https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC YouTube channel domin samun littattafai na Hausa don't forget please like and subscribe , Thank you. https://youtu.be/6-Jrkc2kmmE FREE PAGE ... SHARE FISABILLILAHI 08101235739 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE ONE Ƙarar ruwan sama ya ƙara karfi. Gajimare sun cika sararin gidan, kamar sama na kukan wata muguwar saƙo da duniya ta ƙi karɓa ana iya jin ƙaramin igiyar ruwan da ke gangarowa ta sama — amma abin da yafi damun mutum ba ruwan sama bane — azaba ce, da kuma ɓacin rai da ake sakawa a matsayin “tarbiyya.” KALTUME ta durƙusa gindin murhu, hannu na famar busa wuta, idanunta cike da hawayen da basu da alaƙa da ƙanshin hayaki. Ita da kanta ba ta san me ya fi nauyi ba: yunwar da ke jikinta ko ciwon zuciyar da ke cike da ƙiyayya busa wutar takiye bakin ta da hannun ta iya ƙarfin da Allah ya bata ganin lokacin dawowar Malam ya kawo kai ga talken towo akan wuta ga rashin isasshen wutar . Ƙara hura iskar bakinta taye akasar murhur a banza, kanta ta ƙara ɗagowa sama, ganin gagarumin haɗarin yana ƙara haɓɓaka. Take hawaye suka malallo kan kyakkyawar fuskar nata, ƙara durƙusawa taye da gaske, ganin ta ƙara himma gun zuga wutar ittacen, ko zai kammala kafin Mallam Audu ya dawo daga gona... Dariya da shewa daga bayanta, a hankali Kaltume ta juyo tana ganin Baaba dake tsaye da buta zuwa bayingida ( toilet ) ta ƙara da cewa, "Ye dai mugani, ko tusa zai hura wuta?" Ta shiga ƙaramin bayangida dake maƙale a barandar da ake kewo akuya — ko nace akuyoyyin gidan. Kaltume ba ta tsaya binta da kallo ba, ta ci gaba da duba wutar girken ta, har lokacin da Baaba ta fito tana ɗaga butar sama da niyyar ta watsa mata ruwa a murhur da take famar ganin yana aiki. Aikuwa, taye nasarar, zuba mata ruwan taye ya watse akan ittacen. Kaltume ba ta san lokacin da ta runtuma ihu mai kama da kuka ba, ganin wutar ta mutu murguz, kamar ba ta ye wahalar awwani a ƙasar ittacen ba kafin ta buɗe baki taye magana, sai ga ruwan sama kamar da baƙin ƙwarya nan da nan. Hawayen da ruwan suka mamaye fuskar ta cikin azaba. Ta fara ƙoƙarin mikewa daga durgushen, sai dai kash guiwarta bai amince ba, sakamakon wane azaba da ƙafar take mata tumbin nata ta ƙara himma gun tashi, ga talken masarar yana huce, gaba ɗaya ruwan sama ya shigi ciki, ya zama kunu sai zubewa yakiye inda Baaba ta barta tana dariyar mugunta. Ba zato ko tsammani Kaltume ta tsinci kanta a mugun yanayi, ihu kawai ta yi, tana neman taimako "Har yanzu bakiye hankali ba! Ashe mahaukaciyar! Ina ce ke abincin nawa ke zuba a ƙasa? Wawiya karuwar banza!" Yana duka, yana ihu da surutu a ihun neman ceto, duk suka fito daga dakunan su ba wanda ya je balle ya karɓe ta daga azabtar da yake mata. "Kaltume, nasha wahalar noma, na kawo abinci ki ci! kiye kashi shine za ki min asarar tukunya gida!"yar da sandar hannunsa yayi, ya ɗauko tukunyar, ya kwara mata a jikin ta. Inda taye sauri kifewa domin ta kare cikin ta daga azabar wuta, duk da cewa ruwan sama yasa ya huce, amma har yanzu akai bala’e zafi wanda yayi sillar tarwatsewar dukkan jiyoyin jikinta. Ihu ta buga don wani bakin azabar da ya shiga sassan jikinta... Kamar yadda zai dinga karɓan tuwo daga tulu, haka ya ɗauki sanda ya dinga zuba mata da sukar magana "Wawiya! Ashe ke har yanzu baki yi hankali ba! Abinci nawa kike zubarwa wai ke wacce irin sakaryar ce mata hankali da gumi na kike wasa don ubanki ?" Inna ce ta ga abun ya wuce misali, ganin azaba da wuta, da sauri ta baro nata guntun ɗakin taɓon ta iso tana faman janye sa da cewa: "Kai Audu, zakaye kisan kai! Shikkinan ka kashe ta!" Ganin lallai Kaltume bata numfashi sai yanzu ya lura da mugun ɓarna da yakiye, ganin fatar jikinta na suɓukewa daga ruɓaɓɓon kayan ta... "Ke Ma’u tahu nan!" ta faɗi tana kallon Baaba da take zabga murmushinta hankali kwance. "Allah yasa shegiyar ta mutu na huta da ganin baƙinciki." Wutar murhun da ya dade yana so ya hura ya hana fitowa daga hanyar jikin sa. Kaltume ba ta da iko — jikinta ya saki. Amma zuciyarta tana kuka, tana kuka da Allah... "Ka bar ɗana ya rayu kayi masa jagora... ka sa kada ya zama kamar ni wallahi bada niyya na aikata ba ." zuba mata ido a makance ihu ta buga " Nashiga Ukku uwata na tuba Allah ka gafarta min , cikin ihun azaba ta yanke. numfashi rayuwa ta ɗauke babu kukan da ya isa ya hana mutuwa. Babu idon da ya isa ya ɗaga murya kowa shiru Sai ihu. Ihu daga ciki... ihu daga sabuwar rai da ke ƙoƙarin shigowa duniya...Kai Audu, kamata muyi ɗaki da ita, suna ƙoƙarin ɗaukar ta, sai ga kan jariri na ƙoƙarin fitowa daga cikin mahaifiyar sa da sauri suka ƙarasa da ita ciki. Duk sun yi cirko-cirko suna ganin haihuwar Kaltume da bata numfashi, amma ga yunkurin haihuwa. Tun suna ƙoƙarin tayar da ita, amma Kaltume rai yayi halin sa ba alamar numfashi a jikin ta. Inna ce ta fita zuwa maƙobtan su har ruwan sama ya ɗauke, ba alamar fitowar yaro ga kai ya maƙale. Ganin ba kowa a ɗakin, Baaba ta juya gabas da yamma, hannu tasa ta tura kan yaro da ƙarfin tsiya masifa don ya kuma cikin mahaifiyar sa dake kwance a matsayin gawa mai tururren wutar talken tuwo... Cikin hanzari, Inna ta shigo da maƙobtan su ihu Sallame ta tsala: "Kaltume ta mutu, waiyoo! Allah na mutu, na lallace, shikkinan sun kashe ta, sun yi kisan kai!" Haka ta fita bakin zauren gidan tana tsalalla ihu da wanda suka hallara da masu hallara abin da ya ɗaurewa Inna kai. Ganin yaron ya kuma ciki da kallon tuhuma, ta nufi Baaba da sauri ta antayo idon ta waje: "Na rantse miki Inna, ban yi komai ba. Asali ma na fita don ina tsoron gawa..." Inna ce ta fito daga sunkuye tana hango tillon ɗanta Audu da ya zabga uban tugumi cikin tsoro da fargabar abin da zai iya faruwa a gaba. Da sauri ya matso kusa da Inna: "Ina fatan bata mutu ba..." Cikin murya mai amo da ƙaraji daga bayan sa: Is just a beginning gaisuwa ta musamman ga Sister Ummi Nagode sosai Allah ya saka da alheri Allah ya biya da gidan Aljanna , Allah ya sauke ke lafiya , HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. Ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya...** Itta baiwa daga Allah ce, Ubangiji ke bada itta ga wanda ya so. Duk wanda aka ba wa itta, sai ya sarrafa ta yadda ya ƙi so: wani ta jawo masa arziki, wani kuma ta janyo masa ɗaukaka da masoya masu girma da daraja... PAGE 1 Paid book 300 only , posting daga Monday zuwa Friday in Sha Allah 08101235739 FREE PAGE NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC?mode=ac_t YouTube channel domin samun littattafai na Hausa don't forget please like and subscribe , Thank you. https://youtu.be/6-Jrkc2kmmE FREE PAGE ... SHARE FISABILLILAHI 08101235739 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 2 “You are under arrest, Audu Dogoro!” Juyowa yayi a tsoraci, jin yaren Turawa ta ki hanjin cikin sa suka murɗa, zubewa yayi a ƙasan. Ɗan sandan yafara bigima da rantse-rantse... Cikin firgici da tashin hankali wasu ƙoƴaƴyun 'yan sanda suka shigo gidan, sun zo bisa kiran gaggawa da maƙwabcin su Mallam Sambo ya yi, wanda tun farko yake leƙen halin da ake ciki daga katagangarsa Ganin halin da Kaltume ke ciki da kuma faɗuwar jikin Mallam Audu a kasa yana birgima cikin ruwa da ƙasa yasa ɗayan 'yan sandan ya ɗaga murya cikin ƙarfi: “Nobody moves! kai, Malam Audu Dogaro, ka tashi mu tafi!” Audu, cikin fargaba da rawar baki, ya fara birgima yana cewa: “Don Allah malam 'dan sanda kuyi hakuri! Wallahi ba ni na kashe ta ba! Allah na sani, wallahi ba da gangan ba! Tukunyar ce kawai ta zube... ni dai ban kashe ta ba!” Cikin ƙarya da ruɗu ya fara zubo rantsuwa, yana yunƙurin kare kansa daga halin da ya jefa kansa ciki. Ya koma yana yi wa kansa kuka, yana nannade hannayensa yana roƙon gafara. Maƙobtan sun cika harabar gidan, wasu suna hawaye, wasu suna siffanta ta da kalmomin alhini. Mallam Sambo kuwa ya kura masa ido yana huci kamar wuta , anan wasu ke furta mugayen abubuwan da yake wa Kaltume “Wannan fa ba da wasa bane,” inji ɗaya daga cikin 'yan sandan cikin takaici. “A jikin mace da ciki kayi haka? Wannan fa laifi ne mai girma, kisan kai da yunkurin kashe jariri!” Baaba kuwa tana gefe, tana ƙoƙarin ɓoye dariyar mugunta a fuska. Amma Inna ta kura mata ido tana tafe da gumi, tana ayyana yanda komai zai ƙare. Sai kawai aka ɗaure Mallam Audu da ankwa, aka ja shi zuwa motar 'yan sanda cikin sarkakiya. Mutane na zagin sa, wasu kuma suna kallon shi da tausayi, amma da yawa daga cikin su sun fi yarda cewa akwai wani abu a ciki – ba rashin sa'a kawai ba ne. Baaba ta tsaya cak! Idanunta sun kafeshi ana ja da shi cikin ankwa, zuciyarta na huci kamar wuta da aka watsawa fetur. “Wayyo Audu! Audu na! Me kuka masa?! Wannan ba gaskiya bane wallahi! Ba zai iya kashe mace ba! Wayyo duniya ta bani!” Ta kwalla ƙara, ta zube a ƙasa ta dafe kai, numfashinta na hauhawa. Idanunta suka cika da hawaye, amma zuciyarta cike take da rudani da wata irin firgici da ba ta taɓa ji ba. Cikin wannan rikicin, sai kawai Inna ta rikice. Ta lumshe ido, jikin ta ya yi sanyi kamar daskararre. “Subhanallah!” Ta faɗi a ƙasa tamkar sanda aka sare itace. Kamar ba rai a jikinta. Hankalin kowa ya tashi! Maƙobtan suka nufo da gudu. “Ku kawo ruwa! Ku ɗaga kafafunta!” “Ina mai zare mata mayafi? Tana numfashi?” Wani dattijo ya sa hannu a ƙirjinta yana duba bugun zuciyarta. “Alhamdulillah tana numfashi... amma zuciyarta na bugawa kamar ana kara mata wuta.” Wasu suka ce a kaita asibiti, wasu kuma suka tsaya suna ambato. Maƙobtan sun firgita, gidansu Audu ya koma gidan tashin hankali. Yara suna kuka, mata suna salati, maza kuma sun rude. Wani dattijo daga cikin su ya tsaya yana kallon su yana girgiza kai: “Wannan fa ba ƙaramin al’amari bane. Gidan nan ya haukace. Wannan ba ƙaramin sharrin aure bane , ina gawar Kaltume a Kaita asibitin ƙauye ko za'a samu damar ceton yaron cikin ta cewar wani ɗam cooper ” Kamar hadari su Inna da Baaba suka runtuma da ƙafa suna bin Malam Sambo da wanan cooper min , sai maƙobta su ka biyo su da hawaye da addu’a. Har wasu daga cikin matan ƙauyen suka ɗauki jariran su, suna kuka da sambatu. Asibitin ƙauyen—wani tsohon gini ne da GOVNATI ta manta da shi. Bangon sa ya faɗi gefe, ɗakin haihuwa kuwa yana da bargo na tantanin sauro a maimakon labule. Kujerun dakin jiran gwaji duk sun karya, sai murɗaƙƙen jini a kafet da iska mai wari. Duk da haka, shi ne asibitin da suke da shi. A nan Malam Sambo ya shigo da babur ɗinsa, yana ihu: “Ku taimaka! Ku ceci ta! zai mutu! Jariri yana fitowa!” Wata nurse – mai dogon hanci da rashin jinkai – ta fito da leda a hannu, ta dubi Kaltume daga gefe: “Kai... ashe wannan ce?! Waye ya ce a haifi a gida? Ta yi rajista kuwa?” Malam Sambo na haki kamar wanda zai faɗi: “Bani da rajista! Ku karɓe ta da gaggawa... wallahi ta mutu Amman yaron na motsi !” Sai wani dattijo malamin lafiya ya fito daga wani daki, yana watsa idanu da kausasa murya: “Mun gaji da wannan halin! Duk da gwamnati bata ba mu albashi ba, har yanzu ku zo da matan ku cikin jini, babu kati, babu kudi, babu rajista. Ku na so mu yi aiki da soyayya ne?!” Inna ta faɗi a ƙasa tana kuka: “Don Allah... mu talakawa ne. Katin ba mu da shi, amma ku taimaka. Ku ceci 'yata da jaririnta. Ta riga ta shure... amma ba a gama ba...” Nurse ɗin ta girgiza kai tana faɗa: “Wani likita ba zai taɓa tabawa ba idan ba katin haihuwa. Ko a ƙarƙashin bishiya ne aka haife ta. Wannan ba matsalar mu bace.” Yayin da su ke ta masifa, wata karamar ma’aikaciyar asibiti – mai sauƙin hali – ta leƙo, ta ga halin da Kaltume ke ciki. Sai ta fasa tsawa: “Koma menene, wannan jariri yana cikin rai! Idan kuka bari ya mutu, kun kashe shi da gangan! Bari in kira Likita Bashir. Wallahi, na shiga tsakani.” Ta nufi ɗaki da gudu. Yanzu dakin asibitin cike da mutane ne. Muryoyi sun rikice. Wasu na kuka, wasu na masifa. Malam Sambo yana zamewa daga jini, ya tsaya a gefe yana zubar da zufa. Rayuka biyu ne ke rataye da ƙaramin zaren kulawa da imani. haka wanan cooper ya shiga cikin office nin ya bashi dubu biyar da ban haƙuri domin a ceto wanan abinda yake cikin matar nan... Is just a beginning 🦎KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 PAGE 1 Paid book 300 only , posting daga Monday zuwa Friday in Sha Allah 08101235739 FREE PAGE NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA https://chat.whatsapp.com/LJDc3GDF3Kt3wo6Mp1Bl17?mode=ac_t FREE PAGE ... SHARE FISABILLILAHI 08101235739 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE THREE *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Likita Bashir ya fito da hanzari cikin ɗamarwa, yana ta girgiza kai kamar zuciyarsa ta ƙi amincewa da abin da idonsa ke gani. “Ina marar lafiyar take?!” ya faɗa da ƙarfin da ya ɗauki hankalin duka cikin asibitin. Nurse ɗin da ta kira shi ta nuna wata ƙaramar ƙofa, jikinta na rawa da ɗuwatsu a ido. " can ne, Doctor... jini ne ke ta zuba kamar an buɗe rijiya...!”ba tare da wata tattaunawa ba, sai ya ɗaga hannunsa cikin hanzari, ya umarce su da su ɗauke mata da ake fama da ita zuwa ɗaya daga cikin tsofaffin ɗakunan haihuwa ɗakin nan cike yake da wari, gadon da ke cikinsa na daure da wayoyi, ya ruɓe, ruwan rijiya yana cicciko daga gefe, yana gauraye da jinin da bai daina fita ba. An shimfiɗa Kaltume hannayenta duk sun kumbura fuskarta fara ta kumbura kamar wacce aka ƙwace rai. Idanunta a rufe, bakinta bude kadan kamar mai neman taimako daga sama nurse biyu suka kama ƙafafunta da gaggawa suka buɗe su, yayin da Likita Bashir ya zura safar hannu, zuciyarsa cike da damuwa “mu ceci jariri... sai mu ceci wanda ba shi da laifi!” ya faɗa da huci, yana kai hannunsa cikin mahaifar Kaltume. Sai yaron ya fara motsawa, yana kokarin fitowa daga duniyar duhu amma jinin—jinin nan yana zuba kamar an karya madatsar ruwa nurse ɗaya ta tsayar da numfashinta, tana kallo da hawaye a idonta. “Tayi mutuwa,” wata daga cikinsu ta faɗa cikin sanyin murya mai tsanani “tayi mutuwa tun kafin a zo...” A ƙasan gadon, jini ya wuce ƙafa. Ya gauraye da ƙura, ya kumbura kamar ruwan sama da ba’a dafa ba jikinta na laushi, ba numfashi, ba motsi qmma cikin cikinta, ga rayuwa na ƙoƙarin fito da kukan farko. “Dokta, za a iya ceto yaron?” nurse ɗaya ta tambaya, murya na karkarwa. Likita Bashir ya runtse idanu, ya kalli gadon da bai dace da ɗan Adam ba ya kalli Kaltume, wannan marainiyar Allah da aka saki kamar dabba a kasuwa. Sai ya ce da zuciyar da take dukan azabar gaskiya “Zan yi iya bakin ƙoƙarina amma wannan ba haihuwa bace wannan ƙasa azaba ce, wannan haihuwa kuka ce!” Yayi ƙwace, ya jawo jaririn da ƙarfi hannunsa yana rawa, numfashinsa yana tashi da sauri. daga nesa, aka ji kukan wani yaro mai raɗaɗi, mai rauni, mai kukan ban kwana da duniyar da bai iso ba tukuna kukansa ya sare dakin gaba ɗaya dukkansu suka tsaya cak, da hawaye, da kaɗuwa, wannan yaro ba kawai ya zo duniya ba ne... ya zo ne da ihu, da baƙin ciki, da jini mai ɗumi, ya zo ne da alhini mai nauyin dutsen dutse. Inna ta durƙusa a ƙasa ta aza hannu a kai. wannan ba haihuwa bace – wani sabon babi ne a cikin littafin ƙaddara. Sai wani mutum – dogo, siriri, farin fata – ya faɗo cikin ɗakin da sauri. Likita ne, amma bakinsa kamar ya cika da al’ada ya karɓi yaron yana jijjigashi, yana kallo kamar yana karanta labarinsa ta fuska yron ya yi ihu... amma bai tsagaita ba kamar yana faɗin "ni ne wanda aka kore daga jinƙai, na fito daga cikin azaba... ni ne wanda duniya ba ta shirya karɓa ba..." Mutumin nan ya karɓi jaririn daga hannun likitan, hawaye na zubo masa “wannan yaro ba da wasa aka haife shi ba wannan... wannan shi ne Kaɗangaren Bakin Tulu!” “An barka ne, amma ba a barkar da murna ba. an kore ka, an fasa tulun da kake ciki, aka zubar da ruwan da ya kamata ya rike ka an zagaye ka da tsinuwa kafin ka ɗan sha iska. Amma Allah ya bar ka da numfashi!” Ya fito da yaron zuwa harabar jama’a. Ya ɗaga shi sama kamar ya nuna duniya cewa: “Ko ba a so shi ba, ya zo ko ba a shirya masa ba, ya fito wannan yaron... wannan yaro shine jarumin da ba a nemansa ba amma dole duniya ta karɓe shi!” Mallam Sambo – tsoho mai hangen nesa – ya karɓi jaririn da hannayen da suka girgiza. “Yaro namiji ne! ya fito da ihu! ya fito da ƙarfi da baƙin cikin rasa mahaifiyarsa a cikin zafin haihuwa ya zama Kaɗangaren Bakin Tulu! Tabbas... wannan wata aya ce, aya mai cike da darasi!” Yaron yana ta ihu, yana jijjiga hannu kamar yana faɗa da duniya da zarar ya shigo cikinta. jikinsa ƙururuwa ne, hannuwan sa kamar yana murɗa takobi ne cikin iska. Cooper ɗin likita, wanda ke rike da yaron, ya rungume shi da ƙarfi kamar yana ƙoƙarin ba shi ƙarfin rayuwa da ɗumi hawaye na gangarowa daga gefen fuskarsa, yana kallo cikin idon jaririn kamar yana neman amsar wata tambaya da zuciyarsa ta kasa bayarwa shekaru da dama. “An haife ka ne ba don ka zauna ba, Kaɗangare…” ya faɗa da siririyar murya. “An haife ka ne don ka girgiza tarihin waɗanda suka saba wulaƙanta marasa laifi.” Yaron ya yi kukan da ya tsayar da kowa cikinsa. Yana kallon sararin sama da ido da ba ya ganin komai wata tsohuwa mai suna Inna Uwaliya, tsohuwar unguzoma ce ta kauye, ta durƙusa gefen gadon inda gawar Kaltume take kwance. “Wannan haihuwa ce mai sako,” ta furta da bakin da ke rawar murya. “Wannan yaro... yaron da ba’a so ba ne amma baƙin tulu ya fasa kansa, ruwan da ke ciki ya fito da rana. Wannan yaron... zai ƙone da wuta, zai raba gaskiya da ƙarya!” Likita Bashir ya matso ya lulluɓe gawar Kaltume da farar zani ya juya yana hawaye, ya kalli nurse ɗin da ke kusa da shi. YACE ********* ABUJA Abuja — babban birni mai lulluɓe da kyalli, gine-gine masu ƙayatarwa, cike da gurbatacciyar iska mai ɗauke da kamshin arziki da sirri A cikin anguwar Asokoro, daga cikin jerin manyan gidajen gwamnati da jakadun kasashen waje, akwai wani gida wanda kallo ɗaya ka masa zaka san cewa kuɗi bai da daraja a ciki. Wannan gida ba kawai na gida ba ne Gida ne da ke da murmushin wadata, zuciyar iko, da ƙahon sirrika shi ne gidan Ministan Lafiya: Alhaji Abba. Gidan — mai matakai uku, rufinsa marmara ne na Turai, falonsa na ciki na cike da tagogi masu haske da tagulla, sai fitilun chandelier masu ƙyalli kamar rana cikin dar jikin bangon falon, hotuna ne na manyan mutane — shugabanni da ‘yan siyasa, da kuma wasu hotunan da ke ɓoye manyan al’amura da ke tafiya a bayan fage. A cikin wannan gidan kuwa akwai mutane guda biyar da rayuwarsu daban take — kowanne da nasa salo, da burinsa, da nishadinsa: 1. Alhaji Abba – Ministan Lafiya; dattijo mai mulki, mai iya ɓoye dariya da fushi a lokaci guda kallo ɗaya ba zai nuna maka irin ƙarfin da ke cikin zuciyarsa ba Allah ya mallaka masa dukiya da baisan adaddin sa ba. 2. Hajiya Zulaihat – matarsa ta fari, wacce aka aura tun kafin ya samu minister mace mai kishi da son zuciya, tana rayuwa ne a cikin gida da duhu na siyasar mijinta. 3. Hajiya Maijidda – matarsa ta biyu, budurwa ce wacce aka aura bayan samun mulki. Kyakkyawa, mai juna biyu, tana rayuwa cikin jin daɗi da kewar wasu abubuwan da ba a faɗi. 4. Alhassan – ɗan’uwan Minista, wanda ke zama a gidan ba tare da aiki ba, amma yana cin arzikin gidan mai rainin hankali da shagube. 5. Khadija – 'yar gida, bai kai shekaru 20 ba. ba jini ba, amma tana cikin gidan saboda wata alaka da uwar gida. Kyakkyawa ce, amma tana rayuwa ne a cikin inuwa. A yau, suna zaune a babban falo suna karin kumallo. Wajen cike da pancake, toast, coffee, zaƙi, da kusan komai daga Turai, amma kallon da ke tsakanin su yana ɗauke da abubuwan da ba a faɗa. Rayuwa mai kayatarwa ce, amma kowa a ciki na ɗauke da wani sirri, wani fata, ko wani laifi da ba a bayyana ba kuma ko da yake suna zaman lafiya, wata rana... za su gamu da abinda zai girgiza tsarin su.... MUJEEE ZUWA WELCOME TO A NEW JOURNEY OF KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LJDc3GDF3Kt3wo6Mp1Bl17?mode=ac_t FREE PAGE ... SHARE FISABILLILAHI 300 only 08101235739 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE FOUR 4 *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) PAGE FOUR 4 Asuba ta gabato da sanyi da ƙamshin ganyen lemongrass da aka yayyafa a falo domin dāƙile ƙamshin daddare. Amman cikin zuciyar Hajiya Maijidda — mace mai ciki — sanyi ba ya wanzuwa raɗaɗin cikinta da naƙuda yana tashi yana sauka kamar walƙiya a ɗakin da babu haske. Ministan Lafiya, mijinta, yana can Lagos ya bar gida da jiya don taron kwamitin lafiya na ƙasa ba wanda ya ɗauka zai faru ba shi ba. A lokacin da ya tafi, naƙuda bata da alamar kusa. Amma yau “Wayyo Allah... yallabaiii...!” “Ciki... yana karkarwa... kamar ruwa mai tafasa...” Sai gaban motar gida ya ɗan kaɗa – nurse ɗin da aka kira ya ta iso da ƙyar. Xulaihah, uwargida, ta tsaya a ƙofar falon manya, fuska ɗaure kamar wacce ta gaji da hakuri. “Kada ki shige cikin gidan nan da ambulance. Wannan haihuwa ba zai bar wannan gida ba. In yaro ne ke ciki – sai ya mutu kafin ya sha iska.” Ummi mai duba lafiyar gida, ta tsaya da hargowa. “Hajiya, ai ciki ba a raina masa mutuwa! wannan ba adalci bane. Ko kina tunanin Allah zai zuba ido...?” Zulaihah ta zuba mata harara mai zafi. “Allah da muke kira shi ne na ba ni ɗa — ke kuma kina son a kwace shi daga wurina. Don an ce namiji yana ƙara daraja, da dukiya a gado sai ki ce sai an haife shi...?” Gidansu Minista yana ɗauke da sirri an ce Idan mace ta haifi ɗa namiji a cikin gidan, tana samun cikon gida, gwal , iko da tabbaci a zamanta. Shi yasa Maijidda, da ta haifi mace ta farko kuma ta rasu, take fatan wannan ciki zai dawo mata da ƙima. Amma Zulaihah — bayan sunan uwargida, tana da jinin namiji. Ɗanta, Majeed, yana shekaru goma sha biyar yan gidansu sun fi nuna masa kulawa, Minista ya fi yarda da shi. Yanzu kuma... ana zargin cikin Maijidda zai iya zama ɗa namiji. Zulaihah ta kira wasu daga cikin maidens nata, suka ɗauko wata ƙaramar sanda da ruwan zafi, suka ce: “Muna iya ɗaukar ciki da taimakon zafi da matsa cikin hanji. Hakan ba saba wa doka bane — ba asibiti, ba 'yan jarida...” Umme ta zazzaro ido. “Hajiya! Wannan kisan kai ne fa!” Sai Zulaihah ta ce cikin siririyar murya: “To ki zabi — a haife da sunan ni ce uwargida kuma in koma gefe? Ko in kare gadona kafin su janye min kujera?” Wata mai aiki, mai suna Latifah, ta durƙusa a ƙasan gado, tana share zufar Maijidda da kyakyawar kyalle. “Wallahi idan wannan jariri na mace ne, zamu tuba — amma idan ɗa ne... ya kamata ki ɓoye shi. Ko in taya ki... mu gudu da shi.” Maijidda ta ji kalmomin a cikin firgici, numfashinta na tsinke kamar mai jin karar mutuwa. Kiran asuba na ta ƙoƙarin fasa duhun dare da salati, amma a cikin babban gidan Ministan Lafiya, wani irin duhu ya mamaye zuciyoyin da ke cikinsa fiye da na dare. Hajiya Maijidda – mai ciki, tana kwance cikin zafin naƙuda, tana kiran Allah da numfashi mai sarkewa: “Ya Allah... Na shiga tsanani... Ku taimake ni… ya Rabbi...” Sai wata murya mai sanyi da duhu ta dawo da ita daga tunanin ceto:ma “Taimako ba ya nan. Ki haifi jaririnki — idan Allah ya so mace ne, zamu bar ki da rai. Idan namiji ne... toh, kiyi sallama da duniya da ke da yaron da zaki haifo .” Tana ƙoƙarin tashi da kuka tana neman ƙofa, sai tayi ido hudu da Hajiya Zulaihat, uwargidan da ke kallonta da sanyi amma idanu cike da ƙiyayya. A bayanta kuwa, ƴan aikin Xulaihah ce Hannun su na riƙe da ruwan zafi da abin nade kai. A gefe ɗaya kuma, Nurse Umme ta ke tsaye a jijjiga, amma da bindigar gwiwa a kanta! “Ki motsa ki kira ambulance, ki gwada kaita asibiti — wallahi sai kin gane wannan cikin ya fi ki muhimmanci!” Zulaiha ta faɗa cikin zafin kishi, tana wani mika ƙafafu kamar zakanya. Nurse Umee ta fashe da kuka: “Amma Hajiya... zafi take ji… ciwo! wataƙila ciki ne ke kusa fashewa! Wannan zubar da jini ba alama ce mai kyau ba tana da matsalar haihuwa !” Zulaihat ta sake matsar da bindiga, ta ce: “Ki tsaya mu gani duk wanda ya yi motsi sai dai a fitar da shi da gawa cikin nan zai haifu a nan mu gane ko Allah zai bar ni da sarkin gida ko wata ’yar gata ce zata kwace gareni.” Maijidda tana kwance – hannunta yana ƙoƙarin shan numfashi, idonta sun yi jajir, jinin zufa da hawaye na gauraye da jini daga kasanta. “Ku taimake ni... don Allah... ku ce masa bana neman matsayi... bana neman gado... bana neman komai! Sai dai in haifi nawa!” Amma kowacce murya da ta fito daga bakinta sai ta tashi ne a cikin dakin da zuciyoyi sun mutu da rahama. Sai aka ji wata shigowa — yaron ƙarami Abdul-Majeed, ɗan Zulaihat, ya shigo da sanda yana kallon uwar Maijidda cikin jini. Ya ce: “Mommy Me yasa tana kuka haka?” Zulaihat ta kalle shi, ta ɓoye bindigar hannun ta “Domin tana so ta kwace gidanmu ne, ta haifi ɗan da zai sa ku manta da kai. Amma Allah bai yadda ba. Ka tafi ɗakinka babo wanda zai ƙwace maka matsayin ka a gidan muddin ina numfashi , Nurse Ummee ta fashe da kuka, ta jefar da duk wata tsoro. Ta ce: “Ni ba zan ƙare da rayuwa a haka ba wannan jaririn zai fito, in har ina numfashi!” Amma kafin ta ƙarasa zuwa kusa da Maijidda Zulaihat ta sauke yatsa kan bindiga! TATT! An ji ƙaramin harbi — ba kai tsaye ba, amma an harba kusa da ƙafarta. “Wallahi zata sake haihuwa , yanzu ne! Cikin nan yana fitowa da yardar Allah!!”sai wani abu ya faru wanda ya gigita kowanne numfashi a dakin: Jinin haihuwa ya ɓarke! Ya zubo kamar ruwan rijiya, ya ratsa zanin da ke ƙasan Maijidda, ya haɗu da gumi da zufa. “Ku taimake ni... Allah... ku ce masa… ban mutu saboda soyayya ba… na mutu ne don na yarda da ƙaddara!” Nurse Ummee ta fasa kuka sosai, ta zare hijabi ta nade hannunta Sai wata murya mai ƙarfi ta bugo daga ƙasa cikin ƙirjin Maijidda: “Uhhh... uhhh... yaa Allahhhh!” Sai kuma ƙaran kuka — kukan jariri! Na farko, sai na biyu — amma ɗaya daga cikinsu yana cikin jini sosai. Jariri biyu! Namiji... da mace. Zulaihat ta tsaya cak. Hannunta ya ɗauke da bindiga amma zuciyarta ta firgita. “Me? ta haifi... biyu?!” Nurse Ummee ta dube ta da kallo na tausayin banza: “Ke kadai kika haifi ɗa. Amma wannan matar ta haifi kaɗangaren bakin tulu — biyu ne! Kuma duka suna numfashi.” Zulaihat ta zube a kujera a daidai lokacin, an ji ƙarar buɗe ƙofa — motar asibiti ta iso daga ƙofar waje! Amma kafin su isa — Maijidda ta kalli jariranta, ta fashe da ƙara mai sanyi. Sai ta ce da numfashi na ƙarshe: Nurse Ummee ta daure gwiwa, ta jawo jarirai biyu, ta share musu fuska da jinin uwarsu. Sai ta dora su a ƙirjin Maijidda da hannuwanta da ke rawa da sanyi. “Ki riƙe su... sun riga sun fito Maijidda... ki sumbaci rayuwarki a cikin su.” Maijidda ta kama su, ta rungume jariran da sauran ƙarfinta, sai ta fashe da kuka da dariya a lokaci guda. Idonta cike da hawaye, zuciyarta cike da azaba. Ta ɗaga ɗan namijin da hannunta yana rawa, sai ta ce da karamin murya: “Kai ne... kai ne Kaɗangaren Bakin Tulu... Na haife ka a gaban maƙiyanka... sun kashe ni, amma ba za su kashe kai ba! Zan mutu ba tare da jin daɗin uwa ba... amma zan bar musu KAƊANGARE...” Ta kalli Nurse Ummee da murmushi, ta ce: “Ke ce mataimakiyar Kaɗangare... karki bar su cutar da shi... karki bar su ce ba zai rayu ba...” “Ke ce masa... bana son ya zama mara haƙuri da juriya sai dai idan zai warke da haƙuri TABBAS NA HAIFO IDON DUNIYA NA HAIFU KAƊANGAREN BAKIN TULU na haifu ka a gaban maƙiyan ka .” Idanunta sun lumshe... jikinta yayi sanyi. Sai Nurse Ummee ta fashe da kuka: “Maijidda ta mutu... amma ta bar mana jarirai biyu — kaɗangaren bakin tulu. Daya zai yi sanyi kamar uwarsa… ɗaya zai ƙona... kamar yadda gidan nan ke ƙonewa yanzu...” Sai dai kafin Ummee ta amsa, wata ƙara ta bugu! TAW!! Bindiga. Jariran sun karye daga hannunta! Nurse Ummee ta juyo da hanzari — Zulaihah ce, ta harbe iska .. sai ta bindiga taye akan yaran dukkan biyu kuwa ya tsaya chakk jikinsa ya saki. Tayi shiru amma kafin wani ya motsa, an ji karamin murya daga bakin kofar: “Oyooo Daddy! Yaaa Daddy!!” MAJEED ne, ƙaramin yaron gidan — ya shigo da dariya da nishadi. Zulaihah ta rikice! Ta jefa bindigar a bayan labule, sai ta ce cikin dukan zuciya: “Duk wacce ta ce magana akan wannan... sai dai ta rasa rai! wallahi zan sa a kasheta kamar itama Maijidda!!” Kafin kowa ya ƙarasa wani motsi — an ji ƙarar siren ambulance. Minista ya shigo da ƙarfi da jami’an tsoro masu mara masa baya don su ji ƙarar abu yaran kuwa ihu sukiye wanda ya karaɗe dukkan gidan . Kallon da yayi wa Zulaihah kamar ya fi kisa: “Ina matata?! Ina Maijidda?!” Ummee ta miƙa jariran biyu da hawaye, ta ce: Ta haihu biyu ita kuma ta mutu cikin azaba Minista ya ɗauki numfashi da ɓacin rai — sannan ya juya. Abu ya canza. Rayuwa zata canza. 🥀 Idan Maijidda ta mutu — to da rayuwarta aka rubuta babin farko. Kadangaren Bakin Tulu ya zo. Amma wa zai tsare shi daga guba, kiyayya da mugunta a gidan da aka haife shi? Is just instructions har yanzu ba'a fara labarin ba mujee zuwa free page is going Godiya mai tarin yawa ga masu mun fatan alheri Allah ya saka da dubbun alkaire daram daram tsakani na daku mujee zuwa KAƊANGAREN BAKIN TULU NA BIYU YA Bayyana a Birnin Abuja.. 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LJDc3GDF3Kt3wo6Mp1Bl17?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE FIVE 5 300 only FREE PAGE 08101235739 *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) PAGE FIVE 5 ( Akwai wacce ta biya kuɗi banyi save number ta ba and I don't know u at all idan kinga post nan DM Please Wattsp na yayi disappeared thank you 💕). TSIBIRI Cikin duhun dare da sanyin iska, wata mata tana gudu cikin dajin yankin Maiduguri. Ƙafafunta cike da ƙura da jini, ciki kuma na ƙaton ciki yana girgiza tamkar zai fito kamar wacce ta ratsa azaba, tana ta rawar jiki tana duban baya lokaci-lokaci. "Allah Ka kare ni da abin cikin nan… Allah ka cece mu daga hannun su…" ya faɗa da karamin murya yayin da hawaye suka haɗu da zufa a kumatunta. A lokacin da ta iso gaban kogin Bula, sai ta tsaya ta shaƙi iska – tana ƙoƙarin cewa da kyar ta iso amma karar bindiga ta sake girgiza gabobinta. sai gashi TSAA!! an harbe ta a tsakiyar bayan ta , jinin ya ƙara zuba daga ƙafarta – amma bata tsaya ba, tana ƙoƙarin kare cikin cikinta. Da wani kishi mai ban mamaki, sai kawai ta faɗa cikin kogin tsunduma, ruwa ya ɗauketa da sauri ya niste ta zuwa cikin duhu da ruwan kogin… Ba da jimawa ba, motar jeep mai baƙin gilashi ta tsaya a gefen dajin sai wasu mutane uku masu sanye da baƙin kaya, suka fito, fuskar su a rufe da baƙin mayafi suka tsaya a bakin kogin, ɗaya daga cikinsu ya kalli cikin kogin sannan ya ɗaga waya: Yallaɓai mun kammala aikin mun kawar da ita da abin cikin ta ko gawar ta baza a tsinta ba." sai suka koma motarsu suka bar wuri cikin gaggawa, yayin da kogin ke ci gaba da kwarara da sirrin da yake ɗauke da shi… ( Amma a cikin ruwan kogin akwai tsarkakken jariri wanda Allah ya tanada masa tsira zai rayu, ko da kuwa ba a san yadda ba tukuna. Wannan shine Kaɗangaren Sarauta – wanda ba ruwa, ba bindiga, ba makircin duniya zai iya hana sa bayyanar da ƙaddararsa. ) Tsssshhhhh... Karar ruwan teku yana bugawa da ƙaƙƙarfan dutse a bakin wani tsibiri da ba a tasamma — babu kowa a kusa, sai tsuntsaye masu fari da baki suna shawagi sama, suna kururuwa tamkar suna shaida wani sirrin da duniya ba ta sani ba. A can cikin kwarin kogin, wata mata mai ciki ta farka daga dogon suma, ta gaji, jiki ƙalau. sai ta buɗe idonta da ƙyar, tana kallon rana mai taɓa gashinta mai danshi jiki na rawa, ta fara motsi, tana jin zafin ciki da naƙuda. A lokacin da numfashinta ke yin nauyi kamar zata shude, sai kawai aka fara hango tsohuwar mata mai farar kaya tana karasowa daga cikin ƙasar tsibirin. Fuskarta cike da natsuwa, kamar ba ta da tarihin duniya, kamar kuwa aljana ce ta bakin ruwa, annuri ya lullube ta. Ta ƙarasa wajen matar da ke buƙatar taimako, ta durƙusa, ta ce da ita "ki zauna... kar ki tsorata. Allah na tare da ke. Lokacin haihuwa ya yi, kuma wannan ɗa ba zubin azzalumai bane — jarumin ƙasa ne da murya mai ƙarfi." Cikin hanzari da tausayi, tsohuwar ta taimaka mata – sai aka ji kuka... kuka mai ƙarfi, wanda ya sa tsuntsaye suka firfito daga duk inda suka buya. Jaririn da aka haifa namiji ne – mai cikakken lafiya da farin fata, kamar haske a cikin duhu sai matar ta ɗaga shi sama – hawayen farin ciki a idonta, jikinta rawa, jini yana ƙara zuba daga kafarta, ta ce: "Na haifu KAƊANGAREN BAKIN TULU! Ko ana so ko ba a so… watarana zaka tsaya cikin alfahari ka hana zalunci da murya ka." "Ina fatan ka zama cikakken ɗan jarida – ka daga muryarka a gaban duniya da masarautar ku, har kogin ya rabe biyu daga ƙarfinka. Ka zama farin cikin masu shiru da mafitar masu rauni." Sai ta lumshe ido, ta miƙa jaririn ga tsohuwar, sannan ta faɗi – numfashinta na ƙarshe. Ruwa ya tsaya kamar yana girmama jarumar da ta kawo ɗan ƙasa duniyarta. Tsohuwar ta ɗaga sa sama cikin kururuwa ta tace na saka maka suna SUHAYL yakai bil adama ta shige da jaririn ciki tsibiri… ba a ƙara ganinta ba 🌊 KAƊANGAREN TSIBIRI / SARAUTA Suna: Suhayl Ma’ana: Tauraro mai haske daga cikin duhu Halinsa: Rayuwarsa cike da asiri da wahala. An haife shi a bakin kogi, mahaifiyarsa ta faɗa ruwa bayan an harbe ta. Zai zama ɗan jarida mai zamewa murya ga marasa murya, kuma zai tunkari masarauta da kalmar gaskiya. Shin ya kuke tunanin rayuwar sa zai kasance tsakanin aljannu da namun daji .. shin burin mahaifiyar sa zai cika? shin waye shi ? me asalin labarin jinin sa ? Ina muku barka da juma'a 08101235739 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE SIX 300 only FREE PAGE 08101235739 *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) PAGE SIX 6 ( Akwai wacce ta biya kuɗi banyi save number ta ba and I don't know u at all idan kinga post nan DM Please Wattsp na yayi disappeared thank you 💕). Happy birthday 🎉 to my lovely big brother Allah ya ƙara shekaru masu albarka da amfani more more money in ur bank account.. 25 august.. GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , GAISUWA Gaisuwa na musamman ga masoyyiya ta a bar alhafari ba sister Habiba Ubangiji na tare dake a dukkanin motsin ke da shirun ke.. KANO A cikin ƙasar Kano, a gindin duwatsu masu launin toka, a bakin goggin da ke fitar da iska mai sa sanyi ta huci da dare, akwai ƙauye da lokaci ya ci—amma bai jefar da mutanensa ba. Sunansa: Gidan Rini. Ƙauyen da gwamnati ta manta da shi, da bishiyoyi suka maye gurbin gine-gine, da rijiya ce kaɗai ke zama asibiti, da masallaci ya zama gindin bishiya. A nan ne ake haifar rayuka da ake kawar da su kafin su futo duniya gaba ɗaya. Mallam Sambo ya kura musu ido. Bai ce komai ba. Sai kawai ya rungumi jaririn da ƙarfi kamar yana kare masa duniyar da ta riga ta bijiro da masa da zafi. Zan baka suna Bashir domin ka kasance mai bushara a wanan rayuwar muna godiya ga likita Bashir da ya fito dakai wanan duniyar da taimakon Ubangijin Halitta,, nan Baaaba ta juya da bakin ciki da takaice da sasaqesaqeen abinda zuciyar ta ke gayama ta akan wanan yaron da ta so kashewa tun a cikin mahaifiyar sa . Nan Inna ma ta kama hanyar ta kai tsaye sai wani ruɓaɓen Police station nasu wanda bashi da bambanci da kasuwa mai ɗakunan mashaya da ƴan chacha da zuwan ta taga Audu zaune yana cin kurasa da ganin ta ya miƙi " Inna me ya faru a asibitin" hararra ta buga mai da cewa " ita wanchan ta mutu Amman ta bar yaro mai ban mamaki kamar ba kaine uban sa ba jajajjur dashi kamar uwar sa " nan wani mai uniform na ƴan sanda yazo yace Yaya mekekeso goron bakin ta ta zubar a kusa dashi " to Mallam ɗan sanda abinda aka saba shine yanzu ma ka gayyamin nawa zamu baka ka kashe wanan maganar dukkan ta kawai yayi Amman bai kashe ta ba lokacin ta ne yayi " girgiza kan sa yayi yasan hakan zai faru daman nan yaja tumbin sa da ya zaxzzago yana waige waige ya matsu kusa da kunnen ya " ke kawo dubu goma yanzu sai ku tafe gida " zaro ido taye waje Amman kaima ka fara shaye shaye ko to ko sata zanyi ai banga wanan uban kuɗin ba ". tsaki yaja " kedai anyi tsohuwar banza yaron ke yayi kissan kai zamu rufa masa asiri kicce wai bazaki iya ba to zan kira shugaban mu nawan nan qara mar hukuman....................kai malam dan sanda kai meya sa baka iya magana haka ba karufa min asiri duk inda zan shiga zan fita zan nemo maka dubu goma don ka sake min yarona don shi kadai na mallaka malam audu bawa ni bayan shi duk duniyan nan......................." Cikin azama da gaggawa ta fita tana azama ta zazzago akuyar gidan su tayi wojen malam jauro har tintub be takeyi yi tana qwala kira hakan yasa Malam Jauro ya fito da ga bukkar bayan gida daga jin Salaman Inna yasan me ya kawo ta, " kai Jauro muyi ciniki nawa zaka seya haba innar audu ko gaisuwa babu abu ne na gaggawa ya tashi.............sai yace ya maganar gawan kultume an dawo da ita duk cikina na ciwo na dawo gida,? kaga Jauro ba wannan ya kawo ni ba na kawo maka akuyar sayarwa ne kaban dubu goma ko rance ne ka aramin ga akuyar nan " yace to Allah ya kyauta" ..................bai jima da shiga ba yafito da ɗan kuɗaɗen sa bayan ya rataya akuyar cikin tumakin sa ************* A guje ta shigo police station in ko sallama babo takalmin ta a hannu sai dogon hali takiyin cikin azama Mallam ɗan sanda ya fara lashe baki ganin ta dawo da wuri don tabbas yau akwai dabkee a gidan sa .. tana bashi wanan kudin ya ɗirgasu tsafff sun cimma dubu goma nan aka fitar da Mallam Audu Bayan dawowarsa gida a cikin damuwa da bakin cikim haihuwar Kaltume " akan wanan yaron aka rufe ne a police station don kutumar " ..... kafin ya gama sai ga sallama liman a kofar gida cewa a fito da gawar Kaltume domin a mata wanka da sutura akai ta makwancin ta haka ya kasance Mallam Sambo yayi jagora a inda aka nema Audu aka rasa shi mutane nata tsigume a ƙauye cewar matar sa ta mutu a sanadin sa kuma bai sallar gawar ta ba balle ya Kaita kabarin ta .. 🌾 KAƊANGAREN ƘAUYE Suna: Bashir Ma’ana: Mai bishara, mai kawo haske Halinsa: Jarumi ne mai dogon juriya. Rayuwarsa cike da gwagwarmaya, amma yana da zuciyar son gaskiya da kare talaka. Wanan kinan .. ABUJA Kallon da yayi wa Zulaihah kamar ya fi kisa: “Ina matata?! Ina Maijidda?!” Ummee ta miƙa jariran biyu da hawaye, ta ce: Ta haihu biyu ita kuma ta mutu cikin azaba Minista ya ɗauki numfashi da ɓacin rai — sannan ya juya. Shigowar Zulaihahr cikin dakin ta ta rufe windows nata zuciyar ta sai bugawa yakiye akai akai ta daura hannun ta akan ta "Wayooo Allah na na mutu na lallace nayi kissar sauran ƙirris a kaine gidan Yari na shiga ukku ya zanyi " firgitt ta tashe ta buɗe wardrop nata nan ta zaro wani ƙaramin akwati ta fito da wani abu da aka zagaye da jan ƙyale tashi tsaye taye ta kashe hasken ɗakin gaba daya ta fito da wanan abun tama ɗagawa sama sai ga madubi ya bayyana a cikin sa nan ta ajiye yana kallon kudu ta shaffa da hannun ta guda biyu , akai ta fara wasu sambatu da ba'a ganewa kwatsam sai dakin ta fara girgiza kamar za'ayi ruwan sama " hhhhhhhhhhhhhhh wani murya mai amo da ƙaraji ya ƙauraye ɗakin da wani sautin mara daɗi. sauraro man madubin yayi duhu ita kanta ta tsira matukar gaske nan zufa ta fara kwatanta daga kanta har izuwa tafin kafuffunta ....... "Kinye saki kinye gaggawa kina bachi domin an haifo KAƊANGAREN BAKIN TULU alƙawarin Ubangiji ya cika tabbas bazaki iya komai ba " ya faɗa cikin sarƙaƙiyar Muryar sa mara sa daɗi.. cikin hawaye tana na shiga ukku na lallace me za ayi ka taimake ne banson Yaron nan ya rayu a doron duniya " dariya ya sake ƙyalƙyalewa dashi Yana cewa alƙalamin ya bushe KAƊANGAREN ya fitoo sai dai ita maccen zamu iya kashe ta kafin akaita asibitin Amman wanan yaron bamu isa mu taɓa shi ba " nan ta durgusa taye wani ihu mai bakin ciki yanzu ne za'ayi ka nunamin hanya kaine Ubangiji na .... " Ka duba min kar asiri na ya tuno akaine gidan yari "..Babo wanda zai ye maganar mutuwar ta kowa zai manta da asalin mutuwar ta Amman da sharaɗin cewa dole watarana zamu tambayi ke ladar aikin mu cikin gaggawa tace ta yarda kafin ya saurarre abinda zaice nan ya Kuma da dariya ya ɓace ɓatttt Isowar sa asibiti da yara biyu har na maccen ta mutu nan aka sata a kwali saiga hawaye a idon sa ya share ya ɗaga yaron yana mai cewa " nayi maka suna Rayyan Ubangiji Allah ya kare min kai a gaban ido na da bayan numfashi na Allah ya daukaka darajar ka ya sanya sallama a cikin zuciyar ka da juriya da haƙurin rayuwa da zaka fuskanta ina sonka domin Allah .kuma Allah ya jiƙan mahaifiyar ka RAYYAN 🌆 KAƊANGAREN BIRNI Suna: Rayyan Ma’ana: Kyakkyawa kuma mai albarka Halinsa: Ya taso cikin duhun wulaƙanci da cin zarafin uwar sa, amma ya zama jarumi mai ɗokin kare 'yancin mata da yara. Hankali da ilimi ne makaman sa. Narnah ƙanwar soja ✍️✍️✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 7 300 only FREE PAGE 08101235739 *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) PAGE 7 ( Akwai wacce ta biya kuɗi banyi save number ta ba and I don't know u at all idan kinga post nan DM Please Wattsp na yayi disappeared thank you 💕). GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , GAISUWA Gaisuwa na musamman ga masoyyiya ta a bar alhafari na sister Habiba Ubangiji na tare dake a dukkanin motsin ke da shirun ke.. SUMMARY 🌾 KAƊANGAREN ƘAUYE Suna: Bashir Ma’ana: Mai bishara, mai kawo haske Halinsa: Jarumi ne mai dogon juriya. Rayuwarsa cike da gwagwarmaya, amma yana da zuciyar son gaskiya da kare talaka. Shine yaron da baban sa yayi sanadiyar mutuwar mahaifiyar sa ta hanyar duka da zuba mata ruwan talken towo sanan aka so a kashe she sai dai Allah ya nufa sai yazo duniya . Shin ya rayuwar Bashir zai kasance a wanan ƙauyen da uƙubar cikin gidan su? 🌊 KAƊANGAREN TSIBIRI Suna: Suhayl Ma’ana: Tauraro mai haske daga cikin duhu Halinsa: Rayuwarsa cike da asiri da wahala. An haife shi a bakin kogi, mahaifiyarsa ta faɗa ruwa bayan an harbe ta. Zai zama ɗan jarida mai zamewa murya ga marasa murya, kuma zai tunkari masarauta da kalmar gaskiya. 🌆 KAƊANGAREN BIRNI Suna: Rayyan Ma’ana: Kyakkyawa kuma mai albarka Halinsa: Ya taso cikin duhun wulaƙanci da cin zarafin uwar sa, amma ya zama jarumi mai ɗokin kare 'yancin mata da yara. Hankali da ilimi ne makaman sa. Ya rayuwar sa zata kasance a cikin gidan da Hajiya Zulaihah take zuba capacity? Wanan ba dogon tunani ko nazari bane labarin ne na jarumai guda ukku wanda akaso a hallaka tun suna cikin mahaifiyar su sai dai sun zama KAƊANGAREN BAKIN TULU a barsu su lallata ruwan ciki . a kore su a fasa tulu ko biyo ne ku chigaba da kasance wa da wanan ƙaramar marubuchiyar domin shiga cikin sabon chakwakiya da tunani mai zurfin gaske Amman wanan tafiya ta sauya salon domin wanan littafin anan zai dakata sai wanda suka biya 300 su ne zasu chigaba da samun update akan update ta private nasu . shin ka shirya ? ko kin shirya shiga cikin asalin labarin 08101235739 kai tsaye a wanan number amin magana ina godiya mai tarin yawa *Littattafan da Narnah Kanwar Soja ta rubuta:* *✓ An kammala su:* 1. *Duhu Cikin Haske* *Labari mai taɓa zuciya kan soyayya, iyali, da dangantaka.* 2. *Bayan Wata* *Tarihin abokai da suka fuskanci ƙalubale a wata tafiya mai cike da ƙarfi da bege.* 3. *Farashin So* *Gajeren labari na soyayya, ɓacin rai, da raɗaɗin zuciya.* 4. *Mijin Mage* *Labarin soyayya da rikice-rikicen iyali wanda ke jan hankalin mai karatu.* 5. *Rayuwar Ummah* *Labari mai taƙaitaccen bayani kan sadaukarwa, iyali, da juriyar rayuwa.* 6. *Biyayya Ga Uwa* *Gaskiyar labari mai haɗa farin ciki, baƙin ciki, soyayya, tausayi, da haƙuri.* 7. *Ruhi Biyu* *(Labarin da ya kasance a matsayin ban tsoro da fargabar ruhi ?)* 8. * Hanyar Ruwa* ( Fyaɗe da cin zarafin yara mata ) 9* Ahlin Laashkar* (, Hargitsin sarauta da jarumta na yara mata ). 10* Princess Rahilat * ( Adventure story da ya shiga gidan masarautar na gargajiya salon mulki da bajinta ). 11* MAI CIKI CE ,* ( Nishaɗi salo na musamman ma masoya tare da rikicin masu rikicin) 12* Zaɓin zuciya* ( Soyayya, tausayi , mai karya zuciya ). 13 * Madobin ido * ( Just romance and drama , ga masu lesbian da kwaɗayin duniya). 14* KAƊANGAREN BAKIN TULU* ( Labari na musamman wanda aka fara shi yanzu ). 08101235739 NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 8 300 only 08101235739 KANO (ƘAUYEN RIMI) BAYAN WANI LOKACI ...Suratul Mulk... Bashir na durƙushe gefen rijiya, hannunsa cikin ruwa, yana wanke kayayyaki. Muryarsa ta mamaye sararin ƙauyen, yana maimaita ayoyin Suratul Mulk da nutsuwa irin wadda take saka zuciya ta lafa. A hankali kukan saƙa ya shiga cikin karatun—ba kuka na rauni ba, kuka ne na wanda ya haɗiye damuwa da fata ɗaya: samun rahamar Ubangiji. Kamar wanda aka ɗora masa nauyin duniya, bai ma ji motsin da ke bayan sa ba har sai da wata murya mai cike da ƙiyayya ta katse shi: > “Wai kai! Wani irin mahaukacin yaro ne? Wawa ɗan iska! Mu za ka ishe mu da shegen muryarka? Ina bacci kana damuna da karatu? Wa zaka gaya wa cewa kai mai karatu ne?” Ba tare da ta tsaya ba, sai ta bugo shi da dundun a baya. Bashir ya saba da duka tun yana ƙarami—mai zafi da mara zafi—don haka ya ce cikin ladabi: “Yi haƙuri, Baaba. Ban sani ba kina bacci.” Bai ɗaga kansa ba, ya ci gaba da karatu a hankali. Amma sai warash!—sandarta ta sauka a bayansa. “Don uwarka na hakanaka karatun ne zaka yi?!” Zafin ya ratsa jikinsa ya kai har kwakwalwarsa. A wannan lokacin ya ɗago, idanuwansa jajjir, amma kyawunsu ya fi duka fuskar sa. Idanunsa farare, tamkar an hura haske a cikinsu, sai ƙasan idanun da yake baƙi kamar an zana masa kwalliya da ƙyalli. Baaba ta ce da tsaki “Shegen idonka nan da kake kallo na dashi... wata rana sai na zubar maka dasu.” Bashir ya yi murmushi kaɗan—murmushin da ke da ɗan ɗaci. Duk da rashin ƙiba, yana da wani ƙefin da baya iya ɓoye. Abin mamaki, duk lokacin da Baaba ta kalli idanunsa, sai ta kawar da nata cikin hanzari, kamar tana gudun wani abu da take ji a zuciya. “Allah, ka ba ni mafita,” Bashir ya furta a ransa, yana ɗaure kayan mata da yake wankewa. A nan ne Inna Uwaliya ta fito daga ɗaki, tana tura baki, duk haƙoranta sun zube. Tana riƙe da sanda a hannunta tana mai magana da muryar da take cike da hukunci: “Bashir! Bashir!! Bashir!!!”Da sauri ya amsa, cikin ladabi “Na’am, Inna, gani nan zuwa.” yana rarrafe ya durƙusa a gabanta “Gani, Inna. Kina da wani aiki ne?” kamar wanda ke tsoron kallonta, ya tsaya shiru yana sauraren abin da zata ce a dai dai lokacin da ya gama tambayarta, "Ko kina da wani aiki ne da zan yi miki?" Ta kalle shi da wani irin murmushi mara annuri, sannan ta ce: "Ka tafi bakin rafi ka gama wankinka. Kuma daga yau na sa maka doka — kar ka ƙara mana wanki a gida duk abin da ka ke yi, ka yi shi a bakin rafi." Kalmomin sun zame masa ƙamshi mai ɗaci. bai iya cewa uffan ba, ya kama hanyar fita sai hawaye suka fara taruwa a idanunsa, zuciyarsa na cike da wani nauyi da shi kaɗai ya san yawan sa. Maganganunta sun buga masa zuciya kamar wuka. Kafin ya samu damar cewa komai, ta juya ta bar shi, ta bar masa ƙura da ƙuncin rai. Ya tattara rigunan da ya gama wanke, ya ajiye a gefe, ya kama hanyar bakin rafi. Kowane mataki da yake ɗauka yana jin zuciyarsa na nauyi. Ya kwashe kayan kafarsa, ya ɗora a kafaɗa. Hanya mai nisa, mai sanyi amma a gare shi ta zama hanyar azaba. Yana tafiya yana sheshsheƙar kuka, yana maimaita a ransa: "Wai Mama na... me yasa kika mutu kika bar ni? ne yasa kika tafi kika bar ni cikin wannan duniya babu wanda zai rufa min asiri?" A cikin wannan tafiya, kowace ƙafa da ya ɗaga kamar ta ɗauke wani ɓangare na ƙarfinsa, amma zuciyarsa tana ƙara nutsewa cikin wani daki mai duhu — dakin rashin uwa. Hawayen ba su jira ya isa wurin rafi ba — suka gangaro daga idanunsa cikin sauƙi, suka haɗu da ƙura a fuskarsa ya zauna a bakin rafi, yana jin ƙarar ruwan da yake gudu tamkar yana yi masa waƙar baƙin ciki. Sai ya furta cikin murya mai rauni, wadda da kyar za a ji: "Wai Mama na… me yasa kika mutu kika bar ni? Waye yanzu zai rike ni kamar yadda zaki rigi ne ?Waye zai yi min dariya idan nayi kuskure? Mama… yaushe zan sake ganinki?" Kamar wani yaro ƙanana da aka tsinci a cikin duniyar da babu tausayawa, ya runtse idonsa yana jin sanyi na ruwan rafi a hannunsa, amma zafin rashi a zuciyarsa ya fi kowanne sanyi ƙonewa. A haka ya ci gaba da tafiya, zuciyarsa cike da raɗaɗin zafin rashin uwa, hawaye na zubo masa kamar ruwan sama. Kamar dai duniyar gaba ɗaya ta ɗauke masa ƙauna ta maye gurbin ta da shiru da kunci. Kwatsam, ba tare da ya lura ba, ƙafarsa ta bugu da wani abu — ashe ƙafar mutum ce! A cikin ɗan kankanin lokaci jikinsa ya yi sanyi, ƙafafunsa suka yi laushi kamar za su saki, ya fara faɗuwa ƙasa a hankali, “laauuuu…” Kafin ya kai ƙasa, sai kawai ya ji an ɗan tsinke iska a bayan sa — wifff! — wata hannu ta kama rigarsa ta baya da ƙarfin da bai zata ba. Kamun ya tsaya masa tamkar an dasa shi a wurin, zuciyarsa na bugawa da sauri. Ya tsaya cak, idonsa ya lumshe, zuciyarsa ta fara tunanin ko wannan shi ne farkon wani sabon labari… ko kuma wata sabuwar ƙaddara. ***************************** ABUJA Fitsari ne ya kuɓuce masa ba tare da ya ankara ba, sai ka ji zulllll yana zuba a ƙasa, yana ƙara tsananta kunya da raunin da ke cike da zuciyarsa. Kafin ya iya share hawayen da suka gangaro masa, wata jabbar bulala ta tsinke a bayansa, ta shigar masa da zafi mai tsanani har sai da ya yi wani irin tsalle ya sulale ƙasa kamar ruwan kankara da aka zuba wa wuta. A can ƙasa yake kwance yana rawar zafi, hawaye suna cika idonsa, yana kallon sama da idanu masu taɓarɓarewa. Wannan yaron — kyakkyawan yaro ne, fari sol kamar hasken alfijir, fuska mai santsi wadda da ta dace ta kasance cikin farin ciki da kulawar uwa. amma yau, babu mai rungumar shi, babu mai share masa hawaye — sai duka da zagi da zafi. Hawaye suka ci gaba da zuba kamar ruwan damina, zuciyarsa na amsa masa tambaya ɗaya: “Wai Mama na… me yasa kika mutu kika bar ni a cikin wannan rayuwa…?” Fitsari ne ya kwance masa bai sani ba, sai zulllll… fitsari yana tsalle kwaɗo kamar ruwan sama daga bututun da ya fashe. Kafin ya ankara, wani jabgiggin bulalla ta tsula masa a baya — ƙarar ta cika kunne, jininta ya cunkushe, ƙashin bayansa ya amsa. A zabure ya runtse idanu, ya furzar da numfashi mai zafi, amma kafin ya sami damar tsayawa, gwiwowinsa suka yi rauni suka sulale ƙasa. Rayyan kyakkyawan yaro ne fari sol, fuskarsa tana da ɗan zagaye da ke sa idanunsa su fito fili, manya kuma masu sheƙin ƙwalla. Hawaye suka haɗu da zufa a kumatunsa, suna bin fuskarsa kamar zaren lu’ulu’u. Bakin sa ya ɗan buɗe yana neman iska, amma muryarsa ta kulle cikin kirji, sai kawai jijiyoyin wuyansa suka fito saboda tsananin zafin bulallar da ta ratsa har ƙirjinsa. BORNO 🌙 Suhyayl A tsakiyar dajin Borno, a bakin wani babban kogi mai kaurin iska da hayaniyar tsuntsaye, can nesa daga birnin da jama’a ke cike, akwai wani ƙaramar tsibiri. Tsibiri ce da namun daji ke yawo, kuma baƙon dan adam idan ya shigo, sai ya fuskanci ko dai rahama ko hallaka. A gefen wani dutse mai kaifi, yaro ne ke durƙushe — ba wanda ya isa ya ga fuskar sa ya manta da ita. Fatar jikinsa ta launin chocolate mai sheƙi, idanunsa manya, suna kaɗaɗe da hawaye amma yanayin fuskarsa ya nuna tamkar mai ɗauke da shekaru na wahala. A gabansa tsohuwa ce ta kwanta tana shirin barin duniya, hannunta yana rawar sanyi. Sai ta ce da shi cikin muryar da take dushewa: "Suhyayl... anan ne mahaifiyarka ta zo ta haife ka. Ka sani, yanzu zan bar ka, amma ka ɗauki wannan zobe... Zoben mahaifiyarka ne. Idan ka shiga birni, ka zama ɗan jarida mai gaskiya. Wannan ce wasiyyata… ka rayu da kalmar shahada." Kafin ya iya cewa komai, numfashinta ya tsaya. Suhyayl ya kalli gawar, hawaye na zubo masa tamkar ruwan sama. Ya rik'e hannunta yana girgiza shi: "Waiyooo Mama na! Me yasa aka kashe ki, ban mutu ba? Ina zan tafi yanzu?" Kukan ya ratsa dajin, ya sa tsuntsaye suka tashi. sai zuciyarsa ta lulluɓe da tausayin wannan ƙaramin yaro mai asalin gaskiya amma rayuwa ta fara gwada shi tun yana ɗan ƙarami. Narnah ƙanwar soja ✍️✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 9 300 only 08101235739 KANO – ƘAUYEN RIMI Bashir ya tsaya cak kamar mutum da aka zuba a cikin hoda. Idonsa ya rufe na ‘yan daƙiƙu, zuciyarsa ta buga da sauri kamar ta ji wani sabon saƙo daga sama. A zuciyarsa yana tambayar kansa, "Shin wannan ne farkon wani sabon labari? Ko wata sabuwar ƙaddara ce da zata canja rayuwata?" Kafin ma ya gama wannan tunanin, sai ga Haule — yarinyar da kowa a ƙauyen ya sani da halin tsiya — ta tintsire da dariyar mugunta, tana riƙe ciki kamar mai jin daɗin cin nasara. “Kai! Allah ya kama ka,” ta furta da murya mai ɗauke da jin daɗi. A gefensa, ƙawayen Haule suka zagaye shi kamar ‘yan kallo a wasa, suka zura masa ido suna jiran ganin abin da zai faru. Amma kafin su kai ga wani abu, sai Noor ta taso daga bayan su kamar iska, ta riƙe Hannun Bashir da ƙarfi tana janye shi baya, tana kare shi daga zagayen Haule. Numfashi ya ja dogo, yana mai jin ƙamshin turaren wankan sabulu daga jikin Noor — abin da ya sa zuciyarsa ta buga karo na biyu. Haule kuwa ta harare Noor, idonta cike da fushi da ƙyashi. “Wai ke Noor, ina ruwanki? Ai wannan ɗan uwana ne, . Ki daina shishigi cikin lamarin gida, kin ji ko?” Noor ta tsaya tana kallon Haule, ta na shiru amma idonta na nuna ba zata ja da baya ba. Sai Haule ta ja zanin rigarta da ƙarfi kamar zata kama yaƙi. Amma kafin ta isa kusa, Bashir ya ja hannun Noor a hankali yana nuna mata ta yi shiru. A zuciyar Haule kuwa, ba ta buƙatar jin wani hujja. Ta yi ƙaramar tsalle, ta koma cikin ƙawayenta tana ƙwala musu kira, “Ku tashi mu tafi! Wallahi sai na gaya wa Baaba yau. Zan faɗa masa duk abinda na gani. Sai yaga irin ‘yar banzar da kuke yi a hanya!” Suka tafi suna gudu, suna shewa kamar ‘yan tsuntsu masu cin abinci, suna ɗaga ƙafafunsu da ƙura ke tashi. Bashir ya tsaya yana kallon bayan su har suka ɓace a ƙofar rafi. Ya girgiza kai da ƙaramin murmushi mai ɗauke da takaici. Noor kuwa ta turo baki kamar wacce aka ci amanarta. “Ai ka kyale ta ne kawai, ka san halinta fa? Gobe sai ta je ta ƙara daɗa labari har ta mayar ka ka ci amanar gidan ku.” Bashir ya yi dariyar ƙasa-ƙasa, yana kallonta da ido mai cike da annuri. “To Noor, me kike so in yi? In yi mata dukan tsiya a gaban ƙauyen?” Noor ta murɗa zanin rigarta tana hararar sa. “Eh, ai da ka yi mata raddi ne ko ka ja mata kunne. Ba ta da kyau ka bar ta ta raina ka haka don kawai tana ƙamwar ka kuma ɗiyar Baaba.” “Kin dai san Haule,” ya ce yana ja da baya, “idan ka yi mata raddi, gobe sai ta kawo maka gaba ɗaya ƙungiyar ‘yan ƙauye.” Noor ta yi dariyar ƙasa-ƙasa itama, tana jin wani abu mai daɗi a zuciyarta — domin da alama Bashir ya fi damuwa da haɗa kai da ita fiye da komai. WANI LOKACIN Bakin Rafin Ƙauyen Rimi Iskar safiya tana kadawa a hankali, tana ɗauke da ƙamshin ruwan rafi da aka haɗa da wari na sabulun wanki. Rana ta fara hango ƙasa, ta haska ruwa mai sheƙi kamar gwal da aka jika. Bashir yana tafiya a hankali, yana rike da ƙaramin bokitin kayan wanki, kafafunsa suna tsoma a ƙasa mai laushi. Idonsa ya yi nauyi da tunanin yau ma an ɗora masa aiki kamar kullum. Sai kawai ya ji muryar Noor daga bayan sa, mai taushi kamar sanyi a zuciya. “Ka tsaya ka jira ni mana.” Ya waiwaya. Noor ce ke tahowa, tana riƙe da zanin jikinta da hannunta guda, ɗayan kuma ɗauke da ƙaramin kasko da aka cika da kayan wanki. A fuskarta akwai murmushin rarrashi, kamar ta san zuciyarsa na cike da kunci. Bashir ya tsaya yana jiranta. Suna haduwa, sai ta ɗan yi masa dariya. “Bashir, ka sake, ai wankan ba laifi bane. Idan kana tare da ni, sai ya zama kamar wasa.” Ya kasa ɗaga ido sosai, amma a zuciyarsa ya san gaskiya take. Duk da cewa shekaru kaɗan gare shi, akwai wani irin natsuwa da yake samu idan Noor tana kusa da shi — kamar iska mai sanyi bayan ruwan sama. Suka isa bakin rafi. Ruwa yana kadawa a hankali, yana tafka ƙaramin amo da ke haɗuwa da ƙarar tsuntsaye masu shela a kan bishiyoyin kusa. Noor ta zauna kan wani dutsen da ya yi fadi, ta saka hannayenta cikin ruwa, tana ji kamar tana wanke damuwar zuciyarta ma. Ta fara zuba kayan cikin rafi, tana murza su a hankali. “Ka daina damuwa Bashir, wallahi rayuwa haka take. Amma kai fa zaka ga rana mai kyau a gaba. Kar ka bari Baaba ko su Haule da su Inaa da Baba su bata maka zuciya.” Bashir ya zuba mata ido na dan lokaci, yana jin cewa kalamanta suna shiga shi fiye da yadda zata iya zato. Noor " ina cikin bachi jiya bayan magana dukkan aikin da aka ɗauramin ina cikin bachi a tsakiyar dare Baba ya dawo gida ya hau kaina da dukka cewa tun da aka haifi ne rayuwar sa ta lallace ko kuma tunda ya haɗu da uwata da ƙyar maƙobta suka shigo da Mallam Sambo mahaifin ke sune suka ceto rayuwa ta duk sanda Baba yasha giya ya dawo gida sai ya zuba min rashin mutunci da zanyi hawaye .. Matsowa kusa dashi taye ta dafa kafaɗar da saiga hawaye a idon ta ya cigaba da cewa " ba dukkan Baba nake tsoron ba bana don yana zagin mahaifiyata shin me Mama na taye meye lafinta haka zan chigaba da rayuwa ga aiki gida ga gona , ga duka ga zagi na fara gazawa Noor zuciya ta kamar zata buga duba fa ne fa satar hanya nakiye nake zuwa makaranta Allo da litattafai kuma duk sanadin ke ne , kicce mai rufamin asiri ta hanyar zuwa kina taya ne wahalar .... Dole na kasance cikin yanayi mara mesaltuwa . “Haule fa… ko a mafarki sai ta tsokane n Amma ke… ke ce kaɗai kike sa in manta da komai, duk lokacin da muke tare sai in rasa dalilin ɓacin raina ” Noor ta yi dariya ta ƙanƙance ido, tana ɗan zuba masa ruwa da hannunta. “To sai ka yi min alƙawari, idan na girma ka zama gwarzon da zan rika alfahari da shi.” Ya yi murmushi mai sanyi, sannan ya ɗaga kai yana kallon ruwan da yake gudana kamar yana dauke da sakon wani nesa. “Na yi miki alƙawari.” Iska ta busa ganyen bishiya sama da su, wani ya faɗo cikin rafi ya yi yawo. Wannan ƙaramin lokaci, duk wani bakin ciki ya ragu — domin a gaban Noor, Bashir ya samu kwanciyar hankali fiye da kowane wuri a duniya. Bayan sun gama wankin kayayyakin da aka dibo daga rafin, Noor ta ɗaga leɓenta tana hura numfashi cikin gajiya. "Wallahi Bashir, yau kam hannuna ya gama karyewa," ta ce tana zuba ƙaramar dariya. Bashir ya ɗaga kai yana kallonta da murmushi mai cike da tsokana "ke ai ke da laifi. Idan kin rage gulma da surutu da tuni mun gama tun dazu," ya ce yana miƙe don ɗora bokitin ƙarshe a gefe. Sun ɗaga kayan suka nufi inda suke shanya su kan igiya ƙarƙashin inuwa. Da zarar sun gama, Noor ta samu ta zauna ƙarƙashin bishiyar mangoro, ta jingina bayanta jikin itacen. Bashir ya zauna a gefenta, yana girgiza ƙafafunsa kamar wanda ya gama babban aiki. "Allah sarki, wannan wankau yau ya fi kowanne wahala," Noor ta ce tana ɗaga kofin ruwan da ta zubo daga kwalban roba, tana tsiyaya a bakinta a hankali. Bashir ya ƙyasta ido yana kallonta. "Ke dai kawai kina son a ga kina da rawaƙa wajen magana," ya ce yana yin dariya. Sun yi shiru na ɗan lokaci, sai iska mai sanyi ta buso daga cikin mangoron, tana motsa ganyayen sama. Noor ta ɗago idanu ta kalle shi. "Kai Bashir, idan ka girma, me kake so ka zama?"Bashir ya ɗan yi shiru yana kallon sararin sama kamar yana nazari sosai. “Uhm?” ya amsa ba tare da ya juyo ba, hannunsa na wasa da ƙurar ƙasa. Sai ya ɗaga kansa sama kamar mai nazari, idanunsa na bin gajimaren da ke motsawa a hankali. “Noor, amma ina da wani buri da kuma mafarki.”ta gyara zama, ta matsa kusa da shi, idonta ya cika da sha’awa. “Gayamin mana… ka sani bana son ka rike sirri a zuciya.” Bashir ya yi ɗan murmushi mai ɗan ɗaci, sannan ya ɗan shafi goshinsa. “Ina son wata rana na zama shugaban ƙasa.” Noor ta buɗe baki cikin mamaki, sannan ta rufe tana dariya. “Kai shugaban ƙasa? To ai sai mu sayi sabon gida a Dubai kenan.” Bashir ya ɗan murmusa kaɗan, amma sai muryarsa ta yi nauyi. “Ba kawai don gidan Dubai b zan gina manyan asibitoci kyauta na taimaka wa mata su haihu cikin kwanciyar hankali. Wallahi, Noor, da ace akwaiAsibitochi da yau Mama ta kasance tare da mu.” Muryarsa ta yi rauni, idanunsa suka kaɗa. “Da Mama tana raye, da ban sha wannan kewar da nake yi kullum ba.” Shiru ya cika tsakanin su na ‘yan dakiku, sai sautin ganyen mangoro da iska ke kadawa. Noor ta miƙa hannunta ta dafa nasa, tana jin yadda zuciyarta ta cika da tausayinsa. “Bashir,” ta faɗa cikin nutsuwa, “watakila Mama ba ta nan, amma ni zan kasance maka kamar Mama da abokiyar tafiya har ka cimma burinka.” Bashir ya kalle ta da murmushi mai cike da godiya, sannan ya yi ɗan tsokanar dariya don kau da damuwa. “To ke kuma za ki zama sarauniya ta duniya?” " babo shakka " ta faɗa tana kwanciyar akan kafaɗarsa . Noor ta ce tana dariya, amma a zuciyarta tana jin wani irin nishadi da burin ɗan uwanta.Noor ta yi dariya mai sauti, ta ce, "Ni kuwa zan zama likita, sai in dinga karɓar kuɗin masu kuɗi, na yi musu allura har su yi ihu." Bashir ya yi ihu kamar wanda aka soka masa allura, suna dariya tare har suka manta da gajiyar wankin. Wannan page nin mun barwa Bashir da Noor Barka da shigowar watan haihuwar fiyayyen halitta Annabi MUHAMMADU SALLALLAHU ALAIHI WASALLAMA SSALAM NANARH KANWAR SOJA ✍️✍️✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 10 300 only 08101235739 Memory and Romancing chapter WAIWAYE ADON TAFIYA WAYE BASHIR WAYE MALLAM AUDU WACECCE KALTUME MENENE ASALIN LABARIN WANNAN GIDAN Mallam Audu mutum ne da ya fito daga kauyen Rimi, wanda rayuwar sa ta ta’allaka ne a kan burin yau da gobe, da kuma amfanin gona da mahaifinsa ya bari a matsayin gado. Mahaifinsa ya rasu ya bar masa wannan gona, ita ce ginshiƙin rayuwarsa. Mallam Audu ya yi aure uku, amma daga cikinsu uwargida ta huɗu ce, Baaba, wacce aka masa auren dole ne da dole. Ita ce asalin uwargidan gidan. Yaran sa bakwai gaba ɗaya, amma uku ne kawai suka tsira da rai kafin daga baya ya ƙara aure. Sai ta zo a tarihin rayuwarsu matar ƙaddara — wato Kaltume, wacce ta shigo kauyen Rimi tare da mahaifinta da mahaifiyarta a matsayin ‘yan gudun hijira. Kaltume kyakkyawar yarinya ce wacce kowa zai so ya mallaka a matsayin matar aure. A lokacin da Mallam Audu ya fara ganin Kaltume, zuciyarsa ta kama da ƙauna mai tsanani. Ba tare da bata lokaci ba, ya shiga yaudara da neman hanya, har ya ja abokinsa Mallam Lado ya nema mata aikin gona a wurin shi. Kasancewar baban ta makaho ne ga tsufa a gun mamanta , ittace ke ɗaukar ɗaunyin su inda mai unguwa ya basu muhallin Zama Amma wannan ba don wani abu ba sai domin kawai ya samu damar auren Kaltume. Kaltume kuwa yarinya ce mai nitsuwa da hali nagari, kyakkyawar murmushi mai narkar da zuciya. Duk da cewa shekarunta ba su haura goma sha takwas ba, amma ta kasance abin kallo da sha’awa a cikin wannan ƙauyen. i A wannan tafiya, Mallam Audu ya gabatar da daburinsa, ba tare da wani jayayya ba aka daura musu aure. Shigowar Kaltume cikin wannan gida ya buɗe sabon babin rayuwa, domin soyayya ta rikide ta koma ƙiyayya. Babu komai tsakaninsu sai husuma da faɗa. Duk da cewa ana ta yaɗa maganganu marasa kan-gado akan Baaba, cewa duk matan Mallam Audu ita ce silar barin su gidan, hakan bai hana ta jimre ba. Ga kuma Inna, mahaifiyar Aufu, wacce komai nata ya ɓaci tun da ya auri Kaltume. Wannan ya ƙara mata tsana da tsamin rayuwa a gidan. Duk lokacin da ta kai ƙorafi wurin mahaifiyarta, sai ta bata hakuri tana ce mata: "Watarana zai wuce. Idan ta bar gidan sa, wai zai basu aiki a ƙauyen ƙarƙashin gonarsa." Haka ta kasance har Kaltume ta samu juna biyu. Cikin zabi da kasantuwar bakin ciki, ta ci gaba da rainon wannan cikin. A wannan lokacin ne Kaltume ta sake buɗe sabon babin rayuwar baƙin ciki da takaici. A daidai lokacin da aka sanar mata da mutuwar mahaifinta, a bakin ciki ne mamanta ta yanki jiki ta faɗi. Haka ta ci gaba da kasancewa cikin hawaye da rashin iyaye. Har zuwa lokacin da ta haifi Bashir sanan kuma Allah ya dauke rayuwar ta ... RUHIN MARAICE (My Next Book) BACK TO STORY ABUJA A cikin babban birnin tarayya, wuraren nishaɗi sun cika gari. Wata shahararriyar luxury, wacce ta shahara wajen tarbar yaran masu kuɗi da masu son nuna isa, ta kasance cike da walwala da hayaniya. A cikin Diamond X Lounge, wuri ne da ake kira gidan shakatawar ‘ya’yan masu kuɗi a Abuja, inda kowane dare yake cike da hayaniya da kiɗan DJ mai nau’in Afrobeat, RnB da Techno. Haske ja da kore suna walƙiya, hayaki mai ƙanshi na tashi daga “smoke machine”, ƙamshin barasa da turaren mata na gauraya har ya mayar da iska ɗaya mai narkar da zuciya. Kidan DJ Vee yana ƙara ɗaga hayaniya, hasken fitilu masu launin shuɗi da ja suna walƙiya suna baiwa wajen armashi. Kowanne lungu da saƙo matasa ne tsirara, ko da sun sa kaya sai dai waɗanda suka fi kama da kayan wasa fiye da tufafi. A cikin VIP section, Abdul – ɗan uwan Rayyan – ya zauna a babban kujera mai launin zinariya, wanda aka tanadar ga manyan baki. Babu kaya a jikinsa, kamar yadda yawancin masu zuwa wannan wuri suke yi domin nuna “yancin kai”. A gabansa kuwa, kyawawan mata guda uku sun kewaye shi. Ɗaya daga cikinsu tana zaune a ƙafarsa tana wasa da gabansa cikin fitsara da annashuwa. Ɗaya ta jingina a damansa tana wasa da gemunsa, tana shan giya daga gilashi mai sheƙi. Ɗaya kuma ta zauna a hagunsa tana riƙe hannunsa tana dorawa a ƙirjinta, tana ɗan lumshe idanu tana sakin ajiyar zuciya. Hannayen Abdul duka biyu suna kan ƙirjinsu ya suna yi musu abin da ya so, shi kuma yana murmushi yana barin kowa ya ji daɗin halin da yake ciki. Akwai iska mai nauyi daga turaren wuta da ƙamshin giya, kowa yana sha’aninsa babu wanda yake tsoron Allah. Duk wanda ya shiga wannan ɗaki na VIP, ba wani abu zaka gani a jikinsa face tsiraici, dariya, hayaniya da kiɗan da yake girgiza bango. Wannan shi ne Golden Empire Lounge – inda masu kuɗi ke ƙonewa da zunubi cikin farincikin banza.. Da zarar DJ ya ƙara kiɗa, hayaniya ta narke cikin ihu da shewa: “Yesss! That’s my jam!🔥” “Go girl! Show them!” Sai kuma ga wata sabuwar yarinya ta bayyana a tsakiyar dandalin — ƙaramar budurwa mai jiki siririya, ta durƙusa a cikin tsauri doggy style, wani saurayi a bayan ta yana buga rawa da ita da ƙarfin sha’awa, yayin da wani kuma ya rufe bakinta da sumba yana tsotsa kamar zai sha zuciya. Daga gefe, wani ya sa hannunsa yana matsa ƙirjin ta cikin ƙarfi, ita kuma tana yarfa hannaye tana tsakiya tsakanin jin daɗi da wahala. Club ɗin ya kaure da ihu: “Woooooow! 🔥🔥🔥” “She’s on fire!” “Give it to her, baby!” suna jefa mata kuɗi dollars kamar wacce ta zo yin rawa a gaban jama’a. a haka daren ya ci gaba da tafiya — sha, rawa, ihu, da abubuwan da suka fi ƙarfin ido. Ganin haka, kowa ya shiga cikin ƙarin nishadi. Wasu daga cikin masu ɗan kunya, waɗanda farko suna kallon gefe da mamaki, sai suka ɗauki farin gyale kamar labule suka lullube kewayan su amma hakan bai hana su bin yanayin sex ba. Kamar da an saka wuta a cikin ɗakin, kowanne ya fara bin sahun abin da ke faruwa. DJ kuwa, da alama ya saba irin wannan yanayi, ya canza kiɗa zuwa wani irin romantic night sexy beat da ya cika zuciya da motsi. Nan da nan hasken walƙiya ya sauya kala, ya ɗauki ja mai kauri, ya haɗa da shudi da ruwan hoda, yana ba dakin kamanni irin na finafinan waje. Shi ma ya ja budurwarsa jikin sa, suka rufe kansu a cikin hayaniya, suna chakalle cikin irin abin da suke kira da “ Sexy bebe" (Wa iyyazubillah). Abin da ke faruwa ya nuna cewa wannan wurin ba don ‘yan da suke neman nutsuwa aka gina shi ba, sai dai don masu lalata da neman sabbin hanyoyin wuce gona da iri. ********* Karfe biyar na asuba, hayaniyar club ɗin ta fara raguwa. Wani ɓangare na hall ɗin cike yake da ƙamshin turaren wuta da ƙamshin shan-shan na drinks. Fitilun da suka rage haske suna haska launin ja da ruwan hoda, suna ƙara bayyana fuskokin waɗanda suka kwana cikin gajiya da baccin maye. Yawancin ‘yan mata sun riga sun sulale suna kwance a kujeru ko kan tebura, idanu masu kumbura saboda rashin bacci da gajiya. Wasu ma sai da aka fara tada su domin su shirya fita kafin a rufe wajen karfe shida. Abdul, wanda tun daren jiya ya sha maye da rawa, ya buɗe idanu cikin kasala. A jikinsa kuwa Ramcy ce kwance, tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce aka ɗora mata kaya masu nauyi. Fuskar ta manne da ƙirjin shi, sai kamshin turarenta da gumin dare suka gauraye. A hankali ya hura mata iska a fuska, yana furta cikin kasalalliyar murya: “Baby… one more round please. Morning short sexy…” yana faɗa yana ƙara narkewa yana zagaye hannun sa akan hips nata , Ramcy ta ɗaga ido a shagwaɓe, ta turu baki kamar yarinya tana dariya ƙasa ƙasa, tana lasar gefen lebenta. Sai ta ce cikin murya mai rauni “Baby am tired… kabari sai gobe. Kowa ma ya tafi… Bachi ya rage mana. Wallahi am feeling sleepy.” Abdul ya yi dariya ya ce: “But baby… you know you’re too sweet. Even your sleep face is sexy.” ruff ya rufe bakin sa da nata , nan take suka juya har minti talatin suka ɓata suna wasa cikin nishadi, kafin su sulale daga jikin juna. Jacoub wanda ke kusa da su, yana jan tsumma yana shirin fita, ya dan tafa masa kafaɗa cikin wasa: “Hy dude, kai fa maye ne. Ya isa haka, mu fita. Remain 30 minutes club ɗin za a rufe.” Abdul ya kalle shi da murmushi mai cike da kasala, ya nuna Ramcy yana dariya: “Jacoub… baxaka gani bane? Ramcy is beautiful… so sexy. Morning sex ai ya fi night.” Dukkaninsu suka yi dariya mai ƙarfi, sai Ramcy ta yi dariyar shagwaɓa tana danna wayarta. Nan take suka fice daga wajen, kowannensu na mirza ido saboda rashin bacci da gajiya. A wajen motoci, Abdul ya riƙo hannun Ramcy yana shafa ƙasan tafin hannunta da taushi, ya ce cikin lumshe ido "By dear… see you later. Don’t forget me.” Sai ya sumbaci goshinta da ƙarfi. Ita kuma ta ce cikin shagwaɓa: “Safe trip baby.” Ya shiga motar sa kai tsaye, hanyar Asokoro . Ita kuma ta juya tana kallon bayansa har sai da motar ta bace daga gani, sannan ta shige tata motar .. Haka suka watse kowannensu ya kama hanya, zuciya cike da gajiya amma an bar musu tunanin abin da suka tsallake a daren jiya. Da zarar ya iso, mai gadi ya buɗe masa ƙofa yana lazumin safe. Lokaci kuwa ya nuna ƙarfe shida da rabi na safe. Abdul ya fito cikin tangal-tangal kamar wanda aka shanye masa kuzari, duk energy nasa ta ƙare. Ba tare da wani ɓata lokaci ba, direct ya nufi site nasa yana buɗe ƙofa kuwa sai ga Rayyan shirin tafiya makaranta. Ido hudu suka haɗa. Abdul ya ɗaga tsaki mai ƙarfi yana furta da ƙarfin rai: “Sauran Daddy ya tambaye ka ko ban kwana a gida ba ka faɗa da shegen idon ka? kutumar uwarka idan kace ban kwana ba!” Bai jira amsarsa ba ya wuce ya fāɗa kan gadon shi, ya kife jikinsa cikin gajiya. Nan take bacci ya ɗauke shi. Rayyan ya girgiza kai a hankali, zuciyarsa ta lumshe da damuwa. A cikin ransa yace: “Inna maka addu’a ɗan uwa na.” Yana fita daga ɗakin cikin uniform nasa sai ga Hajiya Zulaihah a tsaye. Ta zuba masa harara kamar wacce ke son tsinke shi da kallo. Amma saboda tana sane cewa yau Minista yana gidan, bata da ikon tsayar da shi ko hanashi tafiya a wannan lokaci. Sai kawai ta wuce gefe tana hararar shi, shi kuma ya ɗaga kai ya ƙyale ta cikin nutsuwa. No more Bad comments on this page 🔥 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 11 300 only 08101235739 BAYAN WANI LOKACI SUHAYL Cigaba da tafiya yake yi, da ɗan ƙaramin kaya a hannunsa. Yana juya gabas, sai ya rasa alƙiblar tafiyarsa. Ya waiwayi yamma, shima ya ƙi yarda da shi. Nan take maganar Kaka ta sake dawo masa cikin kwakwalwa – waccan magana da ta ja masa tsoro da kwarin guiwa lokaci guda “Idan kana tafiya, kada ka waiwaya. Ka doshi gabas, saboda a can aljanna take. Amma idan ka karkata, hanyar za ta dushe maka.” Yanzu kuwa, aljannar da aka ce masa ta gabas tamkar an rufe ƙofa aka toshe ta da duhu. Zuciyarsa ta karye, ya tsaya cak! Sai dai cikin wannan yanayi, kunne ya ɗauki kukan tsuntsaye. Murmushi ya bayyana a fuskarsa, duk da hawaye na dab da zubo masa. Ya tuna wata tsohuwar al’ada: “Inda kukan irin wannan tsuntsu yake, to ruwa na nan kusa.” Da sauri ya sauya tafiyarsa, ya bi hanyar kukan tsuntsun. Ba da jimawa ba, sai ga shi a gaban wani makakke kogi, wanda ya fi na tsibirin da ya taso girma da zurfi. Suhayl, wanda ya saba da rayuwa cikin daji, bai taɓa jin tsoro ba. Ya cire kaya, ya nitsa cikin ruwan kogin. Tsalle, iyo, linƙaya – yana shewa kamar ba shi kaɗai a duniyar ba. Ruwan ya yi masa sanyi, ya saukar da gajiyar tafiya. Sai dai lokacin ya ƙare. Ya fito daga cikin kogin, ya shaƙe jikinsa da sanyi, ya saka kaya, sannan ya ɗauki kwaryar ruwan da ya ɗebo domin guzuri. Da niyyar komawa inda ya fito, ya juya baya. Amma kash! Hanyar tamkar an juya ta da sihiri. Komai ya canza, babu wata alama ta inda ya shigo. Suhayl ya tsaya kallon duhu da sarƙaƙƙiyar hanya. Idonsa ya cicciko da hawaye. A gefe kuma, guguwa ta taso. Hadari ya lullube sararin samaniya. Walƙiya ta fara yanka sama da wal! wal!! wal!!! Numfashinsa ya daskare, zuciyarsa ta hau tsalle kamar ta zame daga kirjinsa. BAYAN WANI LOKACI Gaba ɗaya duniya ta koma masa duhu. Ruwa ya shige cikinsa, amma yanzu babu wata alamar hanyar dawowa. Tsuntsayen da suka ja hankalinsa sun yi shiru, sai kukan sarewa da iska mai sanyi da ke hura ciyayi suka ɗauki gurbin su. Idanunsa sun cika da hawaye, zuciyarsa ta ɗauki nauyi tamkar an daure ta da ƙugiya. Sai walƙiya ta fantsama, ta haska masa duhun da ke kewaye da shi. Cikin hasken nan kuwa ya hango wani dutse mai tsawo, tamkar mai tsoro, kamar ana hango mutum tsaye yana kallonsa. Zuciyarsa ta buga da ƙarfi. “Na shiga uku…” ya furta a hankali, murya na rawa. Ya runtse ido, ya buɗe, amma dutsen nan yana nan tsaye kamar yana binsa da ido. Cikin firgici ya kama hanyar gefen hagu, amma kash! Ƙafarsa ta nutse cikin laka mai ɗaurewa tamkar hannun mutum. Ya ƙwalla ihu, yana kokarin zamewa. Amma laka ta ƙara rike shi da ƙarfi. Wani irin iska mai kaifi ta huro, ta kwashe ganyaye tana tashi sama. Ya yi ƙoƙarin tuna maganar Kakansa – “duk inda ka tsinci kanka cikin tsoro, ka tuna akwai Ubangiji guda ɗaya.” Amma zuciyarsa ta ƙi natsuwa. Kuka ya kubce masa, numfashinsa ya fara sauyawa. Ji yake tamkar tsibirin da ya taso, daji da ya saba, ya barshi. Yanzu shi da daji ne baki ɗaya, babu mafaka, babu makoma. A cikin wannan firgici, sai yaji kamar an bubbuga ƙaho mai nisa, sautin da bai taɓa ji ba a rayuwarsa. "Kaka, ina matuƙar tsoron ruwan sama da walƙiya… ko dai suna ɓoye wani abu ne, kaka?" A hankali Suhayl ya shafa kansa, idonsa na kallon sararin da guguwar ta lullube. Muryarsa ta ɗauki nauyin shekaru dubu dari shida da suka ratsa rayuwarsa a duniya. "Na rayu tare da yara da jikoki da dama… amma a kaina nake ganin mutuwarsu, ko kuma rabuwa da su kamar iska ta kwace. Wannan tsibirin kuwa na zaɓa ne a matsayin mafakar ɓoyewa daga bakin cikin da ya cinye ni." Idanunsa suka kaɗa da hawaye yayin da ya tuna da yarinyarsa — wadda nakasarta ba ta hana ta dariya ba, har zuwa ranar da ruwan guguwa ya zo da jinin ta, ya haɗa da karar harbin bindiga. "Ko da jinin ya cika jikinta, ban taɓa ganin tsoron ruwa a idanunta ba. Ta kasance jaruma, ta koya mini cewa dole ne mu fuskanci daji da ruwa, ko da kuwa sun cika da tsoro. Ka koya juriya, ka zama dutse a cikin ambaliya…" Kafin ya ƙarashe, sai ihu da gurnanin da ba su da tushe suka yankar da tunanin zuciyarsa. Zuciyarsa ta buga kamar za ta tsage, hannunsa ya tsaya cikin iska, idonsa ya yi ja kamar yana hango wani abu da bai dace ba… ƘAUYEN RIMI Bashir da ya gaji da aiki yana nan yana bachin wahala da gajiya kamar baya numfashi kamar daga sama yaji wani irrin azazzabbabin duka a bayan sa wanda bai taɓajin azaba irrin sa ba tabbas ittace murhu ne aka buga masa a bayan sa har sai da rigar jikin sa ta kama da wuta da sauri ya birgina cikin kasa ta mutu tsananin azaba yasa idon sa ya ɗauki na wasu daƙiƙu a hankali ya bude su sai akan Mallam Audu ya fara masifa da hayaniya nan da nan mutanen gidan suka rugu ƙofa da ittace wutan ya biyo shi da duk i zuwa tsakiyar gidan " Nayi nadamar haihuwar ka asararre Yaro tunda na haɗu da uwar ka kwanciyar hankali na ya ƙare dangin tsiya yau ba abinda na mallaka harda gona ta ya ƙare me zanyi wallahi yau sai kabar ƙauyen nan Bashiru daga yau ne ba uban ka ba ne " da sauri Mallam Sambo ya shigo da sanda a hanun sa yana tukara ƙafa dashi tuni maƙobta sun hallara Noor banda hawaye ba a binda takiye " Haba Audu yau kuma da wanan salon zaka tashi maƙobta da asuba nan " ina ruwan ka nace ina ruwan ka tunda na haifu Yaron nan Rayuwa ta ya lallace tun yana cikin uwar sa ina ganin masiffu daban daban akan wanan yaron na shiga ofishin ƴan sanda kuɗi na sun ƙare gashi jiya na rasa gona ta so kawai yakoye na mutu ɗan banza kamar yanda uwar sa ta mutu " Ƙwarai da gaske sai yau zaga gani ai ba'a ruwan duwatsu a banza tun yaushe naki gayama Mallam Kaltume matar masiface da bala'e a rayuwar ka Amman soyayya ya rufe maka ido , yau ga irrin ta nan " cewar Baaba tana ta kumfar baki. Inna dake ganin duk abinda ke faruwa ta zubar da miyau na bakin ta da cewa " Ruwa bazai wanke ba kuma wuƙa bazai raba ba , wanda yaƙi ji ai bayaƙi gani ba ta kuma ɗakin ta ta kwanta , Biyo Bashir da sanda yayi Nan Noor ta afka jikin sa euff ya sauka akan hanun ta bata san sanda taye ihu ta faɗi ta suma ba " zuwa safiya kabar garin nan shegen yaro kai kowa sai tsiyar ka ta raɓa shi sai na tsini ma ɗan asara haihuwar masifa " yana faɗa yayi waje nan Mallam Sambo ya kama Noor ƴar sace aurar gidan sa tunda yaki Allah bai bashi haihuwar macce ba sai akan Noor to be continued – 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t 08101235739 BUNUS PAGE 300 only *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** A cikin babban birnin tarayya, wuraren nishaɗi sun cika gari. Wata shahararriyar luxury, wacce ta shahara wajen tarbar yaran masu kuɗi da masu son nuna isa, ta kasance cike da walwala da hayaniya. A cikin Diamond X Lounge, wuri ne da ake kira gidan shakatawar ‘ya’yan masu kuɗi a Abuja, inda kowane dare yake cike da hayaniya da kiɗan DJ mai nau’in Afrobeat, RnB da Techno. Haske ja da kore suna walƙiya, hayaki mai ƙanshi na tashi daga “smoke machine”, ƙamshin barasa da turaren mata na gauraya har ya mayar da iska ɗaya mai narkar da zuciya. Kidan DJ Vee yana ƙara ɗaga hayaniya, hasken fitilu masu launin shuɗi da ja suna walƙiya suna baiwa wajen armashi. Kowanne lungu da saƙo matasa ne tsirara, ko da sun sa kaya sai dai waɗanda suka fi kama da kayan wasa fiye da tufafi. A cikin VIP section, Abdul – ɗan uwan Rayyan – ya zauna a babban kujera mai launin zinariya, wanda aka tanadar ga manyan baki. Babu kaya a jikinsa, kamar yadda yawancin masu zuwa wannan wuri suke yi domin nuna “yancin kai”. A gabansa kuwa, kyawawan mata guda uku sun kewaye shi. Ɗaya daga cikinsu tana zaune a ƙafarsa tana wasa da gabansa cikin fitsara da annashuwa. Ɗaya ta jingina a damansa tana wasa da gemunsa, tana shan giya daga gilashi mai sheƙi. Ɗaya kuma ta zauna a hagunsa tana riƙe hannunsa tana dorawa a ƙirjinta, tana ɗan lumshe idanu tana sakin ajiyar zuciya. Hannayen Abdul duka biyu suna kan ƙirjinsu ya suna yi musu abin da ya so, shi kuma yana murmushi yana barin kowa ya ji daɗin halin da yake ciki. Akwai iska mai nauyi daga turaren wuta da ƙamshin giya, kowa yana sha’aninsa babu wanda yake tsoron Allah. Duk wanda ya shiga wannan ɗaki na VIP, ba wani abu zaka gani a jikinsa face tsiraici, dariya, hayaniya da kiɗan da yake girgiza bango. Wannan shi ne Golden Empire Lounge – inda masu kuɗi ke ƙonewa da zunubi cikin farincikin banza.. Da zarar DJ ya ƙara kiɗa, hayaniya ta narke cikin ihu da shewa: “Yesss! That’s my jam!🔥” “Go girl! Show them!” Sai kuma ga wata sabuwar yarinya ta bayyana a tsakiyar dandalin — ƙaramar budurwa mai jiki siririya, ta durƙusa a cikin tsauri doggy style, wani saurayi a bayan ta yana buga rawa da ita da ƙarfin sha’awa, yayin da wani kuma ya rufe bakinta da sumba yana tsotsa kamar zai sha zuciya. Daga gefe, wani ya sa hannunsa yana matsa ƙirjin ta cikin ƙarfi, ita kuma tana yarfa hannaye tana tsakiya tsakanin jin daɗi da wahala. Club ɗin ya kaure da ihu: “Woooooow! 🔥🔥🔥” “She’s on fire!” “Give it to her, baby!” suna jefa mata kuɗi dollars kamar wacce ta zo yin rawa a gaban jama’a. a haka daren ya ci gaba da tafiya — sha, rawa, ihu, da abubuwan da suka fi ƙarfin ido. Ganin haka, kowa ya shiga cikin ƙarin nishadi. Wasu daga cikin masu ɗan kunya, waɗanda farko suna kallon gefe da mamaki, sai suka ɗauki farin gyale kamar labule suka lullube kewayan su amma hakan bai hana su bin yanayin sex ba. Kamar da an saka wuta a cikin ɗakin, kowanne ya fara bin sahun abin da ke faruwa. DJ kuwa, da alama ya saba irin wannan yanayi, ya canza kiɗa zuwa wani irin romantic night sexy beat da ya cika zuciya da motsi. Nan da nan hasken walƙiya ya sauya kala, ya ɗauki ja mai kauri, ya haɗa da shudi da ruwan hoda, yana ba dakin kamanni irin na finafinan waje. Shi ma ya ja budurwarsa jikin sa, suka rufe kansu a cikin hayaniya, suna chakalle cikin irin abin da suke kira da “ Sexy bebe" (Wa iyyazubillah). Abin da ke faruwa ya nuna cewa wannan wurin ba don ‘yan da suke neman nutsuwa aka gina shi ba, sai dai don masu lalata da neman sabbin hanyoyin wuce gona da iri. ********* Karfe biyar na asuba, hayaniyar club ɗin ta fara raguwa. Wani ɓangare na hall ɗin cike yake da ƙamshin turaren wuta da ƙamshin shan-shan na drinks. Fitilun da suka rage haske suna haska launin ja da ruwan hoda, suna ƙara bayyana fuskokin waɗanda suka kwana cikin gajiya da baccin maye. Yawancin ‘yan mata sun riga sun sulale suna kwance a kujeru ko kan tebura, idanu masu kumbura saboda rashin bacci da gajiya. Wasu ma sai da aka fara tada su domin su shirya fita kafin a rufe wajen karfe shida. Abdul, wanda tun daren jiya ya sha maye da rawa, ya buɗe idanu cikin kasala. A jikinsa kuwa Ramcy ce kwance, tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce aka ɗora mata kaya masu nauyi. Fuskar ta manne da ƙirjin shi, sai kamshin turarenta da gumin dare suka gauraye. A hankali ya hura mata iska a fuska, yana furta cikin kasalalliyar murya: “Baby… one more round please. Morning short sexy…” yana faɗa yana ƙara narkewa yana zagaye hannun sa akan hips nata , Ramcy ta ɗaga ido a shagwaɓe, ta turu baki kamar yarinya tana dariya ƙasa ƙasa, tana lasar gefen lebenta. Sai ta ce cikin murya mai rauni “Baby am tired… kabari sai gobe. Kowa ma ya tafi… Bachi ya rage mana. Wallahi am feeling sleepy.” Abdul ya yi dariya ya ce: “But baby… you know you’re too sweet. Even your sleep face is sexy.” ruff ya rufe bakin sa da nata , nan take suka juya har minti talatin suka ɓata suna wasa cikin nishadi, kafin su sulale daga jikin juna. Jacoub wanda ke kusa da su, yana jan tsumma yana shirin fita, ya dan tafa masa kafaɗa cikin wasa: “Hy dude, kai fa maye ne. Ya isa haka, mu fita. Remain 30 minutes club ɗin za a rufe.” Abdul ya kalle shi da murmushi mai cike da kasala, ya nuna Ramcy yana dariya: “Jacoub… baxaka gani bane? Ramcy is beautiful… so sexy. Morning sex ai ya fi night.” Dukkaninsu suka yi dariya mai ƙarfi, sai Ramcy ta yi dariyar shagwaɓa tana danna wayarta. Nan take suka fice daga wajen, kowannensu na mirza ido saboda rashin bacci da gajiya. A wajen motoci, Abdul ya riƙo hannun Ramcy yana shafa ƙasan tafin hannunta da taushi, ya ce cikin lumshe ido "By dear… see you later. Don’t forget me.” Sai ya sumbaci goshinta da ƙarfi. Ita kuma ta ce cikin shagwaɓa: “Safe trip baby.” Ya shiga motar sa kai tsaye, hanyar Asokoro . Ita kuma ta juya tana kallon bayansa har sai da motar ta bace daga gani, sannan ta shige tata motar .. Haka suka watse kowannensu ya kama hanya, zuciya cike da gajiya amma an bar musu tunanin abin da suka tsallake a daren jiya yana isowa mai gadi ya buɗe masa ƙofa yana lazumin safe lokaci kuwa ya nuna ƙarfe shida da rabi na safe. Abdul ya fito cikin tangal-tangal kamar wanda aka shanye masa kuzari, duk energy nasa ta ƙare. Ba tare da wani ɓata lokaci ba, direct ya nufi site nasa yana buɗe ƙofa kuwa sai ga Rayyan shirin tafiya makaranta. Ido hudu suka haɗa. Abdul ya ɗaga tsaki mai ƙarfi yana furta da ƙarfin rai: “Sauran Daddy ya tambaye ka ko ban kwana a gida ba ka faɗa da shegen idon ka? kutumar uwarka idan kace ban kwana ba!” Bai jira amsarsa ba ya wuce ya fāɗa kan gadon shi, ya kife jikinsa cikin gajiya. Nan take bacci ya ɗauke shi. Rayyan ya girgiza kai a hankali, zuciyarsa ta lumshe da damuwa. A cikin ransa yace: “Inna maka addu’a ɗan uwa na.” Yana fita daga ɗakin cikin uniform nasa sai ga Hajiya Zulaihah a tsaye. Ta zuba masa harara kamar wacce ke son tsinke shi da kallo. Amma saboda tana sane cewa yau Minista yana gidan, bata da ikon tsayar da shi ko hanashi tafiya a wannan lokaci. Sai kawai ta wuce gefe tana hararar shi, shi kuma ya ɗaga kai ya ƙyale ta cikin nutsuwa. No more Bad comments on this page 🔥🔥🔥🔥🔥 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 13 300 only 08101235739 "Zuwa safiya kabar garin nan shegen yaro kai kowa sai tsiyar ka ta raɓa shi sai na tsini ma ɗan asara haihuwar masifa " yana faɗa yayi waje nan Mallam Sambo ya kama Noor ƴar sace autar gidan sa tunda yaki Allah bai bashi haihuwar macce ba sai akan Noor , Allah yasa mai ƙaunar ta fiyyeda dukkan yaran sa... Duk shiru sukaye banda kuka da shesheƙan babo a binda yake tashi a gidan Mallam Sambo " ka kasance mai biyayya Bashir , ya zama wajibi ka tafe kawai domin gujewa bakin Baban ka ne kullum tsoro na kar yayi sillar mutuwar ka , kaima ka tafe kawai kasance mai Gaskiya Da tsoron Allah, Allah ya maka albarka yana nan yana ganin abubuwan dake faruwa tashi ka tafe " Nan ya miƙi tsaye banda hawaye ba'a binda yakiye da gudu Noor ta biyo sa har kofar zaure ajiyar zuciya Mallam Sambo ya sauke domin tabbass yasan rabuwar su abu ne mai matukar wahala shaquwa ce tun na yarinta. . " Don Allah kar ka tafe ka barni bazan iya rayuwa ta babo kai ba don Allah ko mu tafe tare " tana jikin sa tana wanan surutun " Noor koyar haƙuri zanyi biyayya ne kina ganin abinda ke faruwa nima banason na rabu dake don Allah ke daina kuka a kaina na miki alƙawarin zan dawo gariki ko na tafe zan dawo " nan ta zabura da murmushi a fuskar ta " gayyamin rantse da Allah zaka dawo guna" Noor nayi alƙawarin na rantse miki zan dawo gariki bazan tafe na kasa juyuwa ba kin maye min komai kin kasance min inuwa kin kasa bari na a rana zan dawo ke ma kimin Alƙawarin idan mun girma na dawo zaki aure ne "? Ehhh ehhhh nayi ma alƙawarin Allah ya kare ka , Allah ya tsare min kai kowane numfashi na bazan manta dakai ba ". na suka haɗa hannayen su biyu biyu suka juya sama da ƙasa suka taɓa kan hancin su wannan wasa ne na nishadi su nan Mallam Sambo ya fito ya kama hannun Bashir har bakin ƙauye akan jakin sa ya ƙara mai wa'azi da nasiha nan ya juya ya barshi cikin damuwa da bakin ciki Amman Allah yasa tafiyar sa tafe zaman sa a ƙauyen amfani.. .... ABUJA.. 📖 ABUJA – SCHOOL LIFE OF RAYYAN Rayyan na shiga makarantar su mai zaman kanta (Private College) cikin shirin safe, yana sanye da uniform ɗin white & sky-blue, fuskar sa ta nuna nutsuwa duk da gajiyar dare da tashin hankali a gida. Yana shiga harabar makaranta, abokan sa suka tarbe shi da murmushi: “Rayyoo! Ka makara yau,” ɗaya daga cikinsu, Salim ya faɗa da dariya. Rayyan ya dan murmusa, amma zuciyarsa tana cike da damuwa: “Da ma su san halin da nake ciki a gida…” Aji suka shiga, malamai suna ɗaukar attendance. Rayyan yana zaune a gaban class yana rubutu da nutsuwa. Shi ba mai shige-shige bane, ba mai shiga abubuwan banza, sai dai ɗan jan hankali na ilmantarwa da adalci. Cikin lecture ɗin Physics, malamin ya tambayi Rayyan tambaya mai wuya. Sai abokan class suka ɗaga kai suna jiran amsar sa. Ba tare da jin tsoro ba, ya miƙe tsaye, ya bada cikakkiyar amsa, wanda ya sa Malamin ya ce: “Excellent, Rayyan. I always admire your brilliance and discipline.” Aji ya kaɗa hannu da tafi. Sai dai a zuciyar Rayyan ya furta cikin ransa: “Allah, ka shiryar da ɗan’uwana Abdul. Ni na san ilimi da gaskiya ne hanyar rayuwa, amma shi yana cika dare a club, yana lalata rayuwarsa…” Lokacin break, abokan sa suna tattauna kan football da upcoming inter-school competition. Break time ya shiga ƙarƙashin bishiyar mango da ke bakin filin makaranta, inda yake yawan zama domin ya guji hayaniyar abokan class. Yana jan layi a littafin Physics sai ga Sumayyah ta ƙaraso da murmushi. Yarinyar kyakkyawa ce mai kunya, idanunta manya masu haske. Ta tsaya, ta ce: “Rayyan, yau ma ka zauna nan? Na gaji da zama cikin hayaniya wallahi. ya ɗan murmusa: “To shigo ki zauna mana, ai nan nake samun natsuwa ta zauna a kusa da shi, ta jawo littafinta ta bude. Shiru ya ratsa tsakanin su na ɗan lokaci, sai daga baya ta ce: “Rayyan, kai kullum kana nannade da littafi. Ba ka wasa da kowa sosai. Me yasa?” Rayyan ya ɗaga kai ya dubeta, cikin murya mai taushi ya ce: “Sumayyah, rayuwa ba wasa bace. Ina da burina — in zama likita, in taimaka wa mutane. Ina ganin duk wani lokaci da na ɓata a banza tamkar asara ne.” Sumayyah ta gyada kai: “Hmm, na gane. Ni ma ina da burin zama pharmacist, amma ina jin tsoron rashin nasara.” Ya ɗan yi dariya kadan: “Kada ki ji tsoro. Ki dogara ga Allah, ki dage da karatu. Ni ma zan taimaka miki idan akwai inda kike buƙatar taimako.” Wannan magana tasa ta yi murmushi sosai, zuciyarta ta ji sanyi. Tun daga wannan rana suka fara zama tare — a class suna kusa da juna, a break suna ƙarƙashin bishiya suna hira, a library suna tare suna karatu. Abokan su ma suka fara lura: “Wannan Rayyan da Sumayyah ba a raba su yanzu.” Rayyan ya san duk wata abota tsakanin su cike take da gaskiya da ilimi. Ba soyayya ba ce irin ta banza, amma wata dangantaka ce mai cike da tsafta wadda zata iya zama ginshiƙi a gaba Rayyan ya dawo daga makaranta da jakarsa a hannu, gumi na keto masa saboda gudun tafiya. Bai samu natsuwar shigowa ba, sai ya tarar da ihu a falon. Hajiya Zulaihah tsaye, ta tattare kuɗi a hannu tana nuna Rayyan da yatsa. “Ga shi nan! Na kama shi! Daga makaranta yake dawo da satar kuɗin gidan nan. Ai na jima da faɗa maku, wannan yaro ba zai taɓa zama nagari ba. Sai dai a sa ido, ko yau sai ya tona asirin kansa!” Mahaifinsa ya kasa magana, zuciyarsa ta yi nauyi. Ya zuba wa Rayyan ido kawai, amma ba ya iya tsayawa tsayin daka. Rayyan ya durƙusa ƙasa, hawaye na bin kumatunsa. “Wallahi Daddy… ban taɓa ɗaukar kuɗi ba! Wallahi ban sani ba…” Sai dai Zulaihah ta yi tsalle ta kafe shi da magana: “Ka yi shiru! Lallai yau sai an hura da huru mai tsanani. Na rantse ba zan sake jure maka ba. Idan ba ka ji ba, sai na tabbatar ka fuskanci hukunci!” Mahaifin ya runtse ido, yana jin tamkar duniya ta yi masa nauyi. Bai iya kare ɗansa ba, domin ta gama mallake shi cikin hannun kishiyar uwa. Rayyan ya sunkuyar da kai cikin kuka mai sauti, zuciyarsa ta fashe da tunani: “Me yasa kullum ni ake zargi? Me yasa Daddy ba ya tsaya tsayin daka a kaina? Ina mahaifiyata? Ko ni ba ni da gata?” Rayyan ya durƙusa yana kuka, jikinsa na rawa. Zuciyarsa ta cika da tsoro, amma ba zai iya cewa komai ba. Zulaihah ta zaro idanu tana tsawata masa cikin mugun murya: “Na ce yau sai ka fitar da kuɗin nan! Ko da kuwa ka haɗiye su a cikin hanjinka ne, sai an hura maka har sai sun fito! Daddy ɗinka ba zai tsira ba daga hannuna, ba kai ba kowa ba!” Nan ta ɗaga hannu ta ɗauki wayarta ta kira: “Iro! Ka shigo yanzu, ka kawo min hanyar hukunta wannan ɗan yaro mai musu.” Bai jima ba sai ga wani dogo, jabgaggen tsohon soja, baki fat da kallo mai firgitarwa ya shigo. Idonsa jajaye kamar mai shan jini. Yana shiga ya tsaya kamar dutsen tsaye. “Yallabaiya… me kike so?” Ya ce da muryar da ta fi ƙarfin karfe. Zulaihah ta ɗaga hannu tana nuna Rayyan. “Ka tafe da shi! Ka huce masa da wuta. Ka bashi huro har sai ya fitar da gaskiyar inda ya ɓoye kuɗin Daddy! Na gaji da wannan rainin hankali!” Rayyan ya zuba ido yana kallonsu, zuciyarsa na harbawa kamar za ta faso ƙirji. Yana jin numfashinsa yana rikicewa, hawaye na sauka daga idanunsa. Ya buɗe baki zai yi magana— to be continued 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t 08101235739 BUNUS PAGE 300 only *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 14 / 15 08101235739 TUNATARWA Assalamu alaikum jama'a masu bibiyar wannan littafin, Nagode sosai da kuka min uzuri na wasu kwanaki Wallahii kuna raina ,duk motse sai na tuna cewa akwai hakkin ku akaina , Nagode sosai tabbas rayuwar akwai abubuwa da zai dakatar da kai ko saka cikin wani busy da har ƙwaƙwalwa ka sai ya buga Nagode da wannan uzuri naku ,Allah ya bar zumunci... SUHAYL Kafin ya ƙarashe, sai ihu da gurnanin da ba su da tushe suka yankar da tunanin zuciyarsa zuciyarsa ta buga kamar za ta tsage, hannunsa ya tsaya cikin iska, idonsa ya yi ja kamar yana hango wani abu da bai dace ba… Ihun da ya ji bai yi kama da na mutum ba, bai kuma yi kama da na dabba ba kamar wani abu ne tsakanin ruhi da ɗan adam. Gabansa ya faɗi, amma zuciyar jarumtarsa ta matsa shi gaba. Ya ɗaga ƙafafunsa da nauyi kamar an ɗaure su da sarƙa, ya tsaya cak yana mai ƙoƙarin fahimtar daga inda sautin ya fito, iska ta buso daga bakin kogin da ke gefen tsibirin, ta kwarara tana ɗauke da wani ƙamshi mai nauyi kamar jini da ƙanshi ganye kogin ya fara motsawa da kansa, tamkar ruwa yana da rai a hankali ya ji muryar mace, mai taushi amma tana ƙara sanyi a ƙashin bayansa: "Suhayl ! Suhayl!! Suhayl!!!. Hannu ya kai kunnen sa, yana ƙoƙarin rufe wannan kiran, amma sai ihu ya sake tashi daga cikin kogin — ihu mai kama da na jaririya da ake yankar numfashi da shi. Kafin ya iya ɗaukar mataki, sai kogin ya fara jujjuyawa, yana tasowa sama tamkar rijiya da aka tayar da taƙi. Ruwa ya rinka ɗagawa da kwarara har ya zama kamar hoton fuskar yarinyar nan da ta rasu. Idanunta suka yi haske kamar taurari, tana murmushi gare shi amma cikin murmushin akwai zafi. Suhayl ya durƙusa, hawaye suka cika idonsa, zuciyarsa ta yi rauni: “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un… wannan kuwa wane irin jarabawa ne? Ruhu ko mafarki?” nan take, gurnanin ya koma ƙara mai tsanani, iska ta kwashe ƙura ta buga shi, ya fāɗi ƙasa kamar an ture shi yana kwance yana shafar ƙirjinsa, yana neman numfashi…amma kafin ya tashi, sai ya ji hannun sanyi kamar kankara ya taɓa gefen wuyansa. Gaban ruwan ya tsaya cak. Cikin wani walƙiya mai launin azurfa sai wata mata ta bayyana. Farin kaya ne jikinta, yana yalwawa kamar hazo, yana walƙiya kamar wata baiwar aljanna. Fuskarta kuwa? Kyakkyawa ce da idan mutum ya kalle ta sau ɗaya, sai zuciya ta kasa mantawa da ita har abada. Sai ta tunkaro shi a hankali, ƙafafunta basu taɓa ƙasa ba, kamar tana shawagi bisa iska. Idonta ya cika da annuri, amma a ciki akwai wani baƙin asiri da ba za a iya fasalta shi ba. “Suhayl… ɗana… ka tsaya,” ta faɗa da murya mai sanyi wacce ta huda ƙirjinsa tamkar kararrawa zuciyarsa ta tsaya, jikinsa ya yi sanyi, hannunsa na rawa ,bai san lokacin da ya durƙusa ba, yana ƙoƙarin fahimtar ko mace ce ko ruhi. Nan da nan ta miƙa hannunta, ta dafa ƙirjinsa da tafin hannunta mai sanyi kamar kankara a lokacin da ta taɓa shi, sai zuciyarsa ta yi wani irin bugu, kuma nan take ya ji zafi ya ratsa shi. Ya zaro ido, ya ga zane ya bayyana a ƙirjinsa — zane irin na hallitta, mai siffar wani tsuntsu da fuka-fuki a rufe, amma idanunsa biyu suna walƙiya da ja kamar wuta. “Inna lillahi…” ya furta cikin firgici, jikinsa na karkarwamatar ta murmusa, ta daga hannunta ta nuna gabas. Idonta ya cika da nuni, tamkar tana cewa: “can ne hanyar ka, can ne gaskiyarka, ka tunkari gabas.” Kafin ya iya magana, sai iska ta kwace farin kayan jikinta ya rufe idonsa, a cikin ɗan lokaci ta ɓace – ɓatt! – babu alamunta a tsibirin. Suhayl ya farka daga firgici, yana haki kamar wanda aka tunkuɗa daga cikin ruwa. Yana taɓa ƙirjinsa, yana jin zane ɗin da ta bari ya tsaya masa da gaske. Hawaye suka taru a idonsa, zuciyarsa ta cika da tambaya:“Wacece wannan? Uwa ce ko mala’ika? Ko kuma jarabawar tsibiri ce? Amma ta kira ni ‘ɗana’… Ni ɗan wace uwa ce a doron ƙasa?” MASARAUTAR KANO AL QAMAR GABATARWA: MASARAUTAR SULAIMANU Masarautar Sulaimanu tana a bakin ƙasa, garin Kano — babban masarauta mai madogara, gadoji masu faɗi, da zauren sarauta mai kololuwa. A zahiri ana girmama mai gidan: jaka mai daraja, masarautar ta yi suna cikin kwarjini. A zahiri kuma, talakawa na fama da haraji mai nauyi, jami’ai masu karfi suna yi wa mutane zalunci, kuma an rufe bakin masu adawa. IYALI: GIDAJEN MASARAUTAR SULAIMANU (Roster) . Emir Sulaimanu, mai karfin mulki, sarauta ta gargajiya, yana da ƙarfin son mulki. A fili yana nuna girma, amma a bayan fage yana da tsananin kishin iko da kishi. Yana dafawa neman karuwar iko ta kowanne hali; yana ƙyama ga duk wanda zai kawo ƙarƙashin sa. . Hajiya Binta (Uwargidan Emir) Kyakkyawa, mai tausayi,Rike da sirrin rayuwa:. . Crown Prince Idris, Ƙara mai takobi — son karɓar mulki da sauri. Yana da kishiya ga duk wani sabon haihuwa da zai iya rage matsayinsa makirci: Zai yi komai don hana wani gado ya ci nasara. Princess Amina, Tausayi, ilimi, abokiyar talakawa — ta fara jin rashin daidaito na masarauta. Waziri Musa (Babban Waziri Mai kutse, mai riba daga haraji, yana gudanar da ayyukan asiri Shi ne babban dafa makirci a masarauta; yana sarrafa jami’an tsaro. . Dogo Ibro (Kaptin na ‘Yan Tsaro,Jabɓa, mai bin umarni, tsanani: Aiki da Wazirin Musa; shi ke jagorantar hukunci. Maid (Ungozoma) Mai kirki, sanin sirri; ita kadai ke da ilmin haihuwa na sarauta. *********** BASHIR Fara Tafiyar Bashir Bashir ya tsaya bakin ƙauyen, iska tana kadawa a sannu kamar tana rera masa waƙar ban kwana. Ya runtse idonsa, zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, zuciyar da ke cike da tambayoyi marasa amsa. “Ina zan dosa?” ya tambayi kansa a hankali, murya na rawa kamar mai shirin fashewa da kuka. Amma babu wanda zai ba shi amsa, sai shiru da ƙarar tsuntsaye na sama. Ya dube hanya ta gaba, babu alamar gari, babu alamar mutum, sai wani ƙasa mai fadi da dogayen bishiyoyi suna karkarwa kamar masu ɓoye wani sirri. Ya yi nufin komawa baya, amma zuciyarsa ta tuna masa da kalaman Mallam Sambo: “Kai ka zama tamkar mai tafiya a sahara — ba komai ya kamata ya mayar da kai baya. Ka je, Allah yana tare da mai gaskiya.” Wani irin zafi ya mamaye zuciyarsa, amma sai ya daura hannu a ƙirjinsa ya ce da kansa: “Na amince da kaddara. Na amince da tafiya. Idan mutuwa ce, to a hanya zan riske ta, amma ba zan tsaya nan da tsoro ba.” Ya ɗora ƙafafunsa a hanya. Ƙafar farko ta ji kamar tana sauka a kan duwatsu masu zafi, ƙafar biyu ta zama kamar tana nutsewa cikin rairayi. Amma ya dage. Kowane mataki da ya ɗauka yana jin kamar yana raba kansa da tsohon rayuwarsa. Wani hadari ya fara kunno kai daga nesa, gajimare sun rufe rana, iska ta fara busa ƙarfi kamar tana gwada jarumtarsa. Sai ya ɗaga kai ya dubi sama cikin ƙarfi ya ce: “Ya Allah, idan wannan hanya ce da za ta kai ni ga alkhairi, ka bani ƙarfin zuciya. Idan kuma bala’i ne, ka bani juriya.” Sai ya cigaba da tafiya, cikin tsoro da ƙarfin hali a lokaci guda — zuciya ɗaya tana kuka, zuciya ɗaya tana addu’a. Bayan wasu kwanaki Bashir ya ci gaba da tafiya a kan hanya, zuciyarsa cike da tunani da rashin tabbaci. Rana ta yi zafi, ƙasa ta yi dumi kamar za ta ƙone ƙafafunsa, amma bai tsaya ba — ya ci gaba da tafi. Ba zato ba tsammani, a nesa sai ya hango wata mota mai sauri tana taho kamar iska. Kansa ya ɗauki hankali — amma mota ta ratsa masa a gefen hanya! Direban bai lura da shi ba; motar ta ja sanyi, ta yi ƙusoshi, ta juya sai ta buge shi da ƙarfi. Fannin ƙasa ya yi ƙasa da ƙasa: ƙarfe ya buga ƙashin ƙafarsa, jikin sa ya jujjuya kamar kayan da aka murƙushe. Sai ƙara mai ƙarfi — ƙarar ƙarfen mota, ihu na mutane, murmushi na girgiza. Bashir ya faɗi kamar mattace; numfashinsa ya yi rauni, zuciyarsa na gudu kamar za ta ƙare. Hannayensa suka yi laushi, ya ji zafin jini a fuska. Idonsa ya yi ja sai ƙaran hayaniya ya rufe duk abin da ke kusa. A ransa ya yi tunanin Noor, maganar Mallam Sambo, alkawarin da ya ɗauka — duk sun ratsa a ciki kamar ƙunci. Ya yi ƙoƙarin yin magana, amma murya ba ta fita. Motar ta tsaya a tsakiyar hanya, sai ƙarar ƙafafun maza biyu suka yi kamar mai bacci ya tashi. Sun fito daga gefe — matakan su masu hanzari, sun tsaya kusa da Bashir. Fuskar su kyakkyawa ce, kamar samari na birni, amma idanunsu sun nuna mamaki da tashin hankali. Daya daga cikinsu ya tsaya a ƙafa, ya kalli Bashir da dare-daren rai. Jinin ya yi ta zubo daga jikinsa, ya manne kafafunsa da ƙasa. Bashir kuwa — ba ya iya motsawa, idonsa na kallon sararin sama kamar wanda baya ganewa. Gaba ɗaya jikinsa ya yi sanyi kamar an kurɓaɗe masa ruwan rai. Sauran saurayi ya yi sauri ya cire riga, ya matse ƙirjinsa da lumshe ido — a hankali ya binciki bugun zuciyarsa, yana jin numfashi. Amma har yanzu Bashir ya kasa tashi, bakinsa na ƙoƙarin magana, sai sunansa ya fita ne kawai: “Noor… Mallam Sambo…” Wani daga cikin matafiya ya danna mahaɗin wayar sa, yana ƙoƙarin kira wani mai motar daka, amma a wannan hanya babu wayar hannu mai karɓa sai a duk wani latse ne. Saurayin da ke duba Bashir ya mike ya kalli saman motar, sai ya juya ya ce da sautin damuwa: “Ka dawo nan! Mu ɗauke shi mu kai shi asibitin gari — ko kuma mu samu abin ɗaukar sa!” A lokacin, fuskar daya daga cikin maza biyu ta sauya — a cikinta akwai ƙarfin halin kai da tausayi. Ya timid da cewa ba za su iya barsa a nan ba. Ya kawo hannunsa ya rufe idon Bashir da sauri, yana duba idonsa, sannan ya rufe hancinsa domin ya ji numfashin sa. Sai ya juye ya kalli abokin sa yana cewa:bl “Yaro ne daga wani ƙauye? Ko ɗan wani malami? Mu ɗauke shi cikin mota. Ni zan zauna a gaba in duba hanyar.” Sun ɗaga Bashir cikin ƙoƙari, jini na zuba a kafadarsu, sai ragargazawa ta yi mana. Bashir ya ji ruwan ƙafa yana zame masa, sai zuciyarsa ta yi wasu ƙananan bugun da suka soma dawo masa hankali. Ya ji kamar wani yana rike hannunsa — sautin ƙwallon zuciyarsa ya koma kadan; amma bai iya tsayawa ba tukuna. Ɗaya daga cikin matasan ya lanƙwasa kansa ya yi addu’a cikin ransa; ya jefa Bashir a motar da saurin gaske. Motar ta tashi, ƙaurace-ƙaurace ta bar ƙasa tana fasa ƙura. cikin mota, Bashir ya fara motsawa kankane, idonsa na buɗewa a hankali — yana ganin fuskar wanda ya aje hannunsa kusa da nasa, idon sa cike da tausayawa, yana jin muryar mai kuka cikin rassan magana: “Ka tsaya! Ka kwanta! Ka yi haƙuri! Mu ke tare da kai, ba za mu bar ka ba…” Amma zuciyar sa ta na sake raguwa; duniya ta fara ninkuwa. Kuma a lokacin da motar ta yi hanzari ta shiga cikin karkara, Bashir ya sake faɗin sunansa da ƙarfi: “Noor… Mallam Sambo… kada ku bar ni…” Sannan duhu ya rufe idonsa numfashi sa ya tsaya chakk idon sa suka kafe a sama..... Abubuwan tambaya Shin suwaye suka kaɗe Bashir da mota ? ina suka dosa ? Shin zai rayu ko zai fita cikin wannan lamari na labarin mu ? Waye SUHAYL? ina kaina tambaya nan idan na zauna shin waye shi? ya zai kuɓuta daga wannan dajin ? shin ma zai rayu yakai ga matakin ko nasara ? Gidan sarauta ya shigo cikin lamarin mu ya zata kaya? ina labarin Rayyan da Abdul ? Chakwakiya iya chakwakiya salo iya salo, tafiya ta fara tafiya wanan amsasoshin suna nan a tare da wanan littafin in Sha Allah mujeee zuwa. to be continued 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 16/17 08101235739 KANO Daren Kano ya yi nisa, fitilun masarautar suna kyalli tamkar taurari, amma a cikin ɗaki mai ɗauke da ƙanshin turaren wuta, Hajiya Binta ta naɗe jikinta da farin lulluɓi tana barci. Sai dai barcin ya koma azaba. A mafarkin da take ciki, ta ga yaro mai shekara kusan goma sha biyar hannunsa rike da makami mai zafi, yana ta ƙoƙarin shanƙo ta da shi. Idonsa jajir kamar wuta, muryarsa ta daki kunnenta “Zan dawo! zuciyar ki za ta tsage da azabar gaskiya!” tayi ƙoƙarin gudu cikin mafarki, amma ƙafafunta sun makale a cikin ƙasa mai jini. Gidan sarauta ya koma wuta, kuma daga saman wutar ta hango fuskar mace da aka taɓa sani… Hajiya Hafsah. Wacce ta kasance tsohuwar kishiyarta, wadda aka zarge ta da ɗauke ciki namiji shekaru da suka shuɗe, amma aka kashe ta da makirci don kar ta haifi ɗan gado. Fuskar Hafsah ta bayyana cikin hayaki tana dariya mai ban tsoro, ta na kallon Binta da ido biyu masu cin rai “Binta! kin yi zalunci! Kin ɗauke rayuwata, amma ba zaki iya hana zuriyata dawowa ba. Jinin jaririn da aka kashe zai dawo ne da ƙarfin sarauta!” Cikin tsananin tsoro, Hajiya Binta ta yi ihu — sai ta farke da gumi ya jika lulluɓinta. Numfashinta ya yi nauyi kamar wanda aka tsere da shi. Ta ɗaga kanta sama tana hawaye, zuciyarta cike da rawar jiki anan take, ta hango cikin ɗakinta Hajiya Maryam, wacce ta shigo da sauri da riga mai duhu. Fuskar Maryam ta sha bamban: daɗin rai da makirci suka gauraye, idanunta sun yi ƙyalli. “Lafiya, Hajiya? Kin yi ihu kamar wacce aka kunna da wuta.” Hajiya Binta ta farka daga mummunar mafarki da ta ƙona mata zuciya. Numfashinta na fita da sauri, zufa na zuba kamar an tsoma ta cikin ruwan zafi, ta kasa ɓoye firgicinta “na ga Hafsah…! na ga jinin da muka ɓoye yana dawowa! wataƙila cikin nan nata zai kawo abin da zai ruɗe mu…” Maryam ta yi dariya mai taurin zuciya, ta matsa kusa da ita tana shafo fuskarta da yatsa: “Ke dai ki daina damuwa mun riga mun mallaki sarauta. Duk wanda ya tsaya mana a gaba, sai mu sarrafa shi da dabararmu.” Hajiya Binta ta girgiza kai, hawaye na sauka: “Amma mafarkin nan ba alheri ba ne, Maryam Ina jin kamar masarautar nan za ta shiga bala’i.” Maryam ta kaɗa hannu da izza, ta miƙe tsaye: “Bala’i kuwa sai dai idan mu ne muka ƙirƙira shi, kuma mu ke tafiyar da shi. Ki kwanta ki huta, Binta. Rana ta gabbas ke fitowa ba kuɗi ba kuma yauwa ce ta gari ba ta bari kishiya ta ɗauki matsayi.” Ta fice daga ɗakin da ƙafar ta ta buga ƙasa tamkar aljana. Hajiya Binta ta ci gaba da kuka cikin zuciyarta, tana rike cikinta da hannaye biyu awaje kuwa, iska ta taso daga gefen masarauta, tsuntsaye suka tashi sama suna yi kamar ƙararrawa. Wani fari na wata ya kakkarya cikin duhu, ya haska bangon fada. Sai wata murya daga zuciyar dare ta faɗo cikin kunnenta: “Wanda aka kashe ba ya mutu… Jinin gaskiya zai taso daga ƙasa kamar Kaɗangare.” ******************* Gidan Sarautar Zazzau Alqamar 🌙👑 Masarautar da aka kafa tun ƙarni na da, tana alfahari da tambarinta na “Zanen Wutar Alqamar” – wato wata cike da walƙiya da wuta a jikinsa, wanda ke nuna cewa hasken su ba ya gushewa ko da aka rufe rana. Wannan tambari ana ƙulla shi a kirjin duk wani ɗan sarauta, musamman maza da ake kallo a matsayin garkuwa. A wannan masarauta aka haifi Prince Idris, wanda aka fi kira Idrisul Kawthar, mai ɗimbin kwarjini a idon jama’a. Shi kaɗai ne ɗa namiji da ya rage a gidan sarautar bayan shekaru na asara da makircin mata da kishiyoyi. A idanun duniya, shi ne madubin masarauta. Wannan tunanin ya fi mata duka wani bala’i. Cikin firgici ta kira mai gadin ɗaki: "Ku kira min Idris! Prince Idris yanzu-yanzu ya zo wurina!" cewar Hajiya Binta . Shigowar Prince Idris Sai ga shi ya shigo da ƙamshi da ƙarsashi. Dogo, kyakkyawa, farin kaya ya lullube shi, tambarin Wutar Alqamar na kyalli a ƙirjinsa. Ya kalli mahaifiyarsa cikin damuwa: "Ummah, me ya same ki haka? kin kira ni cikin tashin hankali…" Hajiya Binta ta yi shiru tana huci, daga bisani ta ce da rawar murya: "Idris, al’amura sun fara dawowa garemu. Na hango Hafsah, wacce muka binne tare da asirinmu. Tana dawowa cikin mafarkina, tana riƙe da ɗa namiji! Wannan alama ce cewa zaluncin baya zai dawo ya tarwatsa masarautar mu… Idris! Kai kaɗai ne hasken da ya rage a wannan gida. Kada ka bari wuta ta cinye mu." ✦ Idris ya yi dariya mai ƙanƙanar sanyi, fuskar sa ta kwantar da murya kamar wanda yă san ransa babu matuƙar damuwa. Ya ɗaga hannu ya gyara rawanin ajalin da ke ƙirjinsa — tambarin Wutar Alqamar ya walƙace ƙasa da rana. “Mom,” ya ce cikin sassanyar muryar da ba ta da tausayi, “mafarki ƙarya ne, mafarki ya kan rarrashi zuciya. Kina ƙoƙarin hana mini natsuwa. Ki kwantar da hankalinki — ba za mu sake barin waɗansu su kawo mana matsala ba. Ki faɗa mini, wacece Hafsah game da mu? Ashe kin yi bacci da tunanin haɗari ne?” Ya matsa gabansa ya yi murmushi mai ɗaci. “Ki tuna dai, yayin da muke zaune cikin ƙarfi, mun shirya komai.” Ya sauke murya zuwa ƙasa kamar maganar asiri. “Mun kai ta kogi a dajin nan, an harbe ta sau biyu — ban manta ba. Mun buɗe ƙofa ga barazanar gado, amma mun rufe ta da ƙarfi. Ba wanda zai iya tayar da ita yanzu.” Hajiya Binta ta fasa numfashi, kyallin mafarkin ya riƙe mata tunani. Idanunta sun cika da damuwa, amma da fargaba ta gaɗa baki ta yi ƙoƙarin ƙara haske a murya. “Idris… Allah ya sa mu yi gaskiya. Wannan mafarki… ya na nuna mana wani abu — kamar faɗakarwa. Ka ji muryar ta ce ‘jinin da aka kashe zai dawo’… Me idan akwai gaskiya a cikin wannan mafarki?” Idris ya matso kai ya kusance ta da sauri, idonsa sun yi ƙyalli. “Mom, ki ɗauki hankali. Ba mu da lokaci na hira da jarabar mafarki. Mun riga mun yi abin da ya dace. Duniya za ta zauna, kuma mu za mu ci gaba. Ki rufe bakinki ki huta — zan tsara komai.” Sai ya juya ya nufi ƙofar zaure, ƙafar sa ta doke ƙasa da sautin hukunci. Amma kafin ya fita, ya juya ya ƙara faɗa: “Ki sani, idan har wani yaro zai fito daga cikin ikilisiyar da kuka ɓoye, to zan yi masa abinda ya dace domin kare madafun iko na. Wannan gida ba fili bane na tausayi.” Hajiya Binta ta zauna gaba ɗaya cikin tsananin firgici, zuciyarta na bhaƙa. A waje, iska ta yi ƙarfi, tsuntsaye sun yi kauri, kuma wani ƙaho mai nisa ya bushe kamar sanarwar wani abu mai zuwa. — Zarah, ungozoma — na tsaye a bakin ƙofa, idonta na rikitattu. Ta kalle su da idanun da suka san sirri da yawa, sai ta motsa jikinta ta yi shiru. A zuciyarta ta san cewa mafarkin Hajiya Binta ba zai zama abin banza ba — akwai wata ƙasa ta gaskiya da za ta so ta rufe. Kai a kai labarin ya tsaya, murya na ƙasa ta faɗi cikin duhu: “Wutar Alqamar ba ta faɗi fage da sauƙi. Wani abu mai tsarki zai fito daga cikin ruwan da kuka ɓoye…” ********* SUHAYL – Kaɗangaren Tsibiri Bayan wani lokaci mai tsawo da Suhayl ya ɗauka yana tafiya ta gabashi ba tare da guzuri ko tsoro ba ya kwana a daji yaci ganye yayi sutura da ganye da ya samu, a chan ƙifin hanyar bishiyoyi da ya dosa nan ya fara jin hayaniya ta mutane da dabbobi da bai saba jin su ba , cikin hanzarin ya ƙara kaimi burin sa bai wuce samun abinci ba , yana isowa bai ankara ba yana ganin wasu halittu na mutane da sutura ta jikin su.. Da zarar ƙauyen suka taru a kansa, idanunsu suka fara yawo a jikin Suhayl. Ba rigar mutane yake sanye da ita ba, sai sunaye da ganyaye da ya zagaye jikinsa, tamkar wani ɗan tsibirin almara. Nan da nan yara suka fara tsokana da ihu: “Wayyo, ga ɗan tsibiri! Ga mai ganye , "Sauran manya kuma suka tsaya suna yi masa sambatu, wasu dariya, wasu kuma tamkar suna jin tsoro. Suhayl kuwa sai zuciyarsa ta buga da ƙarfi, tsoro ya kama shi, jikinsa ya fara rawa. Wannan shi ne karo na farko da ya hango irin wannan taro na mutane, kuma bai san ko da gaske su ’yan adam ne ba. Amma kafin ya iya cewa komai, gawata kyakkyawar yarinya ta bayyana daga gefe. Fuskar ta cike da walwala, kyawunta ya tsaya tamkar hasken alfijir. Ta yi dariya mai taushi, ta rufe shi da mayafin da ke jikinta don ya daina jin kunya. Yaran suka yi shiru suna kallon ikon Allah. Ita kuma cikin nutsuwa ta ce: “Suna na NOOR… kai fa?” What the F****k Mujeeee zuwa ***** BASHIR Motar na gudu kamar za ta tashi sama, ƙurar hanya ta mamaye musu baya. Sagir ya riƙe hannun Bashir da jini ke fita ba ƙaƙautawa, yana toshe gurin da ya fi zubarwa da riga. Muhsin kuwa ya riƙe sitiyari da duk ƙarfin zuciyarsa, yana tsalle da hanzari a kan ramuka da gangaren hanya. “Ka tsare shi kada ya mutu min, Sagir! Kada ka bari ya mutu kafin mu kai Kaduna!” Muhsin ya huro, idonsa na zubar da hawaye amma yana ƙoƙarin boyewa. “Wallahi jinin nan ya fi ƙarfin rigata! Ya zuba sosai!” Sagir ya yi ihu, yana tura riga a wurin raunin. Idonsa ya koma ja, zuciyarsa na bugawa kamar ana dukan ganga. Motar ta nufi Kaduna cikin saurin da babu tunani, ƙarar horn na ta fasa iska. Har suka shiga cikin birnin Kaduna, mutane suna kallonsu cikin mamaki. Da suka ƙaraso bakin wani asibiti mai taken “Garkuwa Specialist Hospital Kaduna”, Muhsin ya yi tsayawar gaggawa har tayoyi suka yi ƙara. Nan take ya fito da gudu tare da Sagir suka ɗaga Bashir da aka kusa tsinke masa rai. “Help! Help! Doctor! Yana mutuwa ne! Please ku taimaka min!” Muhsin ya fasa ihu da harshen Turanci da Hausa a haɗe. Cikin hanzari ma’aikatan asibiti suka fito da gadon turawa. Suka kwashe Bashir, jini na riga musu hannaye da kaya. Nurse ɗaya ta danna wayar gaggawa tana kira “Emergency theatre! Prepare for surgery! yaron nan zai mutu idan aka bari haka!” Sai suka zuba gudu da shi zuwa ɗakin tiyata. Likitoci biyu suka shigo da sauri cikin farin kaya, ɗaya daga cikinsu ya yi magana da ƙarfi: “Ku cire masa kaya nan take! Ku danna drip ɗin gaggawa, ku kawo oxygen!” Sagir ya tsaya a bakin ƙofa, zuciyarsa na tsalle-tsalle, jikinsa na rawa. Muhsin ya rungume kansa da hannu biyu yana maimaita: “Ya Allah, ka tsare shi… kada ya mutu a hannuna… Allah ka ba shi rai…” Cikin mintuna aka fara ƙarar kayan tiyata — scissors, scalpel, clamps — an rufe ƙofar operation room. Nurse ɗin ta tsaya a bakin ƙofa ta ce musu: “Ku jira a waje. Ko da nawa ne, sai an yi masa treatment. Amma ku sani… rayuwarsa tana hannun Allah yanzu.” Sagir ya ji jikinsa ya saki, ya durƙusa ƙasa da hawaye. Muhsin kuwa ya jingina da bango yana kallon ƙofar da aka rufe, zuciyarsa cike da tashin hankali. Sai suka fara kiran sunan Allah a bakunan su duka biyu, saboda rayuwar Bashir yanzu ta rataya a tsakanin numfashi guda da mutuwa. Labari na tafiya Something big is ........ g Narnah ƙanwar soja ✍️ ✍️ ✍️ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 18 / 19 08101235739 Bishiyar Ƙauyen Rimi Suhayl ya zauna a ƙasan bishiyar, idonsa na kallon ƙasan ƙasa tamkar yana jin tsoron kallon fuskarta. Amma sautin muryarta ya tsinke shi tamkar iska mai sanyi da ta ratsa zuciya. “Noor… sunan ki Noor? Kin ce a nan aka haife ki, Mallam Sambo shine mahaifinki, Allah ya mai rahma…” sai ta kalle shi a hankali, tana ɗan murmushi da ƙarfin hali: “Eh, haka ne. Amma kai fa? waye kai da baka da kamanni irin namu? kamar baka saba ganin bil’adama ba me sunanka?” Shiru ya biyo baya. Kukan tsuntsaye ne kawai ke cika sararin bishiyar. Suhayl ya ɗaga kai a hankali, idanunsa manya suna ɗauke da wani irin sirri. “Ni… suna na Suhayl ban taɓa sanin gida ba, ban san uban da ya haife ni ba, ban san uwa ba. na taso ne a cikin daji, da namun daji, da ruwa. Tsohuwa ce ta rene ni, ita ce ta rasu ta barni da wannan zoben…” Ya zaro zoben daga hannun sa ya nuna mata yana rawar hannu. “Ta ce idan nabi zoben zai kai ne ga makomata.” Noor ta kalle shi da mamaki, zuciyarta ta buga. Kamar ba a duniya yake ba. Ta sauke ajiyar zuciya tana ɗan girgiza kai. “Subhanallah… toh, Suhayl, wannan ƙauye ne. A nan mutane suke rayuwa, wasu da wahala, wasu da farin ciki. Idan ka yarda, zan nuna maka hanyar gida. Amma ina tsoron yayana idan ya dawo daga gona, saboda shi ba ya son baƙi.” Suhayl ya runtse idanu, yana jin muryarta kamar wacce ta kira shi tun shekaru masu yawa. Ya ɗaga kai ya ce a hankali: “Noor… zan iya zama kusa dake? Ko da a ƙarƙashin bishiyar nan kawai…” - Suhail da Noor suka ci gaba da tafiya a cikin hanyar ƙauyen, cike da nutsuwa. Hira suke yi tana ta ba shi labarin soyayyarta da Bashir, irin alƙawarin da suka sha yi lokacin ƙuruciyarsu. Muryarta ta yi rauni, tana haɗa dariya da hawaye. Sai Suhail ya kalleta cikin mamaki ya ce: “Mene ne soyayya, Noor? na ji ki kina ta maganarta kamar wani abu ne mai ƙarfi.” Noor ta tsaya cak, ta dubeshi da ido cikin rashin tsoro, ta fashe da dariya tana girgiza kanta. “Kai fa ba ka san komai ba! ashe ba ka taɓa ji ba? Soyayya ita ce abin da ke sa mutum ya yi dariya da hawaye lokaci guda, itacce mai sa kamanta da mugun hali ,ko wulakanci tsakanin ka da abin sonka , ittace garkuwa zuciya mai sanya tsinkewar zuciya a bazara da da damina da rani , ittace Allah ya fasa a zuciyoyyin mutum biyu , ita soyayya gaskiya ce mai yinta baya mantatta ko daɗin ta ko azabar ta , Ita ce abin da ya haɗa ni da Bashir har yanzu, ko da ya barni, har yanzu ina jin shi a zuciyata. Amma kai sai ka ce jaririn da bai taɓa dandana rayuwa ba.” Suhail ya yi murmushi ya ɗan sunkuyar da kansa ya ce: “To idan haka ne, za ki koya min? ko kuwa sai dai ki ci gaba da dariya?”Noor ta sake dariya, ta share hawayen da ke gefen idanunta. “Kai kaɗai ne ka san yadda zaka koya wa kanka. Ni fa yanzu kawai bari mu tafi gida, Yaya ya hana ni yin yawo nesa da gida.” Ta juya cikin ɗan tsoro da fargaba, zuciyarta tana harbawa saboda ta manta kanta har ta tsaya da shi a ƙarƙashin bishiyar da suke zama. Suhail ya yi mata rakiya yana jin daɗin yadda hirar ta ɗebe masa kewa, shi ma yana jin kamar ya shiga wani sabon yanayi da bai saba da shi ba. Sannu a hankali suka nufi gidan Noor, tana ɗan dubansa lokaci zuwa lokaci da mamakin wannan sabon bawan Allah da ya shiga rayuwarta a ba zata. Suka iso harabar gidan Noor, da sallama ta shigar da shi. Amma kafin su zauna, yayan Noor ya fito daga cikin gida, ya tsaya yana kallon Suhail da mugun ido. “Noor, wa ya kawo wannan ɗan dajin nan gida? Ba zan lamunci zaman sa a cikin gidana ba.”Noor ta yi shiru, zuciyarta na bugawa da sauri. Ta kalli Suhail, sai ta dubi yayanta cikin tausasawa ta ce: “Yaya, don Allah ka sassauta. Ni ne na kawo shi saboda tausayi. Ka duba fa, mutum ne mai kamanni, bai cancanci a ce a kore shi kamar dabba ba.”Yayan ya girgiza kai, ya ce: “Kin ga irin kamanninsa? gashi da ba a aske ba, mutane ma suna gudunsa. Kina so ace an haɗa ki da irin wannan?” Noor ta yi murmushi mai cike da tausayawa, ta nuna masa gashin jikinsa mai yawa: “Wallahi Yaya, gashin jikinsa kaɗai ya isa mutane su yi tunanin ko mahaukaci ne ya fito. Amma idan aka kula da shi, aka tsaftace shi, za ka ga asalin kyakkyawan saurayin da ke cikinsa.”Sannan ta dubi Suhail da idanu masu nuna tausayawa: “Ka bari nan gaba kadan zan samo maka abin aski. Lokacin nan sai na cire maka wannan gashi, ka ga yadda mutane ba za su ƙara gudunka ba.” Daga nan, ta juya cikin sauri, ta shige gida, zuciyarta na tsalle-tsalle da mamaki da kuma wani irin nauyin tausayi da ta ɗauka akansa. Suhail kuwa ya tsaya a bakin ƙofar gida, ya rasa ko ya shiga ya tsaya ko ya koma, amma abin da ya tabbata shi ne kalmomin Noor sun ratsa zuciyarsa fiye da yadda ya taɓa zato. Bayan kwana biyu, labari ya bazu kamar wutar daji a cikin ƙauyen Rimi. Kowa ya san cewa wani ɗan daji mai suna Suhayl ya bayyana, kuma ana ta danganta shi da kyakkyawar yarinya Noor.Matan gari suka fara gulma: “Ai ku ji abinda ke faruwa! Noor ta samu sabon saurayi, shi ya sa take taƙi amincewa da kowa a ƙauyen nan. Tana cewa wai tana jiran Bashir, ashe ƙarya ne.”Wani dattijo ya ce da raini: “Haba! To ba don ta haɗu da wannan ɗan dajin mai kama da mutum ba ne sai yanzu take dariyar aure? Ashe alkawarin ta da Bashir babu gaskiya.” Wasu kuma suka ɗora da munafurci: “Kunga kuwa? Ai idan aka ce mace ta yi nisa da soyayya sai ta manta alkawarin da ta yi. To Noor ta manta Bashir saboda wannan sabon saurayi kyakkyawa kamar shi.” A haka gulma da magana suka fara yawa, har ta kai ga iyayen Noor ma suna jin zafin maganganun mutane. Noor kuwa tana zaune a cikin ɗaki, zuciyarta cike da rikici. A gefe guda tana tuna Bashir da alkawuran su, a gefe guda kuma tana jin wani abu mai zurfi game da Suhayl wanda ta kasa fassara shi. Sai dai duk da wannan, zuciyarta ta nace: ba soyayya take yi da Suhayl ba, tausayinsa kawai ne ya motsa zuciyarta. Amma al’ummar ƙauye suka riga da sun yi masa fassara daban. ****************************************** BASHIR Ƙofar operation room ta rufe, kowa ya baro su Sagir da Muhsin a bakin ƙofa suna jijjiga da fargaba. Sai ga wani ma’aikacin asibiti mai sanye da farin labcoat ya fito da takarda a hannu, fuskarsa a daure tamkar wanda ya zo da hukunci. “Ku ne danginsa?” ya tambaya cikin gaggawa. Sagir ya jinjina kai da sauri, jikinsa na rawa. Muhsin ya yi saurin tashi daga jingina da bango: “Eh, mu ne, Doctor! Me ya faru?” Likitan ya ɗaga takardar da yake riƙe da ita. “Lamarin yaron nan gaggawa ne. An buƙaci a cire glass daga jikinsa nan take. Amma kafin mu ci gaba, dole ne ku biya kuɗin aikin tiyata. Farashi ya kai (dubu dari uku)ku kawo kafin mu ci gaba, ko ba haka ba…” Kalmomin sun tsaya muryar doctor kafin ya ƙarasa. Amma Muhsin da Sagir duk suka saki baki cike da firgici. “₦300,000!?” Sagir ya maimaita, idonsa ya zazzare, “yanzu-yanzu! amman zai iya warkewa ?”likitan ya gyada kai, ba tare da tausayi a fuskarsa ba: “Rayuwar sa ce a hannun mu. Da kuɗi ne za a iya ci gaba. Ku yanke shawara yanzu.” Numfashin Sagir ya daskare. Ya juya da sauri ya nufi mota kamar wanda aka tsikara da wuta. Yana shiga, ya fara dudduba kujera da tire da dashboard, yana kwaso duk wata kudi da suka rage musu a tafiya. Babu lissafi, babu kirgawa – zare, folo, daloli da naira duk ya hado cikin envelope ya zuba musu. Da gudu ya dawo ya miƙa wa likitan envelope ɗin, zuciyarsa na tsalle. “Ga kuɗi nan, babu matsala! Da shi za a ceto shi, mu ba matsalar kuɗi bane. Rayuwarsa ita ce muhimmanci!” Likitan ya buɗe envelope ɗin, ya hango tsabar kuɗi da papers da yawa har ya kasa kirgawa nan take. Ya kalli Sagir da Muhsin, ya ga idanuwan su cike da hawaye, zuciyarsu a hargitse. “Shikenan.” ya furta a hankali, ya juya da kuɗin. “Ku zauna. Mu zamu yi bakin ƙoƙarin mu. Sai dai ku taya shi da addu’a.”ana nan, ƙarar kayan tiyata ta sake cika ɗaki daga ciki – ana goge jini, ana kira: “Scalpel! Clamp! Oxygen! Hurry up!” Sagir ya durƙusa a ƙasa, ya sa hannayensa a kai. Muhsin kuwa ya rungume bango, idonsa ya lumshe yana hawaye. Dukansu zuciyarsu ta daure a kalma ɗaya: “Ya Allah, rayuwar Bashir ce yanzu tana hannunka…” 😭😭😭😭 To be continued ** Wai sadiqa kina son Bashir nan Amman har yanzu banga cin hanci bafa to 🙄*** 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️ PAGE 20 / 21 08101235739 Sun buɗe ƙofar operation theatre da sauri, da ƙarar takalma da kayan tiyata suka mamaye su. Cikin ɗakin, fitilu masu ƙarfi sun haska fuskokin likitoci biyu Dr. Aisha (surgeon) da Dr. Bala (anesthetist) — suna shirin tunkarar abin da zai iya zama darasi tsakanin rai da mutuwa. Nurse ta zauna ta danna machine ɗin vitals: ƙarfin bugun zuciya, oxygen saturation, da jinin jiki. “BP ɗinsa yana ƙasa. SpO2 baya ƙaruwa. Ana buƙatar blood transfusion nan take!” ta faɗa da hanzari. Dr. Bala ya yi saurin saka catheter, ya fara infusing fluids, yana magana cikin nutsuwa: “Mu daure. Ina son oxygen 100%, intubate shi yanzu. Aisha, ka shirya incision — muna fitar da harsashi, clamp vessel idan akwai bleed.” Sagir da Muhsin sun tsaya a bakin ƙofa, idanuwansu cike da tsoro. Sagir ya rike hannu, ya maimaita sunan Allah da ƙarfi; Muhsin kuwa ya fara kuka a hankali kamar yaron da aka bar shi cikin duhu. Sun iya jin sautin kayan tiyata — scalpel, suction, clamps — duk suna ta aiki. Dr. Aisha ta fara aikin: ta buɗe yankin da aka buge masa, jini ya taru kamar tafki. Hannunta cikakke ne, amma saurin aikinta ƙwarai yake. Ta ce: “Clamp! Suction! Send me the forceps!” Wani ɓangaren nama ya yi ripping; suna duba vessels da jini ke zuba. Dr. Bala ya kira: “Transfusion incoming — 1 unit PRBC’s! Arrange crossmatch yadda suka ce!” Nurse ɗaya ta kawo jaka cike da jini, an haɗa shi cikin drip. A hankali bugun zuciyar Bashir ya fara ɗan ƙaruwa, amma har yanzu pressure ɗin ba ya dawowa yadda ya kamata. Dr. Aisha ta matsa gaba, ta yi searching cikin cavity — sai ta ga wani ƙaramin fragment na harsashi ya makale a ƙashi. Da ƙwarewa ta cire shi, ta yi cauterize a inda take zubar jini fiye da kima. Lokaci ya yi kamar lokaci ya tsaya. Kowane muryar likita, kowane danna da ake yi, kowane clamp da aka rufe yana da nauyi a zukatan waɗanda ke jiran a bakin ƙofa. A wajen, Sagir ya rike hannu yana rawar jiki; Muhsin ya rufe fuskarsa cikin hawayen da ba su da ƙarfi. Bayan mintuna masu tsanani, Dr. Aisha ta tabbatar: “Bleeding controlled glass removed. We’ve packed and closed. Send him to ICU. He’s stable for now, but critical.” Aikin ya ƙare — an sutura, an sa dressing, an cire anesthesia a hankali. Dr. Bala ya ce da tausayawa: “Mun yi iya kokarinmu. Amma ya yi losing a lot of blood. Za mu sa shi a ICU, ventilation zai taimaka. Ku shirya don yi masa transfusion na gaba idan ya buƙata.” Sagir ya zame kafadarsa ya durƙusa, hawaye sun zubo kamar ruwaye Nurse ta fito ta yi magana ga su da murya mai ladabi: “Ku shiga ICU ɗin bayan an shirya. An yi masa stabilization amma yanzu abu ne da lokaci zai nuna. Ku shirya don za a iya buƙatar ƙarin blood, antibiotics, da monitoring na tsanani.” An ɗauke Bashir zuwa ICU, an haɗa shi da machine ɗin ventilation, da drip ɗin blood, da monitoring. Idansa sun rufe; fuskarshi ta yi sanyi amma numfashin artificial yana tafiyar da shi. A wajen gadon ICU, Dr. Aisha ta tsaya gabansu, ta kalli Sagir da Muhsin cikin mugun rauni amma ƙwarin gwiwa: “Mun yi iya bakin ƙoƙarinmu. Rayuwarsa yanzu ta fita daga barazana amma akwai haɗari. Ku yi addu’a, ku san cewa akwai abubuwa da yawa da za mu bi. Za mu sanar da ku duk wani ci gaba.” Sagir ya rungume kansa, ya yi kuka mai ƙarfi, sannan ya miƙe ya ce cikin rawar murya: “Na gode… Na gode sosai. Kai ne ya ceci shi.” Muhsin ya zauna a ƙasa, ya rufe kansa da hanu, zuciyarsa cike da godiya da fargaba. A can nesa, ƙarar motoci da hayaniyar birni sun dawo, amma a nan cikin ICU akwai shiru mai nauyi — shiru wanda ke cike da fatan rayuwa. ABUJA PAGE 14 Rayyan ya tsaya a gaban dutsen ido. Numfashinsa ya ƙara sauri, kamar wanda ya yi tsalle daga barci mai nauyi; zuciyarsa na buga kamar murya mai ƙara. Idanunsa sun yi jaƙeƙe, hawaye sun yi ƙasa amma ba su yarda su zube ba—kamar an ƙulle su da ƙaƙƙarfan alkawari. Kafin Iro ya miƙe hannu yaji muryar ta faɗi masa kamar shawagi: “Ka zauna da gaskiya, ka dogara ga Allah.” Zuciyarsa ta yi rauni; ko da yake ya san gaskiyar zuciyarsa, fargaba ta mamaye sa tamkar guguwa wadda ba ta da iyaka. Zulaihah na tsaye gefen falon, idon ta cike da farin ciki mai launin mugunta — kamar wanda ya mika nama ga zaki. Ta ɗaga hannanta ta miƙa wayar, ta kalle shi da wariya: “Ka ga? Na san za a same ka da laifi. Ka ga yadda kake bayyana yanzu? Sai a ce kai ne…” Muryar ta cike da ƙarfi, tana jin kamar ita ce mai adalci a cikin wannan gidan. Iro ya matso kusa. Kafadarsa faɗi, hannayensa sun yi ƙarfi kamar na mutumin da ya gama koyi da azabtarwa. Yana ɗauke da sanda a hannu, kallo nasa mai tsanani ya bushe zuciya. A kusa da shi akwai wani ƙamshi — mai tura hawaye, turaren fuka da ƙarfin jiki na tsohon soja wanda ya gama shekara yana yaki da mutane da kansa. Rayyan ya yi ƙoƙarin tsayar da magana, amma bakinsa ya bushe. “Wallahi…,” ya fara, amma muryarsa ta yi ƙasa ta toshe. Anan ne tsoro ya fara yaduwa masa kamar ruwa a jikin ɗan adam Jikinsa ya fara rawaya, hannayensa sun yi sanyi, ƙafafun sa sun dinga rawa a ƙasa. Shi kansa ya riga ya san cewa idan Iro ya soma, babu wanda zai tsaya tsayin daka a tsakanin su; mahaifinsa ya rufe baki, ya kalle shi da bakin ciki wanda ya fi ƙarfin magana. Wannan kallon mahaifi ya sa zuciyarsa ta ƙara tsanani—ɗaɗin fatan cewa mahaifinsa zai kare shi ya ɓace cikin ƙunci. Rayyan ya fara yin addu’a cikin ransa, muryarsa ta ratsa cikin sirri: “Ya Allah, kada ka bar ni. Ka shiryar da ni kar ka bar ni cikin zalunci.” Kalaman sun zo musu kamar ƙaramar magani, amma ba su tsinke tsananin fargabar da ke cikin zuciyarsa ba. A wancan lokaci, Iro ya ɗaga hannu—ba don ya fasa magana ba, amma don ya nuna iko. Yana kallon Rayyan kamar wanda yake kallon abu mara rai da zai iya canza masa rayuwa da ɗan bugun sanda kawai. Duk wannan lokacin, Rayyan yana jin sautin zuciyarsa ya bugu fiye da yadda ya saba — har ya yi tunani cewa za a iya jujjuya mazajensa a fili. Ya tafo hannun sa a aljihun riga, ya tura yatsunsa cikin kunnensa ya rufe su a ƙanƙantar murya, sannan ya yi ƙasa-ƙasa: “Ya Allah, ka bani ƙarfi.” Kafin Iro ya fara magana, wani isasshen shiru ya fadi a falon; kowa ya tsaya a tsaye. Rayyan ya ji kamar lokacin ya tsaya cak. Idanun Iro sun ƙara hayaniya, yatsunsa sun matso kusa da sanda. Zulaihah ta yi murmushi mai gamsuwa kamar wanda ya sha ruwan nasara. Rayyan ya san cewa abinsa zai zo yanzu—amma zuciyarsa, duk da tsoro, ta fara samun ƙarancin tsayayye: akwai ƙaramar murya a zuciyarsa wadda ta ce kada ta yi kasa a gwiwa; cewa gaskiya ta fi duk wata azaba. Wannan ƙaramin murya ya ƙara masa ƙarfin hali kadan, ko da yake jikinsa ya baci da tsoro. A nan labarin ya tsaya — Iro ya ɗaga hannu a hankali, kallo nasa ya cika annoba. Rayyan ya shirya fuskantar abin da zai zo, zuciyarsa cike da tsoro amma a lokaci guda cike da ƙoƙarin jurewa. ******* A ɗaki mai duhu, daurin da aka yi masa ya matse ƙafafunsa har jikinsa ya kasa motsawa. Zafin ɗakin ya tsaya a jikinsa kamar wuta, numfashinsa na ƙaruwa yana rawa. Iro ya tsaya tsayin daka, sandarsa a hannu, yana fitar da numfashi mai ƙarfi tamkar dodon da aka aiko domin halaka. “Ina kudin nan?!” muryarsa ta cika ɗakin, tana daɗa tsinkewa a kunne. Rayyan ya runtse ido, hawaye suka fara silalowa daga kuncinsa. Muryarsa na rawa, sai ya ce da ƙarfin zuciya: “Wallahi ban ɗauki kuɗi ba… ba ni ne ba.” Iro ya yi ƙara da dariyar tsoro, ya ɗaga sandarsa ya sauke. Ƙarar bugun ta tsinke shiru, Rayyan ya kifa da ƙarfi, zuciyarsa ta dinga tsalle tamkar zata fito daga ƙirji. Duk da zafin, bai sake ba da amsa ta ƙarya ba. “Ka fiye yi min gardama? Sai na karya maka zuciya kafin dare ya sauka!” Iro ya daka masa tsawa, yana jawo shi gefe ya tura shi cikin dakin da babu tagar haske, babu iska, babu abin gani. An rufe ƙofar da ƙarfi, aka jefa shi cikin duhu da zafi mai ɗaci. Cikin ɗakin, babu abin da idonsa zai iya gani, sai duhun da ya mamaye komai. Hannayensa daure, jikinsa a zube a ƙasa. Numfashinsa ya yi nauyi, amma zuciyarsa ta ci gaba da bugawa. Ya jingina da bango, muryarsa ta yi ƙasa kamar raɗa: “Ya Allah, kai ka sani ban yi sata ba… kai ka sani ban taɓa cutar da kowa ba. Ka tsare ni, ka kare ni.” Wani hawaye ya sake gangaro masa, amma zuciyarsa ta ƙi fasa. Tsoro ya lullube shi, amma dogaro ga Allah ya ɗan ba shi ƙarfin guiwa Cikin tsananin duhun, sai kawai ya ji ƙarar ƙofar a waje. Wata murya ta fito da sanyi, tana kiran suna: “Rayyan… Rayyan!” Ya dago da sauri, zuciyarsa na dukan uku-uku. Shin mafarki yake yi ne? Ko kuwa cetonsa ya kusa? ABDUL Kira ɗaya Abdul yayi wa abokansa cikin dare, muryarsa cike da annashuwa da shirin tashin hankali. “Ina faɗa muku yau akwai dabkee, akwai chasu, akwai ‘yan mata a club. Ku shirya mu tare dare ya ɗauke mu.” Da misalin ƙarfe sha biyu na dare, club ɗin ya cika kamar kasuwa ranar Juma’a. Waka ta gauraya da ihu, hayaniya ta cika wajen. Fitilu masu kalar ja da shuɗi suna walƙiya a bango kamar wutar shaidanu. Samari sun sha kaya sun kawata, wasu sanye da farin kaya masu kyalli, wasu da dogayen wando da riga masu tazara. Ƴan matan kuwa sun cika wajen da kamshi, gashinsu a zube, wasu cikin dogayen siket masu kyan walƙiya, wasu cikin ƙananan kaya masu bayyana dukkan sura. Dariya, shewa da ihu suka gauraye da karar DJ da ke juyar da kiɗa. Abdul ya shigo cikin takama, hannunsa riƙe da kwalbar giya, fuskar nan cike da alfahari kamar sarkin club. Abokansa suka tarbe shi da ihu da tafi, suka hau tsalle suna kiran sunansa. Ya kalli wajen, idonsa ya tsaya kan wata kyakkyawar yarinya mai ruwan fata. Murmushi ya subuce masa, zuciyarsa ta ce “Wannan ce ta dace da wannan dare.” Ya ɗaga kwalbar giya sama yana ihu: “Yau dare ne na Abdul! Mu more kafin gobe ta iso!” Wajen ya kara ɓatsarwa da hayaniya, to be careful continued........ 🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎 BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM 08101235739 BUNUS PAGE 300 only *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** PAGE 22/ 23 TUNATAR WA ( HAPPY FRIDAY ) BUNUS PAGE Ka zama mutumin kirki a rayuwa, kada ka bari tun daga ƙuruciyarka ayi maka mummunar shaida, kada ka yarda shaiɗan yayi galaba a ƙuruciyarka har yasa abin yayi tasiri izuwa har tsufanka. Lallai ka zama mai dattako a rayuwa, lallai ne alamun kyakkyawan tsufa ko akasin hakan yana da alaƙa ne da shekarun ƙuruciyarka" - "Ka daure ka tafiyar da ƙuruciyarka cikin inganci har izuwa tsufanka, kada ka yafiyar da ita cikin halin da za kazo kayi nadama daga ƙarshe" ******* RAMCY Cikin ƙawatuwa ta musamman Ramcy ta iso club ɗin, wandon leda mai matse jikinta ya bayyana dukkan surarta, gashinta ya zubo kan kafada yana walƙiya da hasken fitilu. Idanunta suka sauka kan Abdul, wanda ya jingina da kujera, hannunsa riƙe da kwalbar giya, yayin da wata sabuwar yarinya mai ruwan fata ke zaune kusa da shi tana dariya. Zuciyar Ramcy ta buga kamar ta fito daga ƙirji. Hankalinta ya tashi, zuciyarta ta cika da ɓacin rai da haushin ganin Abdul da wata. Da gudu ta nufi inda suke, bata tsaya da tunani ba ta hankada kujerar da yarinyar ke zaune tana duban Abdul. “Ke Abdul! Ashe haka kake cin amana ta kake bayan ido na ?!” ta hargitse cikin ihu, muryarta ta gauraye da karar DJ , Abdul ya miƙe idanunsa cike da mamaki da bacin rai bai tsaya yin wata magana ba, sai kawai ya ɗaga hannunsa ya zabga mata mari mai ƙarfi. Ƴan mata da samarin wajen suka tsaya suna kallon abin da ke wakana. Ramcy ta dafe kuncinta, hawaye suka taru a idonta, amma zuciyarta ta kasa natsuwa. Ta zuba masa ido tana cewa cikin rawar murya: “Abdul, kai nawa ne! Ai ni kaɗai ce na dace da kai, me yasa zaka nemi wata a gabana?” Abdul ya saki dariya mai cike da raini, yana kallon idonta da wata irin ɗabi’a ta iskanci. “Rayuwa sace Ramcy, kuma nan bariki ne. Ba ki da ikon hana ni sex da wata ko kuma nishadin da nake so.” " Shikkinan zaka gani , sai ka gani Wallahi Abdul sai kasan ka wulakanta ne a idon duniya, ƙarya ne wallahi kaci moreyata ka yardani , wato kanason kace kasha Mangoro zaka yasar da gwalon Mangoro ka huta da ƙudanto wallahi ƙarya ne ". Ya kama hannun sabuwar yarinyar da ke kusa da shi – Zubby – ya ja ta jikin sa, kamar ya ke son gwada ƙarfin mallakarsa a gaban Ramcy. Nan take ya haɗa bakinsa da nata cikin wani irin sumbata mai cike da alfahari da raini. Club ɗin ya kara ɓatsarwa, wasu suka yi ihu, wasu suka yi dariya, yayin da zuciyar Ramcy ta karye ƙalubale. ICU Muhsin ya zauna a ƙasa, ya rufe kansa da hannu biyu, zuciyarsa cike da godiya da fargaba. Wani irin sanyi ne ke ratsa zuciyarsa kamar iska mai ɗauke da hawaye. A can nesa, ƙarar motoci da hayaniyar birni suna dawowa, amma a nan cikin ICU, shiru ya mamaye ko’ina shiru mai nauyi, wanda ke ɗauke da fatan rayuwa da ƙaunar wanda ake jiran ya buɗe idonsa lokaci ya ja, hasken rana ya ragu, har awa biyu suka shige kamar shekaru biyu. Sai kawai likita ya fito da sauri, idonsa cike da damuwa. “Jininsa ya ƙare! muna buƙatar jini nan da nan irin jinin B-negative!”cikin ɗan rikici da firgici, kalmarsa ta bazu a zuciyar Muhsin da sauran dangi. B-negative! — irin jini da ba kasafai ake samu ba Saqir, wanda tun da farko ke tsaye a gefe, ya dafa kirjinsa da sauri “Dokta… gwada da Ni ne irin wannan jini nake da shi.” An kalle shi da mamaki, likita ya ɗauki samfurin jinin nasa da gaggawa. Ɗan lokaci kaɗan ya shige, sai ya dawo da murmushi mai ɗauke da alamar ceto. “Alhamdulillah… ya dace. Jinin Saqir ne daidai da nasa.”An kwantar da Saqir, suka haɗa layin jini zuwa jikin Bashir. Jinin ya fara gudana cikin natsuwa kamar tafkin bege. Lokaci ya shude, ranaku bakwai suka wuce kamar mafarki. Ranar da rana ta farka da haske mai sanyi, Saqir da Muhsin suka zo cikin shiga mai kyau — riga da wando masu kamshi, fuskokinsu cike da murmushi da fatan alheri. A bakin gadon da Bashir ke kwance, wata kyakkyawar mata ce zaune, idanunta a kumbure saboda kuka da rashin barci. A gefe kuma mijinta ya dafa kafaɗarta yana lallashinta da murmushi mai sa zuciya nutsuwa. Shiru ya ratsa dakin. Na’urorin ICU suna ta ƙara da wani irin sauti mai sanyi. Sai kuma… hankali ya karkata gaba ɗaya zuwa kan Bashir. Ƙananan motsi ya bayyana a fuskarsa. Fuskarsa ta yi ɗan rawa, idanunsa suka motsa a hankali — sannan a hankali sosai, kamar wanda ya dawo daga duniyar mafarki, Bashir ya fara buɗe idonsa… Ƙamshin magani da sanyin dakin ICU ne suka lullube dakin. Na’urori suna ta ƙara da sautukan su, kamar shaidar cewa rai da mutuwa suna ta jayayya a cikin wannan wuri. Sai kawai Bashir ya motsa hannun sa ya ɗan yi rawa, idanunsa suka motsa a hankali kamar wanda ke son ya buɗe ko kuma yana gudun abin da zai gani. Likita da ke tsaye ya matsa kusa, Saqir da Muhsin suka kame numfashi, zuciyoyinsu na bugawa da sauri a hankali… idonsa suka buɗe. Haske ya daki idanunsa, sai ya rintse su na ɗan lokaci kafin ya sake buɗewa gaba ɗaya. Idanunsa suka hau yawo a hankali cikin dakin kallon mamaki, kallon tuhuma, da ɗan girgiza kai kamar wanda ke cikin mafarki. Likita ya matsa kusa da gadon, yana kiran sunansa cikin sanyin murya: “Bashir… Bashir, ka ji ni?”ya zuba masa ido, ba tare da ya motsa ba. Saqir da Muhsin suka matsa kusa, zuciyoyinsu suka yi nauyi. Muhsin ya kama hannunsa cikin rawar murya: “Bashir" Bashir ya ɗago kai kadan, ya kalli su, sai ya furta cikin rauni da rawar murya: “Ni… ni wa nake? Sunana waye?” Kamar iska ta busa cikin dakin, kowa ya tsaya cak. Saqir ya kalli likitan da mamaki da tsoro suka gauraya a fuskarsa. Likita ya sauke numfashi mai nauyi, ya furzar da iska daga bakin sa yana girgiza kai. “Na san hakan zata iya faruwa…” ya ce a hankali, yana duban su duka. “Ya bugu sosai a kansa lokacin hatsarin, jini ya zuba da yawa. Wannan ne yasa memory ɗinsa ta samu matsala. Ya manta da kowa, da komai — har da kansa.” Dakin ya dauki shiru. Zuciyar Muhsin ta buga da ƙarfi, hawaye suka fara taruwa a idonsa. Likita ya dafa kafaɗar saqir cikin tausayawa ya ƙara da cewa: “Yanzu hakkin kulawa da shi ya rataya akan wuyanku. Zai iya zama kamar jariri, yana bukatar a koya masa komai daga farko. Ku shirya… tafiya ce mai tsawo.” Sai ya juya ya fita a hankali, yana barin su cikin dakin da ya cika da shiru — shiru mai nauyin tambayoyi da hawaye. Saqir ya zuba wa Bashir ido, ya kama hannunsa a hankali, zuciyarsa cike da raɗaɗi da alkawari a hankali ya furta cikin zuciyarsa: “Ko ka manta da duniya Bashir, ni ba zan manta da kai cewa mune sillar shigar ka wanan yanayi na…” BAYAN WANI LOKACI KAƊAN... Shaquwa mai zurfi ta shiga tsakanin Noor da Suhail duk inda ka ga ɗaya, to ka tabbata ɗayan yana kusa. Suhail ya saba da kallon ta tana dariya, yadda take tura gashinta gefe ɗaya idan iska ta ɗauke shi, yadda take girmama shi da kulawa irin ta zuciya mai tausayawa. A gefe guda Noor ta saba da kiran sa “Suhayl” cikin muryar da take fita da salo mai taushi, kamar kiran da yake ta da ƙauna daga wani ɓangaren zuciya da ba ta san yana akwai ba. Idan suna aikin gona, Noor ce ke kai masa ruwa. Idan suna hutu, shi ne ke lallaba ta da faɗin, “Ke dai kin zama kamar hasken safe ko rana bata fito sai na ganki.” zuciyarta kan buga, tana juyar da kai tana murmushi: “Wannan magana taka ka bari, ba komai bane face wasa.”ya ce cikin murya mai natsuwa: “Wani wasa ne da yake fito daga zuciyar da ba ta iya ɓoye gaskiya.” haka shaquwar su ta zurfafa har ta kai ga Noor ta daina jin nauyin zama kusa da shi. duk inda suka je, sai a ce “su biyu nan sun zama kamar ruwa da kankara, ba su rabuwa.” A ƙauye kuwa, magana ta zama abin ci da sha. Wasu suna faɗa da murmushi, wasu kuma da haushi “wai Noor wacce ta taɓa yin rantsuwa da sunan Allah cewa zata jira Bashir… yanzu ga ta da sabon saurayi.”maganar ta yawaita har ta kai ga iyayenta, zuciyarsu ta yi nauyi da damuwa. Amma Noor ba ta da ikon tsayar da abin da yake girma a zuciyarta — wani abu mai kama da tausayawa amma yana sauyawa zuwa so cikin sannu, cikin sirri, kamar yadda iska ke sauka a dare ba tare da sauti ba. Wani dare tana zaune a bakin tagar ɗaki, tana kallon taurari. Sai ta furta da sanyi a cikin ranta: “Bashir... ka bar ni cikin duhu da alƙawura. Amma wannan zuciya ta... tana neman wani haske ne daga inda ba ta zata ba.”hawayenta ya sauka a hankali, ta shafi kumatunta tana lumshe ido amma a zuciyar Suhail, soyayyar da ke ci kamar wuta ta gama cinye shirin komawa baya. A wannan lokaci, kowa a ƙauye ya yarda Noor ta manta da amana, ta manta da Bashir. Sai dai a zuciyarta, akwai sirrin da ita kaɗai ta sani — soyayya ce mai rikitarwa, tsakanin amanar da ta bari da zuciyar da ta fara jin wani sabon sauti. * What will happened in the next… ✨🌟 KAƊANGAREN BAKIN TULU 💥✨ BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** PART TWO PAGE 24/25 BAYAN WASU SHEKARU Firgit ya farka daga nannauyan baccin da ya ɗauke shi kamar wanda aka nutsar cikin duhu numfashinsa ya yi nauyi, idonsa ya buɗe a hankali kamar wanda ke komawa duniya daga wani wuri mai nisa cikin muryar da ta rikice, sai ya fara maimaita addu’a: “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un…” Kalmar ta tsaya a kan laɓɓansa, tana fita a hankali, tana haɗuwa da rawar jiki da firgici. gumi mai sanyi ya bayyana a goshinsa, yana gangarowa bisa kyakkyawar fuskarsa wadda ta haɗu da tsananin kamala da kwarjini. Yana daurewa, amma fargabar mafarkin da ya farka daga gareta ta kasa barin zuciyarsa ta zauna a hankali ya dafa kansa, hannayensa masu tsawo da haske suka motsa a hankali kamar yana neman kwanciyar hankali daga cikin jikinsa. Sai ya sauke ƙafafunsa — dogaye, masu santsi — daga kan gadon farin zanen da ya lullube shi. Gashin kansa mai laushi ya kwanta luff-luff a kan fatar kansa mai haske, yana ƙara masa wani irin kyau da natsuwa da ba a iya fassara wa. Ya jingina da katangar gefen gado, yana sauke numfashi a hankali, yana ƙoƙarin tuna... amma babu komai. Abin da ya rage a cikin zuciyarsa shi ne wani abu mai nauyi — tsoro, da tambaya, da shiru mai cike da asiri. Hannuwansa biyu ya saka cikin gashin kansa, yana ja da su a hankali kamar mai son tabbatarwa da kansa cewa yana cikin duniya. Doguwar ajiyar zuciya ya saki, sautin numfashin sa ya gauraya da shiru mai nauyi. A wannan karon, mafarkin da yake masa kamar rigar jikinsa yau ya sauya salo — domin komai ya dawo masa bayan dogon lokaci na duhu da rashin sanin kansa, yau ya fara tuna komai yau ne Bashir ya dawo cikakken mutum. Siraran hawaye masu dumi suka fara gangarowa a fuskar sa, suna haɗuwa da ɗan murmushin da bai cika ba — murmushin wanda yake tsakanin farin ciki da firgici. Sai kawai aka ji ƙarar ƙofar da aka turo da sallama, cikin taushi da nutsuwa. Wata yarinya ce ta shigo — kyakkyawa, tsaf cikin doguwar abaya mai kamshi, mayafi mai ɗan haske a kanta zubin ta na nuna tarbiyya da asalin gida mai natsuwa. Da farko ta tsaya cak, idonta a kansa, ta ɗan firgita ganin yadda yake zaune cikin ruɗani da hawaye da sauri ta matsa kusa da shi tana faɗin “Yayah Bashir, lafiya kuwa? Me yasa kake kuka?” Muryarta mai sanyi da taushi ta dawo da shi daga zurfin tunanin da ya nuts ahankali ya kalle ta, idonsa cike da mamaki, da tambaya, da tsoron gaskiyar da ta dawo masa. Ta sunkuya, ta tattara light breakfast ɗin da ta ajiye a kusa da gadon — faranti mai ƙunshe da toast, omelet mai cike da kayan lambu, da kofin warm milk wanda kamshinsa ke tashi cikin ɗakin ta juya a hankali, tana kiran: “Mommy! Daddy! Ya Bashir ya farka!” Muryarta ta ɗan sarƙe, tana haɗuwa da rawar jiki da jin daɗin mamaki ta jinjina kai, tana kallon Bashir da idanun da ke cike da tambaya da bakin ciki lokaci guda. “Yaya na kuka Mommy, wallahi yana kuka!” muryar Khady ta tsinke cikin dakin da ɗan rawar jiki, tana magana cikin hanzari da tsoron abin da ta gani. Idonta ya kaɗa da hawaye, zuciyarta ta buga da sauri kamar zata fito daga kirjinta. Mommy, wacce take a falo tare da Daddy, ta ɗago da mamaki da hanzari ta miƙe tana cewa cikin murya mai daure da fargaba “Khady, ki yi shiru mana! kwantar da hankalinki... let’s go and see him.” Bata ma gama kalmar ba sai ta kama hannun yarinyar, suka nufi ƙofar ɗakin Bashir cikin tsoro da fatan alheri cikin wannan ɗan lokaci ne Sagir da Muhsin ya biyo bayansu, yana riƙe da hankici, fuskarsa cike da damuwa da mamaki. Suna shiga dakin, sai kallo ɗaya ya wadatar. Bashir na zaune turƙus a ƙasa, gaban gadonsa, hannayensa biyu sun dafe fuska, ƙirjinsa yana motsi da numfashin kuka. Kamar ƙaramin yaro da aka wayi gari da tsoron mafarki, yana rawar murya yana maimaita addu’a, hawayensa na bin gefen kumatunsa har zuwa gemu. Mommy ta tsaya cak a ƙofar, zuciyarta ta buga, hawaye suka cika idonta kafin kalma ta fito. Daddy kuwa ya kasa motsi, yana kallon ɗan nasa da wata irin shiru mai nauyi — shiru mai cike da tambaya, mamaki, da godiyar Allah. Sagir ya matso a hankali, muryarsa ta yi rauni: “Bash... Bashir?” Amma Bashir bai amsa ba — sai ma ƙara saka hannuwansa cikin gashin kansa, yana jan numfashi mai nauyi kamar wanda yake ƙoƙarin farfaɗowa daga tarihin da ya daɗe yana mafarki daga gare shi, gashi yau Allah ya.. ##### DUBAI A hankali ta shafa kansa, ƙafafun hannunta sun rungume jikin sa da kulawa mai laushi. Nan ya firgita, zuciyarsa na buga da sauri kamar zata fashe. “Haba Habibty, wallahi na tsoro ta…” cewar Rayyan, murya cikin kaɗan da rashin tabbaci. Harara ta buga mai kai, idanunta suna cike da tausayi da damuwa. “Don Allah, Kaye… auren ma ba zaka daina wannan tsoron ba ko?” Cikin murmushi mai cike da baƙin ciki, ya dawo da hankali a hankali. Murmushin sa ya yi sanyi, cike da wani irin nauyi da ya sha wahala, ya furta, “Habibty … kinan… rayuwa tamkar bani da uba, na azabtu a gidan mahaifina. Wallahi, bazan manta watarana da aka min sharrin sata ba ranar da tafe kowacce rana wahala a guna…” Ya tsaya, ido na kallon ƙasa, zuciyarsa cike da tsoro da fargaba, amma a lokaci guda, akwai wata ƙaramar haske na farin ciki da ke bayyana a gefen fuskar sa — saboda yanzu, a ƙarƙashin kulawar Rayyan, ya fara jin cewa akwai wani wuri mai aminci a rayuwarsa. A cikin murya mai rauni, Rayyan ya faɗi, yana kallon matarsa da idanuwa cike da zafi labarin da ya sha kamar wuta a zuciyarsa. “Sun kawo wani tsohon soja Iri — mutum mai fuska kamar dutse, hannunsa kamar sanda. Sun daure ni a bayan hannu, aka rufe ni a ɗaki mai duhu; babu rana, babu iska, babu ruwa, babu abinci. Rana da dare duk sun tsaya a wuri ɗaya — zafi ya mamaye wajen kamar an jefa ni cikin ƙarfe mai ɗumi, tsawon kwanaki ukku ina azabtuwa A can ne suka fara ‘horon’ — ba horo na ilimi ba, horon azaba. Sun kunna mini fargaba, suka nuna mini wani abu a matsayin ‘shaidar wuta’ — alamun azaba da nufin tsorata ni. Idona ya yi jaƙeƙe, zuciyata na bugawa kamar kararrawa, a duk lokacin sai na ji ƙamshin hayaki na bakin zuciya. Hawayen suka fara cika idona; a lokacin Iro ya ƙi tausayi — ya shafa hawayen da hannunsa mai ƙarfi, amma shafinsa ba tausayi bace, sai tambaya mai sanyi: ‘Tabbas ka sha azaba Hayyaty amma me ya ƙubutta da kai a wancan ranar?’ ya sauke ajiyar zuciya, ya amsa cikin murya mai ƙasa, Muryar da na rawa: ‘Na ƙubutta... saboda ba ni da wata hanya tsoro ne ya ja ni, rashin gida ne, da rashin abin dogaro. Amma ba azabar ta zama banza ba; na rike abin da aka bani, na ɓoye amanar da zata ceci wasu.’ A duk lokacin da na tuna, numfashina na faɗuwa da sauri; amma a zuciyata akwai ƙanƙanin haske — sanin cewa duk wannan azaba ba ta ɓace ba, tana da lokaci tsanani baya tabbata haka daɗi baya dawwama ” A jiyar zuciya na sauke, hawayen na zube kamar ruwan damina — a hankali, numfashin na ya fara rikewa cikin ƙarfi da kuka. Duk da haka, a tsakiyar ƙunci da azaba, sai wani abu ya zo min kamar labari mai dumi a kunne: murya — murya mai ƙamshi na gida, mai cike da tausayawa. “Yaro na… ka natsu, ka daina kuka,” muriyar ta zo a hankali kamar ta fito daga cikin inuwa. Rayyan ya ɗaga kansa da sauri, idanunsa sunɗan yi jaƙeƙe. Bai yi shakka ba — muriyar mahaifiyarsa ce; ta fito masa fili a zuciya kamar ido yake gani. A lokacin, sai na tuna da zanruttukannhikima da ƙawata Suwaiba kimin “Ka kasance ƙarfin zuciya, ka jingina da addu’a, kada ka bari tsoro ya mallake ka.” Wannan ƙaramar muryar ce ta sa zuciyarsa ta ɗan natsu. Ya ɗan yi dariƙa, ya share hawayensa da bayansa na hannu, ya ce cikin rawar murya mai rauni: “Mom… na tsoro… na sha azaba…” Muryar mahaifiyarsa ta ƙara taushi, tana ƙoƙarin mika masa kwanciyar hankali: “Na sani, ɗana. Amma ka ji daɗi — kai ba kaɗai bane. Mun zo tare da kai ka rike wannan ƙarfin zuciyar, mu za mu tafi tare muka samo mafita kada ka manta, hayaniyar duniya ba za ta wuce ba — amma girmanka da kirki zai zauna.” A hankali, Rayyan ya sami ƙaramin natsuwa. Kukan sa ya ragu, numfashinsa ya koma daidaito yana kallon matarsa da idanu masu ƙara laushi, ya ɗauki hannunta, ya matsa kusa da ita da ƙanƙantar murya: “Na gode, kin zo min a daidai lokacin da na fi buƙata.” Ta rungume shi da ƙarfi, kamar tana ƙoƙarin ja masa duka danƙon duniya. suna kallon yadda ƙauna take warkar da raunuka. To be continued............. ✨🌟 KAƊANGAREN BAKIN TULU 💥✨ BY NARNAH ƘANWAR SOJA Follow my Wattsp group 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM *https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ *(J.W.A)* _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ 🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚 (🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚) GARGAƊI Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba , ******** PART TWO PAGE 26/27 A hankali Bashir ya ɗago kansa daga cikin hannayensa, idonsa ya cika da hawaye, amma a ƙarƙashin su akwai wani sabon haske hasken da ya rasa shekaru da dama, hasken tunawa ya dafa kirjinsa, numfashinsa yana fita da sauri, kafin a hankali ya furta cikin murya mai rawa “Mommy… yau… yau na tuna komai. tabbas, nine Bashir.” Mommy ta dafe ƙirji, Daddy ya ja numfashi da kyar, Sagir kuwa ya matso kusa, muryarsa cike da ruɗani “waye kai Bashir? wacece Noor da kake faɗa?” Bashir ya lumshe ido, hawaye na zuba a hankali, yana jin kamar zuciyarsa tana sake rayuwa daga farkon ta ya ɗan murmusa da ciwo a fuskarsa, sannan ya ce: “Sunana Bashir mahaifiyata ta haife ni cikin kurɓattaccen yanayi — ta mutu tana kuka, tana roƙon Allah ya kare ni daga zalunci na taso cikin wahala, cikin azaba, amma akwai wata rana… wata rana da ta sa rayuwata ta zama haske. ya ɗan yi shiru, numfashi na rawa, sannan ya ci gaba: “Noor ce — yarinya ce da ta zama hasken rayuwata mun taso tare, mun yi alkawari na ce mata zan dawo garinta, na dawo da amana, saboda soyayyarmu ta yarinta ba ta gushe a raina ba.” Ya share hawayensa, idonsa ya ƙara ƙyalli kamar wanda yake kallon nisan baya. “Mallam Sambo… shi ne wanda ya raina mu, kuma shi ne mahaifinta. Shi ya sani yadda nake numfashi da wahala, yadda nake rayuwa da fatan wata rana zan dawo da cikakken ni.” Shiru mai nauyi ya biyo bayan kalmomin sa. Mommy ta kasa magana, hawaye suka gangaro ta kumatunta Daddy ya dafa kafaɗarsa cikin taushi yana cewa: “Bashir, tabbas ka zama ƙadangaren bakin tulu — duk wahalar da suka baka tun kafin ka zo duniya, duk ɓacin ran da ka sha, ga shi yau ka fito da haske. Allah ya baka rayuwa mai kyau, da kamala da nagarta. Amma… shin zaka iya tuno gida? kana tuna inda kake fitowa?” Sagir, wanda har yanzu idonsa cike da hawaye ne, ya ƙarasa cikin rawar murya: “Yallabai, motarmu ce ta buge shi shekaru da suka wuce a hanyar gaba da ƙauyen Rimi dake Kano mun ta nema — mun nemi danginsa har muka gaji. Likita ya ce brain dinsa ya samu rauni, jinin kansa yana ƙanƙancewa. Ya ce idan Allah ya yarda, lokaci zai gyara komai...” ya juya yana kallon Bashir da murmushi mai cike da tausayawa: “Yau lokaci ya yi, Bashir. Ka dawo da kanka da labarinka.” cikin ɗakin aka ɗauki shiru — shiru mai daɗi, shiru mai cike da hawaye da godiya. Mommy ta rusuna ta rungume ɗan nata, tana kuka da murmushi lokaci guda. “Alhamdulillah… ka dawo Bashir… ka dawo daga duhu.” Nan ya ɗago da jajayen idanu, muryarsa na rawa kamar mai jin sanyi cikin zafi ya ce: “Tabbas zan gane hanyar daji, zan gane ƙauyenmu.”ya yi shiru na ɗan lokaci, yana kallonsu cikin mamaki da zafin zuciya, sannan ya ci gaba, muryarsa cike da raɗaɗi: “Amma me yasa kuka riga ni da amana tsakaninku da Allah? me yasa kuka kai ni wannan matakin? Su waye ku a zahiri? Ku mutane ne ko kuwa wata jarabawace da aka aiko min da ita?” Sai ya dafe kansa da hannayensa biyu, yana girgiza kai a hankali, hawaye na zuba kamar ruwan sama da bai da niyyar tsayawa. Mommy ta zuba masa ido cikin tausayawa, Khady kuma ta matso da sannu tana ƙoƙarin riƙe hannunsa, amma ya ja hannunsa a hankali, yana cewa“Kada ki taɓa ni yanzu... ban gama fahimtar komai ba.” wannan yanayi ya ɗauki hankali gaba ɗaya, har iska ta ɗauki sassan ɗakin cikin shiru mai cike da nauyi. Sagir ya matso da nutsuwa a fuskarsa, yana dubansa da idon da ke cike da tausayi, ya ce cikin murya mai laushi: “Ka kwantar da hankalinka, dan’uwa… babu abin da ya faru da kai da ba Allah ya ƙaddara ba.”Muhsin ma ya gyara zama kusa da shi, yana ɗan lumshe ido kafin ya ce cikin natsuwa: “Lokacin da muke tafiya da gudu muna shirin shigowa garin Kaduna, a lokacin ne muka buge ka da mota. Mun firgita sosai, hankalinmu ya tashi… muka yi ƙoƙarin taimaka maka. Mun kai ka asibiti, muka bayar da jininmu, da dukiyar mu, har sai da ka warke.” Ya ɗan yi shiru, sannan ya ci gaba da bayani: “Mommy da kake gani ita ce mahaifiyarmu, Khady kuma ƙanwarmu ce. Daddy ne ya ɗauke ka tamkar ɗansa, suka ba ka kulawa fiye da yadda kai kanka ka taɓa tsammani. Aka saka ka makaranta, aka koya maka karatu mai zurfi, har ka kai matakin degree na biyu a fannin Political Science.” Sagir ya ɗan murmusa cikin yanayi na alfahari, sannan ya ce: “Yanzu kai mutum ne mai burin zama shugaba — Shugaban ƙasa! Wannan shi ne burinka, wannan shi ne abin da kake so ka cimma shin yanzu ka gane waye kai?” Shiru ya rufe ɗakin, sai numfashinsa da ke fita a hankali ya durƙusa da hawaye a idanu, zuciyarsa cike da godiya da mamaki. “Na tuna komai…” ya furta a hankali, yana duban Mommy da Daddy da sauran ’yan gidan.“Na gode da kuka bani rayuwa ta biyu.” sai Daddy ya ɗan yi murmushi cikin natsuwa, yana cewa “Haba Bashir, yanzu ba lokacin kuka bane mu shirya, zamu tafi Kano.” duk suka amince, fuskokinsu na cike da kwanciyar hankali da sabon fata. Safe journey Bashir ################### Ana haka, uncle ɗinsa, wato ƙanin baban sa, ya iso cikin ɗakin horo cikin hanzari, idonsa cike da damuwa da fargaba. Sai Umme ta tsaya a gefensa, ta bayyana masa halin da ake ciki: yadda Rayyan ke cikin ɗakin horo ana azabtar da shi, kuma yadda jinin sa ke zuba saboda sun yi tsammanin zai ɗauki kuɗi mai yawa. Da wannan bayanin, uncle ɗin ya miƙa hannu, ya ce da ƙarfi: “Haba, Daddyn Rayyan, kana kallo ne? Ana azabtar da ɗan ka saboda jini da kudi? Ashe menene a zuciyar su? Shin basa ganin cewa babu yadda zai iya ɗauke kuɗin nan? Kowa ya san Abdul ne kadai zai iya kwashe ma kuɗi. Wannan ya ishe!” Da wannan, ya ɗauki matakin da zai ceci ɗansa. Ya yi saurin buɗe ƙofa, ya shiga ɗakin da zafi da duhun horon ya cika, ya ɗaga Rayyan cikin kulawa, yana yi masa kwantar da hankali: “Rayyan ɗana, yanzu ka tsaya. Zan kai ka Dubai zaka samu tsaro, za ka zauna lafiya, kuma za ka cigaba da karatunka a can. Anan ba za ka ƙara jin tsoro ba, ba za ka ƙara wahala ba ,tun bayan mutuwar ka mahaifiyar ka nake so na ɗauke amman Daddyn ka ya hana , kasani yau babo wanda ya isa ya rabani da ɗaukar ka ” Rayyan, cikin shiru da mamaki, ya ji zuciyarsa ta ɗan sassauta. Duk da tsoron da ya sha, ganin uncle ɗinsa da kulawa, da cewa zai samu tsaro da ilimi a Dubai, ya sa ya fara murmushi a hankali, yana jin cewa Allah ya shirya masa hanyar kuɓuta da rayuwa mai kyau. Bayan uncle ɗinsa ya ɗauke shi, Rayyan ya shiga mota cikin sauƙi, duk da cewa zuciyarsa cike da haɗuwa da tsoro da fargaba. Safiyar nan, motar ta fice daga gidan horon, kuma ya ga duhu da zafi suna rabuwa da nesa da su, kamar duhu da azaba sun tsaya a baya, suna kallon yadda yake barin su. A hanya, uncle ɗin ya rike hannunsa, yana masa kwantar da hankali: “Rayyan ɗana, komai da suka yi maka an bar shi a baya. Yanzu za ka fara sabon rayuwa. Za ka samu tsaro, karatu, da damar da ba ka taɓa tunanin samu ba.” Jirgin sama ya ɗauki su daga filin saukar jirgi na Kano zuwa Dubai. Rayyan yana kallon birnin daga sama, hasken dare da taurari sun yi kamar suna yi masa maraba. Duk fargabar da ya sha a baya ta fara raguwa, zuciyarsa ta ɗan sassauta. Da suka sauka, aka karɓe su a tashar jirgin da motoci masu tsaro suka zo, suna ɗaukar su zuwa wani hotel mai tsada. A can, Rayyan ya fara fahimtar cewa duniya tana iya canzawa daga mugunta zuwa tsaro, kuma akwai damar da Allah ya tanadar masa cikin gidan su ɗin, ya zauna yana kallon birnin da tsawo, zuciyarsa cike da sabuwar fata: “Zan yi karatu mai kyau zan zama mutum mai nagarta kuma ba zan taɓa bari mugun zuciya ta dinga rike ni ba.” A nan ne ya fara sabon babin rayuwa, cike da karatu, tsaro, da damar da zai iya amfani da shi wajen gyara rayuwar kansa da ta waɗanda yake ƙauna. Kuma kowanne dare, kafin ya kwanta, yana tuna duk darasin da ya koya daga wahalarsa a gida — da ƙoƙarin fita daga mugun hali zuwa sabuwar fata. Rayyan ya iso gidan uncle ɗinsa, wanda shi ne ƙanin mahaifinsa, mutum mai arziki sosai a birnin Dubai. Gidan cike yake da kyakkyawan kayan ado, fitilun zinariya, da kayan alatu — komai na nuna tsari da daraja. A gefen gidan, Raizah, yarinya ɗaya tilo, tana wasa cikin lambu mai tsabta da ciyayi kore-kore, tana dariya mai kayatarwa. Uncle ɗin ya rungume Rayyan yana cewa “Yaron nan, yanzu rayuwarka zata canza. Ka gama wahala, yanzu lokaci ne ka ji daɗin abin da Allah Ya tanada maka.” an shirya masa ɗaki mai kyau, gado mai launin zinariya da auduga mai laushi, duk abin jin daɗi yana nan. Rayyan ya ɗan yi mamaki, zuciyarsa cike da farin ciki da rashin tabbas: ko da yake yana cikin gidan mai kuɗi, har yanzu akwai raɗaɗin baya da azabar da ya sha. Amma ganin Raizah na wasa a lambu, da murmushin uncle ɗinsa, sai zuciyarsa ta fara sassautawa. A kowane dare, Rayyan zai zauna a dakin karatu mai fadi, yana ganin birnin Dubai daga taga. A can ne zai fara tsara yadda zai ci gaba da karatu da horo, kuma zai koyi darussa masu mahimmanci daga uncle ɗinsa: yadda ake tafiyar da kasuwanci,yadda ake amfani da albarkatun kuɗi don taimaka wa mutane, yadda ake tsayawa da ƙarfi a rayuwa ba tare da barin azaba ta rushe zuciya ba To be continued..... Kasan matsayin ka a siyasa yanzu kana neman takarar zama Senator a Majalisar dokoki ta Kaduna State House of Assembly, kai ne kuma Speaker, kana ci gaba da karatu domin cika burinka na zama Gwamnan Kaduna State nan gaba kadan. A yau, jirgin su Bashir, Daddy, Mommy, Sagir, Muhsin da Khady ya tashi daga Kaduna International Airport da ƙarfe takwas na safe, cikin lokaci kaɗan jirgin ya ɗaga sama cikin sanyi da natsuwa bayan awa ɗaya daidai, sun sauka lafiya a Mallam Aminu Kano International Airport. Bashir tun a cikin jirgi ya kasa samun nutsuwa — zuciyarsa tana ta bugawa da sauri kamar ana buga gangar alhini da suka sauka, duk da Mommy tana ta masa nasiha da Sagir na ƙoƙarin kwantar masa da hankali, ya kasa zama a mota ko jiran lokaci. Tuni aka shigo da motoci masu tsaro zuwa filin jirgin, ‘yan sanda da jami’an gwamnati suna nan suna jiran su, saboda tuni aka sanar da su manufar tafiyar. Ba tare da ɓata lokaci ba suka nufi hanyar ƙauyen Rimi, inda komai zai bayyana. Motoci suka rinka shigowa cikin ƙauyen Rimi a hankali, ƙura na tashi a sama tamkar hadari mai shirin sauka mutane suka fara fitowa daga gidajensu, kowa cikin mamaki da tambaya a fuskarsa. “Lallai yau akwai wani abu!” cewar wani dattijo yana jingina da sandarsa, yana kallon jerin motocin gwamnati da ke shigowa cikin ƙauyen da ƙarar siren ɗin su ke cika iska. ƴan sanda suna gaba, suna gyara hanya cikin girmamawa, yayin da motar gwamnati ke bi a baya a cikin motar kuwa, Bashir ya zauna a gefe cikin nutsuwa da wani irin yanayi mai cike da tunani kallon da yake yiwa kowace kusurwa na ƙauyen tamkar yana neman wani ɓangare na rayuwarsa da ta ɓace shekaru da suka shuɗe. A gefensa, Mommy ta dafa hannunsa a hankali, tana ƙoƙarin kwantar masa da hankali “ka kwantar da zuciyarka, Bashir komai da ka rasa a baya, Allah zai mayar maka da shi cikin alheri.”ya jinjina kai kawai, ya kasa magana. Idanunsa sun cika da hawaye da bai so su zubo ba da suka shiga tsakiyar ƙauyen, yara suka fara bin motocin suna ta dariya da ihu. matasa suna tsaye suna ɗaukar hotuna, wasu kuma suna ta kallon wannan shigar da ba a taɓa gani ba a cikin ƙauyen. Daga nesa, wani tsoho mai farin gemu ya fito daga ɗan ƙaramin gida yana rarrafe da sanda. Kallon motar farko yayi sosai kafin ya furta cikin murya mai rawar sanyi: “Subhanallah... wannan kam irin wannan rana bata taɓa zo ƙauyen Rimi ba.” a wannan lokacin, Daddy ya ba da umarni, motoci suka tsaya. Ƴan sanda suka zagaye wajen, sannan aka buɗe ƙofar motar da Bashir yake ciki. yana sauka, iska mai sanyi ta buga masa a fuska, zuciyarsa ta fara bugu da ƙarfi. Kallon ƙauyen yayi da idanu masu ɗauke da hawaye ganuwar ƙasa, bishiyoyi, da ƙofar tsohon gida da ya fara gane ta a hankali. Mommy ta fita a hankali tana kallon yadda kowa ke rufe baki cikin mamaki. Sai dai Bashir ya tsaya cak, idonsa ya tsaya a kan wani dattijo da yake kusa da wani tsohon gida — murya ce ta fito daga bakinsa cikin rawar murya:" Babaa" Dukkan su suka kalli inda yake kallo. Dattijon ya tsaya shiru, yana ƙoƙarin gane muryar. Sai da ya kalli Bashir sosai kafin ya furta da hawaye suna gangarowa “Kai… kai ne Bashir ɗana?!” a hankali suka nufi juna, duniya ta yi musu kamar ta tsaya cak “Baba… kai ne?” Dattijon ya ɗago a hankali, idonsa ya tsaya kan Bashir — kyakkyawan saurayi cikin kaya masu tsada, takalminsa ƙirar Louis Vuitton, ƙamshin turarensa yana ratsawa har cikin hancinsa sai Bashir ya matsa dafff, ya durƙusa a gabansa, ya dafa kafaɗarsa cikin rawar hannu da hawaye “Baba… kaine ka dawo haka? me ya sameka? me yasa rayuwa ta juyar da kai haka?” Kamar a mafarki, Mallam Audu ya tsaya kallonsa da ido mai girgiza, kamar yana son musanta abin da ke gabansa. Sai dai lokacin da ya ji muryar Bashir — muryar da take kama da ta yaron da ya kore daga gida shekaru da suka shuɗe, muryar da ta yi masa barazana da zafin tarihi — sai numfashinsa ya tsaya. Sandar da yake riƙe da ita ta sulale daga hannunsa ta faɗi ƙasa da ƙarar wargasss! Idonsa ya faɗa da tsoro da girgiza, jikinsa yana rawa sai ya ja baya da ƙyar yana ƙoƙarin fitar da kalma “Wannan... wannan muryar… ba zai yiwu ba…”Hawaye suka gangaro daga idon Bashir, yana dubansa cikin tausayi da ƙauna: “Baba... ni ne… Bashir ɗanka ne… wanda ka kori da hannunka...” Kamar wanda aka jefa cikin wutar zafi, Mallam Audu ya dafe kirji yana kakkarwa. Wani irin zafi ne ya mamaye zuciyarsa — zafin nadama, zafin tarihin da ya shafe shekaru yana ƙoƙarin mantawa da shi. Sai kawai ya furta da murya mai rawa, kafin idonsa su cika da hawayen da ba su da ƙarewa “Yaron da… na kora kamar kare Allahu Akbar!” Sai ya zube ƙasa, sandar sa ta narke a gefe, ƙauyen ya ɗauki ihu. Mommy ta ruga da gudu ta riƙe Bashir, Khady ta kame bakinta da kuka, yayin da Daddy ya tsaya a gefe yana kallon abin da ya faru kamar a fim Bashir ya durƙusa da kuka, yana dafa tsohon da ya faɗi “Baba, ka tashi..." Sai dai Mallam Audu ya riga ya sulale cikin rashin kuzari, idonsa a buɗe, yana kallon sama kamar yana neman gafarar da bai samu ba shekaru da suka shuɗe… """"""$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$""""""" Rayyan ya shiga gidan uncle ɗinsa, zuciyarsa cike da mamaki da ɗan tsoro. Falo ya yi girma fiye da tunaninsa; labulen zinariya suna shafa ƙasa, fitilu masu haske kamar tauraruwa na sheƙaɗa kowane kusurwa. A gefe, Raizah, yarinya tilo mai shekaru goma sha ɗaya, tana wasa cikin lambu mai ciyayi kore-kore, murmushi a fuskarta yana kama da haske mai ɗaukar ido. Uncle ɗinsa ya rungume shi da hannu mai ƙarfi, ƙamshi na turare mai daɗi ya lullube dakin, yana cewa: “Yaron nan, yanzu rayuwarka zata sauya. Ka gama wahala, yanzu lokaci ne ka fara jin daɗin abin da Allah Ya tanada maka.” Rayyan ya ji wani ƙarfi na natsuwa ya lullube zuciyarsa, amma har yanzu fargaba da mamaki na cikin sa. Duk da alatu da kayan alatu, zuciyarsa tana tuna wahalar baya. Amma ganin Raizah, murmushi a fuskarta, da yadda take kallon sa da ƙauna, sai wani ɗan shauqi mai sanyi ya shiga zuciyarsa. An shirya masa ɗaki mai fadi, gado mai laushi da auduga mai tsabta, taga tana kallon birnin Dubai mai haske da dare. Kowane dare zai zauna a dakin karatu, yana tunanin yadda zai fara karatu cikin ƙwarewa da natsuwa, da yadda zai zama mutum mai ƙarfi da hikima a rayuwa. Raizah ta zama wani ɓangare na sabuwar rayuwarsa. Kallo daya kawai daga gare ta, sai zuciyarsa ta tsinke da wani irin jin daɗi, kamar ya dawo gida bayan dogon lokaci. Amma duk da sabuwar rayuwa, Rayyan bai manta da azabar baya ba — waɗanda yanzu za su zama ƙarfi da himma a sabon fara rayuwarsa. A hankali, murmushi ya bayyana a fuskarsa, ya faɗi: “Wannan shi ne farkon rayuwata. Zuciyata zata shigo cikin sabuwar duniya, kuma babu wanda zai iya tsayar da ni.” Rayyan ya juya kallon Raizah, zuciyarsa tana bugawa da sauri. Kyakkyawar fuskar ta, idanuwanta masu sheƙaƙe, da murmushinta mai laushi sun lullube zuciyarsa cikin wani irin shaukin da bai taɓa ji ba. Raizah kuwa, tana kallon shi da ƙauna da fahimtar juna, ta ji wani ɗanɗano na soyayya mai laushi a zuciyarta, kamar ranar farko da duniya ta bayyana mata da haske. A hankali ta matso kusa da shi, hannayenta sun haɗu da na Rayyan, kuma kallo ya zama kamar harafin zuciya da ke bayyana komai da ba a faɗa ba. Rayyan ya ɗan ja numfashi, ya ji dumin Raizah yana shiga zuciyarsa. A hankali ya ƙara matsawa, har idanun su suka haɗu, sai zuciyoyinsu suka yi magana fiye da dukkan kalmomi. A wannan lokaci, duk abin da ya faru a baya — wahala, azaba, rashin tsaro — ya zama kamar gajeren mafarki ne kawai, saboda yanzu akwai wannan haske na soyayya da ke ɗaukar su gaba. Raizah ta ɗan murmusa, ta faɗi cikin muryar sanyi mai shauki “Rayyan… yanzu babu wani abu da zai iya raba mu.” Rayyan kuwa ya rungume ta da ƙarfi, yana jin zafin zuciyarsa da farin ciki a lokaci guda. Wannan shine farkon labarin soyayya da shauki tsakanin su, inda duk wata tsoro ta baya ta narke a cikin wannan sabon haske .. “Kasan fa, Daddy, na jirar mu zamu tafi airport yanzu. Dole muyi wani wankan jarabar kananan,” Raizah ta ce da dariya, idanuwanta cike da walwala da shauki Rayyan kuwa ya murmusa, ya janyo ta a hankali zuwa jikinsa, yana jin zafi mai laushi a zuciyarsa “To, menene, baby? Kinsan fa idan kina tare dani, mantawa nake da kaina,” ya ƙara cewa yana kunce mata tawol cikin shauki... A wannan lokaci wayarsa ta dakkar tar, sai ya ɗaga hannunsa yana murmushi. “Hello… ehh, Uncle,” ya ce cikin sautin nutsuwa, sannan ya gyara muryarsa: “By 11 jirgin mu zai tashi, 10:30 me kukiye baku zo airport ba?” ????????????????? Zuwa ina to be continued. An shigo da Mallam Audu cikin gidan a hankali; an ja shi har zuwa zauren inda Baaba ke zaune. Ta jingine bakinta, yawu na zubo da wari mai ƙarfi; a ƙirjinta sai ƙudaje suke bayyana kamar sun fara samun nama — alamar cewa ciwon ya dade kuma ya tsananta. Ta zauna tana sauraro, idonta a buɗe amma babu yadda za ta iya magana; hawaye na zuba a gefen idanunta kamar ruwan sama. Bashir ya tsaya a gabanta, zuciyarsa cike da nauyi, ba shi da magana; Mommy da Khady suka tsaya a baya, sun dan natsu, sun yi nesa da ita domin gudun ɗaukar cuta gidan ya yi sanyi, shiru na nauyi yana zaune a ko’ina, kowa na kallon Baaba cikin tausayi, yayin da ta ci gaba da sauraron maganganun da ke zagaye da ita, hawaye na zubowa a ƙusuranta. Chan Mallam Audu dake kallon Mommy, ko ƙiftawar ido bai yi ba. Babo yace da murya mai sanyi amma cike da iko:“Duk ku zauna… Bashir, tabbas kaine ƙadagaren bakin tulu!” Wannan kalma ta kada zuciyar kowa dake wurin. Shi ne abinda koyaushe Mallam Sambo ke faɗa — amma yau ne aka tabbatar da ita a fili. Ashe wannan rana ce da za ta tona sirrin shekaru masu tsawo. Wani shiru mai nauyi ya biyo bayan kalmar. Sai wata kyakkyawar yarinya ta matso daga bayan jama’a — ƴar shekara goma, idanunta kamar taurari amma cike da tsoro da mamaki. “Zo nan, ke zauna anan NOOR ,” in ji Mallam Audu yana nuna mata kujera kusa da shi Ya juyo yana kallon Mommy da Bashir, sannan ya ɗan gyara zama. “Yau zan faɗi labarin da nasan cewa hakkin wannan labarin shi ne dalilin da yasa har yau ban mutu ba… Ina ganin rayuwa kalla-kalla, saboda wannan sirri da ke cikin zuciyata.” Mallam Audu ya dafe ƙirjinsa, zuciyarsa na bugawa da ƙarfin da ya wuce na mutum mai rai. Idanunsa sun cika da hawaye, muryarsa ta yi sanyi amma tana ɓoyar da zafin da shekaru suka tara a ciki ya ɗan kalli Bashir, sannan ya sauke numfashi mai nauyi. “Bashir… ka saurare ni da kyau, saboda abinda zan faɗa maka yau shi ne abin da nake jira shekaru da dama in faɗa kafin in mutu. Mamanka, sunanta Ummu Kulsum — mace ce da Allah Ya halitta da ƙima da haƙuri Lokacin da ta zo ƙauyen nan, mutane suka ce ‘yar gudun hijira ce, suka ce ta fito daga arewacin kasar nan saboda yaƙi amma gaskiyar magana ita ce — ta zo ne da wani tsohon makaho, wanda ya ɗauke ta tamkar ‘ya. Mutane suka raina su, suka ɗauka ba su da galihu. Ni kuma… ni ne bala’in rayuwarta.” Ya lumshe ido, hawayen da ya dade yana riƙewa suka sauko kamar ruwan sama. “Na aure ta saboda son zuciya, saboda kishi da ƙeta amma ban aure ta saboda Allah bana zama azzalumi. Na hana ta dariya, na hana ta kwanciyar hankali. Duk sautin muryarta yana tuna min da hasken da ban taba samu ba. Na mata duka a bakin murhu, na wulaƙanta ta har ta gaji da numfashi. Wata rana cikin fushin da ya makantar da zuciyata, na zuba mata ruwan talken towo mai zafi a lokacin ruwan sama. Ta faɗi, ta mutu a gabana.” Ya durƙusa yana kuka kamar ƙaramin yaro. jin irin rawar muryarsa yasa kowa a wajen ya kasa motsi “Tun daga wannan rana, zuciyata ta zama kamar wuta. Amma kafin ta mutu, ta bar kadangare a gidan nan — shi ne kai, Bashir. Duk da ban san ka ba, ban san lokacin da aka ɗauke ka ba, amma kullum ina jin zuciyata tana tsanar ka, tana tsoran ka, tana son ka lokaci ɗaya ashe wannan yana nufin kai ɗan mamanka ne, kai ne amanar da na watsar.” Ya share hawayensa da hannun da ke rawa, yana kallon Bashir da idon nadama. “Rashin addini ya rufe ni, giya ta zama abokiyata, mata suka zama abincina, har na manta da mutuncin rayuwa. Amma yau na fahimci cewa Allah bai manta da ni ba, saboda har yanzu ina numfashi don in furta wannan gaskiya.” Sai ya ɗaga kansa sama, yana girgiza kai kamar mai kuka cikin addu’a. “Ka yafe min, Bashir. Ka yafe min don mamanka. Ka yafe min don Allah. Ka yafe min domin wannan rai da ban cancanci in rayu ba.” Shiru ya cika wajen, kamar iska ta tsaya. Sai muryar sa ta katse natsuwar wajen cikin sanyin murya “Bayan mutuwar Malam Sambo, Noor ta ƙi aure kullum maganarta ɗaya ce — ‘zaka dawo kayi alƙawari…’Amma babu labari, babu wasiƙa.Har ƙauyukka ta bi tana nemanka, wancan lokacin.” Mallam ya share hawaye sa, ta ci gaba cikin murya mai motsa zuciya “Lokaci ya ja, ta girma . Kawayenta sunyi aure, ta ƙi kula da kowa. Sai wani yaro ya bayyana daga daji — yaro mai kallo kamar aljani, amma idanunsa suna cike da haske da hikima Sunan sa Suhayl. Shi ne ya kawo mana haske da ilimin sa na Addini Haske da har yanzu ba mu gane ko daga ina yake ba.” Mallam Audu ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa kukan da ke fitowa daga zuciyarsa bai da sauti, amma ya cika ɗakin da nauyin nadama. Zuwan Suhayl ya zama tamkar sabon safiya ga ƙauyen un daga lokacin da ya shigo, murmushi ya fara komawa a fuskokin mutane, kuma Noor ta zama kamar sabuwar fure a cikin daji. Idanunta suna haskawa da farin ciki, zuciyarta ta cika da nutsuwa kamar ta sami abin da take nema shekaru Lokaci bai jima ba, yayan ta ya aurar da ita ga Suhayl, cikin kalmar da ta ce: “Bangaji da jiran wanda bazai dawo ba ,amman bazan manta da cewa inason Bashir da har abada ba ” Amma, kaddara ta fi ƙarfin burin ɗan adam. Noor ta rasu cikin imani, ta koma ga Mahalicci tana riƙe da sunan wanda ta kasa mantawa da shi — Bashir. Har zuwa mintin ƙarshe na rayuwarta, kalmarta ɗaya ce: “Zai dawo... zai dawo ne...” Ta haifi ɗa mace guda ɗaya, mai kamannin ta da kyawunta, mai nutsuwa kamar mahaifiyar ka ta sakawa yarinyar sunan mamanka — Ummu Kulsum,amma kowa a ƙauyen yana kiranta da suna ɗaya kawai: Noor — domin kamar hasken mahaifiyarta take. Mallam Audu ya ɗan numfasa, yana kallo cikin idon Bashir,muryarsa ta yi sanyi kamar ana furta sirrin da rai ke so ya ɓoye. “Ga yarinyar nan a gabanka, ita ce amanar da Noor ta bar maka kuma ita ce ‘yar Noor. Ka sani, tunda Noor ta haifi wannan yarinya, Suhayl ya bar ƙauyen nan.. Ya ce zai dawo, amma har yau bai sake komawa gun yarinyar sa ba, shekaru na tafiya, lokaci yana shanye mutane, amma har yanzu ana jira.”Ya ɗago da idanu, yana kallon sama kamar yana magana da wata ƙaƙƙarfan zuciya da ta daɗe tana ƙuna. “Wannan shi ne abinda nake so ka sani, Bashir Amma har yanzu akwai wasu abubuwa da na ajiye, ajiyar mahaifiyarka, da kuma ajiyar Noor tana da imani cewa wata rana, kai ne zaka dawo gida ka karɓi amanar nan da hannunka.” Ya yi shiru, ya kalli Noor ƙarama wacce ke tsaye a gefe, idonta yana cike da hawaye amma tana murmushi, kamar zuciyarta ta gane cewa labarin da aka ɗauki shekaru ana jira ya kai ƙarshe. ##$$$$$$$$$$$$$$$##### A gurguje suka shiga wanka, ruwa mai ɗumi yana zuba musu jin daɗin jiki. Sun shirya cikin abaya irin ta alfarma, mai launin koren zinariya da ja mai haske, an yi ado da ƙyallen ƙasa mai tsada, turare mai ƙamshi na musamman wanda har kewayen gidan ya cika da shi. Hannuwansu da wuya an yi musu ado da ƙaramin zinariya da lu’u-lu’u, fuskar su kuma tana haskakawa da hasken soyayya da farin ciki. Da sauri suka fito daga gidan, Raizah ta ɗauki kakar akwati guda ɗaya mai daraja, Rayyan kuma ya lumshe ido yana jin dumin zuciyarsa. Sun shiga mota, direban ya danna gaba, ba tare da bata lokaci ba suka tashi kai tsaye airport na Dubai. A cikin mota, hasken safe ya cika su da kwarin gwiwa, zuciyoyin su cike da bege da shauki. Duk wani damuwa ya narke, yanzu rayuwa ta fara musu sabon babi mai cike da walwala da alfarma. Daddy ya yi murmushi, ido cike da fahimta, ya ce “Daddy, mun makara ne… we are sorry.” Rayyan da Raizah suka yi ƙanƙantar murmushi, suna jin sauƙin zuciya saboda Daddy ya fahimce su nan suka shiga jirgi, kowanne na ɗauke da raƙuman tunani da shauki, yayin da jirgin ke tashi daga Dubai zuwa Nigeria, Abuja. A cikin jirgin, kowane fuska na cike da tsammani da bege, Raizah na kallon Rayyan da wani ɗan murmushi mai taɓa zuciya, yayin da Rayyan yake duba fuskar Raizah cikin shauki. Yanayi na cike da ɗan tsoro amma kuma natsuwa.... A hankali Mallam Audu ya miƙa sandar hannunsa ga Bashir, idanunsa suka kada da hawaye.Bashir kuwa yana kallo little Noor, wacce ta riƙe hannun Mommy tana shiru, kamar zuciyarta na fahimtar nauyin da ke faruwa Duk suka tsaya cikin natsuwa, ƙarar hucin iska kawai ake ji sai Mallam Audu ya zaro wata tsohuwar tsunma daga ƙarƙashin katifa. Tsumar ta yi duhu saboda tsawon lokaci, amma ana buɗewa sai kamshin turaren da ya tsufa ya cika ɗakin “Wannan ajiyar mamanka ce,”ya ce da muryar da ke rawa. “Wannan ganye da wannan leda... da takaddar Noor — ita ta ce in ba shi idan ya dawo... idan Kadangaren Bakin Tulu ya dawo gida.” Bashir ya karɓa da hannunsa, zuciyarsa na tsinkewa kamar ana sare masa numfashi. Ya buɗe tsumma ɗaya bayan ɗaya… Sai zoben zinare ya bayyana — zoben da aka rubuta ƙarami a ciki “ Ummukulchum.” sai kuma hoto guda biyu da aka haɗa cikin takarda mai launin rawaya saboda tsufa. Ya ɗaga hoton farko... Sai Mommy ta sake numfashi da ƙarfi, Daddy ya tsaya cak, Sagir da Muhsin suka kalli juna, idanunsu suka cika da tsoro. “Innalillahi...” kawai aka ji ana furtawa a hankali. Bashir yana kallon hoton — idonsa ya faɗa, jikin sa ya ɗauki rawa “Wannan... wannan kuwa...?” Sai kawai ledar ta zame daga hannunsa ta faɗi ƙasa, hoton na biyu ya zame daga ciki... sai iska ta kaɗa shi a hankali zuwa ƙasan ƙafarsa ya durƙusa yana ɗauka, idanunsa na rawa kamar mai jin kiran da ya ɓace shekaru aru-aru........ A take Mommy ta firgita, hannunta ya saki wayar da ke riƙe da ita, jiki ya yanke mata — ta fadi ƙasa “Mommy!!” Khady ta kurma ihu tana rarrafe zuwa gare ta, Daddy ya durƙusa yana riƙe ta da rawar hannaye, Bashir kuwa ya tsaya tamkar an soke shi da wuka a ƙirji. A zuba mata ruwa cikin tashin hankali, sai ta ɗan motsa, ta buɗe idanu cikin hawaye masu zafi. A hankali ta miƙa hannu ta karɓi hoton daga hannun Bashir, ta dade tana kallonsa kamar wacce ke tafiya cikin wani lokaci daban. Hawayenta suka zubo a hankali, suna sauka bisa fuskarta kamar ruwan sama mai ɗumi. Idanunta suka yi haske kamar tauraruwa daga sama, zuciyarta ta kasa ɗaukar nauyin abin da take gani ta furta cikin murya mai sanyi, tana shafa hoton da yatsunta “Subhanallah... wannan hoton... wannan fuskar... ita ce... ita ce Ummu Kulsum.” A take aka tsaya shiru — iska kawai ake ji tana kaɗawa ta taga. FLASHBACK 🌙 Bakin dare ne — dare mai tsanani da duhu, kamar sararin samaniya ya ɗaure da damuwa. Iskar sanyi na busowa a hankali tana rawar da labulen window ɗin da ke gefe. A cikin ɗaki kuwa, ana iya jin ƙarar ƙaramar fitila mai launin zinariya tana ɗaukar ido da walƙiya mai sanyi. Ɗakin kuwa cike yake da ƙamshi da tsafta. Katifar gadon farin zane ce, an shimfiɗa ta cikin tsari kamar ɗakin ‘ya mace mai kula da kai. A kan gadon, yara biyu ne kwance — ba ƙananan yara ba, ɗaya ‘yar shekara ashirin (20) ce, ɗaya kuma tana da shekara goma sha biyar (15) Dukansu cikin kayan bacci ne masu launin ruwan hoda da fari, fuskar su cike da natsuwa da kwanciyar hankali. ‘Yar babba tana kwance da littafi a gefenta, alamar ta dade tana karantawa kafin bacci ya ɗauke ta Kanwarta kuwa ta rungume teddy bear tana baccin zuciya kamar wata ƙarama da bata san komai ba game da abin da ke shirin faruwa. A hankali wata ta sauko ta haska gefen gadon, hasken nata yana bugawa kai tsaye kan fuskokin su — haske mai kama da annuri. Wani abu mai nauyi a sararin dare, kamar iska ta ɗauke numfashi na wani abu da ke shirin ɓullo wa cikin rayuwarsuDaren da zai zama farkon wata sabuwar rayuwa. Sautin bindiga ya fashe cikin dakin malam, ya girgiza duk gidan. Ummu Kulsum ta tashi cikin tsoro, ta kame hannun Maryam, amma kafin su yi wani abu, an ja su cikin sauri — sai dai yaran sun riga sun ɓuya a wajen babban parlour, a bayan wani ɗaki mai zurfi; suna tsare numfashi, idonsu na zurfi suna kalle abinda ke faruwa kamar an dake musu duniya. Mutanen baki sun faɗo cikin gidan kamar hadari; sun shiga cikin sauri, suna nufi babban tebur. Sun rufe kofa da sauri, suka tilasta iyayen su zauna a wajen parlour, an murƙushe su a wani wuri domin kada su iya motsi — amma yaran suna tsaye ɓoye, suna ganin komai cikin firgigiya da azaba. Shugaban waɗannan bakaken ya buɗe jakar fata ya zaro wasu takardu. Ya juya ya kalli mahaifin gidan da muryar ƙarfin zuciya: “Ko ka kawo mana files ɗin? Ka sani — ko da ba mu samu ba, za mu iya ƙaddamar da hukuncin nan — mu kashe iyalanka a nan.” Kalmar ta fadi kamar wuta a cikin dakin. Ummu Kulsum ta yi ƙoƙarin tsawata, amma an hana ta magana; hawaye sun toshe mata makogwaro. Maryam ta rufe bakin ta da hannunta, zuciyarta na buga kamar za ta fashe. A ɓoye, Ummu Kulsum da Maryam suka matso kusa da juna, hannayensu na rike da tsananin tsoro. Sun ji dukkan kalmomin, sun ga fuskar mugunta a bakin waɗanda suka shigo — fuskar da ba za su taɓa manta ba. A gefen duniya kuma sun yi maganganu game da Alhaji Abubakar Imam — shahararren ɗan kasuwa, tsohon gwamna sau biyu, an yi masa fashi da darar miliyoyi a sansanin gidansa a unguwa mai tsada. Amma a nan, abinda ke zamewa shi ne tambaya: menene a cikin waɗannan files? Kuma shin waɗannan masu fashi suna neman su ne, ko suna amfani da takardun ne don yin barazana? Dakin ya nutse da shiru, sai kawai ƙarar zuciyar yaran da ke ɓoye — numfashinsu na rawa, idanunsu na cike da girgiza. Sannan shugaban ya yi murmushi mai sanyi, ya sake duba takardun kamar wanda zai yi hukunci. Sautin bindiga ya fashe cikin dakin kamar guguwa — ya tashe su daga bacci, ya katse duk wani natsuwa. Ummu Kulsum ta ja kanwarta Maryam cikin ƙirjinta kamar zata ɓoye ta gaba ɗaya; idanunta sun cika da tsoro, muryarsu na yin ihu suna kiran “Mom! Dad!” cikin rawar murya da firgici. Ba da jimawa ba sai wasu mutane cikin bakaken kaya suka bullo cikin ƙofar gidan, fuskar su ƙara duhu a karkashin hulun fata. Sun zo da bindigogi a hannu, suna yawo kamar waɗanda ba su zo neman wasa ba. Wani babban mutum ne yake gaba — murya mai sanyi, ido kamar ƙanƙarar dutse. Ba su tsaya ba; cikin sauri suka kewaye babban parlour. A baya, a ɓoye, Ummu Kulsum da Maryam sun buya cikin ɓangaren da aka ɓoye — suna matsa juna, numfashinsu ya rage, idonsu na duba komai cikin tsoro. Sun ga yadda aka tilasta iyayensu su zauna, an murɗe su a gefe; sun ga yadda mugun nufi ya mamaye gidan. Shugaban ’yan bakin ya ɗago jakar fata, ya buɗe ta da hannu mai kauri. Ya ja takardu, ya nufi mahaifin gidan da talabijin-like stare, ya furta a hankali da murya mai ɓaci: “Ka kawo waɗannan files — ko mu kashe iyalanka a nan.” A gefe guda kuma, suna magana da murya ta ƙasa kamar suna tunanin wani abu mafi girma: labarin Alhaji Abubakar Imam — shahararren attajiri da tsohon gwamna wanda aka ajiye masa asiri, wanda ma an sace masa daruruwan miliyoyi a gandun sa na Kano. Amma a nan, a tsakiyar wannan gida, tambayar ita ce: menene waɗannan files ɗin? Shin sun shafi wannan sunan babban mutum ne, ko kuwa wani abu ne da zai tarwatsa rayuka? Dakin ya nutse da shiru mai nauyi, sai kawai ƙarar rawar tufafi da ƙasa ta zama kamar waƙar tsanani Ummu Kulsum da Maryam sun rike juna, idanunsu a bude, suna kallon waɗanda suka zo — ba su da abin yi amma tsinkayar cewa wannan dare zai canza musu komai. Sautin bindiga ya tarwatsa dakin kamar guguwa; duhun dare ya cika da karar ihu. Ummu Kulsum ta riƙe ƙananan hannayenta, ta matso kusa da Maryam cikin rawar murya: “Ki ɓoye, ki yi shiru… ki rike wannan.” Da ƙarfi Maryam ta ɗauki takarda ta lulluɓe a cikin jakar da Daddy ta ya bata amanar da ba za a sake mika ba, Maryam ta jefar da kanwarta cikin ɓangaren da aka ɓoye, ta murɗe baki da hannu kamar wanda zuciyarsa ke ƙara bugawa , suka shigo — bakaken kaya, fuska ƙasar duhu, bindigogi a hannu. Sun murɗe iyayen gidan cikin babban parlour, suka ja su suka sa su zauna, anan suka kama Maryam A cikin rudanin, ana jin ƙarar ƙudan harbi. An ji ƙarar faɗuwar jiki — mahaifiyarsu ta sauka ta faɗi, jini ya yi jaƙaƙƙe a ƙasa , Alhaji Abubakar, wanda yabaiwa Maryam files, kuma ya ɓoye ta ya tsaya a sandare — idonsa sun yi girgiza. Ya fahimci masifar da ya haifar: matar gidan a ƙasa, yarinya a rauni, gidan ya cika da jini, shima aka kashe shi suka bar gidan inda aka harbi Maryam a ƙafarta Ummu Kulsum — ƙuruciya, amma cike da ƙarfin rai ta zagaye jakar a bayan ta lumshe ido, ta ɗauke su da hannayenta masu rawa. Da ƙarfi ta ƙasƙance ƙofa da ƙananan ƙafafunta, ta tsere cikin duhu, tareda amana a hannunta — takardun da za su iya ceton ko lalata rayuka. Daren ya tsinke da ƙarar gudu. Gidan ya rage cikin ihu da jini; a zuciyar Ummu, akwai tsoro, akwai fatan ceto — kuma akwai nauyin amanar da ta ɗauka. SAFIYA Aka fito da tashin zuciya: an harbi mahaifiyar su — an kashe Mom ɗin. An harbi Maryam ma; sai dai da sa’a an kai ta asibiti, an samu ta raye amma cikin rauni mai tsanani Da safe, ’yan sanda suka kewaye gidan. An samu gawarwaki a gidan; an ceto Maryam, amma Ummu Kulsum ba a same ta ba — ta ɓace. Sakamakon girman sunan Alhaji Abubakar da matsin da ke akwai, an rufe case ɗin Alhaji Abubakar Imam har abada; an rasa gano Ummu Kulsum har abada. A asibiti, Maryam ta faɗi cewa ƙanwar ta ta ɓoye kuma ta ajiye takardun. Wannan ne ya sa Bashir (ko wadanda suke son adalci) suka yi muradin bi da bincike — amma a halin yanzu, Ummu Kulsum ta ɓace, kuma masifar dare ta bar ƙwaƙwalwar mutane da zafi da kuka. Wannan ɓangaren naki mai zurfin taɓa zuciya ne sosai, Sayeeda 🤍. Ga yadda aka ƙawata shi cikin salo mai ɗaukar hankali, amma babu ƙarin labari — daidai da abin da kika rubuta: --- A haka rayuwa ta ci gaba cikin zafi da ciwo. Maryam, bayan wancan masifar dare, ta rayu ƙarƙashin kulawar ɗan uwan mahaifinta. Duk da tsoron da ke damunta da kullum, ta dage ta kammala makaranta cikin nasara. Rayuwa ta yi mata nauyi, amma ta ƙi yin kasa a gwiwa. Daga baya ta yi aure, ta haifi yara uku: Sagir, Muhsin da Khady — waɗanda suka zama tamkar hasken da ya rage a duhun rayuwarta. Sai dai a cikin zuciyarta kullum akwai rami, ramin da sunan sa Ummul Kulthum ne. A gefe guda, Ummul Kulthum kuwa ta ci gaba da gudu, tana tserewa da ƙarfin hali, tana neman tsira daga duniyar da ta fi ƙarfin fahimta. A ƙarshe ta isa ƙauyen Rimi, inda ta haɗu da wani makaho — mutum mai salo da tausayi, wanda ya ɗan kama da mahaifinta. Ta girmama shi fiye da yadda take girmama kanta. Shekaru suka ja, zuciya ta fara mantawa da tsohon rayuwa, har ta manta wacece ita a asali. Cikin wannan sabon rayuwa, ta zama matar Mallam Audu, kuma ta haifi ɗa guda ɗaya — Bashir. Sai dai kaddara ta yi mata dariya — kafin ta san komai, ta bar duniya ta bar shi cikin rayuwar da ta rasa asali, ta bar sirrin da duniya ba ta taɓa fahimta ba. BACK TO STORY Shiru ne ya lullube ɗakin tamkar an dakatar da numfashi. Kowa ya kasa magana, sai kukan da ke tashi a hankali — kuka mai ɗaci, mai cike da jin tausayin lokaci da ɓacin ƙaddara. Mommy ta dafa hoton da hannunta yana rawa, hawaye na gangarowa kamar ruwan sama. Ta ɗago da murya mai sanyi amma cike da raɗaɗi “Ashe ba a banza ba na ɗauke Bashir tamkar ɗana. Ashe yaron ƙanwata ne — Allah sarki! duk matsayinmu, duk kuɗinmu, ashe ke ce, Ummul Kulthum, kika sha wahala a ƙauye kina ɗauke da amanar da muka rasa. Kin riƙe sirrin da ya sa rayuka suka salwanta... Amma kin kasance mai gaskiya har ƙarshe.” Ta share hawayenta da rawar hannu, ta ɗora da cewa “Kai kuma, Audu, yanzu ka ga sakamakon zunubinka ka kashe mace mai imani, ka ɗora marainin Allah cikin wulakanci. amma Allah ya fi hukunta fiye da kowa — yau sakayyar ka ta dawo, tun ba a ji ko ina ba.” Bashir kuwa ya durƙusa a jikinta yana kuka mai girgiza zuciya. Kukan da yake yi ba na rauni ba ne — kuka ne na ganin ƙaddarar da ta zagaye shi da soyayya da asara, kuka na farin ciki da ciwo a lokaci guda. Sagir da Muhsin suka tsaya a gefe, hawaye na tsiyaya a fuskokinsu. Daddy ya kalli dukkansu da idanu masu cike da natsuwa da hikima, sannan ya ce a hankali: “Allah Mai komai da kowa ne. Ku sani, mu duka an rubuta mu cikin littafin ƙaddara ɗaya. Ashe, jini jini ne. Duk abinda Allah Ya tsara shine mafi alkhairi a yau, mun ga amfanin taimakon wanda bashi da komai. Mun ga cewa wahala bata hana arziki, kuma asiri baya bacewa sai da lokacinsa.” Mommy ta rungume Bashir, su Sagir suka durƙusa kusa, suna jin tamkar duniya ta tsaya. Kowa ya yi shiru yana sauraron ƙarar zuciyarsa da ke bugawa cikin sautin kalmar da Daddy ya faɗa: “Alhamdulillah.” ###$$$$$$### Rayyan ya kalle ta — zuciyarsa ta gama tafasa, amma yanzu ta huce cikin nutsuwar wanda ya fahimci cewa zunubi baya buya, kuma Allah baya mantawa. A hankali ya furta cikin muryar da ke rawa saboda ƙoƙarin da zuciyarsa ke yi ta tsayar da hawaye “Aunty… na yafe miki. Duk da abinda kika min, da irin ciwon da kika jefa ni a ciki, na yafe miki har gaban Allah. Ba don kin cancanta ba, amma don zuciyata ta huta daga ɗaukar ƙiyayya.” Shiru ya biyo bayan maganarsa — sai ƙarar numfashinta da ke sauka da sauri kamar mai wahalar shan iska. Kallon ta ya zama tamkar kallon wacce ta rasa komai — hankali, nutsuwa, da rai cikin rawar murya ta fara dariya — dariyar hauka mai cike da tsoro da jin haushi “Hahaha! bana son ka yafe min, Rayyan! Ka ji na faɗa? Bana son ka yafe min!” Ta fashe da dariya tana girgiza kanta, idonta na cike da hawaye da tsoron mutuwa “na tsaneka! ka ji na ce? na tsaneka har abada! ka jawo min haske a cikin duhu, kai ne ka lalata sirrina Na yarda da bokana! na bi shi! na kashe uwar ka! Na nemi kashe ka! Amma Allah ya bar ni da rai don in ga wace irin azaba zata biyo ni to, bana son ka yafe min! Na fi son na tsaneka!” Tana fāɗin haka ta ci gaba da dariya tana jan numfashi cikin wahala. Rayyan ya tsaya — kallon ta kawai yake, fuskar sa babu fushi, babu tausayi. Sai murmushi mai ɗauke da jimami ya bayyana a laɓɓansa. Ya ce cikin siririn murya “Kin fi ƙarfin fushi na, Aunty amma ba za ki taɓa wuce ikon Allah ba.” Cikin wannan yanayi aka ji karar bugun zuciya mai ƙarfi — duk sai ta lulluɓe, ta zube a ƙasa, dariyarta na ƙarewa cikin shiru mai firgitarwa. Rayyan ya rufe idonsa, yana faɗin da sanyi: “Allah ne Mai hukunci. Ina maka aminci, ya Ubangiji.” Sai iska ta buso ta window, ta jawo labulen ɗakin, kamar alamun ƙarshen mugunta, da farkon shiru mai ɗauke da rahama. “INA ABDUL NA?” Kallon Aunty ɗin ya tsaya — idonsa ya cika da hawayen da yake ƙoƙarin dannewa a hankali, muryarsa ta fito cikin rauni, kamar ƙaramin yaro da ke neman abin da yafi ƙarfin tunaninsa “ko dawo min da Abdul yaro na... Ina shi Abdul ɗin na?” Cikin ɗan lokaci parlour ɗin ya cika da shiru sai ƙarar ajiyar zuciya kawai da murya mai sanyi ta Aunty ta biyo baya, tana maimaita kalmomin da ke karyar da zuciya: “Abdul... Abdul ɗin na?”ta fara kuka, ta kalli ƙasa, tana girgiza kai. “Rayyan... Abdul ɗin nan yanzu yana prison. Tun ranar da ya kwashe min Million goma ya gudu, ban sake kallon sa ba. Na sanar da hukuma, suka kama shi a Abuja... a wani gidan da ake aikata batsa da lalata. Na ce su rufe shi, ba ruwana dashi...” Ta dafa kirjinta, muryarta na rawa da nadama. “To ashe bayan ya fito bai koma gida ba. ya lalace, ya zama marar natsuwa, har wata rana ya yi fada da abokin sa — ko wata karuwa ce tsakaninsu, ba na sani ba sai ya kashe shi! Rayyan... yanzu za su masa ɗaurin rai da rai...” Gaban Rayyan ya fadi, kalmomi suka makale a maƙogwaron sa numfashinsa ya yi nauyi, hawaye suka gangaro da ƙarfi. “Abdul... ɗan’uwan da na tashi dashi, wanda aka zarge ni dashi, yanzu kuma... shi ma ya zama fassarar ƙaddarar mu?” Aunty ta durƙusa tana kuka, tana kiran sunan Abdul kamar mai neman gafara daga sama: “Ya Allah! Na lalata rayuwata, na lalata rayuwar ‘ya’yana! Abdul... na yi maka laifi, na jarabci duniya, na rasa komai!” Rayyan ya kalli sama, yana furta da murya mai nauyi da tausayi “Duniya... dukkan zunubi yana dawowa gida.” Sai shiru ya sake ratsa falon — kowa cikin tunani, cikin nadama, cikin natsuwar da bata da kalma. Rabon da suyi shiru irin wannan, tun ranar da aka fara rubuta ƙaddararsu. ZIYARA ZUWA PRISON Suka iso gidan kurkuku, ginin dutse mai sanyi yana ɗauke da inuwa kamar zuciya mai nauyi. Hasken rana ya ratsa taga, amma cikin ɗakin ziyara akwai inuwa — sautin ƙarar kafa, murushin jami’an tsaro, da ƙanƙanin ƙarar gilashi suna cika sararin. Rayyan ya tsaya a bakin gilashin, zuciyarsa ta fara bugawa cikin sauri. A gefe, Daddy da Uncle sun tsaya daidai — fuskar su cike da hadima da tsoro. An kira sunansu; an ja su zuwa inda ake bari sai su ga wanda suke nema. Abdul ya tsaya a ɗakin gefe, bayansa a bayyane a cikin wando mai launin ƙurciƙe. Idonsa sun yi jaƙeƙe, fuskar sa a ɓangaren da take nuna shekaru da wahala. Yayin da suka zo kusa, sai ga shi ya ɗaga hannu ya danna tafin hannunsa a kan gilashi, kamar yana ƙoƙarin shaƙe numfashi daga wajen da ba zai iya shiga ba. Da su gani, sai ya miƙe daga can gefen gilashi, ya fasa murmushi mai rauni. Muryarsa ta fito daga ƙarfin ƙanƙani amma babu ƙarfi: “Rayyan ɗan uwana… ka zo ka ga ni ne " ? "Kai ne… ka zama haka — haske ranar wata a gare ni. Ni kuwa na zama bakar rana. Wannan ne makomata.” Kalamansa sun makale a kunne, kamar wanda ya jefa kansa cikin toka idon Rayyan ya ƙara jaƙeƙe; zuciyarsa ta cika da tsanani. Abdul ya ci gaba, ya juya fuska cikin nadama: “Na bi mata, na bi zumunta, na manta addini, nayi sacce sacce Aka kama ni a Abuja a gidan lalata. Na sha rashin kunya, na sha tako daga ƙarshe nayi kisan kai Gobe za su yanke min hukuncin kisa… Rayyan, ya Allah! Ka roƙo, ka yi addu’a mini, ka yi min yafiya…” sai ya sunkuya ya rufe fuska da hannaye, ƙarar muryarsa ta fado “Ina nadama… ina neman gafara. na tuba — ina neman Ubangiji ya yafe min. Rayyan ka yafe mini ko gaya mini cewa akwai wata hanya, ko gaya mini cewa ba ƙarshen rayuwa bane.” Rayyan ya tsaya da ƙarfi a gefen gilashin, hawaye suka fara taruwa a idanunsa bai iya magana ba nan da nan; zuciyarsa ta narke, amma a cikin ranta akwai ƙurar tambaya da zafi: yadda rayuwa ta jujjuya haka, yadda ɗan’uwan su ya sauya zuwa wannan hali. Jami’an tsaro sun tsaya a gefe, idanuwansu na kula da kowane motsi. Gilashin ya zama shinge tsakanin zuci-zuciya biyu — ɗayan cikin nadama da hukuncin duniya, ɗayan cikin ƙauna da gajiya. Abdul ya ɗaga kai, idanunsa cike da hawaye amma akwai karfin fata a cikin su: “Na san babu yadda zan mayar da abin da na yi. Amma ina son ku sani… na yi nadama, ina neman gafara. Idan za ku iya, ku yi addu’a. Ku yi addu’a gare ni in samu rahama kafin gobe.” Rayyan ya yi kallo na dogon lokaci, sai ya girgiza kai a hankali sannan ya furta cikin murya mai rauni: “Zan yi addu’a… Amma ka sani, gaskiya ba ta ɓacewa — dole ka fuskanta. Zan tsaya tare da ita.” A ƙarshe suka bar wurin, hawaye na cikawa amma akwai wani irin nutsuwa a zuciyoyi — ba farin ciki ba, amma nau’in sulhu da hadin rakiyar ɗan’uwan da ya ɓace. A baya, ƙaramin ɗakin ziyara ya zama shaida: a can an ga yadda rayuka suka haɗu da jahilci, girman zunubi, da kuma ƙananan hasken fata. To be continued ####$$$$$$$$$$####### duba suka isa, kai tsaye suka nufi gidan Daddy Rayyan, duk yanayin gidan na cike da alfarma da kyawawan kayan ado. Rayyan ya shiga cikin shirin ganin Aunty Zulaihat, zuciyarsa na buga cike da ɗan tsoro da bege, domin tun lokacin da uncle nasa ya ɗauke shi, bai taɓa sake zuwa ba. Yayin da suka shiga zauren gida, Daddy Rayyan ya tsaya kallon yaron sa, idonsa cike da mamaki da farin ciki, ba tare da sanin Hajiya Zulaihat ba. Rayyan ya yi ƙanƙantar murmushi, ya ce: “Daddy, ina Aunty Zulaihat?” Daddy ya yi dariya mai laushi, idanuwansa cike da sirri, ya ce: “Mu je ka ganta…” Nan sai zuciyar Rayyan ta tsalle da sauri, amma a gefe guda, wani abu mai nauyi da ban mamaki yana jiran su a ciki, wanda ya sa duniya ta tsaya cak na ɗan lokaci… Rayyan ya tsaya a window, zuciyarsa na bugawa da sauri. Ya ji muryar wani sirri mai nauyi cikin kansa, yana ƙoƙarin shawo kan tsoron da ya cika zuciyarsa. Amma nan ya tsayar da kansa, yace: “Bazai yiwu mu shiga ciki ba….” A hankali ya bude window, ido na lale a hankali, zuciyarsa na rawa da firgici. Sai ya hango dukuniyar kayan ta—duka sun yagi a ɗakin, babu komai mai tsari. Amma abin da ya fi daukar hankali shi ne takiyin da gaske: suna da cizon jiki, ƙuraje da munanan alamun azaba, har da ɗan wari mai ƙarfi da ya ratsa hancin sa. Rayyan ya ɗauki numfashi mai nauyi, zuciyarsa na cika da ƙunci da tsoro, yana tunanin irin azabar da aka yi mata. Duk da haka, wani ƙaramin zuciyar ƙarfin hali ya fara bayyana a cikin sa, yana cewa: “Wannan ba zai karya mu ba… amma dole mu san gaskiya.” Nan zuciyar sa ta yi rawar firgici da bege a lokaci guda, yayin da aka shafi sirrin da zai iya sauya komai a labarin su. Tana hango sa ta cikin window, idonta ya firfito kamar mai hauka, tana daga hannu tana ihu da murya mai cike da ƙiyayya da hauka: “Gashi nan! Gashi nan ka tarwatsa min komai! Ni ne na kashe uwar ka! Na bi boka don in kashe ka! Amma boka ya ce kai ƙadangaren bakin tulu ne! Na rufe bakin kowa domin kada su faɗi gaskiyar da take damuna! Na tsaneka, Rayyan! Na tsaneka!!” Tana faɗin haka tana dariya mai taushi amma cike da mugunta, tana juya jikinta kamar mai shaidan, tana ta rawa cikin hauka da azaba. Uncle ya tsaya cak, jikinsa ya yi sanyi kamar an tsoma shi cikin kankara. Sai kawai ya furta cikin murya mai raɗa: “Sakkayar Ubangiji kenan... kin rina jinin ‘yan uwa! Kin kashe rai ba ɗaya ba, har biyu! Ga bin mallaman tsibo da bokaye! Subhanallah, wannan haukan zunubi ne!” Rayyan kuwa ya durƙusa ƙasa, hannunsa biyu kan ƙirji, yana maimaita cikin rawar murya: “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un... Innalillahi wa inna ilaihi raji’un…” Idonsa ya cika da hawaye, zuciyarsa na rawar firgici da tausayi, yana kallon wacce ta zama uwar zunubi da uwar bala’i, wacce a da ta kira Aunty Zulaihat. #$$$##############$$#$$$$$$$$ Mommy ta rungume Bashir ƙam kamar tana son shigar sa cikin zuciyarta. Su Sagir kuwa suka durƙusa kusa da su, idanunsu cike da hawaye, zuciyoyinsu na bugawa cikin sautin muryar Daddy da ya faɗa cikin nutsuwa: “Alhamdulillah.” Sai a wannan lokacin aka ji ƙaramar murya mai sanyi amma cike da raɗaɗin zunubi — Baaba ce. Ta zauna jingine, yawun bakinta yana zuba, ƙudaje na yawo a gefenta. Hannunta na karkarwa, idonta a cike da nadama ta yi ƙoƙarin miƙewa, amma ƙarfinta ya ƙare ta jarkace kai, ta dafa ƙirjinta sannan ta furta da murya mai sarkewa: “Laifina ne… ni na azabtar da ita… Ni na so kashe Bashir tun a cikin mahaifiyar sa. Amma ya kasance ƙadangare a bakin tulu — na kasa kashe shi na yi masa asiri, na tsine masa, na sa mahaifinsa ya kore shi daga gida. Amma Allah ya dawo da shi da ɗaukaka da girmansa, kamar yadda mahaifiyarsa ta yi haske a duniya gashi yanzu, Allah ya jarrabe ni da muguwar cuta sanadin mummunan aikina…” Bashir ya miƙe a hankali, hawaye na gangarowa daga idanunsa zuwa gefen fuska. Ya matsa kusa da Baaba, ya durƙusa har sai ya kai hannu ya riƙe nata dukan mutane suka kalle shi, wasu cikin mamaki, wasu kuma cikin tausayin zuciya. Ya ɗaga kansa sama, yana magana da murya mai sanyi, amma cike da ƙarfin imani: “Allah ne mai gafara shi ne ya fi kowa sanin zuciyar bawa. Idan har ya yafe min zunubaina, ni ma zan yafe. Baaba… na yafe miki na yafe ma duk wanda ya taɓa zaluntata, saboda yau na fahimci komai ƙaddara ce — kuma cikin ƙaddara akwai alheri.” Mommy ta share hawayenta, tana kallon sa da murmushi mai ɗanɗanon kuka. Daddy ya daga hannunsa sama, ya faɗa da murya mai ƙarfi: “Tabbas wannan rana ce ta yafiya, ta jinkai, ta komawa ga Allah mun gane darasin rayuwa — cewa taimakon wanda ba shi da ƙarfi yana iya zama hanyar samun falala daga Ubangiji.” Khady ta riƙe hannun Mommy tana shessheƙa duk gidan ya cika da nutsuwa, sai iska mai sanyi ta ratsa su kamar sakon rahama daga sama. Wannan shine Babin Yafiya — inda zuciya ta natsu, ran da ake shayar da zunubi da hawayen nadama, kuma a cikin hasken gafara, duk wata duhuwa ta ƙare. Khady ta matso da jaka a hannunta, idonta na cike da wani nauyi amma da fatan rai ta miƙa jakar a hankali ga Bashir, tana cewa cikin rauni “Ga abin da Noor ta ajiye—wannan jakar ajiyerinta ce ka karɓa, " Bashir ya ɗauki jakar da hannu mai rawa. Ya bude ta a hankali; a ciki akwai ƙananan abubuwa ne — zobe na zinariya, wata ƙanana hoton Ummu Kulsum da Noor a lokacin farin ciki, mayafi, da wata wasiƙa mai tsufa wadda aka rubuta da kalaman soyayya da alƙawari. Idon Bashir ya yi jaƙeƙe, tare da goyon da da SUHAYL hawaye suka taru a gefensa , A hankali ya dora jakar a gabansa, ya miƙa hannu ya riƙe hannun NOOR murya tasa ta zamo mai laushi “Na gode… Na alƙawarta zan kula da wannan amanar. Ba zan bari ta ɓace ba.” Sagir ya leka da idanu, ya gyada kai, sai ya ce: “Safiyar gobe za a turo mota. Za mu kwashe ku zuwa asibiti da zarar an shirya — mu ga yanayin jikin nasu , mu tabbatar da cewa kun samu taimako, sannan mu tsara gaba. Ai muna jiran abin da zai fito daga takardun nan.” Bashir ya saki numfashi mai nauyi, ya dage da cewa: “To, mu huta yanzu. Gobe ne za mu tashi da karfin zuciya. Wannan amanar Noor, za ta kasance a hannun mu " Kowa ya yi shiru, sai ƙanƙanin numfashi da hawaye sun cika ɗakin. Amma a zuciyarsu akwai sabon fata: safiyar gobe zata kawo tafiyar da za ta tafi da su zuwa asibiti, kuma wata rana zuwa ga gaskiyar da ke cikin waɗannan takardu. Washegari da safe, garin Rimi ya farka cikin wani irin motsi da bai saba gani ba. Hasken safiya na fitowa a hankali daga gabas, amma a cikin gidan tsohon Mallam Audu, duhu da natsuwa suka lullube komai. Mommy, Daddy, Sagir da Khady duk sun shirya tare da Bashir, suna ƙoƙarin lallasar tsohon nan da Baaba su tashi su biyo su zuwa birni don a kula da su a asibiti. Amma Mallam Audu ya girgiza kai cikin rawar murya, yana cewa: “Ba inda zamu tafi mun isa nan, mun gama. ku bar mu mu mutu cikin tunanin rayuwar mu. Abin da muka shuka, shi muka girba…” Baaba ta yi dariyar ta cikin tsoro, wadda ta fi kuka ciwo. Ta ce da karfin hali amma muryarta na rawa: “Ku bar mu nan ku tafi da kuɗin ku da mulkinku na tabbata abin da muka aikata a baya, mu ne zamu ɗauki ɗanƙon sa. Rayuwa ta ishe ni, amma ku ku cigaba. Allah ya yafe muku, ku yafe mana.” Bashir ya tsaya kallonsu, hawaye na sauka a hankali daga idonsa. Bai ce komai ba sai kawai ya durƙusa gaban su. A cikin ransa yana jin nauyin alheri da tausayin da suka cakuda. Bayan ficewar su, ya tsaya a tsakiyar ƙauyen Rimi, mutane suka taru suna kallon sa. Sai murya tasa ta ɗauka cikin nutsuwa amma da ƙarfi, kamar muryar jagora daga sama: “Ba zan bar wannan ƙauye cikin duhu ba. wuri ne da mahaifiyata ta zauna, da ni na taso cikin wahala zan mayar da wannan ƙauye gida mai alfahari. Za a sake shi, za a sabunta shi.” A nan ya umarci Sagir da Muhsin da su kira injiniyoyi daga Kaduna da Abuja. A cikin kwanaki kaɗan, manyan motoci suka shigo ƙauyen — da injuna, da kayan aikin gine-gine, da manyan injiniyoyi da ma’aikata. Tsoffin gine-ginen da suka yi dutse suka rushe, sabbin gine-gine suka fara tashi. Aka zuba ruwa a rijiyoyi, aka gina makarantar firamare da sakandare, aka kafa cibiyar lafiya, har ma aka shimfiɗa layin wutar lantarki. Mutanen ƙauye suka kasa boye farin ciki. Wani dattijo ya durƙusa yana kuka yana cewa: “Tun asalin ƙauyen nan, ba mu taba ganin irin haka ba. Wani jini ne da Allah ya aiko mana daga sama.” Bashir ya tsaya a bakin titi, yana kallon sabuwar al’umma da ke farawa daga ƙasa. Mommy ta matsa kusa da shi tana murmushi, ta ce: “Gaskiya kana da zuciyar jagora. Kamar yadda mahaifiyarka ta yi mafarkin taimakon jama’a — yau kai ka cika ta da hannunka.” ya kalli sararin sama, ya ɗaga hannunsa da tawali’u “Ba saboda ni ba don su ne — waɗanda suka yi rayuwa cikin duhu amma suka bar mana darasi wannan ƙauye, zai zama shaida ta gaskiya da ƙaddara.” A nan aka ɗora tambarin “NOOR RENEWAL PROJECT”, ƙarƙashin kulawar Hon. Bashir Ummul-Kulsum Foundation. Daga wannan rana, ƙauyen da aka manta da shi, ya zama cibiyar alheri da canji — kuma su Mallam Audu da Baaba suka rayu cikin tausayin Allah har zuwa ƙarshen numfashinsu. Shikkinan Rayuwa... ######## Rayuwa ta ja layinta — Daddy ɗin Rayyan daga baya ya sake aure. Ya samu kwanciyar hankali bayan tsawon shekaru na rikice-rikice da baƙin ciki. Rayyan kuwa, bayan mutuwar Abdul da duk abubuwan da suka faru, ya koma Dubai tare da matarsa ya zabi ya tafi nesa da komai — nesa da tsohon ciwo, nesa da tunanin baya. A can, yana kallon sararin sama a bakin teku, yana tuna irin tafiyar da suka yi daga duhu zuwa haske. "Allah ya yafe mana baki ɗaya..." Yace cikin nutsuwa, yayin da iska ke busa gashin kansa. Zuciyarsa cike da jimami, amma shiru na nutsuwa ya rufe masa rai. Rayuwar ta ci gaba, kamar yadda lokaci baya tsaya wa kowa. $$$$$$$$$ A wani bakin teku a Dubai, dare ne iskar ruwa tana kadawa a hankali wata cike yake yana haskaka fuskar Raiza da Rayyan. Kidan piano mai laushi yana tashi a baya Raiza: (ta saki murmushi tana kallon sama) Rayyan… kana ganin wannan watan? Kamar yana murmushi mana yau. Rayyan yana matsowa kusa da ita "Idan watar tana murmushi, to saboda ke. Wani haske kika zuba cikin rayuwata da ya fi kowane haske da na taɓa gani" Raiza ta ɗan sunkuyar da kai tana wasa da yatsunta "Ka manta rayuwa bata da tabbas gobe ma zata iya juya mana baya... Rayyan ya ɗago fuskarta da yatsunsa to, idan ta juya, zan sake kama hannunki. Domin ko ina take kai ni, ni dai ke nake so — ba lokacin bane, ba duniyar ba — ke ce tawa har abada. Raiza: (ta rufe idonta, hawaye masu daɗi na fita) " Rayyan… I love you fiyyeda a baya wannan so ɗin na da gaskiya, kamar addu’a." Rayyan yana rungumeta a hankali Ni ma ina son ki, Raiza. Allah ya san ban taɓa jin kwanciyar hankali irin wanda ke cikin zuciyata yanzu ba. Rayyan yana dariya, yana sumbatar goshinta Ba zan bari ki tafi ba. Wani lokaci, soyayya bata bukatar kalma — sai dai shiru da fahimta. Kuma shiru ɗin nan, shi ne muryar zuciyata zuwa taki. [ AFTER ONE YEAR Rayyan ya zauna a gaban Raiza, hannu a cikin nata, little Jiddah ta zauna a cikinsu tana dariya ƙanana, idonta na kyalli kamar tauraruwa. Raiza ta kalli Rayyan cikin shauƙi, murmushi ya bayyana a fuskarta: "Rayyan… kaga ga yadda rayuwarmu ta canza, duk wahaloli sun zama tarihi." Rayyan ya ɗago kai, ido cikin ido da ita, ya shafa kaiyar hannunta a hankali: "Raiza… kin san dai, babu wata rana da ba na tunawa da dukkan gwagwarmayar ta, amma yanzu… yanzu ina ganin mu ne cike da farin ciki kina cikin rayuwata kamar rana mai haske." Raiza ta yi murmushi, tana rungume shi da ƙarfi: "Ni ma ina son ka, har abada… kuma little Jiddah nan zata kasance alamar soyayyar mu."Little Jiddah ta miƙe hannayenta, tana ihu cikin ƙauna "Daddy… Mommy… ina son ku!" Daren ya ci gaba da lullube su cikin annashuwa, hasken fitila da taurari suna kyalli a saman, murmushi da dariya na ɗaukar wuri a cikin gidan. Rayyan ya ɗaga Raiza cikin numfashi mai tsanani, ya sumbace ta a hankali, sannan ya kalli little Jiddah: "Zamu kula da ke har abada, karamar zuciya mai daraja." Raiza ta jingina kanta a kafadarsa, idonta cikin annashuwa, zuciyarta cike da soyayya, Rayyan kuma yana jin dadin ganin iyalinsa cikin lafiya da farin ciki. Wallahi ya yi kyau ƙwarai kuma cikakke! 💫 Wannan ƙarshe ɗinki ya haɗa komai: darasi, godiya, tausayi, ƙaddara da soyayya. Ga ƴan ƙaramin gyara da zai sa rubutun ya zama kamar ƙarshe na littafi na ƙwararriyar marubuciya, ba tare da canza ma’anar ki ba 👇 --- KARSHEN LABARI Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! 🌟 Duk wahala, azaba, da rashin adalci sun zama tarihi. Yanzu rayuwa cike take da farin ciki, soyayya da kyakkyawan makoma. 🌟 Duk wani tsanani da wahalar rayuwa wata rana zai zama tamkar labari. Farin ciki baya tabbata, haka bakin ciki ma baya dawwama. Maijidda, wacce ta haifi Rayyan cikin firgici, ta sadaukar da rayuwarta domin ya rayu. Duk da cewa kishiyarta ta yi ƙoƙarin kashe shi, Allah — Mai rayarwa kuma Mai kashewa — ne ya kare shi. Daga ƙarshe Rayyan ya yi aure, ya sanya wa ‘yarsa suna Jiddatulkhair, sunan mahaifiyarsa mai daraja. Bashir, haihuwarsa cike take da tsoro da tausayi. Mugunta da rashin imani sun tura shi barin gari ba tare da ya yi ban kwana da masoyiyyarsa ta yarinta ba — wacce ta sadaukar da farin cikinta domin alkawarin dawowarsa. Amma Allah shi ne Mai tsara ƙaddara: wani baya auren matar wani, haka wata bata auren mijin da Allah bai ƙaddarta mata ba. Wannan shi ne asalin soyayya mara ƙarewa. Anan nake kawo ƙarshen wannan labari nawa, ina neman afuwarku bisa jinkirin posting da wasu ƙaramin kurakurai. Kuskuren da na aikata a sani ko a rashin sani — Astagfirullah! --- Wanda ke son sanin labarin: SUHAYL LITTLE NOOR Sirrin Taqaddarar da Ummu Kulsum ta ɓoye Sirrin kashe uwar Suhayl Da Masarautar Al-Qamar To ya shirya, domin labarin LITTLE NOOR zai biyo nan ba da jimawa ba, tunda Suhayl ya fita daga wannan littafi saboda laifin gudu. 😅 📞 08101235739 MY NEXT BOOKS COMING SOON 💐 1️⃣ DR SADEEQ — Romantic Love Comedy Drama 2️⃣ ƘAMSHIN DUHU 🌔 3️⃣ MASHIƘIYYA CE 4️⃣ RUHIN MARAICE 5️⃣ LUDAYEN JEMAGE 6.. LITTLE NOOR MY PUBLISHED BOOKS 📚 1. MIJIN MAGE 2. DUHU CIKIN HASKE 3. FARASHIN SO 4. MAI CIKI CE 5. RUHI BIYU 6. PRINCESS RAHILAT 7. AHLIN LAASHKAR 8. MADOBIN IDO 9. RAYUWAR UMMAH 10. BAYAN WATA 11. BIYYAYA GA UWA 12. HANYAR RUWA 13. ZAƁIN ZUCIYA 14. ƘADANGAREN BAKIN TULU Tammat bi Hamdillah. 🌺 Alhamdulillahi Rabbil ‘Alamin.