idanunsa zai dinga ganin wasu magic na mutane suna masa yawo a cikin idanunsa, wani lokacin har kukan mace ya keji ya rasa me yake masa daɗi, Mutsin da yaji ya sanya ya buɗe idanunsa tare da sauke ganinsa akan Ammi da take tsaye cikin kayan bacci tai kyau sosai, amma damuwa na shimfiɗe a saman fuskarta, Murmushin dole ta sakar masa kana ta sanya hannu ta ɗauki Aditya wacce bacci ya ɗauke ta a jikin Papi, ba tare da tayi masa mgn ba ya nufi part ɗinsu dashi Lokacin wajan 9 da ɗuriya tana zuwa ta bawa Nanny Aditya dama tuni Anushka tayi bacci, bayan ta bada ita ta dawo inda Deedat ke zaune, ta gefen idanunta ta kallesa taga dai hankalinsa baya kanta dan haka ta share ta ɗauki kindirmon daya sha suger da zuma ta tsiyaya masa a mug kana ta ƙara matsawa kusa dashi tare da kama hannayensa duk biyun ta zamesu daga riƙon da yaywa kansa, fararan idanunsa ya buɗe ya fara ƙoƙarin sakar mata Murmushi, bata tsaya jin wani abu daga garesa ba ta kafa masa mug ɗin a baki, sanyin kindirmon ya sashi sakin ajjiyar zcy yana ɗan matse hannunta daya riƙe, zame bakinsa yay yana sakin Murmushi yace _"it's my turn first lady"_ ya faɗa yana ɗan mannata da jikinsa ya ɗura mata a bakinta, sai da ta shanye rayuwar kana ya sakar mata fuskarta yana faɗin "Yau she za'ai wa Twins ƙanne?" Marai-raice fuska tayi tace "Ba wannan ba, Meke damun Ur Excellence ne? Kwana biyu you're not on your right sense kana sani damuwa" buɗe ido yay yana shafa kanta zuwa wuyanta yace "Uhm! Me zai damu Deedat ne banda damuwar sanyin idaniyarsa?" Kwantar da kanta tayi ƙirjinsa tace "Ur Excellence nifa bana da wata damuwa, kawai ina jin kewa ne" Kallonta yay yace "Sure?" Ta gyaɗa masa kanta yace "Kullum kina nuna cewa you're strong woman, amma damuwar fuskarki a kullum ƙara fallasa asirin zcyar ki take, Why Ayushert?? Me yasa kike son sanyawa kanki damuwa har haka ne? Damuwa bata magani sai dai ta sanyawa mutum wank ciwon nada ban, Ni Mijin ki ne idan wani abu nai mki ki faɗa min _I promise to you I'll change_ zan sauya zan gyara" girgiza masa kai tayi tana ɓoye hawayen idanunta tace "Ba kai min komai ba, kuma har abada bana tunanin zaka min" yace "Then Meke damunki gayamin?" Kuka zata sakar masa ya tashi tsaye tare da miƙar da ita tsaye yace "It's okay! Basai naji ba Allah ya yaye maki kuma ya kawo maki sauƙi" yana faɗin hakan ya jata zuwa flat ɗinsa kansa ne ya sara gabansa ya faɗi da sauri ya kalli a gogo yaga 10 da wani abu, in sha Allah gobe zai ziyarci Likita. Sheikh ya ɗan yi gyaran murya kana ya ɓoye tsoran dake ransa ya kalli Anut Amina yace "Yanzu mene na kuka kuma? _In sha Allah nothing will happen to him, in sha Allah"_ Anut Amina tace "Na kasa nutsuwa ina jin Dadyn Huda kamar baya cikin hayyacinsa, wlh ga bana faɗuwa yake" Arjun yace "Ki kwantar da hankalinki, bari Abba (Barrister) yazo muji kiran da akai masa" Granny ta cire bakin zani tace "Shkknan su kuma yaran duk a gantali za'a neme su a dinga rasawa fisabilillahi? Allah ka dubu idanun bayinka ka dawo mana da wannan bawan Allah" Lumshe idanunsa Sheikh yay yana jin Yadda zcyarsa ke bugawa tsoro da damuwa duk ya gama cikasa, amma ko a fuska bai nuna ba yana ƙoƙarin danne damuwar dake ransa, Mami kallon kowa take domin ita damuwarta a yanzu baya huce Sheikh tana tunanin ta Yadda za'ai ta samu kansa cikin sauƙi, miƙewa tsaye Sheikh yay Arjun yace "Buddy ina zaka?" Bai kulasa ba yaci gaba da tafiya zuwa library ɗinsa, Granny tace "Itama waccen ta aro rashin kirki ta sanyawa kanta, to duk ba sai dai suci kansu ba fisabilillahi? Ni ai ba za'a kashe ni da rai na ba" sarai Arjun yasan da Fannah take kawai yay shiru tunani masu yawa na damunsa, ga lalacewar wayarsa shi dan haushi tunda ya ajjiye ta bai ƙara bi ta kanta ba. A hankali Sheikh ya tura ƙofar library room ɗin nasa, kana ya sanya kansa ciki yana ɗan fesar da numfashi su yake ya keɓe shi kaɗan ko ya samu nutsuwa a ransa, jingina yay a jikin ƙofar yana tunanin mgnar P.a ɗinsa da yace an sace motar Company ɗaya an rasa, to waye ta ɗauka me zaiyi da ita? Mene ma'anar ɗaukan da yay? Duk wannan shine abinda ke damunsa amma babu mai bashi amsar duk wannan tambayar da yay, ware fararan rikitattun idanunsa yay sbd shassheƙar kukanta da yake jiyowa, cikin nutsuwa ya fara taka ƙafafuwan sa tare da jefa manyan idanunsa yaga ga inda zai ganta, a durƙoshe ya ganta ta cure waje guda jikinta sai rawa yake sbd zazzaɓin masassara daya kawo mata ziyara, ga ƙuncin zcyr da yake damunta a kwana biyun nan, uwa uba faɗuwar gaban da take, tsaye yay a kanta yana karantar yanayin ta kasa cewa komai yay sbd idan yay mgnar wannan karan bai san mene za tace masa ba, Musamman daya fahimci abinda yake damunta wajan kashi biyu ne, cikin jikinta wanda har yanzu bata yarda dashi ba shike ƙara sanyata take masifa, ga kuma maƙa sudin abinda yake sata damuwar, wanda ya riga yasan ko menene shi ya ɗauki niyyar ɗaukan mataki cikin gaggawa yana jiran lokaci ne. Cikin nutsuwa ya durƙosa dai-dai inda take tsugune a taushashe ya kira sunanta _"Zahraaah"_ kine ɗagowa tayi sbd haushin sa data keji amma a yanzu tana buƙatar mai lallashinta tana buƙatar mai kula da ita,tana buƙatar mai kwantar mata da hankali da sata farin ciki. Jin tayi shiru taƙi yarda ta ɗaga kanta yasa ya ɗura lallausan hannunsa a wuyanta fiddo idanunsa waje yay sbd zafin da yaji ya ratsa shi da sauri kuma ya ƙarasa zubewa a wajan yana sanya hannunsa tare da jiyowa da ita gaba ɗaya zuwa garesa sosai jikinta ke rawa ta kasa yarda kuma ta kallesa bai tsaya jiran komai ba ya mannata da jikinsa ya rufe tsam a ƙirjinsa tare da fara shafa kanta yana bubbuga bayanta alamar rarrashi, ɗumin da taji yasa ta ƙara narkewa a jikinta harta manta da tsanar da tayi masa mai taimakon ta kawai take nema, jin yadda duk ta shige masa yasa ya sanya hannunsa ya ɓalle bottles ɗin gaban rigar sa faffaɗan ƙirjinsa wanda yake cike da gashi masu kyau da tsari sai Shinny yake ga yadda brest ɗinsa suka buɗe gefen nippy ɗinsa yana zagaye da wasu siraran gashi wanda sukai masa ƙawanya, yana gama buɗe ƙirjinsa yasa hannu ya ware mata Laffaya jikinta yana mmkin yadda take son zama da ƙananun kaya wanda ganinsu kaɗai yake sanyawa ya fita a hayyacinta ya zautar da tunaninsa. Zare Laffaya yay ya barta daga ita sai ƙaramin sket iya laps (Cinyoyin) ɗinta sai kuma wata ƙaramar riga mara hannu wacce ta tsaya mata iya saman cibiyar ta, Booms ɗinta sun cika sosai kamar zasu fasa ƙirjinta hakan kuma baya rasa na saba da cikin jikinta daya fara ƙwari, wani irin sanyi ne ya shiga ratsa mata ƙofofin fatar jikinta zuwa cikin ƙashinta wanda kai tsaye sanyin yake samun gurbi a cikin ɓargon ta, ganin yadda jikinta ke rawa idanunta suna tsiyayar hawaye ga yadda take taune lips kaɗai yasa ha fahimci zazzaɓin ya gama cin ƙarfinta, cikin kulawa ya ware hannayenta kana ya mannata da jikinsa suka sauke ajjiyar zuciya a tare shi ya sauke numfashi ne sbd zafin jikinta daya daki farar fatarsa, ita ta saki ne sbd abubuwa kusan guda biyu na farko sanyin jikinsa wata fara connecting da jikinta, sai kuma wani shock da taji ya kamata fatar jikinta ta fara mutsawa yanayin data daɗe dashi tana dannewa ya fara dawo mata sabo, zagaye hannunta tayi ta riƙe ququnsa tana cije baki, rungome ta yay sosai yana hura mata iska a cikin kunanta a hankali kuma ya fara sutale ƴar fingilar rigar jikinta, idanunta wanda sukai nauyi ta buɗe ta kalli ƙyakkyawar fuskar mai cike da haiba jin hucin numfashinta yasa ya ranƙwafo da fuskarsa sosai hakan yasa ya ƙara matseta a jikinsa, fuskarsu ta haɗe sosai hadda bakinsu yana kan saitin na ɗan uwansa, idanunta na zubar da hawaye suna sauka a ƙirjinsa, bakinta na rawa tace "Na tsaneka Sheikh! Bana sonka" ta faɗa tana riƙe bakinsa tare da fara sha, lumshe idanunsa yay sosai ta bashi da dry, ga zafin jikinta ga masifar dake damunta ga kuma neman mgnar da take a tsakiyar daran, ƙarasa zare rigar yay da sauri ta ƙara shigewa jikinsa sbd bayyanar bawar ƙirjinta. Barrister na zaune cikin mota shida Alhj Kamal yace "Nafa ɗauka wani ke kira ashe kai ne why baka shigo ciki ba?" Wani files Alhj Kamal ya miƙawa Barrister yace "Ga contact ɗinka Nan an kammala abinda kake nema shekara da shekaru yau ya samu congratulations" da farin ciki Barrister yace _"Wow! What a great new?_ Wow Hamdan Balarabe you're lucky dame zan biyaka?" Alhj Kamal yace "Kawai saka samin hannu a wannan file ɗin" da sauri Barrister yace "Ina file ɗin ai ba jira kawo sa kawai, Gsky ga faranta kashi 80 na burina ya cika" Alhj Kamal ya miƙa masa file ɗin yana faɗin "Haba! Nafa san yadda kake son Contact ɗin" hannu ya sanya masa yace "Bari na shiga ciki ngd Sosai, kasan komai ai?" Murmushi Alhj Kamal yay yace "Ba damuwa ngd fa" daga haka sukai sallama Barrister ya dawo cikin Parlon. A zaune ya samesu gaba ɗaya har lokacin kuma Anut Amina kuka take ta rungome Huda, Granny banda share hawaye da face majina babu abinda take, Arjun na zaune yana tunanin halin da Sheikh yake dan hankalinsa bai kwanta ba, Mami ma idanunta ba kan hanyar Library ɗin, Fareeq yay jigum yana ta tunani, Buhaiyya tana zaune da waya a hannunta bincike akai sosai akan gawar su Uncle Sham cikin Sa'a kuma aka samu Sim card a cikin aljihun sa, gaba ɗaya suna securities ɗin kansu ya toshe sun manta da gidan Redio, sosai Accident ɗin ya gigita su, domin har yanzu jini yaƙi tsayawa a jikin gawar Uncle Sham, kai tsaye aka nemi wata ƙaramar waya aka sanya sim ɗin ciki, contact ɗin ciki suka fara dubawa har suka zo kan wata number da akai saving da _DEEDAT BALARABE_ haka nan mai kiran yaji number tai masa dan haka kawai yay dailing number. Suna zaune gaba ɗaya a gida ɗaya sun kasa bacci kowa da abinda yake damunsa, Yana Ya Falta, Mama kolo matar Kawo Madu. Wayace ta ɗauki ƙara Mami dake kusa da wayar tana mmkin tafkekiyar wayar wace domin bata taɓa ganinta ba, Barrister dake tsaye ya kalli wayar yace "Wannan fa? Ina me ita?" Arjun ne yace "Ta Buddy ce" Da mmki Mami da Barrister harda Granny suka kalli wayar kafin Barrister yace "When yay waya?" Arjun yace "Ba jimawa ai Abba" a dai-dai nan kuma wani kiran ya sake shigowa Mami tai saurin ɗauka tace "Bari na kai masa" kallanta kawai Arjun yay tsoro ya shigesa, sai dai bai ce komai ba, kai tsaye Mami ta nufi hanyar Library ɗin. Lumshe idanunsa Sheikh yay yana jin Yadda Fannah ke kissing bakinsa cikin wani irin salo na musamman gaba ɗaya ba a hayyacinta take ba, fesar da numfashi yay tare da fisge bakinsa kwaɓe fuska tayi idanunta a rufe ta buɗe baki zata saki kuka yau saurin rufe mata bakin ta hanyar sanya bakinsa ciki, Wheel hannunsa na cikinta yana shafa tare dayin sama dashi zuwa tsakiyar kyawawan ƙirjinta, cikin wani irin hali ya ƙara sakar mata da wani kalar numfashi mai kama da gurnani, slowly ya zare bakin yace _"Stop cry Zahraaah, I'm here nothing will happen to you Jewel, ok just hug me you'll feel better My dear Fatima Zahraaah"_ cikin kuka tace "I hate you Sheikh Imam hamdan Balarabe na tsaneka, bana son...," Saurin matse nippy ɗinta yay wanda ya sanya tai saurin riƙe mgnar tana maƙale sa, kafin cikin zafin nama jikinsa har rawa yake ya mirginata ƙasa tare dayi mata rufa, ƙarar da yaji da kuma salatin da yaji an tafka yasa ya juya yaga Mami tsaye a kansu... Sirrin mu isn't free book is for sale contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV ✍🏾 22/10/2021, 10:37 - 🤔🤔: Matter's Of The Heart 77-78 _SEASON 7 KITCHEN_ _BAN TAƁA GANIN WAJAN DA SUKA ƘWARE WAJAN TSARA LAFIYAYYAN *CAKE🍰* IRIN 7 KITCHEN BA, SAU TARI NI *NIMCYLUV* BAI GIDANA YA KAN YAWAN TAMBAYTA INA NAKE SAMUN LAFIYAYYAN CHOCOLATE AND MILK CAKE KAMAR HAKA? DOMIN DUK RANAR CIKAR HAIHUWARSA NA NAKE ZUWA A TSARA MIN CAKE NA ABIN MMKI BARI KUJI YADDA ABIN YAKE._ *Mata iyayen nagarta💃🏻💃🏻* Shin kin iya girki? Idan kin iya wane iri kikafi ƙwarewa akai? To ba haushe ya ce dai ko kona da kyau ka ƙara da wanka🛀🏾. Ina muku albishir da cewa Season 7 sun shirya tsaf dan koyar daku yanda zaku haɗa cake na celebration kala kala, da kuma donuts ga kuma bonus recipe na yanda zaki haɗa lemo💃🏻💃🏻💃🏻. Duk wannan garaɓasar za'a haɗata ne da Videos kamar agabanki a keyi💃🏻💃🏻💃🏻. Baya ga haka kuma zamu baki damar mallakar pdf da zaki ajiye abunki a waya dan gaba. Idan bakya sauyawa yara abincin makaranta kullum sai indomie wannan damar ki ce. CAKE ƊIN SUN HAƊA DA; Red Valvet Chocolate cake Vanillah. Ring donuts Filled donut Bamboloni Duk wannan abin zaki iya shine da garaɓasar Naira dubu ɗaya kacal 1k💃🏻💃🏻💃🏻. Maza biya kuɗinki a nan lambar akawunt ɗin. 0026971316 Gtbnk Balkisu musa galadanchi. Saiki tura shaidar biyanki ta nan. 07084161619. Ku tuntuɓi wannan lambar domin ƙarin bayani. 08039424298. Sai an gwada akan san na ƙwarai. __________ Ganin Mami tsaye a kansu ba ƙaramin mmki abin ya bawa Sheikh ba, yama rasa mene zai yi, kansa yaji ya sara da ƙarfi wanda ya sanya yay saurin faɗin _"Yasubuhanallah!"_ lumshe gajiyayyun idanunsa yay ya shiga fesar da numfashi, ba tare da zare Fannah daga jikinsa ba ya gyara zamansa tare da ƙara manneta da ƙirjinsa, cije baki Mami tayi tana jin yadda wani abu mai ɗaci yazo ya shige ta cikin bakinta, abinda take so take burin mallaka shine wata banza ta samesa cikin sauƙi, hannu tasa ta riƙe ququnta tace _"Wow! What a nice couple"_ ta faɗa tana zagayesu kana ta ɗura da faɗin "Da kyau Imam, da kyau how long ka kasance da matar Ubanka? Ashe dalilin daya sanya kenan kaƙi amsar tayin da nai maka kenan ko? Uhm! Finally *TA FARU TA ƘARE...!* zanyi maganinku gaba ɗaya zaka gane cewa ni Saudat idan naso Mallakar abu baya yimin wahalar samu, enjoy your time Sweet Imam ka huta abinka" ta faɗa tana kallon tattausan hannunsa dake saman cikin Fannah, cije baki tayi sai kuma hawayen baƙin cikin ganin Fannah da Sheikh suka shiga zubo mata, wayar ta ajjiye masa tace "Nayi al'ƙawarin sai ka zama nawa ni ɗaya kuma zakai mmki" tana faɗin hakan tai waje tana goge Idanunta, kamar ba ita tai kuka yanzu ba. Wata kamilalliyar ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke what's going on? Meke shirin samun sa ne? What is this? Ya rabb, something bad gonna happen Allah ya kawo komai cikin sauƙi amma Tabbas there's something happens menene? Why bai tunanin cewa da Mutane a gidan ba? Bai damu da ganin da Mami tai masu ba, yadda jikinsa yake a mace yake komai bisa jagoranci zyrsa ba tare da tunani ba. Kansa ya kunce komai ya dulmiye masa, gaba ɗaya ya rasa meye hakan meke damunsa, fesar da numfashi yay a hankali ya ware manyan idanunsa wanda sukai dan jaa ba sosai ba, ya sauke ganinsa a kanta tai lamo jikinsa idanunta a rufe har yanzu jikinta rawar sanyi yake sai tsotsar leɓanta fuskarta har wani yellow take, sosai yake mmkin farin farar ta amma duk da hakan bata kamashi a haske ba, yanayin farin su ba ɗaya bane, haske Sheikh irin na larabawa ne, nata kuma irin na ƴan India ne sbd yanayin jikinta sosai yake ɗaukan hankalinsa, duk wannan abun da yake bai yadda idanunsa sun sauka a ƙirjinta ba, wata wahalalliyar ajjiyar zuciya tare fisgo Numfashinsa, cikin kasalar data gama saukar masa ya nemi rigar ta ya sanya mata, kana ya haɗe ta ciff a Laffayar, tana manne a jikinsa ya miƙe da ita tsaye bai yarda ya fita da ita ba ya nufi wajan duguwar sofa a hankali ya kwantar da tare da zareta a jikinsa, da sauri ta buɗe idanunta wanda suka gama qanqancewa sbd azabar da take sha, ganinsa daf da fuskarsa yasa a hankali tace "You never changed Imam hamdan Balarabe, kullum tsanarka nake" kallon bakinta yay wanda suke mutsawa a hankali take wassafa masa zance dasu, kana ya cilla idanunsa cikin nata, ba tare da yace komai ba, ya gyara mata kwanciya ya ɗura bakinsa a kunanta ya tofa mata addu'a tare da shafa kanta, lumshe idanunta tayi sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe hannunsa tana faɗin "Please don't leave me alone kaji" uhm rigima zalla kenan a cilla masa zafafan maganganu amma jibi yadda take marai-raice fuska, zare hannunsa yay durƙosa dai-dai tsakiyar goshinta cikin dakakkiyar muryarsa mai daɗi da amo yace _"Don't worry Zahraaah! I'll be with you no matter what happen"_ Yana faɗin haka ya juya cike da kuzari ya fara taka ƙafafuwan sa tare da fita ya rufe ƙofar da key kana ya cilla key ɗin a cikin aljihun sa. Mami na fita bata tsaya a Parlo tai shigewarta cikin part ɗinta, Barrister dai da Arjun suna zaune Anut Amina zuwa lokacin ajjiyar zuciya kawai take saukewa, idan ta rasa mijinta ina zata ita da ba'a nan garin take ba? Ina zata kai kanta a wajan wa zata zauna? Gaba ɗaya ta kasa kwantar da hankalinta, Granny sai fatar Majina take tace "Ta badai shkknan? Yaro da ko sauro bai taɓa kashewa ba shine za'a nema a rasa fisabilillahi? Duniya zaki damu ni Faɗimatu wanne kalar gantalallun mutane nake zaune dasu ne? Babu wanda ya damu da halin da muke ciki sai a samu gaba aita zare mana ido dan Allah, ungo number kira min jami'an tsaro yanzun nan" ta faɗa tana miƙawa Arjun wayarta tace "Maza Ranjun ni ba'a sallamawa dniya ni ba, idan ba hedikwata ne sai naje yanzun nan, ah to uban me ze saman tunda zcyta tsaf take ko ada sai dai a cucan ba dai na cuci wani ba, zamani ne dai ya sauya ni" kafin Arjun yay wani abu Sheikh ya ƙarasu wajan yana ɗan dai-dai ta fuskarsa, cikin son kawar da damuwar ransa yace "Anut Amina kije ki kwanta" kallonsa tayi da kumburarrun idanunta tace "Haba Sheikh tayaya kake tunanin zan iya runtsawa ban san halin da mijina yake ciki ba?" Gyara tsaiwa yay kana a hankali cikin ƙasa yace "Just pray, in sha bazan dawo gida ba sai dashi" kafin tai mgn wayar Sheikh ta sake ringing, kallo guda yaywa wayar yaji gabansa ya faɗi koda bai saved number Uncle Sham ba amma yana haddace da ita a qwaqwalwarsa, juyawa yay tare da nufar part ɗinsa yana kiran Arjun da hannu ganin haka yasa Arjun miƙewa yabi bayan Sheikh, daga can ɓangaren mai kiran ya sauke numfashi jin an ɗaga wayar yace "Assalamu alaikum fatan muna magana da Deedat Balarabe?" Shiru Sheikh yay yana maimaita sunan kamar yasan sunan kamar kuma mai sunan ya sani, samun kansa yay da faɗin "Wasalamu alaika Yes! I I'm" ya faɗa yana tsayawa gaban mirror Arjun kuma ya rufe ƙofar ya tsaya yana kallon Sheikh, Mutumin yace "Ma sha Allah! Kana magana da hukumar bincike ta fararan kaya na nan garin Barno" Gaban Sheikh ya faɗi kasa mgn yay sai "Uhm" kawai da yace Mutumin da yace "An samu Accident ne, wanda ɗaya daga cikin mutanan da suka rasa ransu a jikinsa muka samu layin da zamu kiraka fatan zaka halarci asibiti domin bincikar mamatan cikin gaggawa" . Saurin Zama Sheikh yay wani gumi ya fara keto masa duk da sanyin a.c dake cikin ɗakin nasa, fuskarsa ya kifa saman tafin hannunsa ya shiga sauke ajjiyar zuciya da sauri², nan take kuma jijiyoyin kansa sukai raɗa raɗa saman goshinsa, kasa mutsawa yay sbd rawar da jikinsa yake shikenan sauran jigon nasa ya tafi a fili ya shiga faɗin _"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, La'ilaha illah anta Suhubanaka inni kuntuu minnal zaluminn"_ sai kuma ya saki wayar kasa tare da bin wayar suka zube saman carpet, Da sauri Arjun ya ƙarasu inda yake hankali tashe yace "Buddy Meke faruwa? Wane ya kira ka?" Kasa mgn Sheikh yay sbd abinda ya tsaya masa a maƙoshinsa ganin hakan yasa Arjun ya ruɗe tashin hankalinsa ya ƙara nunkuwa akan na da, "Dan Allah ka gayamin lafiya? Mene ya faru kai da waye? Wane kuma ya kiraka" Miƙewa Sheikh yay tare da shiga bathroom bai daɗe ba ya fito fuskarsa na zubda ruwa, kallon Arjun yay yace "Duba mana online ticket na zuwa Barno a cikin daran nan" da mmki Arjun yace "Amma tafiya cikin daran nan Meke faruwa ne? Ga tashin hankali nan duk ya bai yana a fuskar ka Sheikh" Sheikh na zura Light blue ɗin shaddar sa yace "I don't know how to explain you, Uncle Sham sunyi Accident" da ƙarfi Arjun yace "What Uncle Sham? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" da sauri ya kunna net akwai ticket amma sai na biyar ɗin asuba, Sheikh yace "kasai guda Uku" Sheikh yace ukun ne kawai amma shi kansa bai san waye cikon na ukun ba, Arjun waya yaywa Aliyah ya gaya mata basai dawo ba kana ya kira Umma, Sheikh kasa fita yay sbd Bai son haɗa ido da Anut Amina da Huda tausayinsu ya gama cika masa zcy, yasan shi abin tausayi ne then ba komai zai san cewa yafi shiga tashin hankali ba, har zuwa Asuba bai faɗawa Arjun Uncle Sham ya rasu ba, haka kuma kwana yay akan ladduma idanunsa har kumbura sukai. Tun ƙarfe huɗu ya gama shiryawa haka Arjun Anut Amina take ƙyar ta bar Parlon ta nufi Part ɗin Granny, a hankali Sheikh ya tura ƙofar Library room ɗin bayan ya buɗe da key, tana kwance saman kujerar daya kwantar da ita, tsayawa yay a kanta yaga yadda take sauke numfashi da ƙyar sai ajjiyar zuciya take saukewa da alama taci kuka ta ƙoshi, slowly ya ɗago ta gaba ɗaya zuwa jikinsa, ya riƙe ta sosai, ba kowa a Parlon hakan yasa ya shige da ita zuwa part ɗinta, yana zuwa ya nufi bathroom da ita, ruwa mai zafi ya haɗa yana jin yadda take ƙara maƙale masa, a haka ya ware Laffayar tass ba tare daya cire sauran kayan ba ya sanyata cikin jucuzzi turo baki tana kwaɓe masa fuska sai kuma ta buɗe idanunta tana kallon Sheikh tai saurin ɗauke kanta dan bata ma son ta sake ganin mummunar fuskarsa, shima bai damu daya kalleta ba, da sauri ya juya sbd ƙirjinta guda ɗaya da yay tsalle ya fito yana zuwa bakin ƙofa yace "Ki shirya zamu Barno yanzu" da zuwa lokacin ya gama samun impormation cewa hadda su Baba Baa'na, jiri har wani diɓan sa yake, yana fita ya samu Arjun a Parlo sai kuma ga Barrister shima ya fito a shirya ashe shima yasai ticket ɗin tafiyar shida Fannah kowa fuskarsa babu annuri, Sheikh tasbihi kawai yake dan kansa ya kusa kuncewa, part ɗin Granny ya nufa yana zuwa tai saurin faɗin "Imamu akwai abinda kake ɓoyewa, nifa ba mutuniyar banza bace da zaku mai dani wata bi ta can" Kallonta kawai Sheikh yay kana ya kalli Anut Amina yace "Zamu Barno yanzu in sha Allah!" Da sauri ta kallesa tace "Me za kuyi a Barno Sheikh kuma at this hour? Dan Allah idan wani abu ya samu mijina ka faɗa min" Huda dake gefe tace "Ayyya Sheikh Daddy" wani tausayin yarinyar ya kama Sheikh ya sauke numfashi yace "akan Uncle Sham ne" jikin Anut Amina na rawa tace "Mene Uncle? Mene ya samesa kada ka gayamin wani mummunan abu a kansa" ya faɗa idanunta na kawo ruwa Miƙewa tsaye yay yace "Matsala suka samu da police amma Allahamdulillah komai ya daidaita In sha Allah, kici gaba dayi masa addu'a Allah ya kiyaye gaba yanzu addu'ar taki yafi buƙata" yana faɗin haka ya fita daga ɗakin baki Granny ta saki kafin saka salati tana tafa hannu "Muhammadur Rasulullah (S.A.W) shi Shansu meye haɗin sa da wasu Polis fisabilillahi?" Anut Amina sauke ajjiyar zcy tayi sam zcyarta bata yarda da mgnar Sheikh ba, bai taɓa yi mata ƙarya ba hakan yasa kawai ta amince da zan can dan bata son ƙarya ta Sheikh ɗin. Fannah a gaggauce ta shirya cikin wata lafiyayyiyar abaya mai kyau wacce ta kwanta a jikinta, tunda ta fito Sheikh yake Kallonta kana ya kalli Barrister yaga shima ita yake kallo haka nan ransa ya ɓaci, musamman da yaga yadda rigar ta kamata tai mata masifar kyau, ajjiyar zcy Barrister ya sauke kana ya haura upstairs domin ɗauko wayarsa, yana fita Sheikh ya miƙe ya makawa Fannah harara ita kuma ta murguɗa masa baki, bai damu da Arjun dake wajan ba ya shammace ta tare da ɗaga ta sama da sauri ta qanqamesa sbd tsoran da taji, Murmushi Arjun yay domin ya gama gane kishi ke damun Sheikh, tana shure² ya ƙarasa da ita ɗakin ta, tare da direta ya nufi wajan wrdrb ɗinta wani purple ɗin hijab ya ɗauko mata wanda zai sauka har ƙasan ta, fuskarsa ba walwala ya nufi inda take yana zuwa tace "Malam wai meye haɗi na dakai ne? Bazan saka hijab ɗin ba Bashi nai niyya ba" bai kulata ba ya jawota jikinsa tare da zame Vail ɗin kanta, lumshe idanunsa yay sbd ƙamshin sumar kanta daya daki hancinsa, a hankali ya tura hancinsa cikin sumar kanta yana jin yadda take mutsi zata gudu amma No way to run, sbd gama ɗaya ya riƙe ququnta da hannunsa, cikin nutsuwa ya fara fidda numfashi, yana shaƙar ƙamshin dake fita daga cikin gashin, kanta ya ɗaga fuskarsa daf da tata ya manna mata sumbata a jajayen laɓɓanta, da hancinta kana fatar wuyanta Murya can ƙasa a tsakiyar kunanta yace _"Sabahul khair Zahraaah! Mrng Jewel nah"_ ya faɗa yana jan fatar kunanta yana hura mata iska jikinta ne ya saki hakan yasa tai saurin rungomesa hijab ɗin ya saka mata, kana ya riƙe hannunta ya ɗura saman bakinsa yay kisses nasa, sai kuma ya maida hannun saitin zcyarsa yace "U belong to me Zahraaah, Only me kin gane ban taɓa nuna maki ɓacin rai na ba, wlh billahil Azim kika sake kika zauna kusa da Abba uhm" bai ƙarasa maganar ba yaja hannunta zuwa waje. Barrister ya kalli Arjun yace "A'a ina Son yay?" Arjun yace "Wai Anut Fatima yaje kira sbd part ɗinta ta koma tana kuka" kafin Barrister yay magana Sheikh ya ƙarasu Fannah na bayansa sai turo baki take gaba, Sallama sukaiwa su Granny kana suka ɗauki hanyar airport a cikin jirgi Barrister ya zauna kusa da Fannah da sauri ta miƙe taje kujerar dake farcing Sheikh ya zauna ganin haka ya rabu da ita, Sheikh yi yayi kamar bai san da ita a wajan ba. A haka suka ƙarasa Barno lokacin an gama shirya gawar su Uncle Sham a gidan su Fannah, domin tuni labari ya iske masu, tashin hankali ba'a saka masa rana Fannah kusan sumewa tayi lokacin da Tayi arba da gawar mahaifinta, cak Sheikh ya ɗauke ta daga wajan gaba ɗaya kana ya kira Yakura yayar Mama kolo wacce yaga ta fisu nutsuwa, yace ta kula da Fannah sbd Cikin dake jikinta, Yakura kallonsa kawai take sosai yay mata kama da wani ko wata amma ta kasa tunawa, yana tsaye akan Fannah da akaiwa allurar bacci tare da ɗaura mata ruwa wayar Yakura ta ɗauki ƙara tana dubawa ta ɗauka tace "Indoo kinji labarin abinda ya samemu ko? Yau munga jarrabawa ta Ubangiji sai addu'a kawai?" Bai tsaya jiran me za tace ba sbd bugun da zcyarsa take masa yay waje da sauri, yana zuwa ya samu har su Anut Amina sun ƙarasu domin ance a nan Za'ai jana'izar baki ɗaya, Anut Amina na ganin Sheikh ta nufesa da sauri ta riƙesa "Sheikh Mijina farin cikina, Duniya, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" sai kuma ta zube a jikinsa ba Numfashi, matan wajan suka riƙeta shi kuma ya ɗauki Huda ya bawa Ya Falta ita, wacce tunda yazo take mmkin ganinsa a wajan, gaba ɗaya unguwar ta cika da mutane, lokacin da Sheikh yaga gawar Uncle Sham kasa mutsawa yay abun mmki ko ɗigwan hawaye bai ba, a haka ya zauna ya dinga kwarara masa addu'a na samun rahamar Ubangiji. Lokacin da za'a saka Uncle Sham ya kabari rufe idanunsa yay da sauri kuma ya rungome Arjun dake kusa dashi yana sauke ajjiyar rungomesa Arjun yay yana shafa bayansa, dan yasan duk abinda Sheikh yake dauriya ce sai bayan abun zai zauna jinyar kansa da rashin kawon nasa. Wacce ake kira da Indoo duk yadda tasu ƙarasu a lokacin kasawa tayi sbd rashin lafiya. A nan kuma suka bar Fannah. _40 days ago_ Bayan arba'in ɗin su Uncle Sham Fannah ta dawo gidan mijinta ba dan ranta yasu ba, Anut Amina itama tana gidan da zama gaba ɗaya rayuwar duk tai masu zafi. Sheikh na zaune bayan ya dawo daga Police station sbd binciken da ake akan motar Company sa, wacce ya tabbatar masu bashi da wata masaniyar komai, yana sanye da Armless sai 3 gauthier hannunsa riƙe da power horse yana sha, sai system da yake operating a hankali, rabin hankalinsa gaba ɗaya yana kan Fannah rabon daya ganta harya manta, ya azabto rashinta sosai. Ƙofar ɗakin aka buɗe tare da shigowa warin turarenta kawai yasan ita ce, dan haka ko ɗago kai bai ba cikin rangwaɗa ta ƙarasu tare da zama kusa dashi ta ajjiye masa wayarta, kallonsa yakai kan wayar yaga pictures ɗinsa shida Fannah suna rungome da junansu, harda vedio'n, ɗauke kai yay bai ce komai ba yaci gaba da abinda yake tace "Yau komai zai zo ƙarshe, ko dai ka amshi tayin da nai maka ko kuma na fallasa SIRRIN dake tsakaninka da matar Ubanka, daga ƙarshe ma cikin dake jikina zan ce naka ne" rufe system ɗin yay ya miƙe da sauri ta rungomesa cikin zafin nama yay cilli da ita tare da nuna ta da hannu yana faɗin "Ki shiga hankalinki, tayinki kuma akai kasuwa I'm not interested" dry tayi ta shiga zare cire hijab ɗin jikinta duguwar riga ce a jikinta ta yayyaga gaban rigar tasa hannu ta fito da ƙirjin ta ta baza gashin kanta, kwallon ta kawai yay yake kana ya kalli c.c tv Camera ya saki Murmushi, yace "zaki sanya kanki a halaka fa, don't kada ki aikata" kansa tayo gaba ɗaya sukai baya sbd bai tunanin hankan ba, wata gigitacciyyar ƙara Mami ta sanya tare da faɗin "Wayyoooo Barrister ka taimake ni wayyoooo Allah Sheikh ne" Barrister da Anut Amina da Granny da Fannah suka Miƙe da sauri sbd sosai sukaji Muryar Mami yadda take faɗin sunan Sheikh yasa gaba ɗaya suka ruga da gudu zuwa part ɗin Sheikh a tunaninsu wani abu ya samu Sheikh Imam hamdan Balarabe.. Ai weekend lfy🌚🌝 Contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:37 - 🤔🤔: About The Pregnancy 79-80 Da raguwar ƙarfinsa ya yi saurin zame jikinsa yana aikata mata da wani kallon tsana tare warning akan abinda tai masa, Su Granny suna zuwa suka tsaya cak domin abinda suka ganin yafi ƙarfin tunanin mai tunani duk wani mai cikakken hankali ba zai taɓa aminta da wannan Sabon yanayin ba, Musamman Anut da Granny domin Anut Amina juyawa tayi tana mmkin hali irin na Mami domin tun ba yau ba ta riga ta gama fahimtar matar da tsoran Allah sam, ƙaramin tunani da ƙwaƙwalwa gare ta,banda haka tayaya take ƙoƙarin tuzarta wanda duk duniya idan sun taro za'a samu fiye da rabi wanda zasu shaida halin Sheikh ba haka ba ne, Tayaya take ƙoƙarin cin zarafin wanda ya yarda da ƙaddara mai kyau ko akasinta? Shin ko dai akwai wata manufa ne wanda ya sanya tai masa? Ko kuma kawai kalar nata rashin ɗa'ar kenan, tsaki taja domin sai yanzu ne idanunta suke ƙara harshashu mata abinda ta gani. Harɗe hannu Barrister yay yana kallon ikon Allah wanda rabin kallonsa akan Sheikh ne yana son zcyarsa ta gasgata abinda idanuwansa suka gane masa a yanzu, domin bai damu da Mami ba he's knew exactly how is, Musamman ɓoyayyyun halayanta wanda suka bai yana ada ta hanyar binciken sirri da yayi. Granny haɓa ta riƙe tace "Na shiga uku Ni Faɗimatu meye wannan nake? Wacce kalar rashin daraja da ɗaya ce wannan? Saudala anya kina da hankali?" Kuka Mami tasa sakamakon jin Muryar Granny da tayi da sauri ta kalli Barrister suka haɗa ido tana ganin haka tai wajansa da sauri tana faɗin "Allahamdulillah! Allah Nagode maka, wlh Barrister Imam bashi da hankali, mai yasa tsoran Allan sa ya tsaya iya baki ba zcy ba, na shiga uku wai wacce kalar rana ce wannan nake gani,ace Ɗan mijina yana ƙoƙarin aikata zina dani, da naga wannan ranar gwamma naga ta mutuwa ta, Barrister dan Allah kayi hqr domin wannan ba shi ne karo na farko ba, ya cimma burinsa da buƙatarsa a baya, amma yanzu nayi ƙoƙarin kare kai na, daman Imam ya daɗe yana ƙwaɗayin jikina wlh ɗan iska..," ba ƙarasa faɗar haka ba Granny ta sauke mata wasu kyawawan maruka guda biyu a kuncinta tace "Ashe gantalewar taki harta huce tunanin duk wani gantalalle irinki? Tsabar giyar hauka na ɗibanki ki rasa wanda zaki laƙa bawa zam can banza da iska sai Imamu? Bin mata ki kaga yanayi ko menene? Wlh sai na kira maki police yanzun nan" Mami ko kallon Granny ba tayi ba ta riƙe Barrister tace "Believe me Barrister wlh yaronka bashi da gsky, ko ba'a kai na ba, Imam yana da good relationship between he and matarka Fannah, And cikin dake cikinta ma ina da tabbacin na Imam ne ba naka ba" wani jiri ne ya ɗebi Fannah zata faɗi Granny tai saurin riƙeta tana faɗin "Mugun nufinki da sharrin ki ya koma maki ka, Yarinyar dako kallo bata ishi Imamu shine kike jefansa da wannan gantalallan bakin naki" sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe bakin zaninta, tare da face majina wayarta ta ɗauko ta fita waje tana faɗin "Wlh sai Allah ya saka mini, kaf zuri'a ta babu ɗan tasha dan haka kwanan siteshan ya wajaba a gareki shashasha, da ɗuwawo kamar dutse" Fannah kasa koda mutsi tayi idanunta akan Sheikh tana jin kanta na mugun sara mata, abin duniya yay mata zafi, shin da gske wannan cikin na Sheikh ne? Wata zyar tace mata "nasa ne mana, idan bashi ba waye ya taɓa kusantarki" jiri ne ya ɗebeta tayi baya zata faɗi Sheikh dake tsaye yana bin kowa da ido yay saurin riƙeta, Barrister kam ganin abun yake kamar a mafarki ya daɗe yana tunanin wasu abubuwa da yawa amma ya kasa fahimta, shin da gske ɗan cikinsa shike neman matansa? Ko Wannan dalilin ya sanya yaƙi yin Aure ne? Innalillahi wa'inna ilaihir, kallon Sheikh yay da yake riƙe da Fannah wacce gaba ɗaya tama rasa Meke faruwa da ita sbd ko ƙoƙarin zame jikinta ba tayi bata da wani kuzari sbd wani shork daya sameta, cikin jarumta da nutsuwa haɗi da kamewa Sheikh yaja Fannah zuwa saman bed ta zauna, lokacin ko iya buɗe idanunta ba ta son yi, bata ƙaunar Sheikh a yanzu bata sonsa gaba ɗaya, amma mene yasa wannan tunuwar Sirrin ya girgiza tunaninta ne? Meyasa taji sam bata ƙaunar Sheikh ya tuzarta idan mgnar ciki ne zata zubar dashi kowa ya huta, amma mgnar da ake cikin wajan watansa uku zuwa huɗu. Barrister ya ƙarasa inda Sheikh yake tsaye yana ɗan lumshe idanunsa, yana zuwa yace "Imam da gaske ne abinda na keji? Ko kuma sharri ne?" Gajiyayyun idanunsa Sheikh ya buɗe ba tare da tsoron fargabar komai ba yace "Gata can ai saita ƙarasa maka bayani with her evedance" yana faɗin haka ya shige bathroom ɗin dake maƙale a jikin bedroom ɗinsa, Juyawa Mami tayi ta ɗauki wayarta ta shiga gallery ta shiga nunawa Barrister photons da video, rufe idanunsa yay Yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi, da sauri kuma ya saki wayar ya nufi inda Fannah take zaune. Tana ganinsa ta miƙe tsaye da raguwar kuzarinta Ta fara ja baya sbd wutar masifar data gano cikin ƙwayar idanunsa. Yana zuwa ya cafki hannunta tare fisgarta zuwa waje, gaba ɗaya binsa take kawai sbd tasan ita ɗin me laifin ce ta kuma cancanci Duk wani hukunci da Za'ai mata. Suna fita Mami ta saki wani shu'umin murmushi cikin zcyarta take faɗin "You're the best Saudat, u did a great job Wow! Finally Duk yadda za'ai Sheikh sai ya amshi cikina matsayin nasa, daga nan kuma zan san duk yadda nayi na raba Fannah da nata cikin, at the end all his property will become mine, Wow Saudat you're lucky" ta faɗa tana girgiza kanta tana jin komai ya kusa zuwar mata ƙarshe all her dreaming is going to be true. SHEIKH na shiga bathroom ya kifa kansa a tsakiyar shower ruwa ya fara dukansa, ganin abin yake kamar a mafarki but komai dake faruwa is in real life, _"Ya rabb!"_ ya faɗa a taushashe yana furzar da wani zazzafan huci daga cikin bakinsa, ganin ruwan shower bazai masa sbd sosai yake jin zafin zcyarsa na dawowa saman fatarsa, zame kayan jikinsa yay ya ɗura saman hanger kana ya cika jacuzzi da ruwa mai sanyi ya shiga ciki. A hankali ya janye idanunsa tare da Numfashinsa, ya fara shigewa cikin tafkeken jacuzzi wanda ya cika da ruwa, yadda baya fidda numfashi hakan yasa ruwan ya samu damar shigewa cikin hancinsa da kunansa. Granny na fita ta samu Anut Amina tai jigum tace "Maza kira min ƴan sanda yanzun nan wannan munafukar sai ta kwana a gidan ƴan sanda" Anut Amina tace "Granny abin bakai nan ba, nasan Sheikh he'll never do that, amma mubi komai a sannu har a gane Gsky, a bar abun a sirrince sbd bayyanar Sheikh Matsayin babban Malami wanda ake ganin girma da kuma darajar sa, kinga idan aka fitar da mgnar waje everyone zai kalli Sheikh Matsayin bad man and hakan kamar anyi cin zarafin sa ne, an tuzarta tashi a idanun jama'a" Granny tace "Kefa ba ruwana babu abinda zai samu Imamu kamar yadda nake matsa addu'a amma dole ƴan sanda suzo yan zun nan, idan ba zaki kiramin su ba ki faɗa nai waje na nemu taimako wajan jama'a bokan nan babu wanda bai iyata ba" Girgiza kai kawai Anut Amina tayi domin tasan abune mai wahala Granny ta fahimci matsayin Sheikh a idanun jama'a Wayar ta amsa ta kira mata number as she said! Barrister na zuwa part ɗinsa ya cilla Fannah saman kujerar yana mata kallon tsaf kafin cikin ɗaga murya yace "Wannan cikin na waye, nawa ne or Imam?" Shiru Fannah tayi sai Idanunta daya cika da hawaye ta fara shassheƙar kuka jikinta ya ɗauki rawa, hannu yasa ya miƙar da ita tsaye cikin tsawa yace "Am not talking to you? Cikin waye Fatima da gaske wannan cikin na Imam ne? How long Kika ɗauka kina cin amanata? Ace ciki a jikinki kuma cikin ɗa wanne kalar jakanta ne wannan,wlh idan baki gayan cikin waye wannan ba sai na yanka ki ɗakin nan" Zubewa tayi a ƙasan wajan ƙafafuwansa ta saki kuka mai tsuma zcy tace "Na sani i made a very big mistake, amma wlh is not my fault, na gaya maka bana sonka i don't love you anymore amma u don't understand all my feelings, meyasa yanzu zaka tsare ni akan abinda bana da ikon hanashi faruwa? Meyasa tun farko baka janye qudirinka na Aure na ba ka barni da wanda zcyta take so kuma take ƙauna, dan Allah kada ka matsa akan abinda kai zai iya sawa a ɗaure ka" Kallon tsaf yay mata yana wani jinjina kai kafin yace "Wa me? Ni za'a ɗaure bama a ɗaure ki da wanda yay maki cikin ba? Ke Ni ba wannan ba ina magana akan wannan cikin na jikin ki na waye? Wane Ubansa ni Hamdan ko kuma ɗan cikina za ki haifawa ɗa? Wannan cikin ɗa na ne ko kuma jikana tell me Fatima". Kuka tasa sosai ta kasa mgna ƙasan zcyarta kuma tsoro da tsanar abinda tayi haɗi da tsanare Sheikh suka ƙara dirar mata, amma bata ƙaunar Sheikh ya tuzarta bata fatan hakan, belet ɗin jikinsa ya zare yace "zaki gayan ko sai na farfasa maki jiki yanzun nan" kasa mgna tayi sai kuka da take tana jin gaba ɗaya duniyar tayi mata zafi duk kukan da take tana jin abin cikinta na mutsawa kamar yasan akansa ake wannan masifar. Zarara mata belet ɗin yay wanda tsabar gigitar da tayi yasa ta faɗi ta fasa wani uban ihu tare da birgima domin sosai belet ɗin ya sauka a fatar jikinta sbd ƙananan kaya dake jikinta. "Wlh idan baki faɗa min cikin waye ba you'll regret for what you did" Ya faɗa yana ƙara sakar mata wani dukan zafin daya ƙara shigarta yasa numfashinta ya fara sama sbd rabon da wani ya daketa a rayuwa harta manta, azaba tai mata yawa tana jine yana faɗin "Ok, wannan dalilin yasa kike gujemin ko? Bari nai yadda nasu a nan daga nan kuma sai na zubar da cikin kowa ya huta" jin haka yasa Fannah ta buɗe Dukkan muryarta ta ƙwalawa Sheikh kira. Yana cikin jacuzzi ɗin babu alamar numfashi na fita a tare dashi sbd yadda yay kwance luff cikin ruwan, kamar a gabansa yaji saukar muryarta tana kiran sunansa, fisgo Numfashinsa yay da ƙarfi wanda yake ƙoƙarin barin gangar jikinsa nan da nan ruwan ya fara mutsi amma har yanzu ya gagara fitowa daga cikin ruwan sbd yadda ruwan ya shige masa cikin jikinsa. A karo na biyu ya ƙara jin muryarta sai dai a yanzu a rarrabe ta kira sunansa da _"She....ikhhhh!!"_ wani irin zabura yay yana jin yadda santsin jacuzzi yake ƙoƙarin yadda shi amma ya tattaro dukkan wani karfinsa da jarumtarsa ya miƙe tsaye, idanunsa sunyi jajir jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa saman goshinsa. Jikinsa na zubda ruwa musamman gashin ƙirjinsa dana kansa, haka ya jawo bathrobe ya sanya jikinsa, yana layi kamar ɗan ƙwaya idanunsa na rufewa ya nufi waje yana dafe bango a yadda ƙirjinsa da zcyarsa ke bugawa kawai yasan tana cikin matsala wani abu ya faru da _Zahraaansa_. Fannah ganin da gske Barrister yake sbd ta miƙe a hankali ta tattaro dukkan ƙarfinsa ta hankaɗa sa baya, ta fita da gudu zuwa downstairs. Mami waya take da dukkan alamu wayar mai muhimmanci ce tace "kar kaji komai, badai Barrister yay sign a file ɗin nan ba? To da wannan za muyi amfani mu tirkesa, kuma munyi amfani da motar Company Sheikh ne, amma hakan ba yana nufin zamu ɗura alhakin kisa a kansa bane, a'a komai zai tafi akan Barrister wannan contract na yarjejeniyar kisan bashi ka bashi yay sign akai ba?" Daga can ɓangaren Mutumin ya ɗan saki dry yana murza kan motar yace "Exactly! Abin farin cikin files ɗin Property Sheikh dake wajan Uncle e shine na kawowa Barrister matsayin contract ɗin da yake nema, kinga muna da evedance wanda zamu tirke Barrister ya kaisa har gidan yari" Farin ciki fal ranta tace "Kana da brain wlh, Yayinda Barrister ya shiga hannu a nan ni kuma zan fara nawa aikin wajan ganin na mallaki komai na Sheikh, amma kayi duk yadda zakai Sheikh kada yasha super ok" Mutumin yace "Kada ki damu kin san waye ni, akan dukiya zan iya komai, amma kiyi duk yadda za kiyi Sheikh ya amshi cikin jikinki hakan shi zai bamu damar yin komai cikin sauƙi" Miƙewa tsaye tayi lokacin da ihun Fannah ya daki kunnanta tace "Ok kada ka damu kaji komai zai tafi successful" Jinjina kai yay yace "Where is my Cutie hope tana Lfy" tace "Yeah! She's fine I'll catch you later bye" Tana faɗin haka tayi hanging up na kiran. Sheikh na zuwa parlon Fannah na sakkowa daga upstairs idanunta a rufe abin mmkin kuma gaba ɗaya kansa tayo hakan yasa ya daidaita tsaiwarsa gudan faɗuwa, Anut Amina gyara zama tayi tana kallon ikon Allah, Granny ta saki sbd Fannah hijab ɗin jikinta ya cire daga ita sai wani crazy jeans iya cinyoyinta wanda suka ƙara girma, ga half vest cibiyar ta a bayyana ne, wanda cikin jikinta ke sawa tai wannan shigar sbd bata son zafi ko kaɗan, idanun Sheikh a rufe ya shiga mutsa bakinsa yana tasbihi da neman kariyar Ubangiji, sbd gaba ɗaya kansa ya toshe. Fannah na zuwa ta faɗa jikin Sheikh wanda yay dai-dai da tsayawar numfashinta, haka kuma yay dai-dai ta isuwar Arjun da kuma Police ɗin da Granny ta kira wanda mata ne suka shigo mazan suna waje. Barrister shima ya sakko downstairs ɗin yayinda Mami ta fito idanunta yay faca-faca da hawaye. Shigar da ita jikinsa yay a ruɗe kuma ya fara girgiza ta yana ɗan buga kumatunta yana faɗin _"Wake up Zahraaah, don't do this to me ki tashi nothing will happen to you ok!"_ Ganin haka yasa Anut Amina miƙewa ta nufi wajan fridge ta ɗauki ruwa mai sanyi, karɓa Sheikh yay yana ɗaukan ta cak zuwa duguwar kujera, gaba ɗaya suka tsora masa ido Arjun mmki ya hana shi tambayar abinda yake going on! Buɗe ruwan yay tare da shafa mata a fuska, amma ko mutsi ta ƙiyi hakan yasa Sheikh tsorata baya son nuna gazawar sa at all amma Sheikh itace weakness nasa, zai iya loosing control ɗinsa akan ta. Uwa ba gudan jininsa dake jikinta baya son rasa ɗaya daga jikinsu domin su biyun yake kalla ya samu nutsuwa a zcy, miƙewa yay da ita a jikinsa da sauri Barrister yace "Stop Imam, Fatima is my wife not urs ka gane, kada ka sake ƙoƙarin yin wani abu a gareta, duk ko biyun you'll pay for what you have done". Ko tsayawa Sheikh bai yi ba yaci gaba da tafiya Barrister yace "Wlh Imam idan baka sauketa ta faɗa min cikin waye a jikinta ba zan tsine maka, ka bari na ƙarasa kasheta idan yasu tayi bayani a lahira" Cak Sheikh ya tsaya jin kalmar Abban nasa, a hankali ya sauke numfashi yana ɗan taune leɓansa kafin ya juyawa gaba ɗaya ya kalli mutanan Parlon har da police ɗin cikin jarumta da cikar haibarsa da zallar murmushi a fuskarsa yace. "Ok Abba! Amma bari na fara taimakon ta ta samu numfashinta I'll explain you everything" yana faɗin haka ya sanya tattausan bakinsa a saman nata wanda ya jiƙe da yawo gaba ɗaya Parlon suka ɗauke kansu banda Mami wacce take jin zcyarta na bugawa, a sanyaye ya zare ribbon ɗin kanta gashin ya bazo a saman fuskarta wanda ya haddasa rufewar bakinsu dake haɗe jikin na juna, cikin nutsuwa ya maida dukkan hankalinsa ya fara hura mata iskar bakinsa zuwa cikin bakinta yana Murza tsakiyar tafin hannunta, babu jimawa taja wani wahalallan numfashi tana ƙoƙarin sanya wani kukan yay saurin danne mata baki da nasa, cikin ƙamshi da kuma ɗanɗanon bakinsa yasa ta haɗe bakinsu domin ta tabbatar da abinda ta keji, a wahalarce ta buɗe idanunta wanda sukai ta sauke saman Kamila fuskarsa mai cike da haiba, idanunsu ya sarƙe cikin na juna, a hankali ya dinga juya tongue ɗinsa cikin bakinta Wheel idanunsa na cikin nata yana hango zallar soyayyarsa a cikinsa amma wani banzan dalili nata ya hana ta fahimci abinda yake ranta. Idanunta taja zata rufe ya ɗan daki kumatunta hakan yasa ta ƙara ware su a hankali ya fara bata wani hot kisses wanda ya daɗe bai samu ba, Yadda yake mata kaɗai zai sanya ta fahimci yadda yay missed ɗinta. Bakinta ta ware hakan yasa nata bakin ya ƙara shiga cikin nata ciki so da ƙaunarsa wanda yake ƙasan zcyarta ta fara bashi wani lafiyayyan kiss mai tsayawa a zcy Sheikh ji yay yana ƙoƙarin zubewa sbd ƙafafuwansa dake rawa gaba ɗaya ya manta da Mutanan wajan _Zahraaaah_ kawai yake kallo a gabansa dama bayansa, zai ɗauki ko wanne abu wajan kareta bai damu a kansa ba indai Zahraaah zata samu kwanciyar hankali da nutsuwa harta kula da abinda yake cikinta. Arjun ya ɗan saita murya kana yace "Buddy" sai kuma ya buga kujerar wajan, da sauri Fannah ta zare bakinta ta sauka jikinsa tana ƙoƙarin guduwa yay saurin haɗata da jikinsa yana kifa fuskarsa a cikin gashin kanta. Granny bata son lokacin da tace "Muhammadur Rasulullah (S.A.W)" sai kuma ta sanya kuka. Arjun yace "Sheikh me kake haka ne? Kana cikin hankalinka kowa?" Fesar da iska yay idanunsa ya ware ya kalli Barrister hakan nan yaji baya jin nauyinsa kamar da, Barrister wanda ya kejin zcyarsa kamar zata fashe ƙarar yake ƙoƙarin rasa damarsa yace "Are you done? Yanzu explain cikin waye a jikinta?" Fannah kunya ta kamata tana jin kamar ta nutse a wajan, bata san me Sheikh ke taƙa ma dashi ba, amma gaba ɗaya ta nemi tsanar da tayi masa a yanzun ta rasa, jin Sheikh ya shafa jikinta tare da ɗauko mayafin Anut Amina ya naɗe mata jikinta dashi. Tsaiwarsa ya gyara yace "Da Zahraaah da abinda yake cikinta duk nawa ne, i love her kamar yadda nake son kaina da Rayuwata, zan iya bada raina da dukkan abinda na Mallaka akanta, mai Soyayyar gsky fansar rai yake bayarwa akan wanda ya keso bawai ya ɗauki ran wanda yake so ba". Barrister wanda har huci yake yace "Imam ni mahaifinka kake faɗawa haka? Ni kake tarayya da matata ta sunna har kai mata ciki?" Lumshe idanunsa yay ya ƙara buɗewa akan Barrister yace "cikin Zahraaah, nawa ne kamar yadda tun a sali na sameta a kamilalliyar mace, wacce bata san kowanne Namiji ba sai Ni" Kan Barrister ya sara da ƙarfi saman ya daɗe da zarga ashe Fannah ce dalilin samuwar ƙafar Sheikh? Kenan bai taɓa kusantar ta ba ko me? Kasa mgn yay sai cewa yay da yay Maam "arrest him, zanyiwa lawyer na mgn" yana faɗin haka yay upstairs yana dafe kai, Kasancewar Ƴan sandan mata ne hakan yasa ɗaya ta fita ta kira sauran mazan suka nufi inda Sheikh yake tsaye. Arjun da Granny sukai saurin yin wajan Arjun yace "Officer stop muyi mgn anan basai anje gaba ba" wani kallo Officer yay Arjun yace "Malam kai zaka faɗa aikin mune? Babu wanda ya isa ya hana mu tafi dashi sai wanda akaiwa laifin" Fannah ta rikice a yanzu idan aka tafi dashi wa take dashi? Ta rasa mahaifinta ta rasa kawonta kenan bata da sauran wanda zai taimaka mata kuka ta saki Sheikh ya kalleta da idanunsa wanda suka ɗan tara ruwa yace _"I promise to be everything to you! I will take care of you! I will stand by you a ko'ina a kuma ko Yaushe, zan maye maki gurbin koma you've lost, sannan i promise to be your family Duk da kina dasu, Don't cry Again come here Zahraaah Jewel"_ Da sauri ta nufi wajansa tana zuwa ta shige jikinsa ta saki kuka tana rirriƙesa mgn take son yi tace ya tafi da ita duk inda za'a kaishi kada ya barta za tafi samun nutsuwa idan yana wajan, Arjun ganin abun Babba ne ya fita waje idanunsa cike da waye tausayin su Sheikh wannan Soyayyar tasu Forbidden love ce wacce tarayya da junansu haramun ne, kai tsaye number Aliyou Eneye Ahuoyza Deen ya kira domin yay masa hanyar samun babbar lawyer nan Queen Maimunatou Moon. Officer ya fara janye Sheikh, da saurin Anut tace "Dan Allah Officer ku rabu dashi ka bari ai mgn a wajan nan ko me kuke so za'a baku" Officer yace "Mgnar babbace and nasan Sheikh yana da kuɗin da zai babu da komai Amma Uban daya haifesa shi ne ya bada umurnin kamasa" Sheikh rungome Fannah yay sosai idanunsa na ɗan tsiyayar da hawaye kana yay kissing bakinta da hancinta da goshinta da wuyanta, ya ɗura bakinsa a kunanta yace "I love You Zahraaah i love You! I love you so much please take good care of yourself and my unborn child" Yana faɗin hakan ya saketa yana jin Anut Amina na zura masa jallabiya tana sakin kuka, Officer ya maƙalawa Sheikh sarƙa a hannu, ya fara jansa Granny ta kalli Officer tace "Allah ya tsine maka La'ananne mugu azzalumi, kai dai ba zakai albarka ba kuma wlh saika sakar min jikana" kuka Fannah take kamar ranta zai fita tana kiran sunan Sheikh Anut Amina ta riƙeta mutuwar Uncle Sham ta dawo mata sabuwa da yana nan da wannan duk bai faru bazai taɓa bari a tafi da Sheikh ba. Suna zuwa baƙin ƙofa ya tsaya tare da juyawa ya kalli Fannah dake kuka yace "Just wait for me Jewel" yana faɗin hakan ya fita kai tsaye motarsu suka sashi Allah yasa motar a rufe take Arjun yabi motar yana faɗin "Don't worry Sheikh you'll be safe" yana faɗin hakan motar ta fita da gudu zuwa police station.... SIRRIN MU Contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:38 - 🤔🤔: The Evedance 81-82 Da sauri Arjun ya juya tare da komawa cikin gidan yana zuwa ya samu Granny a Parlo tana faɗin "Haihuwar asara, to gidan na kawonka ne da zaka shigo mana? Yau naga sabuwar gantalewa fisabilillahi ni Faɗimatu, wlh gidan zan bari ba zan iya tsiya tunda ake ƙoƙarin kashe min jika nima kashe ni za'ai". Anut Amina ta kalli Arjun tace "Arjun yanzu da gaske sun tafi da Sheikh? Innalillahi wa'inna ilaihir" Arjun yace "Kada ki damu everything will be ok Anut Amina,bari na kira wata lawyer in sha Allah zata tsaya masa". Anut Amina tace "In sha bazai taɓa tuzarta ba in sha Allah". Lafewa Fannah ta sakeyi a jikin Anut Amina tana sakin ajjiyar zcy lokaci ɗaya wani zazzaɓi ya kawo mata ziyara hakan yasa Anut Amina ta kama hannunta zuwa part ɗinta. Tea ta haɗa mata mai kauri ta bata, da ƙyar Fannah ta samu tasha rabi, jikinta na rawa ta kwanta Anut Amina ta ware mata A.c ɗakin kana taja mata kofa tai waje. Barrister yana shiga part ɗinsa ya rufe tare da sanya dry tace "Na san me nake, da biyu nayi wannan, na jefi tsuntsun biyu da dutse ɗaya, you're lovely and smart hamdan, komai ya kusa zuwa ƙarshe komai zai dai-dai am going to be a richer old man hhhh!". Wayarsa ya dailing number Alhj Kamal ringing ɗin farko ya ɗaga daga can ɓangaren Alhj Kamal yana zaune a office ɗinsa yana sauraran complain ɗin wanda yake son Alhj Kamal ya shige masa gaba a shari'ar da za'ai wanda ake tuhumarsa da yinwa wata yarinya fyaɗe, Numfashi ya sauke yace "Barrister kira da rana haka meke faruwa?" Barrister ya saki Murmushi yace "Aiki zakai min" Alhj Kamal ya kalli mutumin kusa dashi yace "Excuse me sir" kana ya baya mutumin baya yace "Uhm aiki akan menene? Kuma wanne irin aiki?" Barrister yace "Zan kai Sheikh court, ina son ka zama lawyer da zai kareni har na samu damar kai Sheikh gidan yari". Wani shu'umin murmushi Alhj Kamal yay yace "Wannan ba damuwa ba ne ai, kawai ka shirya evidence masu ƙarfi wanda zamu haɗa mukai Sheikh ƙasa". Jinjina kai Barrister yay yace "Sai Mgnar Saudat cikin jikinta ba nawa bane, shima ina zargin na Saudat ne". Miƙewa Alhj Kamal yay tsaye kafin yace. "Ba abin mmki bane, idan harya tabbata cikin Fannah nasa ne to babu shakka wannan ɗin ma nasa ne". "Haka ne kam, ba za'a ɗauki lokacin zuwa Court ba, dan haka ka shirya" Barrister ya faɗa yana kallon files ɗin gabansa. Alhj Kamal yace "Ko da gsky ko babu gsky irin wannan shirya ƙaryar mun saba ta, amma akwai abinda zakai min wanda shi ne zai zama gift ɗin shari'ar idan munyi nasara". Barrister yace "kada ka samu zan maka komai" Alhj Kamal yace "Uhm kafa sanni Hamdan, nasan komai naka kada lokaci yazo kace ba haka ba" Barrister yace "Haba babu abinda zan iya ɓoye maka a yanzu ai, kai dai kawai kayi aikinka nima zanyi nawa". Sallama sukai Alhj Kamal ya kalli mutumin gabansa yace "Yanzu kai da gske kai kayi fyaɗen ko bakai bane" kai tsaye mutumin yace "Da gske nine, amma babu abinda kuɗi ba yayi shiyasa ma nazo wajanka domin kayi hanyar da za'a kori shari'ar baki ɗayan ta" Alhj Kamal yace "Banda 4m Mgnar zata mutu" ba ɓata lokaci yay masa transfer kana yay waje abinsa hankali kwance. Arjun kai tsaye gidansa ya nufa ya shaidawa Aliyah komai wacce cikinta ya tsufa, shiru tayi tana mmkin abin tace. "Dear da gske kuma cikin na Buddy ne?". Arjun fuskarsa ba walwala yace "Shine damuwar ai, da ace ba nasa ba ne abin da sauƙi, amma ya amsa yace nasa ne, nasan Sheikh tun ba yanzu ba baya ƙarya hakan baya give up akan abinda yake so, he love Fannah so he can do anything for her wlh". Cikin damuwa Aliyah tace "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Meke shirin faruwa ne". Cikin damuwa Arjun yace "Wlh baƙin ciki na rasa numbers da nayi a wayata yanzu wannan sim ɗin ba komai bane a ciki, ina da try number King Aliyou Eneye Ahuoyza taƙi shiga" Aliyah tace "His wife is my friend, since muna school, munyi boarding school tare da ita Moon ɗin Dad ko?" Cikin farin ciki Arjun yace "Yeah! Queen Maimunatou Sarauniyar Nufaz (Littafin Moon)". Dry tai masa tace "Ga number mene gift ɗina?" Yace "Zan maki kiss guda ɗari yau, banda special abun, and zan siya maki littafin _ABU_MALEEK_ wanda kike ta naci nasan bazai fi ƙarfi na ba" Rungome sa tayi tace "Wow thank you so much ko iya littafin Anut Na'ima ka siyamin wlh ka biya, zanji Abu Maleek da ƴar makauniyar sa, da kuma sauran matansa guda biyu" Miƙewa tsaye yay yace "Naƙi wayon kiss ne dai sai nayi" Yana faɗin hakan yay dailing number a wayar Aliyah yadda za tafi saurin ɗauka. Lokacin da aka isa da Sheikh police station aka fara bincike ba taɓa lokacin Sheikh ya amsa yace da mai cikin da cikin nasa ne kuma duk mallakina ne, gaba ɗaya police ɗin suka tsaya suna kallon Sheikh yadda yake mgna a hankali kuma a nutse with confidence, nan take aka tura Mgnar court domin a yankewa Sheikh hukunci dai-dai da abinda ya aikata. Miƙewa tsaye yay yana lumshe idanunsa tare da motsa bakinsa yana tasbihi ga Allah, a yadda ya kejin sanyi a ransa yasan nothing will happen to him, no more separate with us in sha Allah!. Ƴan sanda biyu ne riƙe dashi suna nufar ɗakin da zasu kaisa kafin gobe a zauna zaman Court, suna ƙoƙarin sanya Sheikh ciki sukaji ance. "Tsinannu La'anannu, wlh kodai ko Haihuwar asara, shegu dakai kamar tankarar". Da mmki Suka tsaya suna kallon tsuhuwar shi daman Sheikh tuni ya fahimci muyar Granny yana dai tsaye idanunsa a lumshe yana jiran yaji wanne kalar zagi zata ƙara. Ɗaya daga cikinsu yace "Haba tsuhuwa wanne abune haka zaki dinga mana zagi a nan, kefa uwa ce, kin haifi kamar mu". Bakin zani ta zare ta fara sharce hawaye tace "Muhammadur Rasulullah (S.A.W) wlh ban haifi gantalallu kamar ku ba, kaf zuri'a ta Babu ɗan ta'adda" police ɗin yace "Haba Baba mu ce maki akai ƴan ta'adda ne? Aiki muke kuma samu akai komai mukai masa akan aikin mu ne, bawai dan ya cancanci ai masa ba, kuma banda abinki ai shi jikan naki ya amsa dukkan laifin da ake tuhumarsa akai, kawai kuje ko fara shirin zuwa Court" Zare ido Granny tayi tace "Ko me? Koto ba, wlh billahi baku isa ba, sai dai na kwana a nan wajan" Bai ƙara kulata ba ya tura Sheikh cikin ƙaramin ɗakin da ake sanya marasa Gsky, Kuka Granny tasa Anut Amina dai lamarin yafi kusa fin ƙarfinta Suda suka zo belin Sheikh sai kuma ai Mgnar court anya wannan abun babu zamba ciki? Tayaya mutum kamar Sheikh za'a akaisa Court Fisabilillahi! Da ƙyar taja Granny zuwa waje ta nemi wani D.S.P yace mata "Hajiya gobe misalin 10:30 za'a zauna a court kawai abinda zance maku ko nemi lawyer" yana faɗin haka yay cikin office ɗinsa. Anut Amina lallaɓa Granny tayi har zuwa mota kana ta shiga itama taja motar zuwa gida. Arjun ya saki ajjiyar zuciya jin an ɗaga kiran cikin Muryar girmamawa yace "Allah ya taimaki Fulanin Nufaz ya ƙara mata Lfy" daga can ɓangaren Jakadiya ta kalli Moon wacce take zaune tana duba wasu files tace "Allah ya ƙara girma da ɗaukaka ya kareki daga sharrin mutum da aljan, me Nufaz gaba ɗaya Giwa kike mai ban tsoro, kura mai kwarjini a idanun jama'a" murmushi Moon tayi tace "Meke tafe dake" kai tsaye Jakadiya tace "Kira ne daga Abokiyar ki, amma ba ita take mgn ba Mijinta ne" Amsar wayar Moon tayi kana Jakadiya ta fice, tana kara wayar a kunanta King Aliyou na shigowa hannunsa riƙe dana babban ɗan sa wanda ya kusa kamashi a tsayi. Gyaran murya Arjun yay yace "Assalamu alaiki Fulanin Nufaz Allah ya ƙara Lfy,Mijin Aliyah ke magana" amsawa tayi idanunta cikin na Deen kafin tai ƙasa da murya tace "Uhm ya akai?" Arjun yace "Muna buƙatar taimako ne akan wata Shari'a wacce za'a gabatar gobe" girgiza kai tayi kamar yana gabanta tace "Anya! Ba lokaci fa" kamar Arjun zai kuka yace "Taimakon Addinin Musulunci za kiyi, nasan idan kikaji wanda tsautsayin ya faɗa kansa zaki taimaka" handsfree tasa tace "waye?" Kai tsaye yace "Sheikh Imam hamdan Balarabe" da sauri King Aliyou ya kalleta tare da jinjina mata kansa tace "Ok akan mene?" Gyara zama yay shima yasa wayar handsfree ya shiga bata labarin komai na rayuwar Sheikh daga lokacin daya fara son Fannah har zuwa yanzu. Deen ya amshi wayar yace "Goodness! Ku shirya Evedance we'll be there in sha Allah!" Daga nan sukai Sallama farin ciki ya cika zcyar Arjun, tashi yay ya shirya tare da yiwa matarsa Sallama. Gajiyayyun idanunsa ta buɗe wanda sukai mata nauyin gaske tana jin kanta na sarawa kamar zai rabe gida biyu, cikin rashin kuzari ta ƙarasa buɗe idanunta tare dayin addu'a ta miƙe zaune, jikinta taja ta Jinjina da frame ɗin gadon Idanunta suka shiga tsiyayar da ƙwallar tausayin kansu Musamman Sheikh da abin yake shirin fin ƙarfinsa. Hannunta ta ɗura saman cikinta wanda ya fara girma tana jin soyayyyar cikin na ratsa ko ina na jikinta dama zcyrta, da ace zata iya zubar da cikin da Tabbas zata zubar domin ta ƙaryata Barrister, amma ta fahimci Sheikh yafi son cikin fiye da komai, ta hangi zallar so da ƙauna a idanunsa, shafa cikin ta fara a hankali tace "Am so sorry sweetheart! A kanka ake wahalar da mahaifinka pls help me to find a solution" ta ƙare maganar tana fashewa da kuka tana faɗin "ya ruguza rayuwarsa because of me, Ya rabb ka kawo min ɗauki" turo ƙofar akai tare da rufewa aka shigo, ƙarasa shigowa Anut Amina tayi ta zauna kusa da ita, hannunta tasa ta ɗago kanta tace "Haba Fatima mene hakan? Ba dai kiyi believe kina son Sheikh ba?" Da sauri Fannah ta ɗaga kai, Anut Amina tace "Then why kike ta kura kanki, kin san mene zaki ki taimakawa Sheikh ai" Baki buɗe Fannah take kallon Anut Amina kafin ta girgiza kai tace "i don't know what should I do, wlh ban sani ba kai na ya toshe Anut Amina dan Allah ki taimaki rayuwar mu nida Malamina kada ki bari a cutar da shi, bashi da kowa wanda zai taimakesa sai ke da Granny da kuma Arjun dan Allah ki taimaki Malamina, wlh zcyta sam ba zata ɗauka ba". Kanta Anut Amina ta shafa tana maida hawayen idanunta tace "Kada ki damu ki dage da addu'a a wannan daren in sha Allah babu abinda zai samesa sai alkairi, amma kuskure Imam yayi tunda bashi da wata shaida ta kare kansa" Girgiza Fannah tayi tace "Akwai shaida Anut Amina nice shaidarsa" Anut Amina kallon anya kina da hankali kowa tai mata tace "Wacce shaida kike da ita?" Miƙewa tsaye tayi tana ɗaukan duguwar riga ta sanya saman ƙananan kayanta tace "Nice Shaidarsa zance nina sanya yay tarayya dani, bada son ransa ba" Miƙewa tsaye Anut Amina tace "Ke back to your right sense please, mgn ake wacce Hankali zai ɗauka, kowa yasan Sheikh Nigeria dama gefenta idan kice kikace ya kwanta dake shi kuma saiya kwanta? Bayan yasan illar hakan? Abinda kukai fa Babba ne matsayin matar mahaifinsa kike da ance wanine ma daban shine, daga jiya zuwa yau na fahimci maƙiyan Sheikh tun yana jariri kawai bani da hujjar kamasu ne, dan haka addu'a zamuyi kawai idan bashi da haƙƙin akan abin zai fita cikin ruwan sanyi" Kuka Fannah ta ƙara sawa tana faɗawa jikin Anut Amina "Ba zan iya ba idan har akace za'a rufesa wlh sai dai a haɗa dani, domin nima mai laifi ce bawai ta ƙarfi yay min ba, dan Allah ki taimaki zuƙatan mu kada ki bari zuciyoyinmu suyi nisa da juna". Rungometa Anut Amina tayi tace "In sha Allah I'll try my own Best, ki daina kukan idan kikai sanadiyyar cikin ya zube ko ya samu matsala fa? Kin san shi ne Abu mafi muni dazai ruguza zcyarsa shi ne zai iya rusa farin cikin sa, kiyi addu'a, muje kici abinci kiyi wanka zuwa safiya muga abinda hali zaiyi" Hannunta taja sukai waje a Parlo suka samu Mami tana Shirin fita suna haɗa ido ta watsawa Fannah harara, ita kam ko inda take bata sake kalla ba, da ƙyar ta samu tasha tea ɗin da fatan dankali wanda yaji bushasshen kifi. Mami na fita kai tsaye police station ta nufa bata sha wahalar ganin Sheikh ba, yana zaune ya tanƙwashe ƙafafuwansa idanunsa a rufe bakinsa na mutsawa a hankali yana Istigifari! Gabansa kuma wani bushasshen abinci ne da ruwan leda guda ɗaya, domin Barrister yace kada a bashi wani abinci mai kyau.. Hannu ta miƙa zata riƙe nasa hannu dake jikin ƙarfan ƙofar yay saurin zame hannunsa, murmushi tayi tace "Ok! Bazan taɓa ka ba idan baka so, nazo maka mafita ne, idan ka yarda ka amshi cikin jikina ni kuma nai al'ƙawarin Taimakon ka, domin idan ka bari kaje Court to tabbas za'a rufe ka ne baki ɗaya za'a haɗa maka da sharrin da baka san dashi ba" Kamar yadda bai motsa ba haka bai buɗe bakinsa ba, shi sam bai damu ba ko hukuncin rataya za'ai masa abinda ya keso kawai Jewel tai farin ciki, ta haifa masa abinda yake cikinta yana da tabbacin zata kula dashi bayan ita ga Anut Amina ga Granny, duk zasu iya kulawa da jininsa. Ɗan sanda take kanta yace "Hajia lokaci ya kusa fa" Mami tace "Look sweet Imam wlh zan fitar dakai domin koshi Barrister a yanzu idan nayi niyyar ɗaure sa zan ɗaure sa, shima yanayin komai a ƙarƙashi na ba tare daya sani ba, nasan cewa jikin Fannah naka ne sannan nasan cewa cikin jikina ba naka bane, haka kuma ko nakasar daka samu Mahaifinka shine sila, kuma shine silar rabaka da mahaifiyarka wanda har yanzu ba'a san inda take ba, akwai muhimmin abinda Barrister yake ɓoyewa a tare dakai wanda har yanzu nima ban sani ba, amma ka yarda ka karɓi cikina ka maidani matarka ta kwanciya a ɗaki, ina sonka Imam ina son komai naka, amma ni duk abinda zanyi babu wanda ya isa ya kamani, Mgna ta ƙarshe kuma mutuwar Uncle Sham ba tsautsayi bane ganganci ana tsane aka shirya hatsarin, kuma anyi amfani da motar Companynka, ko iya wannan zan iya amfani dashi wajan ganin an rufe ka amma bana buƙatar haka" Miƙewa tsaye tayi tace "kayi tunanin kafin mu haɗu a court gobe. Duk inda Arjun da Anut Amina zasu samu evedance na kare Sheikh a Court sun nema sun rasa, time to time kuma suna communicating a waya Shida Moon, itama ta shiga damuwa domin wannan shine karo na farko da Shari'a zata kaita ƙasa, kuma ta ɗauki alwashin fidda Sheikh amma ba wata hujja da zata nuna haka sai tabi duk ta damu kanta, Murmushi kawai Deen ke mata yasan zatai winning na shari'ar kawai ta takura kanta sbd rigima. Da daddare Fannah kasa bacci tayi, a daren kuma ta gayawa su Ya Falta komai dake faruwa hakan yasa sukace suma zaso zo goben. Hankali ya tashi Gashi yanzu har ƙarfe 7 na safe ba hujja ba dalilinta, Barrister kam tunda ya fita cikin daren bai sake dawowa gidan ba, hakan yasa Anut Amina ƙara gasgata zargin da take masa. Yana durƙoshe gaban wani baƙin Mutum wanda ya cika jikinsa da layoyi kala daban-daban yace "Duk yadda za'ai ayi Sheikh ya ziyarci gidan yari bana son ya fito sai na samu cikar muradin rai na" Bokan yay dry yace "Kaga wanda ya yarda da duniya ya manta da lahirarsa, ai tun tuni kayi sake ɗan zaki ya girma kalli nan" Jikin Barrister na rawa yace "Me zan gani waye wannan kamar Deedat? Bayan an tabbatar min ya mutu" Dry bokan yay yace "Wannan shi ne babban kuskuren da kayi, ka manta da baya gabanka kawai kake hange" Dafe kai Barrister yayi yana jin wani gumi na keto masa, kana ya kalli Bokan yace "Mene mafita?" Bokan yace "Kaga ciki mai manta kyautar gobe, kasan abinda muka saba ai idan kana son aikinka yayi". Ba ɓata lokaci Barrister ya zame wandonsa ya juyawa bokan baya, just like yadda maza da maza suke abinsu, suna gamawa Barrister yay waje kai tsaye kuma ya nufi Federal Court of Appeal, domin Lokacin tara da wajan Ashirin, yana hanya Alhj Kamal ya kirasa yake shaida masa babbar lawyern da zata tsayawa Sheikh, tashin hankali ya bai yana akan fuskar Barrister sai kawai ya juya kan motar zuwa wani waje daban. Court ta cika sosai da mutane domin harda wanda ba'ai tunani ba, Fannah na ganin Ya Falta da Yakura ta saki kuka tana riƙe su, rarrashinta sukai kana suka nemi waje suka zauna, Anut Amina na gefe Granny sai share hawaye take, Mami da Bahaiyya na can waje guda, Fareeq kam baka iya gane halin da yake ciki. 11 dai-dai Al'ƙali ya buga guduma Court ta zauna, kai tsaye ya buƙaci ganin wanda ake ƙara ƴan sanda suka nunawa Sheikh waje yaje ya tsaya, kana akace ana neman mai ƙarar kamar daga sama a kaga Barrister ya miƙe tsaye ya nufi wajan shima, Al'ƙali ya karantawa Sheikh laifinsa idanunsa cikin na Fannah ya amsa da "Uhm, da cikin da mai cikin duk nawa ne" Al'ƙalin yace "Ke nan kana nufin da gske kai ne kayi mata cikin" kafin yay mgn Fannah ta miƙe tsaye tace "Ba haka bane, ƙarya yake, nice wacce na tilasta masa kwanciya dani bashi da laifin komai, yana son ɗurawa kansa laifi ne kawai" Guduma Al'ƙalin ya buga tare da tsawatarwa Fannah yace "Is an order, Kada wani ya sake mgn ba tare da bashi dama ba" rubuce² Al'ƙalin yay kana ya buƙaci ko wanne lawyer ya gabatar da kansa, kai tsaye Alhj Kamal ya gabatar da kansa akan shike kare mai ƙara, nan fa tunani ya sauya Anut Amina ta fara duba wacce akace itace Lawyer Sheikh, babu ita babu labarin ta, A hankali Deen dake cikin Court ɗin ba tare da kowa ya lura dashi ba, nan Shima ya fara juya idanunsa yana son yaga ta inda matar tasa zata bayyana, jikin Al'ƙalin na faɗin "Malam Sheikh Imam hamdan Balarabe ko dai baka da lawyer ne?" Miƙewa Deen yay Yana ɗan covering jikinsa da Alƙyabbar jikinsa, kai tsaye waje yay dan bai son idanun jama'a su dawo kansa, Anut Amina ma miƙewa tayi ganin haka yasa Hankalin Fannah tashi zata miƙe Yakura ta riƙeta, shi kam Sheikh ko a jikinsa idanunsa a rufe bakinsa na motsa amma rabin tunaninsa yana kanta, da yana da hali babu abinda zai hanashi rungome ta ya rarrashe. Al'ƙali ya hana duk wasu ba yana da aka bashi daga ciki hadda vedio'n hannun Mami wanda Alhj Kamal ya bayar, gyaran murya yay bayan ya ƙara tambayar Sheikh akan ko yana da hujja dazai kare kansa tunda bashi da lawyer, banza Sheikh yay masa sai buɗe idanunsa kawai da yay, yana buɗe idanunsa ya sauke a kanta wani tattausan murmushi ya sakar mata yana nuna mata cikinsa sai kuma yay mata nuni da tayi Shiru tsit tayi ta shiga sauke ajjiyar zuciya idanunsa ya juya kamar ance ya juya ya hangi Muhammad Jalal Kabeer bobo shida Jalilerh zaune suna kallonsa. Guduma Al'ƙalin ya buga kana ya mayar da glass ɗin idanunsa ya shirya takardun gabansa yace "Bisa ƙwararan hujjojin da suka mata da kuma amsa aikin da mai laifin yayi wannan Court mai adalci ta yankewa Sheikh Imam hamdan Balarabe hukuncin....," Shiru yay sbd jin murya daga baƙin ƙofa bana faɗin "Adakata!!!" Gaba ɗaya mutanan suka maida hankalinsu Miƙewa Barrister yay Sheikh kuma ya ɗan furzar da iska daga cikin bakinsa yana juyawa a hankali Arjun ne a farko, sai Anut Amina hannunta riƙe ta dairy, sai kuma Mama kolo da Yagana, daga can baya kuma wani farin mutum ne da alama shima prvt investigation ne, gefe guda kuma wata farar mata ce wacce tasha ado da wani farin lace amma gefen kanta a fashe yake yana zubda jini, sai Deen dake riƙe da hannunta fuskarsa tai jajir, da sauri aka ware mata rigar ta Deen ya amsa ya sanya mata, hakan na nuni da cewa itace Queen Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen, kuma lawyer mai kare Sheikh Imam hamdan Balarabe... SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:38 - 🤔🤔: Who Is The Killer 83-84 Gaba ɗaya cikin Court ɗin yay shiru idanun jama'a suka dawo kansu Deen, da Arjun da Anut Amina tare Mama kolo haɗi da Yagana. Gyaran murya kaɗan Moon tayi wanda yasa Deen fahimtar abinda take nufi, zame hannunsa yay a nata daf da kunanta yace "All the best My Queen" yana faɗin hakan yaja baya tare da nufar inda Muhammad Jalal Kabeer bobo yake zaune tare da Jalilerh. Cikin nutsuwa Moon ta ƙarasa kallo guda tayiwa Alhj Kamal ta ɗauke kai, kafin ta maida kallonta ga Sheikh, kusan numfashinta ne ya kusa tfy, duk yadda Mijinta yake da kyau da kwarjini amma ƙafar Sheikh Imam hamdan Balarabe Deen bai kama ba, ga wata nutsuwa kamala, da haiba uwa uba kwarjini wanda kallo ɗaya Mutum zai masa ya cika masa idanu. Shiru ne ya biyo baya, Arjun da Anut Amina suka nemi wajan zama, Mama kolo da Yagana suka zauna suma, Al'ƙali ya buga guduma Court tayi shiru, jin shiru yay yawa yasa Moon ta miƙe kamar yadda Al'ƙalin ya bata dama, gyaran murya tayi irin tasu ta matan manya da kuma sarauta tace. "Sunana Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen, nice lawyern wanda ake a ƙara Ngd" Rubuce² Al'ƙali yay kafin ya ɗago kai yace "Shin Lawyern wanda ake ƙara tana da hujjar da zata kare wanda Court take tuhuma akan yima matar mahaifinsa ciki?" Miƙewa Moon tayi tana gyara zaman rigar jikinta kanta a ƙasa tana duba wasu takardu kafin tace "Ya mai girma mai Shari'a kamar yadda kace tun farko tuhumarsa ake ba'a tabbatar ba, kuma wanda ake tuhuma ya amsa laifinsa da dukkan gskyar zcyarsa, to anawa ɓangaren haka abin yake Tabbas cikin jikin Fannah Baba Baa'na cikin Sheikh Imam hamdan Balarabe ne..," ihun Court ta ɗauka aka shiga surutai, Barrister kallon Moon kawai yake hakama Alhj Kamal suna jiran suji ta inda zata kare Sheikh daga wannan abun, guduma Al'ƙalin ya buga akai shiru da idanunsa ya kalli Moon yace "Muna jinki" gyara tsaiwa tayi tace "Uhm! Hujja ta farko tabbatar da cewa cikin jikinta na Sheikh ne" wata paper ta ɗauko wani ya karɓa kana wani ya amsa ya miƙawa Al'ƙali, dubawa ya fara yaga gwajin halitta ne, kuma ya tabbatar da jinin Sheikh dana babyn cikin Fannah abu guda ne, ajjiyewa yay kana tace "Sai abu na biyu, wanda ake tuhuma bashi da laifin komai hasali ma ya samar da cikinne ta hanyar da ake so,hanyar da Addinin Musulunci ya sharaɗanta" nan ma shiru tayi kafin ta juyawa sukai ido huɗu da Barrister sai kawai ta ɗauke ganin yadda zufa ke wanke masa jiki, hakama Mami da Alhj Kamal, juyawa tayi idanunta ya sauka akan Deen ya kashe mata idanu, tare da jinjina mata hannunsa, murmushi tayi tace "Bisa dugun binciken dana fara tun jiya zuwa yau, to Allahamdulillah duk wani binciken da nayi ya tabbatar min da cewa Fannah Baba Baa'na halaliyar Sheikh Imam hamdan Balarabe ce, Ma'ana Matarsa ce ta sunna" a hankali ya shiga ware idanunsa yana sauke numfashi kaɗan² bakinsa na mutsawa yana faɗin _"Astagafirullah wa'atubu ilaik!! Astagafirullah wa'atubu ilaik!! Astagafirullah wa'atubu ilaik!!"_ Jajayen idanunsa ya sauke akan Fannah wacce itama shi take kallo zuciyoyinsu suka shiga bugawa a lokaci ɗaya, yayinda numfashinsu ya fara daidaituwa dana juna, idannunsu a manne, suna jin mgnar kamar dirar mikiya, Sheikh taune leɓansa yay yana son ya tabbatar da abinda kunnuwansa suke faɗa masa amma ya kasa, wani ƙyakƙyawan shock ya kama Sheikh, ya kasa koda mutsi ya zama kamar wani statue. Moon da take kallonsu tace "You have a right to that, kana da ikon kallanta as much as you can, Fannah is your wife" da sauri Barrister ya miƙe tsaye yace "Ƙarya ne, wlh matata ce, ƙarya ne, nina na bada sadakin ta, Ni nace ina sonta ba shi ba, matatace dani aka ɗaura mata Aure bada Sheikh ba" Barrister ya faɗa cike da tashin hankali jikinsa gaba ɗaya gumi ya wanke sa, Al'ƙali ya buga guduma nan take Court tai shiru cikin bada umarni yace "Is an order Kada wanda ya sake mana magna idan ba haka ba yanzu hukunci ya hau kansa" Gyara tsaiwa Moon tayi Idanunta na kan Sheikh tace "Ina son Court ta bani damar tambayar Sheikh Imam hamdan Balarabe wasu tambayoyi" kai tsaye Al'ƙali yace "Court ta baki dama" cike da ƙwarin qwiwwa Moon tace "Sheikh da gske cikin dake jikin Fannah naka ne?" Jajayen idanunsa ya buɗe yana kallon ta kafin ya janye idanunsa ya mayar kan Fannah wacce tai lamo jikin Ya Falta tana sakin ajjiyar zcy sbd kukan da taci ta ƙoshi, ganin da gske bashi da niyyar mgn yasa a hankali Moon tace "Amsar ita zata tabbatar da abinda nake son faɗa a gaban jama'a" fesar da numfashi a hankali yasa tattausan hannunsa ya shafa fuskarsa zuwa gemunsa wanda yake ta ƙyalli, kamar bazai mgn ba sai kuma ya janye idanunsa yana faɗin _"Ya Allah"_ a zcyarsa, a fili kuma ya fidda wani emotional sound kafin a hankali yace "Da cikin da mai cikin duk Mallakin Sheikh ne" jinjina kai Moon kana ta buƙaci ganin Fannah, a hankali ta tashi cike da tsoro sbd sam bata sama tsaiwa gaban mutane irin haka ba, bayan ta tsaya kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta jikinta duk rawa yake, Moon tace "Shin akwai wata halaƙa ta auratayya data taɓa shiga tsakaninki da Barrister Hamdan Balarabe?" Kasa mgn Fannah tayi sbd tambayar tayi mata girma, tsora mata shanyayyun idanunsa yay shima yana so yaji me za tace, domin shi gaba ɗaya ya manta da wannan tunanin ya manta da cewa wani abu zai iya shiga tsakaninta da Abbansa, a karo na farko tsoro da fargabar abinda zata faɗa ya kamasa, addu'a yake idan wani abun ya fara kada Allah ya nufeta da faɗa, dan sam zcyarsa ba zata ɗauka ba, a hankali Fannah ta girgiza kanta cikin sanyin murya wacce ta kama dishewa sbd kuka tace "Babu komai, tun zuwana gidan kawo yanzu" wata Ɓoyayyiyar ajjiyar zcy Sheikh ya sauke yana rufe idanunsa wani sanyi ya fara ratsa masa zcy, jinjina kai Moon tayi tace "Idan Court ta amince zan fara gabatar da shaidun da zasu tabbatar da cewa Fannah matar Sheikh ce" Al'ƙali ya bada dama Moon ta buƙaci ganin Arjun, cike da ƙarfin quiwwa Arjun ya tsaya kana ya gabatar da kansa a gaban Court matsayin mai bada shaida, wayarsa wacce ta samu matsala ya ɗauko yace "A ranar da Allah yaywa Uncle Sham Kawon Sheikh rasuwa wayata ta samu matsala, kafin rasuwarsa ta riskemu ina tare da matata a kitchen naji shigowar saƙo wayata, ban samu damar dubawa sbd wayar ta faɗa cikin hug ɗin tea, tun daga rana na cire sim ɗin na ajjiye ta, na duba ko zanga wanne saƙo ne ya rage a cikin sim ɗin amma ba komai duk sun zauna a wayar, to cikin ikon Allah yau na ɗauko hanyata ta zuwa Court na fara biyawa police station kamar yadda Queen Maimunatou ta buƙata, bayan muntattauna da ita, zamu tawo Court ɗin na samu kira daga matata, tace nai sauri nazo akwai hujja mai ƙarfi dazai kare Sheikh,jin hakan yasa na tafi Queen Maimunatou kuma ta shiga mota ta nufi Court, ina zuwa na samu wayata ta dawo dai-dai kai tsaye kuma ta nuna min saƙon dake jiki" jinjina kai Moon tayi tace "Ko Arjun zai iya karanta mana saƙon yadda kowa zai fahimta?" . Wayar ya buɗe yace "ga saƙon kamar haka;" _Assalamu Alaikum, Mohd na turo maka wannan saƙon ne a lokacin da nake jin kamar bazan iya samu damar faɗar wani Sirrin da baki na ba, da farko ka kula da Imam bashi da wanda ya fika, sai Granny ita kuma wannan a Kullum ƙarfinta ƙara jaa yake, Sheikh yana cikin magauta da maƙiya, na san halinsa mai ɗaukan ƙaddara da rashi Yadda da mutum, amma kai tsaye bazai fahimci wanda suke son kaisa ƙasa ba, abu mai muhimmanci shi ne FANNAH ba Matar BARRISTER bace, matar SHEIKH, na buƙaci abun ya zama sirri sbd na fahimci ita zata zama silar samun ƙafafuwansa Kuma Thank God ya samu lfy, haka kuma ya tabbatar min da Sheikh yayi tarayya da mace ne, ka gaggauta sanarwa da Imam wannan mgnar domin akwai gobarar da take shirin tunkaro sa, bayanin Auran sa da FANNAH da kuma bayanin cikakken Tarihin rayuwar Sheikh yana cikin Dairy na kasa Anut Amina ta ɗauko maka, ka bata hqr sosai ta kula da Huda, ta ɗauki ƙaddarar rashi na, abu na ƙarshe kuma kamar yadda jama'a da kuma ko kuke tunani Sheikh ba ɗan Barrister ba ne, na barku lfy realy miss you so much Arjun ka kula da Sheikh na baka amanarsa!_ Shiru Court tayi, Barrister ya susuci ga samu ga rashi, tayaya? Yaya akai Uncle Sham ya san da wannan Mgnar? Meyasa bai tunanin ɗaukan mataki akan Uncle Sham tun tuni ba? Yanzu duk shekarun daya ɓata ya tashi a banza kenan ko mene? Da ƙarfi ya furta "Ina it can be possible" kallonsa akai a wannan karan hadda Sheikh a kallonsa, tunanin Sheikh da yawa amma ya rasa wanne zai fara, idan ba Barrister bane mahaifinsa to wanene mahaifinsa, mai yasa Fannah ta zama matarsa bayan bai taɓa ganinta ba bare yace yana sonta? Ko kuma ƙaddarar haɗuwa da Airah ita ta haɗasa da Fannah, ada no one replace Airah in his heart, amma yanzu Fannah ta maye gurbin Airah ta samu matsayin da Airah bata samu, wannan da burin samu Allah ya ɗauki ranta. Al'ƙali ya buƙaci ganin Anut Amina tare da Dairy, gabatar da kanta tayi kana ta fara buɗe shafin Farko na Dairy inda aka rubuta. _“TUSHE”_ Deedat da Hamdan yaya da ƙani ne, amma sun haɗu ne ta hanyar Uba uwa kowa da tashi, Hamdan ɗan stepmom ɗin Deedat ne, tun suna yara Allah ya bawa Deedat baya ta tsara art ga kuma son mulki, dan haka tun a secondary school aka fara bawa Deedat muƙami, hakan ya fara damun Hamdan sbd shi mutum ne mai hassada da kuma ƙyashi, amma baya taɓa nuna tsanar Deedat yana barin komai cikinsa ya iya takunsa, mahaifiyar Deedat ta mallaki Property da yawa wajan iyayenta da suka rasu ya rage daga ita sai ni Shamsudeen da nake rubuta wannan bayanin, ni ƙanin mahaifiyar Deedat nan wato Khadijertou, a haka rayuwa ta fara tsayi Deedat ya manyanta, a haka iyayen sukai tafiya babu wanda ya dawo da rasa sosai Deedat ya shiga tashin hankali bashi da kowa saini, daman familyn ba yawa garemu ba, yawanci ba'a ƙasar suke ba, haka dukkan ƙadarorin Khadijertou ya dawo mallakin Deedat Balarabe, ya fara juya kuɗi a lokacin ni kuma ina da aure matata ta fari amma ban taɓa haihuwa ba, ganin Deedat ya mallaki hankalinsa yasa nabar ƙasar, kwanci tashi Deedat ya zama shararran mai kuɗi, hakan yasa ya nemi wata matashiya dangin Kanuri ya aura, watan ta biyu ciff da Aure, akaiwa Deedat ƙuruciya yabar garin baki ɗaya, a hankali kuma aka sanya mota ta takashi, amma sam Deedat bai mutu ina ji a jikina yana raye, ya tafi yabar matarsa da ciki wanda bai san dashi ba, a lokacin ne kuma na dawo Nigeria da zama tare da sabuwar matata Amina sbd Allah yayiwa ɗaya matar tasa rasuwa, ba tare da binciken komai ba aka sanarwa Hamdan cewa Deedat yay hatsari ya mutu motar da ƙone tare dashi, hakan yasa ya ɗauki ragamar komai na Deedat ya barni kaɗan daga ciki nake juyawa, kulawar matar Deedat ya dawo ƙarƙashin Hamdan ba wanda ya san tana da ciki, sai ita da Hamdan ɗin, domin koni basu yarda na sani ba, kullum yana nuna mata sai ta haifesa lfy za'a sanar, lokacin da cikinta ya cika watan haihuwa a lokacin ta fara tsanar cikin sbd asirin da Hamdan yasa akai mata, dan haka tana haifar Imam ta tsallake ta barsa aka ransa inda tayi, sai Hamdan yay farin ciki ya bawa Saudat riƙon Imam, daman tunda ya aureta ya shaida mata cewa Mahaifiyar Imam matarsa ce, daga nan kuma yaje ya ɗauko Granny mahaifiyar Balarabe wato kaka wajan Deedat kenan, kana ya ɗaure mata baki, bokan Hamdan ya tabbatar da cewa idan har bai ɗauki mataki akan Sheikh ba to Tabbas shi ne zai kawo ƙarshen sa, sai ƙwace komai na dukiyar mahaifinsa Deedat, dalilin haka idanun Hamdan ya rufe yasa aka mayar da Imam gurgu tun yana zanin goyo, Saudat Granny sukaci gaba da kula da Imam cikin Aminci" Shiru Court tayi kowa ya fara surutu, Granny kam kasa mutsawa tayi, kanta ya fara sarawa ta shiga tunanin abubuwa da yawa, Sheikh kam kansa motsi yayi, ya sunkuyar ƙasa tare da sulalewa a wajan ya shiga fidda numfashi idanunsa na janyewa tari na son kawo masa ziyara, da ƙyar yake fisgar numfashinsa sbd nauyin da zcyarsa yake masa, tabbatas an zalunci kamaninsa da mahaifansa. Share hawaye Anut Amina tayi kana tace _“MAFARI”_ lokacin da Saudat ta fahimci kaf Dukiyar Barrister ba tasa bace itama ta shiga ƙoƙarin ganin yadda zatai ta samu kasu fiye da rabi na Dukiyar, har kawo lokacin kuma bata son cewa Shaikh ba ɗan Barrister bane. Rashin, Barrister yayi abu baya tuna baya Deedat lfyarsa ƙalau, Yayinda kuma matarsa ta koma daginmu dake Niger da zama, wata rana naje Dubai yin oder sabbin kaya na company Sheikh kamar daga samu naga Deedat nai mmki sosai domin har lokacin bai tagayyara ba, kuɗi da hutu sun zauna masa, daga nan kuma na fahimci yana da babban matsayi sai dai ban san matsayin mene ba,muna haɗuwa matarsa ya fara tambaya ko da nace muje ya koma Nigeria sai ransa ya ɓaci hakan ya tabbatar da kurciyar da akai masa ta nan, ya amshi number na daga ya huce, kwana biyu tsakani ya dira a Niger sunyi farin cikin ganin juna sosai, babu wanda ya tambayi Imam, Deedat bai san da Sheikh matarsa kuma an saya mata mantuwa, daga nan suka sauyawa sabuwar Rayuwa haka kuma ban sake ganinsu ba har kawo yanzu dana rubuta wannan abun" Nan ma shiru Anut y tana share shawaye, Deen kam jin abun yake wani iri ace ɗan uwanka na jini shine bai ƙaunarka, mai yasa kuɗi keson hallaka jama'a ne, murmushi kawai yay sbd tunawa da Oga Damus da yay, Muhammad Jalal Kabeer bobo yay ƙasa da murya dai-dai kunan Deen yace "kana tunawa da tashin bom ne?" Harara Deen ya watsa masa yace "Yeah! Of course, kamar yadda kake tunawa da Governor Mubarak Yahya cibo, Jafar, right?" Taune baki Jalal Kabeer bobo yay yana Rungome Jalilerh yace "Forget the past amma serious sun cutar min da my Jalery?" Ya faɗa yana matse Jalilerh, Anut Amina ta ɗura da faɗin _“REVENGE”_ A lokacin da Barrister ya gane cewa a koda yaushe abubuwa na iya juya masa, kuma ya fahimci halin Saudat da abinda take niyya, kuma ya gane cewa ɗa ɗaya shi ne nasa a cikin yaran da Saudat ta haifa, sai ya ɗauki niyyar ɗaukan fansa ta hanyar ƙarin Aure ya samu wacce zata haifa masa yara masu yawa, cikin Sa'a kuma ya haɗu da Fannah, a lokacin da Barrister ya buƙaci naje wajan Kawo Madu domin mu tattauna dashi nayi mmki sosai, ɗan uwan wajan mijin ƙanwar mahaifiyar matarw Deedat ne, hkne nima ƙanwar mahaifiyar Mamana ta ce, Shira mukai sosai, kafin Kawo Madu ya gayamin cewa Fannah bata son Auren hakan yasa na gaya masa ra'ayi na ina son a juyar da auran kan Sheikh, daga nan nai masa bayanin komai, haka Kawo Madu ya Sanarwa da Baba Baa'na ranar ɗaurin auren aka shaida ɗaurin auren Sheikh Deedat Balarabe, da Fannah Baba Baa'na, domin nace kada a bayyanar da sunan wanda aka ɗaura auran dasu, babban farin ciki na kuma babu abokan Barrister suna can waje shi kuma ya gidan Kawo Madu, aka ɗaura aura na bada kuɗin sadaki a aljihu na, kuɗin Barrister kuma sunan a ajjiyewa kamar yadda ya bani, Abu guda ya ragewa Sheikh a yanzu shine sanin inda iyayensa suke, sannan kaf Dukiyar da Barrister ya tara ba kuɗin sa bane haƙƙin mallakar Sheikh ne, a nan na kawo ƙarshen Rubutu na Allah ya yafe min bisa ɓoye wannan abun da nayi na barshi matsayin SIRRIN MU nida Kawo Madu da Baba Baa'na" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un kawai mutane suke faɗa, Barrister kam tuni ya fara zaucewa, murmushi Moon tace Anut Amina tace ta zauna, Alhj Kamal ya miƙe tsaye yace "Ina da mgn yamai girma mai Shari'a" Al'ƙali yace "an baka dama" Alhj Kamal ya kalli Fannah yace "Shin daman dai kina da ra'ayin tarayya da Sheikh, kuma mgnar baki taɓa haɗa shimfiɗa da Barrister ba ƙarya ne, Sannan..," shiru yay sbd salatin da yaji Granny ta tafka, zumbur Granny ta miƙe ta nufi inda Alhj Kamal yake ta shiga tafa hannu tana faɗin "Muhammadur Rasulullah (S.A.W) wlh kai dai babu kai a ganin Annabi, ba kaji Imamu yace da cikin da mai cikin duk nasa bane? Kai dai anyi a sarar haihuwa ka zauna kaita giggilla ƙarya, to babu gantalalle irinka a nan" tana faɗin hakan ta juya ta kalli Al'ƙali tace "Don Muhammadur Rasulullah maza a nan ka yanke masu hukuncin kisa, a fille kan salllamammu" Da sauri Saudat ta kalli Granny Alhj Kamal yace "Wa muka kashe da za'a kashe mu kuma? Ni meye nawa a ciki?" Moon tai Murmushi tace "Ka shirya kare kanka bawai kare wani abuba" guduma Al'ƙalin ya buga kowa yay shiru kana yay rubuce² zuwa wani lokaci kafin ya ɗago kai yace "Bisa ƙwararan hujjojin da wannan Court mai adalci ta samu ta wanke Sheikh Imam hamdan Balarabe bisa zargin sa da akai, sannan Court ta buƙaci Barrister ya bawa Sheikh kuɗi bisa ɓata masa suna da akai" Kuka Fannah tasa tana rungome Yakura farin ciki fal ranta sai shafa cikinta take, da zata iya da babu shakka wajansa za taje ta rungomesa. Gyaran murya Moon tayi tace "Bayan nan Matar Uncle Sham na ƙarar Barrister bisa zarginsa da kashe mata miji da yay" da wani irin sabon tashin y Barrister yace "What? Wlh bani bane ban kashe kowa nayi niyya amma bani bane" gaba ɗaya aka kallesa Al'ƙali yace "Kace bakai bane, kuma kace kayi niyya mekenan?" Sunkuyar dakai kansa yay kafin yace "Tabbas nayi niyyar kashe Uncle Sham, lokacin da zargina ya tabbata a kansa, na shirya yadda za'ai a kashe sa cikin ruwan sanyi a ranar da ya tafi Barno, amma wanda nasa yay kisan ya dawo yace ai sunyi Accident amma wlh bani bane" gyara tsaiwa Moon tayi tace "Idan akai bane kenan Matar kace Saudat tayi kisan kamar yadda ta faɗa jiya" Mami ji tayi cikinta ya juya da ƙarfi zcyrta ta buga bata son lokacin da tace "Kai Ni kuma yaushe na faɗa kuma?" Ka faɗa Moon ta watsa tace "Ai ko abin naku wasa ne, kun iya haɗa abu amma baku san Yadda zaku kare kanku ba, tun jiya na fara shiri na, jiya kinje Police station wajan Sheikh kin faɗa masa maganganu da yawa" daga nan Moon ta ciro wata na'ura ta bawa wani shi kuma ya bawa Al'ƙali, ana kunnawa Muryar Mami ta bayyana duk abinda ta faɗa jiya sai da kaji, Moon tace "Ɗan sandan daya rakaki wajanki ba ɗan sanda bane, shiri na ne, ni Barrister/Queen Maimunatou Aliyou Eneye Ahuoyza Deen" wani fito Deen yay tare jinjina mata, dole Mami ta fito gaban jama'a tace "Zahiri ina son Mallakar Dukiyar da Barrister yake ƙwaɗayi, fahimtar kuɗin bana kowa bane sai na Sheikh yasa na fara tunanin yadda zan mallaki komai nasa, shiyasa na fara shirin ƙulla tarayya dashi amma duk yadda nasu yaƙi, sai na rabo dashi na fara binciken yadda zan samu komai cikin sauƙi, wata rana naje gidan Uncle Sham yana Tsaka da rubutu sai ya tashi yabar rubutun da yake ban tsaya tunanin komai ba na fara karantawa, a nan nagane cewa Fannah matar Sheikh ce, sai na shirya yadda zan lalata ƙusanci dake tsakaninsu bayan nayi haka kuma, na fahimci ina da ciki sai na shirya ɗorawa SHEIKH cikin, ganin Fannah nada ciki sai hankali ya tashi naga kuma a koda yaushe asiri na shirin tunuwa sai na shirya yadda za'a kashe Uncle Sham, amma kafin hakan wani ya rigani domin Barrister yasa an sace motar Company Sheikh, bayan ya bada file ga wanda zai kisan ya sanya hannu, amma wlh Allah bani na kashe su, wlh bani bace Allah ko yarda dani" Barrister ba ya shiga rantsuwa, daga nan Moon ta kalli Alhj Kamal tace "Idan ba Saudat bace, ba kuma Barrister Hamdan bane, kenan Barrister Kamal ne ya kashe su kamar yadda ya daɗe yana cin amanar abokin nasa, harta kaisu ka samun yarinya shi ne yanzu kaci Amanar Abokiyar hurɗar taka kuma kaci Amanar Abokin naka?" Rarraba idanu Alhj Kamal ya fara ya shiga rantsuwa dafe kai Moon tace "Ok Securities za kuga wani a outside ku shigo dashi" ba taɓa lokaci aka fita aka shigo da wani matashi saurayi Barrister! Mami! Alhj Kamal suna ganinsa suka miƙe tsaye aka shiga kallon kallo... Finally dai na warware dukkan wani ƙulli da yake a littafi😨 let's see who is the killer. SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:38 - 🤔🤔: Released From Jail 85-86 Gabatar da kansa saurayin yayi, kana yay Shiru yana sauraran tambayoyin da Za'ai masa, Al'ƙali yace "Malam Adam, ka shirya faɗin gsky ba tare da tsoro ko fargaba ba? Ka shirya zaka faɗi gsky tsakaninka da Allah?" Wanda ake kira da Adam ya ɗaga hakan yasa Moon tace "Adam a tura ka ka saci motar Company Sheikh haka ne?" Kai tsaye ya amsa mata da "Eh" sai ta kuma cewa "A cikin wannan mutanan wanene ya saka wannan aikin?" Adam ya kalli Mami ya dawo ya kalli Barrister kana ya kalli Alhj Kamal, ɗauke ido yay yace "Duk cikinsu ba wanda banwa aiki ba, sai dai duk nai masu aiki ba tare da sanin cewa inawa wani daga cikinsu ba, Hjy Saudat tasa na sace motar bayan haka, Barrister yasa na ɗauko masa motar bisa dararjar kuɗi masu yawa, dalilin hakan kuma na amince nace na ɗauko masa motar, Amma shi ya amshi motar ne yana son a ɗauko masa drugs a ciki (Muyagun ƙwayoyi) daga nan ban san komai ba sai da Alhj Kamal ya rikani ya bani motar ya gaya min abinda ya keso, wato naje na kashe masa wasu mutane, nayi shiru sbd ban san me zance masa, daga nan nace yaban lokaci ina ta tunani sai kawai nace masa bazan iya ba, dan haka na bar masa office ɗinsa" kallo ya dawo kan Alhj Kamal nan Court ta buƙaci ganinsa, tsayawa yay yana sunkuyar da kai kafin yace "Barrister aboki na ne, wanda bani da kamarsa, tunda na fahimci munufarsa na gane irin manyan kadarorin da yake hari na sauya tunani na, Nima na fara farautar abinda yake so, hakan sa muka haɗa ƙarfi guda Shida matarsa Saudat,ita ta fara zuwa waje na a faɗar ta, tasan nasan komai naka, na Aminci mata sai na kawo mata buƙatata, muka fara zumunci har aka samar da Bahaiyya, wacce ita ɗin jinina ce kuma ƴarta ce, lokaci guda na fahimci Saudat bata da imani tun sanda ta gaya min nufinta akan Sheikh, dan haka Nima na janye daga gare ta na fara aikina ni ɗaya, bayan an kawowa Barrister mota naje nace ya bani aro za'a shigo min da kaya, ba musu ya aramin,har yake bani file ɗin drugs ɗin da za'a kawo masa, kuma burinsa a yanzu ya amshi wani file dake wajan Uncle Sham, daga nan na nemi wani bayan Adam yaƙi na bashi kuɗi wajan 5.6m haka yaje da motar yabi ta kansu Uncle Sham, daga nan ya ɗauko min file ɗin, ni kuma na bawa Barrister file ɗin ya samin hannu, domin na shirya ɗura masa laifin kisan, tun daga ranar makashin da yay kisan ya fita hayyacinsa ya zama kamar mahaukaci, yana ta faɗin ya shiga uku, Tabbas ni na sanya a kashe Uncle Sham da sauran Mutanan domin idona ya rufe kunne na ya toshe kuɗi kawai nake gani da jin daɗin rayuwa" nan aka shiga Allah wadai da Alhj Kamal Al'ƙali yay rubuce² kafin yay gyaran murya yace "Bisa dugun nazari da kuma hujjojin da Court suka samu akan wanda yay kisan dan haka bisa adalci a yadda hukunci yake a Muslunci Al nafs bin nafs, a hukuncin Shari'a kenan, In kuma a kotun turanci ne, Section 221 of Penal Code duk wanda ya kashe wani shine kashe shi ake yi inde da gangan ne, dan haka wannan Court ta yankewa Alhj Kamal da Barrister Hamdan Balarabe hukumcin kisa ta hanyar rataya, Barrister hukuncinsa akan Iyayensa daya kashe Alhj Kamal kuma akan kisan so Uncle Sham, wanda yay kisan kuma Allah ya fara yi masa hukuncin tun daga yanzu, Ina fatan wannan abun zai zama izini ga masu son ransu da son duniya fiye da lahira, ace idanun mutum ya rufe akan kuɗi har ya kashe iyayensa, wannan duniya ina zata damu, Allah ya kyauta ya kuma shirya mana zuri'a" gaba ɗaya aka amsa da Amin wata Ɓoyayyiyar ajjiyar zcy Mami ta sauke a zcyrta tana Allah wadai da hali irin na Alhj Kamal gefe guda kuma tana baƙin rasa shi sbd Bahaiyya, Fareeq kasa zama yay lokacin da ƴan sanda suka nufi wajan Barrister yasu tafi dashi. Dishi² Sheikh ya fara ganin sbd wani bugu da zcyarsa ke masa, a hankali ya fara tari ba tare da kowa ya sani ba, Fannah ji tayi dama babu kowa a wajan tana son ta haɗa ido da Malaminta taga irin farin cikin da zai yi, juya idanunta tayi taga bata ganshi ba hakan yasa ta sulale daga wajan tana dubawa a hankali, Anut Amina ma wajan Sheikh ta nufa sbd ganin yaƙi fitowa kusan a tare har suna karo da juna suka ƙarasa wajan, gaban Fannah ya bada sauti sbd ganinsa da tayi durƙoshe yana tari cikin sarƙewar numfashi, ga jini na zuba daga hancinsa, jikinta na rawa da wani irin sauri har tana ture Anut Amina kafin ta ƙarasa wajan jikin Sheikh ya saki Numfashinsa ya tsaya hannunsa dafe da ƙirjinsa dake masa zafi da raɗaɗi, baya Anut Amina tayi tana sakin salati gaba ɗaya hankalin jama'a ya dawo kanta da sauri Arjun ya ƙara so ganin Sheikh haka ya firgita sa, Fannah kam zubewa kawai tayi a wajan ta kasa aikata komai sai rarraba idanu da take, motsin da taji yasa ta buɗe idanunta hannunsa taga yana rawa yana Shirin taɓa fuskarta, sai a lokacin ta gane bai gama ficewa a hayyacinsa ba, runtsa idanunta tayi tana jin yadda yake son jan jikinsa kusa da ita amma ya kasa, buɗe ido tayi sbd tattausan hannunsa da taji saman fuskarta sai a lokacin ta fashimci hawaye ke zuba daga cikin idanunta, dugun yatsarsa ya sanya ya sharce mata hawayen yana ɗan jawo fuskarta dab da tashi, cije lips ɗinsa yay sbd wani irin azabar ciwo daya keji a zcyarsa, dab da kunanta yana ɗan fesa mata Numfashinsa mai ɗumi cikin ƙasa da murya da sarƙewar numfashi yace _"Matata!!"_ shi kawai ya samu damar furtawa ya riƙe hannunta gam yana faɗin sunan Allah, daga nan Sheikh bai sake fahimtar komai ba, sai farkawa yay ya gansa a saman bed ɗin asibiti. Duhu ya fara gani hakan yasa ya maida idanunsa ya rufe a hankali ya shiga motsa bakinsa yana tasbihi ga Allah daya ƙara farkar dashi a duniya, saukar numfashinta ya ji yana dukan saitin ƙirjinsa wanda yake a buɗe slowly ya ƙara try na buɗe idanunsa sosai hasken room ɗin ke damunsa amma bisa dole ya buɗe idanunsa tare da saukesu a saman drip ɗin dake maƙale a hannunsa. Sosai yay mmki domin bai tunanin a asibiti yake ba, kenan duk yadda yaso danne abun sai da yafi ƙarfinsa kenan, cikin ransa yake faɗin _"Zahraaah my wife_, ɓoye min ya ƙare, zaki kasance da Malaminki, yanzu ne ya dace kisan cewa soyayyyar Malami fiye take data sauran maza" a zahiri kuma wani ƙawataccen Murmushi ne ya suɓo ce masa. Saukar numfashinta ya ƙara dukan ƙirjinsa hakan yasa yay ƙasa da idanunsa,ƙuri yay mata idanu ganin yadda take bacci amma sai marai-raice fuska take ga wasu gudun tun hawaye na bin idanunta wanda suka bushe. Ƙyakkyawar fuskarta ya tsorawa idanu yana jin yadda so da ƙaunar Zahraaansa suke ƙara ratsa zcyarsa, ganinta kawai kusa dashi yasa yaji ya nemi duk wani ciwo ya rasa. Ware idanunsa yay ganin kayan da suke jikinta ba sune wanda tasa a Court ba. Kenan kwana yay a asibitin ko mene? Agogon ya kala yana ɗan runtsa idanunsa yaga wajan biyar na Yamma. Kallonsa ya mayar gareta yaga yadda ta riƙe masa hannu, lafiyayyiyan murmushi ya sauke ya miƙa hannu da shirin shafa kanta yaji an murɗa handle ɗin ƙofar, janye hannunsa yay yana mayar da idanunsa a hankali ya rufe. Arjun ne da Ya Falta sai Moon a bayansu tana shigowa Deen ya shigo sai Oga Muhammad Jalal Kabeer bobo shida Jalilerh. Zama suke A hankali Moon tace "Till now yana bacci sannu Sheikh, yanzu dai no more damuwa". Arjun yace "Wlh idanunsa biyu haka yake ai" Bobo yace "Uhm Gulma yake da matarsa ƙilan" mintsininsa Jalilerh tayi ya riƙe hannunta yana bata kiss ba kunya. Sheikh yana jinsu yana ta laluban kalmar da zai faɗa ne, jin Arjun na taɓa sa yasa ya buɗe ido yana ya mutsa fuska.. Gaba ɗaya suka haɗa wajan faɗin _"Congratulations from, RELESED FROM JAIL"_ kamar zai kuka sbd haushin da yaji na katse masa hanzari da sukai bai damu da Ya Falta dake wajan ba ya sassauta Muryarsa yace "Barakallahu fiikuu, Shukkran, but kun shiga rayuwata". Deen yace "Hhh naka wasa ne, idan zakai soyayyyar ka miye namu, tun kafin kayi mukai wanda zan ɗagawa ƙafa cewa ya fini iya soyayyya _ABU_MALEEK_ " Bobo yay dry yace "Kai wannan ai makauniya ta gama dashi bashi da kunya sam" Murmushi Deen yay yace "Kasan garin da suka je ashe akwai wasu halittu kamar huro masu shan jini akai Sa'a ɗaya ya ciji makauniyar tasa, shi kuma Allah ya tsare sa shine daya koma masarauta ya killace ta ba tare da kowa ya sani ba yake bata jininsa take sha har taji sauƙi" Jalilerh ta zare ido tace "Mayya kawai ya aura wannan" Deen yace "Kaji ƴar iya ba kiji ance cizonta akai" Jalal yace "Abin ya fara zuwa da raini kuma da babban likitan ƙashi kake mgn bada Lawyer ba" Sheikh dai yana jinsu amma idanunsa na manne akan Fannah wacce ta fara mutsawa sbd surutun da ake, tashi tayi tana kwaɓe fuska idanunta ya sauka akan na Sheikh da sauri tai ƙasa da idanunta sbd kwarjininsa da yay mata ga wata kunyarsa daya kamata. Moon tace "End of discussion abar dai Sheikh ya huta yaji ɗumin matarsa" Murmushi Sheikh yay yace "Yawwa Queen, tattara su" Miƙewa sukai gaba ɗaya suna masa addu'a ya amsa da Ameen yaywa Moon gdy. Fita sukai hadda Arjun da Ya Falta ganin hakan yasa Fannah ta miƙe yana ɗan motsa bakinta so take ta tambayesa jikinsa amma ta gagara ganin yana niyyar tashi yasa tai saurin yin bathroom. Ba'a Sallami Sheikh a ranar ba sai washegari bai ƙara sanya Fannah idanunsa ba sbd kullum Granny da Ya Falta suna wajan Mama kolo da Yakura da Yagana sun koma. Yana zaune a Parlonsa sanye da wani tattausan farin voyal mai manyan zane wannan karan ko singlet bai sanya ba, ana kallon ƙwantaccen gashin ƙirjinsa da tsinin brest ɗinsa, yana tunanin rayuwa tunanin Abbansa Barrister ya gama cika masa zcy bai taɓa tunanin haka al'amarin yake ba, wato ashe duk rashin kulawar da yake ƙin basa sbd yasan bashi ya haifesa ba, an kashe masa kakanni haka an nakasta rayuwarsa, daga ƙarshe an kashe masa Kawonsa Uncle Sham. Ajjiyar zuciya ya sauke tunaninta ya faɗu masa miƙewa yay bayan ya gama shan lemon power horse energy, cikin nutsuwa yake taka ƙafafuwansa cike da kuzari a haka ya ƙara so babban Parlo yana zuwa tana tashi sosai kwana biyun nan take jin kunyarsa musamman idan ta tuna abinda tai masa a kwanakin baya, Granny tana ganin ta rangaɗa guɗa tace "Ga Imamu Ga Imamu,ma sha Allah Tubarkallah Ubanka sak babu abinda ya bambanta ka dashi" Lumshe idanunsa yay yana kallon hanyar part ɗinta da tabi, sosa kai yay yace "Granny bari na tambayeta ko taga laptop ɗita" kallonsa tayi tace "Wa kuma zaka tambaya" ƙasa yay da idanunsa yana juyawa ba tare da yace komai ba, ƙasa Granny tai da muryarta tana faɗin. "Yau naga ɓatan nono a ƙirjin budurwa, wai wayo zai min, to Fisabilillahi zai hanashi keɓewa da matarsa ne? Ai sai Allah ya tsine min ko Amina?" Anut Amina ta saki Murmushi tace "Haka ne kam, Allah dama ɗaukan ta yay zuwa wata ƙasar suka huta". Mami tana jin Wayar tayi ƙara ta manna a kunne tace "Kayi min al'ƙawarin aiki me kyau amma tun ba'a je ko ina ba suna tare da junansu" bokan ya saka dry yana faɗin "Kinyi kuskure ai, tunda kika sanya maganin kuma ya tashi a banza baki kwanta da yaron ba, gashi kin bari wani ya ganku dan haka aiki ya lalace" Dafe kai Mami tayi tace "Mene abunyi yanzu?" Bokan yace "To Salammiyya har yanzu ruɗun Duniyar bai gama sakinki ba ne?" Girgiza kai tayi tace "Kawai ka faɗa min sai wasa kake da hankali na" tsawa ya buga mata yace "Kaga wacce bata da rabon duniya bare na lahira daman can kuɗin ki nake ci, amma asiri bazai tasiri jikin Fannah bare Sheikh, kullum tana shan yawonsa bai ɗauke da tasbihi ga kariyar da suke samu daga wajan wasu daban, dan haka kiyi ta kanki nai nawa". Yana faɗin hakan ya kashe wayar kuka Mami tasa tana haɗa ido da Bahaiyya ta zabga mata harara tana faɗin "Wlh Mami kin cuci ne Allah kuma zai saka min kin samar dani ta gurɓatacciyar hanya" A hankali Sheikh ya murɗa handle ɗin ƙofar bedroom ɗin Fannah, tana tsaye gaban mirror daga ita ƙaramin towel, frm head to toe ya fara Kallonta yana ganin yadda ta zama babbar mace ga cikinta yay girma yay mata kyau sosai fatar jikinta sai Shinny take, ko'ina na jikinta a murje gwanin sha'awa gashinta yana ɗigar da ruwa ya sauka har baya ya manne da fatar bayanta ga wani sihirtaccen ƙamshi na turaren AL'AJABU dake fita a jikinta, bai san yaya akai ba sai tsintar kansa da yay a bayanta ya zura hannayensa a cikin aljihun wando yana jefanta da wani irin kallo. Ta cikin mirror'n ta hangosa gabanta ya faɗi da sauri ta juya zata shige bathroom yay saurin faɗin "Stop" cak ta tsaya ta rarraba idanu cikin ƙasa da Murya yace "come here" ya faɗa yana ware mata hannayensa kanta a ƙasa ta fara takuwa zuwa inda yake tsaye tana zuwa dab dashi taja ta tsaya ta kasa ƙarasawa, sauke hannunsa yay yana ɗan cije baki a hankali ya juya zai bar bedroom ɗin yaji ta saki kuka tsayawa yay yana ware manyan idanunsa wanda suke a ɗan lumshe, yadda take kukan ya kusa bashi dry dan haka ya maze tare ta nufarta yana zuwa ya leƙa fuskarta yaga da gske kuka take sosai, fesar da numfashi yay a kasalance yace "Meye kuma? Ba nace kizo ba kika ƙi" turo baki tayi tana buga ƙafa cikin rashin Sa'a towel ɗin ya zame tare dayin ƙasa, runtsa idanu Sheikh yay ya shiga kokawa da Numfashinsa hutar kansa ta ɗauke, wata ƙara Fannah tasa tai kansa da gudu tana zuwa ta ƙanƙamesa dan babu inda zata iya ɓoye jikinta sai jikinsa idan tace zata juya to zai gane mata bombom, da sauri ya dafe mirror'n yana ɗan buɗe ido jin zata yar dashi, ƙoƙarin zameta yay daga jikinsa yana son ya ƙara kallon halittar da Ubangiji ya bata, ita kuma ta sake ƙanƙamesa, rungomesa ta yay tsam a ƙirjinsa yana sauke tagwayen ajjiyar zuciya a jajjere, cikin ƙasa da Murya yace "Why? Me yasa kike ɓoye min?" Kuka ta sakar masa tana tura kanta a ƙirjinsa tace "Am so sorry Sheikh" Murmushi yay mai ƙayatarwa yace "Ban ji ba" bakinta ta ɗura saman kunnansa tace "Am sorry Sheikh" matseta yay a yana wargaje gashin kanta yace "Uhm Speak up" cikin sabon kukan ta tace "Am so sorry, Am so Sheikh Imam Deedat Balarabe, Am so Malamina, Am so sorry my one and only, Am sorry my life partner, Am sorry my sweet darling Imam" baya yay suka zube saman bed cikin ƙasa da Murya yace "All this for what?" Maƙalesa tai tana rusa sabon wani kukan tace "Na baka ba dai-dai ba, na baka rashin kunya" lumshe idanunsa yay yana manna softness hands ɗinsa saman cikinta yana murza kaɗan, yana jin yadda Cikin ke zillo dai-dai kunnanta yace _"Cry as much as you can, i got you okey, you'll not die and nothing will happen to you Again Zah....raaaaaah"_ ya faɗi sunan nata a rarrabe, sautin kukanta ta ƙara bai ƙara ce mata komai ba sai shafa cikinta da yake yana ɗan fesa mata Numfashinsa mai zafi a kunne, sai da tayi mai isar ta kafin yace "It's okay, Kada ki sake try na kuka, All this week,i can't sleep well Zahraaah!! i can't Jewel" tana shassheƙar kuka tace "Why can't You sleep" buɗe ido yay yana Kallonta kafin ya fara sama da hannunsa yana ya shiga murza fatar jikinta yace "Am so Hornyi wanted to squeeze your boobs and play with you, but kin hanani" ya faɗa yana shagwaɓe mata kamar ƙaramin yaro har mmk yake mata, ɗauke ido tayi tana faɗin "Sorry" Murmushi kawai yay yana mirginata gefe yace "Am having a strong boner, Am so!! so!! Hard" saurin rufe ƙirjinta tayi Ganin yadda idanunsa sukai jaa har wani ruwa suke a hankali taji ya sakar mata sexy kuka yana ɗan shassheƙa yace "You didn't allow me to touch your boobs, you didn't allow me to suck them, You didn't allow me to kiss you, I only kissed your lips, Uhm Zahraaah Jewel, haba Fatima Zahraaah! Until now we husband and wife you are pushing me away when u are the only wife i have, Am so so biggggggg!!!! And harddddd, pls Zahraaah accept me as your husband no more separate" ya faɗa yana kifa kansa a tsakiyar ƙirjinta yana sakar mata kukan shagwaɓa kamar ba Sheikh ɗin data sani ba, kansa ta riƙe tana jin soyayyarsa a ranta komai take shi take gani Murya bata fita tace "Go ahead Malamina ka bani sabon lessons" sa sauri ya jawota jikinsa yana sakin ƙarƙƙarfar Ajjiyar zuciya idanunsa a lumshe ya haɗe bakinsu waje guda hawayen idanunsa na ɗiga a kuncinta.... 😨😨 this page dedicated to you Jewel💔🤫 but am still angry rigimammiyya! SIRRIN MU isn't free book Contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV✍🏽 22/10/2021, 10:38 - 🤔🤔: Internal Love 87-88 Lumshe idanunsa su duka sukai kowa na sauraran yadda zcyar ɗan uwansa ke bugawa, Fannah ware idanunta tayi wasu hawaye Masu zafi suka shiga sauka daga cikin idanunta zuwa saman fuskar Sheikh, sosai take jin so da ƙaunar Sheikh na ratsa dukkan wata ƙofa da lungu na zcyarta. Idan tace tayi Sa'a tana nufin tafi ko wacce mace dace da samun jini na gaban kwatance wanda yake rewa dukkan maza _(Bai kai My SHAMNERH ba)_ duk wata soyayya da mace ya dace ace ta samu to tabbatas ta gama samu, ta samu miji mai sonta da kuma ƙaunarta, ta samu Namiji mai kishinta da kuma tausayinta, ta samu bango wanda zata jingina taji daɗi, Allah yay mata baiwa ya haɗata da nagartaccen Namiji wanda ya san Aure dama haƙƙin sa. Bakinta yay ƙarya ya faɗi wani aibo a tare da Sheikh sam babu ko kalma ɗaya da zata iya kwatanta da Malaminta dashi, bakinta yay kaɗan wanda faɗin zallar so da kuma ƙaunar da take masa sai dai kawai ta faɗi abinda zata iya ta barwa ganganar jikinta saura tayi aiki a wajan Malaminta! He kissing her mouth like bai taɓa saninsa ba, wani ɗanɗano nada ban ya keji yana ratsa shi banda sauke mata numfashi da wani gurnani babu abinda yake gaba ɗaya jikinsa rawa yake. Bai san mene yasa jikinsa yake saurin bada shi ga Zahraaah ba, baya iya hiding all his feelings to her, yanzu dai yadda yake kissing bakinta ji yake kamar yanzu yasan Zahraaah, koda yake daman ance masu idan suna da ciki komai nasu sauyawa yake, To anan Zahraaansa ta samu wannan baiwar, sau ɗaya kaɗai ya san jikinta amma yana da tabbacin yanzu ya sauya a yadda ya sanshi. Wahalalliyar ajjiyar zuciya ya sauke tare da zare bakinsa daga nata sbd sauyin daya fara ki bazai iya ɗauka wan long time ba tare daya nemeta ba, and bai shirya hakan yanzu ba, yazo ne kawai how is she yaji lafiyan babynsa, sauke numfashi yay a karo na biyu yana ɗan shaƙar ƙamshin dake fita daga wuyanta wanda kai tsaye yake shigewa cikin hancinsa yake bawa zcyarsa nutsuwa.. Ɗago fuskarsa yay ya kifa a Tata, yana tura hannunsa cikin sumar kanta, Cikin ƙasa da Murya yace "Open your eyes Zahraaah!!" Kunya ce ta kamata sbd yadda yake narke mata kamar ƙaramin yaro, duk yabi ya shagwaɓe kamar ba Sheikh ba.. Sassauta Muryarsa yay yana ɗan bawa karan hancinta sumbata yace "Ohyaaaah!! Buɗe Muga" marai-raice fuska tayi tace "Kunya na keji" juyawa yay yaga shi ne kaɗai a cikin ɗakin taɓe baki yana zama ki daina a fili kuma ya sauke nauyin mgnarsa yace "Kunyarwa?" Tana turo baki gaba tare da juya lip's tace "Uhm kai mana" "Niwa?" Ya bayar mata da mgnarta ƙasa mgn tayi yana matsa tafin hannunta tare goga mata Tattausan laɓɓansa a saman fuskarta yace "Speak up, tunda na ajjiye kema You have to do that kinji Zahraaah Jewel" slowly ta buɗe idanunta tare da sauke su a kansa tana kallo kyautar da Ubangiji yay mata, domin samun Sheikh tsayin na miji ba ƙaramin kyauta bace da kuma dace da tayi. Copping face ɗinsu yay a hankali ya kira sunanta yace "Zah...raaaaaah!!!" Har ranta taji saukar zazzaƙar muryarsa wani kalar sabon yanayi ya fara saukar mata tare da kasala, cikin ƙasa da murya dai-dai kunanta yace. "Kin wadata zuciyata da farin ciki, kin haskaka rayuwata da haskenki, kulawarki a gare ni ta musamman ce, hakan ya sa nake jin kaina tamkar sarkin wata masarauta mafi girma da ƙarfin iko. Ina Son Ki, idan nace Ina Son ki kin zarce duk yadda kike tunani, Zahraaah Jewel Ke ce kaddarar da na jima ina tsimayin tarar da ita a rayuwata, zan kasance a duk inda kike, zan tsaya a duk inda kika tsayar da ni. Ina son ki, adadin son da kalmomi ba zasu iya siffantawa ba" Tsayawa yay sbd nauyin da Mgnar tayi masa amma mgna ake ta rayuwarsa babu batun jan aji da tsayawa nauyin baki idan bai gaya mata yadda yake sonta ba wane zai faɗa mata, lips ɗinta ya kama ya shiga tsotsa kana ya saki ya kama karan hancinta then neck ɗinta ya gangara tsakiyar ƙirjinta numfashinta ne ya kusa ɗauke wa a hankali tace "Sheeeee...ikhhh" sai kuma ta sakar masa kuka, tsayawa yay da abinda yake ya manna tafin hannunsa a saman ƙirjinta yana jin yadda yay missed nasu, bisa jagorancin zcyarsa ya ƙara buɗe baki yana shigar da ita jikinsa yace. _"Fannerhhh"_ cak ta tsaya da kukan ta shiga sauke ajjiyar zuciya wannan shi ne first time da taji ya kira sunanta, ji tayi kamar bayan shi babu wanda ya iya faɗin sunanta, bata san lokacin data zagaye hannu ta rungomesa tana sakin dry, tare da jan gemunsa.. Gira ya ɗaga mata tare da kashe mata ido Ya iyali ji tayi ya ƙara tafiya da zcyarta komansa mai kyau ne, dai-dai kunanta ya ɗura bakinsa yana cizon fatar kunanta kafin yace. "Ina jin labarin soyayya ne a da, tamkar tatsuniya, amma a yanzu bayan na haɗu da ke, na gaskata soyayya wata aba ce wadda ke da tasirin sanya farin ciki a cikin zuciya. Ina fatan zaki kasance tare da ni, domin zama maganin damuwata na tsawon rayuwa? Ina Son Ki, Zahraaah Jewel My Soul" Ya faɗa yana ƙara sanye idanunsa cikin nasa, Wheel hannunsa suna ƙirjinta yana murzasu slowly yana jin wani taushi da tsantsin da suke dashi, hawayen farin cikin samun Zahraaah a rayuwarsa ne ya ganganro masa, da sauri ta manna bakinta saman fuskarsa ta shiga kwashe hawayen, cikin ɗan shassheƙar kuka yace. "Tun ranar da na fara ganin ki, na ji a jikina, watarana hannuwanki zasu zamo masharin hawayena, kuma zasu kasance riƙe da ni na tsawon rayuwa, zuciyarki zata zamo makwancina na har abada. Na gode da irin kulawar da kike nuna min a kullum. Ina Son Ki Sosa" Rungome juna sukai a tare cikin Muryar kuka Fannah tace "Thank you God! Thank you for giving a good man, I can't life without you! Without what's my worth life if i get separate from you than I'll get separate from self (My world) because you are the one i most love Madly! You're the only one my eyes want to see, my ears want hear his voice, I LOVE YOU MORE MOST MY SHEIKH MALAMINA!!" Ɓata fuska yay yana ɗan mirginawa gefe ganin hakan yasa tai saurin mirginawa itama tayi ta haye samansa ware idanunsa yay yace "Ke zaki fasan ciki, kin manta bake ɗaya bace" kwaɓe fuska tayi tace "Why are you sad? Meye na ɓata rai" girgiza kai ya tsora mata shanyayyun idanunsa masu narkar da zcyrta kafin yasa hannunsa ya shafi cikinta wanda yake motsi da alama shima yay kewar mahaifinsa yace "Naga da saura na tunda har yanzu anƙi bani special name Ohhhh Ohhhh!!" Sai yanzu taji kunyar faɗin sunansa da tayi tai ƙasa da idanunta cike da kunya tace "Am sorry, ban sakewa" tashi yay zaune tare da ɗaga ta cak ko nauyinta baiji ya sauke ta saman cinyarsa kunya duk da kamata ta shiga ƙoƙarin rungomesa sbd ta ɓoye jikinta, gaba ɗaya ta shagala ta manta ba kaya jikinta naked take, matsawa yay Baya yana girgiza kansa tare dayi mata dry mai ƙayatarwa wacce ta haddasa lomawar dimples ɗinsa tare da bayyanar teeths gave ɗinsa yace "Noo! Pls komai nawa ne, dake da cikin da komai na jikinki it's mine, koda wasa kada ki ɓoyewa idona ganin komai a jikinki, now tell me wanne suna kika ban?" Wani iri take jinta sosai ta kejin idanunsa a ƙirjinta ajjiyar zcy ya sauke a hankali yace "Uhm" ya faɗa yana shafa ƙwantaccen beared ɗinsa mai kyau daya ƙara tsayi bakinta ya shiga motsa wa cikin rawar murya da Kunya tace _"My hubby"_ lumshe idanunsa yay a hankali ya furta "No" turo baki tayi tace _"Excellency"_ nan ma yace "No" ganin yadda kallon jikinta kai tsaye ba shamaki yasa tai gaba tare da kwanciya jikinsa tana saƙale hannayenta a west ɗinsa tace "To faɗi me zance" cije baki yayi yace "A'a kawai sake wani" Shiru tayi tana tunani sai kuma tace _"Nurul hayat"_ rungome ta yay yace "Accepted i like it" tashi tsaye yay da ita a jikinsa yace "Lemme freshen up ki shirya kimin kwalliya, but ban son barbaɗe² ɗin nan just lipstick and perfume" towel ta ɗauka ta sanya bata yarda yaga bayanta ba, shima bai shirya gani ba tace "To nima bana son Zahraaah ɗin nan" yana yin waje yace "Ni ina so" yana faɗin haka yay waje haushi ya kamata wato ba takai matsayin bata special name ba, ya lallaɓa yay mata wayoo shine zai gudu. Yana fita ya samu Granny zaune a saman danning table tana jin farfesun kaza wanda yaji kayan ƙamshi, bai taɓa jin kunyarta ba sai yau dan haka ya shiga sosa kai tare mazewa ya nufi part ɗinsa yana shiga Granny ta tashi harda gudu, part ɗin Anut Amina ta nufa ta hanki tace "Ban baki labari ba, to wlh sai yanzu ya fito" dry Anut Amina tayi tace "Kema dai Granny shida matarsa" sakace baki tayi tace "To amma dai ai yaji kunyata fisabilillahi amma wlh ko a jikinsa, kai ashe haka Imamu yake? To wlh kakansa Balarabe yayo baya jin kunyar abinda yake so" Murmushi kawai Anut Amina tayi Granny tace "Nace anya ba korar Saudala za muyi ba? Tunda dai Mijinta kashe sa za ayi ita kuma meye namu da ita albarkacin Bareeq take ci" Jinjina kai Anut Amina tayi tace "A'a Granny ki barta Allah na sane da ita ai, ku raba zcyar da tasu da kuma zuwa wajan bokan da tayi ma kaɗai ya ishe ta" Granny tace "To basai dai yanzu taci kanta ba, ko dan Allah?" Anut Amina tace "haka ne kam" Mami na zaune ita da ƙawarta Fariha tace "Fariha komai ya lalace min gashi duk dukiya ta suna hannun Lubna" Fariha tace "Ya dai kamata ki gane Allah ɗaya ne, kiyi hqr ki tsaya iya nan, gashi yanzu nida Abban Taufiq munyi dai-dai na ɗauki duk shawarar da Anuty Ni'ima ta faɗa min, na samu kansa muna zaune cikin Aminci yanzu dana biye maki da yanzu kin halaka ni itama Lubnan ba son gsky take maki ba, yadda take bazawara haka take so ki zama Finally burinta ya cika" Shiru Mami tayi tace "Yanzu dai ki aramin dubu ɗari zani Sokoto Pls" Fariha tace "Wa Ni??? ALLAH yay min tsari tashi kibar min gida kada ki sani a halaka" baki Mami ta buɗe zatai mgn Fariha tai saurin faɗin "Dan Allah jeki Allah ya ganar dake" fita Mami tayi tare dayin gida ta ɗauki niyyar zuwa wajan Lubna gobe. Sheikh ne ya fito daga bathroom sanye da Maroon ɗin jallabiya mai gajeran hannu tana da tsaga daga gaban wuyan rigar, ya ɗura farar hula wacce ake cewa tashi ka fiya naci irinta larabawa, tsayawa yay gaban mirror yana fesa parfume ɗinsa mai ƙamshi, turo Ƙofar tayi a hankali ta shigo babban hijab ne a jikinta har ƙasa, yana Kallonta yasan babu kayan arziƙi a jikinta, Murmushi kawai yay yana tasbihi a ransa, ƙarasawa tayi ta amshi turaran ta ƙarasa fesa parfume. Amsa yay ya ajjiye gefe guda, kafin yace "Bari naje Mosque ina son abinci mai kyau mara nauyi" jinjina kai tayi tana shafa ƙirjinsa tace "Alwala kayi ne?" Janye jikinsa yay yace "Uhm" hijab ɗin jikinta ta cire wasu fitanannun ƙananan kaya suka bayyana wando ne iya cinyarta sai half vest ko bra babu jikinta ta tufke gashinta ya sauka har bayyana, saurin rufe idanunsa yana jin yanayinsa na sauya juya yay zai fita tace "Ai sai na rama" zare ido yay yace "Ki rufan asiri kada ki warware alwalan nan" dry tayi tana ƙara shafa hannunta a ƙirjinsa dake waje Numfashinsa ne ya tsaya yana jin tsigar jikinsa na tashi idanunsa a lumshe yasa hannu ya rungome ta tare da juyar da ita shi kuma ya jingina da jikin ƙofar, bakinta dab da nashi tana ƙoƙarin haɗewa a hankali ya murɗa handle ɗin ƙofar kafin ta sanya bakinta yay saurin janye jikinta tare da tura ta ciki ya fita da gudu yana kulleta a ɗakin... SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 NIMCYLUV ✍🏾 22/10/2021, 10:38 - 🤔🤔: Sheikh And Zahraaah 89-90 Dry Fannah tayi tace "Daka tsaya ai" ta faɗa tana lumshe idanunta tana jin yadda soyayyyar mijinta take Ratsa ko ina na jikinsa, Sheikh daban yake cikin maza, jikinta taja zuwa saman stool ta zauna cikin nutsuwa kuma ta ɗura Hannunta a cikinta tana jin yadda yake juyawa alamar yana cikin ƙoshin lafiya,ganin lokaci na shigewa ta miƙe tare da nufar bathroom ɗiinsa karo na farko kenan data shigar masa toilet banda ƙamshi babu abinda yake, ɓangaren towel daban, haka ma na brush, da kayan gyaran kai ga mayukan shaving kala daban-daban, Murmushi kawai tayi domin ta gama yarda da waye Sheikh da kuma Abinda Ya keso, rigar jikinta ta zame ta rata ye saman hanger. Warm water ta haɗa mai zafi ta zuba bath perfume _summer Fragrances_ a cikin ruwan. Tana gama haɗawa ta ɗauki shaving oil ta ƙara gyara jikinta inda tasan Sheikh yafi so da ƙauna, then ta shiga cikin ruwan ta zauna sai da ya huce ta ƙara haɗa wani kamarsa sai da tayi haka 3times, kafin ta haɗa na wanka da tayi mai kyau, lungu da saƙo sai da wanke tass Sannan ta ɗauki handrayer ta fara gyara kanta ya bushe then ta ɗaura alwala. Kallon yadda ta cika tai ɓul² ƙirjinta ya ƙara cika tamkar wacce ta fara shayarwa hakan ya tabbatar mata cewa cikinta yay girma, towel ta ɗauka ta ɗaura kana tai waje tare da sanya hijab ɗin ta ta nufi part ɗinta. A Parlo ta samu Anut Amina da mai aiki suna jera dinner, kallo ɗaya Anut Amina tai mata ta ɗauke kai domin ta tabbatar yau Sheikh zai ƙara angwancewa a karo na biyu! Mami da kallo kawai tabi Fannah har yanzu tana jin tsanarta, Miƙewa tayi tana jan tsaki itama Fannah ko Kallonta ba tayi ba, Granny kakkaɓe kayan jikinta tayi tana faɗin "To mutum ba sai dai yaci kansa ba fisabilillahi? Ai duniya ba aljanna bace a toh! Kowa zai girbe abinda ya shuka" Bahaiyya ce tace "Anut Fannah ina son kimin lalle irin na kwanaki" da sauri Granny tace "Muhammadur Rasulullah (S.A.W) a dangin wa? Kuna da halaƙa da ita ne? Kul na ƙara ji ban da dai rashin kunya irin ta ɗan yanzu Uwarki da gama jaa mata tsaki yanzu kuma Kice tai maki turami (lalle)?" Fannah tai Murmushi tace "Granny ki barta mana" wani kallo Granny tai mata tace "Matsa can mara kishin zuci, har yanzu Mijinki take son cutarwa ke kinan zaki gwaninta" Shiru Fannah tayi kafin Granny tai magana ƙamshin turarensa ya kawowa hancinta ziyara, a hankali ta ɗago kanta suka haɗa ido ya kashe mata ido ɗaya da sauri ta juya tai ɗakinta tana sakin murmushi kunya ta kamata domin ta gama bayarwa Granny da Anut Amina sun gani. Yana gaba hannunsa riƙe da casbawa sai Arjun dake bayansa Fareeq kuma na biye da su ya sama wani abin tausayi sai janye jikinsa yake, shi kansa ko inda Mami take baya zuwa yama janye jikinsa gaba ɗaya daga gare ta. Zama Sheikh yay a saman kujerar yana motsa bakinsa yana tasbihi a hankali Arjun ma zama yay, Fareeq kuma yaja jikinsa can gefe guda, Arjun yace "Buddy yau da safe kayan da mukai order sun ƙarasu, abin mmkin kuma kayan da aka riƙe maka na shekara da shekaru yau securities ƙasar Cameron sun saki kayan, bayan binciken da sukai ya tabbatar wani yaywa company naka zaƙon ƙasa ya sanya mana hudar iblis a cikin kaya, to yanzu Finally komai yay dai-dai" ya faɗa yana ciro wani file daga cikin aljihunsa ya miƙawa Sheikh, ƙin karɓa yay sai juyawa da yay ya kalli Fareeq. Sanin ma'anar kallon yasa Fareeq ƙarasawa wajan ya nemi waje ya zauna, Arjun ya ɗura da faɗin "a ɗaya company naka na art mun samu riɓanyar riba fiye da yadda muke tunani" karɓar file ɗin yay ya duba kana a hankali yana lumshe idanunsa wanda suke cike da kwaɗayin ganin matarsa ya miƙawa Fareeq, kallonsa Fareeq ya kasa karɓa kawai sai ya sakar masa a cinyarsa, yana maida hankali kan Arjun a kasalance yace "Uhm! Kamar nawa" Arjun yace "ribar da aka samu ta contract ɗin zanan makarantar kwanan da akai, da kuma zanan masallacin da akai gaba ɗaya sune 25.10m" Anut Amina ta miƙawa Sheikh coffee kana ta bawa Arjun sai Fareeq, kurɓa yay kaɗan ya ajjiye yace "Idan ka ɗauke ribar boarding school, ta masallacin akai gidan marayo, ka ɗauki rabi a ribar makarantar kai shagalin suna wa matarka" baki Arjun ya saki kafin yace "Buddy kasan me kake cewa? Wajan 10m nayi me dashi?" Miƙewa Sheikh yay yana faɗin "Idan ka ban ni nayi me dashi, Fareeq zai fara zuwa sabon company as manager na mallaka masa company baki ɗaya" da sauri Fareeq ya miƙe bai san lokacin daya saki kuka yana nufar Sheikh ya rungome sa ba, bayansa kawai Sheikh ya bubbuga ba tare da yace komai ba, Granny tace "Kai dai ka haifu wlh, Allah dai yay maka albarka ya baka zuri'a ta gari ya sauki matarka Lfy, toh! Wa kake dashi da zai maka wannan addu'ar ai sai ni ɗin" murmushi kawai yay yana shafa sajen fuskarsa sosai addu'ar Granny tai masa daɗi ya shige part ɗinsa yana sakin wadataccen murmushi. Arjun Miƙewa yay jiki ba ƙwari zcyarsa cike da mmki hali irin na Sheikh sam bai damu da Dukiyar da ake ta faɗa akanta ba, shiyasa a kullum Allah yake ƙara sanya masa albarka a cikin kasuwancnsa, gashi dai a farko bai taɓa sanin a dadin ƙadarorin daya mallaka ba, amma a koda yaushe burinsa ya taimaki na ƙasa dashi, ya bawa addinin Musulunci gudunmawa. Girma da ƙaunar Sheikh suka ƙara yawa a zcyar Arjun, har bai san me zaiwa Sheikh ya wanda zai faranta masa ba, sai dai fatan cikawa da imani Allah kuma ya sada shi da Iyayensa cikin aminci. Sheikh na shiga part ɗinsa ya zare jallabiyar jikinsa tare da shigewa bathroom ya sakarwa kansa shower a hankali ya shiga sauke ajjiyar zcy yana jin komai nasa na sauyawa, sai yanzu ne ya samu cikakkiyar nutsuwa amma hanyar yanzu akwai miki a zcyarsa wanda bazai taɓa goshewa ba sai sanda yaga Iyayensa idan yana da rabon ganin su. Ware fararan idanunsa yay a cikin madubin bathroom ɗin ya shiga ƙarewa kansa kallo a hankali ya furta _Sheikh Imam Deedat Balarabe_ ya faɗa yana ɗan sakin murmushi. Fareeq part ɗin Mami ya nufa jin tana waya yasa yaja ya tsaya domin yaji mene zata faɗa "Ok in sha Allah goben zanzo indai buƙata ta zata biya burina na sami abinda na keso kada na tashi a tutar babu" Girgiza kai kawai yay jin ƙara yasa ta juya tana kallonsa sai kuma ta kashe wayar tana faɗin "Fareeq ni kake gudu ko? Baka yarda da ƙaddarar ba" Kallonta yay kafin yace "Mami ƙaddara fa kikace, ƙaddara Allah ke kawowa bawansa amma ke da kanki kike ɗurawa kanki masifar da zata iya fin ƙarfi ki nan gaba, na ɗauka U can change amma naga alama You never changed ni nake wannan tunani, kowa yana son Allah ya bashi uwa ta gari amma ke banga alamar zaki zama uwa ta gari garemu ba, yanzu baki dubi Bahaiyya ita abinta da yafi muni ma and macace ita dole gori na rashin uba zai iya kawowa rayuwarta kutse musamman idan lokaci aurenta yazo, Mami wannan sam ba rayuwa bace daga yanzu baza ki sake gani ba" Da sauri tace "Fareeq kada ka manta duk lalacewa ta ni mahaifiyarka ce, duk duniya babu wanda kake da shi sama dani wlh, ko yanzu na faɗi na mutu sai kafi kowa baƙin ciki" Fareeq yace "Wlh Yah Sheikh ya fi ke, kuma da ace zaki ci gaba da rayuwa a haka gwamma ki mutu na huta daki ƙare rayuwarki haka, Mami ki gane cewa hali fa na bin ɗa ko jika ni dame kukeso naji ne, ban samu Uba na gari ba ban samu uwa ta gari ba, yanzu idan Allah ya jarabce ni da samun yara masu irin halinku nace me? Nace masu a wajan kakaninsu suka samu wannan mummunar halin? Wlh kun gama dani" Yana faɗin hakan ya fice daga cikin part ɗin idanunsa cike da hawaye a corner ya samu Bahaiyya tana rera kuka, bai ce mata komai ba ya kama hannunta suka bar gidan baki ɗaya ta nufi wani mall da ita. Sai data gama turare jikinta da turaren AL'AJABU wanda yake ratsa lungu da saƙo na jikin mace, kafin ta ɗauki wani tarare wanda tunda tazo gidan ba tayi amfani da shi ba, shima na tsugune ta saka ya turare mata ƙasanta, kafin ta ɗauki wani lotion mai ƙamshi ta shafa a saman farar fatar ta mai taushi da kuma santsi. Tana gamawa ta ɗauki matte liquid lipstick ta shafa saman laɓɓanta masu kauri da taushi, nan da nan suka ɗauki haske da sheƙi ya ɗauki baƙin kwalli ta zizara a idanunta sai Idanunta ha ƙara haske yay fari ƙwayar idanunta ya ƙara fitowa sosai, Murmushi tayi ganin yadda take wani ƙyalli. Wasu ƙananan kaya ta ɗauka masu black and red colour ta sanya, sket ne mai tsaga ta gaba sai riga mai hannu ɗaya, ɗaya hannun kuma ya sauka a ƙirjinta, gashin kanta dai-dai tsakiyar kanta, sai jikinta ya samu nutsuwa bai matse ba, ya fito sarari domin rigar iya ƙirjinta ta tsaya, ta ɗauki parfume different colors ya fesa a jikinta kafin ta ɗauki babban hijab ta sanya a jikinta, wayarta yay ƙara taga sunan _Nurul hayat_ na yawo tai picking a hankali taji ya sauke zcyarsa yana sakar mata lallausan murmushi kafin tace ya marai-raice fuska Murya can ƙasa yace. "Amincin Allah ya tabbata ga Mrs Imam Deedat Balarabe" Saurin zubewa tayi a wajan tana jin muryarsa na saukar mata da kasala, kamar ba zatai mgn sai kuma tace "Rayuwata" ware idanunsa yay sosai sai kuma yaja ya rufe sbd tunawa da His Fairy da yay, itace silar komai da faruwar komai shikam zai iya rayuwa da ita har gaban abada, amma yanzu zyrsa ta Zahraaansa domin ba'a mgnar wanda babu shi a Duniyar baki ɗaya, ɗan sauti ya sakar mata kafin yace "Ina son ganinki en mata" kwaɓe fuska tayi tace "Aini na huce en mata yanzu kada ka mata soon am going to be come a mother" jinjina kai yay yace "Sure?" Tace "Ehmn" taɓe baki yay yace "Har duniya ta tashi en mata kike a idanun Imam, Ohhh yaaahh maza zo nan inji ɗumin jikin Matata" miƙewa tayi tace "On mah way" yace "Anahh UHIBBIKI" ita kuma tace "Ina sonka Mijina" a hankali ya ɗura wayar a bakinsa ya bada sautin "Muuu'ahhhh" da sauri ta zare wayar sbd wani iri da jikinta yay shi kuma ya ɗan saki Murmushi yana faɗin "Shy girl" ya faɗa yana ajjiye wayar yaci gaba da danna system ɗinsa. Tijama na kwance cikin halin ciwon daya kamata ta kalli Tuɓe tace "Ko yanzu na mutu nasan Airah zatai alfahari dani, Ubangiji na zai alfahari dani" Tuɓe yace "Yake Kakata ba zaki taɓa mutuwa ki barni ba, daman na maki al'ƙawarin kawo komai cikin sauƙi, kuma in sha Allah saura kaɗan Iyayensa su zo garesa, Tana farin cikin ta tuzarta Imam, bata san cewa nice na shiga jikinta na tunzurata ta aikata hakan ga Sheikh ba, domin hakan shi zai kawo komai cikin sauƙi" riƙe hannunsa Tijama tayi tace "Congratulations Tuɓe, Allah ya kare dukkan zcyar da take mai kyau kamar ta Sheikh, aiki ɗaya ya rage maka wanda nake fatan Ubangiji ya baka ikon yi lfy cikin aminci da kwanciyar hankali" Murmushi yayi yace "Yake Kakata wannan aikin bani na fara ƴar uwata Airah itace silar komai, ni kawai ƙareshi ne nawa" Tijama tace "Maza jeka tashi kaje ka ƙarasa naka aiki" Yana zaune daga shi sai boxer mai kyau sai faffaɗan jikinsa da yake a buɗe yaji ta shigo cikin bedroom ɗin domin ta duba taga baya parlon, tun daga sama ya ƙare mata kallo har ƙasa, bai son lokacin daya miƙe tsaye ba sai buɗe idanunsa da yay ya ganshi gabanta, "Uhm" kawai ya faɗa ya amshi tray hannunta ya ɗura saman carpet batai aune ba taji ya zare hijab ɗin jikinta, baya yaja ya shigayi mata wani kallo kafin a bayyane ya saki wata wahalalliyar ajjiyar zcy then yace "Yasubuhanallah! You're lucky Imam, Uhm Tubarkallah" sai kawai yasa hannu ya cirata sama ta ƙanƙamesa abinda ba taɓa ji yayi ba shine waƙa, yana juyi da ita yana faɗin. _“Fatima Zahraaah kece a zuciya! Fatima Zahraaah madubin idaniya!! Fatima Zahraaah kece sanadi na faruwa, laifinki ban gani koda ruwa da iska! So yakan saka wasu harma su fara hauka! Dana tunaki sai naji sanyi a zuciyata! Buri na zuciyata na ganki a gida na muzamma miji da mata haka zai faranta rai na!”_ SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 rayuwa babu tabbas koda yaushe zaka iya wayar gari ka jika a kabari dan Allah kada ka tafi da haƙƙi na😭 Ya ƙare maganar yana sakinta tare da rungome ta tsam a jikinsa yana sakin dryar farin ciki, dai-dai kunanta yace "Thank you! Thank you so much Wify today I'm very happy just because of you, I love you my Moonlight, Ina sonki Kurratul aini" rungome sa tayi tana ƙara shigewa jikinsa sbd cikinta daya tukareta" bai tsaya jiran mene za tace ba sureta sai gado ko abinci da yace ta kawo masa baibi ta kansa ba. Zare ido ta shigayi sbd abun da taji yana mata, a hankali ya ɗaga idanunsa da suka tara ruwa dai-dai kunanta yace "Hug me Zahraaah" ƙanƙamesa tayi sosai tana shirin sakin kuka ya sanya bakinsa cikin nata kafin yace "Now kiss me, kimin kuka Zahraaah, ina son naji kina screaming sbd ni, ohyyyah kiss me Kurratul aini" ya faɗa yana ƙara haɗe bakinsu sosai, jikinsa duk rawa yake, ya shiga karanto addu'ar Saduwa da iyali kafin a hankali ya fara ratsa jikinta, zata rufe idanunta yay saurin zare bakinsa yace "No! Zahraaah look at into my eyes zaki ƙara so na zan ƙara sonki kada ki rufe idanunta mu kalli juna a lokacin auratayya shi ne zamu ƙara shaƙuwa da juna, I love You Zahraaah" Idanunta cikin nasa tace "I love You too Rayuwata, i love You to the rest of my life, I love you more most" idanunsa ne ya kawo hawaye Ganin hakan yasa ta shiga share masa hawayen da bakinta kafin ta haɗe bakinsu, duk yadda tasu daurewa abun kasawa tayi ji take kamar yanzu ne first night ɗinta, lokacin daya samu nasarar ratsa jikinta ta saki kuka tana dukan ƙirjinsa... SIRRIN MU isn't free contact to subscribe 08119237616 rayuwa babu tabbas koda yaushe zaka iya wayar gari ka jika a kabari dan Allah kada ka tafi da haƙƙi na😭 NIMCYLUV ✍🏾 22/10/2021, 10:39 - 🤔🤔: The Accident 91-92 Kiran sallar farko na Subhi Sheikh ya buɗe gajiyayyun idanunsa wanda suke da bacci, domin bai samu ya runtsa a jiya ba sai wajan ƙarfe biyu. Idanunsa ya sauke a kanta tana maƙale da jikinsa ta tura fuskarta tsakiyar ƙirjinsa tana sauke numfashi a hankali. Bacci take cike da nutsuwa gaba ɗaya ta cukukuye shi ko nauyin cikin jikinta bata ji, koda yake ba kowa yasan darajar cikin fari ba. Bakinsa ya ɗura saman goshinta ya bata sumbata kafin yace "Thank you once again Zahraaah na" yana faɗin hakan ya fara ƙoƙarin zame ta daga cikinsa, ta kwaɓe fuska zata saki kuka yay saurin shafa sumar kanta yana hura mata iskar bakinsa lubb ta ƙarayi a jikinsa tana surutai ƙasa², kunansa ya ɗura a bakinta yaji tana faɗin "I love You Sheikh! You're the best Nurul hayat, you make me happy, I love you too Malamina, I love rayuwata" Kallonta kawai yake sai yanzu ya ƙara tabbatar ya gama gina soyayyarsa a zcyar Fannah, ko wanne irin hali ta shiga ba zata taɓa iya mantawa dashi ba. Lumshe idanunsa yay yana faɗin "Allahamdulillah! Thank you God, Thank you for everything" A hankali kuma ya zame jikinsa tare da mayar mata da pillow ma dadinsa, kana ya miƙe yana ɗan kuna dumn light ɗin bedroom ɗin ya nufi bathroom ya sakarwa kansa shower, Sharp-Sharp ya shirya cikin blue black ɗin jallabiya mai taushi da laushi, kana ya fesa perfume ya ɗauki casbawa tare da hirami ya sanya saman sumar kansa, yana tafe yana azkar harya isa Parlo, a nan ya samu Fareeq shima sanye da Jallabiya yana jiransa, yana ganin Sheikh ya miƙe tsaye tare da bin bayansa har zuwa Mosque.. Ganin lokaci bai idda ƙarasawa ya gabatar da sallar Raka'a tul fajjir, bayan nan ya miƙe yaja sallah yana gamawa ya fara yiwa mutane karatu 6 dai-dai gama musu ya ɗura da azkar sai da rana ta fito sannan ya fito daga Mosque ɗin suna tafe jere shida Fareeq, yana sauraran abinda yake cewa "ba haka ba Ya Sheikh kawai ina son na ƙaro karatu ne, wannan dalilin yasa nake son tafiya Singapore" Kallonsa Sheikh yay kafin ya ɗauke yana tafiya cikin gidan yace "Ka nemi duk makarantar da kakeso zan nema baka banda barin ƙasa" Jinjina kai Fareeq yay yace "Shikenan Duk yadda kace zanyi biyayya" Suna ƙoƙarin shiga babban Parlo Mami na ƙoƙarin fitowa, kallon juna sukai ita da Sheikh tunda wannan abun ya faru basu ƙara karo da juna Irin yau ba. Da Murmushi a fuskarta tace "Mrng Sheikh" Sheikh na tafiya yace "Mrng" daga haka bai ƙara cewa komai ba ya huce, ta buɗe baki za taiwa Fareeq mgn yay saurin barin wajan. Waje tayi tare da hawa motar ta, ta nufi gidan Lubna. A Parlo Sheikh ya samu Granny tana ganinsa tace "marhaban lale" idanunsa a lumshe yana azkar ɗin safiya yace "Sabahul khair Granny" Ta washe baki tace "Bikhair Allahamdulillah!" Buɗe ido yay sai kawai ya saki Murmushi tashi yay zuwa wajan fridge ya ɗauki fresh milk mai ɗumi domin ba'a kunna fridge ɗin ba. A mug ya tsiyaya kana yay gaba zuwa part ɗinsa, tsayawa yana dubawa yaga bata ciki juyawa yay zuwa nata part ɗin, haɗa ido sukai da Granny tace "A'a wlh basa ido nake ba, to matarka ko tawa" Tafiya yaci gaba dayi yana dryar Granny a ransa tsofa labari, cike da nutsuwa da kamewa yake ɗaga ƙafafuwansa yake saukewa harya isa part ɗin nata, tun daga Parlo yaji wani ƙamshin mai daɗi ya daki hancinsa shaƙar ƙamshin, nutsuwa yaji tana saukar masa a haka harya isa bedroom ɗinta, tsaye yana aikata mata da kallo tana zaune saman kujera hannunta riƙe da lemon juice mai sayi tana sha, a jikinta taji idanunsa na yawo a kanta, sai take cikin wani cotton ɗin yadi mai laushi haɗe da gashi gashi, dark pink ɗinkin buba, sai kanta data sawa wata huka mai flower kamar bandana, ɗago kai tayi suka haɗa ido, mug ɗin hannunsa ya ajjiye kafin ya ware mata hannayensa Miƙewa tayi kanta a ƙasa ta nufi inda yake tana zuwa taja ta tsaya cije baki yay yace "See u, Madam come closer" ya faɗa yana jawota jikinsa tare da juyar da ita suka fuskanci juna yana ƙara kallon ƙyakkyawar fuskarta yace "Uhm haka ake gaisar da miji?" Turo baki tayi tace "Ina kwana?" Ba tare daya kalleta ba yana zame hular kanta yace "Yana kwano" tura hannunsa yay cikin sumar kanta yana shaƙar ƙamshin turarenta yace "Uhm, bari na kowa maki gaisuwar naga ƴar ƙauye na aura" Ya faɗa yana sanya bakinsa a goshinta ya bata light kiss kana ya dawo idanunta zuwa kuncinta, kafin ya tallafo Haɓarta yace "Lemme give you a special kiss My Kurratul aini" ya faɗa yana sanya bakinsa cikin nata ya bata wani special and hot kiss wanda yasa tai saurin maƙalesa tana faɗin "Uhm" sai da yaji jikinta na rawa alamar saƙonsa yana kai mata Kafin ya zame kansa ya durƙosa dai-dai cikinta ganin zai ɗaga rigar yasa tai saurin shafa kansa Kallonta bisa dole ta ɗauke idanunta ya ɗaga rigar a hankali ya manna bakinsa dai-dai cibiyar ta ya hura kaɗan kafin fara karato addu'ar daya saba, ya shafa a cikin sannan ya fara mata wasa da cibiya da sauri ta zame ta faɗa jikinsa ya rungome ta yana faɗin "Sabahul khair Zahraaah na" idanunta a rufe tace "how was your night?" Kallonta yay yace "Kike tambaya the night was good sbd ke na daɗe banyi bacci mai daɗi irin na jiya ba" Pls Kurratul aini Kada ki rabu dani kinji ya fara yana ɗura kansa a shoulder ɗinta kamar ƙaramin yaro dry tai masa tace "Da Zahraaah da abinda yake cikinta duk Mallakin ka ne" ta ƙare tana dry sarai yasan tsokanarsa take kawai ya share tare da miƙar da ita ya nufi bed tace "Bari na bawa Unborn child ɗina abinci" zamewa ta farayi tace "Haba dan Allah" Wayarsa ta ɗauki ƙara ganin sunan Arjun yasa yay picking a hankali tare da sata a handsfree cikin murna Arjun yace "Buddy My Aliyah ta haifa min ƙyakƙyawan yaro mai kama dakai and kasan menene nama bashi sunan his name is Imam Mohd" farin ciki ya faɗaɗa a fuskar Sheikh yace "Ma sha Allah, congratulations Buddy, thank you Sai nazo ganin little Imam" ya faɗa yana ƙara sakin Murmushi kafin ya miƙe ya fasa abinda yay niyya yace "Ki shirya muje" sosai tai farin ciki daman ta daɗe rabonta da fita sai zuwa asibiti. daman a shirye take perfume ta fesa ta sanya hijab ɗinta a Parlo ta samesa sanye da wata haɗaɗɗiyar shadda wagambari da huma jaddara, yay kyau sai walwali yake kamar ango. Yana ganinta yace "Sai mun dawo" Granny tace "Allah dai ya tsine idon maƙiya" Anut Amina tace "Ya tsone dai ko Granny" Granny tace "To meye ne bambancin? Ba gwamma ya tsine ba daya tsone ida ya tsone idan ya tashi daga aiki ba, ai kinga addu'a ta tazo da sauƙi ko dan Allah?" Anut Amina tace "haka ne kam" Tashin hankali ya bayyana a fuskar Mami idanunta akan Lubna wacce take halin mutuwa babu bakin magana, tace "Na shiga uku dan Allah Lubna tashi ki faɗa masu inda dukiyata take, kada ki mutu ki barni babu ko sisi" Wacce take ɗakin tace "Ai sai dai kiyi hqr domin ko sisi Babu a nan duk kuɗin da suke hannunta mun ƙarar wajan yi mata magani" Mami ta ɗura hannu akai ta fasa ihu tana faɗin "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wai Meke damunta haka ne na shiga uku ni Saudat dan Allah ki rufamin asiri, ko rabi daga cikin dukiyata ne ki ban" Matar mai suna Sailuba tace "Ta kamo da ciwon ɓarin jiki, bayan dawowarta daga wani gari Nima ban san shi ba, mgnar kuɗi kuma ko biyar wannan ba zaki samu ba da zaki taimaka mana ma so muke" Mami bata tsaya jin wani abu ta fita tana faɗin "kin cuceni Lubna, Allah ya isa ban yafe ba, da nabi shawarar Fariha da babu abinda ya sameni, babu miji babu sweet Imam babu dukiyata innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" Tana tafe tana faɗa bata san Lokacin da tazo titi ba sai ƙarar mota da taji kafin tai wani yunƙuri motar tai gaba da ita. Sheikh yabi jaririn da kallo cike da so da ƙauna, yana fatan shima yaga nasa haka, sun daɗe sosai kafin suyiwa su Arjun sallama Fannah ji tayi kamar ta ɗauke jaririn musamman da taji ance sunan mijinta aka saka, daga nan suka huce ganin Dr ya tabbatar da lafiyar Babyn a nan kuma yaga Twins sai kawai yaja bakinsa yay Shiru yaga abinda hali zaiyi zuwa Lokacin haihuwarta. Yana driving yana jifa mata Murmushi suna shira sama², hannunta riƙe cikin nasa tace "Yanzu idan na haifi Namiji wanne suna zaka sanya?" Wani lafiyayyan murmushi yay sbd daɗin da yaji yace "Ina fatan ace baby girl ce" kwaɓe fuska tayi tace "Ni aboki nake so na samawa Mijina mai tayaka aiki" Kallonta yay sosai yace "Ke baki son Taimakon ne?" Girgiza kai tayi tace "Ina so mana, amma nafi buƙatar naka" shafa sumar kansa yayi kafin yace "Uhm, da mace da namiji duk ɗaya, duk wanda Allah ya bani ina so, idan namiji na samu in sha zai samu sunan SHAMSUDEEN sunan Uncle Sham" Fannah tace "Wow Anut Amina zatai farin ciki sosai wlh, idan macace fa?" Jimm Yay kafin yace "Ayshatul-humaira" idanu ta buɗe sosai tace "Wow i like the name, Allah ya kawota cikin Aminci" Yana tsayawa a danja yace "Na sakar maki Ameen" Malt ta gani mai sanyi ana tallah ta kallesa sosai ya gane amma yay masa maza tace "Nurul hayat" buɗe ido yay yace "Baza ki sha ba, abun kan titi" marai-raice fuska tayi tace "pls mana" ta faɗa tana zura hannunta a aljihunsa yace "Ko biyar ba zaki gani ba, rabon da naga kuɗi da idona na manta" da sauri ta buɗe hand-bag ɗinta tunawa da kuɗi ciki ta zaro ɗari biyar ta baya mai Malt ɗin ya bata ɗaya" dai-dai nan danja ta masu hannu. Ganin yadda take juya abun yasa "Gulma ta me ciki" dry tayi tace "Allah kuma naji ban son sha fa" wayarsa na ƙara yace "Na You sabi" yana ɗaga kiran yaji Muryar Bahaiyya na kuka tana faɗin "Ya Sheikh Mami" shiru yay kafin yace "what wrong with her" shiru yay sai kuma yace "Ok shiru to" Juyawa motar yay ya nufi hospital Fannah da ido kawai take kallonsa har suka shiga hospital ɗin, hannunta riƙe cikin nasa suka isa emergency, da sauri Fareeq da Bahaiyya suka faɗa jikin Sheikh suna kuka, bai ya mgni sai jijjagasu kawai sa yay, kafin ya zare jikinsa ya nufi room ɗin da take yana shiga ya rufe idanunsa sbd ganin Mami kwance a saman bed a naɗe mata gaba ɗaya kanta da fuskarta, ga hannunta ɗaya a gutsire an naɗe da bandeji, saurin juya yay faɗin "Subuhanallah!" Fannah zata shiga yay saurin riƙe ta suka nufi office Dr yace "Gsky ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta wanda ya shafi tunaninta, sannan hannunta ya fita sakamakon accident data samu, wanda hakan yake shirin taɓa lafiyar cikinta" Ajjiyar zuciya Sheikh ya sauke yace "Allah ya bata lfy kayi komai ka nema mata nurse mai kula da ita" Yana faɗin haka ya miƙe Buhaiyya tace zata zauna wajan Mami, uwa uwace dan haka Sheikh ya rabo da ita. Lokacin da labari ya samu su Granny hannu ta shiga tafawa kafin ta fara shassheƙar kuka tana sharce majina tace "Allah sarki Saudala Allah ya jiƙanki yay maki rahama" Da mmki Sheikh ya kalleta baice komai ba Anut Amina tace "bafa mutuwa tayi ba" Granny tace "A'a wlh ba ruwana, meye bambanci hannufa ya fita fittt babu na danna kumfuta" Da daddare Sheikh ya gama shirin kwanciya wayarsa tayi ƙara ganin baƙuwar number kawai ya share, ƙara kira akai Fannah dake tsaye ta ɗauka tare da manna masa a kunne, daga can ɓangaren aka sauke ajjiyar zcy kafin ace "Assalamu alaika, Ya Sheikh Aslam ke mgn" Shiru Sheikh yay yana son tuna inda yasan sunan can kuma yace "Ohh Ykk?" Aslam yana kallon Ammi wacce tai shiru tana kallonsa yace "Allahamdulillah, fatan kaima Lfy kake" Sheikh ysa hannu ya jawo Fannah jikinsa yana zare rigar jikinta tare da tura hannunsa cikin ƙirjinta, yace "In sha Allah" Aslam yace "Alfarma nake nema dan Allah" Sheikh yace "Uhm" jin hakan yasa Aslam cewa "Ammina keson gaisawa dakai, ta damu sosai kullum cikin mgnarka take" Miƙewa yay zaune yace "Ok to" da sauri Ammi ta amshi wayar idanunta na kawo ƙwalla bakinta har rawa yake wajan faɗin "Farin ciki na!" Da saurin Sheikh ya runtsa idanunsa yana jin kansa na sarawa shiru sukai kowa na jin sautin fitar numfashin ɗan uwansa, kafin cikin ƙasa da murya yace "Am...Am..Ammi" da sauri Ammi tana kallon Aditya tace "Na'am Farin t na, kullum ina jin wa'azin ka wanda yake samun farin ciki da nutsuwa ,dalilin hakan yasa nake ce maka farin ciki na" Kallon Fannah yay wacce bacci ya fara ɗauke ta sbd abinda yake mata yace "Ngd Sosai Ammi Allah ya saka da alkairi" cike da farin ciki tace "A kullum addu'a nake maka kamar ɗan dana Haifa aciki na, Allah ya tsarekae ya kiyaye ka daga sharrin mutum da aljan ya ɗura ka bisa maƙiyan ka, ya kiyaye ka da kiyayewarsa" wani farin ciki da nutsuwa ya kama Sheikh wanda bai taɓa samun irinsa ba, sun daɗe suna magana hadda su Aditya da Anushka. Suna gama wayar ya ajjiye sai soyayyar Amminsa ta dawo masa sabuwa yay rashinta sosai, juyar da Fannah yay yace "Wake Up Madam, tashi kiyi aikin lada" Kwanci tashi ranar suna yazo aka sawa sunan ɗan Arjun Imam, akwatina wajan biyar Sheikh yay tare da abin yaka Saniyya da rago, Fannah ma ba'a barta a baya ba ta haɗawa Aliyah irin turarensu na kanuri. After 2mnt Cikin Fannah ya tsofa sosai, Sheikh ya dainae dadewa wajan aiki, har kuma lokacin Mami bata farka daga duguwar suman da tayi ba, itama cikinta ya shiga watan haihuwa sbd kusan wata guda ne dana Fannah. Fannah na zaune ta miƙar da ƙafarta wacce ta kumbura sosai, Sheikh na matsa mata duk ta Marai-raice masa sai kuke kuke take ita cikin ya dameta, Kallonta yay yace "Mai ciki gani nan tafe" pillow ta ɗauka ta cilla masa yay saurin cafewa kuka ta saki tana faɗin "Allah daga wannan bazan sake ba" Dry yay sosai tsayawa tayi tana ganin yadda yay mata kyau zati da cikar haibarsa sun ƙara fitowa sosai ya zama babban mutum, musamman yanzu daya ƙara zama Sheikh ɗin gaske, ƙasumbarsa ta ƙara yawa sai sheƙi take. Yace "Da ganki za kizo inda nake kina faɗin pls Nurul hayat, just like Yadda kikai baya pls Malamina ka soni kamar yadda nake sonka" kunya ta kamata ta rasa yadda zatai sai kawai ta fasa ihu tare dasa hannu ta hau dukansa, sai da tayiwa dan kanta Sannan ya lafe jikinsa tana sakin kukan shagwaɓa, rungome ta yay yana faɗin "It's Maman twins" ware ido tayi tace "Twins?" Ya ɗaga mata kira yace "haka nake ji a jikina, kin san mijin naki kwarzo ne da kin sauke zaki daɗa ɗauka" wayarta ta ɗauki ƙara sunan Ya Falta ya bayyana ta ɗauka Ya Falta ta saki kuka tana faɗin "Fannah Mama babu Lfy dan Allah kizo kada ta mutu" da sauri Fannah ta kashe kiran tana sakin kuka, nan da nan Sheikh ya siya masu online ticket ƙarfe ɗaya na rana jirginsu ya ɗaga zuwa Barno. Suna zuwa suka samu Mama kolo tana bacci ansa mata ruwa sai Yakura wacce bata daɗe da zuwa ba, Sheikh na tsaye bayan sun gaisa da jama'ar wajan, kamar daga sama su kaga mace ta shigo a firgice sai twins na biye da ita, Yakura ta miƙe tsaye tana faɗin "Indoo" da sauri wacce aka kira da Indoo ta faɗa jikin Yakura tana faɗin "Yakura i want my child, na shiga uku Yakura i want my child to come back to me" ta faɗa tana sakin kuka... NIMCYLUV ✍🏾 22/10/2021, 10:39 - 🤔🤔: Second To The Last Page 93-94 Hankali tashe Yakura ta shiga faɗin "Ke Indoo mene haka, mene ya faru daza ki shigo kamar an kuroki?" Kuka wacce aka kira da Indoo ta saki tana ƙara riƙe Yakura tana faɗin "Yakura an cuceni, an cuci rayuwar ɗana data Mijina, an sanya min tsanar abinda na haifa daga ƙarshe an mantar dani cewa ina da wani ɗa a duniya bayan su Aditya, me suke nema dani ne? What i have done to them?" Murmushi kawai Yakura tayi tana kallon Sheikh wanda idanunsa ke ƙasa yana duba system ɗinsa, Fannah idanunta akan Indoo kana ta juya ta kalli Mijinta sbd zallar kamar da taga sun yi, Su Ya Falta da Yagana su kawai suke kallo. Sheikh a jikinsa yaji ana kallon sa jin hakan yasa ya kashe wayarsa a ɗan sanyaye ya kalli Fannah ba tare daya kalli saitin matar da take kuka ba, bakinsa yake ta juyawa yana son yace wani abu amma ya gagara, sai kawai ya fara ɗaga ƙafafuwansa ya suma tafiya zuwa waje, Fannah ce ta Miƙe tana satar kallon jama'ar ɗakin taga babu wanda yake Kallonta sai kawai tabi bayansa tana ɗaga ƙafa da ƙyar sbd tsofan da cikinta yay, yana tafiya a hankali yaji ana binsa yanayin tafiyarta kawai yaji yasan ita ce, juyawa yana sauke kallonsa a kanta kafin ya juyawa gaba ɗaya gareta hannunsa saman shoulder ɗinta yace "Ke ba kiji nauyin jikinki ne?" Turo baki tayi tana marai-raice fuska tace "To ina zaka kuma?" Cikin idanunta ya kalla kafin yaja numfashi yace "To na mamajo ne da zan zauna cikin mata?" Girgiza kai tayi tace "Amma Nurul hayat naga kuna kama sosai da wannan matar fa" Juya fararan idanunsa yay sosai a kanta kamar bazai mgn ba sai kuma yace "Wa?" Tace "Wacce ta shigo yanzu mana, Allah Nurul kamar ko har tsoro ta ban" yana sakin Murmushi tare da matsa shoulder ɗinta yace "kada ki firgita min twins dake shirin zuwa duniya Madam" hannu tasa ta shafa farar fuskarsa tare da jan hancinsa tace "Uhm to ina zaka" bakinsa ya ɗura anata hancin ya ciza kaɗan tana lumshe idanunta yace "Waje mana" maƙalesa tayi tace "Nima zani" "uhm" kawai yace yana sukutar ta cak yana mata dry har bakin ƙofar shiga parlon nasu ya direta yana bata side hug yana sumbatar forehead ɗinta yace "I'll be back Kurratul aini" Yana faɗin hakan ya juya cike da nutsuwa da Kamala yana tafe yana ɗan buɗawa a haka yay waje. Fannah hawayen shagwaɓa na zubu mata tai cikin Parlon da turtsetsen cikinta, tana shiga ta nemi waje ta zauna tana ƙara satar kallon wacce aka kira da Indoo domin suma tunda suka tasu basu taɓa ganinta ba. Yakura tace "Yanzu Indoo kuma sai kizo duk a firgice kamar wacce aka kuro, yaushe rabon da mugana da juna kuma da kika tashi zuwa fisabilillahi sai kiyi mana haka, komai nutsuwa yake so" tana share hawaye tace "Haba Yakura, idan banyi kuka ba yaya zanyi? Na yarda da ɗan dana Haifa tun yana zanin goyo, ban san cinsa shansa ba, balle tarbiyyar sa ba, kina tunanin haƙƙin Allah bazai kamani ba da wufintar da kyautar da yaymin ba, ƴar ƴar amanace a garemu dole Allah zai tambaye mu su ranar lahira, yaya muka kula da tarbiyyar su?" Jinjina kai Yakura tayi tace "haka ne kina da gsky, amma ki fara nutsuwa nai mki bayani ƙilan nasan abinda baki sani ba" shiru tayi sai a lokacin ta ɗaga idanu ta kalli su Ya Falta da Yagana kana ta juyo da Kallonta zuwa ga Fannah, ƙuri tai mata da ido kana ta maida kallonta zuwa ga cikinta, a hankali ta sakar mata tattausan Murmushi, Fannah ta saukar da kanta ƙasa tana wasa da hannunta tace. "Nda wattu (Ina kwana)" Kallonta ta ƙarayi still idanunta na kan cikin Fannah tace "K3lewa silai (lafiya lou)" Fannah bata ƙara magana ba sbd kunyar matar data keji, amma a ƙasan zcyarta tambayoyi ne masu yawa, me yasa take kama da Sheikh ɗinta? Wanne yaro take iƙirarin ta tafi ta bari har haka? Then ita ɗin Wacece daga ina take, da sauri ta ware idanunta musamman da ƙwaƙwalwarta ta shiga tariyo mata wasu bayanai da akai lokacin zaman Court Sheikh, kallon matar tayi idan harta haɗa da zan can Court ta haɗa da na wannan matar yanzu waje guda hakan na tabbatar mata cewa wannan Mahaifiyar Nurul hayat ɗinta ce, wani farin ciki mara misaltuwa ya gama Fannah, kullum tana kula da yanayin Sheikh yana da damuwa kawai dannewa yake sbd bai son nuna mata damuwarsa kuma bata huce rashin Iyayensa, Al-hakkamu kenan, gagara misali sai gashi Ubangiji ya dawo masa da Iyayensa a lokacin da basuyi zato ba kuma ba suyi tsammani ba. Shiru tayi kawai tana ƙara satar kallon kamar kafin Yakura tace "Nda amfatoye?(Ya mutanan gida)" murmushin ƙarfin hali Indoo tayi tana kallon su Anushka da suka lafe a jikinta sbd babu wanda suka sani tace "Aslam da Ur Excellence suna waje" haɓa Yakura ta riƙe tace "To maza shigo dasu" kafin ta kalli Fannah tace "Kira min Imam yanzu" dai-dai nan Mama kolo ta fito da bedroom tana ware idanun ganin Indoo wacce ba tayi tunanin gani ba. Sosai sukai farin cikin ganin juna kafin su zauna suna hira ta yaushe gamo Indoo yi kawai take amma hankalinta gaba ɗaya yana kan Fannah su take tace Wacece amma ta gagara tambaya. Sheikh a hankali yake tafiya bawai haka kawai ya fito ba, tunda matar ta shigo ya kasa samun nutsuwa zcyarsa ta shiga bugawa da ƙarfi yana jin kunanta har ƙasan zucyarsa, hasali ma ji yake kamar yasan muryarta amma at where shine abinda bai sani ba, a daddafe ya isa waje inda ya ajjiye mota wacce ya samu lokacin da suka iso Barno. Aslam dake cikin mota a gaba kamar ance ya ɗaga kai idanunsa ya sauka akan Sheikh dake fitowa yana dafe da kansa.. Da sauri ya ɓalle murfin motar ya fito fuskarsa cike da farin ciki ya nufi inda Sheikh yake tsaye yace "Ya Sheikh kai ne da gaske? Gsky Am happy to see you, banyi tunanin ƙara ganinta soon ba" Murmushin dole Sheikh ya ƙaƙaro yana kallon Sheikh, Governor Deedat Balarabe yana kishin giɗe a bayan motar hannunsa riƙe da jaridar darly trust ta yau yana dubawa yaji Wayarsa tai ƙara ganin sunan Maman twins yasa ya ɗaga kiran yana sakin lallausan murmushi daga can ɓangaren muryarta a ɗan maƙale tace "Ur Excellence ka shigo" Jinjina kai yay yace "To rigimammiyya ta" dry tai kaɗan kana ta kashe kiran, daga yafiyar tasa ta sirri ce yasa ko securities babu iya suke nan. Yana fitowa idanunsa ya sauka kan Sheikh dake kallon Aslam yana ɗan faɗaɗa fuskarsa, jin idanu a jikinsa yasa ya ɗaga kansa sukai idanu huɗu da Deedat wanda yake tsaye kamar an dasa shi, kallon kallo aka shigayi kowa yana hango kamar kowannen su a fuskar ɗan uwansa, Aslam yace "Papi, My lovely Dad kenan" Deedat Balarabe shine ya samu damar ƙarasawa wajan yana kallon Sheikh, Sheikh kam bakinsa ne yau nauyi komai masa ya tsaya. Dai-dai nan kiran Fannah ya shigo answering yay yana fidda numfashi kaɗan yaji tace "Nurul kazo" bata jira abinda zai faɗa ba ta kashe wayar, juyawa yay hannunsa cikin na Aslam suka bi bayan Deedat Balarabe! Da sallama irinta bayan mutane Deedat ya shiga Twins najin Muryar Papi suka tashi da gudu suna ganinsa suka faɗa jikinsa riƙe su yay sosai yana shafa kansu, yana jin Aditya na magana yay mata shiru. Daga cikin parlon akai masa iso ya shigo yana shiga Aslam ya shiga sai Sheikh a bayansu, idanun Indoo akan ƙofa tana jiran taga me shigowar, Sheikh kasa buɗe labulan yay shikansa bazai ce ga dalili ba, amma haka nan ya samu kansa da kasa koda kwali motsi, miƙewa Indoo tayi ta nufi ƙofar yana ganin hakan ya juya zai fita tai saurin riƙe hannunsa tana faɗin "Shigo man...," Mgnar ta maƙale mata sbd zoben data gani a hannunsa ba zata taɓa zoben ba, tana haifar sa ta maƙala masa, amma kawo yanzu yaci ace zoben yay masa kaɗan. Da sauri ta juyo dashi gabanta da mmki tace "Farin ciki na" buɗe ido yay wanda ya ɗan janye sai yanzu ya fahimci inda ya santa ta kuma san muryarta. Bakinsa ne ya shiga motsa wa zai mgn Yakura tace "Imam ka shigo mana" hannunsa taja zuwa cikin Parlon yaja ya tsaya ji bazai iya kallon kowa ba sai kawai ya mayar da idanunsa kan Fannah ko kunyar Mutanan Parlon baiji ba. Gyara zama Yakura tayi tace "Allahamdulillah, Allah abin gdy yau Allah ya nuna mana wannan ranar da muke ta jira" duk suka kalleta banda Sheikh dake kallon Fannah ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. Yakura ta ɗura da faɗin "Dukkan abinda ya faru baki da laifin komai Indoo, sharrin maƙiya ne wanda kawo yanzu sunga ƙarshen su Tabbas, mgnar ɗan ki kuma ki sani yana ɗaya daga cikin mutanan da Duniya take alfahari dasu, domin Allah ya dobi maraicinsa ya haɗasa da rayuwa ta gari kuma mai tsafta, Tabbas sai dai kiyiwa Allah gdy, domin duk ladan da Sheikh ya samu kina da naki kason a ciki" Da sauri ta kalli Sheikh shima Deedat ya kalli Sheikh kafin tace "SHEIKH!!!? Ban gane ba" Murmushi Yakura tayi tace "Tabbas Sheikh shine ɗan da aka rabaki dashi kuma shine sirikinku miji a wajan ƴar mu Fannah" ta faɗa tana nuna Fannah kallon faɗa Indoo tayi wato cikin jikin Fannah jikinta ne ko jikarta? Da sauri ta Miƙe ta nufi inda Sheikh yake wanda kawo iyanzu shima ita yake kallo tana zuwa ta riƙe hannunsa tace "Da gske farin ciki na kai ɗan dana Haifa? Am so sorry Am sorry My love pls forgive me" ta faɗa tana rungomesa, Sheikh jin abin yake kamar ba mafarki da gaske Amminsa ce a gaba sa? Da gaske mahaifiyarsa tsaye a gabansa take roƙan yafiyarsa? Tabbas ada yay fushi da ita amma tunda ya gane bata laifin komai, ya shigayi yin addu'a Allah ya karkato da hankalinta kansa ta dawo garesa, sai gashi Al'hakimu ya amsa masa addu'ar sa a lokacin mafi buƙata a garesa, uwa uwa ce wani sanyi da nutsuwa yaji yana ratsa zucyarsa, a hankali kuma yaji hawaye suna bin idanunsa da sauri ya kifa kansa a wuyanta tare da juyawa ya shiga tsiyayar da hawaye, bayansa ta shiga bubbugawa tana faɗin "Don't cry my child, ban ƙara barinka ka yafe min dear". Bakin Sheikh na rawa a hankali cikin narkar da Murya a marai-raice kuma cike da shagwaɓa da nuni da yay kewarta fiye da tunaninta yace "Ammiiii!!" Da sauri tace "Yes! My child, I'm here nothing will happen to you again nothing" lafewa yay jikinta yana shaƙar ɗumin jikin daya daɗe yana ƙwaɗayin samunsa dai gashi yau ya samesa, hannu ta miƙawa Fannah cike da kunya ta ƙarasa inda suke tana zuwa Ammi ta haɗa ta rungome su a jikinta, kafin ta ɗura hannunta saman ƙaton cikin Fannah tana sakin dry tace "Wow! Zan zama Grandmother allahamdulillah! Allah ya inganta my dear" sun daɗe jikinta shi dai Deedat kallonsu kawai yake shima yana son jin ɗumin jikin ɗan nasa amma kunya ta haɗasa domin shi ba kamar Ammi yake ba, yana iya danne abinda ya keji. Zama tayi tana tsakiya suna gefe da gefenta, ganin Fannah na ya motsa fuska yasa tai saurin faɗin "My dear me kikeso akwai inda yake maki ciwo ne?" Girgiza kai tayi tace "A'a Ammi" Kallonta Sheikh yay yace "You're lie Madam, ƙafarta ke zafi Ammi" Cikin tausayawa Ammi tace "Am Sorry ƙilan kin kusa haihuwa ne" Ta faɗa tana miƙar mata da ƙafar taba matsa mata, Sheikh a hankali ya janye jikinsa ya ƙarasa inda Deedat yake idanu suka haɗa sai kawai ya zame kansa ya ɗura saman cinyar Deedat yana sauke ajjiyar zuciya. Shafa kansa kawai Deedat yay cike da so da ƙauna, twins suke lafe a jikin Sheikh sbd daman sun san shi a t.v da kuma wajan Amminsu. Gyara zama Deedat yay yace "Lokaci dana bar gida na fara yawo a titi daga wannan motar zuwa wannan motar a haka har na haɗu da wani mutum mai sanin darajar ɗan adam, kai tsaye ya nufi Kasar Lebanon ina zuwa yasa akai min ta kardar shedar zama ɗan ƙasar, ashe shi ɗan siyasa ne, ba ɓata lokaci ya sani a harkar siyasa har na samu nasarar zama Governor, kullum cikin tunanin iyalina Ayushert nake, ban san halin da take ciki ba, amma ban taɓa tunanin dawowa gida ba, sbd na sani a ambaci sunan Nigeria ma, ana haka wata rana muka haɗu da Shamsudeen daga nan muka huce gida na ɗauki matata Ayushert wacce bai farin cikin ganinta kuma ban sha wahalar tafiya da ita ba, muna zuwa zaman kaɗai ci ya ishe ta musamman da take cikin damuwa iya ke nan mganar jariri, hakan yasa naje gidan marayo na ɗauko Aslam daga nan damuwarta ta ragu, bayan nan da wasu shekaru shi ne muka ƙarin samun albarka iyali ta twins, abin yay tsamari a jiya muna zaune naji Ayushert ta fasa ihu tana kiran My child gaba ɗaya ta fita hayyacinta, da ƙyar na samu kanta a nan tayi min bayanin komai bayan tafiyata, nan nima na samu kai na a so da kuma ƙaunar ƙasata ta 9ja, shi ne asubar fari muka ɗauki prvt jet zuwa nan domin anan tace zata iya samun wani baya nan" Yakura tace "Ikon Allah kenan, Allah kuma abin tsoro, a nan kuma ta basu labarin komai har rasuwar su Uncle Sham" sosai Ammi tai kukan rashin ɗan uwanta kuma ta samu kanta da son ganin huda. Nan suka lalace suna hira abun ya fara damun Sheikh sbd yana son keɓewa da matarsa, da daddare ya faki idanun mutane tana bacci ya ɗaga ta cak sai hotel. Washegari suna tana zaune ne jikinsa daga ita sai bra da inner yana mata tofi yana shafa mata a cikin, duk ta shagwaɓe masa yace "Ni kam na Banu, a haka za'a haifamin guda ashirin?" Turo baki tayi tace "tab sai dai wata ta haifa maka" Kallonta yay yace "Ok aure kike so na ƙara kenan no wahala" da sauri ta kama fuskarsa tace "Wai har naji zcyta ta harba idan yara ɗari kakeso zan haifa maka amma ban jure ganinka da wata" ta faɗa da sucking bakinsa da tongue ɗinsa, Numfashi ya fesar me zafi Wayarsa tai ringing sunan Fareeq ya bayyana yana ɗagawa yace "Ya Sheikh Mami, Mami ta haukace kuma ta haihu ba kaga abinda ta haifa ba, kuma yau za'a gabatar da ratayar su Abba" ya faɗa yana sakin kuka domin abun yay masa yawa. Sosai Sheikh yaji tausayi Fareeq kashe kiran yay ya ɗauki duguwar riga ya sawa Fannah kana ya kira number Aslam ya faɗa masu su haɗu a airport. Ba jimawa jirginsu ya ɗaga zuwa Abuja daga nan suka huce hospital tashin hankali Mami ce sai yagar gashin kanta ta keyi tana ci, haka gashin gabanta gaba ɗaya ta jini ke zuba ta ƙasanta da kuma kanta, sai Ihu take tana faɗin ni nayi Kaza nayi Kaza kai har kwanciya nayi da ƙare, barin wajan sukai a nan Dr ya nuna masu Abinda ta haifa bambancinsa da kare kaɗan ne, domin har fuskar jaririn irinta kare ne ga wanda jela a bayansa, tsoran daya kamata Fannah yasa ta saki ihu tana riƙe mararta da sauri ya ɗauke ta cak ya nufi labour room da ita.... NIMCYLUV ✍🏾 22/10/2021, 10:39 - 🤔🤔: THE END 95-96 🎻🎸I don't know when am coming back I'll be gone for a little while But I will keep myself for me and you🎻🎻 🎸🎸I'll be back for you I don't know what the future brings But I want you to be with me🎸 🎻I go dey hope and pray say make you wait for me 'Cause I'll come back for you🎸🎸 🎻Darling, you hold my love You are my price And I'll run to the finish line My love I no go leave you run🎸🎸 🎻🎻I no go bounce your call You'll be always on my mind Yeah yeah🎸🎸 I'll be so far away Promise you'll wait for me I go think of you everyday my love Yeah yeah 🎸🎸I may not come today But I'll be with you again I go dey pray for you everyday my love Yeah yeah As I'm leaving you behind Am gonna miss your smile🎻🎻 And the joy you bring to my wretched soul Your loving makes me whole This our love will never die Darling promise you will be mine See I dey do this thing for you and me 🎻🎻I'll come back for you Darling, you hold my love You are my price And I'll run to the finish line My love I no go leave you run I no go bounce your call You'll be always on my mind Yeah yeah I'll be so far away Promise you'll wait for me I go think of you everyday my love Yeah yeah🎻🎻 🎸🎸I may not come today But I'll be with you again I go dey pray for you everyday my love Yeah yeah I'll be so far away Promise you'll wait for me I go think of you everyday my love Yeah yeah I may not come today But I'll be with you again I go dey pray for you everyday my love Yeah yeah My love, I think of you tonight 'Cause I no dey by your side Just wait a little while yeah yeah Know that am alright I go see you soon Make you wait for me, my dear🎸🎸🎻🎻 Tana riƙe a hannunsa ya kwantar da ita akan bed ɗin asibitin, gaba ɗaya Sheikh ya ruɗe musamman yadda yaga Zahraaansa tana juyi tana riƙe cikinta tana cije bakin, hakan yasa ya tabbatar da cewa wahalar take sha, Likitoci suka zagaye Fannah da wani labule, sannan sukace ya fita ya basu waje. Kallonsu kawai yay idanunsa duk ya janye sbd damuwa yace "Kuyi aikinku" yana faɗin hakan yaja kujera ya zauna, hannunsa cikin nata yana shafa mata kai yana tofa mata addu'a, ganin take ƙoƙarin yin tsitsarar yay saurin tashi ya fice daga cikin room ɗin yana jan tsaki shiyasa a koda yaushe yara mata suna karatun wannan ɓangaren. Yana fita Granny tace "Yaya? Me aka samu" shiru yay mata ba tare da yace komai ba, ganin yadda yake huci yana sakin ajjiyar zcy yasa Ammi kama hannunsa taja can wani waje ta zauna kana tabar wajan ba jimawa ta dawo hannunta riƙe da gorar ruwa mai sanyi, Kallonta yay ya kalli ruwan hannunta yaga irin ruwan da yake sha ne, tana zuwa ta ɓalle murfin gorar ta zauna dab dashi, ta ɗura masa ruwan a baki sai daya sha sosai, ta janye rubar ruwan tana shafa kansa tare da jawosa jikinsa tace "Just pray for her ok" kai ya ɗaga mata yaci gaba dayin addu'a, can Ammi tace "So tell me something about your Airah" da sauri ya juyar da kansa akan cinyarta suka haɗa ido ta ɗaga masa gira, tace "Uhm all ears" kwaɓe fuska yay yace "Ammi wane ya faɗa maki?" Kafin yay mgn Granny tace "haka kurum ba zan faɗa mata wanda suka taimake ba, na sani ko zataiwa ita Ihrahn gdy" Kallonta Sheikh yay bai ce komai wato Aljanar za'aiwa gdy lallai. Maida idanunsa yay ya rufe ya shiga baya Ammi labari dab da kunanta sbd a hankali yake motsa laɓɓansa ita kawai ta kejin me yake faɗa. Jinjina kai tayi tace "Allah sarki, ace Aljanu sufi mutane tausayi da kuma imani" Shiru kawai yay hankalinsu ya koma kan Fannah, wajan 1hr kafin Anut Amina ta ƙarasu wajan tana Murmushi tace "Congratulations Sheikh Imam Deedat Balarabe" da sauri ya miƙe tsaye idanunsa har wani ruwa yake bai tsaya jiran mene za tace ba ya ƙarasa bakin room ɗin, yana zuwa yaga baby ɗaya wajan Granny ɗaya kuma wajan Aslam. Yasubuhanallah basu ankara ba su kaga ya zube a ƙasa yana sujudul shukri, yana Gsky ga Allah idanunsa cike da hawaye ƙasa mgn yana juyawa yaga Papi da sassarfa ya nufi wajan Deedat yana zuwa ya rungome mahaifinsa yana sakin kuka wanda ya kasa ɓoye shi a yanzu, yau kukansa ya bayyana akan idanun kowa. Murmushi Deedat yay yana faɗin "Lallai yau maza ana farin ciki, Abokina yau hadda kuka ma sha Allah, Allah abin gdy Allah ya ƙara karemin kai da kariyar sa my best friend" mutanan wajan suka amsa da Ameen Sheikh dai na maƙale jikin Deedat sai yanzu yaji kunyar kukan da yay, juyawa yay Papi ya ƙara sakin dry yace "Haka yaran zasu gana da Mahaifin nasu yana kuka" da sauri Sheikh ya ɓoye fuskarsa a jikin Papi yana ɗan sakin murmushi mai sauti, Arjun da Aliyah suka ƙarasu wajan farin cikin da Arjun yake ciki ɓata lokaci ne, yana zuwa ya amshi babyn hannun Aslm yaga macace, fara tass da ita hannunta a baka gashin nan har gaban goshi tana da tawadar Allah a ƙasan lip ɗinta, idanunta a rufe sai numfashi take saukewa a hankali.. Rungometa Arjun yana jin soyayyar Yarinyar a ransa, Kallonta yay yace "Matar Little Imam" Anut Amina tayi dace to ga ɗaya bada ta hannunsa yay ya amshi ɗaya, buɗe ido yay sosai itama macace gashinta har yafi na waccen yawa, ita kuma tawadar Allah ɗinta a saman leɓanta, itama hannu a baki a fili yace *"TAGWAYEN ASALI"* (IDAN MUNA DA RAI DA LFY, yana cikin jerin littafai na). Sukai dry Aliyah ta ɗauke su tana yabawa da kawon yaran baka taɓa bambanci da wanda suke kama a cikin iyayensu to kyau ne ya haɗu waje guda, dole ne ya bada kalar mai kyau, Sheikh fuskarsa cike da farin ciki ya amshi yaran ya rungome a jikinsa, kai tsaye ya huce ɗakin da aka kwantar da Fannah. Tana kwance an sauya mata kaya an tufke gashin sai Numfashin wahala take saukewa, suna jikinsa ya ƙarasa da sauri inda take ya ajjiye yaran can gadon su, ya haye nata gadon gaba ɗaya ya tattaro ta zuwa jikinsa, ya rungome ta sosai, ƙarfin matsar da taji yasa ta Turo baki gaba tana kwaɓe fuska, saurin kifa fuskarsa yay a tata hawayen farin ciki na fita daga idanunsa yace "Thank you so much Zahraaah, kibani abokan rayuwa, Allah yay maki albarka da dukkan albarkarsa, idan nine maƙulin shigarki Aljana ina mai tabbatar maki cewa na baki wannan damar tun tuni" Ya faɗi hakan yana kissing bakinta tare da faɗin"اللهم رب كما انعمت فزدنا" (Ya uban giji kamar yadda kayimin wannan ni imar kaqaramana) "bani da bakin gdy gareka bisa ni'imar da kayi min, ina roƙan ka ƙara min sonka da tausayin na ƙasa dani ina Alfahari da Kasancewa ta musulmi, Allah Ubangiji ka dauwamar da farin ciki tsakanina da matata, Allah ka raya min iyali ga sare min su daga ruɗin duniya" Ya faɗa idanunsa cike da hawaye yadda yake surutai da hawaye yasa a wahalarce ta buɗe idanunta tana ganinsa ta saki kuka tana turesa bai ce mata komai ba sai rungome ta yay tass a jikinsa ko fuskarta ba'a gani. Kwana ɗaya tsakani aka sallame su domin ta kanta ta haihu, Mami kam abu yay gaba aka ɗauke ta zuwa Asibitin mahaukata, abu yazo mata da sauƙi ɗan data haifa ya mutum, kwanan ta ɗaya a asibitin aka nemeta aka rasa, sosai Buhaiyya tai kuka babu uwa babu uba, ana saura kwana biyu suna aka rataye su Barrister Fareeq jikin Sheikh ya faɗa yana kuka a haka suka dawo gida kowa ba farin ciki a ransa da fuskarsa, Arjun kam kusan tarewa yay a Gidan shifa yaywa ɗan sa mata, Umma kam har mmkin so da ƙaunar dake tsakanin Sheikh da Arjun take, saura kwana ɗaya suna iyayen Aliyah suka zo barka tare da kayan barka masu yawan gaske. Gidan t.v da redio da jaridu suka dinga yaɗa haihuwar da akaiwa babban Malami Sheikh Imam Deedat Balarabe. Ranar suna yara sukaci sunan Ammi da Granny Ayushert da fatima ana ce masu *Luna & Lilah* irin kayan arziƙin da Fannah ta samu wajan ƴan uwa ɓata baki ne, washe garin suna suka sauya gida zuwa babban gidan da Sheikh ya gida mai parts da yawa. After 5mnt Aslm ya auri Buhaiyya, Fareeq kuma ya auri wata ƴar uwar Aliyah mai suna Maryam, Anut Amina ta samu wata mutum wanda matarsa ta rasu yana da yara biyu ta haɗa da Huda suka koma su huɗu. Suna zaune a babban parlo yana riƙe da Luna ita kuma tana riƙe da Lilah sai kuka take domin ita rigima ce da ita, tsaki taja tace "wlh na gaji ko a wajanwa ta samu wannan kukan ohhhu" Kallonta Sheikh yay yace "Uhm kagi nan kusan ai gado kika bar mata Madam" Miƙewa Fannah tayi tace "Ok haka kace to gashi nan kasan yadda zakai da ita ta faɗin hakan tana ajjiye masa ita a cinya zata gudu yay saurin riƙeta ya zaunar da ita kusa dashi, kana ya bata roƙan Luna, wacce tai bacci tana tsotsar hannunta. Lilah ya ɗura a kafaɗa ya shiga jijjiga ta yana shafa bayanta, tsitt tayi, yana jin tana tsotsar fatar wuyansa, a haka har yaji tai shiru sai yawon da take wasa dashi ya shiga gangaro masa. Sauketa yay ya ajjiye ta saman cinyarsa, ya juya ya kalli Fannah yaga tai bacci a jikinsa Luna na cinyarta, kallonsu yay gaba ɗaya yana jin so da ƙaunar iyalin nasa na ƙara shiga ransa a yanzu kam bashi da sama dasu domin sune a kusa dashi. Haɗasu yay gaba ɗaya ya rungome yana yiwa Annabi salati. Shekaru goma da suka shige, arziƙin Sheikh ya ƙara nunkuwa fiye dana baya, a lokacin shike jan Babban Masallacin dake Abuja, ya zama babban mutum gidan harda securities, a wannan lokacin kuma Allah yaywa Granny rasuwa sosai yaji mutuwar Granny domin har jinya yayi. Parking driver yay a parking space, fararan ƙafafuwansa ya fara sakkowa dasu, sai kuma hannayensa dake riƙe da wani Babban Alqur'ani, a hankali ya fito baki, ma sha Allah! Farar fuskarsa mai ɗauke da ƙasumba da yawa wacce gaba ɗaya ta kewaye fuskarsa, sai jajayen laɓɓansa ake gani, idanunsa maƙale cikin farin glass, yana sanye da wata farar Gezner, ɗinkin jumper da babbar riga, ya ɗura zanna bukar a kansa sai hiramin dake saman hular, da ɗan sassarfa ya shiga ƙofar da zata dashi da babban Parlo yana shiga ya samu Luna zaune tana duba Umdatul ahhkam, tana saye da duguwar riga milk ta rufe kanta da siririn mayafi, idanunsa ya mayar kan Lilah wacce take bacci tayi ɗai² saman duguwar sofa, ƙamshin turarensa da taji ta ɗago kanta da sauri ta miƙe fuskarta cike da farin tana zuwa ta Rungome sa tace "Mas'ul khair Abbi (Barka da yamma)" shafa kanta yay ya sumbaci goshinta yace "Yawwa friend, where is your Mom?" Da hannu ta nuna masa upstairs yace "Tashi wannan lazy girl ɗin nan, bacci da yamma" "Abbi masifa za tai min" Yana haurawa upstairs yace "Hope tayi Sallah?" Luna tace "She did Friend" sama ya haurawa yana motsa bakinsa alamar azkar yake. Da daddare suna zaune saman dinning yana cin abinci a hankali cike da nutsuwa, Fannah na gefensa ta zama babbar mace sai ƙyalli take Lilah tace "Mamy ina Nuha?" Kallonta Fannah tace "ta manta da bacci" Luna kuma tace "Mamy Nasreen da Nusrah fa?" Kallonsu tayi tace "to duk tambayar ta mecece?" Sheikh na goge bakinsa yana faɗin "Ku rabu da ita TAGWAYEN ASALI, ku shirya gobe jirginmu zai tashi zuwa Oumara" farin ciki ya kamasu a tare suka washe baki, suka kalli juna a tare kana suka kalli Sheikh a tare, Fannah tace "Wannan yaran zasu hukatar da mutum komai zai kunyi a tare nikam kuna sani" Dry Sheikh yay yace "My friends let's go" gaba ɗaya suka tashi suka nufi inda yake rungomesu yay ya sumbaci ko wannan su, kana ya ɗauki chocolate ya basu a tare suka haɗa baki wajan faɗin "Jazakallah bilkhair Abbi" shafa kansu yay yace "Sleep well my friends don't forget to pray" sukace in sha Allah, kallon Fannah yaga tana lumshe idanunta ba tare data sani ba ya ɗauke ta cak, da sauri ta buɗe baki tace "Yaya haka Nurul?" Kiss yay mata yace "Idan kika fara saurin baccin nan nasan akwai ajjiyata a cikin ki" turo baki tayi tace "tab kuma sai nai ta haihuwa" yace "Haka Sheikh Imam Deedat Balarabe yake so, ki ramin zuri'a masu albarka" ya faɗa yana shafa cikinta da sauri maƙalesa tana sakin murmushi. Tijama da Tuɓe suma suka rungome juna suna faɗin Allahamdulillah! Badan ka nemi tsuntsuwar da aka saka asirin Deedat a jikinta ba ka warware layar daga jikinta da bansan yaya zamuyi ba" Tuɓe yace "Bana faɗa maki ba, daman zan dauwamar da farin ciki a tsakaninsu sai sanda Ubangiji ya rabasu" Tijama tace "Allahamdulillah Allah abin gdy" Sheikh yana kwantar da Fannah ta miƙe zata gudu yay saurin riƙeta ya zame rigar jikinta, da yadda ƙirjinta ya cika kaɗai ya isa yaganar dashi cewa ciki gareta. Jin bakinsa a jikinta yana tsotsar cibiyar ta tai saurin riƙeta tana faɗin "Yeah! You got it right, Am pregnant" da sauri ya ɗauke ta ya shiga juyi da ita kafin ya sauke ta ya rungome ta sosai yace "Allahamdulillah Allah Abin gdy" ya faɗa yana zura hannunsa a saman ƙirjinta, murmushi tayi tana rungomesa tace "Da cikin da mai cikin duk mallaki na ne" matse mata ƙirji yay ta saki ƙara tace Ina sonka Mijina" yace "Banji ba dai" ta ɗura bakinta saman kunnansa tace "I love You so much Sheikh" nan ma yace "Me kika ce?" Tace "Anna UHUBBKA Malamina" rungome ta yay sosai yana sakin Murmushi yace "ALLAHAMDULILLAH!!" NIMA NI'IMA DA NAKE GEFE NACE "ALLAHAMDULILLAH" *Komai yay farko yana da ƙarshe, Nagode Allah daya bani ikon farawa lafiya na gama lafiya, hakan ma wata Ni'ima ce🌝, Ina roƙan Allah ya yafe min kuskuren da nayi Sannan Abinda nayi dai-dai ya zama garkuwa ta, ranar lahira, wanda nai masu kuskure su yafe min wanda nai masu dai-dai Nagode Allah, Sorry for the typing errors, Sorry for that* _Ina godiya garekie masoya domin kun nuna min ƙauna Tabbas, daku nake taƙama domine da babu ko da dukkan wata writer da ba tayi rubutu ba, ina fatan za kuci gaba da so na sa son litaffai na, kuma in sha Allah za kuyi alfahari dani nan kusa bada jimawa ba, ana ƙara tafiya ne ƙwaƙwalwa na ƙara buɗewa ina alfahari daku my lovely fans, Allah yay maku albarka_ ```Littafin ABU_MALEEK Alrdy har yayi replacing ɗin SIRRIN MU a zuciyar NIMCYLUV, writing is my dream and hobby, sbd haka ku shirya ako wanne lokaci zaku iya ganin littafin Sarauta wani free wani na kuɗi ina fatan duk wanda yazo za kuyi Accepte nasa, domin bazai fi karfin ku ba, abu mai muhimmanci shi ne aduk sanda ku kaga littafina sbd soyayyar da kukewa Allah da Manzonsa kuyi min share wannan shine soyayyar da zaku nunawa NIMCYLUV.``` *zuwa ga wanda suka karanta min littafin SIRRIN MU a kyauta, ku sani haƙƙina ne, bana Allah ya isa amma a kullum kai niyyar biya na kuɗi na ina wlcm da kai, kamar bashi ne gareku wasu su biya nan duniya wasu kuma sai Alahira, wanda kowa zaije ya tarar da abinda ya shuka a can, masu fitar min da book thank you so much hakan ma ƙauna ce🌚👍🏾 sai a jira zuwan ABU MALEEK, idan Kunyi niyyar biya na zanyi dropping number acct ɗina* *ABU_MALEEK* LITTAFIN NE MAI TSAYI ZAI JE BOOK 1 2 3 IN SHA ALLAH, AKWAI VIP JUST LIKE YADDA NAYI A UNCLE NE, BOOK 1 2 3 NA VIP SHINE 1K WANDA KULLUM ZA'AI POSTING WATA RANA SAMA DA ƊAYA! REGULAR GRP KUMA BOOK 1 2 3 👉🏾500 NE AMMA SU IDAN NAYI POSTING YAU GOBE BA ZAN BA, I ALRDY MAKE MY DECISION, SBS LITTAFIN ABU_MALEEK DABAN YAKE, AMMA KUNA IYA TATTAUNAWA DAN GANE DA KUƊI KOWA YA FAƊI RA'AYIN SA, DOMIN BAZAN FARA POSTING BA SAI AN GAMA PAYMENT, NA BAKU ISASSHEN LOKACIN DA ZAKU IYA BIYA KAFIN LOKACIN😍🥲DUK INDA NA SHIGA AKACE KAI NIMCYLUV HAKA KIKA ZAMA? ZANCE SILAR MASOYA DAN HAKA KO GRO KO PRVT INA MARABA DA SHAWARWARINKU. ZAKU IYA PAYMENT DAGA YAU ZUWA ƘARSHEN NOVEMBER FOR VIP 1K FOR REGULAR 500, BOOK 1,2,3, ACCT NUMBER 0116886423 ACCT NAME SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 FOR NIGER PEOPLE 84506476 IDAN DA HALI DAN ALLAH TA ACCT ƊINA, AKWAI P.O.S EVERYWHERE. IDAN BABU YADDA ZAKAI NE SAI KA TURO MIN SA AIRTIME BA BTU BA, JUST COPY THE PIN AND SEND IT TO ME🌚🥲 THANK you for choosing Sirrin mu And ABU_MALEEK, za kuji ni shiru in sha Allah idan kayi min mgn ta prvt ko ba'a kan lokacin bane zanyi reply, idan nai typing AURAN FANSA zan turawa wata ta Turo kuyi min share😂🤫 ga mayarsa nan Meeyrah ko ita zata jure share. Ina jiran sharshi mai ma'ana Habibaties i love You so much most YADDA DA ƘADDARAR YADDA DA JINNU CIN AMANAR ZUMUNCI SHARRIN DUKIYA👍🏾 SUNE JIGON LABARIN. AKWAI GANDOKI SALON TAFIYAR KURA DUK SUNE A BOOK ƊIN SIRRIN MU SHEIKH AND ZAHRAAAH LOVE'S YOU NIMCYLUV ✍🏾