Muhammad Kabeer Documentation workshop 08160112181 [6/27, 08:59] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Pure Moment of Life Writers (p.m.l)* *Happy Sallah to all Muslims ummah over the world* *Dedicated to my Gorgeous Sister,Fatima Abubakar Radda,always you are looking fine,once again happy Sallah to you and your family.* Bissimillahi rahmanir raheem. *page 1-2* Ruga ce ta Fulani me d'auke da yawan jama'a Dan Rugar tana da girma sosai. Wannan Rugar ba a ko ina take ba se a cikin Garin Gwongola,mutanan cikin wannan Ruga suna da al-adu kala-kala,kuma koda wasa basa sake da al-adun su Sun d'auki al-adun kamar ibada. Malam Audu yana d'aya daga cikin mazauna rugar shida zuri"arsa gaba d'aya. Malam Audu tsohone d'an kimanin shekaru 77 yana da mata d'aya Gwaggo Uwani da yara guda uku duka maza,Hamisu shine babba seme bimasa Shu'aibu,se k'aramin su Mahmoud wanda ake kira da Mudi. Gaba D'ayan yaran na Malam Audu sunyi aure Sun hayayyafa ma kuma suna zaune tare dashi a Gida d'aya, shiyasa akewa Gidan kirari da Gidan gandu,gaba d'ayan su babu wanda yayi karatun Boko acikinsu dagasu har matansu sede na muhammadiyya sukayi. Baba Hamisu kamar yadda yaransu ke kiransa,matarshi d'aya mesuna Saude, da yara guda hud'u,duka maza na farin sunanshi Jamilu,se Uwaisu,Nura,Usman.inna Saude macece mara mutunci ko kad'an bata ragawa duk wani mahaluki A cikin Gidan, shiyasa gaba d'aya Gidan kowa yake jin tsoronta harda shi kanshi Mijin nata yana under her control,be isa yayi abinda ba itace tasashi ba shiyasa kosu sirikan nata tsoronta sukeji, sabida gwanace gurin iya Bin bokaye da y'an bori. Shu'aibu shima matarsa d'aya Furera da y'ay'a biyar biyu mata uku maza,Shafi'u shine babba se Muntari, se Hauwa,Ramatu,Suwaiba,Hauwa da Rahmatu sunyi aure tun tuni,sabida a al-adar Garin yarinya dole sede ta fara jinin al-ada a gidan mijinta, inko aka bari tafara a gidansu to ba makawa y'ar iskace,shiyasa daga shekara goma ake aurar dasu.Inna Furera irin matan nanne da ake cewa bakin ganga,munafukace ta ajin farko, tasan duk Wata hanya da zata bi ta hada mutum fad'a da Inna Saude sabida wannan halin natane ma yasa suke d'an d'asawa da ita Sauden. Baba mudi ma matarsa d'aya me suna Zainabu da y'arsu guda d'aya me suna *UMMU AYMANA*.Zainabu Mace ce me sanyin Hali gata da hak'uri da kawaici,ko kad'an bata da d'aukar lamuranta da zafi,anashi b'angaran Baba mudi shima baya d'aukar rayuwa da zafi shima yanada hak'uri sosai da kawaici. A al-adar Garin yara mata basa zuwa makarantar Boko, sabida acewarsu b'ata tarbiyya takeyi shiyasa kosu mazan basu d'auketa da muhimmanciba, sunfi maida hankali wajan neman kud'insu da kiwo da noma. Baba Mudi yafi kowa rufin asiri a Gidan,dan a Rugarsu kaf babu me arzik'insa sabida d'an kasuwane, har fita yake zuwa wasu Garuruwan ya siyo kaya yazo ya siyar a rugar tasu,ganin hakane yasa mahaifinsa malam Audu k'ark'ashin jagorancin Inna Saude.ya d'oramasa nauyin ciyar da Gidan gaba d'aya da d'aukar d'awainiyar komai na Gidan, wannan hukunci beyiwa Mudi dad'iba,dan inde yaci gaba a haka wataran shima nashi k'arewa zasuyi Amman dayake shi mutum ne me kunya da kawaici Uwa Uba kuma biyayya,shiyasa ko a fuska be nuna yaji haushiba. Tun daga wannan lokacin ko Maggi za'a siya sede a turo gurinshi,suko sauran y'an uwanshi sun mik'e k'afa basa komai sede ya je ya nemo ya kawo adafa suci, kuma ko godiya bazasuyi masa ba, sede ma su zageshi gaba d'aya haushin shi suke ji, hassada suke masa ba kad'anba. Ummu Aymana tun tana jaririya yarinyace kyakkyawa,tana kama da mahaifiyarta sosai gata da hak'uri tun tana k'arama,wannan kyau da Allah yayiwa Ummu Aymana shine yajamata bak'in jini acikin Gidan nasu ko kad'an babu mesonta se Iyayanta,dan har kakan ninta tsoron kulata ma sukeyi sabida kar Saude taji haushi,shiyasa duk inda ta shiga kyarar ta akeyi acikin Gidan, sab'anin wajan Gidan kowa sonta yakeyi. Ummu Aymana idonta irin blue eyes d'in nanne, hakanne yasa y'an gidansu suke kiranta da mayya, sabida acewarsu mayu ne kad'ai keda irin idonnata.har turaran mayu Inna Saude tasa adunga Yi a Gidan wai karta lashe musu kurwa. Wannan al-amari yana k'ona ran iyayanta, sede basu da yadda zasuyi da Sauden sede su had'ata da Allah,kullum Inna Zainabu setayi kuka a d'aki gameda wulak'ancin da akema y'arta a Gidan. Muje zuwa Maman Yusuf. [6/27, 18:45] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Pure Moment of Life Writers (p.m.l)* *page 3-4* Itama Ummu Aymana abun na damunta Amman kasancewarta yarinya shiyasa batasa abun a ranta ba kamar mahaifiyarta. Ko shi Baba Mudi sede ya dunga rarrashin Zainabu dan dole bawai dan shima abun be damunsa ba. Haka suke rayuwa a cikin Gidan batare da cikakken y'enciba,komai se in Saude ce tace ayi sannan a keyi,ta kasa ta tsare. Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah yanzu Umma Aymana shekarar ta Tara saura shekara d'aya a aurar da ita,ga maneman auranta ta ko'ina a cikin Garin kowa sonta yake,ita ko bata masan bidirin dasukeyi a kanta ba bare abin ya dameta. Shi ko mahaifinta zuba ido yayi akan masu neman auran y'ar tashi, domin ya zab'o mata wanda zefi kulawa da ita, wanda har zuwa yanzu be samu ba,dan kowa ya duba se yaga yana da matsala. Hakanne yasa y'an uwanshi suka fara gulmar sa, wai ya tsaya ruwan idone shi yasa yak'i zab'a mata mijin a cikin jerin masu zuwa neman auran nata,shide nashi ido tsakaninshi da su be cemusu k'ala. Inna Saude ce zaune ita da Jameelu suna hira,kai da ganin yadda suka zauna suka natsu kasan zancan me muhimmanci ne, matsawa nayi dan inji me suke cewa. "kai d'annan barifa kaji ingaya maka nifa ba yarinya bace nasan duk abinda nakeyi,dan haka nide umarni na baka, nace kafito neman auran Ummu Aymana ko kuma ranka ya b'aci". Rai a b'ace Jameelu ya fara magana. "Haba Inna so nawa zan fad'amiki ni hanne y'ar Gidan me unguwa nake so?kuma ita wannan d'in da kike so in aura meye hujjarki taso na aureta,?bayan ke ce kika cemana mayya ce.wato ni na aureta ta lasheni kenan ba damuwarki bace?". Wata arniyar dariya Inna tayi sannan tace "K'uruciya dangin hauka,wato bazaka fahimce ni ba sena maka bayani,to ba komaine yasa nace ka aureta ba sedan dukiyar mahaifinta, kaga da zaran ya mutu itace zata gajeshi mu kuma semu k'wace a hannunta cikin sauk'i ,Amman ana maka magana kana wani k'in amincewa, zancan maita kuma wannan hirace nice kawai na fad'i hakan dan a tsaneta badan wai mayyar bace ba". Tunda Inna tasoma yimasa bayani bakinshi yak'i kulluwa gaba d'aya murna da farin cikine ya lullub'eshi cike da nishad'i ya mik'awa Inna hannu suka tafa sannan yace yana dariya. "wato Inna shiyasa nake sonki, nayi imani da ace ba kece mahaifiyata ba da tuni rayuwata ta k'are a masallaci, Amman da yake nononki nasha ganinan ina abinda nakeso,gaskiya na gamsu da wannan shawarar taki kinga nima kwanannan za'a fara Kirana ina amsawa sabida kud'i sun zauna". Dariya Inna tayi shima dariyar yake daga bisani yace yana mik'ewa tsaye alamar ze tafi. "barima kiga naje na fad'awa Baba Mudin tun yanzu dan kar wani yamin shigar sauri" "To maza d'an albarka ay dama da zafi-zafi ake dukan k'ota dan haka kaje kafad'a masa kuma nima anjima zan tara kowa na fad'a masu inga shegen da zece ba hakaba" Ficewa Jameelu yayi fuskarshi d'auke da fara'a kai tsaye shashen su Baba Mudi ya nufa da yake Gidan shashi shashi ne.koda ya isa samun su yayi suna cin abinci ko sallama be yi musu ba ya samu guri ya zauna yana murmushi. Baba Mudi ne ya lura maganace takawoshi dan haka tambayar shi yayi da cewa. "Jameelu na Lura akwai magana a bakin ka dan haka ka sanar dani damuwar ka in ina da hali zan taimaka maka" Wani murmushinne yasake kubcewa Jameelu najin dad'i, dan haka hankalinshi kwance yace. "Baba dama bakomai bane illa iyaka inason auran Ummu Aymana" Cikin tashin hankali Zainabu ta amshi zancan da cewa. "Allah yayiwa y'ata tsari da samun mijin aure irinka,wlh bazaka tab'a samun ta ba matuk'ar ta jikina ta fito, wlh kasha k'arya daga kai har wacce ta turoka,in Ummu Aymana ta aureka tace ta auri wa?mazinaci,d'an giya,koko barawo,kokuma me wasa da sallah azumi senaga dama? Wlh tun wuri kasa wa ranka hak'uri dan wlh bazaka auri Ummu Aymanaba" Tak'arasa zancan tana huci wanda ba Baba Mudi ba shi kanshi Jameelu mamakin hakan yakeyi dan basu tab'a tunanin zatayi magana ba. cikin fushi shima Baba Mudi yafara magana. "Wlh Jameelu duk da munanan halayanka yau da ace kaine dan ra'ayin kanka ka fito kace kana sonta wlh zan aura maka ita Allah ze shiryeka a hankali. to Amman yanzu nasan turoka Saude tayi tunda inda sak'on naka ne da kajima da shaidamin damuwarka, dan haka wlh bazan Aura maka Ummu ba sede duk abinda ze faru ya faru dan haka katashi ka b'acemin da gani" Cikin azababben fushi Jameelu ya fara magana cikin muryarsu ta k'auraye. "Ayyade Alhaji da Hajiya ay shi rikicin duniya Dame rai ake yinshi dan haka ku kwantar da hankalinku shi kunu labarin wuta yake ji shiko tsire zahiri ya gani mu zuba ni da ku". Yana gama magana ya sa kanshi yabar shashin nasu zuciyarsa na k'una. Suko basuyi mamakin d'ibar albarka da Jameelu ya musu ba sabida inda sabo Sun saba abinda yafi hakama tsaf ze iya. Sabida Jameelu ba ya jin magana,sata a gurinshi ko b'era albarka,gashi fasik'ine neman mata a gurinshi kamar masifa,sallah ko se yayi sati guda bekai goshinshi k'asa ba,haka shima lokacin azumi ba kullum yake yiba se.yaga dama. wannan kenan Muje zuwa. Maman Yusuf. [6/28, 10:23] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Pure Moment Of Life Writers (p.m.l)* *page 5-6* Bayan fitar Jameelu Zainabu kuka tasa ta fara magana. "Wlh Malam hak'urina ya k'are, bazan tab'a zuba ido ina kallon zalincin da ake son yiwa Ummu ba wlh,sede duk abinda ze faru ya faru Amman wlh bazan yarda ba". Ta k'arasa zancan cikin kuka. Cikin sigar rarrashi Baba Mudi yace. "Haba Zainabu yaya da hankalinki zaki maida kanki yarinya?cemiki aka yi nima zan amince da wannan had'in gambizar? ay kinsan nima ba yarda zanyi ba, Ummu y'ar muce dole mu tashi mu kare mutuncinta dan haka kisa ranki a inuwa nima ban amince ba kuma se iya inda k'arfina ya k'are matuk'ar ina raye wlh". Murmushin jin dad'i ne ya bayyana akan fuskar Zainabu. Dariya Baba Mudi yayi sannan yace. "Oh Allah ya kawomu zamani wai Zainabu ce take kuka akan kar a cutar mata da y'a,wacce da kina kallo zata fad'i ba zaki tare ta ba dan kunyar y'ar fari". Ya k'arasa zancan cikin sigar tsokana. Rufe fuska tayi tana dariya daga bisani ta mik'e da gudu ta shige d'aki,dariyar shima yayi sannan ya bita d'akin. Shi ko Jameelu daga fitarsa d'akin mahaifiyarsa ya nufa cikin fushi,yana shiga ya fara zage-zage,da kyar Inna Saude ta samu yay shiru ya fad'a mata abinda ya faru,ay bata kai gajin k'arshen bayanin ba tayi kukan kura ta fito tsakar Gidan ta fara bala'i. "Yau za'a yi bala'i a Gidan nan, dan wlh yau sena ga uban da ya tsaya muku da har zaku iskanta min Yaro da raina ban mutu ba". Ay ilahirin mutanan Gidan kan kace me kowa ya taru a gabanta Amman banda Iyayen Ummu Aymana. Da kyar Malam Audu ya samu tayi musu bayanin abinda ya faru. "In banda su tsinannu ne taya dan Jameelu yace yana son y'arsu zasu hana shi sannan kuma harda rakiyar zagi da tsinuwa,to wlh bazan yarda ba dole Jameelu ya Aureta ko suna so ko basa so". Muryar Baba Mudi ne ya katse ta. "kinsha k'arya wlh kin kwana da yunwa, babu wanda ya isa ya had'a Aure tsakanin Ummu da Jameelu matuk'ar nine mahaifinta kuma ina Raye to wlh ke baki isa ba". inji Baba Mudi da yake k'ok'arin k'arasowa gurin shida Zainabu. Mamaki ne ya kama kowa dake gurin ganin ba halin shi bane. Inna Saude cike da bala'i taci gaba da magana. "lalle mudi wuyanka ya isa yanka har ina fad'a kana fad'a,to wlh kataka a sannu niba kanwar lasa bace,dan haka umarni ne na bada dole Jameelu ya Auri Ummu Aymana wlh". Inna Zainabu ce ta amshi zancan. "Tunda ke kika haifa mana ita ba,to wlh baki isa ba,kibar ganin ina miki shuru to wlh shuru ba tsoro bane gudun magana ce,Amman yanzu tunda kika shigo hurumin da ba naki ba dole kiji magana wlh" Inna Furera ce tasoma magana. "Amman Zainabu baki da kunya yanzu har Yaya Saude tana magana kina bata amsa? wlh baki kyauta ba". "kyale ta Furera so take ta nunamin ta haifi y'a d'aya kamar mayya, waya sanima ko itace ta cinye sauran kwayayan haihuwar?". Inji Saude ta fad'i tana hararar Zainabu. "Mun godewa Allah daya bamu y'a D'ayan da kike tada jijiyar wiya akan an hana D'anki Auran ta,da baki hangi mamora a tattare da ita ba da bazaki so Jameelun ya Aura ba". Zainabu ta bata amsa. Nande sukai ta fad'i in fad'a bame saurarawa wani,abun na Saude har mamaki ya dunga basu sabida k'arfin halinta nason yin iko akan abinda bata da iko dashi. Da kyar malam Audu ya samu sararin yin magana. "Wannan ba abin rigima bane Jameelu da Ummu Aymana duk abu d'aya ne, dan haka Gida be k'oshi ba ba za'a kaiwa na waje ba,tunda ya ganta kuma yace yana so to ko ba makawa se anyi wannan Auran". Kuka Zainabu tasa tabar gurin,shi ko Mudi tsayawa yayi ya fuskanci Mahaifinshi yace. "Baba y'ay'a amana ce Allah ya bamu kuma ze tambayemu game da amanar ranar gobe k'iyama,shi ya mana umarnin mu aurar dasu ga mazaje na gari, dan haka bazan yimaka biyayya akan wannan son zuciyar taka ba. Auran Ummu Aymana da Jameelu wlh baze yiwu ba Baba,sabida ba dan Allah suke son hada auran,ba ka gafarceni Baba yau zan bar maka Gidan ka da Garin ma baki d'aya nida Iyalina, na gaji da wannan zaman bautawa wannan tsinanniyar matar da batasan darajar kowa ba a Gidan nan". Ya k'arasa zancan yana nuna Saude. Malam Audu shuru yayi yana nazari akan zancan Mudi wanda yasan tabbas gaskiya ya fad'i. Ita ko Saude ashar ta shiga surfawa Mudi gami da shan alwashin aurawa Jameelu Ummu Aymana ta k'arfin tsiya. tsoro ne ya kama sauran y'an uwan nashi jin yace zebar Gidan, wanda Sun sani insuka barshi yatafi Sun kad'e dan haka dole ayiwa tufka hanci. Maman Yusuf. [6/29, 07:25] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Pure Moment Of Life Writers (P.m.l )* *page 7-8* Sannu a hankali kowa na gurin ya watse,itama Inna Saude dole ta koma d'akinta sabida wanda zatayi bala'in dasu suma sun bar gurin. Baba Hamisu da Baba Shu'aibu ne suka keb'e a k'ofar gida suna tattauna yadda zasu shawo kan Mudi yafasa tafiyar. "Shu'aibu nasani base ka sake maimaitamin ba,tabbas Saude ce taja komai,Amman ya kamata ka fahimta, Saude ba niba ma da nake Mijinta su Malam kansu tsoronta suke ji bata da dad'in sha'ani wlh". Baba Hamisu ya fad'a cikin sigar dake nuna abun na damunshi. "Yaya inaga wannan ba abun tada hankali bane, kamata yayi kaje ka sameta ku fahimci juna ka gano dalilinta nason Jameelu ya Auri Ummu Aymana inaga shine kawai,to kaga idan ka gano se kasan yadda zaka yi kaja ra'ayinta akan tabar maganar zuwa wani lokacin inaga zefi" Shu'aibu ya fad'i yana kallon Yayan nasa. Shurune ya biyo baya na y'an mintuna kana daga bisani Baba Hamisu yace. "Wannan shawarar taka tayi dan haka Bari inje in sameta dan mu shawo kan matsalar da wuri". yana kaiwa k'arshen maganar ya mik'e ya shige cikin Gidan. Shima Shu'aibu barin gurin yayi. Koda Baba Hamisu ya iske Saude a d'akinta har lokacin bata dena zage zage ba,jiki a sanyaye yayi sallama ya shiga d'akin. Bata amsa sallamar ba,shima kuma be damu ba ya sami guri ya zauna yana kallonta, yana tunanin ta ina ze faro mata zancan daya kawoshi, muryar tace ta katse shi da cewa. "Kai nifa bana son munafurci,daga ganinka akwai abinda kake son sanar dani Amman tsohon munafurcinka ya hana ka fad'amin dan haka kayi gaggawar sanar dani abinda ya kawoka kokuma katashi ka bani guri namijin hotiho kawai". Jikinshi har rawa yake ya fara magana cike da tsoro. "Ranki ya dad'e dama akan maganar d'azune, koni na goyi bayan Jameelu ya Auri Ummu Aymana,to matsalar anan shine kinji Ubanta yace zasu bar Gidan wanda in aka bari hakan ta faru kinga bazamu sami damar had'a Auran ba shine nazo na shawarce ki". Ya k'arasa zancan cikin matsanancin tsoro sabida besan yadda zata d'auki maganar ba. Ita ko shuru tayi tana nazari akan batun nashi, tabbas in suka bar Gidan burinta baze cikaba dan haka cike da gamsuwa da bayanin nasa tace. "Haka ne Hamisu to Amman taya ya kake ganin zamu shawo kan matsalar?Dan ni da cewa nayima zan kaisu gurin Boka na kan tudu yayimin maganinsu". Sosai yaji dad'in yadda ta bashi damar shiga zancan dan haka cike da kwarin guiwa yace mata. "ki ajiye batun Boka a gefe kibari mu basu dama in sunk'i amincewa to seki je gurin Bokan asan abinyi,Amman yanzu so nake nasan aynihin dalilin ki nason had'a Auran dan musan hanyar dazamu bi". Ba tare da tsoron komai ba tace "Sabida dukiyar Mudi Ta dawo hannun Jameelu". Baba Hamisu beyi mamakin zancan ba dan dama baya raba d'ayan biyu akan hakanne ta tada hankalin Gidan.. "Wannan tunani ne me kyau kikayi,to ki kwantar da hankalinki yanzu kibar maganar Auran sesun saki jiki akan maganar ta kwanta lokacin mu kuma mun gama shirya duk abinda ya dace mu shirya semu sake d'ago da maganar". Wata uwar shewa Saude ta saki dake nuna alamar taji dad'in batun na Mijin nata. "Gaskiya nagode da wannan shawara kuma zanyi amfani da ita Allah kuma yabamu Sa'a". Amsawa yayi da "Ameen" Anasu B'angaran Zainabu da Mudi kuwa tun komawarsu shashinsu Zainabu take kuka kamar Ranta ze fita akan hukuncin da sirikin ta ya zartar akan gudar y'ar ta, Mudi ne yayi k'ok'arin kwantar mata da Hankali da cewa. "Ki kwantar da hankalinki, wlh Ummu bazata auri Jameelu ba matuk'ar ina raye, kuma ko bayan Raina in kika bari Ta Aureshi ban yafe miki ba,dan haka na yanke shawarar gobe da asubar fari zani tasha in samo mota ta kwashe mana kayanmu mubar musu Garin gaba d'aya dan akan Ummu zan iya salwantar da farin cikina domin nata, dan haka kisa ranki a inuwa Mijin Umma kamili natsatstse nanan zuwa da yardar Allah". Dan dad'i Zainabu bata san sanda ta rungume Mudi ba tana masa godiya. Daga nan had'a kayansu suka shiga yi Dan asubanci zasu yi shiyasa suka fara shirin tun yanzu. Maman Yusuf. [6/29, 09:02] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Pure Moment Of Life Writers (P.m.l)* *page 9-10* Da magarib bayan Sun fito masallaci da sauri su Baba Hamisu suka tsaida Mudi a k'ofar Gida. Ba walwala A fuskarsa ya fara dubansu yace. "Lafiya de ko kuka tsaida ni?". Da sauri Baba Hamisu ya fara magana. "Mudi tabbas mun san abinda aka yi maka ba'a kyauta ba kuma itama Sauden naje na sameta na nuna mata bata kyauta ba kuma ta fahimce ni dan yanzu haka Ta janye maganar Auran,dan haka Don Allah kayi hak'uri ka janye zancan barin Gidan nan" Shu'aibu ne ya k'ara da cewa. "Kuma Mudi in kabar Gidan nan zumuncin mu lalacewa zeyi, Yaran mu ba zasu san junansu ba, dan haka Don Allah tunda itama Yaya Saude ta janye zancan Auran Don Allah kaima ka janye zancan tafiyar". Kallo kawai Mudi ya bisu dashi,dan yasan halin Saude farin sani bata fad'in abu ta dawo ta janye,dan haka kad'a kanshi kawai yayi sannan yace. "To naji kuma nagode Amman yanzu bazan yanke hukunci ba se nayi shawara da med'akina tukuna in yaso daga baya shawarar damuka yanke zaku ganta,in mun yarda mu zauna zaku ga mun zauna in bamu yarda ba zaku ga mun tafi,dan haka kuyafemu duka sabida halin rayuwa". Gaba d'aya jikinsu ne yayi sanyi da batun na Mudi amma basu da zab'in daya wuce suyi fatan alkha'iri,dan haka suka had'a baki gurin fad'in. "To Allah ya tabbatar mana da alkha'iri Amman de ka duba maganar da idon basira". Murmushi ya musu ya shige cikin Gidan. Suma Gidan suka shiga jiki a sanyaye . Koda Mudi ya yiwa Zainabu bayani akan abinda su Shu'aibu suka tare sa suna fad'amasa fafur tak'i amincewa dasu ci gaba da zama a Gidan, dan harda kukanta ita de subar Gidan, dan haka dole Mudi ya amince dasu bar Gidan shine masalaha. Da daddare da misalin k'arfe takwas na dare Mudi yaje yiwa Mahaifansa sallama sabida asubanci zasu yi. Koda ya musu bayanin abinda ke tafe dashi kuka Inna tasa akan bata amince ba in kuma ya tafi to bata yafe mishi shayar dashi da tayi ba. Hankalin Mudi in yayi dubu ya tashi, rasa inda zesa kansa yayi koda yayi yunk'urin bata hak'uri mik'ewa tayi sannan tace. "Wlh matuk'ar kabar Gidan nan bada yawuna ba Allah ya isa ban yafe maka nono na daka shaba har abada". Tana kaiwa nan a zancan tayi shigewarta d'akinta,ta barshi shida Malam Audu. Shima Mahaifinsa cewa yayi in yabar Gidan to ya tabbata su ya Bari ba Gidan ba. Dan bak'in ciki Mudi har kuka yayi,haka ya baro b'angaran Iyayan nasa ya nufi nasu. Koda shigarshi zainabu tsorata tayi da yanayin sa dan haka jiki a sanyaye ta tambayeshi abinda ya faru, be b'oye mata komai ba ya sanar da ita,itama kukan tasa daga bisani ta share hawayenta ta mik'e ta fara maida kayayyakin su mazaunin su. Cikin k'ank'ani lokaci komai yayi tsaf,sannan taje ta kawo musu abinci suka ci,shi de K'ara rarrashinta yake tayi. murmushi kawai tayi tace,"haba Malam ay dole na taya ka yiwa mahaifanka biyayya, in ban taya ka ba waye ze taya ka?Dan haka ka dena ma bani hak'uri, Allah yasa hakan shine alkha'iri". *Bayan Wata Shida* Tsawon wa'innan watannin ba'a sake d'ago da zancan Aure tsakanin Ummu Aymana da Jameelu ba se yau. Saude ce ke zubar da ruwan bala'i a tsakar Gidan tana fad'in, "wlh nagaji dayin shuru yau ko sede ayi wacce za'a yi, in ko aka hana Jameelu Auran Ummu, to wlh zan bashi damar fita yak'in neman Auran ta koda kuwa da kaifin takobin shine tunda abun ba mutunci". Sosai maganganun nata suka firgita Zainabu dan tasan kashe Mutum a gurin Jameelu tamkar kashe kiyashine,shi yasa duk tabi ta firgita gashi acikin daji suke ko hukumar Y'an sanda babu a gurin bare su d'auki mataki. Shiko Mudi ko a jikinshi maganar bata dameshi ba harkokinsa kawai yake yi, abinda ya sanide shine Y'a tashice Ba kuma wanda ya isa ya sashi Aurar da ita ga Wanda be dace ba. Maman Yusuf. [6/30, 06:46] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad @ZahraSurbajo* *Pure Moment Of Life Writers (P. M. L)* *page 11-12* Koda dare yayi su Baba Shu'aibu ne suka sake zuwa gurin Mudi akan zancan Auran. Kai tsaye yace musu. "Ni bazan Aurawa Ummu Jameelu ba sabida be dace da ita ba, kuma wlh babu Wanda ya isa yasani yin abinda be dace ba". Ko sauraron su be sake yi ba ya tashi ya barsu a gurin. Gaba d'ayan su Ransu ya b'aci, dan haka daga gurinshi kai tsaye gurin Inna Saude suka nufa,suna zuwa suka kwashe k'arya da gaskiya suka fad'a mata. Ga mamakinsu se kawai tayi murmushi tace musu, "ku kwantar da hankalinku,aure kamar anyi shi angama, ayni bana magana ta tashi a banza,inde na furta sena tabbatar, dan haka ku tashi kubani guri zanyi nazari". Cike da mamakinta suka bar gurin. Dare ya tsala sasoi baka jin motsin komai sena Shanun da Awakin da suke Gidan,kasancewar duk wani Bil Adama dake Garin ma yayi bacci,dan Dare ne sosai misalin k'arfe biyu na dare. Jameelu na hango d'auke da wata sharb'eb'iyar wuk'a fuskarshi b'oye cikin rawani,ya nufi b'angaran Baba Mudi, koda ya haura ta katanga kai tsaye D'akin da suke kwana ya nufa.yana shiga be b'ata lokaci ba ya samu Dede zuciyar Mudin ya Burma masa wannan wuk'a wacce sabida kaifinta seda ta tsago jikinshi ta caki katifar da yake kwance. Nishi me k'arfin da Mudi ya saki shine ya farkar da Zainabu daga bacci, da sauri ta kunna cocila dan ganin meke faruwa, hakan yayi dede da lokacin da rawanin da Jameelu ya rufe fuskarsa dashi ya kwance. A razane Zainabu ta furta. "Jameelu me ya kawo ka D'akin mu a dede wannan lokacin? me kake nema? Ko kayi makuwa....."maganarce ta mak'ale a mak'oshin ta sanda tayi arba da sharb'eb'iyar wuk'a soke a k'irjin mijnta jini se ambaliya yake. Wata razananniyar k'ara ta Saki ta fad'i k'asa sumammiya, shi ko Jameelu jikinshi na rawa ya fice daga b'angaran, kai tsaye D'akin Mahaifiyar shi ya nufa. Da yake tasan da zuwanshi k'ofar a bud'e take kuma bata bar Baba Hamisu ya kwana a D'akin ba, dan haka da shigar Jameelu da sauri ta tare shi tana tambayarsa Cikin matsanancin tsoro ya bata labarin ya kashe Mudi Amman Zainabu ta ganshi wanda sanadin hakan gata can ma a sume. Wani murmushi na mugunta Saude tayi sannan tace . "Ka kwantar da hankalin ka,kasa a ranka cewa ka kashe banza, ay ka godewa Allah daya baka jarumar Uwa me zurfin tunani,ay sanin da nayi za'a iya samun matsala gurin aywatar da aykin shiyasa na amso kan ta kwana a gurin Boka na kan tudu, dan haka yanzu zanyi Maganin komai". Tana gama fad'in haka ta bankad'a katifar ta ta d'auko wani abu da wata k'aramar wuk'a ta fice daga D'akin ta nufi Garken Shanun Gidan wanda suke mallakin Baba Mudi ne,shi de Jameelu bin ta kawai yake da ido dan gaba d'aya ya gama tsorata. Tana zuwa rami ta hak'a da Wata Wuk'a dake hannunta tana gama hak'awa ta d'auko wasu tarkace a wani Jan kyalle ta saka a cikin ramin Tana Kiran sunan Zainabu, seda Ta Kira so bakwai Amman a hankali sannan ta rufe ramin da kyallan a ciki,da sauri suka koma d'akinta gudun kar wani ya Gansu. Tunda suka koma D'akin in banda dariya ba abinda suke yi sabida ta shaidawa Jameelu manufar abinda Ta burne, ashe asirine ta yiwa Zainabu wanda ita da hankali sede wani Ikon Allah ma'ana ta haukata ta hauka me tsanani. Acan kuwa b'angaran su Zainabu,tana nan kwance a sume kamar a mintsineta se kawai ta farka, tana farkawa ta fara soshe soshe tana cire duk wata sutura ta jikinta,seda tayiwa kanta tsirara sannan ta shiga tik'a rawa akan gawar Mijin nata. Maman Yusuf. [6/30, 12:57] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@ZahraSurbajo* *Pure Moment Of Life Writers (p.m.l)* *page 13-14* Haka Ta kwana akan gawar Mudi tana chashewa ba tare da damuwar komai ba. Da gari ya waye Dariyar Zainabu ce ta farkar da Ummu Aymana Wacce take ta faman shirgar baccinta,koda ta farka mamaki take na ganin mahaifiyar tata tsirara, Amman abunka da yarinta seta rufe idonta wai gudun kar Umman tata tace ta kalleta idon nata a rufe tace. "Umma zaninki ya kwance ki d'auka kisa zan wucene". Dariya Zainabu ta sake fashewa da ita cikin haukanta ta cewa Umma Aymana. "kajimin tsinanniyar mata! uban waye yace miki tsirara nake?dan Kan ubanki duk tulin kayan dake jikina baki gansu ba da har kike cewa nasa zani ayko yau se naci uwarki". Tana gama maganar ta diro daga kan gawar Mudi,tasa hannu ta finciko wuk'ar da aka sokawa Mudin ta nufi Ummu Aymana da mahaukacin gudu, ganin hakane yasa Ummu ta kwasa da gudu zuwa tsakar Gidan su inda kowa ya fito yana harkokin gabansa harda Inna Saude wacce bame cewa ta aykata wani abu mummuna duba da yadda hankalinta yake kwance. Da gudu Ummu tayi cikinsu tun kamin suyi wani yunk'uri Zainabu itama ta fito rik'e da wuk'ar da aka kashe Mudi wacce take d'igar da jini. Hankali atashe suka mik'e kowa ya nemi gurin b'uya da kyar su Uwaisu suka murd'eta suka amshi wuk'ar,itako se dariya take tana fad'in. "Kisan gilla zanyi tunda na koya na iya". Abun d'aurewa kowa kai yayi Inna Saude ce fuska d'auke da damuwa da yanayi na tausayawa kamar gaske tace. "Ikon Allah Zainabu ciwon haukane Kuma ya kamata,watak'ila ma yanzu ne abun ya sameta bayan Mudi ya tafi masallaci". Baba Shu'aibu ne ya katseta da cewa. "Ay yau Mudi ya makara dan ko masallacin be jeba sede ko in asubancin tafiya kasuwa yayi". Ummu Aymana wacce ke b'oye a bayan Inna uwani ce tace. "Ba kasuwa yaje ba dazan fito naga suna wasa da Umma na ta haye kanshi tana rawa, shi kuma yana kwance a kan Gado". Da sauri suka nufi d'akin abunda suka gani ba k'aramin firgita su yayi ba,su duk a tunaninsu Zainabu ce Ta kashe Mudi bayan ta sami tab'in hankali sannan Kuma ta biyo Ummu Aymana itama zata kashe. Cikin jimami suka Fara y'an koke koken su na munafurci wanda zahirin gaskiya murna suke giwa ta fad'i zasuci nama. Cin k'ank'anin lokaci gari ya gama d'auka Zainabu ta kashe mijinta kuma tana neman kashe y'arta a sakamakon haukacewa da tayi. Ayko jama'a se zuwa kallo sukeyi,haka mutanan Gidan suka bar Zainabu ba Kaya kowa yazo haka ze ganta tsirara,tana ta surutai. Ummu Aymana ko kuka kawai takeyi gwanin tausayi,abunka da farar fata tuni har tayi ja sabida kuka,kowa yazo seya tausaya mata,haka aka yiwa Mudi wanka aka sallaceshi aka kaishi makwancinshi, ita kuma Zainabu aka kwashe kayan D'akin tas sannan aka sata a ciki aka mata tirke kamar Wata Akuya aka d'aureta kuma har zuwa lokacin basu suturtata ba. Haka akai Ta zaman makoki har zuwa lokacin da akayi rabon Gado inda sabida da zalinci Ummu Aymana da mahaifiyarta, suka tashi da Saniya daya da Raguna guda biyu acikin Shanu sama da d'ari biyu da Raguna sama da guda hamsin iya gadon da suka samu kenan,sauran ko harda su Saude a cikin jerin magada inda kasonta yafi na kowa yawa dan ko Furera Shanu biyu aka bata.Koda aka ba Ummu Aymana nasu bata damu ba dan bata san me hakan ke nufi ba. Duniya sabuwa ta dawo a Gidan kowa ya samu dukiya se walawa yake yi, sab'anin Ummu da Umman ta kullum tana mak'ale da ita tana kuka gashi ko abinci ba'a ba Umman tata wai a cewar su mahaukata basa cin abinci a k'oshe suke,shiyasa a cikin nata wanda ake bata seta k'i ci ta kawowa Umman nata ga mamakinta seta ga ta cinye tas tana neman k'ari. Kullum Ummu cikin tausayawa mahaifiyarta take kasancewar Zainabu ba Y'ar Garin bace Y'ar Asalin jihar Adamawa ce shiyasa babu wani nata daya san abinda ke faruwa, shiyasa Ummu ke tausayawa mahaifiyar tata. Kwanci tashi rayuwa tayi tsanani garesu dan yanzu ko lomar abinci babu me basu sede tafita bara tasamo ta kawowa mahaifiyar tata,gashi babu Wanda yatab'a yunk'urin nemawa Umman tata magani, d'an Gadon nasu ma wayar gari tayi taga babu su a tirken da suke kwana, koda ta tambaya cewa akayi barayine suka sace haka dole ta hak'ura. Yanzu D'akin da suke kwana tsutsotsine ke yawo ko ina sabida Umman ta tunda aka d'aureta tsawon wata shida koda wasa basu tab'a kwanceta ba a gurin take kashi take fitsari,Ummu Aymana kuma bazata iya gyara mata ba kuma tayi iya yinta ta kwanceta Amman ta Kasa, gashi daga alamu Umman tata bata da lafiya dan ta lura cikin Umman nata se motsi yake gashi lokaci zuwa lokaci cikin na k'ara girma. Ta rasa wanda zata fad'awa sede tai tayiwa Umman nata Addu'a akan Allah ya bata Lafiya. Abinda Ummu bata saniba tun kamin rasuwar Mudi, Zainabu ke d'auke da ciki na Wata biyu wanda ko ita kanta batasan tana dashi ba bare wani na Gidan. *Bayan watanni biyu* Ummu Aymana ta dawo daga barar abinda zasuci kwatsam Ta sami mahaifiyarta a cikin wani mummunan hali na ciwo gaba d'aya ta fita hayyacinta,a gigice Ummu taje cikin Gidan neman suzo su taimaki Umman ta Amman ba Wanda ya kulata dan Saude asiri tayiwa kowa na Gidan akan ya tsani su ummun. Ganin bame Taimako ne yasa takoma gurin Umman tata kamar wasa ta Fara kwance igiyar da aka d'aureta kawai se gani tayi ta kwantu. Kamar jira tana kwanceta umman tata ta kama hannunta ta rik'e da k'arfi tana kuka me tsuma zuciya gami da wani nishi me k'arfin gaske,kwatsam Ummu Aymana se ganin Jariri tayi ya fad'o yana tsala kuka. A gigice ta kwace hannunta daga ruk'on da Umman nata tayi mata ta matsa gefe jikinta na rawa kamar mazari, ita ko Umman D'an na fad'owa ta koma ta kwanta tana maida numfashi sabida ta wahala.. Shi ko Jaririn in banda kuka ba abinda yake yi ga shi kwance cikin kashi tsutsa ta Fara bin jikinshi,tausayin Yaron ne yasa Ummu Aymana d'auko wankakken zani tazo ta d'aukeshi ta lullub'eshi bayan ta cire tsutsar da ke binshi ayko take yanke yaron yayi shuru. Ajiye yaron tayi akan shimfid'a tafita tsakar Gidan tace Umman ta ta Haihu. Ay ila hirin Gidan ba wanda be razana dajin zancan ba,da sauri suka nufi D'akin kowa yana toshe hanci, abinda suka gani shine ya firgitasu wato Yaron babu ta inda ya baro kamannin Mahaifinshi, hakan ke nuna Dan Mudin ne, kuma hakan na nufin Gadon da suka ci na Mahaifinsa sesun dawo dashi ma'ana de ya koresu daga cikin Magadan Baban shi. Ko cibiya basu ji tausayi Sun yanke masa ba haka suka baro D'akin cike da zullumi akan in suka Bari duniya taji labarin haihuwar D'a Namijin da Zainabu tayi,sun bani. Ummu ko tasa Yaron tayi tana kallo k'aunarshi na ratsa zuciyarta, ita ko Zainabu bacci kawai takeyi na huce gajiya. Ummu naso Ta goya yaron Amman wannan mahaifar da zaranta sun hanata yin hakan, kuma taga intaja da niyar ta cire Yaron kuka yake duk da a hankali take jan, kawai seta yanke shawarar ta rage masa tsawonta zefi kawai dan haka Reza ta d'auko sabuwa tazo ta yanke cibiyar,tana yankewa se taga jini na zubowa da sauri ta sami bakin d'an kwalinta ta yanka ta d'aure masa sosai seda taga jinin ya dena zuba sannan hankalinta ya kwanta. Goya shi tayi tafita yin Icce dan tana tsoron ajiye shi Ummanta ta dukar mata shi,da yake tasa hijab kowa yaganta da goyo d'auka yake y'ar tsanace haka har ta isa daji tayo itacen ta dawo gida,had'a wuta tayi ta d'orawa Ummanta ruwan wanka dan ita gani take yanzu Ummanta ta warke zata iya yin wanka,seda ruwan ya tafasa ta kwashe a bokiti sannan ta nufi D'akin domin tashin mahaifiyarta ta a bacci tazo tayi wanka. Abunda ta gani shi ya firgitata wato ba Umman nata a Dakin ba alamarta, Da gudu ta fita waje tana dubawa nanma ba ita, seda tayi tafiya me nisa goye da yaron a bayanta tana neman Ummanta Amman bata ganta ba kowa ta tambaya sede yace yaga tawuce da gudu ba kaya a jikinta. haka Ummu Aymana tagaji ta dawo Gida tana kuka tana addu'ar Allah yadawo mata da Ummanta lfy. Ruwan Data dafa domin Ummanta shi ta juye a baho ta tsunduma yaron a. ciki ta fara yi masa wanka abun ba k'aramin mamaki ya bani ba ganin yadda take masa wankan kamar wata uwar mata,amman dana tuno wayo da dabara irin na bafulatanin mutum kuma mazaunin k'auye se abin yadena bani mamaki ya koma burgeni. tsaf tamasa wanka shiko se kuka yakeyi na alamar yaji dad'in wankan. Duk abinda takeyi gani take yanzu Ummanta zata dawo dan haka guri tasamu a gefe ta kwantar da yaron bayan tashafa mishi man kadai ta lullubeshi da zannuwa guda biyu,seta shiga gyara D'akin dan kar Ummanta Ta dawo taga bata gyara ba. Ummu akwai juriyar ayki kamin lokaci me tsayi ta gama gyara D'akin fess bame cewa shine me tsutsa sede warine har lokacin be dena ba, d'aukar yaron tayi suka shiga D'akin suna jiran dawowar Umman su. Maman Yusuf . [7/1, 08:34] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad @ZahraSurbajo* *pure moment of life writers* *page 15-16* Ummu Aymana tana nan zaune har dare yayi amnan Umman ta bata dawo ba kuma a lokacinne Yaron ya fara kuka wanda ko ba'a faɗa ba yunwa yake ji. Hankalin ummu ne ya tashi tarasa yadda zatayi dashi gashi bame taimaka mata ay kawai itama seta fashe da kukan. Rarrashin shi ta shigayi tana bashi ruwa a hankali bacci ya ɗauke shi be sake farkawa ba se wajan ƙarfe ɗaya na dare,Ummu rasa abin yi tayi ay kawai wata shawarace ra faɗo mata,miƙewa tayi ta ɗauƙi ƙoƙo ta nufi garken Shanun Gidan,tana zuwa ta samu me shayarwa a cikinsu ta tatsi Nononta da yake a ɗaure take bata mata komai ba. Da sauri ta koma ɗaki tasa cokali ta dunga ɗiba tana bashi ay kamar jira yake,take Ya kama sha bada wasa ba,ci gaba tayi da bashi har seda ya fara turoshi waje inta bashi hakan ne yasa ta gane ya ƙoshine,rufewa tayi ta cire mishi zannuwan data rufa mishi ɗazu sabida yayi kashi a ciki. Wasu ta ɗauko ta rufa masa bayan ta goge mishi kashin,Allah sarki bawan Allah ay jin cikinshi ya ɗauka se bacci,itama baccin tayi cike da kewar Ummanta. Washe gari da safe tayi masa wanka ta goyashi tasa hijab ta fita barar abinda zata ci bata dawo ba se Azahar,tana zuwa ragowar Nonon jiya data rufe shi ta ɗauko taba Ƙanin nata yasha ya ƙoshi ya koma bacci. Haka ta dunga ɗawainiya da ƙanin nata har tsawon kwanaki biyar,kuma dama tun bayan rasuwar mahaifinta Inna Saude bata sake zancan Auranta da Jameelu ba sabida dama dukiya sukewa kuma sun samu. Gaba ɗaya sun gama tsaida shawarar kashe yaron ko kuma salwantar dashi,amman basuyi shawarar dasu Malan Audu ba su eh su sukayi shiyasa su Malan Audu basu da masaniya. Jameelu aka wakilta akan kashe yaron kuma ya amince ze aywatar. Da daddare misalin ƙarfe goma na dare yaron cikinshi ya fara ciwo gashi cikin ya kumbura, hakane yasa tsoro ya kama Ummu ta kwantar dashi ta nufi gurin Inna Saude domin ta faɗamata ko zata taimaka mata. Tana zuwa ƙofar Ɗakin abinda taji ne yasa takasa ƙarasawa cikin Ɗakin,muryar Saude ta jiyo tana ba Jameelu umarni akan yaje yanzu ya kasheta ita da Ƙaninta kuma ya tabbatar ya musu irin kisan da yawa Mahaifinsu. A gigice Ummu ta baro gurin jikinta se ɓari yake yi har faɗuwa take gurin gudu, a haka ta ƙaraso Ɗakin nasu tana zuwa ta sungumi Ƙanin ta dake ta faman kuka sabida ciwon da cikin shi ke masa ko hijabinta bata saba tafice da mahaukacin gudu daga Gidan. Tana fita ba jimawa Jameelu ya shiga Ɗakin domin aywatar da mugun nufin shi sede yayi rashin sa'a domin sunbar Gidan. Da sauri ya fito yabi bayan su dan ya fahimci basu jima da fita ba. Ita ko Ummu gudu take irin na ceton Rai rungume da Ƙanin nata shiko se kuka yakeyi,Garin lokacin damina ne dan haka hadarine baƙiƙirin a sama Ruwa gab yake da sauka. Ganin hadarin sosai hankalin Ummu ya tashi amman hakan be hanata cigaba da gudunba musammam data fahimci kamar anbiyo sawun su,a haka har ta shiga ƙurgummin Dajin Garin bata dena gudunba. Shigarsu Dajin keda wuya Ruwa ya kece kamar da bakin ƙwarya harda ƙanƙara,amman hakan be hana baiwar Allah Ummu Aymana ci gaba da gudu ba duk da cewa ko gabanta bata gani sabida tsananin duhun dajin. Ci gaba tayi da gudun har takai dede inda tagaza ci gaba da gudun dan tana zuwa dede gurin taji kamar an riƙe mata ƙafa tayi tayi ta ɗaga ƙafarta amman abun yaci tura hakanne yasa ta durƙushe a gurin tana kuka tana roƙon Allah akan ya kawo musu agaji,gashi daga ita har ƙanin nata ruwa ya musu shegen duka wanda hakanne yaja ƙanin nata ya suma sabida wahala. Tana nan durƙushe ruwa na dukansu taji wani abu me santsi yana bin jikinta hannu takai tana shafawa dan ta gasgata tunaninta ilai kuwa abinda take zargine wato *Maciji* muje zuwa. Maman Yusuf. [7/1, 15:36] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad @zahrasurbajo* *pure moment of life writers* *page 17-18* Runtse idonta tayi taci gaba da shafa micijin har zuwa sanda tazo dede kanshi da sauri ta shaƙi wuyan macijin sede ga mamakinta seji tayi babu komai a hannunta. Da sauri ta buɗe idonta abun da tagani shine yayi matuƙar bata mamaki gami da farin ciki,umman ta tagani zaune akan wata kujera ta alfarma cikin shiga ta alfarma tana mata dariya. Da gudu ummu ta miƙe ta ƙarasa gurinta tana kukan murnar ganinta,tana zuwa rungumeta rayi ita kuma tasa hannu ta amshi yaron dake hannun ummun. Ga mamakin ummun ruwan da akeyi yadena sauka akansu sannan gurin ya wadata da haske tamkar rana,koda ummu takai dubanta gaba ƙaton kogin garinsu ta hanga wanda da ace taci gaba da gudun da takeyi ba makawa ciki zata faɗa dasu. Gidiya tayiwa Allah sannan takai dubanta gurin ummanta wacce tun ɗazu inbanda murmushi ba abinda tace mata,cike da murna ummu tace. "Ummana da badan Allah ya taimakemu kinzoba da tuni mun mutu dan Allah tunda kinji sauƙi kar ki kuma cire kayanki kuma yaronki se kuka yakeyi". Murmushi umman kawai tayi sannan ta kamo hannun ummun ta zaunar da ita akan cinyarta,zamanta keda wuya se ganinsu tayi ita da ƙanin nata a wata bukkar kara ga wani abinci me rai da lafiya se kuma madara me kyau itama,kuma abinda ya bata mamaki shine ita de da tasan darene yanzu kuma safiyace kuma tana jin ƙarar motoci daga inda take. Ta duba ko ina bata ga umman tasu ba ƙanin ta kuma gashi cikin ƙoshin lfy harda kayan sanyi a jikinshi,se ɗaga ƙafa sama yake yi yasa hannunshi a baki yana tsotsa. Lokacinne ummu ta gama yarda Allah ne ya turo wannan aljana ta taimakesu dan ko shakka batayi da aljana ta haɗu,godiya ta sake yiwa Allah sannan taja kwanon abincin batare da tunanin komaiba ta kama ci har ta cinye tasha ruwa,shima ƙaninta madarar ta bashi amman yaƙi amsa alamar a ƙoshe yake ,daukarshi tayi sede ga mamakinta tana ɗagashi se taga ashe akan kuɗi yake kwance ƴan dubu dubu guda goma da sauri tasa hannu ta ɗauki kuɗin ta ƙulle,a zaninta sannan ta goya ƙanin nata ta fito daga cikin bukkar. Koda ta fito se taga ashe a bakin titi suke motoci se wucewa sukeyi.abun sosai ya bata mamaki kuma daɗin daɗawa titin ba irin na garinsu bane,ƙara ɗaure ƙaninta tayi a baya da kyau ta saka hijab ɗin da tagani a rumfar ba me cewa ɗane a bayan nata kasancewar tana da girman jiki duk da cewa shekaranta goma sha ɗaya lokacin. Ƙarasawa tayi bakin titin se ta hango wata tasha daga can gaba kaɗan dan haka can ta nufa,tana zuwa taga motoci da mutane a ciki ita kuma gashi batajin yaran hausa bare ta fahimci inda kawai wata mota da taga ta kusa cika ita taje ta shiga itama, dama mutum ɗaya suke jira tana shiga akazo karɓar kuɗin mota,Ayko ansha fama kamin ta fahimci yawan kuɗin da zata bada sabida kaf gurin bame fahimtar yaranta itama kuma bata fahimtar nasu ,a cikin kuɗin da aljana ta bar musu ta bada kuɗin motar,sannan direba yajasu suka tafi inda ummu batasan inda zasu ba. Tafiya suke amman taƙi ƙarewa Ummu har gajiya tayi da zama ga ƙaninta se ƴan koke koke yakeyi, sakkoshi tayi ta rungume ta bashi madarar da yaƙi sha a bukkar nan dan taho mishi ds ita tayi dan tasan ze buƙata anjima, Jama'ar cikin motar se mamaki suke daga ƙarshe se suka dena sabida kama ta jini da suka gani se duka suka ɗauka ɗantane sabida sunsan fulani da auran wuri. Basu isa inda zasu ba se cikin dare gaba ɗaya Ummu ta gama gajiya,haka suka iso tashar garin da suka zo kowa ya sauka itama saukar tayi tasake goya ƙaninta a baya ta lulluɓeshi da hijab,cikin tashar ta shiga tana ta waige waige wanda kowa yaganta yasan ƴar ƙauye ce. Ganin bata gane kan tashar bane yasa ta fito ta bi wani titi me yawan hasken fitulun kan titi abin yayi matuƙar burgeta, nan ta shagala da kallon fitulun har dare ya tsala bata sani ba,ci gaba tayi da tafiya a ƙafa har ta iso wani guri me yawan mata sanye cikin shiga ta zubar da mutunci duk,wani me tsoron Allah in ya musu kallo ɗaya baze ƙaraba sabida tufar dake jikinsu ita da babu duk ɗaya. Kasancewar Ummu batasan meye karuwanci ba shiyasa ta ɗauki shigar tasu a matsayin al-adar Garin, haka taita binsu da kallo,yayin da gefe ɗaya kuma motoci ne na alfarma ke fakawa suna ɗaukarsu. Can ɗan nesa dasu taje ta zauna tana ci gaba da kallon ikon Allah, tanason fahimto abinda hakan ke nufi,dan ita de taga kamar masu motar wacce tafi fitar da surarta suke ɗauka, hakanne yasa Ummu fahimtar ashe al-adar Garin me kyauce tunda masu kuɗin garin ma masu irin shigar suke taimakawa,FCT ABUJA KENAN take taji itama tanason kasancewa ɗaya daga cikin matan da ake ɗauka a motocin,domin a taimaka musu,waige waige ta farayi na inda zata hango inda ake siyar da irin kayan dan ta siya itama Carab idonta ya hango mata wani boutique daga can nesa dasu kaɗan, ayko da sauri ta miƙe ta nufi gurin domin siyan irin tufar da ta gani a jikin waincan matan. Muje zuwa Maman Yusuf [7/2, 08:47] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Follow me on whattpad@zahrasurbajo* *pure moment of life writers* *page 19-20* Gudu gudu sauri sauri Ummu take yi har ta ƙarasa boutique ɗin. Da sallamarta ta shiga,da yake ba musulmai bane ba wanda ya amsa mata,sema binta da ido da sukayi azatonsu ma mahaukaciyace. Ido Ummu tashiga warewa tana kallon kayan dake ciki,can ta hangi wata riga ayko seta musu magana da fulatanci akan tanason rigar,ayko gaba ɗayansu suka kwashe mata da dariya,dan basu san me tace ba. Wata sassanyar murya taji daga bayanta cikin harshen fulatanci tana mata magana,da sauri Ummu ta waiga inda ta jiyo muryar,wata kyakykyawar budurwa ajin farko ta gani zaune akan kujera tana mata murmushi. Sosai Ummu taji daɗin ganinta sabida itama sanye take cikin irin shigar,dan inba idon Ummu bane yay mata ƙarya ba, to da tace shigar wannan budurwa tafi ta kowacce acikinsu muni, dan kayan dake jikinta daga kan na shanunta se gabanta kawai suka rufe amman sauran jikin duk ana gani. Cikin harshen filatanci budurwar tacewa Ummu. "Ƙanwata me ya fito dake da daddare haka?sannan waccan Rigar da kikeson siya me zakiyi da ita? ko ke matar aurece?". Idon Ummu ne ya kawo ruwa sharewa tayi sannan tace. "Ni ba anan nake ba mota na hau kawai ta kawoni nan,kuma ni ba matar aure bace,inaso in siya ne in saka inyi kamar yadda kikayi sabida nima masu motocin can da suke taimaka muku nima su taimakamin". Ta ƙarasa zancan cikin kuka. Dariyace ta ƙwacewa wannan budurwa cikin dariyar tayiwa sauran na shagon bayanin da Ummu tai mata ayko suma gaba ɗaya dariyar suka sa, sun jima suna dariya sannan sukayi shuru. Budurwarce taci gaba da magana. "Ƙanwata ay ko kin siyi Rigar bazata miki kyau ba sabida ke yarinyace baki da cikar halittar da Rigar zata miki kyau,sannan wa'incan da kike kallo ba taimakonsu ake yiba kasuwace in masu motar suka zo wacce ta musu ita suke siya seta shiga su tafi,dan haka ko kinsa kinje bazasu zaɓe kiba". Abunka da bafulatanin mutum ay gaba ɗaya tsorone ya kama Ummu najin cewa siyan matan dake gurin akeyi. Budurwarce tace. "ya sunanki ?" "Ummu Aymana" "Da kyau,ni kuma sunana Husna,amman anan kowa da Ƴarfillo yake kirana,ni ƴar Garin Yola ce karatu ne ya kawoni nan Garin". Ido Ummu ta bita dashi kawai dan bata jin zata faɗa mata daga inda ta fito. Ƴarfillo ce taci gaba da cewa. "Ban taɓa yin taimako ba a rayuwata amma yau na tsinci kaina da son taimaka miki,sede kuma ni ba yanzu zan tafi Gida ba, dan nazo gwada sa'a tane nan,akwai wani ɗan sarki da yake wucewa tanan duk bayan wata uku,to sometimes yana tsayawa anan ya ɗauki wacce zata tayashi kwana dan baya iya bacci seda mace a kusa dashi, to na jima ina zuwa amman ban taɓa sa'ar ganinshi ba, sabida ina zuwa a makare shiyasa yau na fito da wuri,dan haka kimana addu'a Allah yasa ya zaɓeni in ya zaɓeni kema zakiji daɗi dan zan ba wata ƙawata ke ta kaiki Gidana seki dunga yimin shara da gyaran Gida ina biyanki". Farin cikine ya bayyana akan fuskar Ummu da sauri tace mata. "Allah yasa ya zaɓe ki in kuma ya zaɓeki Allah yasa daga kanki ya gama zaɓar wata kuma har abada". Jin daɗin addu'ar da Ummu tamatane yasa ta rungume Ummun sede tudun goyon da taji a bayan tane yasa tayi saurin sakinta gami da ɗaga hijab ɗin Ummun,Jaririne yake ta faman shan baccin shi hankali kwance. "Ummu Aymana Jaririn waye a bayanki?". Cikin kuka Ummu tace. "Ƙanina ne". "Ƙaninki kamar ya?ina Mamanki take da zata barki ki fito mata da Yaro?". Kwashe labarinta tayi kaf ta sanar da Ƴarfillo amman bata faɗa mata sunan Garinsu ba. Sosai Ƴarfillo ta tausayawa Ummu da Ƙaninta dan har kuka seda tayi,gyarawa Ummu goyon tayi da kyau suna cikin hakane suka jiyo ƙarar motoci alamar Ɗansarkin yazo, da sauri Ƴarfillo taja hannun Ummu suka nufi gurin dandazon karuwan. Duk inda ƴarfillo ta wuce sede kiji ana tsaki badan komaiba sedan tafisu kyau da haɗuwa,zuwansu gurin ba jimawa tawagar Ɗansarkin ta ƙaraso, nanfa mata aka shiga gyarawa ko za'a dace. Motocine guda biyar huɗu iri ɗaya se ɗaya daban,guda huɗun baƙaƙene Range Rover new model se ɗayar kuma fara Bugatti.duka baƙin glass ne ajikin motocin,suna ƙarasowa gurin parking sukayi ba kuma wanda ya fito,zuwa can se wani mutum ya fito a ɗaya daga cikin baƙaƙen motocin kai tsaye inda su Ummu suke tsaye ya nufa,yana zuwa gurin ƴarfillo yaje yace mata. "you are lucky, yallaɓai yace ki biyoni". Yana gama magana ya juya ya tafi,Ƴarfillo wata shewa tayi yayin da sauran karuwan suke jin haushinta hannu Ummu taja zuwa gurin Shema'u Duniya ƙawarta, tana zuwa cikin sauri tace. "Don Allah ki kaita Gidana gobe zan miki manni inna dawo". Bata jira amsar ta ba tajuya tanufi motocin Ɗansarkin, tun kamin ta ƙaraso wani ya fito ya buɗe mata bayan motar da Ɗansarkin yake ciki ta shiga ya kulle suka ja motocin suka bar gurin. Shema'u Duniya Ranta a ɓace taja hannun Ummu suka nufi Gidan Ƴarfilon, ta kai Ummu Gidanne badan komai ba sedan tasan Ƴarfillo bata ƙaramar kyauta. Suna zuwa Gidan tayiwa Maigadi bayani shi ya buɗewa Ummu ƙofar falon ta shiga ita kuma Shema'u Duniya ta juya ta wuce. Maman Yusuf. [7/2, 20:11] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad @zahrasurbajo* *pure moment of life writers* *page 21-22* Shiga cikin falon tayi ta nemi guri ta zauna tana kalle kalle alamun ƙauyanci,kwanto ƙaninta tayi a baya wanda shima ya tashi daga bacci yanason abinci amman hasken daya gani ya hanashi yin kuka sede turo harshe waje da yake yi. Kwantar dashi tayi tafara neman inda zata ga abinci ko ruwa,a tsorace take zaga gidan har Allah ya kaita dinning area,tsyawa tayi tana kallon kulolin dake jere kan dinning ɗin batasan ko menene amfaninsu ba amman haka kawai taji tana shaawar ganin meye a cikinsu. Ƙarasa tayi gurin hannu tasa da niyar ɗagawa se kawai taga ta buɗe dayake baa kulle ba ande kawai ɗora murfinne,ganin abincine aciki Ummu batasan sanda dariya ta ƙwace mataba ɗauko kular tayi gaba ɗayanta ta dawo falon ta zauna. Har zata soma cin abincin se ta tuno da ƙaninta fasa ci tayi ta miƙe ta koma inda ta ɗauko kular dubawa tayi tsgani ko zata sami abun bashi,flaks ɗin data gani akan table ɗin ta ɗauka jin shi da tayi da nauyine yasa ta fara kici-kicin buɗeshi har de Allah ya bata saa ta buɗe,murfin flaks ɗin ta tara sannan ta,juyo abinda ke cikin flaks ɗin,damammiyar costard ne tasha madara amman dayake Ummu batasan ko meye ba ɗan dangwalowa tayi a hannunta ta ɗanɗana jin ɗanɗanonta ne yasa ta amince ƙaninta ze iya sha batare data cutar dashiba. komawa tayi gurinshi ta ɗaukeshi tafara bashi ayko bawan Allah jin,sabon ɗanɗano ay tuni ya buɗe baki yana amsa,bata ƙyale shiba seda ta fahimci ya ƙoshi sannan ta kwantar dashi itama taci abincin ta ɗanɗanon da taji har addu'a tayi akan Allah ya bata irinshi a Aljanna,tana gama cin abincin tafara neman gurin alwala amman bata ganiba haka ta haƙura ta dawo falon ta rungumi ƙaninta tana tunanin inda Allah kuma ya jehosu.anan bacci yay awon gaba da ita da Ƙanin nata. Ƴarfillo. shigar ta motar keda wuya taji wani sassanyan ƙamshi wanda bata taɓa jin irinshi ba,dubanta takai gun Ɗansarkin wanda ke kwance a lungun kujerar motar yana latsa wayarshi,bata iya ganin fuskarshi sabida rufe take cikin rawani idonshi ma sanye yake cikin baƙin glass,maana hannunshi kawai take iya gani. matsawa tayi kusa dashi ga mamakinta se taga ya ɗaga mata hannu alamar dakatarwa batare daya kalli inda takeba,jiki a sanyaye ta koma gefenta ta zauna cike da mamakin wannan bawan Allah,dan ita de tasan duk cikakken ɗan barikin daya ɗauketa tun,a mota yake fara wasanni da ita amman taga wannan ko kallo bata isheshi ba. Basu ɗauki wani lokaci me tsayiba suka iso guest house ɗinshi,faɗin haɗuwa da tsarin gidan ze ɗaukemu tsawon lokaci bamu gama ba. Koda suka isa ƙofar Ɗansarkin aka fara buɗewa yafita,seda ya jima da fita sannan aka buɗewa Ƴarfillo ƙofa ta fice itama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyar ɗansarkinne yamata jagora zuwa ɗakin dayake,amman kamin su barta ta shiga seda suka amshi wayarta da jakarta sannan sukayi serching ɗinta sosai suka tabbatar daga ita se kayan jikinta take sannan suka bata izinin shiga,shigar ta ɗakin seda kanta ya kusa juyewa sabida tsabar haɗuwar ɗakin,ga wani ƙamshi na musamman dake tashi a ɗaki dubanta takai kan doguwar kujerar dake ɗakin,jikake tim ƴarfillo ta faɗi ƙasa badan komaiba sedan kyau da cikar zati da tagani atattare da wanda yake zaune akan kujerar,wanda ko baa faɗa mata ba tasan shine Ɗansarkin. Shiko ya harɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya yana ƙare mata kallo,sanye yake cikin singlet da wando three quater duka farare,gashin kanshi baƙi kwance akanshi,farine sosai gashi da dogon hanci daya dace da tsarin fuskarshi,koya ya motsa bakinshi beauty point ɗinshi seya fito,gamida haɗaɗɗiyar wushiryarshi wacce ta ƙarawa bakinshi kyau,yana da tsawo da faɗi jikinshi a murɗe yake alamar dake nuna maabocin training ne shi,fuskarshi kuma zagaye take da saje wanda ys kwanta lub a fuskar tashi. Ƴarfillo jiki na ɓari tamiƙe tsaye gaba ɗaya se taga ta raina kanta duk kyan da take taƙama dashi sabida taga wanda ya fita. Wani arnen murmushi Ɗansarkin ya saki sannan ya motsa bakinshi da niyyar magana kamar wanda aka yiwa dole. "A tsarina in anyi checking ɗinki a waje in kin shigo gurina nima inayin nawa dan haka ki cire kayan jikin ki yanzu dan inga irin hajar dana ɗauko danni ko gado bana hawa senayi checking ɗin dan haka ina jiranki". Tunda ƴarfillo take yawon karuwancinta bata taɓa haɗuwa da irinshiba,bata da zaɓin daya wuce tayi abinda ya buƙata,cire kayanta tayi haihuwar uwarta ta tsaya a gabanshi,shi kuma yana ta kallonta daga ƙarshe de seda yasata ta ɗaga har ƙafofinta yasa hannunsa a ........yaji yanayin matsewarta. seda ya duba komai wato general check off sannan ya miƙe ya isa kan gado yamata nuni data biyoshi. muje zuwa. Maman yusuf. [7/3, 13:52] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *Whattpad @zahrasurbajo* *Pure Moment of Life Writers* *page 23-24* Ƙarasawa ƴarfillo tayi kan gadon cikin takunta me ɗaukar hankali,tana hawa yareema ya ruƙota ya shiga ɓatar mata da tunani wanda tunda take bata taɓa haɗuwa da wani namiji dayasan kan hanya irin shiba. Cigaba yayi da wasa da ita irin wasan da zamuce ko a gidan aure ba kowane yake sakin jiki yayi shiba,ƴarfillo takai matakin da bazata iya cigaba da amsar wasannin nashi ba burinta kawai yayi abinda yasa ya ɗaukota,ga mamakinta kuma shi yaƙi cire kayan jikinshi duk,abunda yake mata da kayanshi a jikinshi. Koda taga ya ɗago yana kallonta ta ɗauka zece ta gyara ne zeyi ay seji tayi ya mata abinda bata taɓa tsammanin ze iya ba wato s bakin shi da yayi yana sucking ɗinta,tun tana daurewa ƙarshe de sabida daɗi ihu tashiga yi kamar numfashinta ze ɗauke,seda ya ɗauki kusan minti goma tana mata haka ganin tana shirin sumewa ne yasa ya ƙyaleta ya miƙe ya shige toilet. Ƴarfillo se jiyo sautin ruwa tayi alamun wanka yakeyi,wasu zafafan hawayene suka shiga sunturi akan fuskarta sabida takaici,shi wanne irin azzalumine seda ya bari takai matakin da bazata iya jurewa ba sannan ze barta,cigaba tayi da kukanta yayinda marar ta tafara murɗewa sabida shaawar data taso mata. Ya jima a toiet ɗin sannan yafito,ga mamakin ƴar fillo sanye cikin kaya yafito ba kamar yarda tai tsammanin ze fito ɗaure da tawulba,se ƙamshi yake bazawa abinshi kan kujera yaje ya zauna ya hakimce yana kallonta. Kukan tane tafara damunshi dan haka cikin ɗaurewar fuska yace. "ke kilaki meye na kuka kuma?kodan ban tara dake bane kike kukan?inko hakane kinada ayki,danni da kika ganni nan mutumne me kishi bana haɗa rami da kowa,in kin ganni a rami to nawane maana ni nafara samar dashi,inko kikaga nayi iya haka to ramin banawa bane kenan shiyasa nake checking kamin na rufta,dan haka wlh inde kece ko zaa tashi duniya iya abinda ze dunga haɗani dake kenan,kina da ƙira me kyau shiyasa nake tunanin zaɓarki a matsayin me zuwa tayani kwana aduk lokacin dana shigo garin nan". Wani kukan tasake fashewa dashi tana roƙonshi akan yazo ya biya mata buƙatarta,miƙewa yayi ya buɗe wata loka ya ɗauko wani abu ya wurga mata sannan yace. "ni adaline shiyasa bana zalinci a wannan harkar,dan haka ga wannan kiyi amfani dashi ki biyawa kanki buƙata in kingama kiyi musu magana zasu kawoki inda nake". Ko sauraronta beyiba ya juya ya fice daga ɗakin cikin tafiyar ƙasaita. Ƴarfillo bin abinda ya wurgo mata tayi da kallo, irin.......mazane amman na roba,da kamar ta yardar se kuma tafasa tayi amfanin dashi,ba laifi ya rage mata zafi,miƙewa tayi ta shiga toilet tayi wanka sannan ta fito ta maida kayanta,tafice tana fita masu tsaronshi suka taso suka mata rakiya zuwa ɗakin da yake. A kwance tasameshi cikin kayan bacci ya lumshe ido akan tsttausan gado,tana shiga hannu ya miƙo mata ba musu ta ƙarasa inda yake itama ta kama hannun nashi janta yayi ta faɗa jikinshi yaja bargo ya rufesu yayinda ya rungumeta akan faffaɗan ƙirjinshi,zatayi magana ya haɗe bakinta da nashi ya shiga kissing ɗinta seda yaga jikinta ya mutu sannan yace. "Sorry Baby is time for sleep". Tanason magana haka dole tayi shuru har bacci yayi awon gaba dasu duka. Asuba tagari ƴarfillo. Ummu bata farkaba seda gari yayi haske sosai shima kukan ƙanintane ya tasheta da sauri ta miƙe ta ɗaukeshi,ashe kashi yayi shine yake kukan. cire mishi kayan jikinshi tayi abinda ya bata mamaki shine zaran cibiyarshi yafaɗi gurin yayi baƙi kamar wanda ake gasawa,(abunda ummu bata saniba shine wannan aljana data taimakesu ita tagasa mishi har seda ta faɗi). Gogo mishi tayi da kayanshi sannan ta goyashi a baya,gabs ɗaya zamsn gidan ya isheta taƙosa me gidan ta dawo. Anasu ɓangaran ƴarfillo kuwa farkawa tayi taganta ita kaɗai akan gadon da sauri ta diro tana waige waigen inda zata ganshi,motsi taji a bayanta da sauri ta waiga,danƙari abinda tagani sosai yabata mamaki,Ɗansarki tagani sanye cikin kakin soja,a gaban rigar daga hsnnun hagu ansa NIGERIAN ARMY,daga ɓangaran hannun dama kuma ansa COL AYMAN ABU AYMAN. Abun ba ƙaramin mamaki ya bata ba haka taita binshi da ido,shiko wani killer smile ya sakar mata sannan yace. "Suprise,Suprise,Suprise,ko baki faɗaba nasani,sabida ni haka nake kullum cikin ba mutane mamaki". Murmushi tayi sannan tace. "Wannan gaskiyane,tun jiya kake bani mamaki,sede abunda yafi bani mamaki shine duk wacce kataɓa ɗaukowa a inda ka ɗaukoni babu wacce ta ta taɓa faɗin kamanninka sannan babu wacce tasan sunanka,kawai de sede suce kai ɗansarki ne,but ni kuma naga gashi ina ganin kamanninka kuma kayan jikinka ya nunamin sunanka,ko meyasa hakan?". "Yarda da kene yasa hakan,kuma tabbas ni ɗansarkine,kuma ni sojane ina riƙe da miƙami me girma a gidan soja,so idan kika bari wannan labarin ya fita waje se na tabbatar dana ɓatar dake a doron duniya dan babu wacce tasan hakan seke,inason mutum me sirri inde kika riƙe sirrina zan cigaba da baki mamaki,so nagode da tayan bacci da kikamin,dan haka ga tukuici". wani ƙaramin akwati ya miƙa mata sannan ya juya ze fita da sauri ƴarfillo tace. "Prince ko sunana baka tambaya ba bare ayi zancan phone number". Murmushi yayi sannan yace. "Inada mantuwa may be ko kin faɗamin kan na fita daganan na manta dan haka kije gida nagode kuma ba'a kawomin ziyara inde bani ne nayi gayyatar ba,ki kiyaye,na barki lfy". yana kaiwa nan a jawabinsa yasa kai ya fice daga ɗakin,se ƙarar jiniya tajiyo. Cikin sauri ta miƙe ta kimtsa ba batun sallah ta ɗauki akwatin daya bata ta fice daga ɗakin,se alokacin kunyar kayan jikinta takamata tana tunanin tayadda zata keta gari a haka,rasa abunyi tayi dan haka ƙarasa fita tayi zuwa falon gidan wanda ya gaji da haɗuwa jiki a sanyaye,tana fitowa ta tarar da wani yana jiranta,kayanta ya bata sannan yace. "Prince yace a maidake gida". murna ce ta kamata da sauri tabishi abaya zuwa gurin wata haɗaɗɗiyar mota ya buɗe mata baya ta shiga yajata zuwa Gidanta. Maman yusuf. [7/4, 09:40] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Muhammad *follow me on Whattpad @zahrasurbajo* *pure moments of life writers* *page 25-26* Cike da farinciki ƴarfillo ta,shiga falon gidanta gaba ɗaya ta manta dasu Ummu da suke Gidan se yanzu data gansu ta tuno,da sauri ta ajiye kayan hannunta ta nufesu. "Ayya ƙanwata kuyi haƙuri na barku ku kaɗai wlh na mantane"tafaɗi tana daukar Ƙanin Ummu wanda se tsala kuka yakeyi. Sannu da zuwa Ummu ta mata,amsawa tayi cikin sakin fuska sannan tajasu zuwa ɗakinta,toilet ta shiga ta ɗebo ruwa tazo tayiwa Ƙanin Ummu wanka wanda tunda yazo duniya be taɓa samun irinshi ba sosai ta wankeshi,sannan ta naɗeshi a tawul tun kan tagama naɗeshi ya fara bacci kwantar dashi tayi sannan taja Ummu zuwa toilet ɗin itama tamata wanka na haƙiƙa ta tsefe mata gashinta ta wanke sannan suka fito. Dukansu ita tamusu shafa,acikin ƙananun kayanta ta samoma Ummu riga da wando wanda zasuyi mata ta bata tasa shikuma Ƙanin Ummu Megadi taba kuɗi yaje ya siyo masa riguna harda pampers da safa da takalmi,harda madarar jarirai,kamin wani lokaci Ƙanin Ummu yafito fess a matsayin cikakken Jariri me cikar gata. Itama wankan tayi ta shirya cikin kayan mutunci sannan ta dafa musu indomie sukaci, shikuma ta dama madarar ta bashi yasha ya ƙoshi sannan ra goyashi be jima ba yayi bacci,itama Ummu baccinne ya ɗauketa a gurin,ɗaukarta ƴarfillo tayi ta kaira ɗaki ta kwantar da ita akan gado shima Ƙaninta kwantar dashi tayi a kusa da Ummun sannan tabisu da kallon idonta na zubar da hawaye na tausayinsu so da ƙaunarsu na ratsa zuciyarta. Falo ta dawo ta ɗauki Akwatin da Ayman yabata ta buɗe, wani ihu tasaki na ganin abinda ke ciki kuɗine dollers.juyesu tayi tana ƙirgawa,miliyan biyu da rabi ta gani numfashinta har kusan ɗaukewa yayi dan daɗi,kwashe kuɗin tayi zata maidar cikin Akwatin kawai se taga wata ƴar takarda ta faɗo Ƙasa da sauri ta ɗauka tana dubawa,complimentary card ɗinshi ya bata. Ƴarfillo rasa inda zata sa kanta tayi dan murna,tabbas wannan Ayman ɗin bazata taɓa rabuwa dashiba,duk wuya duk runtsi seta mallakeshi,musamman inta tuno abinda ya wakana tsakaninsu jiya jitake kamar tayi tsuntsuwa ta koma su maimaita,sosai ta kamu da mahaukaciyar soyayyarshi a ranta,wacce take fatan takaisu ga Aure. Da la'asar ta ɗauki su Ummu suka shiga gari mota ta siya ta milyan biyu sannan ta siyowa su Ummu sutura da duk wani abu da za suyi amfani dashi,daganan Asibiti tawuce dasu inda takai Ƙanin Ummu aka duba lafiyarshi aka basu magunguna sannan aka rubuta nau'in abincin daya kamata abashi. kasuwa ta shiga ta siyo masa sannan suka wuce Gida cikin sabuwar motar ta da yake dama ta iya driving motarce de bata da ita. Me karatu nasan zeso yasan aynihin labarin ƴarfillo,to muje zuwa dan sanin wacece ita. *Wacece ƴarfillo* Husna Adam shine cikakken sunanta,ƴar Asalin Garin Yola ce,mahaifanta sun rasu da daɗewa,su uku ne a Gidansu ita da ƴan'uwanta maza guda biyu. Tun tasowar husna bata jin magana sam macece meson mu'amala da maza,ko kaɗan bata da kunya,ƴan uwanta sunyi faɗan,sunyi dukan amman taƙi jin magana sam,daga ƙarshema da taga zasu takurata shine ta gudu Abuja da sunan karatu amman sheƙe Ayarta kawai takeyi,dede da rana ɗaya bata taɓa zuwa makarantar ba to dama ay seda Admission ake zuwa Ita kuma Bata dashi,ƙarya tayiwa ƴan uwan nata dan tasamu ta gudu,ayko tunda ta shigo Garin Abuja da wasa bata ƙara bin hanyar Garinsu ba sim card ɗinta ma yarda shi tayi tasa sabo gudun karsu nemeta. Husna kenan wacce a yanzu sunanta ya koma ƴarfillo. *Cigaban labari* Suna isa Gida Ummu sabida ɗoki tasa aka fara gwada mata kayanta,shiko Ƙanin Ummu se wasanshi yake yi,ƴarfillo ko ta biyewa Ummun se gwada mata take yi. Suna cikin hakane Shema'u Duniya tazo Gidan,da faraa ƴarfillo ta tarbeta,itako Shema'u hannu ta miƙawa ƴarfillo tace. "Inji dumus,kyan alƙawari cikawa". Dariya ƴarfillo tayi sannan taciro dubu ɗari ta ɗorawa Shema'u a hannun,wata uwar ƙara ta saki sannan ta rungume ƴafillon tana godiya. "Meye na godiya sekace kyauta na baki aykifa kikamin na biyaki so kidena godemin"ƴarfillo ta faɗi cikin dariya. Daganan hira suka shigayi akan Ɗansarki duk yadda Shema'u taso jin wayeshi ƴarfillo taƙi faɗa mata sede ta bata amsar da sauran matan suke badawa wato Ɗansarkine. Shema'u bata so haka ba amman yata iya tunda dama kowa in taje ta dawo haka take cewar. Se dare ta musu sallama ta tafi cike da mamakin su Ummu da ƴarfillo ta ajiye a Gidanta da sunan zata taimaka musu. Maman yusuf [7/4, 15:48] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@zahrasurbajo* *page 27-28* Har dare ƴarfillo takasa bacci sabida tunanin Ayman gashi tanason kiran wayarshi amman tana tsoron kartayi laifi a gurinshi,hakade ta yiwa su Ummu wanka bayan sunci abinci ta kwantar da Ummu ta goya Ƙaninta a baya dayake rigima yakeyi yaƙi yayi bacci. Haka taita jijjigashi har tasamu shima yayi baccin ta kwantar dashi,tsakiyarsu ta shiga ta kwanta itama cike da tunani gami da kewar Ayman. Cikin dare wayarta ta farkar da ita sabida kiran daya shigo,da kamar karta ɗaga sekuma ta ɗaga muryar da tajine yasa tamiƙe zaune ba shiri ta furta. "Prince Ayman". Dagacan ɓangaran yafara magana cikin isa yace. "Wanne irin abune haka? nufinki yau bazanyi wasa dake ba kenan ko me?,". Cike da tsoro ƴarfillo tace. "Ranka ya daɗe tuba nake kaine kace baa kawo maka ziyara se kayi gayyata shiyasa banzoba wlh". Tsaki yayi sannan yace. "To number na kuma me ya hanaki kira?". "Shima gudun kar inyi laifine yasa bankiraba". "Good to laifin dakike gudun yi to kinyi,ns baki 30 minutes inganki a gabana". Bakin ƴarfillo har rawa yake tace. "Wlh inason zuwa gurinka sede akwai wata amana a hannuna yanzu wanda bazan iya fitowa na barsu su kaɗai adede wannan lokacinba sabida suna buƙatar kulawata wlh don Allah karkayi fushi dani". Ƙit,taji ya kashe wayar hankalinta inyayi dubu yatashi,miƙewa tayi tafara sintiri a tsakar ɗakin,tabbas bazata iya barinsu taje gurinshiba adede wannan lokacin,ko jiya dan bata shaƙu dasu bane amman yau kam bazata iya fitaba. Ƙanin ummu ne ya tashi daga bacci yana kuka da sauri ta nufeshi ta ɗaukeshi ta haɗa mishi abincinshi tabashi yasha taci gaba da jijjigashi,kamar daga sama taji ana buga ƙofar falon gidan,tsorone yacika zuciyarta sabids tasan basuyi da wani zezo tayata kwanaba. A firgice tafito ɗauke da Ƙanin ummu a hannunta tanufi ƙofar leƙawa tayi dan ganin ko waye amman bataga kowaba har tajuya,zata koma se taji anci gaba da bugawa,bakinta ɗauke ds addua ta buɗe ƙofar. Sanye yake cikin ƙananan kaya wanda suka amshi zubi da tsarin halittar shi,Prince Ayman kenan Ɗansarki me abun mamaki. Da sauri ƴarfillo ta matsa masa hanya ya shige cikin falon ita kuma ta maida ƙofar ta rufe,ta bishi zuwa cikin falon,jikinta se rawa yakeyi,fuskarta ɗauke da mamakin ganinshi a Gidanta. Zama yayi akan ɗaya daga cikin kujerun ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana bin jaririn dake hannunta da ido kamin daga bisani yace. "No wonder naji kin buɗe da yawa she mejego ce,amman gaskiya Kin iya shiga bariki tunda har ɗa kika ajiye,amman ina fatan de kin tanaji amsoshin da zaki bashi sanda ya girma yamiki tambayoyi gameda waye ubansa?". Hawayene suka biyo fuskarta sannan tace. "Wallahi Prince ba ɗa na bane hasalima su biyune da yayarsa ƴar kimanin shekaru goma sha ɗaya sanin kanka ko ni ƴar shekara Ashirin da biyar ban isa ajiye ƴa me shekaruntaba,kuma nima wlh taimakonsu nayi bansan daga inda sukeba dan wlh ko suna wannan yaron bashi dashi". Daganan,ta kwashe labarin haɗuwarta da su ummun ta faɗa mishi. "Muje inga yayar tashin"shine abinda Prince ya furta. Miƙewa tayi tana gaba yana binta a baya har zuwa ɗakin,da shigarsu ɗakin ummu ta ɓararraje tana shan baccinta gashin kanta duk ya bazu akan gadon wani akan fuskarta,sanda idonshi ya sauka akanta gabanshine yayi mummunar faɗuwar dabe taɓa yiba. Hannu ya miƙa ya kwashe gashin fuskar tata ya maidashi baya sannan yabi fuskar da kallo,steel gabanshine yaci gaba da faɗuwa badan komaiba sedan kamannin da ummu take masa da masoyiyarsa ta mafarki wacce yayiwa alƙawarin baze kusanci kowacce mace ba a duniya se ita,kuma wacce yake jiran bayyanarta agareshi domin suyi aure,itace wacce ƴan uwanshi da mahaifanshi ke fushi dashi akan yaƙi amincewa da zaɓin da suka yimasa sabida ita. Gaba ɗaya tunanin shi yatafi besan inda yakeba seda Ƴarfillo ta taɓoshi ita a tunaninta duk tausayinsune yasa yatafi dogon tunanin.miƙewa yayi yana me cigaba da kallon ummu Aymana sannan daga bisani ya miƙa hannu ya amshi ƙanin nata a hannun ƴarfillo yana kallo,hannun ƴarfillo yaja suka dawo falon,sannan yace. "Se yanzu na amince ds zancanki gaskiya kinada imani wanda banyi tsammanin me zaman kanta,zata mallakeshiba,kin ƙara samun wani matsayi azuciyata kuma wannan yaron zan sa masa suna yanzu insha Allahu kuma,zan zama uba agaresu yayinda kike mazaunin uwa a gurinsu muddin kika sake kika koyar dasu tarbiya irin taki wallahi zakisha mamakin,hukuncin dazsn miki,daga yanzu duk wata ɗawainiyarsu tana hannuna na ɗauka". "insha Allahu zan yi iya bakin ƙoarina wajan ganin na inganta tarbiyarsu,sede hakan baze hanani innaji buƙata ta tasomin nsƙi neman me kawatmin da itaba tunda de kassn jiki da jini". "Ban,amince ki shigo da wani ƙato domin biyan buƙatarkiba,duk lokacin da buƙatar hakan tataso miki just call me zan taimaka miki amman bazanyi sex dakeba sede i promised you zanmiki abinda ze kawar miki da duk wata shaawa data taso miki,ina fatan kingane?". Murmushi tayi gamida ɗaga mishi kai cike da jin daɗi sabida a ganinta haƙarta zata cimma ruwa. Huɗuba yayiwa yaron inda ya raɗamasa sunansa wato Ayman jinior,sosai ƴarfillo taji daɗin,sunan,ɗaukarshi tsyi taje ta kwantar dashi sannan ta dawo gurin Prince suka shiga ɗaya ɗakinnata inda suka aykata mashaarsu son ransu ammande be kusancetaba sede wasannin kuma be cire kayanshiba sam. Haka sukaita abu ɗaya se karfe huɗu na asuba yabar Gidan tare da alƙawarin ze dawo da daddare. Taku har kullum Maman Yusuf. [7/5, 06:43] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@zahrasurbajo* *page 29-30* Koda da gari ya waye dare yayi prince yazo Ummu na bacci sede Ayman jinior ne beyi bacciba,haka yatafi batare da yaganta ba. Washe gari yasa ƴarfillo takai ummu makaranta irin wacce ke haɗe da islamiyya in ta tafi tun bakwai na safe se shida na yamma zata dawo yayi hakanne dan ya rage zamanta tare da ƴarfillon,kuma school fees gaba ɗaya ya biya tundaga primary har ta gama secondry ya biya mata. Sosai ummu taji daɗin sata a makarantar da akayi se godiya takewa ƴarfillo a zatonta itace ta sata,tundaga wannan lokaci zaman ummu a gidan yayi ƙaranci koda yaushe tana makaranta,in dare yayi kuma tayi bacci. Haka rayuwa taci gaba da tafiya ga ummu cikin kwanciyar hankali ita jinior duk abinda sukeso ko babushi a nigeria inde sun nuna sunaso se Prince yasa ansamo musu shi ko menene kuwa.babu abinda prince yakeso irin yazo ya tadda ummu batayi bacci ba ƙwayar idonta kawai yakeson gani dan tabbatar da hasashenshi,uwa uba kuma yanaso magana ta shiga tsakaninsu dan yaji da wacce kalma zata fara yimasa magana,dan masoyiyarsa ta mafarki akwai wani suna da take kiranshi dashi wanda duk duniya babu me kiranshi dashi se ita.sede duk zuwan da yakeyi tana bacci inkuma yaso zuwa da yamma yanayin aykinshi baze barshi ba. Muamala tsakaninshi da ƴarfillo kuwa ba abinda suka fasa,kullum ba ranar banza,kuɗi kuwa sanadin su ummu ƴarfillo bazata iya faɗin nawa ta mallakaba,gashi prince ya semata wani danƙareren gida acikin garin Abuja ta koma dama wanda take ciki haya takeyi. Faɗin kyau da haɗuwar Gidan ƙauyancine dan gama babuce kawai babu a gidan.ɗakin ummu daban haka na ƙaninta,ankashewa ɗakunan dukiya bata wasa ba. *Bayan shekaru Biyu* Yau jummaa ummu tana gida ba makaranta dayake duk ranar jummaa basa zuwa,tsifa ƴarfillo tayimata ta gyara mats gashin sabida anjima zasuje saloon ayi mata kitso. Sanye take cikin Riga da wando ja da fari ƴsn kanti wandon three quater ne yayin da rigar armless ce,gashinta an ɗaureshi da rimbom fari da ja,ƙafarta sanye cikin takalmi shima fari da ja. *UMMU AYMANA*kenan baiwar Allah. kyau iya kyau ummu tana dashi duk wani abu da ake kira kyau ga ƴa mace ummu ta mallakeshi tun yanzu da take da shekaru goma sha uku a duniya,fitowa tayi falon gidansu cikin tafiyarta me ɗaukar hankali gurin ƴarfillo ta nufa wacce ke ƙoƙarin ɗaurawa jinior igiyar takalminsa amman yaƙi tsayawa se wahal da ita yakeyi.ummu na ƙarasowa hayewa bayanta tayi wanda hakanne ta tilastawa ƴarfillo sakin abinda takeyi ta riƙeta,cike da shagwaɓa cikin gurɓatacciyar hausarta wacce kowa yaji yasan bafulatana ce tace. "Mummy har yanzu baki gama shirya jinior ba bare mutafi da wuri,nifa kinsan banason rana wlh,shimane shegen jiniorn ya tsaya yaƙi tsayawa"ta faɗi gamida dungurewa jinior kai wanda bemasan tanayiba wasan shi yake da teddy bear ɗinshi. "Lalalala kika zagi me sunan daddy tonide bs ruwana kuma sena faɗa masa kin zageshi". A gigice ummu take kallon ƴarfillo kai da gani base sn faɗa makaba ta tsorata bakinta har rawa yakeyi gurin furta. "Don Allah karki faɗa masa wallahi bazan ƙaraba,kuma dama kinga ni ban taɓa ganinsaba zakisa yace baze bari inganshi ba,nide kiyi haƙuri". Dariya ƴarfillo tayi sannan tace, "to karki kuma zaginsa kinji ko". Daganan gama shiryashi tayi sannan ta kwashesu a mota zuwa gurin saloon,akan hanyarsu ta zuwane Prince ya kira ƴarfillo a waya ɗagawa tayi cike da farinciki. "Ina kuma kika kwashi yaran kukaje nazo gidan duk ba ƙwanan?kinsanfa banason yawo". Prince ya faɗi cikin muryar dake nuna bashida walwala. "Ayya prince wlh naje kai Aymana saloon ne ba wani guri najeba". *Aymana*itace kalmar da prince yashiga juyawa akan bakinsa kamin daga bisani yace. "Wacece kuma haka?,ina kika baro ummu da kika tafi yawon raka wata saloon?". dariyace ta ƙwacewa ƴarfillo sannan tace. "Prince kenan to ay ummun ce Aymanar,duka sunanta ne koda yake kai da ummu kawai kasanta to sunanta Ummu Aymana". "Hasbunallahu waniimal wakil"itace kalmar data fito daga bakin prince badan komaiba sedan tsananin mamakin yadda akayi take ɗauke da sunan masoyiyarsa wato Aymana. Ƴarfillo ce ta katse mishi tunani da cewa. "Prince lafiya kuwa?". Da kyar ya furta. "lafiya lau,ko a ina kike please kiyi gaggawar zuwa gidana yanzu na baki 30 minutes"yana gama faɗa mata haka ya kashe wayar. Hankali atashe ƴarfillo ta juya aƙalar motar zuwa Gidan Prince dan a rayuwarta babu abinda ke ɗaga mata hankali irin ganin Prince cikin damuwa. Tana zuwa dayake ansanta buɗe mats get akayi ta shiga,tana yin parking ta ɗauki jinior a hannu ta kama hannun Ummu suka,shiga cikin gidan. Muje zuwa. taku har kullum Maman Yusuf. [7/5, 16:58] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@zahrasurbajo* 😝😝😝😝😝😝 *Tun kan a haifi uwar me sabulu balbela take da farinta,Alhamdulillahi Allah shi ya haska surbajo a zukatan mutane ba wata ƙungiya ba,kuma tunda Allah shi yawa surbajo riga babu wani wanda ya isa ya tuɓe mata,wallahi nan gani nan bari dukiyar uban wani,shiga nayi dan ƙashin kaina batare da shawarar kowa ba kuma yanzu ma na fita ba tare da na shawarci kowa ba,sabida ina da ikon zaɓawa kaina abinda yadace dani,hhhhhhh lalle surbajo kina da matsayi a zukatan al-umma tunda har ake bin groups ana cireki dan kin zaɓi abinda yake dai-dai,hhhhhh lalle na yarda KUNU LABARIN WUTA YAKE JI SHI KO TSIRE ZAHIRI YA GANI,duk mesona ni kaina to mu ɗora daga inda muka tsaya,duk me sona dan ƙungiya ya kamata ka dena dan angulu ta koma gidanta na tsamiya* *page 31-32* Suna shida falon gidan ƴarfillo ta ajiye su ummu sannan ta shiga ɓangaran da prince yake. Yana ganinta ya miƙe yana murmushi rungume juna sukayi sannan ƴarfillo tace. "Prince ka ɗagamin hankali wallahi ban ɗauka,zan sameka cikin nishaɗi ba". murmushi yayi sannan yace, "se gashi kuma kin samenin,ina kika bar su Aymanan?". "suna falo" "ok to muje mu gaisa dan so nake zan fita". dariya ƴarfillo tayi sannan tace. "wlh prince kanada rigima yanzu dama dan ka gaisa dasu ummu ne yasa kace inzo?" dariya shima yayi sannan ya ɗaga mata gira ya kashe ido ɗaya yace. "Laifine dan uba yaso gaisawa da ƴaƴanshi?" "rufamin asiri ni bance ba muje ka gaisa da kayanka" tana kaiwa nan taja hannunshi zuwa falon. gab da,zasu shi falon Prince ya ƙwace hannunshi daga nata,juyowa tayi tana kallonshi murmushi ya mata itama ta mayar masa suka ƙarasa shiga falon,lokacin da suka shigo yayi dede da lokacin da ummu take wasan hajijiya a falon jinior yans dariya juyowar da zatayi ta faɗa ƙirjin Ayman,kwantar da kanta tayi a ƙirjinshi sabida jirin da take gani sedr ƙamshin turaren da tajine ya haddasamata ɗagowa da sauri dan ganin shi ɗinne na mafarkinta ko ba shi bane. Ɗago idonta keda wuya suka haɗa ido ita dashi,bakinsu ne yafara rawa wajan son furta kalma,atare kalmar ta fito daga bakunansu,Prince yace. *HAYATI* ita kuma tace. *QURRATU AYNI* Gaba ɗaya prince rasa inda zesa kansa yayi dan tsananin farincikin dayake ciki na haɗuwa da hayatinsa da yayi bayan ya kwashe tsawon shekara biyar yana mafarkinta da ita yake kwana da ita yake tashi,kullum so da ƙaunarta ke ɗawainiya dashi. A nata ɓangaran itama Ummu tayi matuƙar farincikin ganinshi sabida shekara uku kenan tana mafarki dashi yana taimaka mata kuma yana bata labarai masu daɗi itama kullum se tayi mafarkinshi amman bata taɓa faɗawa kowaba. Ƴarfillo ce ta katsesu daga kallon ƙurillan da sukewa junansu,da sauri suka ɗauke idanuwansu akan juna kowannensu yan murmushi. Cike da mamaki ƴarfillo tace, "Qurratu ayni,hayati,dama kunsan junane da jimawa?" Murmushi prince yayi wanda tunda ƴarfilo take tare dashi be taɓa yimata irinshi ba,sannan yace. "Kema de kinjiki da wani zance,ina na taɓa ganinta ma inba yauba,suna kuma da kikaji na kirata dashi tana kama da wata ƴsr film ɗin larabci ne to kuma jarumar sunanta kenan Hayati shiyasa kikaji na kirata dashi" . murmushi tayi wanda ke nuna ta gamsu da bayanin nashi,sannan tace. "Haba nifa ince,amman kaga ummu harda wani cewa Qurratu ayni,ni nasan larabcin da ake koya matane a islamiyya shine ta karramaka da sunan a farkon haɗuwarku". Murmushi Prince yayi sannan yace,"wannan gaskiya ne" Ranar wuni sukayi a Gidan Prince sam ya hanasu tafiya saloon ɗin da ƴarfillo ta takura cewa yayi ta kawo kayan kitson shi zema Aymanan kitson. Dariya sosai abin yaba ƴarfillo dan ta ƙureshi seta miƙa masa jakar kayan kitson ummun,ayko kiran ummun yayi taje kan kujerar da yake kai kwantar da kanta yayi akan cinyarshi yashiga kitsa gashin,. Ba ƙaramin mamaki abin yaba ƴarfillo ba bakinta har harɗewa yakeyi wajan yimada tambaya. "Prince taya ka iya kitso haka? abun yafa bani mamaki sosai wlh" Murmushi yayi sannan yace. "ba abin mamaki bane ƴarfillo, sabida shekara biyar na kwashe ina yin wannan kitson a mafarki wanda koda wasa ban ɗauka zan iya yinshi a zahiri ba, segashi kuma nayi,wannan kitson da nayi wallahi ya ƙara gasgatamin mafarkina" Dariya sosai ƴarfillo tayi sannan tace. "lalle ka amsa sunanka Ɗansarki me abun mamaki,kace mu yanzu ba ruwanmu da saloon kawai da mun tsefe kai muyo nan" ta ƙarasa zancan tana dariya shima dariyar yakeyi. Ita ko ummu aymana duk inda Prince ya juya idonta na kanshi so take yamata irin hirar da yake mata a mafarki wani sain har bacci zantukan suke sata,shima idonshi nakanta so kawai yake tamasa shagwaɓar da take masa untanjin bacci a mafarki tace se ya goyata,amman dayake shi yafita wayo yanayine da system gudun kar ƴarfillo ta ɗagosu. ƴarfillo ko koda taga ummu na kallon Yman ɗauka tayi dan yau ne tafara ganinsa shiyasa take kallon nasa shiyasa bata ɗauki abun serious ba. Ba su suka baro gidan Prince ba se bayan ishsha'i tare da rakiyar prince da muƙarrabansa. Hmmm me karatu nasan ya ƙosa da son sanin waye Wannan prince ɗin,to muje zuwa. *WAYE PRINCE AYMAN* Taku har kullum Maman Yusuf. [7/6, 09:26] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@zahrasurbajo* *page 33-34* Ayman Abu Ayman shine sunanshi,saurayine ɗan kimanin shekaru talatin da uku a duniya. Ɗa ne ga Sarki Abubakar,Amman tundaga ranar da aka haifi Ayman mahaifinshi yamaida sunan shi Abu Ayman shiyasa yanzu kowa da wannan sunan yasanshi,sarkin dake mulkar masaurata mafi Girma a faɗin ƙasar nigeria,wato masarautar kano. Abu Ayman adalin sarkine me tsoron Allah,yanada mata biyu da ƴaƴa huɗu dayake Allah be bashi haihuwa da yawa ba shiyasa yake tsananin son ƴaƴan nashi. Hajiya Zaituna itace uwar gida wacce ake kira da Hajiya babba,ƴaƴanta uku duka mata,Zainab,khadeeja,Hafsa. Se Hajiya Jameela wacce ake kira da gwaggo amarya itace mahaifiyar Ayman,shi kaɗai Allah ya bata,kuma shine ƙaramin gidan dan sauran duk sun girmeshi. Gidan babu kishi acikin shi shiyasa gaba ɗaya kulawar Ayman ta koma hannun Hajiya babba tana sonshi kamar ita ta haifeshi dan seda yayi wayo ne ya gane ba itace mahaifiyar shiba,haka suma sauran yaran gwaggo amarya na nuna musu soyayya ta aynihi. Gaba ɗayan yayyan nashi sunyi aure dan haka shikaɗaine yarage yanzu a cikin gidan,se kuma ƴaƴan yayyan nashi da suke gidan. Tun tasowar Ayman mutumne da beson hayaniya ko kaɗan dan koya hayaniya take yanzu kanshi ze fara ciwo shiyasa Mahaifinshi ya turashi Oxford University dake turai yayi karatun shi acan bayan ya gama primary da secondry ɗinshi a Nigeria. Zuwan Ayman Turai karatu be lalata tarbiyar da iyayenshi suka bashi ba har yagama ya dawo gida,babu wani abu daya sauya daga ɗabiunshi. Bayan ya dawone ya nuna yanasom shiga aykin soja,fafur Abu Ayman yaƙi amincewa sabida acewarshi in Ayman ya shiga aykin soja aka turashi yaƙi aje tsautsayi yasa akashe shi acan shikenan ya rasa magaji dan haka shi be,amince ba. Duk yadda Ayman yaso shawo kan mahaifinnashi amman fafur yaƙi amincewa,hakanne yasa Ayman dena cin abinci har na tsawon kwana biyu,ganin,Ayman na ƙoƙarin kashe kanshi da yunwane yasa Sarki Abu Ayman amincewa da buƙatar Ɗan nashi,kuma ya tsaya masa har yasamu matsayi babba a gidan sojan. Tunda Ayman yafara aykin soja mutumne shi me juriyar wahala dan har mamaki yake ba abokan aykinnashi dan inyana ayki babu me cewa daga gidan sarauta yafito,hakane yasa ya dunga samun promotion har zuwa yanzu dayake riƙe da miƙamin Conel. Anyi mishi transfer daga wannan jaha zuwa wannan kuma yaje yaƙe yaƙe da dama inda daga ƙarshe de aka ajiyeshi a garin Abuja wanda har yanzu acan yake aykin. Ayman ba iya aykin soja da mulkin mahaifinshi ya dogara dashiba,Ɗan kasuwa ne inda A halin yanzu har kamfani gare shi guda biyu,da na yin takalma da jaka,dakuma nayin atamfofi,sosai Allah yasa albarka acikin harkokinsa shiyasa yake da tarin dukiyar da koshi kanshi besan yawanta ba. Ayman a ɓangaran addininshi mutum ne me tsantsar ruƙo da sallah baya wasa da ita sam kome yakeyi aka kira sallah ze ajiye yaje yayi sallah sannan ya dawo.mutum ne shi me tsananin tausayawa na ƙasa dashi yanada tausayi sosai dan ko a hanya yaga wani na buƙatar taimako yana tsayawa ya taimaka masa Yau Jumma'a yaune Ranar da Ayman ya shirya dan zuwa Ganin gida kano,dayake shi be fiye son tafiya a jirgi ba shiyasa yake da masu tsaron shi har mutum ashirin da biyu motocin dake take masa baya guda huɗune kowacce mota akwai mutane biyar a cikinta se tashi wacce ke ɗauke da mutane uku direba me buɗe masa ƙofa se shi kanshi. Haka motocin suka jeru akan titi daga Abuja zuwa kano inda suke ta sharara gudu,gab,da zasu shiga garin Kano dede wani titi daze sadaka da garin kofa in ka wuce ƙauyen gwarmai kaɗan kamar ance Ayman ya waiga. Wata mace ya hango kwance agefen hanyar tana murƙususu wanda ke nuna alamar bata da lafiya,da sauri yabada umarnin a tsaya, ba musu duka motocin sukayi parking a gefen titin,shida kanshi ya fita yaje inda matar ke kwance tana ta kuka,sallama ya mata,amman da ƙyar ta amsa sabida halin da take ciki,umarni yayi da a ɗauketa asata a mota. Nan da nan akasata a motar da yake ciki,suka ja zuwa cikin garin kano kai tsaye Asibiti aka kaita likitoci suka rufu akanta kamin wani lokaci har ta dawo cikin natsuwarta inda ta buƙaci likitan daya kira mata wanda ya taimaketa dan tayimishi godiya. Dayake koda suka kaita Asibitin Ayman be tafiba dan haka likitanne yafito yace masa. "Ranka ya daɗe mara lafiyar da ka kawo tanason magana dakai". Batare da damuwar komaiba Ayman ya miƙe yabi bayan likitan zuwa ɗakin da matar take. muje zuwa Maman yusuf. [7/7, 08:54] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *follow me on whattpad@zahrasurbajo* *ONE WITH GOD IS MAJORITY* *Page 35-36* Koda shigarsu ɗakin matar tana zaune tana kallonsu. Likitan juyawa yayi yafice yayinda Ayman ya matsa kusa da ita yamata ya ƙarfin jiki,cikin faraa ta amsa da cewa. "Jiki Alhamdulillahi yayi sauƙi,nagode da taimakon dakamin bazan taɓa mantawa dakaiba,kai mutumin kirkine wanda yadace da abun kirki,banida da abin biyanka,sede ka faɗamin abinda kake nema a duniya na tayaka da adduar samun shi" Murmushi Ayman yayi sannan yace. "Nagode sosai da wannan yabon da kikamin,kuma ni azahirin gaskiya jin daɗin rayuwar duniya Allah be rageni da komaiba,na farko ya yoni musulmi,yabani kyau,ya bani ilimi,yabani mulki,yabani ƙarfi da lafiya,ya bani dukiya,sannan yasanyamin sonsa da ƙaunarsa a zuciyata,kinga Allah yamini komai,abu ɗaya nake fata tamin kuma yanzu shine ya bani matar aure tagari domin samun zuria tagari,na ƙarshe shine yasa in ajalina yazo yasa na mutu cikin imani,shine kawai burina". ya ƙarasa zancan yana kalon matar.murmushi tayi Sannan tace. "Duk mutum nagari dole nagartacciyar mace ze aura,dan haka zantaya ka da addu'a nagode da karamci irin naku na bil adama". Tana gama faɗa masa haka ta ɓace a gurin. A razane Ayman ya miƙe yafara waige waige amman ba bu ita ba dalilinta. Da gudu yafice daga ɗakin sede bekai ga inda yakeson zuwaba ya yanke jiki ya faɗi ƙasa sumamme. Da gudu securities ɗinshi suka nufoshi yayinda wasu kuma suka nufi ɗakin,da matar take amman basu gantaba,da sauri suka ɗaukeshi zuwa Asibitin da yake ganin likita. Emmergency aka kaishi tuni likitoci suka rufu akanshi dan bashi taimakon gaggawa,wanda seda suka kwashe awa uku akanshi kamin su samu numfashinshi ya dedeta. Sanda labarin ya samu ƴan gidan su hankali a tashe suka iso Asibitin,halin da suka,ganshi seda suka zubar masa da ƙwalla. Tsananta bincike akayi akan a gano matar daya taimaka,ko ina jamian tsarone akan tituna suna bincikar ababen hawa😝domin kamo matar. Wasa wasa seda Ayman Yayi wata biyu a kwance ba magana,abun ba ƙaramin ɗaga hankalin duk wani me sonshi yayiba,daga ƙarshe de na gargajiya aka koma yimasa inda Allah yasa aka dace yafara samun sauƙi,kamin sati uku ya,warke sarai ba me cewa yayi jinya,koda aka tambayeshi abinda ya firgitashi be ɓoye musu ba ya sanar dasu komai,ayko kowa seda ya girgiza dajin batun. Daga ƙarshe de addua suka shiga tayashi akan,Allah ya tsare shi,aduk inda yake. Tundaga wannan Lokaci Ayman yafara mafarki da wata yarinya ƙarama tana kuka gata a tsakiyar zakuna tana miƙo masa hannu akan ya taimaketa. Kusan kullum seyayi mafarki da ita,sannu sannu har takai ga ya taimaki yarinyar har soyayya tashiga tsakaninshi da ita,kullum inya kwanta da kalar mafarkinta da zeyi,tun abin be damunshi har yafara ɗaga mishi hankali,Hajiya babba ya sanarwa,addua tace ya dunga yi Allah ya tabbatar da alkhairi. Sannu a hankali son yarinyar ta mafarki yafara shiga zuciyarshi,har yayi girman da yakejin inde ba ita ya aura ba baze iya rayuwa ba. Kullum cikin nemanta yake ko ze ganta sonta na wahal da zucuyarsa,kuma duk sanda zeyi bacci se tazo masa a mafarkinsa sunsha hirarsu ta masoya ta tafi,ganin hakane yasa Ayman siyo maganin bacci ya ajiye duk sanda kewarta ta dameshi se yasha ya kwanta bacci dan ya ganta. Gaba ɗaya yafice daga natsuwarshi burinshi kawai ya ganta,ba abinda ke burgeshi da ita irin blue ice ɗinta,uwa uba shaawarta kullum ƙaruwa take a zuciyarshi,Addua kullum yinta yake dan ganin burinshi ya cika. Ganin halin dayake cikine Magaifinshi ya yanke shawarar yimasa Aure ko ze samu kwanciyar Hankali,koda ya tuntuɓi Ayman da zancan son yimasa Aure,fafur ya tubure akan shi ba yanzu zeyi Aure ba. Tun Mahaifinshi na ɗaukar abun wasa harde yaga da gaske yakeyi dan haka ya yanke shawarar ɗaura masa Aure da yarinyar takwaransa sarkin sokkoto,wacce ta gama karatu amman har lokacin Allah be kawo mijin aure ba, *FIDDAH*kenan ƴa ga sarkin sakkoto. Muje zuwa Taku har kullum. Maman Yusuf. [7/7, 22:13] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *DA BAZARMU WRITERS* *ASSOCIATION* *Page 37-38* Lokacin da Ayman yaji hukuncin da mahaifinsa ya yanke na haɗashi aure da fiddah har suma yayi,duk da besanta ba amman ya tsaneta. Kuka ya dunga yi da idanunshi kamar ba soja ba akan mahaifinshi ya fasa auran dolen da yake shirin yi masa,kunnen uwar shegu Sarki Abu Ayman yayi da roƙon da Ayman ɗin yake masa. Memakon Ayman yaga an fasa se gani yayima anata shirye shirye har kuɗin gaisuwa ankai,ba abinda ke ɗaga masa Hankali irin,alƙawarin da yayiwa Aymana wato hayatin sa na cewa shi mijintane ita kaɗai,daga ita ba ƙari har ƙarshen rayuwarshi. Yau mahaifinshi ya matsa masa akan yaje su gana da fiddah,bashi da yadda zeyi haka ya ɗauki hanyar sokoto,koda ya isa sun karramashi sosai kowa se murnar ganinshi yake,daga ƙarshe de aka turo masa Gimbiya Fiddah domin su gaisa. Tafe take kuyanginta na binta a baya suna riƙe da kasan rigarta dake jan ƙasa,yayin da dogarai su kuma keta faman yimata kirari,a haka har ta ƙaraso falon da aka saukeshi. Lokacin data shigo kanshi a ƙasa yake ƙamshin turarantane yasa shi ɗagowa dan ganin waye. Ganinta yayi zaune a ɗaya daga cikin kujerun falon tana ta faman sakar masa murmushi gami da kashe masa ido ita ala dole zata ja hankalin shi. Ba tare da damuwar komai ba Ayman ya kalleta yace. "Don Allah kije kicema yayar taki ta fito haka mu gaisa, nifa ba kwana zanyi ba bare ta ɓatamin lokaci a banza"ya ƙarasa zancan yana me duban agogon hannunshi. Zancan nashi ba ƙaramin ƙular da Gimbiya Fiddah yayi ba,wato ma dan rainin wayo ita bata kai matsayin wacce zata zama matarsa ba sede yayarta. Fuska a haɗe tace. "Bangane nakira maka yayata ba, gurina kazo ko gurin yayata?". Cike da mamaki ya maida kallonshi kanta,sannan yace. "Wai kina nufin kece wacce aka turoni gurinta?". Murmushine ya kubce a kan fuskar Gimbiya ta ɗauka abun arziƙi ze faɗa da saurinta tace. "Haba koda naji nasan dan baka ɗauka ni aka baka bane yasa kake ta fushin nan, to ay nice Gimbiya Fiddah".ta ƙarasa zancan tana fari da idonta. "Kan bala'i!!! Wallahi da sake,yanzu ke in banda balagar zuci uwar me zakimun a gidan auran idan na aureki? ,tambayarki nake Uban me zaki iya mun inna Aureki?"ya faɗi cikin ɗaga murya. Ido Fiddah ta ƙwalo waje tana kallonshi cike da tsananin mamaki, daurewa kawai tayi ta bashi amsa da cewa. "Duk abunda kowaccen macan Aure takewa mijinta shi zan maka inka Aureni". "Da wannan tsukakken kwankwason nakine zaki min abinda cikakkun mata ƙosassu suke yi a gidansu na Aure?"ya tambaye ta kamar ze doketa. Gimbiya tafara fusata dan haka amsa ta bashi da cewa. "Kabar Raina allura wlh itama ƙarfe ce,kuma da ƙosassun matan a gari mahaifinka ya tsallakesu yace Ni Gimbiya Fiddah ni nafi dacewa da Yarima Ayman". Ayman sabida tsananin takaici da baƙin ciki ko amsa be bata ba ya fice daga falon. ko takan yiwa mahaifinta sallama be biba yabar masarautar zuwa tasu Masarautar. Cikin dare ya iso kano dan haka dole ya haƙura da son ganin mahaifinsa zuwa gari ya waye,amman fafur ya gaza yin bacci dan baƙin cikin zaɓin da mahaifinsa ya masa. Tun daga sallahr Asuba Ayman ɓangaran mahaifinshi ya nufa yana zuwa ko gaisuwa beyi ba ya fara ƙorafi. "Haba Abba meyasa zakamin haka? taya zaka rasa wacce zaka zaɓamin se waccan tsinken sakacan?,ni wallahi bana sonta ko kaɗan banga abinda ya burgeni a tattare da ita ba , ita ba irin macan dana keso bace,dam haka nide wlh aka aura min ita se anyi danasani,tunda nace banaso". Marin da mahaifinshi ya ɗauke shi dashi ne ya dawo dashi daidai,Ayman cike da mamaki yake kallon mahaifin nashi,dan tunda yazo duniya dunguri mahaifinshi be taɓa yi masa ba, yau gashi akan waccan talatsuruwar ya mareshi. Ji yake kamar yaje ya kamata da duka,mahaifinshine ya katse shi da cewa cikin kakkausar murya. "Ni sa'an ka ne da zaka zo gabana kana faɗamin magana son ranka?to ita naga ta dace da kai kuma ya zamar maka dole ka zauna da ita matuƙar nine mahaifinka,tunda ita kace tsinken sakace ce ina taka naman,?wawa kawai shasha wanda besan abinda ya dace dashi ba"ya ƙarasa zancan cikin fushi. Zuwa lokacin Ayman kuka yake sosai na takaici,zuciyar ƴan mazance ta motsa ya miƙe a fusace ya dubi mahaifinsa. "Wlh Abba ko kasheni zaka yi bana son Fiddah ,zan ƙara maimaita maka wlh bana ƙaunarta muddin aka aura min ita akwai matsala, kuma wlh tunda aka ƙi ji ba za'a ƙi gani ba",be jira amsar Abban nashi ba yasa kai yafice daga ɗakin yabar Abban nashi cikin matsanancin mamaki. Taku har kullum Maman yusuf. [7/8, 21:55] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 *DABAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *Ayi haƙuri da wannan kamin safiya* *Page 39-40* Ran Sarki sosai ya ɓaci game da abinda Ayman yamasa amman se ya shanye duk ɓacin ran nasa. Shi ko Ayman yana bari gurin Abban nashi kayanshi ya haɗa yabar garin be musu sallama ba ya koma bakin aykinshi. Tafiyar da Ayman yayi ita ta ƙara tunzura mahaifinshi nason ganin ya aura masa Fiddah,dan haka tuni ya matsa aka tsaida ranar auran. Fiddah amarya de gyara take sha abinku da ƴan sokoto sosai suka haɗata ta haɗu,tun saura sati biyu bikin masarautar sokoto tafara shagalin bikin. Saɓanin masarautar kano,dan ko angon basu ganshi ba bare suyi shagalin bikin. Duk wayoyinshi kashe su yayi gudun karma akirashi,yayinda kullum Hayatin sa na zuwa ta ɗebe masa kewa,shiyasa duk yamance damuwar da ke damunsa. Rana bata ƙarya. Yau dubban jamaa suka shaida ɗaurin auran Ayman tare da Amaryar sa Gimbiya Fiddah,ɗaurin auran da akayishi batare da sanin Angonba danshi gaba ɗayama yamanta da wata Fiddah. Ana gama ɗaurin Aure aka sako Amarya da muƙarrabanta a jirgi zuwa kano,sosai dangin Angon suka tarbeta duk wani abu na alada sun mata shi,daganan aka kaita gurin Sarki Abu Ayman,sede ga mamakinsu a mota suka sameshi a zaune,ana kawota yace ta shiga mota ba musu aka sata aciki,tana shiga direba yaja basu zame ko inaba se airport suna zuwa komai is ready dan haka shiga kawai sukayi jirgin ya ɗaga zuwa Birnin tarayya wato Abuja. Basu daɗeba suka isa motoci suka tarar suna jiransu,shiga sukayi aka kaisu Gidan Ayman wanda besan bidirin da ake yiba danshi ba gwanin shiga social media bane bare yaji an masa aure,tv ko yadena kalonta sabida hayatinsa tana da kishi. Dayake week end ne tana gidan yana bacci,har ɗakinshi sarki Abu Ayman yashiga tare da Fiddah wacce se kuka takeyi,suna shiga yamata umarni da ta zauna,zaman tayi sannan shi ya ƙarasa gurin gadon da Ayman ke kai yana bacci se murmushi yake base nfaɗa muku ba shida Hayatinsa ce. Girgizashi yayi,da sauri Ayman ya miƙe a fusace dsn ganin wannen ɗan rainin,wayonne. Carab ya haɗa ido da mahaifinsa,wata kunya ce gami da mamaki suka kama Ayman duƙar da kanshi yayi ƙasa ya kasa magana kuma ya kasa kallon idon Abban. "Ba wani abu bane ya kawoni ba amaryarkace na kawoma wacce aka ɗaura muku aure yau,gatanan na kawota inde ka haifu kuma kacika tantiri,inna fita kabiyo da gawarta,". yana kaiwa nan ya juya gurin Fiddah yace. "Ki ta haƙuri kinji aljanna baa samunta a kwance,na barki lfy" Godiya Fiddah takeyi tana kuka a haka Abu Ayman yafice daga gidan cike da tausayinta,jirgi l Ya lula dashi da muƙarrabansa zuwa kano. Jikin Ayman gaba ɗaya yayi sanyi game da kalmar tantiri da mahaifinshi ya kirashi da ita. Ko kallon inda take beyiba yafice daga ɗakin ya koma wani ranshi a bace,tabbas Abbanshi yagama cutar dashi tunda ya aura masa waccan skeleton ɗin,tabbas ko tantama bayayi yasha alwashin yimata hukunci dede da abinda aka masa. Maman yusuf [7/9, 19:01] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *FATY AXLAND THANKS FOR THE CARE AND SOPPORT,DA BAZARMU WRITERS NA GAISUWA* *page 41-42* Haka suka wuni a ɗaki ba wanda yaje gurin ɗan uwansa,Fiddah ta sha kuka har ta godewa Allah. Se yanzu take danasanin ƙin bin shawarar ƙawarta JIDDAH ABBAS,domin seda ta gargaɗeta akan karta yarda ta auri Ayman tunda ya nuna ƙarara baya ƙaunarta,amman se tayi kunnen uwar shegu da shawarar Jiddan ta biyewa ta ɗayar ƙawar tata wato SALMAB JB,inda ta nuna mata ay ansha yin hakan ayi aure namiji baya sonka kuma daga ƙarshe yadawo yana sonka. Ci gaba tayi da kuka amma bata karaya ba har yanzu bata sauka akan tsarin Salmab ɗin ba,tanaji a ranta cewa watarana Ayman ze sota. Shiko anashi ɓangaran ganin ya gaji da zama a ɗakinne yasashi fitowa falo ya zauna,ya kunna kallo ji yake gaba ɗaya ya takura acikin gidan,wallahi da badan yana gudun kar Abban shi ya mishi bakiba da ba abinda ze hana be saketa a darannan ba. Da misalin ƙarfe takwas na dare Fiddah ta fito zuwa falon gidan dan neman abinda zataci sabida yunwa take ji sosai,dinning ta nufa shima dakyar ta gano inda yake. Kulolin abincine a jere a gurin wanda da gani yanzu kuku yagama jerasu dan ko alamar taɓawa babu,da sauri taja kujera ta zauna ta zuba abincin tafara ci ,ta kusa cinyewa Ayman ya nufo gurin,yana ganinta yaji duk duniyar tamasa zafi,rai a ɓace ya nufeta,tana ganin ta nufota ta miƙe a tsorace tana raba idanu. yana zuwa ɗauketa yayi da wani gigitaccen mari,ze fara balai idonshi yadauka kan ayka aykar da gimbiya tayi,ba komai bane se fitsarin daya gani yana biyo ƙafafunta,sabida tsabar zafin marin da taji,takasa kuka ta ido setacan,jikinta ɓari yake kamar mazari,sabida tunda take a duniya batasan zafin duka ko mariba,dan babu wani mahaluki daya taɓs yimata ɗaya daga cikin su se yau. Dariya ce ta kwacewa Ayman wacce besan sanda tafito ba kujera yajs ya zauna yana kallonta yana dariya,gaba ɗaya tagama fitsare jikinta da fitsarin. "Kan balai fitsari kikayi daga ɗan wannan mari? toko lallai ba,shakka in na miki wani kalar se kinyi kashi,kuma wallahi bazaki jamin abin kunyaba ke da kanki zaki gyara gurin bazansa masu ayki ba,ni nayi mamakin ma yadda akayi wannan fitsarin me uban yawa ya taru a wannan marar taki,maza ki ɗauko abin gyarawa ki gyaramin gida tun kan afara jiyo kukanki a gidanku". Fiddah baki ya mutu se hawaye wanda tasamu suka fito da kyar,har zata wuce yasata ta dawo sabida ganin dayayi fitsarin na ɗigowa daga jikin siket ɗinta. "bazaki gama lalatamin gida da ƙazanta ba,dan da gani ko dama can ke ƙazamiyarce,dan haka sede ki cire wannan kayan adede inda kikayi fitsarinki,in kuma ba hakaba na lahira se yafiki jin daɗi ". Ido ta waro da kyau dan tabbatar da abinda kunnanta yajiyo,ganin ba alamar wasa ko wargi a tattare dashine yasa tagane da gaske yake nufin rabata da kayanta. tsugunawa tayi tafara bashi haƙuri. "Prince don Allah kayi haƙuri kabarni da kayana a jikina wlh zan,goge duk inda na ɓata".ta ƙarasa zancan cikin kuka. "in tunaninki zan ga wani abune a jikinki ya burgeni to kidena kawai raayina kenan wallahi sekin tuɓe kayan nan anan inko ba hakaba wlh inna fara dukanki se gari ya waye". Jiki na ɓari Fiddah ta fara tuɓe kayanta tana kuka abin gwanin,tausayi amman prince be tausaya mata ba,tuɓewa tayi gaba ɗaya daga ita se pant da bra da sauri tajuya masa baya tana ci gaba da kukan yayin da ta kare ƙirjinta da hannayanta. "Kan uba toshi pant ɗin da kika barifa,ko nufinki shi bazaki cireba? shi dayafi ma kowanne shan fitsatin". Haƙuri zata bashi da amman ganin ya miƙe yana shirin kwance belt batasan sanda ta cire pant ɗinba sabida tsabar gigita har da bra ɗin ta cire ta tsaya a gaban tana kyarma. Wata uwar dariyace ta kwace masa wacce yayi iya yinshi dan ganin ya shanyeta tunda Fiddah tafara cire kayan amman abun yacu tura,dan dariya ko magana ya kasa se dariya yake yana nuna ta. Se lokacin Fiddah ta gane Ayman yayi niyyar tozartatane shiyasa yace ta tuɓe a gabanshi,da gudu ta ruga ɗakin da Abba yakaita ɗazu, kulle ƙofar tayi ta faɗa kan gado tashiga rusa kuka. Shiko Ayman gudun Fiddah ma dariya ya ƙara bashi,wanda dalilin dariyar ne har yafaɗa kan fitsarin be saniba. Jinshi cikin fitsarinne ya ƙatse dariyar da yake da sauri ya miƙe tsaye,a fusace ya nufi ɗskin da ta shiga. yayinda ita kuma tana tsaka da kukanne wayarta ta shiga ƙara,dubawa tayi dan ganin me kiran. *Salmab jb lagos*,shine sunan da tagani da sauri tashare hawayanta ta ɗaga wayar. to ko me zasu tattauna ita da aminiyar tata? Muje zuwa Maman yusuf. [7/10, 07:06] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *Page43-44* "Hello ƙawata wlh kamar dama kinsan nemanki nakeyi".Fiddah ta faɗi cinkin damuwa. Daga can ɓangaran Salmab tace. "Amarya da damuwa kuma,kode Prince ya kashe boss ne?"ta ƙarasa maganar cikin dariya. "hmmm wannan ay tafi ƙarfin kashe boss kawai harda actor ɗinma duk yakashe"ta kai ƙarshen zancan cikin kuka. Hankalin salmab ne yayi matuƙar tashi a gigice take tambayarta abinda ya faru. Da ƙyar tasamu Fiddah tai mata bayanin komai daya faru. Wata uwar shewa Salmab tayi gamida kwashewa da dariya daga bisani tace. "Tur wallahi,kinban kunya yanzu har akwai wani wulaƙanci da ɗa namiji ya isa ya miki baki rama ba?wlh babu shi,to bari kiji in gaya miki,koda wasa karki sake nuna kina tsoronsa,dazaran yafara dukanki wallahi ki riƙe masa gabansa tsaf zaki ga yadena ya koma baki haƙuri,haba ƙawata me akayi akayi prince da har ze saki kuka,?kuma tunda shi yasa kikayi tsirara,to karki sake kisa kaya daganan zuwa shekara se in da kansa ya samiki,kuma ko uban waye a gidan ki fito haka wlh zaki ban labari". Tunda Salmab ta fara huɗubarta Fiddah take dariya,duk da batayi mamaki ba,dan Salmab bata tsoron kowa duk wanda ya mata se ta rama. Godiya Fiddah tayiwa Salmab sannan ta kashe wayar,hakan yayi daidai da ƙarasowar Prince ƙofar ɗakin,buga ƙofar ys shiga yi cikin zafin rai yana kiran sunanta. "Ke!!!dan ubanki bazaki fito ki gyara gurin can ba,gashi kinsa nima fitsarin ya ɓata kayana,kinsan Allah in Baki fitoba nidake ne". "wlh bazan gyara ba sede ya shekara a haka,angaya maka ni baiwar gidankuce?,uban wa yace kamin marin dayasa nayi fitsarin?wlh sede ka gyara amman ni bazan gyara ba,mugu kawai". cewar Gimbiya Fiddah daga cikin ɗakin. Ayman zuciyarshi har tafasa take sabida baƙin ciki,dukan ƙofar yashigayi iya ƙarfinsa amman taƙi buɗuwa,cikin zafin rai yace. "in har kinsan kin haifu cikin ubanki to kizo ki buɗe ƙofar nan na faɗamiki uban dayace na marekin". Ba musu Fiddah tazo ta buɗe ƙofar,sede yana shiga ta cafke gabanshi da hannunta iya ƙarfinta,ƙara Ayman ya saki,sannan jikinshi ya kama rawa,ko motsi ya gaza yi idonshi ya rufe yayin da hannunshi ke nuna alamar tayi haƙuri. Dariya Fiddah tayi na ganin taci nasara,shawarar Salmab ta mata rana. "wlh daga yau se yau koda wasa kakuma yunƙurin dukana se na maka kaciya sabida ni ba baiwa bace bare kasa a gaba kana azabtarwa". Gyaɗa kai Ayman yake alamar yaji ya amince,sakar masa tayi amman kamin tasaki seda ta murɗa. Ayman kasa motsawa yayi ita ko toilet tashige tayi wanka ta fito ko tawul bata sako ba,ta haye kan gado tayi shigewarta bargo. D ƙyar Ayman yasamu ya iya ficewa daga ɗakin,ya nufi nashi,har ya kwanta yatuno da fitsarin dasauri ya miƙe yaje ya gyara gurin,yadawo yayi wanka ya kwanta,(Anya Fiddah taci bulus kuwa?) Wai wacce irin surace da Fiddah dayasa Ayman ke mata dariya🤔? Fiddah ko ince muku model,fara ce sosai bata da tsayi amman ba gajera bace,tana da yalwar dogon gashi a kanta baƙi me ƙyalli,tana da idanuwa masu haske gami da girma daya dace da kyakkyawar doguwar fuskarta me ɗauke da dogon hanci me kyan tsari,bakinta ƙaramine me kyau,yayinda ƙirjinta ke cike fam da na shanu,cikinta zuwa marar ta a shafe suke sosai yayinda ƙugunta ya buɗe daga ƙasa wato cocacola shape,in tana tafiya jikinta babu inda baya rawa kamar tarwaɗa,Gimbiya Fiddah kenan. Shiko Ayman ba komai yakewa dariyaba se shafewar cikin nata dan shi anashi ganin ba haka mace ya kamata ta zama ba,sabida kullum consider yake da Hayatinsa wacce take yarinyace ita amman yana mata kallon babbar mace. muje zuwa. Maman yusuf Muje [7/11, 13:25] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud. *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *ATTENTION!!!!readers har yanzu fa muna cikin labarin Ayman ne tun kamin ya haɗu dasu ummu Aymana,so kudena ruɗewa munkusa ɗawowa ci gaban labarin,sannan don Allah kuyimin uzuri na rashin ganin post akai akai,yanayine ya sauya,surbajo neman kuɗi take,dan haka dole nafi karkata can,zan dunga yin iya bakin ƙoƙarina wajan ganin na muku,nagode,ga ƴar bautar ƙasa nan nafara posting Allah yasa ya karɓu a zukatanku ameen*. *page 45-46* Ayman kwana yayi beyi bacciba sabida baƙin cikin fiddah,kuma bakomai yasa ya kwashe fitsarinba sedan gudun abun,kunya amman da bazai kwasheba. Ba abinda yaba ayman mamaki irin kama gabanshi da fiddah tayi aranar da aka kawota gidanshi,kuma take yawo tsirara a gabanshi batare da taji kunya ba,wanda shi a ganinshi tabbas fiddah ƴar duniya ce dan inde basu ba ba wata amarya da,zata iya yin hakan a daranta na farko. haka ya kwana wannan tunanin,gamida neman mafita,ita ko anata ɓangaran bacci take harda munshari batare ds damuwar komaiba. washe gari da asuba fiddah,Waldrope ɗinshi ta buɗe ta ɗauki doguwar rigarshi tasa tayi sallah,tana idarwa ta tuɓe ta maidar mishi inda ta ɗauka,takoma baccinta. Bata farkaba seda gari ya waye,tayi wanka,ta ja handbag ɗinta ta ɗauko kayan kwalliya ta tsantsara,tana gamawa ta mayar tafice daga ɗakin timbir timbir abunta tana juya mazaunai. A daidai wannan lokacin Ayman ne zaune a falo shida Abokinsa Faisal daya kawo mishi ziyara suna hira,jin motsin tahowane yasa Ayman maida hankalinshi hanyar dayaji motsin,shiko faisal hankalinshi nakan tv ko motsinma be jiba. Fiddah ya hanga tafe tana rangwaɗa kai ka rantse da Allah cikin kaya take,tsallan da Ayman yayi daga inda yake yadira gabanta me karatu inda kana gurin se kaji tsoro. yana isa girinta beyi watawata ba yasureta da gudu zuwa ɗakinta,harga Allah Fiddah bataga Faisalba amman da Ayman yafara faɗa mirtsikewa tayi tabashi amsa da cewa. "kaga malam ka isheni ina abun yake,da har zakayi kishin wani yaganni tsirara,to bari kaji ni nan dakake ganina wlh jina nake kamar da kaya ajikina dan haka kabarni naje mugaisa kawai,"ta fara yunƙurin kwacewa daga ruƙon daya mata. "Haba silinder baki da hankaline zaki fita tsirara wannan ay tozartani zakiyi,in wani yaganki a haka pls kisa kaya se kizo ku gaisan". "Ayni duƙ abinda ze tazartaka sonshi nake,kuma kaya wlh bazan saka ba,silinder da kake faɗi kuma wannan ƙarya kake wlh,dubeni da kyau,full option ce ni"tana kaiwa nan a maganar tagirgiza mazaunanta da ƙirjinta cikin wani yanayi daya jefa ayman cikin wani hali wanda ko farkon ganinta tsirara be taɓa jiba. Bin ta ya dunga yi da ido tana jujjuyawar,da kyar ya fauke idonshi ya kamota ya zaunar da ita akan gadon sannan shima ya tsugunna,ya ɗora hannayanshi akan cinyarta ya kamo hannunta,ya fara magana. "in kika fita a haka mutuncinkine ze zibe dana masarautar ku da tamu,don Allah kisa kayanki kinji princess". Wata uwar harara ta doka mishi,sannan tace. "wlh bazan sakaba🙄"ta ƙarasa zancan dayin fari da idanuwanta. Ayman ganin da gaske takeyine yasa yamiƙe ya ɗauko wasu riga da wando acikin kayansa yazo ya fara saka mata,kuma bata ƙi yarda ba tsayawa tayi tsaf ya shiryata. komawa gefe yayi yana kallonta,tabbas se yanzu ya fahimci fiddah macece ta nunawa aboki,ammam da ko ganimta yake akasin hakan. itako se wani juyi take tana wani gantsarewa ita ga haɗaɗɗiya. hularshi ta cire tasa akanta sannan ya jata zuwa falon inda Faisal ke zaman jiranshi. Mamakine yakama faisal na ganin Ayman ya ruga da gudu wanda shi besan dalilin gudunba,shiyasa yazauna yadawo yatambayeshi abinda ya faru. muje zuwa takuce har kullum *Surbajo* [7/11, 20:14] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀🎀 *DA BAZARMU WRITERS ASSICIATION* *AISHA ALIYU GARKUWA WANNAN SHAFIN NAKINE NAGODE DA ƘAUNAR DA KIKE NUNAMIN* *Page 47-48* Koda suka fito falon faisal ba ƙaramin mamaki tayi ba dan shi ya ɗauka neman mata yafara,binsu kawai yake da ido har suka sami guri suka zauna. Ayman se kare fiddah yake bayason Faisal ya ganta,kada haƙuri Faisal yayi ,tambaya yafara da ita. "Ayman bangane bafa,wannan kuma wacece?". Dariya,Ayman yayi sannan yace. "Fiddah kenan ƴa ga sarkin sokoto,matar da mahaifina ya auramin batare da sanina ba,its means de uwargidana ce". "wlh se yanzu nagane ta,dayake a social media kawai nataɓa ganinta.but,meyasa baa gayyacemuba?" inji faisal wanda ya faɗa yana dariya. "Kai kenan abokin ango kana ƙorafin baa gayyaceka ba,ni kaina angon,ina bacci se farkawa nayi aka miƙo min ita". Dariya suka sa shida Faisal ɗin,yayinda Fiddah tacika fam,da takaici,gaisheta faisal yake amnan ko kallo be isheta ba,illah ma tsaki da ta masa tabar gurin. jikinshi ne yayi sanyi amman Ayman ya ƙarfafa masa guiwa ta hanyar bashi labarin abinda ke tsakaninsu wato haɗasu akayi,shiyasa taji haushi. Faisal be jimaba yabar gidan,bayan Ayman yamasa rakiya gurin,fiddah ya koma wacce yasameta ta riƙe ƙugu tana girgiza kai da gani kasan balai take ji. "Yanzu dan rashin mutunci shine harda faɗa masa haɗa mu akayi bakai ka ganni kace kana so ba,ko?". "To ƙarya nayi?ba haɗamun akayiba?koko na taɓa cewa ina sonki?ke da bakinki kince Abbana nane yaga kindace dani ya zaɓamin". ya ƙarasa zancan yana dariya. Iya takaici fiddah taji shi rasa me zata ce mishi tayi kawai seta rushe da kuka,ƙarar wayar Ayman ce ta katseta,ɗauka yayi yace. "Ranka ya daɗe antashi lafiya?". Hakan daya cene yasa ta gane da Abbanshi yake wayar. "Gobe ku taho Kano sabida zaayi taron bikinku,dangin,Fiddah ma tuni suna nan,saura kaƙi kawota,tantiri" Shine abinda sarki ya faɗi ya kashe wayarshi. Ran Ayman be masa daɗiba,game da wannan sabon sunan da mahaifinsa ke kiranshi dashi,hakan na nufin har yanzu ma daya aura masa Fiddahr bedena fushin dashi ba kenan?. jiki asanyaye ya miƙe yafice daga ɗakin. Itama Fiddah jikinta ne yayi sanyi tausayinsa ya kamata,tabbas tasan sabida itane suke samun saɓani shida mahaifinsa. Miƙewa tayi tabi bayanshi.. Koda tashiga ɗakin a tsaye ta sameshi,zuwa tayi ta dafa kafaɗar shi,juyowa yayi yana kallonta. "Don Allah kayi haƙuri nasan nice silar faruwar komai insha Allahu ze wuce,don Allah kayi haƙuri"ta ƙarasa zancan cikin kuka. Tausayinta ne yakamashi besan sanda yajawota ya rungume ba,ita ma rungumeshi tayi,sannu a hankali na tsinto bakin Ayman acikin na fiddah yana kissing ɗinta. gaba ɗaya yagama burkita mata seti,itama fara mayar mishi tayi,haa abunfa mamaki yaci gaba da bani,ay banyi auneba se hangosu nayi akan gado. anya,Ayman ne kuwa,kode mafarki nakeyi?. Sosai Hankalin Ayman yabar jikinshi,wasa yake da duk jikinta,wani ya tsotsa wani ya shafa,kai abinde baa cewa komai,tuni yafara rabata da kayan jikinta,wanda hakanne yadawo da fiddah daga duniyar daɗin data tafi. da sauri ta riƙe mishi hannu tana bashi haƙuri,amman ina wanda yayi nisa bejin kira. Kuka fiddah tafara amman Ayman kamar kurma bemasan tanayiba. ya rabata da kayanta gaba ɗaya,yafara karanto adduar saduwa da iyali. ألهم جنبني من الشيطان و جنب الشيطان ما رزقتنا. Fiddah ido fa ya raina fata,sede kamar wanda aka tsikara taga ya saketa ya murgina gefen gadon. Kallo ta bishi dashi kana,daga bisani ta sauka ta ɗebi kayanta ko sawa bata tsaya yiba ta kwasa aguje zuwa ɗakinta tana yiwa Allah gidiya daya kuɓutar da ita daga azabar first night🤓. Tana shiga ɗakin ta maida ƙofar ta rufe harda key. wanka tayi sannan tazo ta haye gadonta tana tuno abinda ya wakana a tsakaninta da Ayman,duk inda hannunshi ta taɓa ajikinta ji take kamar a lokacin yake taɓawar. Fulo ta rungume tana dariya.har bacci yayi awon gaba da ita. Muje zuwa. Surbajon kuce [7/12, 21:14] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud.. *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *YASMEEN TAFEESU KINFI SAURAN MATA WANNAN SHAFIN NAKINE ALLAH YA ƘARA DAUKAKA,YA HAƊA KANMU DAN ALFARMAR ANNABI,AMEEN* *page 49-50* Anashi ɓangaran Ayman kuwa ba komai ne yasa tafasa kusantar Fiddah ba sedan tuno alƙawarin dayayiwa Hayatin sa nacewa shi natane,kuma itace Mace ta farko da zata fara ɓareshi a leda,shiyasa yafasa kusantar Fiddah. Da ƙyar ya samu ya zubar da abinda ya taso masa akan gadon,wanka yashiga ya jima a toilet ɗin sannan ya fito. Kwanciyarshi yayi cike da tunanin Hayatinsa,kullum burinshi da fatanshi shine yaushe ze ganta?,a haka bacci ya ɗaukeshi me nauyi inda ya dunga mafarkin Hayatinsa. Washe gari da wuri dukansu suka tashi,suka shirya suka kama hanyar kano,amman seda suka tsaya a wani boutique,ya siya mata doguwar riga,dayake akwai gurin sa kaya anan ta saka sannan suka nausa birnin dabo. Duk abinda yadace ayi shi akayi awajan taron bikin nasu jamaa da dama sunje,daga ƙarshe aka musu fatsn,zaman,lafiya taro ya watse. Gidan Ayman na Abuja Aka kawo kayan Amarya Fiddah ba abinda baa sa ba,take gidan ya ƙara haskawa gwanin shaawa. Tunda suka dawo Abuja Ayman yamaida jikin fidah filin wasa amman koda wasa be taɓa kusantarta ba,abun na damunta hakanne yass ta tuntuɓi ƙawarta salmab akan ta bata shawara. Ce mata tayi ta tambayeshi taji dalilinshi in babu daliline se su ɗauki mataki. koda fiddah ta tambayi Ayman cemata yayi bashida lafiya ne yanzu hakama yana neman magani ne. Sosai Fiddah ta amince da abinda ya faɗa mata ,shiyasa ko salmab taƙi faɗa mata sabida gudun tona masa asiri,shiyasa ita kuma salmab ta ɗauka komai yayi normal ne shiyasa fiddah bata faɗa mata ba. Kullum cikin yi.masa addua take akan Allah ya bashi lafiya,dan tausayinshi takeji sosai,sede yayi wasa da ita yasami biyan buƙata bade ya kusanceta ba. wasa wasa abu har ya kai shekara guda,Fiddah haƙurinta ya ƙare dan haka tace ita,de sede suje asibiti,adubashi ita wlh ta gaji. Nuna mata Ayman yayi in yaje Asibiti tonon asirinsane ,amman rayi haƙuri ze fita india adubashi,a haka ya shawo kanta ta bar batun Asibitin. Daga ƙarshe de Ayman daɗin baki yayiwa fiddah akan taje gurin mahaifinshi ta faɗi matsalarshi wataƙila su samo masa magani. Allah sarki Fiddah ba wayo dan haka shiryawa sukayi sukaje kanon dan ita a ganinta ta hakanne kawai zaa samu mafita. Koda ta shaidawa Abbansa matsalar dake tattare da ayman sosai yayi mamakin hakan,amman se yabata haƙuri yace ta shiga gida zeyi magana da mahaifinta. Koda ya sanar da mahaifinta,shima ya girgiza da batun,inda de daga ƙarshe suka tsaida magana ɗaya wato a raba auran inda rabon matarshi ce in yasamu lafiya a maida auran. Kowa ya gamsu da shawarar dan haka kiran Ayman sarki yayi ya umarceshi daya saki fiddah,sabida asamu a nema mishi magani inyaso daga baya a maida auran. hmmm Ayman an iya tuggu, Ay in faɗa muku rushewa yayi da kuka akan shifa yanason matarsa ya zaa raba su,kowa seda ya tausaya masa,da ƙyar aka shawo kanshi ya saketa saki ɗaya. ita ko fiddah batasan bidirin da akeyiba,seda takardar sakinta ta iso gareta,yanke jiki tayi ta faɗi sumammiya,a gigice sukayi kanta,da kyar ta farfaɗo se kuka takeyi abin tausayi,shiko jairin A ranar ya koma Abuja duk azuwan baa kyauta masa ba an rabashi da masoyiyarsa. Tun,a hanya yake dariya ganin ya nunawa iyayanshi shi ɗan zamanine,tunda yace bayaso akamasa dole gashi cikin ruwan sanyi sun,warware da kansu. Koda Ayman ya koma Abuja jinshi yake kamar an,sauke masa nauyi,ko kaɗan bayajin kewar fiddah. Ita ko kullum cikin kuka taƙi cin abinci, a ganinta Ayman na sonta fin ƙarfi aka musu wajan rabasu,gashi in takira wayarshi baya ɗauka,a ƙarshe ma se ya turo mata text massage. "Ke a tunaninki kinada abin faɗamin ne?bayan kinje kin haɗa ƙarya da gaskiya kin faɗa kinsa an rabani dake,dan ba kya sona ay base kinmmin hakaba,dan haka karki sake nemana". Hankalin Fiddah sake tashi yayi na ganin Ayman ita ya ɗorawa laifin mutuwar auransu,kuka take harda majina. shiko dariya yake harda ƙyaƙyatawa. surbajon kuce. [7/14, 10:13] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra muhammad mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *kuyi haƙuri da rashin jina da ba kuyiba jiya nagode* *PAGE 51-55* Tunda Ayman ya rabu da fiddah yakejin hankalinshi a kwance,har wata sabuwar natsuwa ce take shiga sabida ya rabu da ƙaya. Fiddah ta yanke shawarar sanar da salmab abinda ya faru da ita,dan haka kiranta tayi a waya ta faɗa mata.koda salmab taji labarin rasa me zatace mata tayi,rai aɓace ta fara magana. "ke,wacce irin banza ce don Allah,?gaba ɗaya Ayman ya maidake sokuwa,wawiya kuma kin maidun,in bashi da lafiya ne taya zeji shaawar wasa dake kuma har yayi releasing?,meyasa baki faɗamin ba tun farko?". "Wlh salmab,gani nake inna faɗa miki kamar na tonawa mijina asirine shiyasa ban faɗa miki ba"Fiddah ta ƙarasa,zancan cikin kuka. "Ya miki kyau ay, baki faɗa min ba gudun karki tona masa asiri,ay gashinan ke ya tona miki naki Asirin".salmab ta bata amsa cikin fushi. "Don Allah ƙawata kiyi haƙuri nayi kuskure,pls ki nemamin mafita wlh ina ƙaunar Ayman,bazan iya rayuwa babu shi ba ki taimaka min". "Ba komai pricess,zan taimaka miki,next weak zanzo sokoton,ki kwantar da hankalinki,tunda yace bashi da lafiya ne ni zanje,insa amasa abinda ze samu lafiyar a maida Auranku". "Wayyo ƙawata bansan da wanne baki zan gode miki wlh". "karki damu munzama ɗaya,zanmiki kamar yadda zanma kaina se kinjini". Daga haka sukayi sallamah kowa ta ajiye wayar. Ranar Fiddah wuni tayi cikin farinciki wanda har ƴan gidansu seda suka gane hakan,ita ko ba komai yasata farin cikin ba sedan tasan Salmab inde tace zatayi abu to mutum yajira kawai dan babu makawa se tayi ɗin. Salmab ko gurin wata yar me ganye ta nufa,Bayarabiya ce matar,tun kamin Salmab ta mata bayanin abinda yakawota matar ta rigata faɗa mata. Salmab batayi mamaki ba sabida shuumancin Iya Bisi ya wuce hakan. "Yenzu ke yaro da kinzo nan mene kana so nayi?"Iya Bisi ta tambayi Salmab. "So nake kisa masa ƙarfin shaawar dazeji baze iya rayuwa ba inba mace a kusa dashi ta hakane kawai Auran sa da ƙawata ze koma normal"Salmab ta bata amsa. "hhhhhhhh kai yaro wannan kanada wayo fa,so amma de inna misi wannan abu de akwai masalafa,ze koma very stubborn,kana gani nayi ba komai, sabida matanshi zeji wuya a gurin shi".iya bisi ta shaidawa salmab. "ba damuwa kiyi kawai in yaso bayan anmaida auran asan abinda zaayi a rage ƙarfin abun"inji Salmab. Daga haka iya bisi tashifa surkullenta zuwa can sega laya a hannunta,miƙawa Salmab ɗin tayi gamida shaida mata,a tsohuwar rijiya zasu wurga layar. Godiya Salmab tayi mata sosai sannan ta biyata ta amshi layar ta baro gidan. Tun a hanya ta sami tsohuwar rijiyar ta wurga layar sannan ta wuce gida. koda raba Fiddah labarin abinda ya faru sosai Fiddah ta tsorata,seda Salmab ta nuna mata ba komai a ciki sannan hankalinta ya kwanta,ta koma Adduar Allah yasa adace. Ayman kwana biyun nan ya rasa abinda ke damun shi,haka kawai yana zaune se yaji gabanshi ya tashi,ga wata mahaukaciyar buƙata dake taso masa,rasa yadda zeyi yakeyi,lokacin kewar Fiddah ta fara damunshi,amman zuciyarshi na shaida mishi kar ya kuskura ya dawo da ita. Abu yakai abu dan Ayman yanzu har cikinshi ke ciwo in abun ya motsa,yaje asibiti,har ya gaji. Yau yayi dare a gurin Ayki,se wajan sha biyu na dare ya baro gurin aykin,tafe suke shida masu tsaron lafiyarshi,kamar ance ya waiga,acan gefen titi ya hangi mata,wainda suturar jikinsu ita da babu duk ɗaya,take yaji gabanshi ya miƙe,kan yace wani abu har yafara jiƙewa,da sauri yayiwa direba umarni daya tsaya,ba musu suka tsaya yagama kalle matan sannan ya bada umarnin aje azo mishi da ɗaya daga cikin matan. Sosai abun yaba masu tsaron nashi mamaki,sabida sunsan halinshi shi ba manemin mata bane amnan ya suka iya tunda ya buƙata dole su ɗauko masa. Zuwa sukayi suka kira masa mutum ɗaya acikin ƴanmatan,tazo ta shiga motar suka tafi. Koda suka shiga ɗaki shida budurwar rasa me ze mata yayi ita ko tuni tayi fatali da kayan jikinta,sanda idon Ayman ta sauka akan na shanunta besan sanda yajata zuwa kan gado ba,wasa yake da ita na fitar hankali,wanda ita kanta yarinyar ɗauka tayi saduwa da ita yakeyi,se ihun daɗi takeyi shima yana tayata,ahaka hae yasamu yayi releasing batare da ya kusanceta ba. Ay tun daga wannan rana Ayman ya maida hakan aykin shi se ya ɗauko budurwa a gurin tazo yayi wasa da ita iya son ranshi ya sallame ta batare daya kusanceta ba. Awannan halin nashi ne har Allah ya haɗashi da ƴarfillo,a gurin daya saba ɗaukar ƴanmatan. *CIGABAN LABARI* Koda su ƴarfillo suka koma gida wanka tayi tasa ummu ma tayi ita kuma tayiwa jinior suka kwanta. Tundaga wannan rana Ayman ya maida gidan ƴarfillo gurin zuwanshi ko lokacin ayki ne seya baro office yazo gidan. Abun har mamaki yake ba ƴarfillon dan ta ɗauka duk dan ita yake zuwan shiyasa ta ƙudiri aniyar ƙara shigar da kanta gurinshi. Ita ko gimbiya fiddah kullum cikin kallon hanya take na ganin Ayman yazo gareta amman shuru kakeji,Salmab se ƙara kwantar mata da hankali takeyi akan ze zo. Ayman ya gama gane cewa ƴarfillo na sonshi,shiyasa kullum cikin tunanin ta inda ze ɓullo mata da ummu yake,yana tsoron faɗa mata ta cutar mishi da ita. Bayan Shekara uku Ummu Aymana duk wanda ya ganta yasha karya yace bata haɗu ba,ɓangaran diri inta juya baya zaka ɗauka nicki minaj ce kamace kawai ta banbantasu,dan Ummu tafi nicki kyau nesa ba kusa ba dan kwayar idonta blue ce hakanne yabata damar kama da Ashwairiyya Rai,dan wasu acikin ƙawayanta,Ashwairiyya nicki suke kiranta. Ummu miskilace ta sosai da sosai dan miskilancin nata har ƴarfillo be cireba,kowama yimasa takeyi,dayawa mutane sun ɗauka wulaƙancine gareta,in kaga ummu na faraa prince ne yazo gidansu,shima ba sosai take yiba,dan yanzu fushi take dashi,so take ta samu damar tuhumarsa akan ya sanar da ita abinda yasa suke shiga ɗaki shida ƴarfillo su jima. Sabida ummu mace ce me tsananin kishi ko kaɗan batason ganinshi da wata macan,inde ba ita ba,gashi ko so ɗaya basu taɓa samun damar keɓewa su biyu sunyi hirar soyayyarsu ba. Ummu Aymana kenan matashiyar budurwa ƴar kimanin shekaru sha shida. Yau abun na Ayman ya motsa mishi,ba sauƙi sena Allah,ba abinda yafi firgitashi irim yadda zuciyarshi ta azalzaleshi da son ganin Ummu a daidai wannan lokacin,tabbas yana tsoron,wannan lamari,amman bashida zaɓin daya wuce hakan. Waya yaciro ya kira ƴarfillo bayan ya daidaita natsuwarshi. Ƴarfillo ganin yana kiranta jikinta har rawa yakeyi sabida bata gida tana tare da wani Alhaji a guest house ɗinshi,shi take zuwa gurinshi ya biya mata buƙatar ta tunda Ayman ba yimata yake ba. A tsorace ta ɗaga wayar. "yauwa ƴarfillo ki ɗan dafamin tuwon semo da miyar ganye kiba Aymana ta kaimin gida ni ina office". Da har gabanta ya faɗi amman jin yace ummu takaine yasa hankalinta kwanciya.amsa mishi tayi da "to prince yanzu zata kawo maka amman ka ayka driver ya ɗaukota dan kar ta ɓace". Tana katse kiran takira ummu ta bata umarnin ta girka tuwon,yanzu yanzu prince ze ayko a ɗauketa ta kai mishi. Ba dan tasoba ta shiga kitchen ɗin bata jimaba ta kammala,ta zuba a basket sannan taje tayi wanka tayi kwalliya ta shirya acikin wata doguwar riga pink,yayinda ta yafa gyale sky colour,da takalmi shima sky se wayarta ƙirar iphone7 golden colour,gaskiya ta haɗu ga gashinta baƙi da ake hangowa ta cikin gyalan me uban yawa. bata jima da shiryawa ba direban ya iso,dayake jinior yana makaranta dan haka ɗaukar basket ɗin tayi tafice daga gidan,kai tsaye tashiga motar driver yaja ta zuwa gidan prince wanda kecan cikin mawuyacin hali na shaawar data motsa mishi. surbajon kuce. [7/15, 08:40] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud. DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Slm masu yimin magana ta private kuyi haƙuri don Allah ba wulaƙanci bane yawanku ne yasa nake gaza baku amsa duka,masu bina suce inturo musu littafi,kuma kuyi haƙuri inde ba,documents mutum yake so to magana ta gaskiya ko kinyimin magana zayi wuya na turo miki dan nayi nisa gaskiya,ku kuma masoyan book ɗina kuna ina da har zaa nemi littafina baku bada ba har se anbiyoni ana tambayata,da wanne zanji,typing,posting,ko shearing,wlh da mutum yace na turo masa littafin da nayi nisa gwanda nayi typing na page guda,dan haka don Allah kuyi haƙuri,duk me shi in an tambaya don Allah ku bada saboda in antambayeni bana samun damar bayarwa pls,in kuma kunji haushi kuyi haƙuri tuba nake* *page 57-58* Suna isa gidan direban ya ɗauki basket ɗin yayin da ummu tabishi a baya zuwa falon gidan. Koda suka shiga falon masu tsaron lafiyarshi ne kawai aciki suna,mazurai da idanuwa,ɗaya daga cikin su ne yayi wa ummu nuni data shiga daga cikin ɗakin da Prince yake. Ba musu ta amshi basket ɗin ta nufi ɗakin,da sallamarta ta shiga sede bataji an,amsa ba,dayake ɗakin ciki da falone se ta ajiye basket ɗin a falon ta nufi cikin ɗakin. akan gado ta hango shi ya duƙunƙune yana rawar sanyi,da sauri ta nufeshi,cike da fargaba,bata san sanda ta haye kan gadonba,ɗago shi tayi tana tambayarshi. "Qurratu ayni meyake damunka haka?kake zaune a gida baka je asibitiba,pls tell me".tafaɗi lokacin hawaye na zubowa daga idonta. Sam Ayman besan itace ta shigo ba,seda yaji muryarta,sabida tsananin ciwon da cikin shi yake mishi,da kyar ya buɗe idonshi da sukayi ja ya saukesu akanta wacce sabida ruɗewar da tayi tama yarda gyalanta a ƙasa bata saniba. Ci gaba yayi da ƙare mata kallo,yayinda shaawarshi se ƙaruwa take,tambayarshi ummu ta sake yi cikin damuwa. "Hayati,ina cikin matsanancin hali wlh ina da ƙarfin shaawa wacce in ta tashi bana taɓa samun kwanciyar hankali inde ba fitarwa nayiba,ki taimakeni don Allah,nasamu natsuwa a jikinki". Da sauri Ummu ta sakeshi ta suka a gadon,cikin fushi tace. "Ashe ciwon iskanci ne yake damunka shiyasa ka kasa nufar Asibiti to nide bazaka samu abinda kake neman ba wlh". Ayman dunƙulewa yayi ya gaza motsawa,zuwa lokacin yafara fita daga hayyacinshi,da kyar yace mata. "naji to amman don Allah ki taimakeni ki kiramin ƴarfillo tazo yanzu pls",ya ƙarasa zancan da kyar. Wani dun ƙulallan baƙin cikine ya tsayawa ummu a wuya. "me zaka mata inna kiratan?". "abinda nanemi alfarmar kimin kika ƙi,shi zan roƙeta tamin". "Ashe ko zaka mutu inde se na kiratan". Be sake ce mata komaiba sabida ko yayi niyya ma bazai iya ba. Ummu nanan se cika take tana batsewa ita,a ganinta ƙarya Ayman yake mata kawi dan ya biya buƙatarsa da ita. Bata gama tunaninba ya katse a sakamakon hango Ayman da tayi yana mirginowa daga kan gado,jikake tim ya faɗo,kanshi ya bugu da tiles ya fashe. Wata ƙara ummu ta ƙwalla ta nufeshi da sauri,ɗagoshi tayi,ay shi yana jinshi a jikinta beyi wata wata ba ya haɗa bakinshi da nata,kai da ganin yadda yake kissing ɗinta kasan baya cikin hayyacinshi. Ummu tausayinshi ne ya mamaye zuciyarta,take so da ƙaunarshi suka sake motsa mata,yayinda shaiɗan ke ƙara ƙawata mata hakan,a matsayin taimako ne zatayi. Sakar mishi jiki tayi yaci gaba da sarrafata sannu a hankali har hannunshi ya sauka akan zip ɗin rigarta,ya zuge shi take rigar tayi ƙasa dede kwankwasonta,bayyanar na shanunta cikin brezia seda numfashin Ayman ya kusa ɗaukewa,da sauri ya miƙa hannunshi gurin,ya shiga wasa dasu cikin salon,da ya rikita ummu wanda dan daɗi har ƙara matso mishi dasu take yi shi kum yana murzasu,sannu a hankali hannunshi ya sauka kan maɓallin bra ɗin itama ya cireta,yana cirewa ya kafa bakinshi akan na shanun yafara tsotsa,wayyo ummu ay jinta take kamar baa duniya takeba,Prince yasan takan mata,haka ya dunga bi da ita salo salo,amman har yanzu hannunshi bekai ƙasan ta ba iya karshi kan na shanunta wanda suka ƙara kumburowa sukayi ja sabida hannu da bakin da suka ji,ci gaba yayi da murzasu,ummu idonta a rufe yake tana enjoying abinda yake mata gaba ɗaya ta gama jiƙewa,sabida hakan. Wata runguma Prince yayi mata yana gurnani kamar tsohon zaki,abin har tsoro ya bata,zuwa can kuma se taji jikinshi ya saki,ta fahimci hakanne ta hanyar nauyin da taji ya ƙara akanta. Da ƙyar ta iya tureshi,idonshi a rufe yake,da sauri,ta maida bra ɗinta taja rigarta sama ta zuge da kyar,sauka tayi a gadon d sauri ta fice daga ɗakin,ko takan direba bata bib tafice bakin titi,ta tsaya jiran mota se ganin direban tayi ya biyota yace ta shiga ya maida ita gida ba musu ta shiga sabida se a lokacin ta lura rigarta duk ta yamutse sannan ga jinin prince daya ɓata rigar. Koda suka iso gida ƴarfillo bata dawoba dan haka da sauri ummu ta shige cikin gidan tana shiga toilet ta faɗa tayi wanka ta wanke kayan ta shanya,taje ta shirya sannan ta dawo falo da niyar kiran ƴarfillo se alokacin ta tuno da wayarta dake ajiye akan gadon Ayman. Muje zuwa. Surbajon kuce. [7/17, 20:39] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra muhammad mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 59-60* Safa da marwa ummu ta shiga yi a falon tunaninta ta yarda wayarta zata dawo hannunta dan tasan ko giyar wake tasha bazata iya komawa gidan prince ba kuma da sunan ɗaukowa ba. A nashi ɓangaran prince tunda ya samu yayi releasing wani sanyin daɗi ne ke ratsa shi jin shi yake beda wata damuwa a rayuwarshi,kunyace ta kamashi lokacin daya tuno da wacce ya samu biyan buƙatar,sosai yayi danasanin aykata hakan ba kaɗanba. Miƙewa yayi ya shiga wanka ya jima yana wankan sannan ya ɗauro alwala yazo yayi Sallah rakaa biyu yakai kukanshi gurin Allah akan wannan ƙarfin shaawa da take damunsa Allah ya yaye masa idan lalurace,sabida ya fahimci gab take da kaishi aykata aykin danasani. Yana idar da sallah kan gadonshi ya koma ga mamakinsa wayar Aymana ya gani tana ringing,amman kasancewar a silent take shiyasa beji ƙarar ba. *sweet mum* shine sunan dayaga ya bayyana akan screen ɗin,wayar wanda ko baa faɗa masa ba yasan ƴarfillo ce,da kamar baze ɗaga ba se kuma ya ɗauka,tun kan yayi magana ta rigashi. "Ummu wanne irin wulaƙanci ne haka ina kiranki ba zaki ɗauka ba,me kikeyi daya ɗau hankalinki haka?to maza kije ki kunnamin heater ɗakina ki tambatar ruwan ya tafasa kamin ki kashe,sabida nan inda na kwana babu ruwan zafin tafasasshe, gani nan dawowa nima,". bata jira jin amsar ummun ba ta kashe wayar. Shiko prince tsananin mamakine yasa ya kasa cire wayar a kunnenshi,najin cewa ƴarfillo baa gida ta kwana ba,hakan na nufin taje gurin wani ƙato kenan. Be jira komaiba ya fice riƙe da wayar ummun a hannun shi key ya amsa yaja motar da kanshi,zuwa gidan su ƴarfillon duk da yana kunyar haɗuwa da ummu amman ya zama dole yaje domin inganta tarbiyyar ummu da ƙaninta. Koda ya isa layin kamin ta ƙarasa gidan yasami wani lungu yayi parking,dayake magriba tafara yi,shiyasa ya fito hankalinshi kwance ya nufi cikin gidan,megadin su yaje masallaci dan haka har ya shiga ba wanda ya ganshi. lokacin daya tura ƙofar falon ya shiga,ummu ce zaune tana koyawa jinior,home work,sam bataji motsin shigowar shiba,se sallamarsa taji. irin dungurawar da tayi gurin gudu daga falon koni seda abin yabani dariya,da mahaukacin gudu tabar gurin ta ruga ɗakinta ta kulle. murmushi prince yayi sabida dama yasan zaayi haka,dan ummu macece me kunya,bare kuma yanzu da wani abu na kunyar ya shiga tsakaninsu. Guri ya samu ya zauna yayinda jinior yazo jikinshi yana murnar ganinshi,shi ya ƙarasawa jinior homework ɗin,sannan yayi alwala a toilet ɗin,falon ya yi sallah,tv ya kunna bayan ya idar da sallah,shi da jinior suka zauna suna kallo. ita ko ummu tunda ta shige ɗaki ƙirjinta ke bugawa da ƙarfi,tabbas da tasn ze zo gidan baabinda ze kaita zama a falon har yazo ya sameta,kunyarshi sosai takeji gami da kunyar Allah,dan tayi danasanin abinda ya shiga tsakaninsu ɗazu har kuka tayi akan Allah ya yafe mata. Ƴarfillo se dare ta dawo,misalin ƙarfe tara na dare,sanye cikin shigar da base prince yasha wahalar tambayarta daga inda takeba. cikin sanɗa ta shigo falon dan ita,azatonta suna ɗaki jinior da ummu,abinda ta ganine shi yasa ta zubar da jakar hannunta ba shiri,prince ne tsaye yana mata kallo irin,na tsana me tsanani. Itako jikinta kamar mazari inbanda rawa ba abinda yakeyi,zubewa tayi a gurin zata fara magana,amman se taga yabi hanyar ɗkinta,hakanne yasa ta gane,yana buƙatar sirri wato beson su ummu suji. Kamar wacce kwai ya fashewa a ciki haka tabi bayanshi,zuwa cikin ɗakin nata. Tana shiga ya ɗauketa da mari,sannan ya fara magana cikin matsanancin fushi. "Bana buƙatar jin komai daga gareki,ƴar akuya,dama ashe abinda kike aykatawa kenan,to Allah ya tona miki asiri wlh baki isaba,duk kyautatawar da nake miki ashe a banza kenan?". "Dakata malam,in ka manta bari in tuna maka,karuwa ce ni,wacce ka sani,a sadu dani a biyani shine sanaa ta,babu ta yadda zaayi ka ajiyeni batare da kana biyamin buƙata ta ta wannan fannin kace in zauna bazanje in samu me biyamin ba,in so kake naci gaba da zama ka aureni ne se kaji daɗin kafamin dokokin,amman yanzu wlh kaji na rantse dole ne na fita abiyamin buƙata,sabida ƙaton gida da milyoyin kuɗi a account ba su kaɗai bane buƙatata ba,ina buƙatar savice kullum dan baze yiwu in zauna inata over flog a banza ba". Sosai ƴarfillo ta bashi mamaki,cikin fushi yace mata. "hakan da kika ce dede ne,dan dama tsohuwar kilaki dole se ana service kullum gudun karta dunga over flog ɗin kamar yadda kikace,to ki sani wlh ko giyar wake nasha bazan iya aurankiba,inna aureki ince na auri wa,tun wuri in mafarki kike gwanda ki farka,kuma baki isa ki ɓata tarbiyyar su ummu ba wlh". "Daɗinta de tare dasu ka ganni ba kaine ka kawomun su ba,kuma over flog ay ba iya tsohuwar kilaki ce take yiba,tsohon kilaki ma yanayi,kuma ..." Marin da Ayman ya kifa matane yasata yin shuru ba shiri,duka ya rufeta dashi,tamkar soja ya kama ɗan boko haram,ihu take iya ƙarfinta,wanda ya jawo hankalin ummu dake rufe a ɗaki,a gigice ta buɗe ƙofar ta nufi ɗakin ƴarfillon. Koda ta shiga ɗskin ba ƙaramin mamaki bane ya kamata ba,tsayawa tayi takasa ƙarasawa,cikin,shi kuma Ayman be gantaba ya shiga surfawa ƴarfillo zagi. "in kina karuwancinki kisan wanda zaki dunga yiwa,dan ubanki dan ina wasa da jikin ki shine har zaki buɗe baki ki kirani tsohon kilaki,?to wlh yau sena nuna miki ni cikakken ɗan barikine me lasisi". Cigaba yayi da dukanta,ummu wacce ta gama gasgata abinda kunnenta ya jiyo ta hanyar lura ds irin suturar dake jikin ƴarfillo,wata ƙara ta saki sannan ta xube ƙasa sumammiya. Da mahaukacin gudu Ayman yayi kanta,kiran sunanta yake amman ina ko numfashi batayi,a ruɗe ya kinkimeta yafice daga ɗakin,wanda hakan yayi daidai da fitowar jinior yana kuka koda yaga Ayman ya fice ds ummu binsu yayi a baya yana kukan,. Ayman na zuwa gurin motarshi ya saka ummu aciki ze juya ya shigane yaga jinior,da sauri ya ɗaukeshi ya saka acikin motar yaja da mahaukacin gudu,zuwa Asibiti. Surbajon kuce. [7/18, 10:09] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATIONS *Page 61-62* Suna isa Asibitin likitoci suka rufu akanta,wanda da taimakon Allah bata jimaba ta farfaɗo se kuka takeyi,prince kasa rarrashinta yayi. Koda aka sallamesu ƙin binshi tayi seda ya zare mata ido sannan ta yarda ta shiga motar,jansu yayi zuwa gidanshi nanma dakyar ta shiga cikin gidan kuka kawai takeyi. Suna shiga cikin falon yajawota ya rungumeta,yana bubbuga bayanta alamar rarrashi,itako kamar me jira ta shiga kuka sosai,cikin kukan ta fara magana. "Dama mummy karuwace ashe?kaikuma farkanta,wannan wacce irin masiface kuka jefa kanku aciki?wlh da nasan haka kuke bazan zauna ku ci damu da haram ba,in sonta kake meyasa baka aureta ba?". Kukane ya sarƙeta ta kasa ci gaba da maganar,shi ko Ayman runtse ido yayi kawai yana sauraronta,ya rasa da wacce kalma ze rarrasheta,ƙwace jikinta tayi ajikinshi taja hannun jinior zasu fice daga gidan. da hanzari yasha gabanta,ya fara magana. "Hayati zaki iya yimin kowanne irin hukunci in ɗauka amman bazan taɓa bari ki gujeni ba shine hukuncin da bazan yarda dashi ba wlh kinji na rantse". yana gama maganar yakira securities ɗin gidan ya basu umarni kamar haka. "Duk ranar da kuka bari wannan ta fita acikin gidannan a bakacin ranku,wlh sena harbeku dukanku". bejira amsarsuba yaja hannun jinior suka shige ɗaki suka barta tsaye tana kuka. Suko securities ɗin tsorone ya kamasu sosai,sabida ogansu be taɓa kafa musu doka me tsanani irin hakaba,kuma sun sanshi sarai,duk abinda yace zeyi ba makawa se yayin. Har dare ummu nanan a falon taƙi shiga ciki se kuka takeyi abinci ma anbata taƙi ci,prince yayi rarrashin har ya gaji,daga ƙarshe fitowa yayi ya sureta gaba ɗayanta ya shige da ita ɗakin,lokacin jinior yayi bacci. ƙoƙarin kwacewa takeyi amman ta kasa har seda ya shigar da ita,abinci ne ajiye a ƙasa zama yayi sannan itama ya zaunar da ita yafara ɗura mata abincin,in taƙi buɗe baki ya toshe mata hanci,a haka har taci ta ƙoshi,gaba ɗaya ya ɓata mata kaya. Umarni ya mata da taje tayi wanka,amman taƙi jawota yayi yafara ƙoƙarin cire mata kayan,da gudu ta shige toilet ɗin dariya hakan ya bashi miƙewa yayi ya gyara gurin ya fice a gidan ya nufi gidan ƴarfillo. koda ya shiga gidan a zaune ya sameta tana gasa bakinta daya kumbura a sakamakon dukanta dayayi ɗazu. Tana ganinshi miƙewa tayi da sauri,tana neman gurin ɓuya,dan ta ɗauka dukanta ze sake yi. Dariya yayi sannan yace, "kishiga ki haɗomin duk wani abu da kikasan na ummu ne da jinior yanzu ki kawomun". "ban gane ba ina kakai min yara?". "Namaida ruƙon su hannuna sabida baki da isasshiyar tarbiyyar da zaki basu,yanzu ummu ta fahimci ke karuwace,taya kike tsammanin zan cigaba da barin tarbiyar uwar ƴaƴana a hannunki,ayna kashe kaina inde na bar hakan ta faru". "What!!!!!" Ƴarfillo ta tambaya jikinta na ɓari. "Nufinka ummu ce uwar ƴaƴanka?". "ƙwarai kuwa itace uwar ƴaƴana wacce zan aura insha Allahu,". "kutumar ubancan kayyasa,ashe ko zaayi bura uba kenan,wlh baka isa ka auri ummu ba nice nafi cancanta daka aura,dan haka wlh ko zanyi yawo tsirara se naga bayan duk wata mace dake ƙoƙarin rabani dakai,kasha ƙarya wlh". Har kumfa ke fitowa a bakinta dan masifa, Dariya furucinnata ya bashi,dan haka shigewa yayi ɗakin su ummun ya jido komai daya gani,yakai mota,sannan yadawo gurin ƴarfillon yace. "Ƙe baki isa ki sani ko ki hanani ba,dan haka zan auri ummu koda dagani se itane muke son auran a duniya,kuma ki xuba ido ki gani". "Hakan ze farune in na mutu,amman wlh ka rubuta ka ajiye,ni ƴarfillo sena rabaka da duk wata mace da ka nuna kanaso,shege ka fasa tsakanina dakai,shiyasa akace in kaga mutum arana inda hali ka ƙara tunkuɗashi ciki dan da zaran ka kawoshi inuwa tofa kai ze wurga Ranar,daga kai har ummu baku san wacece ƴar fillo ba labarina kukeji,da sannu,zan baku mamaki". bata jira amsarshi ba tashige ɗakinta kamar kububuwa,shi ko dariya yake har yafice a gidan dan tabbas abun abin dariyane. Surbajon kuce. [7/21, 08:25] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *slm masu karatu,zuciyata ce(ɗana yusuf) babu lafiya shiyasa kuka jini shuru,pls a sata a addu'a* *Hafsat Ɗaheer,Esha Mustapha,duk da kundena sona yanzu,ni ina sonku wannan shafin nakune domin nuna soyayyata a gareku,nagode* *page 63-64* Kai tsaye gidanshi ya koma koda ya isa gidan tuni ummu tayi bacci,ajiye kayan yayi yabar ɗakin ya tafi nashi ɗakin. Tundaga wannan lokacin kulawar ummu da jinior ta koma hannunshi,makaranta in zaa kai su akwai kyakkyawan tsaro musamman ummu,ko class ta shiga gefen window da ƙofa duk sojojine,hakan be mata daɗi Amman bata da yadda zatayi. Anata ɓangaran ƴarfillo ko kwana tayi tana kuka,gami da tunanin mafita,daga ƙarshe de ta samu mafitar,dan kwana biyu da zuwan Ayman,jirgi ya ɗaga da ita zuwa ƙasar china. Yau tunda asuba marar ummu ke mata ciwo,wanda dama duk lokacin da zatayi period haka takeyi,se murƙususu takeyi a ɗakin ta rasa inda zata sa kanta gashi duk ta ɓata jikinta kasancewar bata da always,ga jinin rushing yakeyi. kuka takeyi sosai,dan azabar da takeji,jinior ne ya fice da gudu yaje ya faɗowa Ayman.tare suka dawo ɗakin,hankalinshi sosai ya tashi rasa yadda zeyi yayi. Waya ya ciro ya kira office ɗinsu inda ya bada umarnin a turo mushi soja guda ɗaya ta mace,ayko ba jimawa aka turo masa tana isowa,ta ƙame ta sara masa,amsawa yayi sannan ya mata jagora zuwa ɗakin da ummu take ya nuna mata ita,sannan ya ƙara da cewa. "Bansan ya zan kula da ita bane shi yasa nasa a turo ki,so pls help me". Murmushi sojar tayi,sannan tace. "don't worry oga i will handle this problem insha Allahu,abinda nakeso kawai ka ayka asiyo mana always". Amsawa yayi da to,ita kuma ta shige ɗakin,ɗaukar ummu tayi kamar jaririya ta shige da ita toilet,shiko Ayman kunya yakeji ya ayki wani siyo always ɗin dan haka da kanshi yaje ya siyo ya dawo,carton guda ya siyo mata na always ɗin. Koda suka shiga toilet,wanka sojar nan,me suna tamilola tayiwa ummu,sannan ta gasa mata marar da ruwa me zafi sosai wanda dan daɗi ummu har bacci tayi a toilet ɗin,sosai ta samu sauƙin ciwon. Suna fitowa hakn yayi daidai da shigowar Ayman ɗauke da carton ɗin always😆,ummu da sauri ta ɓoye a bayan tamilola,itako dariya takewa Ayman,sannan tace. "Oga wannan always amman harda na haihuwa ko kasiyo?". Murmushi yayi kawai ya ajiye ya fice,be jimaba ya dawo ɗauke da mopper,ya goge inda ummu ta ɓata da jinin,ba ummu ba har tamilola seda tayi mamaki,shiko ko ajikinshi ya fice daga ɗakin . Shiryawa ummu tayi tana ta yiwa tamilola godiya musamman da ta fahimci musulma ce ita bayarabiya,sallama ta musu ta tafi,bayan Taba Ayman shawara akan ya kai ummu Asibiti. Bayan tafiyarta,shiryawa yayi yasa aka kai jinior makaranta shikuma ya shiga ɗakin ummu,inda ya sameta a kwance,koda ya shiga ƙin tashi tayi,zama yayi a gefeɓ gadon sannan yace. "Hayati ya jiki?ki taso muje asibiti a dubaki a baki magani kinji". "Ni ba inda zani,ka barni kawai naji sauƙi".ta bashi amsa cikin muryar mara lafiya. Murmushi yayi ya miƙe yaje ya ɗauko mata takalmi da hijab,sannan ya dawo gurin gadon,hannu ya miƙa mata alamar ta kama,harara ta wurga masa sannan ta gyara kwanciyarta,almar babu inda zata. "ko ki taso mu tafi kokuma wlh,na ɗaukeki". Ɗan ƙaramin bakinta ta turo gaba tana ƙunƙuni. "Au Hayati dan nace kizo muje asibiti shine kike zagina?"cewar Ayman. ido ummu ta fiddo waje sannan tace. "Nifa ban zage kaba,kai qurratu aynin nan kacika fitina wlh,da takurawa mutane"ta ƙarasa maganar cikin shagwaɓa. Murmushi yayi kawai ya miƙa mata hannun ba musu ta miƙa masa nata ya tada ita tsaye,hijab ɗin ta amsa tana juyawa a hannunta,sannan tace. "Nifa in zan fita bana saka hijabi sallah kawai nake dashi". "Cabɗi jan nufinki haka zan barki ki yafa gyale ki fita ko ina na jikinki yana juyawa ƙartin banza suna kallemin ke?to wlh bazan iyaba danma kiji". Baki ta turo gaba sannan ta saka hijab ɗin tasa takalmi suka wuce Asibitin. Bayanin da likita yayiwa Ayman sosai yaba ummu kunya,dan ji tayi kamar ƙasa ta tsage ta shige ciki.muryar Ayman ce ta ƙara mata wata kunyar. "So doctor yanzu dole se in tayi aure mijinta ya sadu da itane zata dena wannan ciwon marar?". "Haka nake nufi,amman wasu ko sunyi auran be denawa,sakamakon ciwon infection dasuke ɗauke dashi"cewar likita. Sosai Ayman ya masa godiya ya amshi magungunan da aka bata suka fice,kai tsaye office yace driver ya wuce dasu. koda suka isa office ɗin,kan kujerar dake office ɗin taje tayi kwanciyarta,shi kuma ya kama aykinshi basu baro office ɗinba se biyar na yamma,suka isa gida. Da daddare Ayman ya kirata falo dakyar tazo,kuɗi ya bata masu yawa akan ko zata buƙaci wani abu sabida gobe da safe zeyi tafiya zeje kano. Ummu jiki a sanyaƴe ta amshi kuɗin,gamida yimasa adduar zuwa lfy da dawowa lfy,ta miƙe ta shige ɗakinta,shima nashi ya wuce,bakomai ze kaishi kano ba se neman yardar iyayenshi akan a ɗaura musu Aure shida ummu. Asubar fari,ya ɗaga zuwa kano wanda tunda ya rabu da fiidah rabonshi da ita. Sosai danginshi sukayi murna da zuwanshi,ba ma kamar mahaifinshi,kowa se farinciki yakeyi. Bayan komai ya lafane,ya shige ɓangaranshi,yayi wanka ya shirya,wayarshi tayi ƙara,koda ya duba abokin shine ismail,ɗauka yayi ya koma kan kujera ya zauna,yafara magana. "mutumina gani a kano fa" Dagacan ɓangaran ismail yace. "amman wlh naji daɗin hakan sabida nima jiya na shigo garin,amman yanzu ganinan zuwa gurinka". Kashe wayar sukayi,inda baa jimaba ismail yazo. Hira sukeyi sosai,inda ismail yafara jajantawa Ayman game da lalurar da ta sameshi,wacce ta jawo har aka rabashi da matarshi. Wata shewa Ayman yayi wacce tayi daidai da ƙarasowar mai martaba,sarki ƙofar ɗakin,zuwa yayi dakanshi dan ya tambayi Ayman cigaban daya samu game da lafiyarshi. Abinda yaji Ayman na faɗi ne yasashi tsayawa shida fadawansa a ƙofar ɗakin. Acikin ɗakin ko Ayman ne yace. "Kai wlh lafiyata ƙalau,ba abinda yake damuna kawai na musu takune irinnamu na yaran zamani,tun farko nacemusu bana son Auran amman suka ƙi yarda suka auramin abinda bana so,niko shiyasa namata wayo nasa tazo ta faɗawa sarki wanda nasan ba makawa sarki cewa zeyi a raba auran kuma ilai hakan akayi ,yanzu ma zuwa nayi akan auran danakeso nayi da wacce nakeso"ya ƙarasa zancan cikin dariya. Dariyarce ta maƙale sanda yayi arba da fuskar me martaba sarki ɗauke da matsanancin fushi😡jikin Ayman rawa ya farayi sabida ko baa faɗa masa ba yasan sarki yagama jin komai. "Banyi mamaki ba Ayman dan tantiri kamar ka ya aykata abinda ka aykata,yana ɗaya daga cikin ayyukanku maida iyayanku yara,to bari kaji in faɗa maka,wlh tlh blh,inde nine mahaifinka baka da matar aure a duniya se fiddah,ko bayan raina ka auri wata mace bayan ita Allah ya isa ban yafe makaba duniya da lahira"yana gama faɗin haka ya juya ze fita. A gigice Ayman ya kamo ƙafar mahaifinnasa yana kuka,yafara magana. "Abba kayimin rai inba ummu bazan iya rayuwa ba hasalima sonta ne yasa nakasa bin abinda kakeso,wlh in kace bazan auretaba mutuwa zanyi". hankaɗeshi sarki yayi,sannan yace. "Ayman!!!koda se ka aureta ne zaka shiga Aljannah ƙarshe kenan to wlh bazaka Aureta ba,inkuma ka tsallake maganata Allah ya haɗaka,da masifar da tafi ƙarfinka"be jira amsarsaba yafice daga ɗakin. Wanda hakanne ya haddasawa Ayman yanke jiki ya faɗi ƙasa sumamme,sarki ko waigowa beyiba ya fice,ismail ne ya nufi Ayman A gigice,ganin baya numfashine yasa ya leƙa waje yakira securities ɗin Ayman ɗin suka ɗaukeshi zuwa Asibiti. surbajon kuce. [7/22, 08:36] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Har yanzu you are the best to me nothing can change your position in my heart,stay nice maman Giɗaɗo* *page 65-66* Emergency aka shiga da Ayman,likitoci suka duƙufa gurin ceto rayuwarshi. Shiko me martaba daya shiga cikin gidan matanshi ya kira ya shaids musu abinda Ayman ɗin ya masa,da kuma irin hukuncin daya yanke masa. Mahaifiyar Ayman ta goyi bayan hakan ɗari bisa ɗari,Hajiya babbace de taja da hukuncin inda tace. "Haba ranka ya daɗe!taya zaka kafawa ɗanka irin wannan mummunar dokar?yau in ta Allah ta riskeka kuma fiddah ɗin da kakeso ya Aura ba macan arziki bace,ya kake so yayi?ko ko so kake ya dauwama cikin baƙin ciki?". "Duk abinda zesa Ayman baƙin ciki,zanyi iya bakin ƙoƙarina wajan ganin nasashi a cikin sa,ni akace na bishi ko shi akace ya bini?da har zan kafa masa doka ya karya,sabida ya raina hankali da girmana,wlh kinji na rantse inde ina numfashi,Ayman ya gama Auran wata mace a duniya bayan fiddah,sabida shima yaji irin baƙin cikin da na ji,in kuma ya ƙetare dokata,wlh na sallamawa duniya shi har abada". Yana kaiwa nan yace musu. "Kuje na sallameku,kuma duk wacce ta sake ta bishi Asibiti,a bakin Auran ta". Jiki a sanyaye suka fice a ɗakin,ita kanta yanzu mahaifiyar Ayman se yanzu ta gane illar dake tattare da furucin na sarki,amman basu da zaɓin daya wuce suyiwa abin addua Allah ya sanyaya zuciyar shi. Acan Asibiti kuwa,Binciken likitoci ya nuna Ayman ya kamu da ciwon zuciya,dan haka suka ɗorashi akan magani. Tsawon wata biyu ya kwashe a Asibitin sannan ya sami sauƙi,kuma tsawon wannan lokacin ba wanda yazo dubashi acikin ƴan gidansu,ismail ne ds body guard ɗinshi suke jinyar shi,dan haka ya takura akan a sallameshi koda aka sallameshi daga Asibitin ko ta gidansu be biba ya ɗauki hanyar Abuja,dan kullum da tunanin ummu yake kwana yake tashi,bashi da burin daya wuce yasa ta a idanunshi. A nata ɓangaran ummu tunda Ayman yayi tafiya ta rasa natsuwarta,kewa da tunaninshi duk sun addabeta,ga gabanta dayake yawan bugawa wanda yasa ta shiga cikin tunani inda take ganin duk inda Ayman yake bashi cikin kwanciyar hankali. Kullum cikin yi masa addua take ta rasa da wanne zataji,in ta gaji tayi kuka jinior ya tayata,kullum haka suke. Yau ko tunda ta tashi gabanta ke faɗuwa,ta rasa dalili,dan haka seta duƙufa addua akan Allah yasa alkhairine. Da misalin ƙarfe tara na dare Ayman ya iso garin Abuja,direct gidanshi aka wuce dashi,bayan sun sauke ismail a nashi gidan. Koda suka iso gidan,shi kaɗai ya shiga cikin falon gidan,a daidai wannan lokacin ummu na zaune,a falon tana aykin tunaninshi,shiko jinior tuni,ya jima dayin bacci a ɗakin. Sanye take cikin rigar baccinta,maroon colour,da kaɗan ta wuce mazaunanta,tasa rigar ne kasancewar taga su kaɗaine a gidan. .Ayman da sallamarsa ya shiga falon,Ummu a gigice ta ɗago kanta dan ganin shi ɗinne da gaske ko gizon daya saba matane,ganin shi a tsaye yana mata murmushi ne ya sata kwalla ihun murna sannan ta rugo da gudu ta rungumeshi,sam ta mance kalar shigar dake jikinta,shiko Ayman tunda ta taso da gudun yaga yadda rigar tayi a jikinta,ƙwaƙwalwa da numfashin shi ne suka tashi Ayki na wasu ƴan mintina,sanda ta rungumeshi na shanunta suka haɗu da ƙirjinshi kusan faɗuwa yayi,dan faruwar hakanne ya jefashi cikin wani yanayi wanda be taɓa samun kanshi a ciki ba. Itako ummu dan murna har da ɗan dukan bayansa take sosai tayi murna da dawowarsa,shiko ɗagata yayi yana jujjuyawa da ita a falon a haka har suka ƙarasa ɗakinshi. Kai Abu tun,ana na murnar ganin juna har yazo ya sauya darasi,bakin Ayman na hango acikin na ummu yana kissing ɗinta,yadda yake kissing ɗin da gani kasan baya cikin hayyacinshi. cak ya ɗagata ya ɗora a kan gado,yaci gaba da sarrafata,ummu irin matannanne masu ƙarfin shaawa da zaran namiji ta taɓesu,basa iya controling kansu,bare kuma yanzu da abin ya haɗu da sharrin so,ga shaiɗan acan gefe yana buga musu ganga. Ayman fa besan a wacce duniyar yake ba,tuni ya jima da fatali da duk wata sutura dake jikinsu,ci gaba yayi da sarrafata ta yadda yake so,sanda bakinshi ya sauka akan.....yafara sucking,ummu numfashinta har ɗaukewa yakeyi,take ta fara ambaliya,ganin hakane yasanya Ayman cilla kwallonsa a raga😳. Se a wannan lokacin tunanin ummu ya dawo gareta,wanda shi kuma Ayman ya rasa nasa a daidai lokacin,kuka take na neman ya kyaleta amman ina bemasan tanayi ba,hasalima yadda take kukan shima kukan yakeyi. be saurara mata ba,seda ya sami biyan buƙatarshi,se alokacin ya fahimci abinda ya aykata,a firgice ya ɗagata ya diro a gadon,dan gani yake kamar mafarkin daya saba yine,sanda ya tabbatar ba mafarki yake ba,rushewa yayi da kuka matsananci yana buga kansa da bango faɗi yake. "Na shiga uku,Abba ka cuceni,meyasa Abba kamin haka,me na maka,dan kawai nace banason zaɓinka,gashi ka janyo nayi abinda har na mutu bazan dena nadamar aykata shiba,why Abba,yau ina zan saka rayuwata",cigaba yayi da buga kansa a bangon,har seda ya fashe jini ya wanke masa fuska amman be denaba. Ummu dake kwance tana kuka na baƙin ciki wai yau itace aka maida ita cikakkiyar mace ba ta hanyar aure ba,se yanzu danasanin zama a gida ɗaya da Ayman ya kamata,tabbas sunyi kuskure,a matsayinsu na masoya hakan ba daidai bane sabida so abokin shaiɗanne,dan gashi yau yakaisu ya baro su. Ganin Ayman na ƙoƙarin kashe kanshi ne yasa ummu ta miƙe da kyar ta maida rigarta ta nufeshi,dafashi tayi itama tana kuka,waigowa yayi dan ganin waye ganin itace da sauri ya rungumeta yana kuka yana faɗin. "Ki gafartamin Hayati,na cutar dake nasani,amman don Allah ki yafemini zan iya kashe kaina in baki yafeminba"kukane yaci ƙarfinsa,wanda itama kukan takeyi,da kyar tace. "Qurratu Ayni,bani kayiwa laifiba,hasalima ni da kai duk masu laifine,Allah mukayiwa laifi,dan haka gurinshi zamuje neman tuba,in kuma akwai wani laifi da kamin na yafe maka duniya da lahira"kwace jikinta tayi a nashi tana kuka ta fice a ɗakin ta nufi nata,jikinta ta tsarkake sannan ta dawo ts kwanta akusa da jinior ta rungumeshi tana kuka me tsuma zuciya. So da ƙauna,da son ganin mahaifiyarta,na ƙara bijirowa zuciyarta kamar kullum. Surbajon kuce [7/22, 14:15] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Hhhh na samu saƙonni na yabawa dana zagi,to duk na gode,ummu Aymana de ni nake rubutawa,duk wacce taga yadda nake jan littafin beyi mata ba to yakamata ta fara rubuta nata a yadda takeson yakasance,wannan nawa ne,kuma banason a bini pc ace zaa min gyara kowa ta riƙe gyaranta in yaso innayi posting se ta gyara a zuciyarta,tunda Allah ma be iyawa ɗan adam ba ni wacece da zan iya muku,wanda kuke ƙaramin kwarin guiwa na gode sosai* *page 67-68* Ranar kwana sukayi kowa zuciyarshi ba daɗi babu kamar Ayman wanda cikin dare zazzaɓi ya rufe shi yayi kuka har hawaye ya ƙafe a idonshi,yayi nadama taƙin ƙarawa,tsoron Allah da abinda ya aykata su suka kamashi. Ummu Aymana ko gani take ƙarshen jin daɗinta ne yazo,shiyasa hakan ta faru da ita,koma menene tasan hakan yana daga cikin ƙaddararta,inda Allah be ƙaddaro mata ba baze sameta ba. Yanzu ba abinda takeso da buri irin taga mahaifiyarta,shine kawai burinta,dan bata ji zata iya ci gaba da zama tare da Ayman. Washe gari tinda asuba Ayman ya samu waya daga office ɗinsu akan ya shirya,takarda ta fito da sunanshi acikin wainda aka tura course ƙasar jamani,na tsawon shekara guda. Sam Ayman beso hakaba dan yanaso ya zauna ya ba ummu kulawa dan yanaso tayarda ba kowane dan yasan mace a waje yake gudunta ba musamman su da ƙaddara ta faɗa musu. Koda gari yayi haske kowa cikinsu na kunyar haɗuwa da ɗan uwansa,haka Ayman ya shirya ya fice gurin Ayki,inda aka bashi takardar shi ta tafiyar nan da kwanaki uku masu zuwa. wuni yayi a gurin Ayki inda daga ƙarshe de ya daure yakira hajiya Babbah ya sanar da ita tafiyar da ze yi ƙasar jamany,fatan Alkhairi taimasa,sukayi sallama. Tana kashe wayar taje ta shaidawa me martaba,shiko beyi ƙasa a guiwaba yakira amininsa akan gobe yanaso a maida Auran,dama sun daɗe da zancan maida auransa da fiddah. Haka akayi washe gari aka maidar da auranshi da fiddah batare da saninsa ba,akaro na biyu,se kiranshi Sarki yayi ya bashi umarni akan kar ya sake ya tafi batare daya tafi da fiddah ba . Ayman be damuba dan yanzu ya gama yarda mahaifinshi yafi kowa ƙinshi a duniya,hasalims godiya yamasa. Fiddah ko tayi rawa tayi juyi na murna anmaida auran ta,salmab ko baa magana sosai ta tayata murna gamida shawarwari. Ayman visa tare da fiddah ya nema,kuma yasamu,dakyar ummu ta tarda tazo sukayi sallama inda ya miƙa mata ATM card ɗinshi ya kuma faɗa mata pin ɗin Gami da mata alƙawarin komai wiya komai rintsi ze dawo gareta ya aureta,ta riƙe mushi kanta amana,kuma ta rufe sirrinsi,. Haka suka rabu suna kuka,sosai ummu taji ɗacin tafiyarshi bataso yafara tafiya ba ita taso tafara gudunshi,amman tsarin Allah shine daidai,fatan alkhairi ta masa sukayi. .washe gari da safe Ayman ya wuce airport yana isa fiddah ma ankawota jirgi is ready shiga kawai sukayi suka ɗaga ƙasar jamany. Safe trip Ayman. Surbajon kuce. [7/22, 16:27] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 69-70* Ummu Aymana bayan tafiyar shi ji tayi duniyar ta mata girma tanaso ta fita neman mahaifiyarta amman batasan ta inda zata fara ba gashi tana tsoron zuwa garinsu dan batasan me zasuyi mata ba. Haka ta haƙura taci gaba da addu'a,akan Allah ya bayyana mata ita aduk inda take cikin sauƙi. Ayman tunda suka isa jamany a wani gari me suna Balyn,ajiye fiddah yayi a gidan da aka bashi shi kuma ya haɗa tarkacanshi ya koma hotel da zama. Waiwaye. Ƴarfillo ta isa ƙasar china da niyyar ayiwa Ayman Asirin da ze manta da ummu har ƙarshen rayuwarsa,ita kuma asa sonta a zuciyarshi kota halin ƙaƙa. Tayi nasara inda aka gudanar mata da duk abinda take buƙata akace ta jira lokaci kawai. Ayko farinciki a gurinta baa magana,zamanta tayi a ƙasar,acewarta se ayman ya nemeta,zata ɗawo. Kullum cikin saurare take taga Ayman ya nemeta,shiyasa wayarta bata canja number whatsapp ɗinta ba sabida tadan in ya kirata be samuba ze mata magana tacan. Wannan kenan. Bayan wata biyu da tafiyar Ayman,ummu gaba ɗaya ta rasa abinda yake damunta,ko sunyi waya da Ayman cikin tambayarta yake abinda ke damunta amman ta rasa abinda ke damunta kwatakwata bata jin daɗin jikinta,hakanne yasa yace ta jira ze turo doctor ya dubata. Ayko haka akayi yaturo maya likitanshi,gwajin farko likita ya tabbatar mata tana ɗauke da ciki har na tsawon watanni biyu. Ummu ji tayi kamar a mafarki likitan yake shaida mata wannan saƙon na baƙar qaddara,gudun tonawa Ayman Asirine yasa ta danne duk damuwarta ta nuna tayi farinciki,sabida Ayman ya turo shine da sunan ita matarshi ce. likitanne ya kira Ayman ya masa albishir da ƙaruwar daya samu. Hasbunallahu waniimal wakil,itace kalmar dake fita a bakin Ayman har likitan ya masa sallama besan me yakw,cewaba seda yaji wayar ta cinke sannan. Kuka ya rushe dashi kamar yaro yana faɗin. "ka gani ko Abbah kaga abinda kajawowa zuriar ka ko,da akwai rabon haihuwa a tsakaninmu kuma rabon yana kusa ne amman ka hanani raya sunnar maaiki da ita,kasa na raya sunnar shaiɗan sanadin haka harda rabo,why Abba,me na maka har haka,wlh fiddah da kakeso na raya sunnar da ita hakan ze farune amman da gawata". Haka yay ta sambatu shi kaɗai yana kuka ya rasa inda zesa kansa har zuwa dare. Ummu ko da ƙyar ta iya tashi a inda take kuka take me tsuma zuciya. Se dare Ayman ya samu ya kirata. .tana ɗagawa ta rushe mishi da kuka faɗi take. "am finish,qurratu ayni,am finish". Cikin kuka shima yake bata amsa. "No hayati,you are still my life,my wish,my happiness,without you am nothing,pls stop saying that my heart is burning,faruwar hakan ya ƙaramin sonki a zuciyata,wlh ina tare dake,kuma don Allah karki salwantar da abinda ke cikin ki Allah ya fimu sanin,dalilinsa na wanzar dashi a tsakaninmu,ki soshi kibashi kulawa tamkar sauran ƴaƴa,wlh hayati ba abinda ya ragu a son da nake miki,ina sonki keda abinda ke cikin ki don Allah ki tayani sonshi"ya ƙarasa maganar cikin kuka. "tabbas nasan jarabawace Allah yakemin tun daga ƙuruciyata har zuwa yanzu,na godewa Allah da zaɓata da tayi yake kuma gwadani,ko kaɗan bazanyi baƙinciki da abinda Allah ya tsaro a rayuwata ba,cikin jikina bashi da laifi bashi ya kawo kanshiba,kawoshi akayi ya zama izina agaremu,dan haka na godewa Allah daya nunamin kuskurena tun a duniya". Haka sukai ta kuka a wayar da kyar Ayman ya rarrasheta tayi shuru,sukayi sallama akan ze kirata anjima. Sede me suna gama wayar saƙon da ƴarfillo ta turo masa na ya manta da Aymana ya iso gareshi. ya ajiye wayar kenan yaji kamar anbuga mishi abu akai,kawai se yafara mamakin abinds ya sashi kuka,a iya bincikensa ya rasa dalilin kukan nasa. Cikin dare tunanin ƴarfillo ne ya takura zuciyar Ayman,ji yake kamar ze mutu in beji muryarta ba. waya yaciro yakirata be shigaba hakanne yasa ya turamata voice note ta whatsapp. Surbajon kuce [7/23, 08:49] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *duk matsayin Ayman da adduarsa,nasan ko kama ƙafar manzon Allah beyi ba,kuma anyiwa Annabi asiri ya kamashi duk da kusancinshi da Allah,tunda Allah ya jarabci annabawansa da jarabawa kalakala,babu wani mahaluki dayafi ƙarfin jarabawar Allah,akwai mutanan da suke cikin jarabtar rayuwa da tafi na ummu Aymana,so tari in Allah yana jaraba bawansa mutum ji zeyi kamar Allah baya sonshine yasa yake masa hakan,to bakomai yasa Allah jaraba bayinsa ba sedan gwada ƙarfin imaninsu, littafina yana tafiya akan turba me kyau,sabida duk abinda na rubuta yana faruwa da gaske,daidaikun ranaku ne zan hau facebook banci karo da posting akan anyi zina an samu ciki an zubar ko kuma ankashe yaron ko kuma anyardar ba,shi kenan kuma se ace marubuci bazai rubuta abinda yake faruwaba,sede yatafi a tsaye ba wata lanƙwasa,kuma inaso iyaye su sani dan ka haifi ɗa to hakan bayana nufin kaine keda alhakin tsara masa rayuwa ba,mahaifin Ayman yayi tsauri da yawa wanda duk wani uba me irin tsaurinsa ƙarshe hakan baze haifar masa da ɗa me ido ba yadda iyaye keda hakki akan ƴaƴansu haka suma ƴaƴan ke dashi,wani baya haifar ɗan wani,haihuwa da mutuwa,da aure basa jira in lokacinsu yazo dole se anyi su,haihuwa ko ba aure in lokacinta yazo wlh se an haifa a titi,aure ko ba tsayayye in lokacin yayi se anyi,mutuwa ko ba ciwo in,ajali yay kira dole a tafi,shiyasa nake kira ga iyaye,su dena tsaurarawa akan zaɓin ƴaƴansu matuƙar sun bincika babu wata illah to su daure su aura musu dan wlh rabo shi ba ruwanshi da akwai aure ko babu in lokacin shi yayi zuwa yake.zanci gaba a yadda na tsaro labarin,ba wani lamari da ze canjani akan hakan,hasalima jarabtar da star ɗin littafin zata fuskanta,shine maƙasudin sawa littafin suna UMMU AYMANA* *page 71-72* Kamar a mafarki ƴarfillo taga saƙon Ayman,ihu tasa na murna,daganan ta tura masa numbern ta na china. Wasa wasa soyayya ta shiga tsakaninsu me ƙarfi,Ayman ko bacci baya iya yi in beji muryarta ba.gaba ɗaya sungama tsara yadda zasu gudanar da rayuwar auransu inda Ayman yayiwa ƴarfillo alƙawarin auranta da zaran ya dawo gida nigeria,fiddah ko kota kirashi baya ɗauka sabida ya tsaneta,ita ko ummu gaba ɗaya ya manta da ita da labarin ta. Baiwar Allah ummu yau wajan watanni biyar kenan rabonta da jin muryar,Ayman ko ta kirashi bata samu,faɗin tashin hankalin da take ciki baze misaltuba,ga cikinta yanzu ya tsufa dan watansa bakwai. Kullum cikin addua take akan Allah ya sauketa lfy,ba abinda yafi mata daɗi da ta samu ta gama secondry school ɗinta tun cikin na ƙarami. Rayuwa ta fara yiwa ummu zafi sabida ko securitie ɗin da Ayman yasa A gidan yanzu babu su,uwa uba ATM card ɗinshi in taje cire kuɗi bazasu ciruba. Ayman ganin yana zaune besan dalili ba sede yaga ancire kuɗi a account ɗinshi ne yasa yayi magana da bankin akan a dakatar da account ɗin har se ya dawo,danshi besan wanda yake cire kuɗinba. Sannu a hankali ummu ta fara siyar da duk wani zinari nata dan ta samu ta rufawa kanta asiri da ƙaninta, shima kamin wani lokaci kuɗin sun ƙare. Yau Ayman yayo waya ga megadin gidan nashi wanda su Ummu ke ciki ya bada umarnin a kulle masa gidan dan aciki ze ajiye fiddah itako ƴarfillo sabo ze gina mata yadda zasu ji daɗin rayuwarsu. Me gadin abun ya bashi mamaki sabida yadsn akwai ummu aciki,amman be ce komaiba ya amsa umarnin ogan nasa,cikin gidan ya nufa dan ya sanar da ummu saƙon oga. Ita ko ummu tun cikin dare take fama da ciwon mara,kasancewar watan haihuwarta ya tsaya,amman dayake batasan ya abin yakeba haka tai ta murƙususu ita kaɗai har zuwa lokacin da me gadin yazo. Lallaɓawa tayi tazo kiran megadin,koda ya sanar da ita saƙon Ayman to kawai tace,dan tasan ze iya yimata abinda yafi hakama tunda ya iya gudunta sanda ta fi buƙatarsa. cikin gidan ta koma dakyar ta iya haɗa kayansu taja hannu jinior suka fice a gidan tana kuka ga mararta dake ciwo kamar zata fashe,dakyar take iya ɗaga ƙafa. Sun ɗanyi tafiya me tsawo taji bazata iya ci gaba da tafiyarba,kasancewar gurin akwai yalwar bishiyoyi ,gindin wata bishiya ta ƙarasa dakyar,kuka take jinior na tayats,abun gwanin tausayi,ummu ji take kamar zata mutu. Unguwar ta manyan masu kuɗi ce dan Anan Gidan shugaban ƙasa ma yake,inda ummu take kwance ƙofar wani gida ne,me ɗan karan kyau kai da ganin gidan kasan meshi yaci ya tada kai. Haka ummu taita fama ga faya ta fashe amman haihuwa shuru zuwa lokacin har numfashinta yafara sarƙewa. jin ƙarar buɗe get ɗin gidanne yasa jinior rugawa da gudu gurin,wata arniyar motace ta cinno hancin ta waje,da sauri jinior yasha gaban motar yana kuka. Da sauri na cikin motar ya fito,saurayine,kyakkyawa na ajin farko wanda kallo ɗaya zaka masa kasan naira najin tsoronsa. Ƙarasowa yayi gurin jinior yana tambayarsa lafiya. Shiko jinior yana ganin mutumin ya fito da sauri ya kama hannunshi yafara janshi har seda yakawoshi inda ummu take kwance. Agigice mutumin ya ƙarasa kusa da ita,taɓata yayi amman ina ko numfashi batayi a gigice ya ɗauketa ya nufi motarshi da ita yayinda jinior ke biye dashi abaya. Gudu yake na fitar hankali har ya iso Asibiti. Daga saman Asibitin an rubuta, *Doctor Na'im Chiroma,Special Hospital.* yana parking da sauri ya ɗauketa yayi cikin Asibitin da ita,duk wani maaikaci na Asibitin seda ya kamu da tsananin mamaki na ganin doctor ɗinsu ɗan ƙwalisa ɗauke da me tsohon ciki kuma yana kwasar gudu mutumin dako sauri be iyaba. Kai tsaye labour room ya shiga da ita,duk wani abu daya dace shi ya mata har ya samu numfashinta ya dawo,ruwan naƙuda ya ɗaura mata. kamin wasu mintoci ummu tafara kukan neman taimako,hannun shi ta riƙe da ƙarfi tana salati,gaba ɗaya tausayinta yagama cika shi,injin scarning ya matso dashi kusa da ita inda yafara yimata scanning ɗin dan ganin yanayin kwanciyar yaron. Ilai kuwa yaron a karkace yake,dan haka hannu yasa ya gyara mata,ummu ji tayi kamar zata mutu,sanda yake gyara kwanciyar yaron. Ba jimawa Allah ya sauketa lafiya,inda ta haifi ɗa namiji tamkar Ayman ne yayi kakin yaron.babu,wata halitta ajikin yaron wacce ba irin ta Ayman bace. muje zuwa. surbajon kuce. [7/23, 18:58] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Hameedan Hamman ɗinta,Ummu faix,Bilshop(Hizba one😜)wannan shafin nakune nagode da irin kulawarku gareni,adduoinku sunamin daɗi,Allah yabarmu tare cikin aminci* *page 73-74* Murna sosai Doctor yayi da nasarar daya samu,ta ceton ran ummu da abinda ke cikinta. Shiko jinjirin se tsala kuka yakeyi alamar dake nuna yana cikin ƙoshin lafiya. Ummu tayiwa Allah godiya daya turo me taimakonta,ta kuma gode masa daya rabata da cikin lafiya. Dayake Asibitin private ne komai akwai a ciki dan haka kayan jarirai doctor ya bada umarnin a kawo,ayko ba jimawa nurse har ta gama shirya babyn ta kawowa doctor shi. Gurin ummu ya kaishi wacce fitowarta daga wanka kenan. "madam hala haihuwar fari ne wannan naga tunda yazo duniya baki buƙaci a kawo miki shi ba,kinajin kunyar shi ne?"doctor Na'im ya wurga mata tambayar yana dariya. Ɗago ido ummu tayi ta kalleshi,ji tayi gabanta ya faɗi da sauri taƴi ƙasa da idonta tana murmushi. miƙa mata yaron yayi,hannunta na rawa ta amsheshi,tana amsar yaron ya buɗe ido yana kallonta,yana turo harshenshi waje.wani matsanancin kukane ya kufcemata,rungume yaron tayi cikin kuka take faɗin. "Na gode maka Allah daka bani shi,babu bsƙin ciki a zuciyata na game da samun shi,Allah ka gafartamin laifin dana aykata na samar dashi,ya Allah albarkacin naƙudar haihuwar sa danayi,da rainon cikinsa da nayi,ya Allah ka dubeni ka gafartamin na tuba ya Allah natuba"ta ƙarasa zancan cikin matsanancin kuka. Gaba ɗaya kan doctor ya gama ɗaurewa gameda furucin na ummu,yana buƙatar ƙarin haske game da hakan amman ya barwa cikin shi. Miƙewa yayi ya fice yaje ya shigo da jinior,da gudu jinior yaje ya rungumeta yana kallon babyn yace. "lah Aunty kin siyo mana baby ne?". kai ummu ta ɗaga masa wasu hawayan na ƙara biyo fuskarta. Ɗakin hutu aka kaisu,se a lokacin ummu ta ciro nono taba babyn ay kamar jira carab ya cafke yafara sha,tanajin zafin tsotson da yakeyi amman ta daure sabida tasan in ta shayar da yaron ma Allah ze ƙara yafe mata. Da daddare doctor ya shigo ɗakin,lokacin jinior har yayi bacci ummu da babyn ta ne kawai idonsu biyu,tana riƙe da hannun babyn tana kallonshi shima ita yake kallo abin gwanin sha'awa.har doctor ya samu guri ya zauna ummu batasan ya shigo ba hankalinta nakan babynta wanda da gani zeyi wayo sosai.ba abinda yake ƙara faranta ran ummu se kama da yaron yakeyi da Ayman,wanda tasan ko giyar wake yasha be isa yace ba nashi bane.ɗauke babyn da akayi shi ya dawo da ummu cikin hayyacinta a gigice takai raruma zata kwace ɗanta,ganin doctor tsaye akanta riƙe da babyn shi ya haddasa mata jin kunya. "wannan kalar soyayyar da kike nuna masa ita zata sa ya ganeki da wuri mu kuma uncles ɗinsa ya dunga yimana ƙiwya". Ummu de murmushi kawai takeyi,ta kasa magana,har seda doctor ya sake jefo mata tambayar data hargitsa kayan cikinta. "Madam zuwa yanzu ya kamata ki sanar dani inda ƴan uwanki suke domin aje a sanar dasu halin da kike ciki musamman baban yaron nasan yana can cikin damuwa". kuka ta rushe dashi me tsuma zuciya,cikin kukan take faɗin. "Dama duk abinda ka tambaya ina dasu dana shaida maka inda suke,wannaɓ ɗan da kake gani babanshi be damu ɗashi ba,hasalima ya gujemu tun cikinshi na wata biyu bamusan inda yake ba,ƴan uwa kuma bani dasu ksga kenan babu wani wanda hankalinshi ke tashe da rashin ganin mu,da ace mahaifiyata na kusa dani shine zan iya faɗa mata komai game da ɗana,dabida uwace kawai zata iya share kukan ƴarta"ta karasa faɗi cikin kuka. Tausayinta ne ya mamaye zuciyar doctor,cikin sanyin murya yace. "na gamsu da bayananki,amman ina roƙon,alfarmarki da ki bari in kawo mahaifiyata gareki domin ta share kukanki,mahaifiyata mace ce me tsoron Allah,dason ɗan da ba nata ba fiye da kanta,namiki alƙawari inde ta muamalanceki zaki iya mantawa ma da taki mahaifiyar"ya ƙarasa zancan yana dubanta cikin tausayawa. "ko baka yabi mahaifiyarkaba nasan mutuniyar kirkice ta lura da irin kirkin ɗanta,na amince ka turota gareni,amman batun mantawa da tawa mahaifiyar abune me wuya"ta sake fashewa da kuka. "to nagode da damar da kika bani,yanzu zan wuce zan tafi da wannan ƙaramin dan,asamu ayimasa wanka,amman se kin amince". "Doctor kenan!ay tunda ka iya ɗaukomu batare danasan inda kaina yakeba kataimakemu baka cutar damuba to banajin zaka iya cutar damu sanda na dawo cikin hayyacina,dan haka kaje dashi ɗin". Murmushi yayi sannan yace, "to nagode da yarda dani". Miƙamata babyn yayi sannan ya ɗauki jinior yafice daga ɗakin. Kai tsaye gida ya nufa,yana parking ya ɗauki jinior ya shige dashi cikin gidan a falo ya sami mahaifiyar tashi se safa da marwa takeyi. yana sallama ta nufeshi a gigice tana faɗin. "Haba ɗan umma yanzu dan Allah abinda kayi ka kyauta kenan taya zaka tashi ka kashe wayoyinka kuma kaje kayi zamanka a waje har ƙarfe goma na dare"ta faɗi cikin damuwa. Se a lokacin ta lura da jinior dake rungume a kafaɗarshi,da sauri ta miƙa hannu ta karɓeshi,tana tambayarsa ina ya samo ɗa. Shiko jinior matar na karɓar shi a hannu doctor ya buɗe idonshi a firgice,ƙureta yayi da ido,itama kallonshi take cike da mamakin irin kallon da yaron yake mata,zuwa can kuma se jinior ya saki ajiyar zuciya yakwantar da kanshi a ƙirjinta gamida riƙe mata riga alamar dake nuna yana gudun a kwace mishi ita. Murmushi doctor yayi sannan ya kwashe duk abinda ya faru ya sanar da ita,Allah sarki baiwar Allah harda kukanta,sallama doctor ya mata ya wuce ɗakinshi ita kuma ta haura sama ɗauke da jinior. Ko cikin dare al amarin jinior ci gaba yayi da ɗaure mata kai,dan gama miƙa hannu yake cikin rigarta,kamar yadda yara suke in suna buƙatar nono,gefe ɗaya kuma hannun shi ɗayan na riƙe da rigarta,tausayin shi ne ya kamata gamida sonshi,tabbas ta fahimci yans cikin kewar mahaifiyarshi ne shiyasa yake mata hakan,rungumeshi tayi sukayi bacci. washe gari da wuri suka tashi sabida zasuje asibiti gurin ummu. gurin me gadi doctor yaje yasashi ya ɗauko jakar kayan su ummu,wacce suka bari tun jiya a ƙofar gidan. Hajiyar shi ya kaiwa ta buɗe ta cirowa jinior kayan daze saka sannan ta ciro na me jego tamayar ta rufe,da kanta tayiwa jinior wanka dan so ds tausayin yaron tun daran jiya suka gama cika zuciyarta,shirya shi tayi tsaf ts bashi abinci yaci,sannnan doctor yazo ya ɗauki kayan abincin da ta shiryawa me jego na abinci,suka fice zuwa Asibitin. Koda suka iso Asibitin maaikatan Asibitin se duƙawa suke suna kwasar gaisuwa gurin mahaifiyar doctor ahaka suka nufi ɗakin da ummu take. Ummu wacce ke tsaka da baccinta ita da babynta a gigice ta farka,kamar wacce aka tsoratar,gabantane ya shiga faɗuwa da ƙarfi,miƙewa tayi tsaye,hakan yayi daidai da shigowar su doctor. Kallon kallo suka shiga yi tsakanin ummu da mahaifiyar doctor,kallo irin nason gano a inda suka san juna,a lokaci guda suka tuno. ƙara ummu Aymana ta ƙwalla tana faɗin, *UMMA NA !!!!!*. bata ƙarasa faɗi ba duka suka yanke jiki suka faɗi sumammu. muje zuwa. Surbajon kuce. [7/24, 09:49] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *banida lfy pls pray for me* *duk meson book ɗina ko wanne irine ya nema a group,ko yaje page ɗina na whattpad ze samu acan amman kar abini pc ace inturo,nadena turawa dan wlh ina rasa inda zansa kainane,na rasa wa zan kula,so pls wanda suka nema ban tura musu ba kuyi haƙuri ku kuma masu shi don Allah in,an nema ku dunga bayarwa pls* *page 75-76* A gigice doctor ya nufi mahaifiyarshi yana kiran sunan ta amman ina ko motsi batayi, a sukwane ya fice a ɗakin zuwacan se gashi ya dawo da kayan ayki da nurse na biye dashi da gudu. Kai da ganin yadda doctor ya ruɗe ya gigice kasan akwai soyayya me ƙarfi tsakaninshi da mahaifiyar tashi. Ceton ransu suka shigayi gaba ɗaya,wanda ba jimawa dukansu suka farka. Ummu kuka umma kuka,rungume suke da juna dukansu,ba abinda sukeyi se kuka ganin hakane yasa doctor ya tattara su gaba ɗaya suka wuce gida,Dan karsu tara masa mutane. Koda suka isa gidan basu bar kukanba ,gaba ɗaya sun saka doctor cikin damuwa da ƙyar ya samu sukayi shuru sannan umma ta fara magana. "Haƙiƙa na yarda Allah maji roƙon bawane tunda Allah ya bani lafiya nake nemanki ƴata,Allah be haɗamu ba se yanzu nagode masa daya sadani dake,sede na shiga damuwa ganinki ɗauke da yara har guda biyu wanda ban sanki dasuba ko kinyi Aurene?". Kuka ummu ta fashe dashi ta rungume mahaifiyarta,ta kamo hannun jinior tasa ana umman tace. "Umma wannan ɗanki ne na cikin ki,ke kika haifeshi,ranar da kika haifeshi kika ɓace ban sake ganinki ba se yau,shi kuma wannan jinjirin....."se ta rushe da kuka ta kasa ƙarasa maganar. da kyar tasamu kukan ya barta tace. "shi kuma wannan jinjirin umma ɗana ne wanda na sameshi bata hanyar aure ba"ta sake rushewa da kuka. Ba umman ba doctor kanshi seda ya faɗo daga kan kujera. .Kuka umman tasa me tsuma zuciya tace. "Nasan haka zata iya faruwa dake ƴata,nasani,wlh banyi baƙin ciki ba ,da ace kashe shi kikayi ko kika zubar da cikin ko kika yardar dashi wlh zuciyata se ta buga da baƙin ciki,ƙaddarace wacce tana iya samun kowa,Allah ya gafarta miki zunubin da kik aykata shi kuma in rayayyene Allah ya albarkaci rayuwarsa". Daga ummu ta kwashe labarin komai ta faɗawa ummanta,Cikin kuka umma ta rungume jinior tana faɗin. "Allah sarki ɗa na tun jiya kake nunamin alamar ni mahaifiyarkace amman ban fahimta ba sabida nasan ban haifa ba se yanzu nagane hakan se yanzu naga kamannin mahaifinka a tattare dakai,Allah na gode maka daka kuɓutar da zuriata daga sharrin masharranta,na gode daka bani ƴa maabociyar imani nagode ya Allah". Haka sukai ta kuka dakyar umma tafara bada nata labarin bayan ta baro ƙauyan su. *waiwaye* Tunda na baro ƙauyan bansan inda nake nufa ba,bansan me nakeyi ba. haka na dunga rayuwa cikin daji da bakin titi,har Allah ya kaini garin kano,na jima a garin kano sosai ina yawon haukata. Kwatsam rana ɗaya nazo tsallaka titi motar ciroman kano kuma gomnan bankin nigeria ta bugeni. Basu wuceba seda suka kaini asibiti,anan aka dunga bani kulawa,ƙarƙashin jagorancin ciroman,seda nayi shekara guda a Asibitin mahaukata na dawanau amman kullum ba sauƙi se na Allah. Ba inda ciroma be kaini neman maganiba amman ban warke ba,seda wata aljana tazo ajikina ta shaidawa ciroma asiri akamin sannan ta faɗi inda aka birne asirin,acikin gidan,mu na ƙauye,kuma tabashi shawara akan ya ayka da mota aje garin a zuwan anzo siyan takin kashin shanu na gidan,wanda inde aka tashi ɗiba zaa ɗebo harda asirin. Ayko haka akayi ciroma ya ayka dayake idonsu rufe yake da son kuɗi shaf sun mance da mugun ƙullin da sukayi,haka aka haƙo harda asirin da suka burne,koda aka kawo kashin shanun ciroma da kanshi yadunga tonawa har yagano asirin ya ɗauka yaje ya ƙona. faruwar haka shine sanadin samun lafiyata,ciroma yaci gaba da bani kulawa. Ana tsaka da hakane Allah yayiwa matar ciroma rasuwa wato mahaifiyae na'im,tun bayan rasuwarta,se ciroma ya nemi na amince da ya aureni sabida ya samu me kulawa da ɗansa ƙwaya ɗaya da ya mallaka wato naim,sabida mutuwar mahaifiyarshi har so tayi ta taɓa kwakwalwarsa. To na amince mukayi aure da ciroma,tunda mukayi aure ciroma yaso aje akamo su jameelu,ni na hanashi sabida ina tunanin kina hannunsu kar su illatamin ke. Yanzu haka na haihu da ciroma inda na haifi ƴanbiyu,duka maza,amman yanzu suna kano,gidan sarkin kanon kasancewar sarkin shida ciroma uwa ɗaya uba ɗaya suke,to shine yanemi alfarmar in an tashi yayesu akaisu gidanshi to yanzu sunacan. murna sosai ummu ta taya mahaifiyar tata gameda ci gaban da tasamu. Ranar wuni sukayi cikin farinciki inda umma tayiwa ummu wankan jego na asali kuma ta wanke jikanta wanda Naim yayiwa huɗuba da sunan sarkin kano kasancewar sarkin yana nuna masa ƙauna sosai amatsayinsa na wan mahaifinsa.suna kiran yaron da Abu Ayman🤔. Ummu batasan Ayman ɗan sarkin kano bane dan tunda suke be taɓa bata labarinshiba.shiyasa bata kawo komaiba a ranta. Shiko doctor,kamannin da Abu Ayman yake masa da na ɗan uwansa Ayman yafi komi bashi mamaki,amman ya danganta hakan da ikon Allah ne. muje zuwa. surbajon kuce. [7/25, 08:41] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Da badan zan roƙi addua daga bakunanku ba da ba abinda zesa nayi typing,pls kusani a addua wlh banida lafiya amman ko wuƙa aka nunamin bazan iya faɗin abinda kemin ciwoba,kawai ni de naji banda lfy,ku taimakamin da addua don Allah*. *page 77-78* Rayuwa tayiwa ummu daɗi sam ta mance da damuwarta,Ayman ne kawai in ta tuno take shiga damuwa. Shiko doctor son da yake nunawa Abu Ayman koshi ya haifeshi iya abinda zemasa kenan,kullum ya fita se yadawo masa da abin wasa,ko sutura,bashi da ayki inyadawo daga Asibiti se na rainonsa. Yau ciroma ze dawo daga tafiyar dayayi,ya jima baya ƙasar,dan besan ma anga ummu ba. Gidan gaba ɗaya ya kaure da gyare gyare da dafe dafe,kowa beda sukuni,sabida ciroma mutum ne da bayason ƙazanta,kuma ba laifi mutum ne shi me zafi,shiyasa kowa ya,shiga taitayinsa kamin ya iso. Da Azahar ya iso gidan,Umma se murna take da ganin mijinnata,haka shima dan ya gaza bari su keɓe tunda tazo taryarsa ya rungumeta,abun kunya yaba ummu Aymana. Bayan yayi wanka ya kintsa ya sauko ƙasa domin yaci abinci,anan yaci karo da Naim goye da Abu Ayman yana jijjigashi azuwan dole se yayi bacci,shiko abu Ayman inbanda ware ido ba abinda yakeyi alamar dake nuna bashi da niyyar baccin. Dariya ciroma yayi sannan yace. "ikon Allah naim ina kuma ka samo yaro ɗan turawa haka harda goyashi?"ya ƙarasa tambayar cikin dariya. Saukeshi yayi abayan yana dariya shima yace. "daddy jikankane yake wahal dani wlh". "jikana kuma?to kawoshi inganshi inga jikan nawa". Kaimishi shi yayi ya karɓeshi,yana duban fuskar yaron,ya waigo da ssuri yana tambayar naim. "Ah ah wai matar Ayman harta haihune,basu faɗaminba,?yaushe sukazo nigeriar ba suna germany ba?". Dariya naim yayi sannan yace. "Daddy kenan ay wannan kamace kawai da ikon Allah amman wannan ba ɗan Ayman bane,hasalima jikan mommy ne na gurin ummu Aymana da ta ɓace". Fuska ɗauke da faraa yace. "Amman kai da mommyn taka baku,da kirki yanzu har wannan abun farincikin ze faru amman baku faɗaminba?,ina ƴar tawa take? tazo na ganta mana". Da sauri naim yaje ya kira ummu tana zuwa ta durƙusa tana gaisheshi. Fuska cike da faraa yake amsawa,sannan ya mata barkar haihuwar da tayi sannan ya tambayeta a inda tayi aure da kuma wanda take auran. da gudu ummu ta miƙe tabar gurin tana kuka,jiki a sanyaye ciroma yakai dubansa fuskar umma itama kuKan takeyi. miƙawa naim Abu Ayman yayi,naim na amsarsa yabar gurin. Shi kuma ciroma yafara tambayar umma meye matsalar. Bata ɓoye masa komaiba ta sanar dashi,duk abinda ya faru. .Runtse ido ciroma yayi yana huci kaida ganin yanayinsa yakai ƙololuwa gurin ɓacin rai. "yanzu wanne mara imaninne ya aykatawa ƴata haka,waye shi?!!!!!"ya faɗi sanda ya buga tebur ɗin dake gabanshi da ƙarfi,idonshi yayi ja gashin jikinshi duk ya miƙe. Da kyar umma ta shawo kanshi ya zauna,yana huci. "Ranka ya daɗe wlh wannan tambayar munyiwa ummu ita tun kamin kazo amman taƙi bamu amsa sede tace tayi aƙawarin rufa masa asiri dan haka bazata karya alƙawarinba,wai se randa shi da kanshi ya buƙaci ta furta". "wannan ay zancan banzane,taya zata rufawa wanda yatona mata asiri asiri,shiɗin ɗan uban waye daze mata wannan keta haddin?kiramin ita yanzu"ya faɗi cikin ƙaraji. Da sauri umma taje ta kira ummu. "ki faɗamin sunan shegen daya miki wannan taasar da inda yake da kuma aykin da yakeyi". cikim kuka ummu tace. "Da badan nasan makomar me karya alƙawariba ranar gobe ƙiyama wlh da ba abinda ze hana ban tona masa asiriba,kodan baƙincikin daya sama zuciyata na guduwa da yayi ya barni,kayi haƙuri daddy,wutar me karya alƙawari daban take a lahira,ni me laifice gurin Allah bangama wanke wannan ba bazan ƙarawa kaina waniba,bazan iya faɗa makaba"ta sake rushewa da kuka. "tashi kije"daddy ya umarceta. Jiki a sanyaye ummu tabar gurin. Shiko daddy ranar wuni yayi cikin takaici da baƙin ciki,ji yake daze ga mutumin da se ya harbeshi har lahira. Washegari da rana,tawagar sarkin kano ta sauka a gidan ciroma. yazo yima ɗan uwannasa sannu da zuwa. Gaba ɗaya gida ya kaure da murna,haka suka keɓe shida ciroma wanda yake ɗauke da Abu Ayman a hannunsa suna hira. "wannan ɗan waye kuma ka jajibo,kiyashi uban jayejaye?"sarki ya tambayi ciroma yana dariya. murmushi ciroma yayi sannan ya kwashe labarin komai ya sanar da sarkin. yadda ran sarki ya ɓaci ko na ciroma be ɓaci haka ba,faɗi yake. "duk ranar da aka gano wannan azzalumin dole se ya ɗanɗana kuɗarsa,wlh bazamu yarda ya cutar mana da ƴa abanza ba". Da kyar ciroma ya rarrashi sarki yayi shuru,miƙa masa Abu Ayman ɗin yayi.ya amshe shi. A gigice ya miƙe tsaye yana kallon yaro yace. "ciroma kaga abinda nake gani kuwa kode ido nane,?Ayman ɗana fa nake gani yana jinjiri". Dariya ciroma yayi sannan yace. "kamace kawai da kuma ikon Allah amman in banda abunka taya ayman ze haɗu da ummu mutumin da baya ma ƙasar". Shide sarki yasan ana kama amman be taɓa ji ko a labari ana kama irin haka ba inde ba ɗan mutum ba. gaba ɗaya jikinshi yayi sanyi,zuciyarshi tagaza amincewa da kamace kawai,ba abinda ya ɗagawa sarki hankali irin wani tabo daya gani a tafin hannun Abu Ayman wanda shida Ayman suma duk suna dashi kuma iri ɗaya. "Banyarda kamace kawai ba"itace kalmar da sarki ke maimaitawa a zuciyarshi. muje zuwa. Surbajon kuce,pls kusani a addua. [7/30, 17:44] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Liman yazo Sallah tazo,muje zuwa masoyana Allah ya sa muga Annabi,(S,A,W)* *Page 79-80* Wuni Sarki yayi rungume da Abu Ayman yana jin wani yanayi tattare da yaron,yanaji ajikin shi koda ga ina yake jinin sa ne. Ba ƙaramin firgita sarki yayi ba sanda yaji an ambaci sunan mahaifiyar yaron da suna ummu,sabida inde ba mantawa yayi ba,Ayman ya taɓa furta sunan a gabanshi sanda yake roƙonsa ya amince ya auri ummu. Gumi ne ya shiga karyo masa,da kyar yasa akayi masa kiran ummun,sannan bayan tazo ya buƙaci kowa yabasu guri zeyi magana da ita,ba musu kowa yabar gurin harda ciroma. Jiki a sanyaye ummu tashigo falon,yayinda gefe ɗaya kuma take mamakin abinda yasa sarkin yace tazo. Kanta a ƙasa ta gaisheshi,ya amsa sannan yace. "Ɗago kanki ki kalleni ƴata". A kunyace ummu ta ɗaga kai tana kallon shi. A razane ta miƙe tsaye tana binshi da kallon tsana,gami da nuna shi da ɗan yatsa tace. "dama kaine ka badda kama ka shigo gidannan?mayaudari azzalumi,mugu,Wallahi Ayman bazan yafe maka ba ka cutar dani ka cutar da ɗanka,ka gudu kabarni se yanzu kadawo......."hawayen dake zuba a idon sarkine yasa ummu lura da kyau,ashe ba Ayman bane,kawai tsabar kamace dan se yanzu ta lura wannan ɗin ya girmi Ayman. Da sauri tasa hannu ta toshe bakinta jikinta na rawa,musamman ganin hawaye a fuskar sarkin yafi komai ɗaga mata hankali,tsugunawa tayi a gabanshi tana kuka ta kama ƙafarshi ta soma da cewa. "Don Allah kayi haƙuri ɓacin ran dana shigane da ƙunci yasa na ɗauka kaine Ayman,tabbas Ayman ya cutar dani kuma ya yaudareni,amman hakan bazesa na karya alƙawarin da nayi masa ba,Ayman ya shaidamin mahaifinshi babban mutum ne a ƙasarnan,haka zalika shima babban mutum ne,dan haka na rufe sirrinshi,dan kar duniya tayi tur,dashi da mahaifinshi,na mishi alƙawarin zan rufe sirrin har se lokacin daya buƙaci in buɗe,se gashi yau cikin rashin sani na karya alƙawari,don Allah ina roƙonka,ka rufawa Ayman da mahaifinshi asiri,banaso duniya ta zagesu musammam ma mahaifinnasa wanda beji ba be gani ba,don Allah kar ka tona wannan sirrin nawa na roƙeka". Ta ɗago ido tana kallonshi cikin kuka,wanda shima zuwa lokacin gemunshi yagama jiƙewa da hawayen. Muryar shi na rawa,yace. "ba wanda zan faɗawa,amman se kin bani labarin komai game da haɗuwarki da Ayman ɗin,kar kimin ƙarya,dan idan kikayimin zangane". Ba musu ummu ta kwashe komai ta sanar da sarki tundaga kan mafarkin da sukeyi ds juna har zuwa taimako daya dunga yimusu,bata ɓoye masa komaiba,ta ƙarasa bashi labarin tana kuka. Zuwa lokacin sarki ya gaza yin kukan illah na zuci da yakeyi share hawayenshi yayi ya daidaita natsuwarshi,sannan yace. "Gaskiya Ayman be kyauta miki ba,na tausaya miki,shiyasa nayi shaawar haɗaki aure da ɗana,guda ɗaya dana mallaka,nayi imani ze soki ze kula dake da ɗan dakika haifa batare dayayi laakari da hanyar da aka bi gurin samar dashiba". "Nagode babah da wannan karramawa,sede wlh duk da abinda Ayman yayimin har yanzu zuciyata taƙi tayi fushi dashi ma bare ta tsaneshi,na koya mata hakan amman taƙi koya ,koda na amince na auri ɗanka,zan aureshi ne badan ina so ba sedan rufe,asirin kaina dana ɗana,Ayman kawai nakeso,kuma shi kaɗai zanso har abada"ta ɗurƙushe a gurin tana kuka. jikin sarki rawa ya farayi sabida yayi imani shine silar faruwar komai,shine ya tarwatsawa wainnan masoya tarihin soyayyar su,shine silar wanzuwar yaron dake hannun sa wato Abu Ayman,inbe haɗasu Aureba ina zekai wannan Alhakin daya ɗauka,yayi danasani mara iyaka,da kalaman daya furtawa Ayman,wanda yasan da badan suba ko aɓoyene Ayman zeje ya Auri ummu batare da saninsa ba,amman kaucewa kalaman ya janyo jikansa yazo bata hanyar Aureba. Share wasu zafafan hawaye yayi,sannan yace. "ba komai ƴata nagode da amincewar da kikayi nasan a sannu zaki mance da wancan Ayman ɗin ki saba da Ayman ɗana". Da sauri ta ɗago tana kallonshi jin yace sunan ɗanshi Ayman. Murmushi yayi dan ya fahimci mamaki takeyi. "tabbas sunan ɗana Ayman,wanda yanzu haka baya ƙasar ze dawo nan da ƴan watanni,da tuni ma yadawo to an ƙara masa lokaci ne shiyasa be dawoba,ina fatan kinyi farinciki da zaɓin nawa?". kai ummu ta ɗaga tana murmushi,cike da jin kunya. Janta da hira yaytayi abun har mamaki ya dunga bata,sabida ta ɗauka sarakuna ko magana ma wuya take musu. sun jima suna hira yayinda sarki cikin hikina ya dunga recording video na ummu da ɗanta,a wayarshi batare da ta gane ba daga bisani ya sallameta ta shige cikin gida. Koda sarki ya tuntuɓi ciroma game dason Aurawa Ayman ummu,sosai ciroma yay murna gamida fatan alkhairi,itama umma murna tayi,shiko naim ji yayi kamar duniya aka ɗora masa akai sabida nauyin da zuciyarshi da kanshi suka masa. Tunda ya fara ganin ummu ya kamu da sonta ya za'a yi masa shigar sauri?,shi Ayman ko labarinta be taɓa jiba bare ya ganta kuma yana da matar shi amman kuma za'ace za'a ƙara masa da ummu?,gaskiya ba'a masa adalci ba. *WAI INA AYMAN NE?* Surbajon kuce. [8/1, 09:03] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Saƙone zuwa gareku members na duka groups ɗina,nace novels kawai nakeso a group ɗina baya gashi banason komai,duk wanda ya turo abu saɓanin novels komai ƙanƙantarsa zan cireshi,batare dana kalli kusancina dashiba,kuma inna cireki karki biyoni pc,neman baasi,kina ganinki a waje kije ki bincika kin karya doka ne,ko wannan abun da ake cewa duk meson book kaza yasa sunansa a ƙasa to banda groups ɗina,dan inkinturo zan turaki waje,naga kunfarayin na ummu aymana ma,to shima ku dena karku tura groups ɗina kar ku tura na wani,ni na yarda da soyayyarku gareni base kunsa sunanku ba,dan inaga tunda kuka shigo group ɗina ay no need kucemin ku masoyanane,tunda kuke aciki nasan soyayyarce ta kawoku,ba komai yasa nasa wannan dokar ba se danmu masu siyan datar naira ɗari ɗari da hamsin,in ana ture turennan saurin ƙarewa takeyi,dan haka akiyaye nagode* *page 81-82* Ayman anashi ɓangaran. Yanzu ƴarfillo ta baro inda take ta dawo gurin shi a garmany,tare suke kwana a hotel ɗin dayake,ya mance da ummu da duk wani abu daya shafeta,fiddah ko haushinta yakeji wanda ya rasa dalilin dayasa yakejin haushinnata,sede duk ƙarshen wata yana ayka mata da kuɗi,ta hannun drivern sa dan tayi amfani dasu. Son da yakewa ƴarfillo yanaji duk wanda yanemi taɓa masa ita ze iya kawar dashi a doron duniya,sone na hauka wanda da gani ba tambaya kasan na Asirine. Ƴarfillo ansamu duniya,an kuma samu abinda akeso wato zuciyar Ayman,dan yanzu har kuka yake mata akan tabarshi ya kusanceta,sosai yake kusantarta ba dare ba rana,tade zama tamkar matarshi,ga wani matsi da tayi amfani dashi na hanashi jin daɗin kowacce mace a duniya inde ba itaba,shiyasa in yana kusantarta,har ihu yakeyi dan daɗi,duk da wannan sheƙe ayar bata taɓa tunanin yanada aureba. Fiddah baiwar Allah tayi kuka tayi kuka har ta dena yi,gaba ɗaya tayi baƙi ta lalace ta fita hayyacinta,ko abincin kirki bata iya ci,sabida baƙin cikin Ayman,ta rasa inda zata sa kanta,ta nemi number salmab amman bata samuba kullum cikin try take,yau ko taci saa ta sameta. bugu ɗaya salmab ta ɗauka,tana mata tsiya. "Amarsu kenan an manta damu kode ɗan babane ya ɓoyeki?" Kuka fiddah ta rushe dashi,tana faɗin. "na shiga uku salmab,na lalace,ina cikin ƙuncin rayuwa,inkika ganni zeyi wuya ki ganeni,Ayman ya azabtar dani,fiye da tunaninki,tunda muka iso ƙasarnan ban sake ganinshi ba ya ajiyeni yayi tafiyarsa"ta ƙarasa zancan cikin kuka. "ke kika bashi dama fiddah rashin wayonki ya fara damuna, sekace ba mace ba,da duk matsala ba kya iya warwarewa kanki ita sede ni,inna mutu kuma,waye ze dunga yimiki,?,to wlh tun wuri in zakiyi hankali kiyi,kicire tsoronsa aranki,ki ɗaura ɗamarar ƙwatarwa kanki ƴenci da kanki sabida kema macece". "To yanzu salmab ya zanyi,nace miki ko ganinsa banayi,taya zan kwaci ƴencina,sede fa duk ƙarshen wata ya turo driver ya kawomin kuɗi,taya kike tsammanin zan ganshi?" "kaji sakarya,au dama har akwai ɗan ayke a tsakaninku amman kike cewa bakisan inda yake ba?to duk ranar da driver ɗin yazo kibishi yakaiki wajenshi,kuma duk balai karki kuskura ki baro gurin,kicire tsoro aranki na faɗa miki". Daga haka sallama sukayi kowa ya ajiye wayar. Shuru fiddah tayi tana tunanin baiwa da basirar da Allah yayiwa salmab,ita kods wasa bata taɓa tunanin bin driver ɗinba se yanzu da Salmab tasa ta a hanya. Ayko acikin satin driver yazo kawowa fiddah saƙo da sassafe,dan haka batayi wata wata ba tace yakaita gurin ogan nashi,ba musu ya ɗauketa suka tafi. Sanda suka isa hotel ɗin lokacin Ayman yana tsaka da saduwa da abar ƙaunarsa,se gurnani yakeyi,dayake hotel ɗin,ɗakunan jerasu akayi rukuni rukuni,dan haka base kabi ta reception zaka isa ɗakunan ba. Har ƙofae ɗakin driver ya raka fiddah sannan ya juya ya tafi,nucking ta shiga yi amman shuru ba a zo an buɗeba. Kasa kunne tayi dan taji kamar kuka daga cikin ɗakin,ilai kuwa gurnanin Ayman tajiyo,ɗauka tayi bashida lfy ne dan haka ta shiga dukan ƙofar,suko basu sanma tanayiba,murɗa hannun ƙofar tayi ga mamakinta se tagama ashe a buɗe take dan haka ta tura tashiga da gudu ɗakin,ba kowa a falon dan haka ɗakin da gurnanin yake fitowa ta nufa. taku har kullum surbajo. [8/1, 10:31] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* *ƘUNGIYAR MU TAIMAKI KANMU MATA!!! WANNAN SHAFIN NAKUNE,ALLAH YA CI GABA DA DAFA MANA AKAN MANUFARMU TA ALKHAIRI,DUK WANDA CUTACE A ZUCIYARSHI YA ALLAH KADA KA KAWOSHI CIKINMU DOMIN TSARE DUKIYARMU DAGA FAƊAWA HANNUN DA BE DACEBA,AMEEN* *Page 83-84* Tana zuwa shiga tayi ɗakin. Abinda ta ganine yasa ta fara ganin jiri na ɗibarta,Ayman kwance da wata mace wacce ba tashiba acikin yanayin dako ita da take matarshi basu taɓa kasancewa a hakanba Basusan ta shigo ba Ayman andage se rabawa ƴarfillo duty yake,yana zuba santi. Hawaye ne ke bin fuskar Fiddah na baƙin ciki,rasa me zata musu tayi kamar ance waiga ay kawai se ta hango,wata sanda kakkaura a ajiye a gefen gadon irin ta sojojin nan,batayi wata wata ba ta ɗauki sandar ta bugawa Ayman A tsakiyar kanshi,wata ƙara yasaki ya gamida ɗaga ƴarfillo ya faɗi ƙasa sharab jini na fita akanshi. A gigice ƴarfillo ta miƙe sede kamin tayi wani yunƙuri tuni fiddah ta runtuma mata sandar,dukanta fiddah tashigayi d sadar iya ƙarfinta Ihu ƴarfillo takeyi amman fiddah ko alamun tsayawa bata dashi. Tuni fiddah ta karya hannun ƴarfillo gamida yimata targaɗe a wasu sassan jikinta,Ayman ganin fiddah na shirin kashe mishi ƴarfillo ne yasa ya ƙoƙarta da ƙyar ya miƙe ya cakumi fiddah ta baya ya dannata toilet yayi maza ya kulle ƙofar da key. Zuwa lokacin tuni ƴarfillo ta suma dan azaba,d kyar ya iya samata kayant shima yasa sannan yay waya asibiti akazo da Ambulance aka kwashesu zuwa Asibitin. Fiddah ko ihu take tana jijjig ƙofar amman a banza ba me jinta,ganin hakane yasa ta haƙura ta zuna a toilet ɗin tana ci gaba da kukanta. koda suka isa Asibitin anyi musu duk abinda yadace,ƴarfillo tafi shan wuya dan targaɗe har huɗu da karaya ɗaya fiddah ta mata ajikinta,baya ga faffasa mata jiki da tayi ya kumbura kamar wacce tayi hatsari. A daran aka sallami Ayman danshi ciwonshi kaɗanne,kuma anyi dressing ɗin gurin. kai tsaye hotel ya nufa ya buɗe fiddah,tana fitowa ta ɗaga sandarta zata ƙara runtuma masa,da sauri ya kwace sandar,sannan ya wurgar da fiiddah ɗin ya shige toilet ya tsarkake jikin shi ya fito ɗaure da tawul a ƙugunsa. Afusace fiddah ta miƙe ta ɗaukeshi da mari har guda biyu sannan tace. "Fasiƙi, mazinaci,wanda baya tsoron Allah,wallah kaji kunya,dama abinda kake aykatawa kenan,shiyasa ka kasa sauke nawa hakkin dake kanka,to na godewa Allah da ban taɓa haɗa shimfiɗa da ɗan akuya kamarka ba,wlh bana ƙaunarka kasake ni kawai,wawa bunsuru kawai". Ran Aymam inyayi dubu ya ɓaci dajin kalaman fiddah,dama a cike yake da ita game da dukar masa ƴarfillo da tayi, "Ke dan kan ubanki har kin isa ki kirani da wainnan sunayan?waye ubanki,mekike taƙama dashi?". "sede ubanka,kuma ubanka shine ubana,ina taƙama da duk wani abu dakake taƙama dashi,ɗan akuya"fiddah ta bashi amsa batare da tsoron komaiba. "Ubankine ɗan akuya baniba,dan a gurinshi na koya"Ayman ya faɗi sanda yake tunkarota cikin fushi. ja d baya fiddah tayi sannan tace. "hhhh me ya haɗa biri da gada kuma da zakace a gurin ubana ka koya?Ay kowa yaga abinda kake aykatawa ko tambya baze yiba agurin,bunsurun ubanka ka koya". *Tassssssssssss!!!* Ayman ya ɗauke fiddah da mari gamida rufeta da duka seda ya mata lilis sannan yace. "Tunda nace ubankine ya koyamin akuyanci kin ƙaryatani to bari innuna miki da gaske shiɗin ya koyamin,dan nacire miki tantama،abinda zanmiki yanzu inkinje gida ki tambayi uwarki zata tabbatar miki da haka ubanki ya mata ta samar dake". Be jira komaiba ya cire tawul ɗin dake jikinshi yacirewa fiddah kayanta,kuka take takasa hanashi,tanaji tana gani yana ƙoƙarin kusantarta,amman tsamin da jikinta yayi yasa ta gaza hanashi. Ayman ko be saurara mata ba harseda ya rabata da budurcinta,ta ƙarfin tsiya,ya dirjeta son ranshi,duk da baya jin daɗin komai amman yasha alwashin seta gane kurenta akan abinda tayi masa tayiwa ƴarfillonsa. Seda ya gaji dsn kanshi ya ɗagata ya shige toilet ya sakarwa kanshi ruwa. Fiddah kuka take wanda tunda aka haifeta bata taɓa yin irinshi ba,tayi danasanin,auran Ayman ba iyaka tana nan zaune yafito ya shirya ya fice ya kyaleta. Da ƙyar ta iya rarrafawa zuwa toilet ta tsaftace jikinta,ba abinds yake ƙona ran fiddah kamar ganin Ayman be jima da Aykata zinaba yazo ya kwanta da ita wannan abu koni ya bani takaici. Ta jima a toilet ɗin sannan taji daɗin jikinta ta fito ta maida kayanta ta fice daga hotel ɗin gidanta ta nufa ta haɗa duk abinda tasan natane,ta nufi Airport cikin ikon Allah tasamu jirgin yawo danhaka ta biya kuɗi masu yawa ta samu visa ta shiga jirgi ya ɗago da ita zuwa gida nigeria. Shiko Ayman daya fita Asibitin ya koma inda ya tarar ƴarfillo ta farka se masifa take akan se ya sanar da ita wacece tamata wannan aykin,dakyar a tsorace ya shaida mata fiddah matar sace. ba ƙaramin firgita tayi dajin cewa yana da mata ba,ashe ta kashe maciji ne bata sare wuyanshi ba,hakanne yasa ta tada mada da darun akan cewa sede a ɗaura musu aure a yau ko ta tafi tabarshi,Ayman ji yake in ƴarfillo ta tafi ta barshi tamkar rasa rayuwarsane,dan haka haƙuri yadunga bata itako taƙi yarda. Ganin hakane yasa yaje yasamo wasu musulmai su biyu ya biyasu sukazo suka ɗaura musu aure a Asibitin. Wannan alamari yasa ƴarfillo da Ayman cikin farinciki mara iyaka,burin ƴarfillo yacika,a sannu zata nunawa fiddah da duk wani wanda ya nuna baya sonta da Ayman banbancin dake tsakanin,tagari da ƴarbariki. Muje zuwa,Surbajo ce. [8/1, 18:53] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 85-86* Cigaba sukayi da rayuwarsu har zuwa lokacin da ƴarfillo taji sauƙi,ko ƙuda Ayman bayaso ya taɓa masa ƴarfillonsa,sosai yakejinta Aransa. Cigaban labari. Naim duk yadda yaso yaga ya hana auran ummu da Ayman amman ina abu yafi ƙarfinsa,dan gama ummu na gama jinin biƙinta aka ɗaura Auranta da Ayman bisa jagorancin Sarki da ciroma. Ɗaurin Auran daya sami halattar jamaa da dama. Se bayan an ɗaura aurene sarki ya tara matansa ya musu bayani,gamida nuna musu video na ummu da ɗanta. Kuka gaba ɗayansu suka sa suna faɗin. "kaine silar komai,da ace kabarshi ya aureta tun farko da wannan abun kunyar be samemuba". "Tabbas nine sila sabida dama komai be faruwa seda sila,tun farkon rayuwar yarannan Allah ya rubuta se hakan ta samesu kunga ko babu me ja da hukuncin Allah,kude kawai kubar maganar muyi musu,fatan alkhairi". "to munji amman de kasan akwai azumummuka na kaffara da zakayi ko?"inji hajiya babba. Dariya yayi sannan yace. "na fiki sanin haka tunda nine nayi rantsuwar,tun ranar dana sawa raina zan aura masa ita nafara yin Azumin wanda ahalin yanzu na gama". Hakade sukai ta tattaunawa gameda Alamarin Ayman ganin yanzu kwata kwata ma be damu daya kirasu su gaisaba saɓanin da da kullum se sunyi waya,fatan alkhairi suka masa. a ranar da aka ɗaura Auran ummu da Ayman a daran fiddah ta iso nigeria,wanda kuma Aranar aka ɗaurawa Ayman Aure da ƴarfillo a germany,sede anriga daura na ummu sabida na ummu da shaɗaya na safe ne yayinda na ƴarfillo ya kasance gab da magriba. fiddah ba gidansu ta sauka ba gidan iyayan Ayman ɗin ta sauka,fuskarta a kumbure haka ma jikinta sabida dukan da Ayman ya mata. Sanda mahaifansa suka ganta ba ƙaramin ruɗewa sukayiba suka shiga tambayarta abinda ya faru. Cikin kuka fiddah ta kwashe komai ta sanar dasu,yenke jiki me martaba yayi ya faɗi ƙasa sumamme,a gigice akayi Asibiti dashi. Likitoci suka duƙufa ceto rayuwarshi,da kyar suka samu numfashinshi ya daidai ta,amman sede ya kamu da hawan jini sosai,yana buƙatar hutu. Haka akaita fama a asibitin seda yayi sati biyu sannan aka sallamoshi gaba ɗaya bashi da kwanciyar Hankali,wai ɗanshi ne ya zama mazinaci irin haka. Haƙuri yaba fiddah,sannan yasa aka buɗe mata part ɗin Ayman na gidan ta zauna ,inda sarki ya shaida mata ze kwato mata ƴencinta amman beso ta sanar da mahaifinta komai shima mahaifintane. Fiddah ta gamsu da hakan,dan haka ta zauna a gidan,amman koya ta tuno abinda Ayman yamata se kuka ya kubce mata. Anata ɓangaran ummu kuwa gyarata ummanta takeyi ba kaɗanba,abun har ummu tagaji dashi,yayinda kuma take ci gaba da shayar da ɗanta,wanda ta ɗauki son duniya ta ɗora masa,gashi yaron kullum daɗa wayo yakeyi. shiko naim sabida baƙinciki barin ƙasar yayi dan tabbas yana son ummu amman bashida zaɓin daya wuce ya nesanta kanshi da ita dan samun natsuwa a zuciyarshi. Wani ɓangaran sarki yasa aka gina masa acikin gidsn nasa,me girman gaske,inda akayi gurin zaman mace biyu se kuma turakar miji,yasa aka ƙawata ginin da duk wani abu da zamani yakawo na ƙawata ɗaki ,ba abinda baa zuba ba a gidan sannan yasa fiddah tazo ta zaɓi inda takeso,sannan yamata bayani akan yayiwa Ayman Aure ne da ummu. Fiddah ta firgita dajin cewa anmata kishiya ba kaɗanba,amman seta ɓoye damuwarta a gaban sarkin tayi fatan alkhairi. Sati biyu tsakani aka kawo ummu gidan mijinta,ita da jaririnta,wanda da ummanta taso ta amsheshi amman sarki da ciroma suka hana ,sukace ay inda zaa kaishi gidan ubanshine dan haka acan tafi cancanta ya rayu. Dole umma ta bar mata badan ranta ya soba. Sanda iyayan Ayman da yayyanshi mata suka ga Abu Ayman seda sukayi kuka sabida tausayawa rayuwar yaron,nan sukaita nan nan dashi kowa nasonshi. Sarki sawa yayi aka kira fiddah da ummu yamusu nasiha akan su zauna lafiya. kowaccensu amsawa tayi da insha Allahu. Daga haka ya sallamesu ummu itama ta shige ɗakinta daya gaji da haɗuwa tana tunanin waye angon nata ya kamannin shi suke,haka de taita tunaninta. Shiko Abu Ayman yanacan gurin kakanninsa suna nuna masa gata. Wata biyu da tarewar ummu,Ayman ya diro nigeria shida tauraruwarsa ƴarfillo. Kai tsaye gidanshi na Abuja ya nufa da ita inda suka ci gaba da shaƙatawarsu. Sarki a jarida yaga ssnarwar dawowar sojojin da aka tura germany tun watanni biyu da suka wuce,dan haka rai aɓace yakira Ayman a waya. Da kyar ya ɗauki kiran,nan sarki ya rufeshi da masifa akan duk abinda yakeyi yazo ysna son ganinsa,da Ayman kamar baze jeba se ƴarfillo ta,zugashi akan suje ɗin bawanda ya isa ya rabasu. da wannan shawara ta ƴarfillo yasamu kwarin guiwa yashirya suka kama hanyar kano cikin so da ƙaunar juna. muje zuwa surbajo ce. [8/2, 08:08] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMAN* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud. DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *page 87-88* Sun isa kano da Azahar,tundaga get ɗin fada fadawa suke zubewa suna kwasar gaisuwa har zuwa ƙofar shiga cikin gidan. motarsu na parking suka fito,Ayman ya saƙala hannunshi,a ƙugun ƴarfillo,ita kuma ta kwantar da kanta aksn kafaɗar shi ahaka suka nufi cikin gidan,fadawa kowa ya saki baki yana kallon ikon Allah. Da sallamarsu suka shiga falon lokacin sarki na zaune shida matanshi suna hira. Fuska ɗauke da mamaki sarki da matanshi suke kallon su Ayman har suka sami guri suka zauna,ga mamakinsu kan cinyar Ayman Ƴarfillo ta zauna tawani narke ajikinshi tana shafa ƙirjin shi. A yadda suke ya gaida iyayan nashi,sabida tsabar ruɗewa babu wanda ya amsa acikinsu,Ayman ya tallabo fuskar ƴarfillo yace. "honey meet my parents" A yatsine ta ɗago kanta tamusu kallon uku saura kwata,sannan ta ɗaga yatsun hannunta tace. "hy guys,whasap" Sarki bakinshi na rawa yace. "Ayman ina kasamo wannan ahlul nar ɗin?,ƴar wacece? meye haɗinka da ita?". Rai aɓace Ayman yace. "Haba Abba wanne irin cin fuskane wannan,dazaka wani kirata ahlul nar,to matatace dana Aura a germany se me?" Tassssss Sarki ya kifeshi da mari ya ƙara masa wani sannan yace cikin fushi. "in baka girmamani amatsayin mahaifinkaba, a matsayin sarkinka i deserved resfect from you,dan haka kayi hattara,uban waye ya aura maka auran da ita dahar zaka dubeni kace matar kace?" Ayman wanda zuwa lokacin ranshi ta gama ɓaci,taya sarki ze zagar masa ƴarfillo sannan shima kuma ya zageshi?miƙewa yayi yana huci kamar ze doki sarkin yace. "kaga malam baze yiwu kazageni kazagi iyalina at the same time sannan kace bazanyi maganaba,dama kirana kayi danka zageni,to zan ɗauki komai amman bazan yarda kazagarmin mata ba,dan tana ƙima da daraja fiye da komai agareni" Sarki wan marin ya kifawa Ayman,wanda yay daidai da isowar wani marin daga mahaifiyarshi,cikin kuka tace. "Ayman baka da hankaline akan mace kake faɗawa mahaifinka irin wainnan kalaman?" A fusace Ayman yaba mahaifiyarshi amsa. "Dan yana mahaifina Allah nane shi daze sani agaba yana zagi yana duka?,ke bakiji cin mutuncin da yake min bane se nawa kika gani?,wlh yasake sa hannunshi ajikina sena rama,nifa akan matata wlh zan iya raba mutum da ranshi" ya ƙarasa maganar yana huci alamar abinda ya faɗi ze iya aykatawar. Sarki kanshi ba ƙaramin ɗaurewa yayiba tabbas yasan Ayman ba kanshi ƙalauba dan yasanshi farin sani,amman duk da hakan,se ya koya masa hankali. Dogarai sarki yaba umarni da cewa. "Kuita dukanshi se ya dena motsi,umarnina ne" yana gama bada umarnin ya fice a falon,suma su hajiya ficewa sukayi. Suko fadawan kimanin su goma ƙarti majiya ƙarfi suka nufi Ayman suka fara duka tun yana ramawa har ya koma kare kanshi,ƴarfillo ko ihu take tana basu haƙuri amman ina ko sauraronta basuyiba. Basu dena dukanshibs seda suka tabbatar daya suma,sannan sukaje suka sanar da sarki. Umarni ya musu da su sasu a kurkuku shida matar tashi,in ya farfaɗo su gana masu azaba daidai da abinda suka Aykata. Ayko haka sukayi suka kwashesu zuwa kurkukun gidan suka rufe,ƴarfillo se ihu take tana dana sanin biyo Ayman kano. wasa wasa seda sukayi sati guda rufe a kurkukun nan ana gana musu azaba,duk sun fita hayyacinsu, sarki kuma yace bazaa ƙyalesuba harse Ayman ya nemi afuwa,shiko Ayman taurin zuciya yaƙi neman afuwar,se yau da ƴarfillo tasashi agaba tana masifa,shine ya roƙi afuwar aka fito dasu aka gurfanar dasu agaban sarki. "Nasan zuwa yanzu ka fahimci koda ni ba ubanka bane toni shugabankane,inaso kasani,na ƙara ɗaura maka aure da wata yarinyar,fiddah ma matarka tananan,dangaka dole ka sauke hakkinsu dake kanka". "kan balai,cemaka akayi ni bunsurune dazakai ta taramin mata toni wlh ba ruwana dasu,ni ga matata nan kuma ita nakeso,kasan yadda zakayi da sauran". Daga haka jan hannun ƴarfillo yayi suka fice a gidan suka dawo Abuja ransu a ɓace gameda kaskancin da sarki ya musu. Muje zuwa surbajon kuce. [8/2, 10:02] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *wannan shafin nakune manyan mata maganin ƙanana na gode da kulawarku gareni,mss wahidah,hauwa bukar,Respectable,Allah yabar ƙauna yabar zumunci,one love,#ana tare* *page 89-90* Sarki ya gaza runtsawa tun zuwan Ayman kullum cikin tunani yake nason gano aynihin abunda ya sauya masa ɗabiun Ayman,amman ya rasa gane bakin zaran. *(Ni danake gefe nace a raina,sarki kenan to taya zakace ka kasa gano bakin zaran bayan kaine kamasa baki da cewa in ya tsallake umarninka Allah ya haɗashi da balain dayafi ƙarfinsa,to Ay ƴarfillo itace balain daka roƙa masa Allah ya haɗashi da ita)* Haka ya kasance cikin damuwa,duk wani ɗan uwan Ayman ya shiga damuwa gameda lamarin,saɓanin matan shi wainda basu san wainar da ake toyawa dan basu da labarin komai sabida ɓangaransu dabam kuma ba koyaushe suke fitowaba se bayan sati biyu suke fita zuwa cikin gidan domin gaida surukansu,shiyasa basu da labarin komai. Fiddah ce suke waya da salmab. "Salmab nifa banga amfanin asirin da mukayiwa Ayman na ƙarfin shaawaba,inbanda ma ɓacin rai daya jawomin dan haka nide kije kice a karya kawai na haƙura". "hakane ƙawata,tabbas beda amfani tunda ƙarshe de kishiyama akayimiki,kuma ni danke nayi tunda bake kaɗai ze amfanawaba yau ɗinnan zanje gurin iya bisi ta karya shi, ki kwantar da hankalinki kina tare da salmab insha Allahu sekin juya zuciyar Ayman yadda kikeso kuma zakice na faɗa miki" hira suka ɗan taɓa daga bisani sukayi sallama. suna gama wayar Salmab ta nufi gidan iya bisi tamata bayanin komai,nan take ba wani musu iya bisi tayi tsubbace tsubbacenta ta karya Asirin. Godiya Salmab ta mata ta biyata kuɗin aykinta ta wuce gida,tana isa takira fiddah ta sanar da ita angam komai. Ayman yana tsaka da kwasar garar ƴarfillo suna ta ihun daɗi shida ita,se jo yayi sandar girman ta kwanta,abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,yayi iya yinshi ta miƙe taƙi,sema ƙara kwanciya take kamar an ɗaura ruwa a leda. Hakane ya tilasta mishi sauka akan ƴarfillo badan ranshi ya soba. Itako wacce ta gama hawa network jin shurune yasa ta dawo hayyacinta. "ya naga ka sauka,banganeba?"ƴarfillo ta tambaya Tsaki Ayman yayi sannan yasa hannun ya cire myafin daya rufa ajikin shi ya nuna mata yadda abar ta koma. "yanzu nufinka haka zaka barni da ruwa cike da mara ban zubarba bare in samu sauƙi?" "Haba horney ya zanyi,abunnanfa ba laifi na bane sanin kankine innaɗau hanya bana tsayawa senaje bus stop,ko a checking point ban tsayawa,kawai de yau may be ta gajine shine take hutawa"ya ƙarasa maganar yana shafo ƙirjinta. "Tonide gaskiya baze yiwuba dole kasan yadda zakayi ka rabani da wannan ruwan"ta ƙarasa zancan cikin shagwaɓa gamida shafo mishi abar. "Baby rigima kenan,wato ba yafiya kenan sena biya ko?" kai ta ɗaga masa gamida kashe mishi ido ɗaya. Ayko ba musu ya kwantar da ita akan gadon,ya ɗaga ƙafafunta ya ɗora akan kafaɗarshi yayinda shi kuma yake zaune,hannu yasa ya ɗago ƙugunta sama daidai bakinshi,ba tare da ɓata lokaciba ya kafa bakinshi a gurin yafara tsotsa,yana ɗan zira hannunshi aciki. ihun daɗi ta shigayi,dan some times da Ayman ya kusanceta tafi ƙaunar yamata wannan abun dan ji take kamar ansata a aljannah dan daɗi. Haka Ayman yay ta mata,kamin wani lokaci bakinshi yagama jiƙewa,sabida ƴarfillo ta fitar da abinda ke damunta. kwanciya sukayi kowa na maida numfashi gamida ajiyae zuciya. Tundaga wannan rana komai ya sauya da Ayman se ya kusanci ƴarfillo so bakwai a rana koma fi ammaɓ yanzu da kyar yakeyin huɗu. Abun ya fara damunta,sabida ya riga daya gogar da ita dayin dogon zango,hakanne yasa suka fara samun saɓani,inda tanuna ita bata aminceba dole se yaci gaba dayi mata yarda ya sabar mata. Shide se haƙuri yake bata sabida yayi iya yinshi amman yagaza yin abinda takeso ɗin,ganin baze mata yadda yadda take so bane yasa tafara neman wasu mazsn a waje suna biya mata buƙata. Sarki ne zaune a gaban malaminsa yana masa istahara,bayan ya gama ya ɗago yana masa bayani. "A zahirin gaskiya,Ayman ya faɗa tarkon mace ne shaiɗaniya,inda ta haɗashi da baƙaƙen Aljanu,suka cire son kowa da tsoron kowa aranshi sukasa nata,a halin yanzu in tacr ya kashe mutum kowaye ze kashe koda kuwa kai mahaifinsane,sannan akwai bakin uwa ko uba me ƙarfi daya kamashi wanda baze sakeshiba harse in wanda ya masa bakin ya furta ya yafe masa wannan sune matsalar Ayman,wacce Allah ya nunamin". Ajiyar zuciya sarki yayi sannan yace. "Tabbas ni nayiwa Ayman baki wanda bansan ya kamashi ba amman yanzu na yafe mass Allah ya gafarta masa,abu na biyu kuma yazaayi arabashi da baƙaƙen aljanun?". murmushi malam yayi sannan yace. "To masha Allahu hanyar karya sihirin me sauƙice,kawoshi zaayi nan amasa ruqiyya,sannan asashi a addua adunga sadaka da yardar Allah komai ze warware". Godiya sarki yayiwa malamin sannan ya sallameshi. Kan sarki yagama kullewa ya rasa yadda zeyi yasa Ayman yazo kano amasa ruqiyyar,dsn yasan ko kiranshi yayi baze ɗaga ba,zuwa can shawara ta faɗo masa. Dogaran sa ya kira su goma yasa suje su ɗauko masa shi a Abujar,inda ya ƙara da cewa. "ko A sume ne ko a karye inta kama ku kawominshi a yau,ɗinnan,wannan umarninane" da haka dogaran suka ɗauki hanyar Abuja,inda basu jima sosaiba suka isa,kuma sukayi saa Ayman ya fito ze fita ƴarfillo tayo masa rakiya security ɗinshi zagaye dashi. Rai a ɓace ya tsaya yana kallon dogaran. . Ɗaya daga cikin dogaran ne yace, "Allah ya baka nasara da yawan rai,Sarkine ya bada umarnin mu kaimasa kai koda kuwa a sumene,yace yana buƙatarka a yau,tuba nake yallaɓai,umarnin sarkine". Ayman sanin dayayi dogarai basa kin aykata abinda sarki yasasune yasa bece musu komaiba,kuma baya buƙatar su kunyatashi a gaban yaran shi,dan haka juyawa yayi yanufi motar fadawan,gamida yiwa ƴarfillo sallama,ranta besoba amman tasan halin sarkin inta hana Ayman zuwa may be ya turo akamata dan haka taba Ayman goyon bayan zuwa. yana shiga motar fadawan suka juya dashi zuwa kano. Se cikin dare suka iso kanon. Subajon kuce. [8/3, 07:29] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Wannan shafin nakune masoyana,islaha tasiu,Billyn shantaly,mrs mahmud,jeedda(D&W novels)Aisha yar'aduwa,nagode da kulawarku,Allah yabar zumunci#ana tare* *page 91-92* Tunda dare yayi dole ɓangaranshi ya nufa domin ya kwanta inyaso da safe sa gana da sarkin. Koda isarshi ɓangaran yayi mamakin ganin gurin ba yarda yabarshi ba alamu sun gwada wani yayi rayuwa aciki bayan shi. Ranshi sosai ya ɓaci game da shigar masa ɗakin da akayi,haka ya kwanta rai aɓace ga kewar ƴarfillo data dameshi. Washe gari da sassafe ya isa cikin gidan,da shigarshi ba gaisuwa Kawai ya Baƙaci ganin sarki,su hajiya basuji haushinshi ba dan sarki ya musu bayanin matsalarshi dan haka kai tsaye suka bashi damar ganin shi. Koda ya shiga gurin sarki shima be gaisheshi ba illa cewa da yayi. "jiya kasa anje antaho maka dani,ka raboni da matata,to bari kaji in nufinka cin mutuncin dakasa akamin wancan karon kakeson kasa ayimin yanzu to wlh baka isaba dede nake dakai,wlh kasa wani ya tinkaroni sena harbeshi,ko kaine da kanka"ya ƙarasa maganar yana zaro bindigar dake ƙugunsa. murmushi sarki yayi sannan yace. "Haba Ayman maida wuƙar,niba mutuncinka zanciba,hasalima haƙuri nakiraka na baka,sannan mu tafi tare can Abujan dan naba ita iyalin naka haƙuri,dannasan ban kyautaba,kayi haƙuri kaji". Karkuso kuga bakin Ayman,yadda yake washeshi dan sarki yace zeje yaba ƴarfillo haƙuri,cike da murna yace. "Na yafemaka amman gaskiya karka kuma,danni ina girmama mutum ne dede da yadda yake girmama matata,dan haka ni yanzu na shirya inka shirya kazo mu wuce kawai dan tanacan tana jirana". Murmushi sarki yayi sannan yace. "Ay tun asuba na shirya,sabida nasan sammako zakayi,dan haka ashirye nake muje kawai amman zan ɗan tsaya wani gida nan gaba kaɗan zan amshi saƙone na alkyabba danasa ayiwa sirikar tawa dannasan da wuya idan kasai mata,kaga kuwa matar ɗan sarki ay dole seda alkyabba". wani farincikine mara misaltuwa ya mamaye zuciyar Ayman,dan haka ranshi fess suka fice daga gidan shida sarki cikin rakiyar dogarai ƙarti majiya ƙarfi. Tafiya sukayi batafi ta minti biyarba suka iso gidan Malmin,dayake yasan da zuwansu,dan haka komai a tsare yake. Sarki ze fita a motar Ayman yace. "yakamata mu shiga tare dan na zaɓar mata kalar datafi so dannasan kalarta" "To ba matsala zi muje ka zaɓar matan,nima zanfi son a kaimta wacce tafiso"sarki ya bashi Amsa. Daga haka suka shiga cikin gidan har cikin ɗakin malamin. Kan Ayman ne yafara juyawa tunda ya shaƙi hayakin dake fita a ɗakin na magani. Jirine ya shiga ɗaukarshi zuwacan ya yanke jiki ya faɗi,fadawan nanne suka ɗaukeshi suka ƙarasa shigar dashi cikin ɗakin. Nanfa malam ya shiga Aykin shi,Ayman se kururuwa yake yana banƙarewa,se fadawane suka danneshi,fisge fisge ya shiga yi,haka malam yaci gaba da karatunshi. Aljanunne suka fara magana,inda suka ce. "kadena ƙonamu haka mu turomu akayi jikinshi,ba laifinmu bane,mu baƙaƙen aljanune,akwai wata aljana musulma,dake tare dashi,tana taimaka masa,to dazamu zo jikinsa,seda muka kasheta,tukuna mukazo dan karta ɓata mana ayki,amman yanzu zamu fita kadena ƙonamu haka". Malam be saurara da karatunshiba ci gaba yayi,sukai ta ihun su seda ya tabbatar sun jigata sannan yabasu damar fita tare da gargaɗin suka sake dawowa se ya halakasu. Ba musu suka fice inda Ayman yadunga atishawa har sau uku,sannan ya koma ya kwanta sharab a ƙasa,malam yacewa fadawan su sakeshi yanzu shine bacci yakeyi. Haka malam yaci gaba dayimasa turare da magunguna har zuwa lokacin daya farka bakinshi ɗauke da kalmar shahada. A firgice ya miƙe zaune yana waige waige,zuwacan ya miƙe da gudu,ze fice,da ƙyar fadawa suka kamoshi,shiko se dambe yake ze kwace,ahaka suka dawo dashi. Se a lokacin idonshi ya sauka kan me martaba,kawai se ya rushe da kuka,yana faɗin. "Don Allah ku ƙyaleni gurin Hayati zani,nasan tana cikin wani hali wanda take buƙatata akusa da ita,kubarni naje naga awanne hali take don Allah"ya ƙarass maganar cikin kuka ya rarrafa ya kama ƙafar me martaba yana roƙonsa. muje zuwa surbajon kuce. [8/3, 12:24] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 93-94* Rungumeshi sarki yayi yana bubbuga bayansa,sannan yace. "kwantar da hankalinka,zakajw gurinta amman yanzu muje gida ka huta tukuna,banason musu inka musa zan hanaka zuwa". Shuru Ayman yayi yana kallon sarki,kamar wani wawa. Godiya sarki yayiwa malam sannan ya kama hannun Ayman suka fita zuwa mota aka jasu zuwa gida. Koda suka isa gidan part ɗin Ayman sarki yakaishi yasashi yayi wanka sannan yabashi magungunan da malam yabashi. Addua yasashi yayi sannan ya kwanta be jimaba bacci ya ɗaukeshi,ja mishi bargo sarki yayi,sannan yafice daga ɗakin,kai tsaye ɓangaran matan Ayman ya nufa. Ba ƙaramin mamaki sukayi da ganinsa ba dan be taɓa zuwa ba sede su suje. Gaisheshi sukayi sannan kowa tasamu guri tazauna tana sauraronshi. "mijinku ya haɗu da iftilai irin na aljanu,danhaka yau an rabashi dasu,dan haka yanzu yana part ɗinshi yana bacci kuje ku kula dashi,sauran bayanin in ya farka ze muku,so kuyi haƙuri da zaman da kukayi na tsawon lokaci batare da kunji daga gare,shi ba" Godiya sukayi su duka sarki yamusu sallamah ya tafi. Kan ummu ne ya ɗaure tarasa gane kan wannan lamari,wai wa take aurene,?tana mamakin yadda suke nunawa ɗanta so alhalin sunsan ba ɗan halak bane,abubuwan suna bata mamaki kwarai da gaske,ko yanzu da sarki yazo daze fita da Abu Ayman ɗin ya tafi,haka tai ta tunani,daga ƙarshe de tayi shigewarta ɗakinta dan bata jin zata fara kai kanta gurin angon nata batare dashine ya nemetaba. Su fiddah kuwa sarki na fita ta faɗa wanka tajima tana wankan sannan tafito,shima dan tana gudun kar ummu ta rigata zuwane,kwalliya tayi tagani ta faɗa da english wears sannan ta ɗora alkyabba akai tafice kuyanginta suka mara mata baya zuwa ƙofar ɗakin Ayman ɗin,dakatar ɗasu tayi a waje ta shige ita kaɗai. Lokacin farkawar Ayman kenan daga barcin,da sallamarta ta shiga,tana shiga ta cire alkyabbar taƙarasa bakin gadon cikin takunta me ɗaukar hankali. Shiko Ayman kallo yabita dashi,sannu a hankali hotunan abubuwan dasuka faru a baya yadunga dawowa kwakwalwarshi,ba abinda be tuna ba game da alaƙarshi da ƴarfillo,da keta haddin da yayiwa fiddah a germany duk ya tuno. Dafashi fiddah tayi,cikin sassanyar murya tace. "long time no seen,any way you are highly wellcome"ta faɗi gami da rungumoshi jikinta. ga mamakinta se ji tayi shima ya rungumeta,ya raɗa mata,"thanks you baby"a kunne. ƙara rungumeta yayi yaci gaba da cewa. "Nasan na cutar dake da yawa,amman bansan dalilin dayasa namiki abinda namiki a germany ba,don Allah ki yafemin nagane kuskurena ki gafarceni,hakan baze ƙara faruwaba". Wayyo daɗi fiddah ji tayi duniyar tamata kaɗan sabida girman da kanta ya ƙara yi. cike da shagwaɓa tace,"ya wuce bakomai,me martaba yamana bayanin matsalarka,Allah yakyauta gaba ya ƙara tsarewa". "matsalata kuma?to meyace yana damuna kuma keda wa yayiwa bayanin?"ya faɗi yana jan hancinta. dariya tayi sannan tace. "yace Aljanune suka shigeka,kuma nida bazawarar amaryarka me ɗanyen goyo yamana bayani"ta ƙarasa zancan cikin dariya. murmushin takaici yayi sannan yace. "Nidama yanzu nake mamakin alaƙata da ƴarfillo,ashe da aljanu ta haɗani,to wlh sena nuna mata nima aljanine"ya ƙarasa maganar yana huci kamar tana gabanshi. Fiddah cigaba tayi da mishi kissa da kisisina,shiko hankalinshi ba akanta yakeba tunaninshi taina ze fara neman hayatinsa,da kuma kalar hukuncin dazeyiwa ƴarfillo. Fiddah ce ta katseshi da cewa, "ya kamata kazo muje ku gaisa da amaryar taka"ta ƙarasa maganar tana dariya. "Don Allah kidena yimin wannan zancan,inma zaa ƙaramin aure,se arasa wacce zaa auramin se bazawara,yaushe farashina yayi faɗuwar da har bazawara,zata iya samuna a matsayin miji,?gaskiya Abba be kyautaminba yabarni naji dake ma mana"ya ƙarasa zancan yana miƙewa. Takalmi yasa yafice daga ɗakin,kai tsaye ɓangaran iyayanshi ya nufa,yana shiga yaci karo da Abu Ayman,zaune cikin kekenshi na yara yana wasanshi,ya gunguro zuwa bakin ƙofar. Gaban Ayman ne yayi mummunar bugawa lokacin da idonsa ya sauka akan yaron. muje zuwa surbajon kuce. [8/4, 09:48] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITER ASSOCIATION *Page 95-96* Abu Ayman na ganinshi yafara miƙa hannu,alamar ya ɗaukeshi,yana ta tsillo nason zuwa gurin Ayman ɗin. Jiki a sanyaye Ayman yaje ya ɗaukeshi,ya ƙarasa dashi cikin falon inda ya sami iyayansa zaune suna hira. Sunyi mamakin ganin shi ɗauke da yaron amman se suka kauda hakan a fuskokinsu. Guri yasamu ya zauna yagaishesu yakuma nemi gafarar su abisa abinda yadunga musu,yafe mishi duka sukayi gamida yimass jajen Allah ya kyauta gaba. Hira ake amman shi hankalinshi nakan Abu Ayman dake ta wasansa a jikinsa hankali kwance.yaron ya shiga ranshi,sosoi,shi inba idonshi ne yake masa ƙarya ba gani yakw ma kamar shida yaron suna kama,kode yaron ɗaya daga cikin yayyan shine. "Hajiya wannan yaron waye kyakkyawa dashi haka?kuma gashi bashi da kuiya"Ayman ya tambaya. "Ayya yaron amaryar kane"hajiya babba tabashi amsa. Shuru Ayman yayi yana nazari zuwa can yace. "to amman hajiya fisabilillahi,taya Abba ze auramin bazawara me ɗanyan goyo kamar wannan?ay koda dolene se an auramin ita yakamata ajira ta yaye yaron ko ba hakaba?"ya faɗi cikin damuwa. Dariya dukansu sukayi kana daga bisani mahaifiyarshi tace. "Raayin hakan Abban naka yayi sede in ka isa da kanka se kasaketa,tunda baa kyauta makaba". "Allah ya baku haƙuri ni ba haka nake nufiba"Ayman ya faɗi gamida miƙewa ya ajiye Abu Ayman ya juya ze fuce. Ayko Abu Ayman kuka yasa yana miƙa hannu alamar ze bishi,mamaki ne yakama su hajiya,Ayman shima yayi mamakin hakan haka ya juyo ya ɗaukeshi ya fice dashi zuwa fada. koda suka isa fada nan fadawa sukai ta kwasar gaisuwa,sarki dubansu yake cikin matsanancin farin ciki,nanma Ayman yafiyar sarkin ya nema sannan ya shaida masa yanason gobe ze wuce Abuja da sassafe. fatan Alkhairi sarki ya masa,yakuma gargaɗeshi akan yayi adalci tsakanin matan shi yaji tsoron Allah,kuma inze yankewa ƴarfillo hukunci shima ya tuno Allah,sannan yasa wani bafade ya nuna masa ɓangaran da matan nasa suke,godiya Ayman yayi sosai. miƙewa yayi yabi bafadan abaya zuwa part ɗin matan nasa,suna zuwa bafadan ya juya shi kuma yashiga ɗauke da Abu Ayman a kafaɗarsa wanda yayi bacci. Bin gurin yayi da kallo ba laifi yanayin gurin ya burgeshi,falon ya shiga da sallamarshi ba kowa a falon dan haka guri yasamu ya zauna yana daddanna wayarshi. saƙwannin ƴarfillo yake dubawa sabida ta kirashi be ɗaukaba,shine ta turo mishi saƙon ze dawone ya haɗu da ita.ranshi ne ya ɓaci da ganin saƙon. yana nan zaune har yagaji da zama ba wacce ta fito se maaikata keta faman zuwa suna kwasar gaisuwa. miƙewa yayi yabi wata hanya wacce yake tunanin hanyar ɗakice dan baze iya cewa ƴan aikin su nuna masa ba. tafe yake har ya ƙaraso ƙofar ɗakin turawa yayi ya shiga,fiddah ya samu zaune kuyanginta na matsa mata ƙafa. Da sauri kuyangin suka fice guri yasamu yazauna yana kallonta ita ko,se harara take jefo masa dan fushi take dashi akan abinda ya faɗa mata ɗazu. ya gano hakan dan haka murmushi yayi yace. "gimbiyata fushi ake da yariman ne?to ayi haƙuri tuba nake a ɗan saki fuskar Kar ruwan sama ya sauko". Dariyace ta ƙwacewa fiddah wacce bata shiryaba sannan tace. "shine kamin kazo gurina kafara zuwa gurin bazawarar ka ko?,bayan nice yadace kafara zuwa gurina" Hancinta yaja yana murmushi yace. "Wayace miki naje gurinta?" "se an faɗamin bayan ga yaron tanan a hannunka"ta bashi amsa tana turo baki gaba. Dariya yayi sannan yace. "toni banjeba acikin gida naganshi yasa kuka sena ɗaukeshi to na ɗaukeshi shine kuma yayi bacci,ni amshe shi ma ki kaimata shi naga garin a hadari tasa mishi rigar sanyi".yafaɗi yana miƙa mata shi Wata uwar harara ta wurga masa sannan tace. "tabɗijan dan raini kawai ita bata taɓa zuwa gurina ba bayan nice babba dan yada kai se inkama infara zuwa gurinta wlh bazan jeba". "To ba se kinmin rashin kunyaba niba matsalatabace Wannan tsakaninku,yanzu de haɗamin ruwan wanka bari nakaishi na dawo kimin wankan"ya faɗi yana shafo fuskarta. Murmushi tayi gami da miƙewa ta nufi toilet domin haɗa masa ruwan. ficewa yayi Yana duban inda zebi daze sada shi da ɗakin amaryar tasa. Sannu a hankali har ya iso bakin ƙofar dayake tunanin nanne ɗakin. taku har kullum surbajo. [8/4, 12:23] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 97-98* Tura ƙofar yayi ya shiga da sallamarsa. A firgice ummu tamiƙe daga gaban mirror tana binshi da kallo tana ja da baya. Shima binta yayi da ido na mamakin abinda yasa ta miƙe a firgice haka,kamar mara gaskiya. Batare da damuwar komaiba yaje ya kwantar da Abu ayman akan gadon shi,sannan ya juyo gareta. Guri ya samu ya zauna yana binta da ido itako se zaro ido take kamar mara gaskiya jikinta se rawa yakeyi. "wannan rawar da jikinki yakeyi na lafiyane kuwa kode bakida gaskiyane?"ayman yatambaya yana bin ɗakin da kallo. Kai ta girgiza jikin nata na cigaba da rawa. Murmushi yayi yace. "kode dan angon naki,beyi miki shigowar da kowanne ango yakeyi bane?". Namma girgiza kai tayi,miƙewa yayi yace. "Any way dama ba wani abune ya kawoniba yaro na kawo miki,pls kisa masa kayan sanyi garin akwai hadari kar sanyi ya shigeshi,kum ki kashe Ac dake ɗakinnan,dan mura take sasu,nabarki lafiya"yana kaiwa nan yafice daga ɗakin. Da gudu ummu tabi bayanshi takulle ƙofar da mukulli ta jingina bayanta a jikin ƙofar tana haki,cike da mamakin ganin Ayman,ba abinda yafi bata mamaki kamar yadda ya nuna be santa ba,hannu takai kan fuskarta,dan share gumin daya karyo mata,jin abinda ke fuskrta ne yasa ta nufi gaban mirror da gudu tana ƙarewa kanta kallo. marks ɗinnanne baƙi da ake shafawa afuska domin cire gashin fuska da duk wani dattin,fuska shine a fuskar tata hasalima ta gama shafashi kenan Ayman ɗin ya shigo,shiyasa be gane taba. Godiya tayiwa Allah daya rufa mata Asiri,wato Ayman shine mijin data aura kenan,danƙari lalle dole ya saketa dan bazata zauna da mayaudariba,kuma mugu,lalle da sake. kwanciya tayi akan gado tana ta tunanin ta inda zata ɓullowa lamarin,inda ta tsayar da shawarar cigaba da rufe fuskarta gareshi da wannan marks ɗin har zuwa sanda ta shirya barin gidan,dan ba abinda zes ta zauna dashi,se yanzu tagano abinda yasa sarki kuka sanda take bashi labarinta,da dalilin dayasa kowa na gidan yakeson Ɗanta,ashe dan sun san ɗan jininsu ne shiyasa. Shiko Ayman yana fita ɗakin fiddah ya koma,wankan suka shiga tare kamar yadda ya buƙata ita ta taimaka masa yayi wankan suka fito suka shirya,sannan suka fito domin cin Abinci. Ummu ma ta fito sede still fuskarta shafe da marks haka suka ci abincin Ayman da fiddah se soyewarsu sukeyi agabanta basu damu da ita ba,dan ko kallon inda take Ayman beyiba,amman ya rasa dalili ɗazu daya shiga ɗakinta bugun zuciyarshi ya ƙaru haka yanzu ma da take zaune a gurin,wanda bayajin hakan sede idan hayatinsa ce a gurin. Haka suka gama cin abincin kowa yamiƙe yabar gurin,ummu ce tafara miƙewa,A firgice Ayman yake kallon tafiyarta,wanda inde ba gizo idonsa yake masa ba irin tafiyar hatinsa kenan. fiddah ce tajanye hankalinshi ta hanyar tsayawa agabanshi,miƙewa yayi suka wuce ɗakinta. *Zuciyarshi ta gaza natsuwa game da Amaryar tashi,meyasa ta shafa abu a fuskarta,?meyasa ta ruɗe da ta ganni? meyasa taƙi yimin magana? meyasa tafiyarta ke iri ɗaya data hayati?meyasa ɗanta yake kama dani?meyasa mahaifina ya zaɓamin ita amatsayin mata,?wacece ita?meye sunanta?ƴar waye ita?daga wanne gari take?in bazawarace meya rabota da gidan mijinta shi aka ƙaƙaba masa?*. Wainnan sune tarin tambayoyin da Ayman yakewa zuciyarshi wanda amsarsu sede ita amaryar ce kawai take da amsarsu,sawa yayi aranshi in yadawo daga Abuja ze titsiyeta akan dole ta amsa masa su. Ranar shida fiddah ankwashi soyayya fiddah jinta take awata nahiya ta daban,sosai taji daɗin lamarin. Washe gari da sassafe yakama hanyar Abuja,ysna isa gida ƴarfillo yasamu tana shaƙatawa da wani ƙato acikin gidan dan batayi tsammanin dawowarsa ranar ba dan ds taji shuru ta ɗsuka a kurkuku sarki yasake sashi. Gora ya ɗauka ya shiga yimusu rotse,da gudu kwarton yafice da wandonsa a hannu,inda Ayman yaci gaba da shirgar ƴarfillo,dsga ƙarshe,tarugu yaɗauko a kitchen ya fasashi ya tura mata a gabanta can ciki,sannan yaci gaba da dukanta yana laantar ta gamida furta kalmar saki wanda basu da iyaka. Tuni ƴarfillo tajima da sumewa,sojoji yakira yace sukaita gard room se ya nemeta. koda aka fice da ƴarfillon kuka ya rushe dashi asakamakon shiga ɗakin da ummu take ada dayayi,wanda tunda suka dawo dags germany be shigaba,hotonta yagani,maƙale a bango tana dariya,ciroshi yayi ya rungume yana ci gaba da kuka,zaninta yagani na atamfa shima akan gado wanda yayi imani mancewa tayi dashi,ɗaukarshi yayi yarungume yana kuka. Ranar har cikin dare yana yawatawa agarin Abuja neman ummu amman ba ita ba alamarta haka ya haƙura yakoma gida. . Wasa wasa seda ya kwashe tsawon watanni uku a Abuja yana neman ummu amman bata ba alamarta gaba ɗaya ya susuce yafice hayyacinshi,kuka yayishi ba iyaka,kullum cikin tubarwa Allah yake abisa abubuwan daya aykata tare da neman taimakon Allah Akan ya bayyana masa ummu a duk inda take. Ƴarfillo kuwa,ashe dukan da Ayman yamata da wanda yasa ska mata a gard room yayi sanadin,karyewar ƙafafunta duka biyu,kuma gashi baa gyaraba har seda suka ruɓe dan,Ayman ya mance da ita koda sojojin suka kirashi suka masa bayanin abinda ke faruwa cewa yayi su fitar daita su yardar,Ayko haka sukayi bakin titi sukaje suka yarda ita ,anan tasamu wani yataimaketa yakaita asibiti aka yanke ƙafafuwan dan sunriga dasun ruɓe,duk abinda ta mallaks seda ys ƙare akan ƙafar,daga ƙarshe dole ta haƙura ta amshi keken guragu tafara bara abakin titi. Yau Ayman ya yi niyyar zuwa kano dan haka da wuri yatafi.ta jirgi wanda befi 40 minutes ba ya isa kano. Da safe ya iso dan ko ƴan gidan basu farkaba,kuma aƙaida a ɗakin ummu ze sauka,dan haka can yanufa,cikin saa ya tura ƙofar a buɗe take,gs mamakinsa bacci take amman still fuskarta shafe da wannan baƙin abun. be damuba,tashinta yayi abaccin miƙewa tayi tana kallonshi,gaba ɗaya yayi baƙi ya rame,tausayinshi ne ya kamata,cigabs tayi da binshi da ido shima ƙureta yayi da ido cike da mamakin yadda kwayar idonta ke iri ɗaya da hayatinsa. dakyar suka ɗauke ido akan juna,kayan hannun shi ya ajiye akan gadon sannan yanufi gadon Abu ayman wanda farkawarshi kenan yana so yayi kuka. Ummu bin kayan daya ajiye tayi da ido,hotontane da zaninta,seɗan wani pream daya rubuta. *Hayati where are you please,?don Allah kizo gareni dake da abinda kika haifa,ina sonku da zuciyata da ruhina,gab nake da haukacewa akan rashinki,na nemeki har yanzu akan nemanki nake bangankiba,nasan kina fushi dani, bayin kaina bane aljanune suka shiga tsakanina dake kigafarceni* abinda taga ya rubuta kenan se ɗan ƙaramin hotonta da yasa atsakiyar rubutun. So da ƙaunarshi da tausayinshine suka dawo sababbi acikin zuciyarta,zama tayi ragwab riƙe da pream ɗin tana kuka. Sautin kukan tane yadawo da hankalin Ayman kanta,ƙarasowa yayi gurinta ganin pream ɗin a hannunta ne yasa ya ɗauka haushin abinda taganine yake sata kuka.ji yayi shims yana kukan cikin kuka yace. "inhar wannan kukan naki na kishi nane to hakan ya gwada kina sona ,to inde da gaske kina sona dole kiso abinda nakeso wato wannan ta jikin hotonnan,ina sonta bazan ɓoye miki ba itace rayuwa da zuciyata,ina rayuwane da soyayyarta,duka mata mazane idan ina tare da ita,inamata son dani kaina bansan yawan shiba,da sonta nake ji nake gani nake magana,nake tafiya,gab nake da rasa rayuwata asakamakon rasata da nayi,bazan iya rayuwa babu ita ba,pls kitayani da addua Allah yaba hayati haƙuri ta dawo gareni dan wlh inba hayati a rayuwata ku kanku bazakuji daɗin zama dani ba sabida alfarmarta kuke ci"yaƙarasa maganar yana kuka sosai kamar wani yaro, kuka sosai ummu takeyi,Ajiye Abu ayman yayi ya juya ze fice,da sauri ummu ta ruƙo rigarshi,waigowa yayi yana kallonta da gudu ta ƙarasa jikinshi ta rungumeshi tana faɗin. "am here qurratu ayni,am realy sorry,i dont mean to hot you". muje zuwa Surbajon kuce. *duk wanda yaji daɗin page ɗinnan sharhi zeyi inyatashi comments bawai ace thanks ba😎* [8/5, 09:59] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 99-100* A tsorace yake kallonta,tabbas muryar ta hayatinsa ce to amman fuskar fa? Hannunshi na rawa ya ɗago da kanta daga ƙirjinshi yafara bare abun da ta shafan har ya cire shi duka fuskarta ta bayyana. "YA ALLAH!!KAINE SARKIN DAKE MULKI BATARE DA FADAWA KO ƳAN MAJALISUBA,KAINE KAKEYIN ABINDA KASO ASANDA KASO AKAN WANDA KASO BATARE DA SHAYIBA,SARKIN SARAKUNA ME DUNIYA DA LAHIRA DA ABINDA KE CIKINSU,TSARKI YA TABBATA AGAREKA,TSIRA DA AMINCI KA ƘARASU GA SHUGABAN HALITTA ANNABI MUHAMMAD S,A,W"wannan shine kalaman dake fita abaki Ayman runguma yayiwa ummu kamar ze maida ita ciki dan ji yake kamar zaa kwace masa ita. Kuka suke dukansu rungume da juna sun kasa magana,da kyar ummu tasamu ta tsaida nata kukan sannan tafara share hawayenshi,shiko beda shirin denawa. Janshi tayi zuwa bakin gado suka zauna,sannu a hankali yafara tsagaita kukan amman har yanzu riƙe yake daita yaƙi saki. "Hayati ina kika shiga tsawon wannan lokacin?inni ban neme kiba hayati me ya hanaki nemana? ko kina fushi danine?hayati ina cikin jikin ki Allah de yasa ba zubar min kikayiba,ya akayi kika zama mata agareni bayan ni inacan inata nemanki,?". Kwashe duk abinda yafaru tayi tasanar dashi sannn ta ƙara da cewa. "dan haka ga ɗanka can yana kallonka"ta nuna Abu Ayman Da sauri Ayman yaje yaɗauke shi yana kuka yana shafa kan yaron cikin kuka yace. "ina sonka ɗana,ko duka duniya zasu ƙika ni ina sonka,Allah ne yabani kai lokacin da banyi zato ba,nagodema Allah daya bani kai nagode"ya ƙarasa maganar cikin kuka. yafiyae ummu ya nema itama ta nemi nashi duka suka yafewa juna. Labarin hukuncin da yayiwa ƴarfillo yabata cikin kuka tace. "is wrong,qurratu ayni,bata cancanci hakaba,bata cancantaba,duk abinda tamaka dan tana sonka ne wanda kasani so aminin shaiɗanne,yakamata kafi kowa sanin haka,duba da abinda mu muka aykata,mu waye ya hukuntamu,Allah ne ya hukuntamu dakanshi meyasa ita baka bari Allah yamata hukuncin ba,in baka saniba zan faɗa maka har gobe ƴarfillo uwatace,babu wani yanayi ko halinta daze canja hakan,inasonta fiye da tunaninka sabida tamin rana,wanda da badan ita da ikon Allah ba da Allah kaɗai yasan halin dazan faɗa,dan haka baka kyauta minba"ta ƙarasa cikin kuka. Rarrashinta yashiga yi yana bata haƙuri,dakyar ta haƙura,suka shiga tsokanar juna shida ita. kamota yayi ya ɗorata akan cinyarshi,yana shinshina wuyanta,miƙewa tayi zata gudu kamota yasake yi,yana shafa marar ta,yace cikin kunnenta. "Hayati me kika tanadarmin anan ne"ya ƙara mats marar tata. kunyace takama ummu da sauri ta miƙe zata gudu sake ruƙota yayi,ita kuma ta cusa kanta a ƙirjinshi,dariya yayi yace. "ok to nagane wato sede inna shigane zan ji komai ko?"ya ɗaga mata gira duka takaimishi a ƙirji ta kwace kanta ta shige toilet domin tayi wanka. miƙewa yayi ya rage kayan jikinshi shima ya shige toilet ɗin. lokacin ummu ta gama tuɓe kayanta,ganinshine yasa ta faɗa cikin kwamin wankan ta rufe fuskarta faɗi take. "Don Allah kafita haba qurratu ayni,wannan ay rashin kunyane"taƙarasa maganar kamar zatayi kuka. Dariya zancan nata ya bashi,me makon yabata amsa ƙarasa cire kayan shi yayi ya shige cikin kwamin. Ummu sejin hannunshi tayi yana shafo ƙirjinta cikin salon da bazata iya kwatantawaba. Ture hannun nashi tashiga yi tana ƙoƙarin gudu amman ina Ayman be bata dama ba memakon ma ya ɗauke hannun nashi sema bakinshi dayake ƙoƙarin kaiwa kan na shanunta.kuka ummu tasa mishi tana faɗin. "Don Allah kadena wlh bana so ni kadena". Kashe mata ido yayi yana binta da kallo,kai da ganin yanayin idonshi kasan ya kamu,da kyar yafurta. "Hayati in ni kuma ina sofa,bazaki iya yimin abinda nake soba kenan?" Shuru tayi ta kasa magana,runtse ido tayi tanajinshi yana gama jagwalgwalata. Da ƙyar Ayman ya barta sukayi wankan sannan ya naɗota a tawul ya ɗauko ta ya fito da ita. da kanshi ya shiryata sannan shima ya shirya,tare suka yiwa Abu Ayman wanka cikin so da ƙaunar juna,suka shirya shi sannan suka fito zuwa dinning domin karyawa. Ayman ɗauke da Abu Ayman,yayinda ya saƙalo hannunshi ya riƙo ƙugun ummu,ahaka suka nufi dinning inda fiddah ke zaune tana zaman jiran fitowar ummu domin batasan Ayman yadawoba. A gigice tamiƙe tana kallonsu,jikinta na rawa suko basu san tana kallon suba,dan ko gabansu basa kallo junansu kawai suke kallo cikin yanayi naso da ƙaunar juna suna musayar kalamai. Sabida rawar da jikin fiddah yakeyi har ture flaks ɗin ruwan tea tayi bata saniba. Ƙarar faɗuwar flaƙs ɗinne yasa su Ayman maida hankalinsu gurin. muje zuwa surbajon kuce. [8/5, 20:26] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 101-102* Har suka ƙaraso gurinta kallonsu take cike da mamaki. Bakinta na rawa tace. "yaushe ka dawo ni ban saniba?kuma wanne irin sabon wulaƙancine wannan,dahar kake rawar ƙafa akan wannan bazawarar me ɗanyan goyon?". Murmushi Ayman yayi yasake gyarawa Abu ayman kwanciya,ya shafo gefen fuskar ummu ya kashe mata ido sannan yace. "Ɗazu da sassafe na shigo,sanin a ƙaidance itace da girki ne yasa nashiga ɗakinta,ko kaɗan ba wulaƙancibane,sede yanzu ne kike so na gwada miki wulaƙancin idan bakinki ya sake kiran hayati da bazawara,koda yake ba laifinki bane rashin sanin wacece ita agareni shi ya janyo kike cemata hakan,to ki saurara dakyau kiji,Hayati itace,my first and last love,akanta aurena dake na farko ya lalace, taƙaice de kamar yadda kunnenki yaji sunan dana kirata dashi Hayati itace rayuwata inba ita ni ba komai bane,wannan ɗa kuma da kike gani ɗana ne nida ita wanda ƙaddara ta faɗa mana muka samar dashi bata hanyar aureba,ina fatan kingane matsyinta a gurina". Wata uwar shewa fiddah tayi sannan tace. "Allah nawa,wato yanzu har Allah yakaimu lokacin da zaayi zina a haihu amaida hakan kaddara?matsayinta kuma nagane sosai,dama ay ko ba akanka ba duk inda mazinaci yake karuwarsa tafi matarsa ta sunnah matsayi agurinsa,ba se ka wahal da kanka gurin yimin dogon turanci ba simple kawai kace dadiro tace ada zanfi ganewa". Kamin ta rufe bakinta ya ɗauketa da mari,wanda ya haddasa mata kifewa agurin,sannan yace cikin matsanancin fushin da be taɓa yiba. "Lalle ke jahilace, ace miki ƙaddara har kina da ja game da hakan?any way kin faɗi gaskiya,tabbas ummu koda hakan tashiga tsakanina daita,tafiki daraja agurina nesa ba kusaba,kuma dadiro da kika kirata,ay baa ajiye dadiro se ka gamsu da test,da ƙirar halittarta,wanda akasarai seka duba kaga abinda tafi matar taka dashi sannan kake ajiyewa,ki dubeta da kyau ba abinda bata fiki dashi ba nafili dana baɗini,duk da bata hanyar aure nafara saninta ba,wanda nasan kaddara tace to ina me shaida miki,babu mace kamarta,ina alfahari dakasancewarta matata,kisa aranki har abada darajarki bazata kamo darajar takalminta agurina ba tunda baki da mutunci". Daga ummu har fiddah kuka suke,ummu taji zafin maganganun fiddah ita kuma fiddah maganganun Ayman ne ke tafasa zuciyarta,tayi danasanin furucin da tayi,dama hausaw sunce in baki yasan abinda ze faɗa besan abinda zaa mayar masa ba. Ayman jan ummunsa yayi kan dinning ɗin yazuba abincin yadunga bata abaki hartaci ta ƙoshi,sannan shima yaci suka tashi sukabar gurin inda fiddah ke zube tan ta risgar kuka. Alkyabba ummu tasa suka nufi gurin me martaba ita da Ayman,d ɗansu. me martaba tunda ya hangosu bakinshi yaƙi rufuwa dan yasan ko baa faɗa masa ba sun gano junansu. waazi yamusu sosai gamida neman yafiyarsu abisa abinda yamusu,yafemishi sukayi,daganan suka wuce cikin gida gurin iyaye mata,anan suka jima anata hira,se azahar suka koma ɓangaran su. basuga fiddah ba kum basu nemin sanin inda takeba suka ci gaba da alamuransu. Ummu se gudun zama kusa da Ayman takeyi dan taga take takensa,koda dare yayi duk a tsorace take dashi,sata yayi tayo alwala sukayi sallah rakaa biyu domin nuna godiyarsu ga Allah,bayan sun idarne,taga yafita ba jimawa yadawo ɗauke da ledoji guda biyu. Kajine lafiyayyu,da madara sassanya,haka yadnga bata a baki har seda ta ƙoshi shima yaci,wanka tashiga binta yayi kamar ɗazu seda yagama jagwalgwalata yabarta suka fito koda suka fito ummu naƙoƙarin zuwa gaban mudubi domin tashafa mai amman ina se jinta tayi anɗauketa cak baa ajiyeta akoina ba se akan gado. "jan ajin ya isa haka,hayati,tunda safe miyauna yagama tsinkewa,amman naga ke ko ajikinki"ya raɗa mata akunne sanda yake ƙoƙarin jan bargo ya rufesu. "Don Allah kabarni insa kaya ko fant fa babu ajikina,ni wlh ban iya bacci da tawul ba pls kabarni nasa kaya"tayi maganar tana shirin yimasa kuka. Hannu yasa ya shafo ƙasan nata cikin wani salo wanda seda numfashinta ya tsaya na wucin gadi,sannan ya ƙara yin ƙasa da murya yace. "Hayati wanne irin fant kuma kina tare dani,toni bari kiji wlh sa fant ɗin danma yazama dolene da wallahi sena haramta miki sashi,danni bani da wanda nake kishi dashi kamar ganin fant a manne da alƙaryata,sam banason ganinki dashi matuƙar kina tare dani". Turo baki tayi gaba cikin shagwaɓa tace. "wlh baze yiwu in zauna ba fant ba salon inje watarana inyi wawan zama a gabanka kamin dariya ko?". ƙara matsarta yayi yana ƙoƙarin kwance tawul ɗin yace. "waya faɗa miki mace na wawan zama agaban mijinta?in baki sani ba bari infaɗa miki ayshi wawan zaman mace a gaban mijinta sunan shi,come inside am ready so kinga,ay rage hanyane,dan haka nide na faɗa miki duk randa naga fant ajikin ki kina tare dani nida kene"ya faɗi yana ƙarasa kwance tawul ɗin. Tun daga kan tafin ƙafarta yafara kissing ɗinta har zuwa sanda yazo headquater,tunda ya kafa bakinshi agurin be cireba seda yaga ummu daɗi nashirin sata suma sannan ya dena ya haura sama zuwa branch office,wasa yashigayi dasu cikin salon da ummu bazata iya jurewa ba,ganin yadda take kamoshi,ga kuma uban ruwa datake zubarwa ne yasa yagane ta ƙosa yayi signing,dan haya be ɓata lokaci ba gurin cika mata quantainer da kaya,wanda dama already tana bakin tekun dan haka acikin jirgi aka auno ta zuwa ƙasar da gwauro ko gwauruwa masu tsoron Allah basa zuwa. muje zuwa Surbajon kuce. [8/7, 07:32] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 103-104* Kai jamaa abunfa bana wasa bane,ina daga waje nace wato ba iya Anwar ɗin ilham ne yake kukaba,dan ga Ayman ɗin ummu nan ma shima ya taƙarƙare yana zunduma ihunshi son ranshi. Basu gama signing papers ɗinba se gefin asuba,ummu duk ta gaji,se kukan shagwaɓa take masa. Jawota yayi ya rungume ya tsuramata ido,cike da mamaki akan fuskarshi,da ace bashi da kanshi yafara kusantar ummu ba labari aka bashi, dase yace ƙarya ake mata,dan shide jinta yayi ya ɓare sabuwa a leda,ga wata niima wacce shi be taɓa sanin ana samun irinta a duniya ba. Abunda Ayman be saniba shine,ummu tana cikin jinsin matannan da ake ce musu mace me mukulli,wainda su nauin halittarsu duk lokacin da namiji yazo kusantarsu,a sababbi ze jisu,dan bayan angama saduwa dasu gurin na komawa ya haɗe,shiyasa ake cemusu me mukulli,basu da yawa acikin al umma,se wacce Allah ya zaɓa yake yinta a haka. Ayman rarrashinta yashiga yi yana samata albarka,itako se ƙara narke masa takeyi. Ruwan wanka yaje ya haɗa musu sannan ya dawo ya ɗauketa suka shiga wankan,ya rigata fitowa dan haka canja musu zanin gado yayi,dan wancan inmutu be lura da abinda yake kaiba,ze ɗauka fitsarin kwance ɗaya daga cikinsu ya shimfiɗa akan gadon. Komawa toilet ɗin yayi ya ɗaukota suka kwanta,rungume da juna,Ayman son ummu ne ya ƙaru azuciyar shi,sonta na ƙaruwa a ranshi ne aduk wani lokaci da zuciyarshi ya buga,yabata wani matsayi na musamman a zuciyarshi. Washe gari tare sukai wanka,sukayiwa Abu Ayman,suka shirya,suka nufi dining,yau ba fiddah,bata fitoba dan haka cin abincinsu sukayi sannan ummu tawuce ɗakinta shi kuma Ayman yanufi ɗakin fiddah domin duba lafiyarta. Koda ya shiga ɗakin a kwance yasameta tana chatting hankalinta kwance,kamar ba abinda yake damunta. Gaisheshi tayi wanda yayi mamaki matuƙa da tayi hakan dan yasanta sarai,in sarautar ta motsa ko kallo be isheta ba. "pricess me ya hanaki fitowa cin abinci jiya da yanzu?"Ayman ya tambaya. Murmushi tayi sannan tace. "Ay ba,se ka tambayeniba ya kamata ka nemo amsar da kanka,amman tunda ka tambaya zan baka amsa,abinda yasa kaga ban fitoba ba komai bane illah kawai banaso ina zuwa inda bani da darajar da takai ta takalmi,inda aka ɗaukeni ɗaya da ɗa namiji sabida rashin amfanina,shine kawai yasa banjeba"ta ƙarasa maganar cikin murmushi. Se yanzu Ayman yaji kunyar kalaman daya faɗa mata,wanda yasan de itace bata da gaskiya,amman kalaman sunyi tsauri da yawa ga duk wani adalin miji,be kamata yayi suba. ƙarasawa yayi kan gadon da take,jawota yayi ya rungume yana shinshina wuyanta,har ya iso bakinta inta ya zira harshenshi aciki,yana jujjuyawa,cafkewa fiddah tayi suka shiga kissing ɗin juna,yayinda hannun Ayman kuma ke murza na shanunta,cikin salo da kwarewa. Seda yaga suna shirin yankar visa ne yasa ya kyaleta,ya rungumota jikinshi ya raɗa mata a kunne. "Baby am really sorry for everything". Murmushi fiddah tayi ta ƙara cusa kanta a ƙirjinshi,sun ɗauki lokaci mw tsayi sannan yamata sallama ya fice daga ɗakin,ɗakin ummu ya koma koda ya shiga isketa yayi kwance tana bacci sabida jiya bata samu bacciba,se Abu ayman dake gefenta idonshi biyu yanata wasa da ƙafarshi. Lulluɓeta yayi da bargo ya kunna mata Ac,sannan ya ɗauki Abu ayman suka fice zuwa fada,domin gaida me martaba. itako fiddah ba komai ne yasa bata nuna ɓacin ranta ba,illah wayar da sukayi da aminiyarta salmab,wacce itace tabata shawara akan karta sake ta nuna taji haushi,inda tamata albishir akan jibi zatazo kanon,dan yanzu haka tana Abuja gidan kawunta. Sosai fiddah taji daɗin ziyarar da ƙawar tata zata kawo mata,wannan shine dalilin daya hana fiddah nuna ɓacin ranta. Ayman tarasu yayi yamusu nasiha kan su zauna lafiya,inda ya raba musu kwanan girki inde yazo kano wato kwana ɗaɗɗaya,sannan ya ƙara da cewa inze tafi Abuja ze dunga tafiya da ɗaya acikinsu,in yadawo ze dawo da ita ya ɗauki ɗayar,dukansu sunyi amanna da hakan. me martaba dakanshi yayiwa ciroma da umman ummu bayani akan abunda yafaru tsakanin ummu da Ayman,dukansu sunyi mamaki,inda ciroma yaɗau zafi akan dole se an hukunta Ayman,dakyar umma tashawo kanshi ya haƙura suka ɗauki hakan a mazaunin ƙaddara. Yau take Sallah. amman a gurin fiddah domin kuw yau ƙawarta Aminiyarta salmab jb lagos ta dira acikin gidanta tsakiyar ɗakinta. Muje zuwa surbajon kuce. [8/7, 08:29] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *Page 105-106* Ihu fiddah take na murnar ganin salmab,nan tashiga hidima da ita,seda salmab taci tayi kat sannan suka fara tattaunawa game da matsalarsu. Shi kuma Ayman yau da daddare ze koma Abuja kuma da fiddah ze tafi hakanne yasa yanufi ɗakinta domin shaida mata ta shirya kayanta,zasu tafi Abuja anjima,zuwanshi ƙofar ɗakin yayi daidai da sanda fiddah take cewa. "Salmab nafa tsorata da sake yiwa Ayman Asiri,kina ganin wancanma damuka masa na ƙarin ƙarfin shaawa,ƙarshefa ɓigewa yayi da neman mata,ni bansamu biyan buƙata ba,dan haka nide kibar wannan zancan,damade na mallaka kikace to da sena amince". Salmab shewa tayi sannan tace. "Shifa matsoraci ako ina yake baya suna,kicire tsoron Ayman aranki,ki fuskanci hanyar da zaki bi kiyi maganin matsalarki,shine kawai,amman bawai ki tsaya namiji yana gasa miki magana ba". Ayman dake waje jikinshine yakama rawa hawaye na fita akan idonshi,ashe duk wannan zinar dayay ta aykatawa fiddah da ƙawartane sila,sune suka masa asirin da be ita haƙuri se ya kusanci mace,zuciyarshi ke tafasa sabida ɓacin rai,juyawa yayi yaje ɗakinshi ya ɗauko belt ya koma ɗakin. Da ƙarfi ya tokari ƙofar ta buɗe,a razane salmab da fiddah suka miƙe suna kallonsa. "Kun cuceni amman kanku kuka cuta baniba,kunsa na samar da ɗa ta hanyar zina adalilin mugun asirinku to wlh ban yafe muku ba har abada,ke kuma fiddah kije nasake ki saki ɗaya". Ihu fiddah ta kwalla tana bashi haƙuri amman ina ko sauraronta beyiba,ya ware iya ƙarfinsa yashiga dukansu da belt ɗin,babu ma kamar salmab dan kamin wani lokaci tuni halittar,bakinta ta sauya,ihu suke suna neman,agaji amman ina ya kulle ƙofar,cigaba yayi da dukansu,tuni saƙmab ta jima ta sakin fitsari ajikinta. Zuwacan Allah yabasu ikon buɗe ƙofar suka fice da gudu,shimako yabisu da gudun yana dukansu,ganin sun rasa me taimakonsu ne yasa suka ruga zuwa fada,shima ko be tsayaba binsu yayi.. Da ƙyar me martaba ya rarrashi Ayman yadena dukansu,sannan ya tambayi abinda yafaru,Ayman duk abinda kunnensa yaji,shi ya faɗawa sarki. Ran sarki in yayi dubu ya ɓaci najin cewa,sune silar gurɓacewar tarbiyyar Ayman,amman se yabar ɓacin ran aransa,inda yaci gaba da ba Ayman haƙuri. Ayman shaida mishi yayi shifa ya saketa kuma be yafe mata ba. Sarki beso sakinba amman tunda anriga anyu beda yadda zeyi. Fiddah tsinewa salmab tashiga yi gamida da nasanin saninta da tayi a rayuwa,gashi tajawo an saketa,ta cuceta,haka suka rabu baram baram Salmab tajuya lagos da kumburar baki,da Allah ya isan Ayman. Tunkamin fiddah ta isa sokoto me martaba yakira mahaifinta yamishi bayanin abinda tayi be ɓoye masa komaiba,mahaifin fiddah mutumne me hankali da fahimta dan haka shima ya goyi bayan hukuncin da Ayman ya yankewa fiddah. koda ta isa gida ta tarar da hukunci agurin mahaifita me tsanani,inda taci gaba da danasanin ƙin bin shawarar ƙawarta jidda,tabiyewa salmab gashi takaita ta baro. Ayman da ummu ya tafi Abuja inda taji daɗin hakan,dan tazo kusa da ummanta. Ummu ko kaɗan bataji daɗin sakin fiddah da Ayman yayiba amman bata da ikon warware sakin,dole ta haƙura ta rungumi mijinta da ɗanta. Yau da wuri Ayman yadawo daga office,kallo ɗaya ummu tamishi tasan da magana,a kitchen yasameta tana girki,hannu yasa yakashe gas ɗin,ya sureta se ɗaki. Wasa yashigayi da ita na fitar hayyaci,seda yagama jagulata sannan yace cikin muryar dake nuna akame yake. "nifa naƙi wayon kullum ni nake tsotse ki amman ke koda wasa baki taɓa gwadawaba da. Haka yau kema inason inga taki ƙwarewar". murmushi ummu tayi,sannan tace aranta,"ashe ko zan baka mamaki". Hannu tasa ta turashi baya ya kwanta,sannan itama,tabishi,hannu tasa acikin.....taciro sandar girma,tafara yimasa tafiyar tsutsa ajikinta da hannunta,tana ɗan sa ɗan yatsa tana ɗan danne bakin famfon,tana matsawa,zuwacan tasa harshe tafara lasowa tundaga kan tagwaye,zuwa sama,kamin daga bisani ta kafa bakinta akai tafara tsotsa. Ayman rasa inda zesa kanshi yayi,dan dadi,gaba ɗaya yafice daga hayyacinshi,ummu miƙewa tayi tahaye ruwan cikinshi,kunsan abun turn by turn ne to yau ummuce da duty,dan haka ita tafara yin signing ɗin yau da kanta,ayman hannu ya miƙa yana wasa da na shanunta,yayi da ita kuma take musu signing,daga ƙarshe kifewa tayi akanshi tasa mishi su abaki yashiga tsotsa. bidiri bireɗe, in ana sallah baa magana, Ummu seda tasa Ayman yayi releasing har so huɗu alokaci guda,wanda koshi dakanshi bayayin hakan,dakyar suka haƙura da juna badan sun gajiba,wanka suka shiga suka fito,Ayman se mamakin ummu yakeyi,wato dama bahaushe yace bar ganin mutum shiru shiru. Tana shirin ficewa daga ɗakin ya jawota ta faɗo jikinshi,ɗan kukan shagwaɓa tasa. "Hayati ya akayi kikasan hanya haka,kinsa Allah na ɗauka befi kijamu daganan zuwa zuba ba kice kin gaji,segashi kinjamu har china,pls meye sirrin?". Dariya tayi ta ɓoye fuskarta ajikinshi sannan tace. "A gurinka na koya,kasan ance magaji mafiyi"tana gama faɗin haka ta ƙwace jikinta ta ruga da gudu zuwa kitchen. Shiko Ayman kan gado yakoma ya kwanta,dan bayajin yau ze iya moruwa dan ummu ta zuƙeshi da yawa🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣Ashe ba daɗi kenan ita kullum se ya zuƙeta. (gareku matan aure ba koyaushe ne zaki bari mijinki yamiki signing ba yakamata kema kidunga yi masa,ta hakane zamu ƙwato mazanmu daga halaka ta neman matan banza,dan da irin wainnan abubuwan matan suke siye zukatan mazajenmu,wanda munsani mazajenmu cokaline su basu da burin daya wuce sujisu a daɗi,dan haka mu kiyaye,inasaka wainnan abubuwanne dan mu ƙaru,agidajan auranmu) taku har kullum surbajo. [8/7, 17:11] Zahra surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀 *UMMU AYMANA* 🎀🎀🎀🎀🎀 Zahra Muhammad Mahmud. DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION *page 107-110* Rayuwa suka ci gaba dayi me kyau da tsabta da nagarta,kowa burgeshi sukeyi. watan Abu ayman Shida,ummu tasamu ciki,hankalinta in yayi dubu yatashi,shiko Ayman munarsa ta gaza ɓoyuwa,ita ko sam hankalinta be kwantaba. Cikin kwanakin Abu ayman yafara rashin lafiya,dan haka suka kaishi Asibiti aka dubashi aka bashi magani,ummu gaba ɗaya hankalinta ba a kwance yakeba game da ciwon na ɗan nata. Kwanan shi biyar da fara ciwon Allah ya amshi abunsa,daga ummu har Ayman,a sume aka kaisu asibiti asakamakon rasuwar ɗan nasu. me martaba kanshi seda hawan jinin shi yatashi asakamakon rasuwar jikan nashi. Da kyar da rarrashi kowa ya dauwama yabarwa Allah ikon sa,amman ummu duk sanda taga wani abu nashi se tayi kuka haka shima Ayman. Ayman ne tatambayi ummu aynihin labarinta,bata ɓoyw mishi komaiba ta faɗa mishi,ranshi iya ɓaci dan haka shiryawa yayi shida ummun da jamian tsaro da umma da ƙanin ummun suka nufi garin gongola domin kamo su jameelu. koda suka isa garin sunyi mamakin ganin gidan a ƙone amman a haka mutanan gidan suke rayuwa acikin shi. Tuni iyayen malam mudi sun jima da rasuwa,se saude wacce suka tarar da ita ta gurgunce asakamakon ciwon suger daya ruɓar da ƙafafun aka yanke,shiko jameelu ƙanjamau ta mishi mummunan kamu,baba shuaibu kuma makancewa yayi,yayinda ko abinda zasuci yafi ƙarfinsu tunda sukayi gobara a gidan. Haka aka tarkato su a motar jamian tsaro suna ta kuka suna neman gafarar su ummu. ummu,da umma seda sukayi kuka na tausayin su sauden,daga gongola,ummu da umma Adamawa suka wuce dangin umman. kowa yayi murna da ganinsu ba kaɗanba,satinsu ɗaya suka wuce Abuja domin sauraran ƙarar da Ayman ya shigar kotu tasu jameelu. Sun halarci kotun inda aka yankewa jameelu hukunci kisa ta hanyar sare kanshi da takobi,ita kuma saude ɗaurin rai da rai,yayinda su baba Hamisu,da shuaibu da furera aka yanke musu zaman gidan kaso na shekara guda ko zaɓin tara dayake basu da komai haka aka tarkatasu prison. namma su ummu se kuka suke. Washe gari aka,zartarwa da jameelu hukuncinsa. Rayuwa taci gaba da tafiya yadda akeso cikin ummu se ƙara girma yake,ummu taga tattali a gurin Ayman ba ɗan kaɗanba,komai shi yske mata,siyayyar haihuwa kuwa dubai yaje ya siyo duk abinda akeso. Cikin ikon Allah watan haihuwarta ya tsaya,tana fara nakuda bata jimaba ta haifo ɗanta namiji kyakkyawa tamkar ubansa,faɗin murnar da Ayman yayi bazata misaltuba,haka kowa na dangin yadunga rubibin zuwa dubata. Ranar suna aka sawa yaron sunan sarki suna kiranshi Abu Ayman. Duk wata kulawa ta duniya babu irin wacce Ayman beyiwa ummu ita da ɗanta,bashida burin daya wuce ganin farin cikinsu,haka itama batason abinda ze ɓata ran mijin nats. yau Asabar ɗin ƙarshen wata,a irin wannan ranar ne ummu da Ayman suke zuwa shopping ɗin abinda basu dashi. Kamar kullum sunyi shiga ta ƙasaita suda ɗansu,suka nufi,shoprite dake Abuja. .Sunyi siyayyarsu kaf ansa musu amota suna shirin shiga mota wata mata gurguwa ta ƙaraso gurinsu tana bara. duk canjawar da ƴarfillo zatayi ummu bazata mance taba,dan haka ummu na kallonra ta shida ta da sauri tanufeta ta rungumeta tana faɗin. "mummy kece kika dawo haka?" Aruɗe ƴarfilli tabi ummu da kallo se alokacin ta ganeta,kuka tasa tana neman gafarar ta,itama ummun kuka take tana faɗa mata ta yafe mata. koda Ayman ya ƙaraso yagansu a haka beyi mamaki ba dan yasan akwai tsaftatacciyar soyayya a tsakaninsu,sharrin fiddah da na shaiɗanne kawai yashiga tsakaninsu,dan haka jan ummu yayi zuwa mota sannan yadawo ya tura ƴarfillo zuwa bayan motar ta shiga yasa keken nata a boot yaja motar suka dawo gida. koda ƴarfillo tagane sunyi aure harda ɗa ba ƙaramin daɗi tajiba,cigaba tayi da neman gafararsu su kuma suka yafe mata. wata biyu tsakani,suka ɗaga zuwa ƙasar egypt inda zaayiw ƴarfillo ƙafar roba,anyi mata cikin nasara inda Ayman yanarkar da dukiya me yawa dan amata me kyau dan ya faranta ran ummu,ayko anyi matan,sarai take tafiya akanta. Tun tana iya godiya har tazo ta kasa sede kuka,tsoron Allah ne yakamata sosai,tashiga tubarwa Allah akan abinda ta aykata abaya. Daga egypt saudiyya suka wuce da ita,acan ta duƙufa neman gafarar Allah tana kuka . koda suka dawo nigeria,har yola suka kaita gurin ƴan uwanta suka basu haƙuri,irama ta nemi yafiyarsu suka yafe mata,taci gaba da zama a yola tana roƙon yafiyar Agurin Allah. Itama fiddaj tasamu dakyar da taimakon ummu Ayman ya yafe mata,inda ahalin yanzu tayi aure,agidan gomnan sokoton,inda take auren gomnan. Salmab itama,tayi danasanin shawarwarin data ba ƙawarta,har sokoto taje ta nemi gafarar fiddah ta yafe mata. ummu ce kwance akan gado Ayman namata tausa ita kuma tana masa shagwaɓa. cikin wasa tace masa. "se wani matsamin kake da ƙarfi salon na tsufa da wuri ka auro wata ko?" Dariya Ayman yayi yajawota jikinshi ya rungume,ya raɗa mata a kunne. "Hayati inda ke arayuwata,duk sauran mata mazane,ke kaɗaice macen danake kallo a matsayin mace,ba tsufaba ko mutuwa kikayi zanci gaba da sonki har ƙarshen numfashina,akanki nasan so akanki narufe" Mirginowa tayi sosai itama ta rungumeshi tana dariya,shima dariyar yakeyi ya ƙara da cewa. "Ummu Aymana ta Ayman,mummyn Abu ayman,sirikar Abu Ayman,fara me farar aniya,anbuga dake anbarki kainuwa dashen lillahi" "Kai qurratu ayni wannan kirari haka kode fadanci kakeyine"taƙarasa maganar tana dariya. "Hhhhh ashe kingane,gaisuwace da roƙon iri"yafaɗi sanda yakamota yafara ayka mata sakonni na maaurata. *ALHAMDULILLAHI* *GODIYA TA TABBATA GA ALLAH ME KOWA ME KOMAI,TSIRA DA AMINCI GA ANNABIN MU MUHAMMAD S,A,W* *ANAN NAKAWO ƘARSHEN WANNAN LITTAFI NA UMMU AYMANA KUSKUREN DANAYI ACIKI ALLAH YA GAFARTAMIN,ABINDA NAYI DAIDAI ALLAH YABANI LADAN,ALLAH YASA SAƘON DANA TURA YA ISA GURIN WAINDA YADACE,ALLAH KUMA YASA MUDACE AMEEN* *KU BIYONI CIKIN ƳAR BAUTAR ƘASA* *TAKU HAR KULLUM,ZAHRA SURBAJO*. Masha'Allah, Allah yaƙara basira da hikima Mun yaba sosai bisa wannan namijin ƙoƙarinki a cikin wannan littafin naki ummu aymana, Allah yasa mu amfana da fadakarwa da kikayi a ciki, Daga ɗaya daga cikin dubannin masoyan wannan littafi Muhammad Kabiru,Admin na mk, hausa novels group. 08160112181. Sai munji sabon littafinki dake hanya.fatan alkhairi.