*TSUMMA MAKUNSHIN CUTA* Wolf in sheep's clothing oumyasmeen Da sunan Allah mai rahama mai jin kai Dukkan yabo da godiya ya tabba ga Ubangijin talikai ya Ubangiji ka bani ikon rubuta dai-dai. GARGADI gargadi ban yarda wani ko wata su yi amfani da daya daga cikin shashi na littafin nan ba ta ko wacce siga indan kunne yaji jiki ya tsira Wannan littafin ƙirƙirarran labari ne duk wanda ya ga yayi dai-dai da rayuwar sa to ya dauka arashi ne. Bismillahir ramanir rahim Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 Episode 1 Wata iriyar iska ke kadawa garin yayi ni'ima abinka da lokacin damuna ga kuma sanyin yammaci gyara kwanciyar ta tayi tana kallon waje tana tunanin anya kuwa yau ba za'a yi ruwa juyawa tayi tana cewa ai ina zaune a gurin nan idan naga an fara yayyafi na ɗauke masa kayan sa rufe idanuwan'ta tayi bacci na fusgarta a haka har ya kwashe ta. lokaci ɗaya ruwa ya kece kamar da bakin kwarya da sauri ta tashi tana zare idanuwanta tayi fiki fiki ga kayan ya ZAHID nan a zube akasa farare ne tas amma saboda ruwan da ya kece ga kuma akuyoyin nanne sun dawo daga kiwo suna neman malaɓa sun turmusa mai su sunyi wani irin baki ga rariyar bayi ta toshi dazu yake cewa idan ya fita zai nemo me gyara ya duba yaga me ya toshe musu ita sun hadu da kwatar bayi da ƙasa sun koma launin milk irin dark milk din nan me kama da ruwan ƙasa kuka Areej ta saka domin tasan yau me rabata dashi sai Allah ga nanne bata nan ta tafi ƙauye anyi mutuwa. wata ƙila ma ba yau zata dawo ba rasa ina zata saka kanta tayi taji dad'i dif ruwa ya ɗauke dafe kirji tayi jin alamun tafiya daga soro tamkar wata munafuka ta leko kan'ta ido hudu sukai dashi yana sanye da riga da wando jeans shi mutum ne me kyankyami dan haka ya shiga cewa joud joud tamkar wata wacce ake tuhumar ta da laifin kisan kai sai share gumi take tace '' sun tafi makaranta basa nan.., lokaci ɗaya ka kalli hanyar bayi farin gani yayi da kayan sa da suka koma wata kala abin kyankyami bazai iya mai da kayan nan jikin sa ba cikin takaici yace '' ke zo..., jikin'ta ya soma rawa ta zo gaban sa ta tsuguna tace '' gani.., ɗauke ta ya yi da mari sai da ta kifa kuka ta saki cikin ɗacin rai yace '' kina cikin gidan nan dan tsabar rashin kula da abin da ya dace ki bar min kayana suyi haka maza dauko su ki saka ruwa da hypo ki wanke su.., Cikin kuka tace '' bamu da hypo ɗazu najwa ta wanke mana kayan makarantar mu.., ganin irin kallon da yake mata da sauri ta hadiye sauran zancen ta ta tashi ta fara ɗiban kayan ta zuba a botiki juyawa yayi ya fita. tana kuka tana wanke kayan nan nanne bata , bata wanki joud ce ke yi ko najwa hannun ta ne ya fara ciwo amma bata dena ba jin sallamar nanne da sauri ta ɗago ta tawo a guje ta rungume ta , ta saki kuka cikin tashin hankali nanne tace '' auta waya taɓa min ke.., kuka ta ƙara rushewa dashi tace '' yaya ZAHID ne na kwanta bacci ban sanu ba kayan sa suka zobo suka ɓaci..., share mata hawaye tayi tace '' kiyi hakuri kinji auta zo mu shiga daki.., binta tayi har suka shiga daki zama tayi ta cire mayafin'ta tace '' yau baki wanka ba ko.., zumburo baki tayi ta kauda kan'ta ajiyar zuciya nanne ta saki tace '' auta auta kazanta ko tun kina jaririyar ki bakya son wanka bakya son a taɓa miki kanki Areej rayuwa za tayi haka kuwa..? wata ran fa gidan wani zaki maza tashi ina da ragowar ruwan zafi a flask nayi miki wanka na wanke miki kai tunda bakya son zuwa gidan kitso ni nayi miki., rufe bakin ta ke da wuya Areej ta saka kuka harda ɗora hannu aka ta saki ihu sosai take wage baki take zuba ihu nanne zuba mata ido tayi tana kallon ta , tashi tayi ta fita tsakar gida tana shure shure ta zauna a cikin ruwan nan cikin sauri aunty jamila ta shigo tace '' Areej lafiya kike kuka..?, ina nanne ta dawo ne ...?, da hannun ta ta nuna mata daki nanne fitowa tayi tace '' jamila mun wuni lafiya..?, nanne ina wuni kim dawo lafiya ya hakuri...?, cewar jameela. Alhamdulilah tafiya qalau hakuri da godiya daga cewa ta tashi nayi mata wanka shine ta zauna tana wannan uban kukan yawa wanda na dake ta.. Nanne ta faɗi haka cikin jimamin halin Areej ɗazu ma tana bacci ta fita da ace idon ta biyu tabbas sai ta bita irin yaran nan ne masu ƙawa zuci bata iya zuwa ko ina kullum tana katarar ta bata yadda da kowa sai ita. Aunty jameela tace '' to ai wannan ne sauki ne ZAHID yana waje bara na kirawo shi ke wacce iri ce a rana sai kiyi kuka yafi sau bakwai.., dif tayi jin ance za'a kirawo ZAHID ta share hawayen ta tace '' uhmm aunty jameela Wallahi bata yi min wanka a hankali ta dinga dirje min naman jiki na kuma jiya har ganyen magarya ta tai min tsarki dashi kuma da zafin sa ta wanke min kaina dashi shine yau ma wai zata wanke min, dan Allah ba ana yin kwaskwarima ba tai min mana dole sai tai min wanka.., ubanki za ayi miki ba wanka ba wankin da na saka ki kenan kika zauna kina yiwa mutane fitsara zaki tashi ko sai nayi ball dake ina wankin da kikai..?, dashi tayi jikinta duk ruwa ta labe a bayan nanne tana zare idanuwanta Nanne tace ''sannu tunda ta zama tamola ai dole ka buga kwallo da ita,zahid wallahi ka kiyaye ni wannan yar yarinyar zaka saka wanki ka taɓa ganin ta wanke ko da da pant din'ta ne..? ƙasa yayi da kansa yace '' nanne idan.., kafin ya ƙarasa tace '' bana son jin komai yi tafiyar ka.., Aunty jameela ta dunkure mata kai tace '' yar yar baka me kirar tifa.., kuka ta saka tana share hawayen ta nanne tace '' kiyi shiru auta ka'aba ma baka ce da masu zubin taliya yar murji gwara kosasshen mutum.., dariya aunty jameela tayi tace '' nanne dan Allah ki dinga rufewa yar nan baki kukan ta yana tada min me kano..., taɓe baki nanne tayi tace '' aini a gidan nan ba sarka na sakawa kowa ba dan haka kofa a buɗe take duk me son fita ya fita wannan yarinyar tawa tafi karfin ku.., murmushi aunty jameela tayi tace '' uhmm uhmm nanne ba'a san inda rana zata fadi ba .., zaro ido nanne tayi tace '' wani a'a wallahi sai dai a wani gurin badai anan ba kuje can ku ƙarata.., wanke kafarsa ya gama yi sannan ya dauko mukullinsa dakin sa a zaune yake ya juya ya bude dakin sa ya shiga bayan ya ajiye ta kalminsa a kofar dakin nasa. yana shiga ya kunna fitilar wayar sa da yake dakin yana da duhu sai kamshi ke tashi a hankali wayar sace tayi ringing da sauri ya daga ganin masoyiyar sace abar kaunar sa karawa yayi a kunne ta sakar mai kukan shagwaɓa lallaɓata ya fara yi yana cewa '' sweet me ya faru wane ya taɓa min ki sai inda karfina ya kare..?, wani kukan ta kara fashewa dashi tace '' sweet kaza nake son ci wallahi yau tun da safe nake jin kwaɗayi gashi mama bata da kudi ga kudin ankwon nan shiru kuma kasan mun kusa bikin bayan sallah ne ga zumi na karatowa.. Dan shiru yayi ya shafa sumar kansa yace '' Wallahi a dai yanzu bani da kudin da za kici kaza saidai kudin da nake hadawa zan baki na anko idan shi zan baki sai na baki kinsan lamarin rayuwar ne sai addu'a ba sosai ake samu ba idan kinga muna samo lokacin jarabawa ne ta ESSCE za azo a siya secrect card kinga ga makaranta da nake zuwa bana na samin damar zama a CAFÉ din sosai ba kamar da ba., tamkar yana gaban ta , ta hade ranta tace '' zaka fara ko ..? ni wallahi na rasa me yake damuna mace kamata na tsaya ina soyayya da wanda idan bukatar dubu dari ce ba zai iya yi min ba .., tana gama fadar haka ta kashe wayar ta hankalin sa ne yayi masifar tashi yana mugun son juhud yar shuwa , Allah ya ɗora mai sonta duk da mutane da dama cewa suke jummai Dubai yar duniya ce ba zata taɓa bashi yar ta ba ajiye wayar sa yayi ya fito ko me ya tuna sai ya chanza kaya kawai da wanka zai yi da dauki wayar sa ya chanza takalmi ya leƙa tsakar gida nanne tana yiwa Areej wanka tayi tsit da ace baya nan da makota ma sai sun san da yin wankan nan ta gyara ko ina tsaf akuyoyin ta ma ta mai dasu gurin su idan ba kwana za kai a gidan nan ba , ba zaka taɓa sanin ana kiwon a kuyoyi ba da sassafe ake sakin su bayan an basu abinci da yammaci su dawo shigowa yayi yace '' nanne zan fita wa'yannan kayan a bawa wani na hakura da su.., da sauri Areej ta rungume nanne tace '' nanne rufe ni kar yaya ya ganni ba kaya., murmushi nanne tayi tace '' to shikkenan zan bawa Nabeel ya rage su daman naga kayan nasa sun fara mutuwa Allah dai ya buɗa muku ya dafa muku.., amin ya Allah yace juyawa yayi ya fita tace '' Allah ya tsare hanya amin ya ƙara cewa ya fita cikin sauri da yake gidan jummai Dubai dillaliya yana bayan gidan su dan haka cikin mintoci kalilan ya isa aika yaro yayi yace '' ana sallama da juhud.., ba jimawa yaron ya dawo yace '' wai tace ka shigo.., to yace ya shiga sallama yayi jummai da take zaune daga ita sai shimi ga tulin kayan mata da na shafe shafe a gaban ta , ta amsa tace '' wa'alaikis'salam a'a Abdallah kai ne..?, cikin jin nauyin ta ya durkusa yace '' ina wuni mama.., lafiya qalau mun wuni lafiya kaganni jin wannan iskar na tube na saka shimi kasan idan akai ruwa wani zubin gari zafi yake barin idan ba me yawa bane irin dai wannan wanda ya zo gangara.., kansa yana ƙasa yace '' haka ne wallahi ina juhud take..?, hmmm mutuniyar taka tana nan wai tayi fushi nace aikuwa zan kiraka takanas nayi maka faɗa ni da nake cewa abin nan duk ɗaya ne ai kwaryar sama ce take dukan ta ƙasa , idan bakai mata ba wazai mata..? ehyi malam Abdallah na hanata kula kowa saboda kai to kaga idan kuma kana hanata abubuwa nayi mata adalci kenan da na hanata kula kowa sai kai cewa nake ai wannan abu dan liman ne dana na'ibi na baka juhud halak malak kayi yadda kake so da ita shi ne zaka tila min kasa a ido. shiru yayi yana sauraran ta yace '' insha'Allahu zan gyara amma mama nina wallahi bani dashi bawai haka kurum na hanata ba jiya ma tsiran dubu hudu na siya mata yau to bani dashi.., yanzu malam Abdallah koni ai na cinye tsiran dubu hudu balle juhud wannan farar fatar da kake gani tana burge ka ba karamin kuɗi take ci ba me auren juhud sai me hali ko me karfin zuciya irin dai kai.., murmushin karfin hali yayi shi wannan son zuciyar ta shi yake hada shi da su dan mutunci suna da kirki amma akwai son zuciya ajiyar zuciya ya sauke yace '' hakane yanzu tana ina .., tana cikin daki juhud juhud fitowa tayi da wani material me tsada a jikin ta sai zabga kamshi take murmushi yayi mata tace '' shigo ciki mana yawa wani bako.., tashi yayi ya shiga zama yayi akan kujera yana bin dakin da kallo murmushi tayi tana murza zoben hannun ta tace '' duk fushin da nake dakai idan na kalle ka sai hankali na ya kwanta naji damuwata ta hayaye.., dan matsawa yayi yace '' ko zaki koma daga can.., ɓata rai tayi tace '' kamshin turare na ne be maka ba ..?, ah wallahi yayi min sosai kinyi kyau ya faɗa yana dauke kansa da ya fara juya mai yana tsoron sabawa Ubangiji amma tun ba yau ya lura ba tarbiyar juhud da tashi ta banban ta ita gani take ba wani abu bane waye warta ta danne ilimin addinin'ta amma a hakan gani yake zai iya gyara ta , ta koma yadda yake son ta. fita tayi ba jimawa sai gata da robar ruwa da ta lemo ta ajiye mai da glass cup tace "' bisimallah ka jika mako shin ka..," Alhamdulilah yace yana kallon ta sai wani bankaro mai kirji take gata daman ba karamar mace ba wannan abubuwan ne suke rudar maza suke mata layi. ɓata rai tayi tace '' mama mama.., da sauri mama ta shigo ashe wando ne a jikin ta three quarter kannan yaci kananun kalba ta ƙari tace '' juhud me ya faru kike min kiran hukuma ke kenan bakya girma..?, turo baki tayi gaba tace '' mama kinga wai ba zai sha ruwan da na kawo mai ba.., maida gashin ta baya tayi tace '' haba kai kuwa ZAHID yawa ba gidan ku ba kaki cin komai a duk lokacin da ka zo.., murmushi yayi yace '' bana jin ƙishi ne amma next time insha'Allahu zan tawo banci komai ba sai kunce shi wannan haka yake da ci.., ya ƙarshe maganar cikin barkwanci. dariya mama tayi tace '' a'a ba za mu gaji da kai ba., ta fada tana fita daga cikin dakin gyara zama yayi yace '' yanzu me kike so ayi.., far tayi da idanuwanta tace '' uhmm bani da wata bukata hankalina ya kwanta nagan ka daman na fadi haka ne domin ka zo nasa baka dashi, Allah dai ya buɗa maka ka samu abin yi, muyi aure.., cikin jin daɗin maganar ta yace '' amin ya Allah Nagode sosai Allah ya bar min ke.., murmushin jin dadi tayi tace '' amin ya Allah., hira sukai sosai sannan yayi mata sallama ya tafi, fitowa tayi tana danna wayar ta , ta zauna a kusa da mama tace '' mama yau zaki fita ne..?, gyara zaman kayan ta tayi tace '' a'a ba inda zani so nake yi kafin na tafi Maiduguri na siyar da wa'yannan kayayyakin to kinga kwana biyu ba wani kaya ma da aka kawo min kuma mutuwar auren nan yinta ake yi bara na kirawo hajiya shatu muji gurin ta ko da kaya kinsan an bani cigiyar kaya to wallahi bana so suga gazawa ta.., ajiye wayar ta tayi tace '' kuma fa hakane ni ma nan da anjima zan fita.., Hajiya jummai Dubai ta dauki wayar ta , ta soma laluben number hajiya shatu cikin saa ta shiga sai dai har ta gama ringing ba'a dauka ba tsaki tayi tace '' tsiya ta da Hajiya kenan wallahi sai ta tafi sabgar gaban ta , tabar wayar ta ba tare da ita ba yanzu karki yi mamakin tana gida bata dauke ta ba , ta fita.., Mama hakuri za kiyi bara na koma daki na kwanta kafin lokacin fitar tawa yayi juhud ta faɗa tana tashi daga zaman da tayi shiga cikin daki tayi ta kwanta ruf da ciki wayar ta , ta dauka tana dannawa gajiya tayi da danna wayar ta ɗaga katifar ta , ta dauko wata kwalba buɗe ta tayi ta kafa a bakin ta tas ta shayen ta ko guntu bata bari ba kwanciyar ta , ta gyara ta limshe idon ta da yake mata dishi dishi cikin yanayi na mutuwar jiki tace '' mama idan karfe tara tayi ki tashe ni., ta komar da idon ta , ta rufe wani bacci me dad'i ya kwashe ta. Wannan kenan. shigowa yayi yana cije lips din'sa fuskar sa duk yanka wata yar ƙaramar huka ce a hannun sa nanne da take madafa ta leƙo tace '' a'a hafizu yau kai ne a gari..?, Cikin yanayin rikakkun yan daba yace '' eh wallahi nanne me zan samu kinga ciki na yawa anmin yasa ni wallahi ba ka fito ba daga gidan yarin nan abincin ma da zaka samu kaci cikin kwanciyar hankali babu sai an tada kura.., cikin mamakin kalaman sa nanne tace '' kai hafizu yanzu abincin kurkukun ne yafi na gidan mahaifin ka..?, harshe ya zaro ya lashi hukar hannun sa yace '' billahilazi yafi na nan gidan har fa dabge ake mana ke ba ra in tela miki Lokacin da na tafi lagos nanne tamu ta gargajiya me cika min cikina alkur'an kare ake ɓangare mana yaji kayan hadi ji za kiyi kamar kina cin ta wahaidu kazar larabawa idan kuwa na zauna a gu ba wanda ya isa ya zauna a buga caca kai bariki tayi a rayuwa ke rayuwar agege karkashin gada ba abin da ba'a samu idan dare yayi mu bazaza makabartu sabuwar gawar da aka kawo mu tone tsinanniya tas mu kwashe yan kuɗaɗen mu idan kuma babu mu dauki kaya sai kuma muci mushe musha ruwa.., kai kai kai hafizu kanka ɗaya kake wannan zance ina bacci nake jin tashin muryar ka wata mata ta faɗa tana fitowa daga ɗaya kofar da take kallon bayin nanne. haɗe rai yayi yace '' iyamu bana son ciki da annamimanci ke nake bawa labari ne ..? nanne wannan matar da kike gani duk wani hali da muka shiga ita , taja mana kema wallahi ki dena yarda da ita Alkur'an tsumma ce.., da sauri nanne ta tashi tace '' haba hafizu wannan ba mahaifiyar ka bace kake jifan ta da mugayen kalamai.., iyamu kuka ta fashe dashi tare da kifa kan'ta a kafaɗar nanne tausayin ta ne ya kama nanne ta soma rarrashin ta kwafa hafizu ya saki yace '' wallahi nanne ankar saboda kina cika min cikina ya saka duk abin da naga zai cutar dake da ya'yan ki nake nuna miki hanya amma ke bakya andasata (understand ) ba ruwa na jizos ba Allah mabane an'aike ne ankar ankar itama waccan zan tela mana tafi ta daga sabgar rocas yasin ko na sabule mata tafar cikin ta tas nayi mata ƙaramar tiyata.., Hafizu ya zaka tafi mahaifiyar ka , tana cikin wani hali Nanne ta faɗa cikin wani irin yanayi. Chak ya tsaya ya juyo yace '' yasin nanne dan kece nifa na ma manta da wannan sunan ke kike tuno min dashi ne idan wani ne ya fadi wannan sunan da sai dai yaga haƙoran'sa suna yawo a ƙasa tas sai na cire mai su tofa dan kece nake raga miki.., shege tsinannan ne karka raga mata dan ubanka wallahi hafizu ka kiyaye ni. iyamu ta faɗa cikin ɓacin rai hmmmm iyamu iyamu wallahi ki guji ranar da zanyi wa kowa na gidan nan zindir har kura ta cewa da kare maye gwara ni ba zambo cikin aminci nake yi ba kuma wallahi ido na idon wannan abin sai na hako shi duk ba ke kika samu a cikin bala'i ba. rarrashin ta nanne take yi dakyar tai shiru sannan suka zauna nanne tace '' hakuri za kiyi da lamarin yaran nan kowa da yadda Ubangiji ya tsara mai rayuwa idan aka saka hakuri da juriya sai kiga Ubangiji ya kawo afuwa be kamata ki dinga tsine mai ba kina la'antar sa iyamu kama ta yayi ki dinga tausasar zuciyar ki tare da faɗa masa magana mai daɗi. sai kiga ya shiryu ya bi kan turba kukan nan da kike mai ba ƙaramin bala'i bane a rayuwar sa dan Allah ki dena jifan sa da mugayen kalamai. ajiyar zuciya ta sauke tace '' Allah yana gani ba saboda dashi nake kuka ba nanne kalli irin maganar da yake fadi wai bana zama dake tsakani da Allah..., kara rushewa tayi da kuka taci gaba da cewa ai saiki zargi wani abin a zuciyar ki tunda zuciya bata da ƙashi idan ba kyautata miki ke da ya'yan ki ba me zanji a rayuwa ta iya so da kauna kin nuna min shi idan na musguna miki dai-dai da rana ɗaya sai Ubangiji ya kama ni haka dazu abin da jamila tai min banji dad'i ba wai na dauko farar alawa na bawa Areej ta karɓe ina kallon ta , ba komai nasan ba laifin ta bane irin maganganun da hafizu yake yi ne shi ya saka zargi ya shiga zuciyar ta ni kuwa ina zan saka kaina kowa yana yi min wani irin kallo me cike da ma'anoni kala kala duk kuma hafizu shine sanadi. kama hannun ta nanne tayi tace '' karki damu wallahi ko ɗaya matsayin ki yana nan a zuciya ta Allah ya dada shirya mana yaran mu.., kuka ta ƙara rushewa dashi tare da rungumar ta tana cewa Nagode nanne hakika ke faccala ce ta dabam Allah ya bar mu tare. amin ya Allah tace , tana tashi ta duba targen ta zuba gari ta fara sannan ta mai da tukunya ta rufe lokacin iyamu ta tashi daga bakin kofar dakin ta zama tayi tana jiran dawowar Areej. jin kukan ta asoro da sauri ta tashi ta leƙa tace '' ZAHID wai me yake damun ka da yarinyar nan yanzu daga aiken ta siyan Maggi sai ka dake ta me ta yi maka..?, karaf Areej tace '' ganin sana yi a gidan wannan yar iskar matar me tara mata shi ne nace mai lah daman anan budurwa ka take sai ya dinga dukan baki na har muka ƙara so gidan nan abokin sa ma yaya Tahir sai da ya hana shi., kai nanne ta girgiza tace '' ZAHID ba sai na tsaya ina maka dogon bayani ba ita dai Areej kasan matsayin ta a gurina bazan zuba ido ba naga ɗaya daga cikin ku yana ƙoƙarin takura mata ba ko dan kaddarar da ta same ta be kamata ku tausaya mata ba kuji ƙanta ba amma kai halin ka yafi na kowa, kowa yana nuna mata so da kauna ban da kai Allah ya ganar dakai gaskiya..., har ta gama maganar ta be ce komai ba sai da Areej tabar gurin yace '' nanne kiyi hakuri naga ranki ya ɓaci.., bakomai Allah yayafe mana baki ɗaya , ta faɗa tana barin gurin bude dakin sa yayi yana shigowa tahir ya shigo shiga cikin gida yayi ya durkusa har ƙasa yace '' nanne ina wuni an wuni lafiya.., cikin sakin fuska tace '' lafiya qalau alhamdulilah ya maman taku.., tana lafiya qalau ya su Areej yar lukata.. murmushi nanne tayi tasan ya fadi haka ne dan ya saka Areej kuka ai kuwa ashe tana kusa ta leƙo tace '' na faɗa maka nanne zata kai ni gurin rage tsoka tace tsoka ce tai wa Kamatuna yawa.., dariya yayi ya fita yana cewa da ta kuwa kyauta nanne tace '' ina gama girkin nan kafin su najwa su dawo zan miki kitso..., idanuwanta tane ya ciko da kwallah tace '' nanne dan Allah kiyi hakuri mu bari sai gobe.., haɗe rai tayi tace '' gobe yau she.., tunani ta shiga yi da sauri ta za bura ta shiga cikin daki a guje jakar ta , ta dauko tace '' an bamu assignment Dan Allah ki bawa yaya yayi min ni idan na kai mai yana yi min yana rankwashi na yace min me kan kwakwa ina tsayawa wasa bana karatu kuma nanne duba fa ki gani ...... kalli rubutuna ina yin me kyau haka ma aunty din ajin mu tace.., amsar littafin tayi sosai rubutun Areej ya bata dariya ita kan'ta idan za'a saka mata huka a wuya ta faɗi me ta rubuta ba lallai ta iya fadi ba Areej a kwai wasa da shiririta su, suke hanata fahimtar karatu tace '' Areej zo.., ɗurkwusawa tayi tana kallon littafin nanne tace '' haka malamar ku ta rubuta treesing ne fa amma ga yadda kika sauya musu kamanni kalli tittafin naki yawa ankwato abakin ƙura Areej kefa yanzu kin fara girma kina ECC 3 wata shekarar primary zaki shiga.., idanuwanta tane ya kawo ruwa daman bata da wuyar kuka tasan yau sarai yaya sai ya jibge ta zama tayi tace '' nanne gyara min in dauko pencil ki fiƙe da sharpener domin yayi kyau sosai yauwa harda cleaner.., ke bayan magariba idan su joud suka dawo kuzo na ga littafin ku mu kuma yi karatu sannan wallahi gobe idan baki tafi islamiyya jikin ki zai faɗa miki kin gama cika wa mutane kunne sannan ku zauna haka siddan ba cuta kike ba., shiru tayi tana kallon sa haɗe rai yayi yace '' ina miki magana kin kafe ni da idanuwa zaki bar kallo na ko sai na shigo, dauke kan'ta tayi ta kwantar dashi a cinyar nanne tace '' yaya kai hakuri.., jin maganar nabeel a soro a guje ta tashi ta fita rungume shi tayi tana tsallen murnar dawowar sa , aya ya fito da ita a aljihunsa amsa tayi tana washe hakoranta duk cin zuma tace '' yaya nabeel nagode amma gobe idan ka fita aiki madara nake so.., ɗagata yayi dakyar yace '' yar gidan nanne madara tafi karfina ban miki alkawari ba amma idan na samu hali zan siyo miki ita..., murmushi tayi ta kunce ledar ta watsa kusan goma abakin ta , tace '' to nagode.., Nabeel sauke min ya'karka fasa mata kai naga dakyar kake ɗaukan ta . sauketa yayi yake cewa nanne barka da yamma kin dawo lafiya Lafiya qalau alhamdulilah ya aikin naku da fatan dai komai lafiya ajiyar zuciya ya sauke yace '' alhamdulilah sai godiyar Allah yaya barka da yamma.., to Allah ya temaka ZAHID yace '' barka dai mun wuni lafiya ya aikin naka.., Alhamdulilah yana zama yace '' nanne wannan yar taki ce yawa bata san garin nan ba kullum dada fara shi take yi.., tagumi tayi tace '' wallahi zan ɓatar muku akan yiwa yarinyar nan ba'a sai kun saka ta kamu da cutar gudawa ta zazzage ku barmin kaya ta .., dariya nabeel yayi yace '' an barmiki iya nanne yar gidan nanne ikon Allah.., ya fadi haka yana doko ta komawa kusa da nanne tayi ta zuba mata aya a kan cinyar ta tace '' kema kici..., murmushi nanne tayi ta dauka tana ci. ZAHID yace '' kinde ji menace sauran kice kin manta.., bata fuska tayi zuciyar ta ba dad'i tace '' to.., komawa yayi fitar da da mintina kaɗan sai ga su joud da najwa gaishe da nanne sukai joud tace '' Areej bani ayar take inci naga ta jiƙa.., ɗaya ta dauka ta bantara ta miƙa mata harara ta watsa mata tace '' rike kayar ki aini ba mayya bace ba.., dariya najwa tayi tace '' maganin ki kamar baki san halin ta ba da shegiyar rowa idan kinga ta bada kayanta to nanne ce ko ya nabeel.., munfi kyaurata mata ne shi ya saka ta bamu cewar nabeel ba wacce ta , tanka shi suka shiga ciki cire kayan makaranta sukai suka fito, suka amshi girkin nanne nanne tashi tayi ta dauko kum da kibiya Areej tana yan aya bata san ta tsaya akan ta ba sai ji tayi ta cire inner cap din ta kuka ta saka , zare mata ido nanne tayi ta zauna akan kujera tana taje mata tulin sumar ta , ta usul ba relaxer ko ɗaya ga ƙarfi kuka ta dinga yi har da majiya har aka gama kitson ZAHID da yake cikin ɗaki shi da Tahir suna hira yaja tsaki yafi cikin kwando cikin tsokana Tahir yace '' nifa wallahi kana takurawa kanka me yarinyar nan tayi maka kuruciya ce wata rana ba za tayi ba..., kwafa yayi yace '' idan suka barta ba tare da tsawatarwa ba wallahi haka zata ' shi abin takaici idan kaga hakoran ta to cine shi yasaka kwakwalwar ta , ta zama ta dusa bata iya fahimtar komai kaga saboda da ita na dauko wancan dankon a hanya dazu yau nasan hmmm balallai naga abin arziki a cikin littafin taba ga ƙin makaranta wallahi yarinyar nan ita take jawa kanta nayi mata duk wani abu da banyi niya ba , amma nanne ta dinga faɗa kenan ina jiye mata lokacin da za tai mata Aure ta kasa zaman auren ba shikkenan ba sai ta dawo baya ta gyara kuskuren da tayi..., kwanciya Tahir yayi yace '' to aini ne mijin..kaga kuwa bazan hulakanta ta ba ..., kai dakata wallahi ba zaka jawo min raini ba haka kurum ana zaune kalau ZAHID ya faɗa har cikin zuciyar sa dariya Tahir yayi ganin yadda yayi maganar yace '' kai abokina ina harda su tada jijiyoyin wuya da ina cewa kai zaka fara kafamin gwamnati ..., a'a gwamnatin tarayya zan fara kafa maka wallahi Tahir ka fita a idanuwana da wannan maganar taka me kama da kasha kwaya.., tashi zaune yayi yace '' a'a giya nasha dan rainin hankali ni kuwa ina yar gidan dillaliya...?, dan ya tura masa haushi ya fadi haka ai kuwa ya tura masa a fusace yace '' kaga malam lamarin naka yafara yawa zo ka fita ya za ayi ka dinga cewa mahaifiyar matar da zan aura mutunci ba zai yiwu ba kamata yayi a matsayin ka na amini na ka dinga daraja ta Kana marta bata amma kai kake fara kushe alakar mu.., dole na kushe idanuwanka sun rufe kana shirin aikata babban kuskure a rayuwar ka haba abokina yawa wanda aka jefe ko akai wa sammu da fa kai kake kyamar rayuwar su amma yanzu ka saka kanka a ciki babbar damuwa'ta kar fa ta jaka wata hanya ba me bullewa ba..., toshe kunnuwan'sa yayi yace '' wallahi da ace wani ne ya faɗa min wannan maganar da tuni na dade da shafe shi a cikin rayuwa ta waikai Tahir me ya saka baka so a zauna lafiya ne..., *TSUMMA MAKUNSHIN CUTA* Wolf in sheep's clothing Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 Episode 2 Saboda ina son fahimtar dakai abin da ka manta. tashi yayi ya fita jin ana ƙoƙarin kiran sallar magariba dai-dai lokacin malam ya dawo Tahir shima bin bayan sa yayi daukan kayan da malam ya kawo sukai suka shiga da shi cikin gida shi musu albarka yayi tare da amsa gaisuwar da suke mai. daukan buta yayi da nanne ta ajiye mai ya dauro alwala suma su kayi, suka tafi masallaci a sukwane hafizu ya shigo yana cewa idan na yarda Allah ya tsine min albarka nanne nanne zo ki gani dan Allah yau wallahi wasu zasu bakunci Ingila me tukwane kuttumelesin kan baban ubancan lallai yau fa za ayi ta da dan kamfai idan na yarda nayi yawo tsirara sai da na shigo cikin gidan nan na ƙara tabbatar wa jiki na ya bani a cikin gidan nan aka cinye min kudin naman aska da sauri nanne ta fito tana ƙoƙarin tada sallah tace '' lafiya hafizu me ya faru kake wannan kikirari...?, zaro huka yayi ya soke a kugunsa tare da saka karan sigari da sauri nanne tace '' haba hafizu a cikin gidan namu za ka sha mana sigari kayi hakuri idan ka fita ka sha.., cire ta yayi ya saka a kunnen sa tace '' dan girman Allah duba ki gani duba aska da kyau be rame ba.., da sauri ta kalli karen da yake nuna mata wani irin baki ba kyen gani tace '' ni banda wata rama ba me ya faru.., kina nanne na dade ina so ki an kare ko ba haka ba lamma.. abokin nasa ya cije baki yace ''hakane ka dade kana nuna mata way.., yauwa lamma amma bata ganewa badai zance mata damsil basiratu ba tunda ko ba komai tafi waccan matar da wallahi idan bata sauya halin ta ba kaga dai ban yi wani karatun isilama nayi ba amma dai nasan ae yaneee to idan baya gyara halinta ba naru ce makomar ta kinga nanne ina umara na dinga turo kudi a siya wa aska yaci ya koshi abarshi da ciwon rashin ganina to wannan baiwar Allah sai ita take ci a cikin ta ko baki ga yadda ya rame ba daga zuwa umara na sati uku na dawo shine ya fita daga kamanninsa na tambayi wanda nake bawa kudin ya kawo mata yaci Alkur'an yana kawo mata amma zanyi maganin su dole a fito min da kudi na ko yau mutum yayi kwanan ingila me tukwane Nanne tace "kayi hakuri hafizu nawa ne kudin naka na baka sai ka bar maganar bana son ƙara jin wani tashin hankali.., kama karfen taga yayi yace '' ah wallahi ko karfanfana dattin aljihu bazan karɓa ba wacce dai ta cinye min kudina ta fito min dashi tun kafin nayi alkafura a kan ruwan cikin ta na caccaka mata wuƙa.., toshe kunnuwan'ta tayi domin zancen nasa ba ƙaramin daga masa hankali yayi ba. Kai da sauri suka juyo hamdala tayi ganin ZAHID domin dai-dai yake da shi tsoransa yake jima shiga daki tayi ta barsu fuskar sa ba annuri yace '' me nace maka kwanaki..?, dauke kan'sa yayi daga kallon sa yace '' i get .., kwafa ZAHID yayi yace '' kai kuma karka ƙara shigo mana gida domin gidan nan ba sa'an wasan ka bane .., jan karansa yayi yana cewa albasa batai halin ruwa ba billahilazi ba uban da ya isa ya hanani shugowa da wanda na ga dama cikin gidan nan ni za'a tozarta a gaban abokina.. shiga daki yayi ya zauna yace '' nanne ki dena tsayawa ki saurari wannan yaron kine na sakar mai fuska kamar hakan da kike yi ya ƙara samin damar yin abin da ya ga dama cikin gidan nan ya shigo da wanda ya ga dama kuma kusan abokanan sa ba , mutanen arziki bane kinga su joud mata ne be kamata suna cuɗan ya da irin mutanen nan ba ko dan tarbiyar su.., haka ne wallahi ZAHID abin da ya saka daman nake jan shi ajiki kaga irin su ba'a nuna musu tsana soyayya ake nuna musu ajawo su a jiki sai suyi hankali amma idan ana kyarar su ba za suji da dad'i ba haka iyayen sa kawai sai dai hakuri da addu'a Allah ya shiryar mana da zuri'a baki ɗaya.., amin ya Allah yace najwa ta dauko mai tuwan sa zama yayi yana ci Areej sai matse kwalla take nanne ce ta taɓa jikin ta , taji zafi da sauri tace '' subbanallahi Areej me yake damin ki..? jikin ki zafi raɗau.., kwantar da kan'ta tayi tace '' kaina ke ciwo da kunne na.., joud tace '' nanne ba dole tai cuta ba yarinyar nan wasan ruwa fa take idan ta shiga bayi dan ruwan da muke ajiyewa wallahi tas sai ta karar dashi dan Allah ki siya mata fo ta dinga abin ta muna wanke mata.., da sauri ta tashi ta kalli joud tace '' Allah ya kiyaye tab ni za kiyiwa tsarki wallahi ina neman tsari da wannan ƙaddarar nanne ka wata lukutar magana wai ni za tai wa tsarki sai kace yarinyar goye.., dariya nanne tayi tace '' kyale ta ba wanda zai dinga yi miki tsarki.., kwanciyar ta , ta gyara tace '' ai wannan abin ma salon su ganni ne yara su shigo suyi mini dariya nanne zafi nake ji.., joud tace '' da nafi kowa murna wallahi., Hararar ta tayi tamkar idanuwanta za su fado ƙasa nanne tace '' tashi na cire miki rigar kya sha iska.., satar kallon ZAHID tayi da yake cin abincin sa hankali kwance tamkar baya gurin duk abin da suke yi ko tari be yi ba wayar sa na hannun sa yana daddanawa mai da kallon ta tayi gun nanne a hankali tace '' nanne ba kince ba kyau wani ya ga tsiraicin wani ba kuma Ubangiji yana babbaka mutum lokacin mutuwar sa be ba ya mutu kalli yaya yana gurin ni ba zan cire ba naje na mutu.., Murmushi nanne tayi tace '' haka ne tafi daki ki cire ki saka me dan ƙaramin hannu ta shan iska.., ihu ta saka za ta fara tirje tirje suka haɗa ido da ZAHID yace '' maza ku shirya lokacin karatu yayi..., da sauri ta ɗago tace '' yaya ni zazzaɓi ne a jiki na bani da lafiya ko nanne..?, ko sharafa kike yi sai kinyi karatun nan gobe ma idan zan fita ni zan dauke ki nakai ki ba nabeel ba. wani yawu ta hadiya ta tafi daki kaya ta canza ta dauko jakarta ta fito lokacin har ya fara yiwa su najwa zama tayi ya gama yace '' zo.., zuwa tayi kusa dashi gaban tana faduwa dauko littafin ta yayi ya fara buɗawa zaro ido yayi yace '' Areej me kika rubuta nan.., muci muci ta fara da idanuwanta taja baya dan ƙo hannunta yayi yace "'zaki magana ko sai na kwaɗe ki ..?," Dan Allah yaya kai hakuri aunty namu ce mana tayi botiki botiyun kofi cofiyun kofa kofiyun haka ta karanta mana what a you mad..?, tuni idanuwanta suka cika tab da kwalla still bata dena taunar ayar ta ba ga wata kuma a hannun ta kallon nanne yayi yace '' kinga ko nanne wallahi yarinyar nan nagaji da halin ta wacce malama ce dan Allah zata faɗa mata wannan maganar da munafurci ne da ita ce kan gaba wajen bada labarin abin da ya faru.., Shiru nanne tayi jin maganar iya ta dawo tace '' to bakin mugu wannan yarinyar dai bada ban Allah yayi ta kosasshiya ba wallahi mijina da tuni ka dade da ramar da'ita irin kune ku hana matan ku sakat ka bakar jaraba kullum cikin azumi.., kunya ce ya kama shi ya saki hannun Areej agaban su joud iya ke faɗar haka kai sha'anin iya sai ita nanne tace '' iya sannu da zuwa..?, zama tayi dakyar tana sakar salati tace '' wallahi maryamu bazan amsa gaisuwar ki ba tunda kema kin zama bakar muguwa me hana da ya danƙi hannun ta ki dauki muciya ki buga masa a hannu salon Ya karya min jika ta to yasin kana karya ta hmm ranar caji moshan za mu tafi.., iya kiyi hakuri yanzu nake shirin yi mai magana. nanne ta fada cikin sanyin nan nata Uhmm kyaji dashi ciwon ajali a ɗayan tsa kowa na hango shi na hasko shi da fitila ta Hajara Hajara hajara uwar bakin hali.. da sauri iyamu ta shigo tace '' iya sannu da zuwa.., wani kallo tayi mata tace '' bana bukatar gaisuwar ki naji ance wannan dan neman ya dawo tun a hanya lado sirikina ya faɗa min wanda yake aurar yar gidan kanwata mariya yake min jaje to akul akul karna ji karna gani billahuwar ramanu hajara ranar da dakin ya dauki kayana tofa dole sani ya sake ki agidan ku zaki kwana ina dalili haka kurum me ya nadani da shi ba dai uban sa na haifa ba to bana son zazzagar albarka abarni ma da ciwon hawajan jinin da yake damuna da hasfatatus (hepatitis ) da yake idi me camiris (Chemist) yana namijin kokarin akan wannan ciwo nawa da tuni wani labarin ake ba wannan ba kwanaki maganin dubu biyar na siya har yanzu ina dashi ina watsa uku zuwa hudu na kwanta cikin salama shi ya saka za kuga dakyar nake tashi sallah asubayi.., iya yaushe kika kamu da wannan ciwo likita ne ya gwada ki yace kina dashi juraij ya fadi haka yana kallon ta cikin mamaki tana da wannan ciwo amma lafiyar ta lau to yaushe ma ta kamu dashi.. cire mayafin'ta tayi tace '' mijina hmm daman cuta tana cina ranar nan na kunna gida radio suna wannan shirin da nake ji duk sati na kiwon lafiya ana hira da kwararran likita a Babban Asibiti wallahi kaf abin da ya faɗi ba wanda bana ji shi shine banyi ƙasa a gwuiwa ba na tambayi bukar kudi banma faɗa mai me zanyi da shi ba dan kar na daga mai hankali na tafi gurin idi me Chemist ya bani sauki goma ya haɗa min aunti battatik (anti biotics).., turƙashi iya hannu ta ɗora akan bakin ta tace '' shii bana son jin komai ku kuma da kuke dariya ku ci gaba dayi ku fito kuyi son ran ku masu kan luɗaya ni bani da duhun kai da naje aka bani magani gashi nan ina kan matakin farko haka yace min kuma naga amfanin haka domin bacci ina samun sa ishashshe. shiru suka yi nanne ko matsi ta kasa dole ta saka ZAHID yaje ya jawa idi kunne ko ta kara zuwa ya bata magani karya bata zata zame musu yar kwaya. kusan faduwa tayi da sauri ta ɗafa bango tace '' amma dai Hajara anyi mara kirki wallahi babban burin ki, ki kaini ƙasa to wallahi ubanki ma nafi karfin sa bake ba kurwar sani dai da kika gama shaye ta tas kika rufe sai yadda kikai dashi to wallahi nafi karfin ku duk abin da kuke yi a gidan ku na tsafi yana kunne na tas.., a hankali tace '' iya kiyi hakuri ban san kin tashi ba.., hajara ina kuwa zaki san natashi ta ina zaki sani bakin hali da munafurci ya rufe miki zuciya da ido. shiru tayi ranta na suya ta rasa yadda za tayi da iya wata iriyar jarababbiyar mata ce ita ta iya masifa haka kurum sai ta zauna tana girgiza kafa a tsakar gida tana kallon mutane daddai ba wanda ta kyale a cikin sirikan ta gwara gwara nanne tana raga mata amma itama idan cin mutunci ya biyo ta kanta ranar tas za tai mata ke najwa dauko min mukulli ki bude min kofar nan.. tashi najwa tayi ta fito buɗe kofar tayi tace '' sannu Allah yayi albarka jameela jameela kina ina kina jina kin yi muƙus a daki ga dodo ta dawo nifa bana so na shigo cikin gidan nan ban ganku reras ba yawa yan matan amarya bana son fitina na lura yanzu abin da kika tsira ki dinga ware kanki kina kulle kanki a akurkin dakin ki me kama da shagon dan cirani wallahi ina mamaki ta yaya kike iya numfashi a dakin nan ranar da hamza bashi da Lafiya na shiga hmmm dawowa nayi da ciwon saman kai kwanya ta ciwo ta dinga yi yawa wata jaririya sabuwar haihuwa muɗigata sai harbawa take yi zafin dakin ki ya tada min da muɗigata ta haka na dinga addu'a ta koma ni jikina yana bani gidan nan anyi buso yasin zan kirawo malamai daga maradi abokin malam ne Allah ya jikan rai zai zo yayi addu'a duk dan kutumar uban da yayi min buso a cikin gidan mijina dan ya raba kan zuri'a ta tas zai koma mai kan sa dan haka magana nake muku da babbar murya duk wanda yasan yayi ya cire shi tas.., aunty jameela shigowa tayi da yake kofar ta , tana waje ba'a cikin gidan take ba tace '' sannu da zuwa sallah nake yi lokacin da kika shigo ina idarwa naji kiran ki.., Allah ko ta sallah..? to nayi nisa bana kuma dawowa kim sani yan uwanki suyi miki bayanin duk abin da nace Allah ya isa koda harafin magana kuka boye kunsani sarai ni bana munafurci bakuma nason annamimanci.. shiru su nanne suka yi har ta shiga daki ba wanda ya tofa tashi zama aunty jameela tayi tace '' yaya me ya faru..?, Nanne tace '' gashi nan shi ta shigo tana zai daki Areej shikkenan ta fara faɗa.., murmushi tayi tace '' Areej yar gata .., fadi da wai ki ƙara da ihu Areej yar gata ce dan ta rasa wani gibi na rayuwar ta bawai yana nufin mu ba zamu cike mata shi ba , Iya kiyi hakuri wallahi bada wata manufa na fada ba banza tai mata tashi ga bayi sallama tayi musu ta fita iyamu ta koma ɓangaren ta. da sauri nanne tace '' maza tashi kije ki kwanta karki min bacci anan.., Nanna batai fa sallah ba cewar najwa. Nanne tace '' najwa yaushe rabon ki da kika areej ta saka goshin ta a gabas..?, Joud tace '' to ita dai mutuwa bata sallama wallahi rabona da ganin ta saka goshin ta a ƙasa tun wancan azumin shima saboda fita a sham da yake ta mai da abin kamar zuwa yawo ne shi yasaka take yi. ZAHID yace '' bata sallah kamar ta.., da sauri areej ta hau kan cinyar nanne tana zare idanuwanta. dariya nanne tayi tace '' tashi kije ki kwanta.., Malam ne ya shigo yace '' auta waya taɓa ki naga kina taɓa idon ki zaki tsiyar ki cikawa mutane kunne..?, da hannu tai mai nune da su dariya yayi yace '' dan Allah ku sakarwa yarinyar nan mara tayi futsari wannan wa ce irin rayuwa ce haka.., ZAHID tayi yayi yace'' malam sai da safe.., To Allah yayi albarka yauwa zo.. dawowa yayi ya zauna su kuma su najwa suka shiga dakin su yace '' gani malma.., dan jim yayi sannan yace '' Alhaji yace kaje ka dinga yi mai direba ga hakan ma alfarma yayi maka saboda wai Company sa yana da ma'aikata da yawa zaka dinga kai yaransa makaranta daza man ban zan da kake yi ka gama karatu ba aikin yi.., Runtsai idanuwan'sa ZAHID yayi yayin da jijiyoyin kasa suka fito raɗa raɗa kanin mahaifinsa yana da damar da zai kaishi ko ina yayi aiki karatun ma dayaya ya ƙara sa ba inda beje ba neman aiki takardun'sa basu da wasu tangarda da first class ya fita amma ko ina yawa an musu baƙin shafi ba'a daukar sa da yayi wannan aiki gwara ya wuni beci ba ko da miliyan zai bashi akwai ranar da yaga yar tasa ta baɗa mai ƙasa ta wuce shi talauci hauka ne da ya zauna a inda za'a dinga hulakanta shi gwara ya bar gurin cikin son ya fahimtar da mahaifan nasa yace '' malma bawai zanƙi bin umarnin ka bane a'a ina so na tsira da mutunci na kaga nan gurin da nake zuwa ina dan samun abin da zan rufawa kaina asiri ba kyara ba hantara amma can sai abin da na gani kuma ba lallai zuciya ta , iya jurewa ba kaga na bata zumuntar da ke tsakanin mu bana so na zama nini silar rushewar wannan ahali koda zuwa nayi na faɗa muku za kuji ba dad'i ballantana bazan iya faɗa muku laifin dan uwanku ba ni kuma matsayin mahaifi yake a guri na, aiki lokaci ne wata rana sai labari bakowa aiki haifa da arziki ba kowa sai da ya sha gwagwarmayar rayuwa nasan abin da kake hange karfin ka ya kare ga najwa ga joud ga Areej wacce lokacin ba zaka iya yi mata komai ba saboda shekarun girma sun ƙara cim maka yanzu ma insha zamu zame muku katanga ni da dan uwana duk wani abu da ake yi ana samun halak zamu bi musa mo muku dan rayuwar mu ta inganta amma wannan aiki na Alhaji bazan iya ba zato yake yi haka zamu dawwama to insha'Allahu dan zaki zai girma alfarmar annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama wani ma sai ya more mu sai yaji daɗin mu karatun yaran nan insha'Allahu bazan gaza ba zan dauke shi har matsayin da zasu sami ilimin da suma zasu tallafi na kasan su... Limshe idonsa yayi wani sanyi yana ratsa shi tabbas yasan ZAHID gwarzon namiji ne tsayayye duk abin da ya fadi yana ƙoƙarin cika shi ne Gwauron numfashi ya saki yace '' Allah ya dafa muku ya baku abin da kuke nema ta hanyar halak ya tsare rayuwar ku gaba da baya ya raba ku da fitinar zamani..., ZAHID yace amin a zuciyarsa nanne ma albarka ta saka musu sannan ya tashi ya fita kai tsaye fita yayi a kofar gida yaci karo da Tahir tafiya cafe su kayi suna hira ganin me rake yayi ya tsaya, ya siya musu Tahir ya fara sha yace '' kuma raken akwai zaki wallahi kagan sa tamkar sugar.., da alama dai santi kake yi mu samu guri mu zauna anan karka fadar min a hanya na rasa inda zan kai ka.. Tahir yace '' wallahi koma m zaka fadi sai dai ka fadi domin kai baka ji zaƙin raken nan ba.., Tahir sweet da sauri suka juyo jin muryar juhud tana sanye da hijabi har kasa ga niqab a fuskar'ta murmushin jin dadi ZAHID yayi domin duk wayewar juhud tana burge shi idan zata fita tana rufe jikin tane, ta nuna cewa tasan abin da yake mata ciwo yace '' sweet ina zaki.., kallon sa tayi me cike da ma'anoni kala kala sannan ta lumshe idonta lokaci ɗaya ta bude su tar akan kyakkyawar fuskar ZAHID yace '' unguwa zani nan soron dinki.., ZAHID ABUBAKAR ABDALLAH GALADANCI yace '' ko mu tawo rakiya ne..., maida idanuwanta ƙasa tayi tana wasa da yan yatsunta tace '' a'a Nagode barshi hakan zai zama da takura tunda ba kai kaɗai bane..., murmushi yayi yana kallon Tahir da ya kasa cewa komai sai Yanzu yace '' juhud barka da dare.., kan'ta yana ƙasa tace '' barka dai ya harkoki.., Alhamdulilah yace yana zama a kan wani benchi. To Allah ya dafa muku ya baku abin da kuke nema. Amin ya Allah yace sallama tayi musu, ta tafi dukan kafadar Tahir ZAHID yayi yace '' tashi uban son jiki yawa ba namiji ba.., dariya yayi yace '' GALADANCI naga kai ka dade da zama soja shi ya saka na bar maka fagen daga.., dariya yayi ya shafa sumar kan'sa yace '' wallahi ka tuno min da school ina kewar ta kai gabaki ɗaya ma karatun ina kewar sa da ba dan kanne na ba da sai na kara kuru na tafi karatu idan na tafi bansan wazai kula da su ba Nabeel bekai girman da zai dauki ragamar rayuwar su ba.., Dafa shi yayi yace '' karka damu abokina Allah zai dafa mana insha'Allahu zamu cika burikan mu, Tashi yayi suka fara tafiya suna hira har suka isa CAFÉ din su tarar da aiki sukai dan haka ko wanne ya zauna a mazaunin sa ZAHID buɗa laptop yayi yace '' Abdul Rahman ka samu kuwa website din nan ya buɗe ni wallahi har tsoron shiga nake yi ina shiga zai wullo ni waje.., dariya dukkan su sukai wanda aka kira da Abdul Rahman yana zaune yana bushe gyaɗar sa yace '' ina fa kai yanzu da ace ya buɗe da network ai da yau sunana rich man.., dafe goshi ZAHID yayi yace '' wallahi bansan ya zanyi da mutanen nan ba jibi yadda kowa yake jira kuma kamar sun saka headline din rufewa ko..?, Wallahi sun saka karka damu yanzu haka jina nake kamar wani attajiri tun da ina cin dawisun talaka.. dariya dukkan su suka saka Asim yace '' shege shi ya saka tun dazu kake susar kunne da mukulli sai kaje kunnen ka ya burme.., duka yakai mai yace '' dan Allah GALADANCI me ya ragewa takala yanzu ya Nigeria banda yayi susar kunne yaju dad'i idan da hali ka dan hada da yar gyaɗanli kana susar kunne kana tauna gyaɗa.., kai kurum ZAHID ya girgiza domin in da basu sun saba wannan musum ga kuma mutane ana ganin su da kima karsu fara yar tanki tanka girman su ya zube fara danna laptop din'sa yayi yace '' ni dai wallahi ku cire ni a wannan batu ina da abin yi.., Dole kace kana da abin yi zai kai wa me idon cin naira cewar Abdul Rahman. Tahir yace '' la la Abdul Rahman kayi shuru wannan mutumin baya son gaskiya., tashi yayi ya leƙa wajen da mutane ke zaune ana ciki wani form na daukan aiki gwamnati ce ta fito dashi zata dibi malaman makaranta masu NCE yace "wanda ya ke kan layi yayi sauri ya zo ya haɗa komai website din ya buɗe..." Wani ne ya taso ya shigo cikin sauri yake shigar mai da komai ya tura addu'a ya dinga yi Allah ya saka ya shiga kar su rufe portal din sanin kowa ne aiki yana karanci yayin da matasa suka rasa abin yi fitina ce ga al'umma bayan sune kashin bayan al'umma din wata ran sune iyaye me gaba ake so ta haifar ne yana wannan tunani yaga sun dawo mai da shi dafe kansa yayi yace "kawai abdulraman ka bawa sauran hakuri yaƙi yi..." dariya yayi yace '' ashe bari ba shegiya bace da uban'ta ni yau nasan zamu yi tsalle mu duro da oga haka kurum ina zaman basir yace ko purewater ba zaka iya dauka ka siya ba sai abin da ya baka.., da sauri Tahir yace '' duk wannan uwar gyadar da kuɗin sa ka siya.., ɗaga mai gira yayi yana gyara zaman rigar sa da duk ta kode amma akwai guga saita glasses din'sa yayi ya zura yace '' galadanci ya kayi shiru ba zaka shigar min fadan nan bane..?, Mutumin da ake cike mai portal yace '' ba dole yayi shiru ba ka dauko abin da yafi karfin sa.., dariya yayi yace '' a'a galadanci baya taɓa gazawa damu mu nan da kake ganin mu tawaga ɗaya ce ko wanne a cikin mu da yan kwanaki ya girmi wani tare mukai kuruciya muka tashi shi ne babban mu duk wani faɗa shike tare mana tsakanin mukwai amana da son juna saboda haɗin kanmu kuma course ɗaya muka dauka muka zo muna aiki a waje ɗaya dan haka saniya bata taɓa gazawa da kawonta ko galadanci..., kai bana son shirmen banza kayi abin da nace kafin ya dawo ka nemo mai kuɗin sa. Tashi mutumin yayi yace '' to Allah ya bamu nasara da sa'a mu fita daga cikin wannan matsalar..., amin ya Allah suka ce bayan abdulraman ya dawo ya zauna yace '' kuyi karo karo ku biya min kudin gyadalli..., Tahir da takaici ya rufe shi ya ciro totuwar rake yace '' wallahi ko kobo bazan bayar ba raken nan ma ba zaka sha ba dan rainin hankali kamar shi yafi kowa son cin dadi kwadayin ka yayi yawa karfa wata ran ya dauko mana abin da zai samu cikin tashin hankali kai baka taɓa yadda da babu baka taɓa zama a inda Ubangiji ya ajiye ka ..., yauwa guy's nafa yanke shawara domin zaman nan haka zaman jiran tsammani nagaji dashi gabaki ɗayan mu computer science muka karanta ita kan'ta gwammati tasan bara zana ne mu a gare ta idan har ta barmi ba abin yi.. Asim da zancen ya fara shiga jikin sa yace '' haka ne wallahi ci gaba muna jin ka.., To yasin bazan ci gaba, ba sai ka bani rake shi wancan yace bazai bani ba kai asim bani nasha.. wullo mai gutsire ɗaya yayi yace '' sai kace maye daman tun da naga kana kallo na , nasan cewa akwai wata a ƙasa.., daukan sa ,yayi ya tauna bayan ya gama tsotsewa yace '' kan bura ubancan ba dai zaƙi ba yau dukkan mu nan munkai munzalin riƙe mata amma saboda talauci da yayi mana kan'ta mun kasa yin aure gwara ku kuna ma da budurwa ni kuwa saboda yanzu abin da na lura matan yanzu consumer ne ya saka na zama zero tension misalin ƙarfe ukun dare nayi kutsai wata na'ura kuma mallakin gwamnatin tarayya ce na gana makudan kudade da ke cikin account ɗin wanda idan muka cire harta ya'yan ya'yan mu wallahi baza suyi talauci ba wacce shawara kuka yanke mun dade muna cewa a gudu tare a tsira tare bama rabuwa cikin ra'ayi ɗaya kullum muna tare. ZAHID sai yanzu yaga dacewar yayi magana yace '' abdulraman idan na fahimci zancen ka so kake mu fara yahoo ina tarbiyyar da iyayen mu suka bamu idan mun fara sata imanin mu yayi rauni karka manta me Ubangiji yace a cikin Surat Al-Mā’idah (Sura ta 5), Aya ta 38–39 Aya ta 38: "وَالسَّارِقُ وَالسَّارِقَةُ فَاقْطَعُوا أَيْدِيَهُمَا جَزَاءًۢ بِمَا كَسَبَا نَكَـٰلًاۭ مِّنَ ٱللَّهِ ۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ" Aya ta 39: "فَمَن تَابَ مِنۢ بَعْدِ ظُلْمِهِۦ وَأَصْلَحَ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَتُوبُ عَلَيْهِ ۗ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٌۭ رَّحِيمٌ" aya ta farko Ubangiji yana cewa “Namiji mai sata da mace mai sata, ku yanke hannayensu a matsayin sakamako bisa abin da suka aikata, azaba daga Allah. Kuma Allah Mai iko ne, Mai hikima.” ta biyu yana cewa To, wanda ya tuba bayan zaluncinsa (wato satar da ya yi) kuma ya gyara, to lallai Allah Yana karɓar tubansa. Lallai Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai.” Iillolin da sata ke haifar wa suna da yawa duk wanda zai saka hannu ya dauki abin wani sai an cire mai imanin sa sannan sata tana da ga cikin mayan zunubai ita bin jini take , baka tunanin a ko wanne lokaci Ubangiji zai iya kiran mu, kuma dole mu amsa kiransa idan ya kira mu alokacin da mun saka hannu za mu ɗauki abin wani Ubangiji ya zare ran mu me za mu ce da wanne ido zamu kalle sa karka manta kowa akan abin da ya mutu akan shi za'a tashe shi be kamata dan tunani ya gushe ba hankali shima ya gushe ina ilimin addinin mu yake kaf cikin mu nan ba wanda ba zai iya zama ya rubuta Alkur'ani me girma ba saukar mu nawa Ubangiji fa yana ragawa wanda be sani ba akan wanda ya sani kuma ya take sanin sa karka manta me yace azaba ta tabbata ga wanda yayi ilimi sannan baya aiki dashi to mu yanzu mece ribar mu kaga suci aduniya suci a lahira. shiru suka yi jikin su yayi sanyi abdulraman yace '' tabbas idanuwana sun rufe na kasa tuno maganar Ubangiji hakika samin aboki kamar ka sai an tona muna godiya da fadakar da mu da kayi insha'Allahu haka zamu gudu tare mu tsira tare sheɗan ko sheɗaniya be iya ya raba tsakanin mu ba mudin jini ƊAYA NE..., rungume shi sukai suna farim cikin sanar da su da yayi tun kafin suyi nisa gurin aikata babban zunubi abdulraman dauko system ɗin sa yayi ya goge abin tare da fita daga cikin duk abin da zai nuna acewa anyi musu kutsai cikin na'ura.. Tahir yace '' yadda bamu da gata sai na Ubangiji aka kama mu wallahi sai igiya tayi saura a jikin mu domin sai me tsawon rai zai rayuwa kaga mun saka iyayen mu a wata damuwa da sai ranar da mala'ikan mutuwa ya tsaya a kan su zasu manta da ita wasu a cikin mu ta sanadiyar haka iyayen su su mutu wa gare ya waya ko ina talaka ne a ƙasa.., Wannan haka yake daga haka kowa ya koma akan aikin sa assalamu alaikum da sauri suka amsa tare da gaishe shi amsawa yayi yace '' jiya da yau nawa kuka haɗa.., kallon kallo aka shiga ZAHID yace '' sakamakon network da yake bamu matsala sannan Portal din shima baya shiga sosai to ba wani abu muka haɗa ba.., Cire hularsa yayi yace '' oh nayi magana da commissioner yace sun rufe amma wani hanzari ba gudu ba , big man..., Da yake haka yake cewa ZAHID lokaci zuwa lokaci yace '' na'am oga.., Yauwa nasan aikin nan sai kai kafi computer ƙwaƙwalwa so nake ka haɗa min link irin na wannan wanda aka rufe din nan muci gaba da amsar kuɗin mu da irin wannan cuwa cuwar ake hayewa lamarin rayuwar nan komai yayi tsanani kuma kuna da buƙatun rayuwa dan haka mu hadu mu rufawa kai asiri muci gaba da amsar kudin mu sannan duk wani me CAFÉ da yazo ku bashi portal code shina kude ne me tsoka.. ran ZAHID ne ya ɓaci irin wannan aiki ba dashi ba dame al'umma za suji 1500 da suke tsira da ita , itama sai an kwace musu wannan wanne irin TSUMMA ne zambo cikin aminci kenan fa yadda da sukai da su shine zasu ha'ince su to wallahi ba dashi ba kauda kai yayi. Oga nura yace '' big man dakai fa nake kai min shiru ba zakai bane ko yaya na sanka da kawo kabali da ba'adi yawa ba dan zamani ba....?, *TSUMMA MAKUNSHIN CUTA* Wolf in sheep's clothing Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 Episode 3 ZAHID dauke kan'sa yayi yace '' gaskiya oga bazan boye maka ba bazan iya wannan aiki ba saboda gallazawa al'ummar musulmi ne idan muka mutu mu cewa Ubangiji me da wanne ido zamu kalle sa , ni ko kobo bazan iya ci a ba saboda wannan kudin, kudin haramin ne kuma na zalinci mutane suna ji da yanayin garin nan sannan a ɓullo da wata hanyar cuta su basu sani ba su zo su kawo kudi suna ganin cewa za su samu abin nan ƙarshe kuma ya zo ba riba basu samu ba wallahi Ubangiji ba zai barmu ba zai iya yafe hakkin dake tsakanin mu dashi amma na mutane bazai iya yafewa ba dubban mutane dubu nawa za mu cuta wani kafin lokacin mu yayi shi ya riga mu gidan gaskiya wani har bada baza mu iya sanin inda yake ba balle mu bashi hakuri ya yafe mana, ni ba zan iya cutar rayuwata ba na ginata da haramin ita haramin bin jini take da tsoka nata rusa zuri'a, bazan iya kaiwa iyayena haramun suci ba.., da hallacan da kata min tun kafin a haife ka nasan wannan jabi zo ka fitar min daga shago na zuciyar maza fa takai iya wuya ZAHID be yadda da hulakanci ba bayayi kar amai cikin zafin rai ya dauki laptop din sa yace "' da dai nayi maka wannan aiki gwara na bar gurin nan sannan ina me sheda maka barin gurin nan bawai yana nufin nabar rayuwata bane zan ci gaba da rayuwa ina me baka shawara ka tsabtace zuciyarka dan wata ran zata iya kai ka ga halaka da kake cewa kasan wannan tunkafin a haife ni sanin ka be amfana maka da komai ba , ina darajjaka ina mutunta tsofan ka sai dai kai baka gani, na barka lafiya..." gabaki ɗayan su suka tawo suka dauki kayan su abdulraman yace '' tun da har ka kori ZAHID kamar dukan mu ka kora daga yau mun ajiye maka aikin ka ba me yi sai Allah zamu ci gaba da gwagwarmaya har mu cimma gaci.., sakar baki yayi ya cire hularsa shaf ya manta shegun kaya ne haka suke yawa kashin awakai lokacin da zai dauke su aiki cewa sukai in har ba zai ɗauke su duka ba sun hakura sanadiyar zuwan su CAFÉN sa ya kafa tarihi me girma, saboda kwarewar su gurin aiki kullum kazo a cike yake dam da mutane wani yawu ya hadiya yace '' wallahi kuka sake kuka bishi duk wanda ya dawo bazan amshe shi ba.., dariya Asim yayi yace '' oga kenan kamar baka san suwa ye yan kungiyar aminan juna ba to mu idan muka bar guri mun barsa kenan bama begen sa sai dai shi gurin yayi begen mu.., Tahir yace '' faɗa mai da manyan baki ga tsiyar ka nan mun bar maka ..., ni kuke faɗawa wannan maganar to wallahi kuyi kuka da kanku zaku gani. ZAHID yace ''da addu'ar iyaye muke takama dan haka ba abin da za mu gani sai alkairi.., har ZAHID yaje bakin kofa ya juyo yaga suna binsa girgiza kai yayi zai yi magana Abdul Rahman yace '' karkace komai nasan abin da zaka fadi da mun san da wannan to kamar yadda bamu san da shi ba haka Ubangiji zai budo mana hanyar samu ta inda ba muyi zato ba..., zuciyar sa ce ta karye saboda alkawarin da yayiwa mahaifansa dafa kan'sa yayi yace '' ya Allah ga salihan bayin ka ya Ubangiji kafi mu sanin abin da ke boye Allah ka tallafi rayuwar mu.., amin suka ce suka fita daga wajen baki ɗaya har suka iso hanyar gidan su ba me cewa komai kowa ya kasa magana kowa da abin da yake sakawa aran sa da yake al'adar su ce yau su kwana a dakin wannan gobe gidan su wannan za su wanda a cikin su baya iya wannan ZAHID duk dare zai dawo ya kwanta duk da tsakanin su ba nisa.., yau kwai sai suka yanke shawarar kwana a dakin ZAHID bude musu yayi suka shiga bayan sun ajiye kayan hannun su, suka shiga cikin gidan domin gaishe da su nanne su danyi barkwanci suka dawo dakin sa Tahir jin gina yayi da bango yayin da hasken wutar lantarki ya haske mai fuska da yake kwai wuta Asim ne yace '' guy's ya naga jikin ki duk yayi ba dad'i daman fa ko haka bata faruwa ba ni wallahi ina gab da ajiye wannan aikin wahalar me mutumin nan yake tsinana mana ban da yaron nan da suke hawa sama su doro akan ya daukan hakkin sa.., Dariya Abdul yayi yace '' sai ya duba yanzu yaga ba dari shidda.., da sauri Tahir yace '' gyadar har ta dari shidda kaci...?, gira ya ɗaga musu ba tare da yace komai ba kai ZAHID ya girgiza yace wallahi na tabbatar wannan mutumin bazai barmu haka ba sai yazo ka bashi kudin sa... be ida rufe bakin sa ba suka ji ana bugu tashi ZAHID yayi ya buɗe turus yayi ganin yan sanda a kofar dakin su suba yan iska ba yace '' barka da dare yallaɓai.., Kai ne ZAHID ABUBAKAR ABDALLAH GALADANCI..? dakyar ya iya daga mai kai dan sandan ya fito da ankwa yace '' your ander arrest.., dakewa yayi yace '' ko zaka iya nuna min ID da dalilin ka mani..?, jin wannan maganar suka taso da sauri domin suka me ke faruwa Asim yace '' ba inda za shi indan kuma kun matsa sai dai a tafi damu gaba ki ɗaya me yayi muku ZAHID bashi da wani abokin faɗa hayaniya bata dame shi ba..., naushi dan sandan nan ya kawowa Asim ya kauce yace '' za kuyi bayani ne wallahi sai na saka ku a matsalar da baku isa ku fita daga cikin ta ba maƙiyin ku ma sai ya tausaya muku.., murmushi ZAHID yayi yace '' rai be isa yayiwa dan uwansa wani abu ba face haka Ubangiji ya tsara dan haka karya kake,kai mana abin da Ubangiji be mana ba muje Ubangiji yana tare da me gaskiyar..., Dariya yan sanda su kayi Tahir yace muje kar wanda ya sanarwa da su nanne za su shiga damuwa be ida ƙarasa wannan maganar ba sai ga Areej ta fito tana cewa yaya galadanci ga kayan ka ka manta da su nanne tace kar mu kwanta bacci ka tashe mu.. da sauri ta juyo leƙowa tayi ta kalli yan sandan da suke tsaye a gurin agigice ta zubar da kayan hannun ta tare da rushe wa da ihu tsawa ya daka mata sai dai bata dena ba ta kamkame shi ya banta yau sharabon da suyi irin wannan kusanci tun bayan fara girmanta da kuma ƙin karatun ta kasa ko da motsi yayi sai kuka take tana cewa yaya kace su tafi bana son ganin su, su suka zo suka tafi da baffa be ƙara dawowa ba..., durkusawa yayi ya tallofo habarta yace '' wayan can daban wayan nan daban kiyi shiru ki dauki kayana ki kai min daki na kar wanda kika faɗawa komai kinji.., Kwantar da kan'ta tayi a kafaɗar sa tace '' yaya ina zaku...?, murmushi yayi yace '' unguwa.., da daren nan ita ba'a bari a tafi da rana eh maza kiyi abin da nace ko kina so na dake ki..?, kai ta girgiza mai ɗauka tayi ta shiga daki su kuma suka fita har sun fara tafiya ta tsaya ta fito bayan ta fito yace '' to matsa kulle gidan ki shiga gida..., Duka dan sandan ya kai mai ya riƙe hannun sa yace '' ban ga dokar da ta baka dama ba ka dake ni batare da an tabbatar da laifina ba duk da baka faɗa min laifin da na aikata..., Tahir yace '' muka dai aikata amma ba mamaki wancan na jadun tsohon ne.., kullewa tayi ta saka musu sakata ta shiga gida, tana shiga ta tarar da nanne ta jiranta faɗawa jikin'ta tayi tai shiru tana tunani tace '' nanne yau naga irin wa'yanda suka zo rugar su baffa suka ɗauke shi..., da sauri ta ɗago tace '' Areej bana son karya a ina kika gansu...?, kwanciyar ta gyara sai kuma hawaye ya fara bin fuskar'ta tace '' wallahi na gansu sun tafi da su yaya galadanci kuma har ƙoƙarin dukan sa suke amma yace nayi shiru zai dake ni idan na faɗa muku dan Allah karki faɗa masa na faɗa miki..., kasa kwakkwaran motsi tayi yayin da areej bata dena kuka ba iya da take ciki daki ta fito kwankwasa musu kofa tayi dakyar nanne ta tafi ta buɗe kofar iya tace '' maryamu lafiya naji yar nan tana kuka.., kafin nanne tayi magana Areej tace '' wa'yanda suka zo suka tafi da baffa ne , suka zo suka tafi da ya galadanci.., La'ilaha'illahu Muhammadun Rasulullahi sallahu alaihi Wasallama Allahumma ajirni fimasiba akilli kairan minha ke Areej bana son rashin hankali da gaske ne da idon ki kika gani. cewar iya Areej tayi banza da ita Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 Episode 3 ZAHID dauke kan'sa yayi yace '' gaskiya oga bazan boye maka ba bazan iya wannan aiki ba saboda gallazawa al'ummar musulmi ne idan muka mutu mu cewa Ubangiji me da wanne ido zamu kalle sa , ni ko kobo bazan iya ci a ba saboda wannan kudin, kudin haramin ne kuma na zalinci mutane suna ji da yanayin garin nan sannan a ɓullo da wata hanyar cuta su basu sani ba su zo su kawo kudi suna ganin cewa za su samu abin nan ƙarshe kuma ya zo ba riba basu samu ba wallahi Ubangiji ba zai barmu ba zai iya yafe hakkin dake tsakanin mu dashi amma na mutane bazai iya yafewa ba dubban mutane dubu nawa za mu cuta wani kafin lokacin mu yayi shi ya riga mu gidan gaskiya wani har bada baza mu iya sanin inda yake ba balle mu bashi hakuri ya yafe mana, ni ba zan iya cutar rayuwata ba na ginata da haramun ita haramun bin jini take da tsoka nata rusa zuri'a, bazan iya kaiwa iyayena haramun suci ba.., da hallacan da kata min tun kafin a haife ka nasan wannan jabi zo ka fitar min daga shago na zuciyar maza fa takai iya wuya ZAHID be yadda da hulakanci ba bayayi kar amai cikin zafin rai ya dauki laptop din sa yace "' da dai nayi maka wannan aiki gwara na bar gurin nan sannan ina me sheda maka barin gurin nan bawai yana nufin nabar rayuwata bane zan ci gaba da rayuwa ina me baka shawara ka tsabtace zuciyarka dan wata ran zata iya kai ka ga halaka da kake cewa kasan wannan tunkafin a haife ni sanin ka be amfana maka da komai ba , ina darajjaka ina mutunta tsofan ka sai dai kai baka gani, na barka lafiya..." gabaki ɗayan su suka tawo suka dauki kayan su abdulraman yace '' tun da har ka kori ZAHID kamar dukan mu ka kora daga yau mun ajiye maka aikin ka ba me yi sai Allah zamu ci gaba da gwagwarmaya har mu cimma gaci.., sakar baki yayi ya cire hularsa shaf ya manta shegun kaya ne haka suke yawa kashin awakai lokacin da zai dauke su aiki cewa sukai in har ba zai ɗauke su duka ba sun hakura sanadiyar zuwan su CAFÉN sa ya kafa tarihi me girma, saboda kwarewar su gurin aiki kullum kazo a cike yake dam da mutane wani yawu ya hadiya yace '' wallahi kuka sake kuka bishi duk wanda ya dawo bazan amshe shi ba.., dariya Asim yayi yace '' oga kenan kamar baka san suwa ye yan kungiyar aminan juna ba to mu idan muka bar guri mun barsa kenan bama begen sa sai dai shi gurin yayi begen mu.., Tahir yace '' faɗa mai da manyan baki ga tsiyar ka nan mun bar maka ..., ni kuke faɗawa wannan maganar to wallahi kuyi kuka da kanku zaku gani. ZAHID yace ''da addu'ar iyaye muke takama dan haka ba abin da za mu gani sai alkairi.., har ZAHID yaje bakin kofa ya juyo yaga suna binsa girgiza kai yayi zai yi magana Abdul Rahman yace '' karkace komai nasan abin da zaka fadi da mun san da wannan to kamar yadda bamu san da shi ba haka Ubangiji zai budo mana hanyar samu ta inda ba muyi zato ba..., zuciyar sa ce ta karye saboda alkawarin da yayiwa mahaifansa dafa kan'sa yayi yace '' ya Allah ga salihan bayin ka ya Ubangiji kafi mu sanin abin da ke boye Allah ka tallafi rayuwar mu.., amin suka ce suka fita daga wajen baki ɗaya har suka iso hanyar gidan su ba me cewa komai kowa ya kasa magana kowa da abin da yake sakawa aran sa da yake al'adar su ce yau su kwana a dakin wannan gobe gidan su wannan za su wanda a cikin su baya iya wannan ZAHID duk dare zai dawo ya kwanta duk da tsakanin su ba nisa.., yau kwai sai suka yanke shawarar kwana a dakin ZAHID bude musu yayi suka shiga bayan sun ajiye kayan hannun su, suka shiga cikin gidan domin gaishe da su nanne su danyi barkwanci suka dawo dakin sa Tahir jin gina yayi da bango yayin da hasken wutar lantarki ya haske mai fuska da yake kwai wuta Asim ne yace '' guy's ya naga jikin ki duk yayi ba dad'i daman fa ko haka bata faruwa ba ni wallahi ina gab da ajiye wannan aikin wahalar me mutumin nan yake tsinana mana ban da yaron nan da suke hawa sama su doro akan ya daukan hakkin sa.., Dariya Abdul yayi yace '' sai ya duba yanzu yaga ba dari shidda.., da sauri Tahir yace '' gyadar har ta dari shidda kaci...?, gira ya ɗaga musu ba tare da yace komai ba, kai ZAHID ya girgiza yace wallahi na tabbatar wannan mutumin bazai barmu haka ba sai yazo ka bashi kudin sa... be ida rufe bakin sa ba suka ji ana bugu tashi ZAHID yayi ya buɗe turus yayi ganin yan sanda a kofar dakin su suba yan iska ba yace '' barka da dare yallaɓai.., Kai ne ZAHID ABUBAKAR ABDALLAH GALADANCI..? dakyar ya iya daga mai kai dan sandan ya fito da ankwa yace '' your ander arrest.., dakewa yayi yace '' ko zaka iya nuna min ID da dalilin ka mani..?, jin wannan maganar suka taso da sauri domin suka me ke faruwa Asim yace '' ba inda za shi indan kuma kun matsa sai dai a tafi damu gaba ki ɗaya me yayi muku ZAHID bashi da wani abokin faɗa hayaniya bata dame shi ba..., naushi dan sandan nan ya kawowa Asim ya kauce yace '' za kuyi bayani ne wallahi sai na saka ku a matsalar da baku isa ku fita daga cikin ta ba maƙiyin ku ma sai ya tausaya muku.., murmushi ZAHID yayi yace '' rai be isa yayiwa dan uwansa wani abu ba face haka Ubangiji ya tsara dan haka karya kake,kai mana abin da Ubangiji be mana ba muje Ubangiji yana tare da me gaskiyar..., Dariya yan sanda su kayi Tahir yace muje kar wanda ya sanarwa da su nanne za su shiga damuwa be ida ƙarasa wannan maganar ba sai ga Areej ta fito tana cewa yaya galadanci ga kayan ka ka manta da su nanne tace kar mu kwanta bacci ka tashe mu.. da sauri ta juyo leƙowa tayi ta kalli yan sandan da suke tsaye a gurin agigice ta zubar da kayan hannun ta tare da rushe wa da ihu tsawa ya daka mata sai dai bata dena ba ta kamkame shi ya manta yau sharabon da suyi irin wannan kusanci tun bayan fara girmanta da kuma ƙin karatun ta kasa ko da motsi yayi sai kuka take tana cewa yaya kace su tafi bana son ganin su, su suka zo suka tafi da baffa be ƙara dawowa ba..., durkusawa yayi ya tallofo habarta yace '' wayan can daban wayan nan daban kiyi shiru ki dauki kayana ki kai min daki na kar wanda kika faɗawa komai kinji.., Kwantar da kan'ta tayi a kafaɗar sa tace '' yaya ina zaku...?, murmushi yayi yace '' unguwa.., da daren nan ita ba'a bari a tafi da rana eh maza kiyi abin da nace ko kina so na dake ki..?, kai ta girgiza mai ɗauka tayi ta shiga daki su kuma suka fita har sun fara tafiya ta tsaya ta fito bayan ta fito yace '' to matsa kulle gidan ki shiga gida..., Duka dan sandan ya kai mai ya riƙe hannun sa yace '' ban ga dokar da ta baka dama ba ka dake ni batare da an tabbatar da laifina ba duk da baka faɗa min laifin da na aikata..., Tahir yace '' muka dai aikata amma ba mamaki wancan na jadun tsohon ne.., kullewa tayi ta saka musu sakata ta shiga gida, tana shiga ta tarar da nanne ta jiranta faɗawa jikin'ta tayi tai shiru tana tunani tace '' nanne yau naga irin wa'yanda suka zo rugar su baffa suka ɗauke shi..., da sauri ta ɗago tace '' Areej bana son karya a ina kika gansu...?, kwanciyar ta gyara sai kuma hawaye ya fara bin fuskar'ta tace '' wallahi na gansu sun tafi da su yaya galadanci kuma har ƙoƙarin dukan sa suke amma yace nayi shiru zai dake ni idan na faɗa muku dan Allah karki faɗa masa na faɗa miki..., kasa kwakkwaran motsi tayi yayin da areej bata dena kuka ba iya da take ciki daki ta fito kwankwasa musu kofa tayi dakyar nanne ta tafi ta buɗe kofar iya tace '' maryamu lafiya naji yar nan tana kuka.., kafin nanne tayi magana Areej tace '' wa'yanda suka zo suka tafi da baffa ne , suka zo suka tafi da ya galadanci.., La'ilaha'illahu Muhammadun Rasulullahi sallahu alaihi Wasallama Allahumma ajirni fimasiba akilli kairan minha ke Areej bana son rashin hankali da gaske ne da idon ki kika gani. cewar iya Areej tayi banza da ita Ke dan kwal'uban ki, kina ji ina miki magana kin yi shiru...?, cewar inna Areej shiru tayi mata , ta dauke kanta nanne tace '' tashi na duba dakin sa .., kama haɓa iya tayi tace '' ba shakka anya kuwa maryamu kina son ganin annabi salim alim batare da an fara tsoma ki a wuta ba ke da baki je kin gani yana nan, ba, ko baya nan shine kika buge da kwaɗawa mutane salati..?, sauran kadan hawan jini na ya tashi dan ji nayi kirjina kamar ana kidan disko dakyar na iya tashi.., iya kiyi hakuri , ban ɗauka maganar ta , gaskiya bace bara naje na duba.. da sauri iya ta , tashi tace '' maza zauna ke , tun da dai har yanzu ba kisan darajar haihuwa ba da ciwon haihuwa ba , ni na sani joud joud.., zama nanne tayi tana bawa iya hakuri. banza tayi da ita joud da suka fara bacci tasowa tayi tana mustsuka idon ta , tace '' iya gani.., maza dauko fitila mu fita, fitila kuma babu hasken farin wata ne. da sauri inna tace '' ke dan ubanki bukar bawai tsoro nake ji ba ai wallahi ko lokacin da na haifi ubanki bilyaminu banji komai ba ko tsoron haihuwar fari da ake ni ban tsorata ba..,dan haka sha zaman ki, ta faɗa tana fita soro ta nufa tun daga bakin kofar shigowa cikin gidan ta fara cin karo da tashin hankali dakewa tayi ta shiga cikin soron kamar mutum ta gani da babbar riga ya lulluɓe kansa saka kafa tayi domin ta , tabbar wa da idon ta abin da ta gani ji tayi an ya kushi kafar ta , tare da yin haushi ba karamin firgita iya tayi ba Hafizu ne ya tashi yana cewa wanne dan bantan uban ne ya taɓa min ƙare na. Hawani haushi ne ya kama iya cikin masifa tace '' uwar kace Hajara wallahi Allah bara na tashi uban ka idan ni na haife shi to yau dole ka fitar da wannan baƙin karen daga cikin gidan nan, domin ba zaka jan yo min jini na ya hau ba., Hafizu yace '' hattara dai iya billahilazi bakin rijiya ba gurin wasan yaro bane yanzun nan sai na bawa reza naman ki.., innalillahi wa'inna ilaihir raji'un hafizu wallahi ko giwa ta rame tafi ƙarfin rami sani sani sani sani haka ta shigo cikin gida tana kururuwa kiran sani. Kawu sani cikin bacci yaji maganar iya tashi yayi zuciyar sa na bugu ya dubi hajara yace '' innalillahi me kuma ya faru kin ji iya ke kira na.., ina zan sani muje dai mu ji meke faruwa, Allah dai ya saka ba wata matsalar bace. Hajara ta faɗa tana miƙe wa tsaye daukan fitila yayi suka fito a tare wani kallo iya tayiwa iyamu tace '' na kira ki..ne kika dauko ƙafafuwan ki masu kama da kwarashi kika biyo shi..? Iyamu ki, kiyayeni wallahi. ban da tsabagen iyaye na kirawo ɗana kin biyo shi zingwui zingwui ke ga me miji ko..? to koma kina cewa tak zan saka sani ya sake ki, kije gida aci gaba da shan miyar kuka.., wannan cin mutunci da iya tayi mata ba karamin kona mata rai yayi ba dan haka ta , ta fara tafiya a hankali tamkar wacce kwai ya fashewa a ciki.. kai kuma sani na juyo gare ka , kamar ance juya taga tafiyar da iyamu take yi da sauri tace '' wato ban isa ba na kafawa miki sharadi sai kin taga maganar da za muyi shi ne ita kike son ji ko, to dawo kiji..?, Cewar iya. dan Allah kiyi hakuri wallahi cikina ne ke ciwo bawai karya dokar ki nayi ba. Iyamu ta fadi haka idon ta na ƙasa. gudun karta ƙara wani lefin banza iya tayi mata , taci gaba da cewa '' kai sani ga danka can yana cewa zai bawa karen sa nama na ya cinye ka shiga tsakani na dashi kafin na gayyato hukuma cikin wannan zancen.., ran kahu sani ne ya ɓaci yace '' dan girman Allah iya kiyi hakuri zan yiwa tubkar hanci dole yau, ya fitar da wannan karen daga cikin gidan nan.., majina ta fyece tace '' wallahi ban taba zaton hafizu zai iya cewa zai bawa kare nama na ba sani kai na haifa sanin kan kane bana saka damuwa ta a raina balle a je ga na saka damuwar wani amma Ubangiji ya jarabce ni da ciwon hawan jini duk kaffa kaffar da nake da rayuwa ta., jikin sane ya yi sanyi yace '' kiyi hakuri inshallahu ba zai ƙara ba , zan jamai kunne nasan yanzu haka ma , bana cikin hayyacin sa ya faɗa miki wannan maganar iya kiyi hakuri dan Allah ki dena kukan nan..., iya da idon ta , tar yake ba hawaye amma sai aikin fyece majina take tana shashsheƙar kuka tace '' barni nayi kuka sani, yan zun nan yan caji moshin suka kama zahid.. wannan yarinyar areej ce take faɗa min.., Kahu sani yace '' innalillahi wa'inna ilaihir raji'un ba mu ga ta zama ba ,.ina yaya yake yazo mu tafi.., Nanne tace '' yana dakin sa da bari nayi zuwa safiya sai aje aga me yake faruwa..., da sauri iya ta juyo tace '' maryamu kin fara shaye shaye ne bani da labari domin wannan maganar taki kama take da ta yan maye, kuma na gode da laɓen da kike mana, nazo ina meetan (meeting ) da ɗana kina tsaye kina jin mu sarai na ganki tsayawa nayi naga ita gudun ruwan ki Maryamu yanzu da kika ji amfanin me zai miki...?,kuma wallahi ina gab da ɗaukan kyakkyawan mataki akan ki., shiru tayi, tama ƙasa magana. tafiya tayi har dakin bukar ta , taso shi gaban sane ya fadi jin abin da iya take fadi to su yanzu ina za su. Sani yace '' to yanzu idan ma mun fita bamu san wacce police station yake ba amma mu baru zuwa safiya dole a neme mu..., Malam bukar yace '' hakene mu bari zuwa safiya.., Iya ban da aikin fyece majina ba , abin da take. ganin ko wanne yana shiga daki ta buɗe nata dakin ta shiga.. Wannan kenan. Beb wannan banza saurayin nan naki yana fa hannun mu.. da sauri juhud ta kalle sa tana tashi daga jikin sa kamo ta yayi yana ƙoƙarin kissing din ta kau da kan ta , tayi ta ƙara narkewa a jikin sa tana wasa da yan yatsun sa, tace '' Please me yayi kuka kama shi...? ,, hannu ya ɗora a kirjin ta tana messaging din breast din ta , bece komai ba , wata yar ƙaramar kara ta saki tana cewa Please magana nake maka.. Juhud ta faɗa a rarrabe saboda sosai sakon nasa ke gigi ta mata kwanyar kan'ta cikin wani irin nishadi yace '' saboda sun yi faɗa da uban gidan sa, shine ya saka mu, mu nona mai iya kacin sa.., kai ta gyaɗa tana kokarin zura hannu a cikin boxer din sa tace '' Please my love ka sake shi wallahi Zahid ba ruwan sa.., ido ya kura mata yana cewa nima daman da , tamu dashi bana kaunar sa tun da har yake kokarin takara dani... Cewar abdulrazak. tashi tayi tana yi mai kiss a kumatun sa tace '' kai hakuri ka sake shi, shi ƙansa yasan ni nafi karfin sa, wallahi ba son sa nake ba tausayin sa nake ji, ba ƙaramin sona yake ba.., Abdulrazak yace '' daya san ke kunama ce , dame matso inda kike ba.., wasa ta farayi da ramin cibiyar sa tace '' Please kayi abin da ya dace a yau ina so Zahid ya kwana a gida..., Abdulrazak yace '' kudin da aka bani fa..? nayi yaya dasu...?, sauka tayi daga ƙansa tana ƙoƙarin saukowa daga kan gadon ta suke ya riƙe hannun ta yace '' kiyi hakuri zan yi abin da kike so, yau so nake mu kasan ce cikin jin dadi.., abdulrazak ya faɗa yana ɗaga mata gira., juhud tace '' okay to, kira su a yanzu, su sake, shi., daukan waya yayi yana cewa an gama ranki ya dade. dariya tayi tace '' tare da naka..., komawa tayi jikin sa ta kwanta shi kuma a lokacin ya ƙara waya a kunne ya bawa yaren sa umarni su, saki su Zahid. yana gama fadar haka , ya kashe wayar sa,ya ajiye. kansa ya ɗora kan breast din ta, ta saki wani irin nishi. tana zura hannu a cikin gashin kan sa da yaci gyara. cikin so da kauna ta kura mai ido tana cire hannun ta , daga kan sa ta ɗora akan..., iya yawan sharing din ku da reacting din ku iya yawan reading more din ku TSUMMA MAKUNSHI CUTA Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 ________________________________ _________________________________ Episode 4 Wayar tace tayi ringing da sauri ta tashi zaune, ta dauka tana cewa mama ce , taga dare yayi ban dawo gida ba..,, A.S.P Abdulrazak yace '' to kice mata ba yau za ki dawo ba.., da sauri juhud ta kalle sa tace '' maman zan cewa a waje zan kwana ba yau zan dawo ba..?, Juhud ta faɗa tana kafe shi da idanuwanta A.S.P ya shafa sajen'sa yace '' gani nayi duk sana'ar ku ɗaya, dan kin ce mata haka , ba wani abu za tace ba.., Saboda takaicin maganar sa juhud bata ce mai komai ba , ta shiga, haɗa kayan ta , saka rigar ta , tayi ta zuge zip din tana cewa naga alert kar na tafi kace ba zaka , bani kudina ba.. haɗe rai yayi yace '' alert kuma..? har me muka yi, ina cewa ko rage zafi ban yi ba.., ajiye wayar ta , tayi a cikin jakar ta , tace '' kuttumar uban nan kayyasah Abdulrazak saka idon ka cikin nawa, kai min kallon tsaf ban yi kama da , macen da zaka yi wa , haka ba , kasan ni abin kunya baya na bashi wallahi nayi gaba, yan zun nan sai na haɗa maka mutane a cikin hotel din nan , wa ya faɗa maka bariki karya ce..? ko ana zuwa bariki babu kudi, to ko karen sigari zaka siya sai ka , saka kudi balle mace wacce iya kudin ka iya wacce zaka dauka.., cire bleat ɗin'sa yayi yace '' kar ki nemi ki raina min hankali ce miki a kayi sata nake , nake kwaso kudin da , ba abin da nayi dake, ki dinga zancen na baki kuɗi, a'a kuttumar uban kudi zan baki zaki tafi ko sai na saluɓe miki fatar jikin ki..?,, Ihuuuuuuuuuu Abdulrazak kana da hankali kuwa..? to idan ma , kwaya kasha kai saurin dawowa cikin hayyacin ka naji alert wallahi idan ba ka , bani ba zaka gani.. ta faɗa tana barin gurin. dogon tsaki tayi, ya zauna yana dafa ƙansa. besan yarinyar nan yar tasha bace sai yau. ko da yake gado tayi. ya fadi haka a cikin ran sa. daukan waya, yayi, ya soma laluben number laylah abuja yana kyau tata zaton, bata , tafi gida ba , domin jiya sun haɗu a club. danna kira yayi, sai dai har ta , katsai bata, dauka ba , tsaki ya ƙara ja, gaskiya yarinyar nan , ta gama dashi. opay din sa ya shiga, ya tura mata 50k , daman da ace sun kwana tare 200k zai bata, yana gama, tura mata , ya ajiye wayar sa, yana kwanciya akan gadon hotel din. wayar sace tayi ringing da sauri ya dauka ganin, sunan matar sa , yaja dogon tsaki, shi besan ma dalilin da ya saka yake ci gaba da zama da , wannan jakar ba... ɗagawa yayi yana daka mata tsawa tare da cewa lafiya kike kirana ina gurin aiki...? jikin ta ne yayi sanyi cikin raunin murya tace '' abban su amatu, har yanzu fa, bamu ci komai ba , rancen da nake ne ma yau na nema ban samu ba.., tsaki yaja yace '' to nima ba ayi mana albashi ba , tun ruwan shayin da abokina, ya kawo min muka sha ban ƙara saka komai a' ciki na ba,, yana gama fadar haka ya zare wayar daga kunnen sa, ya kashe ajiye ta , yayi akan gado yana jan , dogon tsaki. POLICE STATION. ba ƙaramin mamaki, sukai ba. lokacin da suka ga yan sandan sun ce , su tafi, sun sake su, Tahir yace '' Zahid kaga ikon Allah ko..?,, da yake bamu da hakkin'sa gashi Ubangiji ya saka mana , ita daman rayuwar nan. idan baka da hakkin mutum, to wallahi ba jimawa Ubangiji zai maka sakayya dai-dai, da abin da , ya , aikata maka Allah ya ƙare mu da son annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama., ZAHID da jikin sa yayi sanyi yace '' amin ya Allah.,, Abdulraman yace '' amin ya Allah, amma dai wannan mutumi anyi dan akuya, wallahi, baya ne shi man ta alkairi., Asim yace '' tsayuwar me muke yi anan..? kun san dai ba za mu samu mota ba, tafiya suka fara ba wanda ya cewa, da wani qala har suka isa gida buga kofar gida ZAHID ya fara yana fatan Allah ya saka Nabeel ya zo ya buɗe mai.. Su abdulraman, suna tsaye a bayan sa , sai jin salati sukai, ashe iya ce tazo, ta buɗe kofar, kallon su ta gama yi tana sakin salati tace '' yan nema sun ji addu'a sun sake ku, tun da wannan auta, ta faɗa min abin da yake faruwa na hau kan buzu gashi nan tun kafin aje ko ina sun ga , ba za su iya ba , sun sake ku, yasin na zauna ina yi musu me tsakuwa, wa ya isa ya ja da yar gidan malam jikar malam matar malam., ZAHID takaici ne ya ishe, shi. bece komai ba , ya raba ta , ya wuce su asim biye mata suka yi, har da shewa suna hira. yana shiga dakin sa ya zauna yana cije lips din sa, lallai zai yi maganin yarinyar nan,.wato da yace , kar ta faɗa sai da ta faɗa sai da ta nuna mai ita me kunnan kashi, ce. yana cikin wannan tunanin yaji shigowar su Tahir zama suka yi Tahir yace '' Allah ya shiryi areej, sai da ta faɗa, wallahi daman gudun tashin hankalin , da za su shiga muke yi, shi ya saka muka ce kar ta faɗa.., kwafa Zahid yayi yace '' Allah ya kai mu safiya zan yi maganin ta , yarinya kamar an yi mata wahayin magana, bata taɓa gani tayi shiru, sai ta , tofa, tata..., haba babban yaya ayi mata afuwa cewar abdulraman ya faɗa yana , kwanciya akan katifa. banza yayi mai. wannan kenan. Iya tana shiga cikin gida ganin kofar kowa a rufe sai, ta bawa zuciyar ta , hakuri ta , shiga daki ta kwanta , bacci. Flash back bangaren juhud kuwa tana fitowa cikin Sa'a , ta sami abin hawa, shiga tayi ko ciniki ba su yi da shi ba , ta ciro wayar ta, tana dannawa cikin kwanciyar hankali.. ke dan uwarki kawo wayar nan , kamar daga sama taji wannan magana. da yake ba , ita kadai bace a kwai wani a cikin napep din. ko ɗar ba taji ba , ta ɗago kanta, ta kalle'sa, ta haɗe rai tace '' dan uban ka , ba zan bayar ba , uban ka ne ya siya min...?,, mari ya kifa mata, da sauri ta sauka daga napep din ta fita a kuje, ganin tayi cikin loko kar su, shiga su jawa kan su, suka hakura. da kafa ta , ƙarasa gida buga gidan su ta fara yi, jin sa a kulle taja ƙaramin tsaki ta buɗe jakar ta , ta ciro key,, buɗe kofar tayi ta , shiga tana rufewa, hijabin ta , ta cire tana jan dogon tsaki, domin ta fara zargin mama bata gidan, ta kira ta , ita kuma gudun fadan mama sai ta kasa ɗaga wayar ta, ta mai da jaka ta , tawo ashe ma bata gidan.. tana zuwa kofar da zata sada, ta da parlour su, taga takalmin hajiya rukayyah. ranta ne ya ƙara ɓaci , domin tasan zuwan matar nan ba alkairi bane shiga cikin parlour tayi tana turo baki.. washe baki hajiya rukayyah tayi tana cewa yauwa faduwa ta zo dai-dai da , zama ga yar albarkar nan ma ta dawo. zo nan ya'ta ga , guri nan ki zauna. zama tayi tana haɗa ran ta , tamkar anyi mata albishir da yau zata mutu. kama haɓar ta , tayi tana cewa saki ranki mana yar albarka.. da sauri mama ta kalli gefen fuskarta, tace '' juhud wa ya mare ki..?, juhud tace '' yan kwacen waya, na haɗu su , Allah ya rufa asiri basu, kwace min ba na fita a guje ban da mari , ba abin da sukai min..., Mama tace '' Ubangiji ya kiyaye gaba.., Amin juhud tace , tana kallon hajiya rukayyah. Hajiya rukayyah tace '' hice ko kin dauki number napep din,...?, juhud tace '' dakyar fa, nasha,, to Ubangiji ya kiyaye gaba ya'ta daman wata magana nazo da ita ,ta alkairi da fatan ba za kiyi fatali da ita ba. cewar Hajiya rukayyah. cikin zuciyar juhud ta ayyana cewa anzo gurin daman tasan ruwa baya tsami banza tace '' to ina jin ki..,, yauwa ɗiya ta , yar albarka, daman wani Alhaji ne , ya ganki yana son ki, yana da kudade a a hannun sa ke kanki zaki huta muma, mu hutu., wayar ta , ta ciro ta miƙo mata , Juhud, amsa tayi, bata ce komai ba kurawa fuskar mutumin ido tayi, miƙa musu wayar'tayi. ta miƙe zata , tafi mama tace '' juhud wannan wanne kalar iskanci ne..?, juhud tace '' mama bazan iya auren sa ba, be yi mini ba , kallon sa ma da nake yi amai yake neman sani., Hajiya rukayyah da ta fara fusata tace '' amai kuma ana zaune qalau.?, yes amai juhud ta faɗa tana shiga dakin ta , domin a gajiye take , bata da lokacin wa'yannan maganganun, aure ne ba yanzu, za tayi ba kwanciya tayi akan gado ta ƙurawa ceiling ido. tabbas tana kaunar Zahid sai dai ba zata kashe kan'ta ba , ta raya shi, saboda , bashi da kudi aiki kuma yaƙi samuwa , Allah ya sani bata, kaunat talauci da , duk wani abu da zai haɗa ta , da talauci dan haka dole ta nemi mafita , duk da a yanzu aure baya gaban ta , to tana samun abin da ake yi da aure me za tayi da aure tarin ciwon kai, haka kurum wani ya dinga juya , ta ina ba zata iya ba. da wannan tunanin bacci yayi awan gaba da ita. ba tare da , tata shi tayi wanka ba , Parlour kuwa jummai Dubai ce , tace '' kinga tun da juhud tace , bata so to wallahi Allah, ba zata so mutumin nan ba dan haka , kawai mu hakura, tun da Alhamdulillah dukiyar nan tana samun iya dai-dai gwargwado.,, Hmmm amma wallahi yarinyar nan taɓa tan rai. cewar Hajiya rukayyah. Jummai Dubai tace '' a haba karki damu Ubangiji ya bata wanda zuciyar'ta, zata amince dashi wanda ya kwanta mata arai.., amin ya Allah, hajiya rukayyah, tace tana tashi tsaye. Hajiya jummai Dubai tace '' badai tafiya ba...?,, zaro ido tayi tace '' wai rufan asiri haka kurum na haɗu da yan bana bakwai su karya min kafafuwa dakin juhud zan shiga na kwanta.., Cewar hajiya rukayyah. jummai Dubai tace '' wallahi kuwa ni yanzu zan fita.., Hajiya rukayyah tace '' a dawo lafiya aike a mota za a kai ki, kina cikin A.C wallahi kin ji dadin ki wannan alhajin ba ƙaramin kudi yake kashe miki ba.. kaɗai bari ba dai ke kin tsaya sai mace ba , ni nama rasa me kuke ji wallahi, ko da yake kowa akwai kiwon da ya karɓe shi. cewar jummai Dubai. Hajiya rukayyah tace '' wallahi kuwa.., ta ƙarashe maganar ta , nata shiga dakin juhud ita kuma ta fita tare da rufe musu kofa... kai kace wata budurwa ce , tafiya take tana rangwada Alhaji saminu sakar baki yayi yana kallon ta, gaba ki ɗaya ta gama tafiya da imaim sa. da yake murfin motar a buɗe yake shiga tayi tare da kashe shi da wani irin kallo tama rufo kofar. ji yayi tamkar ya rungume ta ya mai da ta ciki ba me iya kallon ta , sai shi. tana gama rufe kofar , driver ya fara tafiya riko hannun sa tayi tana mai fari da ido tace '' ya hajj barka da wannan lokaci..., kiss yayi mata ya cire bakin sa yace '' barka dai abar kauna ta.., murmushi tayi. tana yi mai wani irin kallo. me tafiya da ruhi da zuciyar mutum. cikin gida kuwa hajiya rukayyah tana shiga ta cire mayafin ta , ta kwanta a kusa da jiuhud , ƙurawa kirjinta ido tayi da yake doguwar riga ce a jikin ta , atamfa kuma ɗinkin da akai mata me irin bayyana jiki ne ,ga dai shi nan kaya , ta saka amma marabar'ta da tsirara kalilan ne. ta dade tana turawa juhud kalaman soyayyah, amma sai ta kalla tayi banza da ita. limshe ido tayi, ta ɗora hannun ta akan kirjin juhud tana matsawa a hankali juhud da yanayin yayi mata , dad'i domin a lokacin mafarki take , suna tarawa da ZAHID domin ba wanda take burin, su kasan ce dashi sama dashi, tana nuna mai sai taga be ma fahimci yaren ta ba , kawai sai ta hakura, saboda tasan idan ta , takura kwaɓar ta ce , za tayi ruwa. sau tari takan yi tunani , bawai son sa take ba sha'awar sa take kyakkyawa ne na bugawa a jarida, zai fitar da ita kunya, tana da yaƙinin ko a bangaren auratayyah zai kasance jarumi., ganin yadda take bata hadin kai domin bata hanata abin da take mata ba sai ta, zuge mata zip din rigar ta , ta kashe fitilar dakin. duhu ya mamaye hasken da yake cikin dakin, itama cire, kayan ta tayi. ta kwanta a jikin ta, tana sakin wata iriyar ajiyar zuciya tare da manna kirjinta, dana ta. juhud da ta fara fahimtar mace, ce ba namiji ba da sauri ta farka tana ture hajiya rukayyah. hajiya rukayyah ta ƙara kamo ta tana cewa Please ko kaɗan ne ki bari na samu nutsuwa dake. Juhud ji tayi tamkar ta sharara mata mari gaskiya wannan matar bata da hankali idan bin matan za tayi, taje tabi masu aji mana nono duk ya fara saki kamar slippers wanda ya fara mutuwa, saboda saka shi da ake yi duk sun bi sun yi sharaf sharaf ashe daman bra take sakawa push-up ' ita ke ɗago mata su, su tsayayya tamkar wasu zakarun da suke faɗa. ganin tayi shiru tana kallon ta , bata fahimtar kallon da take mata , da yake dakin duhu ne dashi, sai take zaton, ta amince matsa mata breast ta fara da , sauri ta , ture hannun ta , cikin bala'i tace '' wallahi rukayyah wahainiyar ki, ta kiyaye rama ta , ashe daman ke dabba ce ina kallon ki a matsayin uwa ashe ke ba wannan kallo da ki ke min ba to wallahi idan zan bi mata , bazan iya bin karya ba tsohuwar guzuma ki bari ki fara gyara lungo da sako, ki tada komaɗa wa'yannan nonuwan da sukai ƙasa, ki tada su, suyi sama. '' jikin hajiya rukayyah ne yayi sanyi ta kamo hannun juhud tace '' wallahi kallon ya'nake miki, ki tausaya min ko kaɗan ne nayi.., juhud ranta ne ya ƙata ɓaci tace '' waike rukayyah baki da zuciya ne..?,, Hajiya rukayyah tace '' wallahi in dai akan ki ne bani da ita,, juhud tace '' na shiga uku, a'a wannan zunubi ba dani ba , ke waya faɗa miki ina bin mata da zaki zo min da wannan maganar..? to wallahi Allah tun kafin na tuno miki asiri gurin mama ki fice min daga, daki.., jikin Hajiya rukayyah ne yayi sanyi tace '' to,, tashi tayi ta fita daga dakin. juhud da sauri ta , tashi ta rufe kofar ta , ta dawo ta kwanta tana sakin ajiyar zuciya, bata mai da rigar ta ba sai ta ƙarasa cirewa ta ja blanket ta kwanta. wannan kenan HOTEL POV JUMMAI DUBAI. driver ne yayi parking a gaban hotel din da Alhaji saminu ya kama. da sauri jummai Dubai ta kalle sa tace '' ya hajj yau kuma a hotel za mu sauka...?,, Alhaji saminu yace '' eh wallahi babban dana ya dawo daga Ingila so, a wannan gidan yake sauka, saboda baya son takura,, Hajiya jummai tace '' to shikkenan babu damuwa nan din ma yayi, amma mu dubu ko ina , saboda kasan wasu, suna saka Camera musamman ma kai da kake dan siyasa, ni kuma yar kasuwa sai ya zame mana matsala.., wata muguwar dariya yayi ya miko mata hannu suka tafa yace '' gaskiya hajiyar shedanu ba ƙaramin kaifin basira kike dashi ba , kwata kwata ban yi wannan tunanin ba , ni da nake son fitowa takarar gwamna kiris ake jira ayi min sharri domin a ɓata kuri'a ta kai juya kai ni gidana da yaka Lamido road.,, driver nasan juyawa yayi yana yacewa to shikkenan Alhaji. Hajiya jummai Dubai tace '' ya hajja nawa ni kaɗai..., wallahi bafi da karfi domin nidin naki ne kankana uwar ruwa, ana taba ki, kiyi ambaliyar ruwa kefa duk abin da na baki a duniya wallahi Allah ban biya ki ba , domin ba ƙaramin dad'i kike saka ni naji ba i love you so much. cewar Alhaji saminu. dariya tayi tace '' Allah ko ya hajj...?, wani kallo yayi mata yace '' ina hawa mulki duniyar karuwa da yan film ba ƙaramin dadi za suji ba domin zan jiƙa ku, barin ke da kike jakadiya a masana'antar shirya finafinai ki, sasu, su baza min uban campaign ina hawa tukuicin da zan baku na dabam ne..,, hajiya jummai Dubai tace '' baka da wannan damuwar amma ni abin da nake so tun kafin ka hau mulkin nan muyi aure kaga na ƙara zama mallakin ka , kai kaɗai, Alhaji saminu yace '' ke wanne aure ai wannan rayuwar tafi dad'i, ke yanzu kina wayayyiyar mace , sai kuma ki dinga zancen aure..? me makon kiyi min zance na baki makudan kudade ki tafi kasar waje ki bunƙasa kasuwancin ki gaskiya na raina wayon ki..,, kan Hajiya jummai Dubai ne ya ƙara kumbura tace '' kuma fa haka ne ya hajj abin kauna ta..., TSUMMA MAKUNSHI CUTA Ina meson logo ko invitation card To ga dama ta samu Werleedert graphics design ta zo muku da graphic design na ban mamaki Invatation card VEDIO invatation Logo Banner Poster Menu Acount sticker Graduation stickers Business sticker Save the date Business flayer Birthday flayer Engagement Event program invatatin Walimah invatation Wedding invitation Vedon invatation Zaku neme ta a kan wannan number +234 901 257 6569 ____________________________ _________________________________ Episode 5 Washe baki yayi yace '' ato ke dai Allah ya nuna mana lokacin zafa kuji dadi wallahi za kuyi ɓarna da dukiya yadda ranki yake so.'' Hajiya jummai Dubai tace '' Allah ko ya hajj to Ubangiji ya nuna mana lokacin.'' ta ƙara she maganar ta, tana riƙe mai hannu murmushi yayi mata , ta mai da mai da martani, tana yi mai wani irin killing smile me kashe zuciya da gangar jiki. gaban wani katon mansion suka tsaya, horn driver yayi. da sauri security din gidan suka buɗe ƙatuwar gate ɗin. a guje ya shiga cikin gidan, gida ne me uban yalwa sai mota ashirin tayi parking ba tare da wata, ta goge wata ba. HAJIYA JUMMAI DUBAI da kallo kurum take bin ko ina tana mamakin irin dukiyar Alhaji saminu dole ta ƙara zuwa gurin malam gobe da nisa ya ƙara mallake mata shi, ta yadda ba zai iya guje mata ba , ya sakar mata bakin aljihu. dafa ta yayi yana shafa fuskar ta yace '' abar kauna tunanin me kike yi..?.'' Alhaji saminu ya tambaya cikin kulawa. da sauri tace '' a'a bakomai wallahi mu fita ko.?.'' Hajiya jummai Dubai ta faɗa ɗi haka tana murmushi. Alhaji saminu yace '' okay babu damuwa?.'' driver ne da ƙansa ya buɗe mata murfin mota, ta fito kitso da akai mata na ƙari ta mai da baya tana yafa mayafi a ƙafa ɗa tana tafiya dadɗai, sai girgiza rusa rusan nonuwanta, take ita a la dole ga yan mata nan. tare da girgiza kugu, hakan kuwa ba ƙaramin sumar da Alhaji yayi ba , tamkar wani soko haka yake bin ta da kallo har suka isa hamshaqin parlour sa. wanda ya gaji da haduwa ta ko ina babu bakosa kai kace , kana hadaddiyar daular larabawa. zama tayi akan kujera wani irin sanyi da laushi ne suka rasa mata gangar jiki da ɓargo. hannun sa ya ɗora akan kafadar ta yace '' bismillah mu shiga daga ciki ko..?.'' tashi tayi tana cewa ato shikkenan mu shiga, ai Alhaji idan aikin kane babu gajiya babu sanyin jiki, Hajiya jummai Dubai ta fadi haka tana tafiya dadɗai tare da murguda duwawu. ganin dakin da ya shiga sai tabi bayan sa, samin sa tayi har ya fara rage kayan sa, taya shi tayi, tana yi mai wani kallo na ƙasan ido..?.'' hannun sa ya ɗora akan kugun ta yace '' hajiya wallahi da ace ina da ikon mai da ki ciki da na mayar da ke saboda kar kowa ya ganki sai ni kaɗai, ni dai fatana ba dai a bawa kowa wa'yannan kayan nawa, domin wallahi duk randa naga haka sai na kusan sumewa..?.'' bata bari ya ƙarasa zancen sa ba ta haɗe bakin su, wani irin kiss take mai cikin kwarewa ba ƙaramin rikita mai lissafi tayi ba. wanan kenan. Nanne nanne nanne. da sauri nanne ta , tashi tana mustsuka ido tace '' areej me ya faru..?, raka ni fitsari za kiyi areej ta faɗa, tana tashi tsaye. fitila ta kunna tace '' ungo tafi kije dakan ki..?.'' amsa tayi batai mata gardama ba , ta fita da gudun ta duk kuwa da tsoron dare da take yi, cikin rawar kai ta tura bayin tare da haske cikin bayan gidan da fitila. da sauri ZAHID ya tashi areej yarda fitilar tayi, ta zun duma ihu tare da rufe idanuwanta. a fusace ya kamo ta ya fito da ita ji yayi tamkar ya dauke ta da mari, ko ya samu sassauci a cikin zuciyarsa dan ma yana da yaƙinin ba , abin da ta gani, domin yana ƙoƙarin mai da wandon sa , ta shigo. har yanzu da ya fito da ita bata bude idon ta ba cikin kakkausar murya yace '' areej me kika gani..?.'' ya fada haka ne domin yana son ƙara tabbatar da zargin sa. a hankali ta buɗe idon ta , ta kalle sa tace '' au daman kai ne ba aljani na gani ba..?'' wani sanyi ne yaji ya shiga zuciyar sa, har izuwa babban ɗan yatsan sa hamdala yayi a ransa a fili kuwa sai yace '' a'a abin da yafi aljani kika gani..?'' da sauri tace '' yaya dan Allah karka tafi ka tsaya nayi fitsari amma fa ka rufe idon ka, domin ba kyau wani ya kalli wani ba kaya, yauwa yaya yaushe ka dawo sun sake ka kenan..?.'' dafa ƙansa yayi yace '' karki cika ni da surutu maza kiyi ina jiran ki..?.'' to dan Allah karka tafi. areej ta fadi haka cikin shagwaɓa. banza yayi mata , ya ɗora hannun sa akan bango. iyamu fitowar ta kenan wani murmushi tayi najin dadi dama tazo da zata rusawa Maryamu farin cikin'ta dagewa tayi ta zun duma ihu tare da kuru ruwa da sauri areej ta , tashi tsaye ko mai da pant din ta ba tayi ba , ta rungume ZAHID tana cewa wayyo Allah yaya ZAHID. Mutanen gidan ne suka fito ZAHID da yake kokarin raba jikin sa dana areej amma ta kankama sa iyamu kuka ta saka tana cewa Iya yau nake ganin tashin hankali ZAHID ya rasa wazai nema sai yar uwar sa, tare naga sun fito daga bayi. nanne ji tayi duniyar na juya mata , haka ma malam, aunty Jamila da mijin ta a lokacin suka shigo suna tambayar lafiya. ƙara maimaita abin da ta fadi tayi ZAHID saboda tsabar mamaki yama kasa musanta zargin ta da kallo kawai yake bin su areej da har yanzu nata jikin sa aunty jamila ce ta cire ta , daga rungume shi da tayi tana cewa a'a wallahi ko da ban gani da ido na ba ZAHID ba zai taɓa aika haka ba, Iyamu ta share hawaye tace '' haba jamila da ZAHID da AREEJ duk ya'ya na ne gyara kayan ka ai ba zai zamo sauke mu raba ba, laifina ɗaya da nayi ihu abin ne ya razana ni ya girmi ƙwaƙwalwa ta amma kuyi hakuri.?.'' ta faɗa tana kara rushewa da kuka. IYA tace '' ya'yi ɗin Allah ya sakaa kwance kika gansu turmi da tabarya kowa ya tafi ya kwanta bana son dogon zance, jikin kowa a sanyaye ya tafi nanne kasa rintsawa tayi kallon areej tayi da taka ta mutsu mutsu nanne tace '' areej me kuka yi a cikin bayi..?.'' turo bakin ta , tayi tace '' bafa abin da mu kayi cemai nayi ya tsaya nayi fitsari tsoro nake ji kuma a waje ma nayi, na shiga bayi sai naga yaya sai nayi ihu shi ne ya fito dani yana yi min faɗa fitilar ki ma tana cikin ban daki.'' shiru tayi ta koma ta kwanta a hankali bacci ya dauki areej nanne kuwa tama kasa bacci, iya aminta ta yarda da iyamu dan haka, bata zargi komai ba , duk da wani shashi na zuciyar'ta yana ƙaryata hakan saboda ta yarda da ZAHID ta amince masa amma sanin halin dan yau sai, Allah dan haka bata musa ba , Wannan kenan.. kamar yadda bacci ya ƙauracewa nanne haka ya ƙauracewa ZAHID ban da juyi ba , abin da yake yi lura da halin da yake ciki Tahir ya tashi yace '' ZAHID lafiya me yake faruwa..?.'' gyara kwanciyar sa, yayi yace '' bakomai?.'' Tahir yace '' a'a, kar mu yi haka dakai abokin kuka ba'a boye masa mutuwa, wata ƙila faɗa min da kayi shi ne samin sauki a cikin zuciyar ka...'' ZAHID yayi shiru yana sauraron sa, sai da yakai ƙarshen maganar sa, yace '' Tahir wallahi areej ta saka ni a matsala wacce har ƙarshen ruwata bazan iya goge wannan taɓon ba daga jiki na...?.'' tashi yayi zaune yace '' kana yi min bayani a dunkule ka fito fili ka faɗa min me ya faru..?.'' rintsai ido yayi ya soma bashi labarin abin da ya faru yaci gaba da cewa babbar damuwa ta halin da iyayen mu zasu shiga Tahir sanin kan kane ni babbar mace ma ban bi ba balle wannan da bata da komai idan na neme ta amfanin me neman ta zai min. cewar ZAHID. Tahri yayi shiru yana tunani can kuma sai yace '' gaskiya wannan matar bata kyauta ba daman kuma can tana da mugun nufi akan ka, saboda me dan taga haka zata tara mutane..?' amma yice ko ka musa kai magana..?'' ZAHID yace '' wallahi Allah Tahir magana ma na kasa yin ta gani nake kamar a mafarki abin nan yake faruwa ba zahiri bane.'' Tahir yace '' kash dama bakai haka ba hakan ne zai ƙara karfafa mata gwuiwa su, kuma su ɗauka gaskiya ne abin..?'' Hmmm Tahir gaskiya bata bukatar ado ko rantsai rantsai yau duk wanda yayi maka sharri, to ka ɗauka taki ya zuba maka wallahi koman daran da ɗewa ubangiji zai saka maka Cewar ZAHID. Tahir yace '' kuma Hakane Ubangiji ya fito da gaskiya..?., amin ya Allah Zahid ya fadi haka yana mai da kai ya kwanta. Washe gari. fitowa suka yi domin tafiya sallar asuba a soro suka hadu da malam da Nabeel gaishe da shi suka yi kamar yadda yake amsa musu haka ya amsa musu fuskar sa bata nuna damuwar, komai. tare suka tafi masallaci bayan an idar suka fito, da sauri Malam ya juyo jin kiran dan uwan nasa gaisawa sukai cikin faɗa Alhaji bilyamin yace '' wato bukar ka nuna min iyaka ta ina cewa danka ɗana ne har ni zance yazo da dinga kai yarinya ta makaranta yace ba zai iya ba good yayi kyau to wallahi abin da nake baku kuke rainawa na dena kuje can ku ƙarata ai daman tsiyar talaka kenan an faɗa muku kudin nawa kwaso su nake da zan dinga diba ina baku..?.'' malam kasa magana yayi sai bin dan uwan nasa yake da ido zuciyar sa namai wani irin tafasa buɗe baki ZAHID yayi zai magana malam yace '' ka tafi ba ruwan ka..?.'' Alhaji bilyamin yace '' dan Allah bukar barshi da wallahi yau sai na nuna mai, shi ba kowa bane ba wato kai na mara kunya ko...?.'' hmmmm sai ya ja kwafa yana saɓa babbar riga da sauri ya shiga cikin gidan har yana neman tun tuɓe. Malam da ZAHID bin bayan sa, suka yi su abdulraman suka tafi gida shiga cikin gidan sukai babu kowa a tsakar gidan. ZAHID shiga dakin mahaifiyar sa, yayi bakin sa dauke da sallama. Joud amsawa tayi tana gaishe dasu. Zama Zahid yayi yana amsawa yace '' ina nanne..?'' tana daki ta bashi amsa tana ci gaba da yin guga. shiga cikin dakin yayi ya durƙusa ƙasa yace '' nanne ina kwana.., nanne ciki ciki ta amsa mai areej da sauri tace '' yaya ina kwana..?.'' wani irin soya zuciyar sa, ta shiga yi sakamakon amsa mai da mahaifiyar sa tayi ba yadda ta saba amsa mai ba. kasa amsawa areej yayi ya cije lips din sa na ƙasa ya kasa ko da motsi ne. Nanne tashi tayi tana kama hannun areej domin tayi mata wanka kar lokacin makaranta ya kure. jikin sa a sanyaye ya tashi ya fito. IYA da take cikin daki ta kwala mai kira, amsawa yayi tare da shiga cikin dakin yana cewa Iya ina kwana IYA tace '' rasa kunya ba zan amsa gaisuwar ka ba yanzu har wuyan ka ya isa yanka da wannan yawon ɓaɓal ɗin da kake ba gwara ka tafi gidan kahun ka ba , kai ma ka samu na sakawa a bakin salati amma da yaje kai dan taura ne uban girman kai ba za ka yi ba...?.'' Zahid bece komai ba domin idan yace zai magana tofa, ba abu ne me kyau ba zai fito daga bakin sa dan haka shirun nasa yafi alkairi. IYA tace '' tashi dan nema daman nasa ba zakai magana ba wannan miskilancin naka yana ban haushi kirawo min sani da bukar ka kirawo min sunusi.., tashi yayi bece komai ba , ya fita, kai tsaye gidan aunty jamila ya shiga yana sallama amsawa tayi tana fitowa daga kitchen tace '' Zahid kai ne da sassafe Allah ya saka lafiya ba wani abu kuma ta ƙara cewa ba..?.'' ZAHID yace '' a'a bakomai ina kwana.., ajiyar zuciya ta sauke tana amsa gaisuwar sa. ZAHID yace '' kahu sunusi yana nan..?.'' Aunty Jameela tace '' a'a baku haɗu dashi ba aikuwa ce min yayi ya yafi gaishe da iya nima yanzu zan zo gaishe da ita., zahid yace '' to bara na faɗa mata., ya faɗa yana juyawa be jira me zata ce ba , fita yayi ya shiga cikin gidan su yana saka Ƙafafuwan sa a dokin kofar iya ya kusan sumewa saboda tashin hankalin da yaji. Mu hadu a arewa book domin jin yadda zata kaya 08141785374 littafin nan dubu daya ne tafiyar telegram. 8141785374 amina alhsan Muhammad opay Ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374