*1/9/2020* *DA WATA A 'KASA!!* Writing by *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~ *🌎Manazarta Writes Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~ _*BABU MAHALU'KIN DA YA ISA YAYI WA MUTUM ABINDA ALLAH BAI MASA BA, BAMA NEMA GURIN KOWA!! GURIN ALLAH MUKE NEMA ALLAH KAYI MANA BADAN MU BA👏🏻*_ *PAID BOOK!* _*'KAGAGEN LABARI NE BA'AYI DAN ACI ZARAFIN WANI KO WATA BA, WANDA YAGA YAYI DAI-DAI DA YANAYI NA RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NE!!*_ ~~~~~~~~~ *_BAN YARDA A SAUYA MIN YANAYIN LABARI NA ZUWA WATA SIGA DABAN BA, WANDA YA SAUYA MIN YANDA RUBUTU NA YAKE KO KUMA YA SIYAR MIN DA SHI TO BAN YAFE BA!_* ~~~~~~~~~ *_KAUDA KANKI!! AKAN ABINDA BAI SHAFE KI BA!! KANA KUMA IDAN BA ZAKI FA'DI ALKAIRI BA TO MAFI ALKAIRI A GAREKI KIYI SHURU DA BAKIN KI!!_* ~~~~~~~~~ _*WALLAHU GALIBUN ALA AMRIHI!!!!*_👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻 *YA ALLAH KA BAMU RINJAYE A KAN MA'KIYANMU* ~~~~~~~~~~ *SADAUKARWA GA:* *WANI BAWAN ALLAH* *INA RO'KON UBANGIJI ALLAH YA JI'BANCI AL'AMURANSA YA BIYA MASA DUKKANIN BU'KATUNSA NA ALKAIRI YASA YA GAMA DA DUNIYA LAFIYA👏🏻* ~~~~~~~~ *Free Pege 1* *"Gaje* Ke Gaje kina ina ne waiko baki san na shigo gidan bane.'' ? Matar da aka kira da wannan suna ta fito daga garken awakai da wani 'katon buhu a hannunta, tana fad'in "Maigida wannan kiran fa Allah yasa dai lafiya naji ko sallama ba kayi ba kana ta 'kwala min kira." Ya shiga karkad'e guntuwar tabamar dake gurin ya shimfid'a ya zauna had'e da cire wata hula me kunnuwa daga kansa, yasa hannu ya sharce gumin dake saman goshinsa yace."Ke dai zo zauna kiji labari mai dad'i." Gaje ta aje buhun hannunta tana washe ha'kora tace"Da alama dai yau kasuwa tayi kyau ko kuma ka samu gara'basa wani ya kawo tallan shanu a arha ." Yace"Duk babu ko d'aya Ina Asiya take."? Tace"Yanzu yanzu ta tafi rafi jidon ruwa." Ya washe bakinsa yana kallonta yace." Ashe yarinyar nan Asiya 'kashin arzi'ki ne da ita, yanzu nan maigari ya kirani fada ina zuwa yake shaida min cewar yana nemawa babban yaronsa Isma'il auran Asiya saboda yaga kaf garin nan babu mai nutsuwarta da hankalinta ai a take na amince nace na bashi." Ya'karasa maganar yana dariya hade da gyara zamansa. Wani irin shan kunu tayi ta 'bata fuska sosai tace" Shi yanzu Isma'il din ne yake cewa Asiya duk tafi matan garin nan nutsuwa da kamun kai? me ya gani a jikinta da har zaiyi sha'awar auranta, duk matan dake garin nan ya rasa wacce zaice yana so sai wannan shashashar mahaukaciya, kai kuma ka shigo kana wani murna da dariya." Mai Shaniya jikinsa yayi sanyi da jin abinda matar tashi take fad'a yace."Yanzu Gaje kina so kice mun Asiya bata kai matsayin da Isma'il d'an maigari zai aureta ba, meye aibun yarinyar ? kodan bake ce kika haifeta bane yasa kike wannan maganar."? Gaje ta fashe da kuka tana fyace hanci tace"Da kyau! a gwara kayi min gorin rashin haihuwa wato kai har kana da bakin magana ka manta irin hidimar da nayi da Asiya ko? Uwarta tana shaifarta ta mutu ta barni da wahala nice kashinta da fitsarinta har ta girma amma saboda tsabar butulci irin naka zaka goranta min." Mai Shaniya jikinsa yay sanyi yace."Gaje duk abin nan fa bana tashin hankali bane! ni a ganina wannan abun na farin ciki ne da murna, yanzu idan Asiya ta auri Isma'il dan gidan maigari ai mun zama abun kwatance a gari wallahi nasan maigari sai ya bani rawani, sannan ko ke za'a dinga girmamaki idan kika shiga cikin 'yan uwanki mata." Gaje ta gyara d'aurin d'ankwalinta a cukune tace"Wannan al'amarin fa ba zai yuwu ba Malam domin ni nasan Asiya ba cikakkiyar mace bace ko manta lalurar da tayi a lokacin da take yarinya 'karama tare da kai muka dinga sintiri zuwa gurin me magani daga karshe aka samu maganin da ya magance mata 'kurajan gabanta, to tun daga sannan gabanta ya bud'e sanyi ne da ita sosai dan yanzu haka idan ya tashi haka za kaga tana ta susa kamar zata yage gabanta." Mai shaniya yace."Gaje yanzu ya za'ayi? na d'okanta da al'amarin nan wallahi ina so Asiya ta auri Ismail dan gidan maigari." Gaje tace"Aikuwa aure ba zaiyi ba dan kasan ranar da Isma'il ya tabbatar da cewar Asiya ba budurwa bace to a ranar zai saketa, Ismail bai cancaci ya auri mace irin Asiya ba, hakanan Asiya bata cancanci ta auri namiji saurayi kuma santalele kamar Isma'il ba." Mai shaniya ya goge hancinsa yace."Gaje kaina duk ya d'aure wallahi ban san me zancewa da maigari ba gashi nayi masa al'kawarin bawa d'ansa Asiya." Gaje ta gyara zamanta tana kallonsa tace"Kaga Mai shaniya babu maganar rufa rufa a harkar aure! kawai ka fito fili ka sanar masa abinda ke faruwa, Idan Isma'il yaga xai iya auran Asiya a haka babu budurci to sai ya bada sadaki, Idan yaga bai zai iya ba to anan fadar kafin ka fito ka bada kyautarta wanda yaga zai iya auranta da sunan bazawara sai ya bada sadaki ko dubu biyar ko dubu uku ka daura mata aure ka huta." Mai Shaniya jikinsa duk yayi sanyi yace."Wallahi Gaje duk na dauka yarinyar nan ta samu lafiya ashe da shauran ciwo." Gaje ta ta'be bakinta tace"Malam kenan nice nake ganin ikon Allah! Asiya fa kullum hannunta na cikin wandonta tana susa babu dare babu rana mussaman idan ta kwanta bacci da daddare, gani nakeyi ma anya kuwa cutar sanyi ce kad'ai da ita kodai aure take so ne take sa hannunta a gabanta, ita dai ta sani! ni dai shawara nake baka ka bada ita sadaka kuma dik wanda zaka bawa to ka shaida masa cewar bata da lafiya kuma bata da budurci." Mai shaniya yace." Gaje maganarki abar a duba ce kadafa yarinyar nan ta janyo min abun kunya a gari ace kulluma yarinya hannunta a cikin wando."? Gaje na 'kokarin yin magana ta shigo gidan kanta d'auke da tulu madaidaici, taci uwar d'amara!! Zaninta ya d'angale sama 'kwarinta duk a waje! Can inda randunan su na ruwa suke ta nufa ta juye a hankali ta ajiye tulun ta d'an sassauta d'amararta ta cusa hannunta cikin zaninta ta samu nasarar zura hannunta cikin wandonta ta hau susa tana lumshe idonta. Gaje ta zunguri Mai shaniya tana nuna masa ita.....Mai shaniya yayi zumbur! ya mi'ke! hankali a tashe ya nufeta hannunaa rike da zabgegiyar bulalar da yake 'kora shannunsa ya lafta mata ita a gadon bayanta......"Shegiya me kike sosawa a cikin wando."? Abinda ya fad'a kenan yana sake lafta mata bulalar a jikinta, kuka takeyi tana bashi hakuri ta zube gwiwanta a 'kasa. Yace."Dan Ubanki ba zaki fad'a min abinda kike sosawa a wandonki ba"? Tana kuka tace"Wallahi babu komai Baffa kayi hakuri bana sosa komai."? Gaje ta taso daga inda take ta kwad'a mata mari tace"Ma'karyaciya gashi nan har yanzu hannunki guda na cikin wandonki zakice babu komai." Da sauri Asiya ta zaro hannunta daga cikin zaninta tana kuka tana fad'in bana sosa komai Baffa kayi hakuri." Mai shaniya ya jefar da bulalar hannunsa yana kallon Gaje yace." Yanzu naga zahiri Gaje naga Zahiri! to wannan yarinyar ba zan bari ta wulakantani ba, yanzu yanzu zan nufi Fada domin na shaidawa maigari abinda ke faruwa aure zanyi mata na huta." Gaje tace"Yanzu kayi magana Malam maza tashi kaje fada ka sanar da maigari abinda ke da akwai. Mai shaniya ya dauki hularsa ya kwafa, ya zura wani takalmi sauciki irin na roba kwataf-kwataf sai kace kuturu ya futa daga gidan rasa a 'bace! *GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK ZAKU TURA #300 TA WANNAN ACCONT 'DIN......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURO TO SAI KI SAMENI TA WANNAN NUMBARS 'DIN SAI NAYI MIKI BAYANIN YANDA ZAKI TURA KUDIN.......* *08089965176* *07084653262* *MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BU'KATAR SHIGA VIP GRUOP TO SAI KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR* WhatsApp numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege2* Asiya ta dur'kushe bakin randunan ruwa tana wani irin kuka me tsuma zuciya tana takure jikinta da ya ji'ke da ruwa, taji saukan dundu a gadon bayanta, gantsarewa tayi da sauri ta mi'ke tsaye tana zazzare ido hawaye ya kwaranya daga idanunta. Gaje ta watsa mata da'kwa da'kwan idanunta kamar gurjiya cikin tsawa! tace" 'Dauki tulu maza ki cigaba da d'ebomin ruwa shegiya munafuka anamimiya me halin uwarta tun kina 'kan'kanuwarki dake kin iya zura hannu a wando kina jangwale jangwale, haka uwarki take jarababbiya ce! Allah dai ya rabani da bala'i.! Ta'karasa maganar tana kai mata rankwashi a kanta. Asiya ta d'auki tulu da sauri ta kama hanya zata fita daga gidan, Gaje tace"Saura kuma kije ki dad'e irin jiya wallahi kika dade baki dawo ba to ki nemi me baki abinci a gidan nan."! Da sauri ta fita daga gidan tana kuka had'e da gyara d'aurin d'amararta daya sakwarkwace! da sauri take tafiya tana sake gyara tulun dake kafad'arta, takalminta guda ya tsinke ta ajiye tulun a hankali tana neman leda ta d'aure takalmin ta soma jin alamun tafiya a bayanta, d'an juyawa tayi ta hango Isma'il na kokarin zuwa inda take. Da sauri ta dago ta dauki tulunta ta cigaba da jan takalmin dake a kafarta ba tare data d'aure ba......Isma'il ya shiga 'kwala mata kira "Asiya tsaya mana ya kike sauri ne ? ki tsaya akwai mahimiyyar maganar da zamuyi dake." 'Kin tsayawa tayi ta cigaba da saurinta har sai da ya cimma inda take yasha gabanta yana kallonta da fad'in "Haba Asiya ya ina magana kuma kina jina kike tafiya ko dan kinga na damu dake ne."? Sunkuyar da kanta tayi 'kasa tana goge fuskarta, tace" Ina Wuni."? Yace."Lafiya Asiya ya gida ya kwana biyu." Shuru tayi masa dan dama can ita ba mai magana bace." Yace."Dazu mahaifinki da mahaifina sun tautauna kan maganar auranmu dake mahaifinki ya shaidawa mahaifina cewar ya mallaka min ke sadaki zan turo yanzu sai kuma kayan lefe a daura aure." Shuru tayi masa kanta a 'kasa, Yace."Asiya kina farin ciki ko."? Ta d'ago kanta tana kallonsa duk da cewar yarinya ce kuma bata san meye so ba, sannan kuma tana cikin 'kauye sam Isma'il baiyi mata ba, bata jin sonsa ko kad'an a cikin zuciyarta, kuma bata jin tsanarsa, to amma bata da za'bi sai abinda mahaifinta yace idan Isma'il d'in ya za'ba mata a matsayin miji dole ta zauna dashi. Yace."To tunda ba zakiyi min magana ba muje na rakaki d'ibar ruwan." Jerawa sukayi suna tafiya a tare Isma'il sai hira yake mata tayi shuru tana sauraransa domin bata da abinda zata ce. ***** Cikin wata irin shigar 'kananun kayan da suka masa mugun kyau! yake sakkowa daga steps bibbiyu yake had'awa har ya sakko 'kasan makeken parlorn da yaji kayan alatu da komai na jin dad'in rayuwa, Wata macace nagani kan kujere mai cin mutum daya tana zaune cikin kwalliya da romot na tv a hannunta, tana waiwayowa nagane mahaifiyarshi ce saboda tsananin yanda suke kama dashi, kai tsaye inda take yana nufa, cikin wata irin tafiya irin ta nigogi yana d'an kallan tsadaddan agogon dake daure a hannunsa. 'Dan 'bata fuskarta tayi tana kallonshi har ya 'karaso inda take zaune ya d'an risina kafin ya zauna kan kujerar yace."Mommy barka da Safiya." "Barka dai wato dama kana nan baka fita daga gidan ba Hafeez wai me yasa kake hakane."? Ya d'an shafa kanshi cikin yanayi na damuwa yace." Wai shin Mommy dole ne sai naje d'aurin auren ne? dani ko babu ni za suyi d'aurin auransu ni wallahi na tsani wannan halin na Dad dole sai yace na shiga cikin mutane wanda hakan ni ba ra'ayi na bane bana son hayaniya da damuwar jama'a shi kuma Dad ya kasa fahimta. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali tace"Hafeez kullum ana nuna maka abinda ya dace kana kauce hanya, idan yau mune to bamu ne gobe ba mahaifinka na d'ora kan dukkanin harkokinsa ne saboda kasantuwarka babban d'anshi, sannan kuma idan baka soma halartar d'aurin aure gami da jana'iza ba sai yaushe? kada fa ka manta yanzu kana matakin shekaru ashirin da bakwai a duniya, Hafeez ka girma yanzu dan Allah duk ka ajiye wani shashanci da kakeyi ka fuskanci abinda ke gabanka duniyar nan bata da tabbas." Yace."Mommy shekaru ashirin da bakwai kawai shine kike cewa na girma? Mommy ina girman yake ajikina don Allah."? Yafad'a yana nuna mata jikinsa......Murmushin takaici tayi tace."Ai dama kai ba zaka ga girmanka ba sai dai a gane maka, yanzu don Allah meye amfanin irin wannan shigar dake jikinta kabi ka sanya wandon da ya matseka da riga matsatstsiya kamar zata yage! dubi askin dake kanka Hafeez." Tafad'a tana nuna shi da hannunta.....Murmushi takaici yayi ya rasa yaushe Mommy za ta gane abinda duniya ke ciki yanzu meye aibu kan abinda yake yi shi a ganinsa ba komai bane tunda yana sallah yana salati da azimi duk wani abu da zaiyi a duniya zaiyi ne domin jin dadin rayuwarsa, dreesing ko yawancin wasu abubuwa duk ba wani abu bane a ganinshi, haka ra'ayinsa yake saka 'kananun kaya baiga aibu kan hakan ba amma iyayensa kullum cikin fad'a suke ya rasa yanda zaiyi dasu. Mi'kewa yake 'kokarin yi yana 'bata rai! Tace"Ai dama duk ranar da aka fad'a maka gaskiya zaka yini kana jin haushin mutane, to na daina damuwa da fushinka Hafeez abinda kakeyi ya soma isata. "Wai don Allah Mommy me nakayi ne!? Haba Mommy kada ki saka min ciwo mana! kullum sai kuce ga abinda nayi ni kuma banganshi ba Mommy ina muku ladabi da biyayya me kuma zanyi muku! Haba Mommy Haba Mommy ni bana son haka Wallahi." Yana tafiya yake wannan maganar had'e da watsa hannayensa alamun 'bacin rai." Ta bishi da wani irin kallo har ya bude kofa ya fita daga parlon....Girgiza kanta tayi ta maida hankalinta kan tv tana nemawa d'an nata shiriya gurin ubangiji. Yana fita ya nufi parking area Wata dun'kulalliyar mota ya shiga tun kafin ya 'karaso bakin gate din maigadi ya bud'e masa ya figi motar a guje ya fice daga gidan. Sai da ya hau kan kwalta sosai ya ciro 'katuwar wayarshi mai kyau da tsada gami da tsaruwa ya soma kiran wata numbar. Yana d'aga wayar Yace."Yane kana ina gani na fito yanzu na d'anyi bacci ne wallahi." Isha'k Yace."Ina Gidan Huzaifa ka samemu a can." Yace."Okey ganinan zuwa." Kai tsaye titin Yahaya gusau ya nufa inda gidan abokin nasa yake mai suna Huzaifa. Suna zaune a parlon gidan Huzaifa da Isha'ik suna hira Fadila matar Huzaifa taci kwalliya da wasu masifaffun 'kananun kayan da sukayi bala'in fito mata da sufar jikinta, babu ruwanta sai zurga zurgarta take tsakanin parlo da kicin tana aikace akaicenta........Hafeez na isa gidan Huzaifa kai tsaye da yayi parking din motarshi cikin gidan ya nufa ba tare da neman iso ba. Ya shiga da sallama a bakinsa, Fadila dake kokarin fitowa daga kicin da fulas a hannunta ta amsa masa tana watsa masa wani irin kallo, shima idanunsa yasa cikin nata yana wani 'kan'kancesu yace."Madam Ya gida."? Murmushi tayi had'e da d'an ta'be bakinta ta wuceshi tana fad'in "Gida na nan lafiya." wani mayataccen kallo yabi ta dashi mazaunanta sunyi masifar d'aga masa hankali lokaci 'kan'kani duk wata sha'awarshi ta tashi. Cikin kasala ya 'karasa cikin palon ya zube kan kujera yana dafa goshinsa.....Huzaifa yace."Guy na fahimci abinda ya sanyayyar maka da jiki daga shigowarka." Hannu ya bashi suka tafa yana mutsika goshinsa had'e da d'an lasar lips d'insa da suka d'anyi duhu kad'an, Yace."Huzaifa Fadila tayi wallahi ." Isha'ik ya kwashe da dariya yace."Hafeez baka da dama, wallahi, kullum kai kenan cikin kalle mana mataye kai ka'ki auran komeye dalili oho."! Huzaifa ya saki dariya yana kallon Hafeez din Cikin kulawa yace." Guy kayi kawai abunda kakeso!! mu muka baka dama matayenmu naka ne mun yarda da kanmu mun amince da junanmu abotarmu ta taimakon juna ce yanda muke kwasar ganima kaima kana da iko da kazo ka kwasa gurin duk wacce kake da sha'awa. Kuyi sharing pls👏🏻 *GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124..........BINTA UMAR GTBANK...IDAN KATIN WAYA MUTUM KE SON TUROWA TO SAI YA SAMENI TA WANNAN NUMBARS DIN.......07084653262_08089965176 SAI NAYI MIKI BAYANIN YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN NIJER IDAN KUNA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS........* 90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE *IDAN KINA DA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP SAI KIYI MIN MAGANA TA WANNAN NUMBAR* WhatsApp numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ _*Kauda kanki akan abinda bai shafeki ba!! Kana kuma idan ba zaki fad'i alkairi ba to kiyi shuru da bakinki🕺*_ ______________________ *PAID BOOK!* *Free Pege3* 'Dan kallon Huzaifan yay yana so yayi magana sai kuma yaja bakinsa yayi shuru yana sake yin release kan kujerar had'e da dan rintse idonshi yana janyo numfashi da 'kayar! Isha'ik ya daga hannunshi a hankali yace."Wallahi kada ka jefa kanka cikin matsala Hafeez meye wani abun damuwa da tunani cikin wannan al'amarin, yarda da amintaka ce ta sanya muka mayar da kanmu 'yan uwan juna ni ina ganin dan kayi sex da d'aya daga cikin matanmu ba wani abun bane na tabbata Safina yanda take jin maganata komai na Umarceta dashi zata amince dashi saboda haka kayi shawara my friend kaji dad'in duniyarka ba wani aibu bane." Idanunsa ya bud'e wanda suka d'an risina kad'an yace."Isha'ik ban ta'ba jin sha'awar yin sex ba irin yau Fadila ta tabbatar min da ni d'in lafiyayyan namiji ne, wallahi bakaji yanda nakeji ba a jikina a halin yanzu amma babu komai zan duba maganarku nagode my friends. " Huzaifa ya bashi hannu suka tafa yana dariya yace "Ko kaifa Guy yanzu ne zaga bambanci kuma zaka tabbatar da abinda muke fad'a maka dangane da wannan harkar." 'Dan ta'be bakinsa yayi yana murmushi wanda ya tsaya iyakacin le'bensa, ya d'an d'age girarashi goshinsa ya tattare hannusa yakai kan ash tire din dake kan dogon senter teble din dake gabansu ya dauki kwalin sigari ya zaro guda ya soka a bakinsa, leghatr ya futo da ita ya kunna yayi mata wata wawar zu'ka ya wani lumshe idonsa yana feso haya'kinta ta baki ta hanci........Muryar Fadila yaji tana cewa "My ga abincin nan fa na shirya muku a dainnig." Ya wani bud'e idonsa da sauri yana yana kallonta, Itama shi ta d'an kalla tana fari da idonta tace."Wai My me ya samu Hafeez ne naga tunda ya shigo sai wani salau salau yake yi babu kuzari a jikinsa." Huzaifa na 'kokarin mi'kewa yace."Kece kika janyo mishi rashin lafiya dan haka sai ki bashi magani." Yar dariya tayi tana girgixa jikinta nonowanta sukayi wani tsalle! Hafeez yaji kamar ya shid'e! ya kafeta da fitinannun idanunsa yana zu'kar sigarinshi, Tace."Wai hakane Hafeez me nayi maka to."? Shuru yay mata kawai ya 'kureta da ido..... Huzaifa da Isha'ik suka nufi daining suna magana, Fadila ta d'an matsa jikin kujerar da yake zaune tana wani lumshe idonta da wata irin murya tace"Hafeez me nayi maka? My yace."Wai nice." Ya d'an dage girarshi yana kallonta da ido d'aya, magana yake son yayi mata sai dai ya kasa kawai sai ya danne sigarin dake hannunsa kan tire din gabanshi sigarin ta mutu ya mi'ke a hankali ya bar mata gurin, Hafeez mugun miskili ne dan wani sa'in magana wuya take masa kuma baida saurin sabo da mutune shiyasa bai wani saba da matan abokan nashi ba, gaisuwa ce kawai ke had'asu, sai dai yau yayi masifar shiga mugun yanayi dangane da matar abokinsa Huzaifa, yana ganin mutukar bai kawar da kwadayinsa ba a kanta zai iya mutuwa dan wani irin abu ne ke taso masa. Fadila tabi shi da wani irin kallo gabanta na fad'uwa, tana bala'in son Hafeez da sha'awarshi, duk cikin abokan mijinta tafi kaunarsa, kuma tana so ya fad'a tarkonta domin tasan mutukar ya d'and'ani zumarta sai ya haukace mata kamar yanda Huzaifa da Isha'ik ke haukace mata idan suna sex da ita. ***** Mai shaniya ne gurfane gaban maigari suna magana. Maigari ya gyara zamansa ransa a 'bace! yace."Mai shaniya ka tabbata wannan magana taka gaskiya ce cewar yarinyar ka Asiya ba cikkakkiyar mace bace."? Mai shaniya yace."Kwarai kuwa ranka shi dad'e! wallahi ni ban sani ba sai dana koma gida bayan bari na fada nake shaidawa mai d'akina abinda muka tattauna da kai, nan take tabbatar min da cewar yarinyar ta rasa budurcinta tun bayan wata gagarimar rashin lafiya da tayi a matuncinta, na tabbatar da maganar mai d'akina ranka ya dad'e tunda nima naga zahiri da idona to shine nace ni bazan munafurce ka ba, kan wannan al'amari zan fad'a maka gaskiya kan cewar a sanar da yaro idan yana ganin zai iya auranta a haka to shikkenan idan kuma baya so to zanyi kyautarta ga duk mai so sai ya biya sadaki kawai a daura aure." Maigari ya gyara zamansa kan kujerar yana gyara zaman babbar rigarsa yace."Inaa! ai yarona ba zai ta'ba auran wannan yarinya ba mai shaniya kayi kyan kai daka fad'a min abinda ke da akwai baka munafurce ni, yanzu idan na shiga gida cin abinci zan sanar da yaro abinda ake ciki sai ya duba wata yarinyar a cikin gari dai-dai dashi." Mai shaniya yace."Ranka ya dad'e wallahi naso wannan al'amari amma tun daga haka ta kasance to babu alkairi a ciki, saboda yanzu." Yafad'a yana wurga idanunsa kan jama'ar dake zazzaune a fadar, ya cigaba da cewa "Saboda haka yanzu ni Ayuba Mai Shaniya na bada kyautar yarinyar 'yata Asiya idan da wanda yake so a cikin fada to yayi magana sai ya bada sadaki a daura aure." Alhaji bawa mai kalwa yayi maza ya d'aga hannunsa yana washe ha'koransa wanda da suka cinye da dattin goro bakin yayi dagaje dagaje, gefe da gefe dik abun goro yace."Mai shaniya ni Bawa mai kalwa zan auri wannan yarinya ga sadaki na." Ya d'an gyara zamansa yana janye babbar rigarshi ya ciro kudi 'yan dubu dubu guda bakwai a jiye gabansa fuska a sake yace."Ga sadakin Asiya nan dubu bakwai don tafi karfin dubu biyar s gurina duk da ka tabbatar mana da cewar ita d'in ba budurwa bace amma dai nasan ba za'a rasa wasu abubuwan ba a tare da ita wannan dalilin ne ya sanya na 'kara dubu biyu kan dubu biyar d'in." A take fada ta kaure da hayaniya dan babu wanda ya ta'ba tsammanin Bawa mai kalwa zai kar'bi auran Asiya sanin da sukayi mutum ne mai kud'i a cikin 'kauyen kuma me fad'a a ji yana da gonaki da shanu masu yawa, shi kansa maigari wani lokacin sai da umarnin Bawa mai kalwa yake aiki a fada, Maigari yace." Masha Allah Alaji Bawa muna taya ka murna da farin ciki Allah ya sanya alkairi ha'kika ka cancanta a yaba maka domin kai d'in mutum ne mai taimako da tausayi yanzu idan ba kai ba d'in waye zaiyi wannan jahadin? dan haka kai Mai shaniya maza gurfana a gaban Alaji kayi masa godiya bisa ga karamcin da yayi maka." Mai shaniya da jikinsa ke rawa yana mamakin al'amarin ya gurfana gaban Alaji Bawa yana godiya had'e da fad'in" Alaji nagode kwarai ka rufa min asiri naji dad'in wannan karamcin." Maigari yace."Yanzu abinda za'ayi shine zamu tsayar da ranar d'aurin aure gobe idan mun zauna a fada, saboda haka kafin fada ta tashi, kai Mai shaniya ka bada dubu biyun nan dake kan kudin da Alaji ya baka na sadakin 'yarka domin a kasaftawa jama'a ladan ganin ido." Mai shaniya jiki na rawa ya cire dubu biyu a kudin ya ajiye gaban maigari yana fad'in "Ranka shi dad'e godiya nakeyi." Maigari yace."Na sallami kowa fada ta tashi sai gobe idan Allah ya kaimu." Kowa ya mi'ke ya zura takalminsa ya 'kara gaba. Maigari ya kalli Alaji bawa dake zaune a gefansa yace."Alaji ka kar'bi auran yarinyar alhalin kana da mata hud'un shin sad'aka zakayi da yarinyar nan ko kuma 'kwar'kwarah."? Alhaji Bawai ya gyara zamansa yana wani murmushi ya 'bantari goronsa yana taunawa yace."Yanzu yanzu ina komawa gida zan sau d'aya daga cikinsu in maye gurbi da 'yar gidan mai shaniya, haka kawai ina ji ina gani wannan gara'basar ba zata wuce ni ba, yarinya 'kankanuwa irin wannan mai kayan more rayuwa a jikinta nasan idan na aureta zan 'barje gumina kuma zan tada ko mad'ata! dama shegu duk na gidan sun sakwarkwace ko wacce daka shigeta zakaji kamar bakin rijiya guri a bude a bushe, yanzu Allah ya rufa min asiri zan gwangwaje." Maigari yayi wata mahaukaciyar dariya yana sake gyara zamansa yace."Babu shakka maganarka gaskiya ne Alaji, gaskiya sam tunani na bai kawo nan ba nima ina jin in sau wata daga cikinsu in samu 'yar 'karama in gwangwaje." Mahaukaciyar dariya suka kwashe da ita suna tafa hannu. **** Hafeez da 'kyar yaci abincin da Fadila ta had'a musu, suka wuce gidan Isha'k! nan d'in ma bata sauya zani ba dan itama Safina cikin matsatstsun kaya take amma ba ingilsh wear bane material ne wanda akayi mishi d'inkin banza duk sassan jikinta a waje, gashi sam Safina bata da kunya ta dinga rungume Isha'k d'in a gabansu tana masa soyayya, hankalinsa yayi masifar tashi mutuka, sallama yayi musu ya bar gidan, dukaninsu sun fahimci halin da yake ciki amma dai sun bashi dama ya yanke shawarar kan abinda zai fishsheshi idan ya bu'kaci Sex da matayensu zasu lamunce masa, tunda duk harkar dama ta taimakon juna ce sun tabbata duk ranar da yayi aure shima zai mallaka musu tashi matar idan sun bukaci hakan......... A jigace! ya shiga gidan, Mommy da Farhana suna zaune a palo suna hira, ya shigo ba tare da ya kalli inda suke ba ya soma hawa steps zai haura samansa....."My son." Muryar Mommyn shi ta dakatar dashi ya d'an juyo yana kallonta, cikin yanayi na damuwa yace."Mommy."!!!! Ta tsira masa ido tana kallonsa na minti biyu kafin tace"Fushi kakeyi ko."? Hannu ya d'ora saman goshinsa yana murzawa yace."Mommy me ya faru zanyi fushi."? Tace."Kan maganarmu ta d'azu mana." 'Dan ya mutsa fuska yayi yace."Mommy bazan ta'ba fushi dake ba wallahi bana jin dad'i ne."? Hankalinta a tashe "Meke damunka."? A marairaice yace." Nima ban sani ba Mommy."? Tace."Okey kaje ka kwanta bari na kira Dr Hisham yazo ya dubaka ok." Yace."My Mommy nagode." Ya cigaba sa hawa saman domun isa dakinshi.....Mommy ta dauki wayarta ta soma neman numbar Family Dactor d'insu, sai dai wayar na ringing ya'ki dauka. Rai a d'an 'bace! ta shiga giran numbar maigidanta yana d'agawa yace."Ganinan kan hanya yanzu muka taso." Tace."Yalla'bai Hafeez bai da lafiya." Professor Aliyu ya girgiza kanshi yana murmushi yace."Wato kun had'a baki dake dashi ko? saboda kun san idan na dawo zanyi muku fad'a kan abinda kuka aikata." Tace."A'a Wallahi ba haka bane ni kaina banji dad'in rashin zuwan Hafeez d'aurin auran nan ba wallahi dan d'azu kaca-kaca nayi masa ya fita to sai kuma yanzu ya dawo gidan jikinsa babu dad'i." Professor yace."Koma dai menene ni ba zan yarda da 'karyar wannan yaron ba, yana so ya maidani 'karamin yaro ne kawai kullum idan yasan yayi min ba dai-dai ba sai ya shirya 'karyar rashin lafiya, yanzu ina kano ina kaduna ace ana auran 'yar babban aminina dake kanki kin sani amma Hafeez ya kasa hallata haka ina kallo yaran abokaina suka dinga zuwa banda Hafeez ai ya nuna min iyakata." Ta sassauta murya tace" Kayi hakuri dan Allah kada ka 'kullaceshi Kasan halin Hafeez sarai bashi da son jama'a ga shegen muskilancin tsiya duk da nasan abinda yayi d'in bai kyauta ba amma kayi masa uziri saboda halayyarsa." Yace."Shikkena nayi masa Allah ya sanja min shi ya bar wad'annan halayen dan basu da kyau ko kad'an." Tace."Yanzu na kira doctor wayar na shiga bai dauka ba......Yace."Mybe yana da da mara lafiya ne bari yanzu xan kirashi." Tace."Okey to." Kashe wayar tayi ta mi'ke ta nufi saman Farhana tabi bayanta duk jikinsu a sanyaye kwata kwata basa kaunar 'bacin rain Hafeez d'in idan kuwa bashi da lafiya dukaninsu hankalinsu tashi yake. Kuyi Sharing pls👏🏻 *MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN NAN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATIN WAYA MUTUM ZAI TURA TO SAI YA SAMENI TA WANNAN NUMBAR 07084653262.....ZAN FAD'I YANDA ZA'A BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDI TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA DA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP TO SAI KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR* What's app *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege4* Cikin wani irin yanayi Mommy ta sameshi, yayi shame! shame kan bed d'inshi yana fitar da numfashi a sama-sama! ga joystick d'in tayi wani irin mi'kewa tsaye! koda ya fahimci an shigo dakin sai yayi maza ya janyo bargo ya rufe jikinsa hade da takure kansa, jikinsa ya shiga kyarma yana had'a wata uwar zufa! Hankalinta a tashe ta isa inda yake, bargon dake jikinsa take 'kokarin janyewa yana sake ri'keshi sosai a jikinsa baya so taga yanda gabansa yake a mi'ke! Farhana ta soma kuka tana fad'i Bro me ya sameka." Bude idonsa yayi wanda sukayi jawur ya riko hannunta murya na rawa yace."Baby cikina ne." Mommy ta koma palo da sauri ta dauki wayarta ta sake kiran Dactor lokacin yana kan hanya yace."Ganinan zuwa Hajiya." Wayar ta kashe da sauri ta koma dakin nashi. Har yanzu Farhana na zaune kusa dashi ya rike hannunta sai rintse idonsa yake yi, ita kuma sai kuka take tana masa sannu. Zama tayi kusa dashi tana tofa masa addua hankalinta ya tashi da rashin lafiyar dan nata, Yace."Mommy cikina ne ke ciwo da marata." Cikin rawan murya tace"Myson yi hakuri Dactor yanzu zai iso. Kira ya shigo wayarta koda ta duba Dr Hisham ne, Tace."Farhana jeki shigo dashi." Farhana ta mike da sauri ta fita, Minti uku suka shigo dakin tare. Dr Hisham ya ajiye jakarshi a gefe yana kallon hafeez din yace."Sannu Hafeez meke damunka." Mommy tace"Tun d'azu yake murkususu cikinsa ne ke ciwo." Ya dan tsuguna yana kokarin yanye blanket din jikinsa, Hafeez ya rike tamau, idanunsa ya rufe dan yaki kallon Dr din ma, Mommy tace"Wai meye ne sai faman rungume bargo kake ne! Ka bud'e jikinka mana sai zufa kakeyi." Dr ya kalli Mommy a nutse yace."Hajiya zamuyi magana dashi yanzu." Mommy tace"Mu baku guri kenan."? Dr yace."Eh." Mommy ta mike jikinta duk a sanyaye suka fita ita da Farhana. Dactor Hisham yace."Hafeez kasan abinda ke damunka."? Ya d'an bude idanunsa yana kallonshi a nutse yace."Na sani."!? Dr Hisham yace."Menene."? kai tsaye yace."Sha'awa ce." Dr Hisham yace."Very good! Kallo guda nayi maka nagane abinda ke damunka sai kuma ka sake tabbatar min da gaskiya ganin yanda kake rungume bargo baka so a janye Mommynka taga abinda ke faruwa da kai." Shuru yayi wa Dr din.....Dr Hisham ya cigaba da cewa" Zan d'ora ka kan magani wanda zai taimaka ammafa solution anan shine kayi gaggawar aure dan shine mafita a gareka." Ya bud'e idanunsa sosai yana kallon Dr din yace."Nasan kasan waye Mahaifina ko."? Dr Hisham yace."Sosai kuwa ni san Professor. " Yace." Idan da tani ne da tuni na dad'e dayin aure mybe ma na haihu, matsalar duk tana gurin Dadyna baya so nayi aure yanzu ban san menene dalili ba." Doctor Hisham yace."A wanan lavel d'in kuwa tilas ya ha'kura ya sauka daga kan ra'ayinsa ya barka kayi aure ko dan samun nutsuwa da kwamciyar hankalinka tunda kai Allah ya hallice ka cikin jinsin mutane masu tsananin bukata." Lumshe idonsa yayi yana dan cizar lips dinshi yace."Dr kasan halin Dady da ra'ayin ru'kau! idan ya kafe kai da fata kan abu babu me iya tursasashi, ni wallahi koda yace bazanyi aure yanzu be dameni ba sai cikin 'yan kwanakin nan da nake fama da muguwar sha'awar mace." Cikin tausayi Doctor Hisham yace."Kada ka damu Hafeez zamu zauna da Dadynka zamu tattauna kan maganar.'' Hafeez shuru yayi masa yana d'ora hannunsa saman mararsa data cika tayi fam! sai murd'a masa takeyi. a hankali yake shafa saman marar tashi yana lumshe idonsa, Doctor yace."Kaci abinci yanzu." Daga kanshi yayi sabida yaci abinci gidan Huzaifa, Dr ya bude jakarsa ya fito da kwallin magani guda biyu ya 'balla masa ya bude karamin fridge dake gefan bed ya dauki ruwa mai dai-dai cin sanyi yace."Kasha wannan maganin zakaji sassuci sau uku zaka sha gobe da jibi." Ya mike zaune a hankali ya kar'bi gorar ruwan da maganin ya watsa a bakinsa ya aje gorar ruwan ya koma ya kwanta yana fad'in "Nagode Doctor." Dr Hisham yace."Daka zauna maganin ya narke sai ka kwanta." Yace"Dr kyaleni kawai zai narke a haka." Dr Hisham ya rufe jakarsa ya mi'ke a nutse yace."Insha Allah zan zauna da Dadyn naka zamu tattauna kada ka damu." Girgixa kansa kawai ya rufe idonsa, Dr ya juya ya fita daga dakin.......Dr na kokarin saukkowa 'kasa Professor na kokarin hawa, suka had'u Dr ya mika mishi hannunsa yana masa barka da zuwa. Professor yace." Ya jikin nasa." Doctor Hisham yayi jim! kafin yace."Da sauki Za'ace." Professor hankalinsa ya tashi yace."Mu koma dakin nasa kayi min bayanin abinda ke damunsa. Doctor Hisham yabi bayansa, Professor ya tsaya kan d'an nasha yana nazarinsa, har yanzu jikinsa nannad'e yake da blanket, Yace."Hafeez." Jin muryar Mahaifin nashi yasa ya bude idonshi yana kallonshi, sai kuma ya soma yun'kurin mi'kewa zaune yana fad'in "Daddy barka da dawowa gida." Professor ya zauna gefan bed din yana nazarin d'an nasa yini guda da yayi be ganshi bai sa yaga duk ta rame Yace."Hafeez meke damunka."? Hafezz ya d'ora idanunsa Kan Doctor kan idanun Professor.... Dr Hisham yace."Yalla'bai, Hafeez na tare da matsala gaskiyar magana yana bu'katar mace a tare dashi." Professor ya wani 'bata ransa yana kallon doctor din yace."Wato had'a baki kukayi ko? kai yanzu Hisham sai ka bada goyon bayan nayi wa Yaron nan aure da wuri.'' Doctor Hisham yace."Kwarai kuwa Yallabai ai Hafeez ya isa aure shekarunsa fa ashirin da bakwai zuwa da takawas idan da yayi aure da wuri ma da tuni ya haihu." Professor ya shiga girgiza kansa yana yi musu wani kallo yace."Ba zanyiwa Hafeez aure yanzu ba dan har yanzu be kai munzali ba ina so yafi haka hankali sosai alhamdullhi muradai na akanshi sun soma cika yayi karatu mai zurfi sosai zai iya taka ko wane irin matsayi a yanzu, ina so ya fuskanci yanda ake mu'amula da mutane ya kuma daina wasu d'abi'un da yake yi to mutukar naga sauyi a tattare dashi babu shakka zanyi masa aure da duk macen daya kawo min." Dr Hisham ya girgixa kanshi cikin nutsuwa yace."Yallabai ka amince ka lamunce masa saboda gudun afkuwar matsala kota ciwo ko kuma wani abu makamancin wannan." Professor ya wani sha kunnu yana kallon Doctor Hisham din yace."Da alama yanzu zamu 'bata dai kai tunda ka kasa fahimtata kana iya tafiya tunda ka bashi magani." Doctor yace."Tuba nake yallabai." Jakarshi ya dauka ya mika masa hannu sukayi musabaha kana ya bude kofar dakin ya fita da sauri. Professor ya mai da hankalinsa kan Hafeez wanda ke cikin tsananin 'bakin ciki da 'bacin rai kan abinda Dad dinsa ke masa, kullum yana kallonsa a matsayin yaro 'karami a gurinsa mara kuma hankali da iya mu'amula wai shin wane girma ake so yayi? wane hankali akeso yayi, sannan kuma wace irin mu'amula ce bai iya da jama'a ba, mutumin da ya cud'anyya da jinsin mutane daban daban to wace irin mu'amula ce bai iya, 27years ace dashi yaro ace dashi bai da hankali wannan wace irin rayuwa ce!? "Hafeez."! Muryar mahaifin nasa ta dawo dashi nutsuwarsa ya bud'e idanunsa yana kokarin kauda 'bacin ran dake fuskarshi....." Na'am Dady." Yafada yana kallonshi. Professor Yace."Abinda Doctor Hisham ya fad'a a kanka gaskiya ne ko."? Ba tare da wata gargada ba yace."Hakane Dady."! Professor ya tsira masa idonsa yana kallonsa lallai Hafeez bai da kunya, Yace."Okey to na fahimta, ina so ka bud'e kunnanka da kyau ka saurareni, ni ban hanaka aure ba amma ina so kasani sai naga canzarwar ka akan yanayin d'abi'unka sannan zan amince maka da kayi aure." Yana gama maganarsa ya mi'ke ya fice daga dakin hannunsa rike da cot d'inshi da ya cire a mota........Ya jima yana kallon guri guda tun bayan fitar mahaifin nasa daga dakin yake ta faman tunane tunane! wane d'abi'u yake yi ne? Yana sallah yana salati yana azimi da zakka ya sauke farali har sau biyu to menene abinda yake yi wanda ya kafurcewa musulunci.....Shan taba(Sigari) ko kuma saka 'kananun kaya da yin aski sune laifi? to kuwa idan hakane ashe zai ta dawwama bashi da aure akan me? kamar yanda yake da ra'ayin ri'kau shima haka yake dashi kan abinda yasa kansa, saboda haka ko ya amince masa da yayi aure to ba zaiyi ba wallah! ai ba lallai sai ta hanyar aure bane zai biyawa kansa bukata, dole ne ma ya dauki shawarwarin abokainsa domin cikar muradinsa insha Allah kuma bazai kara yi masa maganar aure ba duk ranar daya bukaci yayi auran shi kuma zai ce dashi bai shirya ba." Shi kadai yake wannan sa'ke-sa'ken a cikin ransa.......Ya amince da shawararsa ta kar'she xai amsa gayyatar abokanansa zuwa gidajensu. ****** Tana takure jikin dangar kara inda garken awakai yake tana kwance dogon gashinta daya jike jagab sabida jidon ruwa, wani lafiyayyan ba'kin gashi ne mai kyalli sai dai yayi masifar daud'a sai warin manshanu d'anye yake, tana gama tsefewa ta dauki manshanu ta kuma kaftawa a kan kana kuma ta shiga tufkewa gashin da hannunta........"Ke dan ubanki zo nan."! Muryar Gaje ce ta daki dodon kunanta, da sauri ta mi'ke ta nufi kicin inda take aikin raba abinci......Gaje ta watsa mata ruwan dake cikin kwanon da tayi kwasar towo tana harararta tace"Maza dauke min kwanukan abincin nan kije ki jera minsu cikin dakin kan tabarmar da mahaifinki ke cin abinci." 'Kwallah na 'kokarin sauko ta d'an karkad'e kod'ad'an zanin atamfar dake cikinta....Gaje ta d'aga abun ruwan kwasar towon ta watsa mata a jikinta gabadaya tace"Gashinan na watsa miki gabadaya sai ki karkad'e! Ja'ira mara mutumci yanzu ke a haka har wata tsabta ce dake? Zaki kwashe min kwanonin abinci ko zaki tsaya karkad'ewa."! Cikin tsawa tayi maganar wacce ta sanyata zabura! da sauri ta soma daukar silbobin abincin hannunta na rawa ta nufi dakin nata. Gaje taja matsiyacin tsaki tace" 'Yar iska yarinya da ido kamar na mayu." Asiya ta dawo da sauri ta dauki 'karamar silbar dake dauke da miyar karkashi, bisa tsautsayi hannunta ya goce miyar ta zube a jikin Gaje da kuma 'kasan gurin." A fusace! tace"Ni kika zubawa miya a jiki Asiya."? Tuni jikinta ya shiga kyarma ta zube a kasan gurin tana hawaye "Dan Allah babata kiyi hakuri wallahi ban sani ba." Gaje ta kai mata wani wawan kutufo a fuska, a take bakinta ya fashe! Gaje ta fito daga kicin din afusace! taje ta dauko wata murtukekiyar bulala dake tsa'kale a tsakar gidan, kawai tana zuwa ta shiga labta mata a jikinta. Asiya Ihu takeyi a gurin tana sosa jikinta, hakuri take bata amma kamar 'kara zugata takeyi lafta mata kawai takeyi a jikinta kamar ta samu jaka. Aguje! ta tunkud'eta! tayi waje da gudu kanta babu dankwali tana wani irin kuka, taje ta 'buya bayan wata katuwar bishiyar mangwaro.....Gaje ta fito daga gidan tana hakki! hannunta rike da bulalar tana rarraba idanunta a gurin, da taga bata ganta ba sai ta girgiza kanta ta juya tana fad'in "Duk inda kika shiga kika fito zaki shigo gida ki sameni ne." Kuyi sharing 👏🏻 *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KI SAMENI DA WANNAN NUMBARS 07084653262_08089965176.......ZAN FA'DI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA DA BUKATAR VIP GRUOP TO SAI KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR* WhatsApp *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌎MANAZARTA WRITES ASSO* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege5* Takure jikinta tayi jikin bishiyar mangwaron tana wani irin kuka mai tsuma zuciya, jikinta sai rawar d'ari yake kasancewar lokacin sanyi ne gashi Gaje ta watsa mata ruwa ajikinta, kuka take sosai tana tunano irin ba'kar azabar da matar babanta ke gana mata, tunda ta taso ta fahimci cewar ba itace mahaifiyarta ba dan 'ke'ke da 'ke'ke! Gajen ke tabbatar mata da ba itace ta haifeta ba, munafukar uwarta ta mutu dan haka da haihuwarta gwara babu, duk aikin gidan itace keyi tun bata kai shekarun hakaba take jidon ruwa yini takeyi aiki! a gidan Gaje ta hana babanta yasa ta a makaranta tanaji tana gani 'kawayenta zasu tafi makarantar allo ita kuma Gaje ta dora mata tallah! bata da sutturar arziki duka kayanta kala uku ne, sai tayi wata guda ba tayi wanka ba, dakin da take kwanciya guntuwar tabarma ce da kullin kayanta wanda take filo dasu, ko fitila babu a dakin gashi dakin irin na kasa ne ya rube kasansa duk danshi, rana zafi sanyi haka take rayuwarta cikin dakin, Gaje sau daya kacal take bata abinci a rana shima sai babanta na gidan, sannan zata zuba mata idan baya nan sai dai ta sud'e ragowar tukunya ko kuma idan tazo wanke wanke ta sud'e kwanuka, duk sanda Gaje taso yi mata mugunta data gama abincin zata jika tukunyar da ruwa, kuma ta hanata, haka take yini da yunwa ga aikin wahala. Hawaye ta share ta kwanta kasan bishiyar jikinta na wani irin rawa zazzabi ne keson kamata, lumshe idonta tayi tana tunani gwara ayi mata auran ko ta samu sassaucin wannan masifa! Hasken torchlight ta gani a kanta! mike zaune a furgice tana zare ido. babanta ne tsaye a kanta, kafin tayi wani yun'kuri ya gaura mata mari! "Dan ubanki nan kikazo kika kwanta saboda kin san kinyi laifi ko? Hawaye ya soma gudana a kuncinta murya na rawa tace" Baba kayi hakuri."! Yace."Ni bani zaki bawa hakuri ba Gaje zaki bawa hakuri saboda baki da kunya kiyi mata 'barna saboda ta hukuntaki sai ki tunkud'eta ki gudu! to kina da wani gidan ne bayan wannan."? Ta shiga girgiza kai tana hawaye. Ya buga mata razananniyar tsawa! da fad'in "Tashi muje ki bata hakuri Kafurar yarinya mata na wahala dake kina mata rashin arziki Allah dai ya kusa rabani da wahalar ki idan na kaiki dakinki na huta da wahala." Da sauri ta mike tana makyarkyatar jiki, tayi gaba yana binta a baya yana xaginta. Gaje na zaune a tsakar gida da kwanonin abinci a gabanta da alama basu dade da gama cin abincin ba, suka shigo gidan. Tace."Malam a ina ka samota? yarinyar nan neman duniya nayi mata banganta ba." Yace."Tana can bayan bishiyar mangwaro ta kwanta." Gaje ta bude bakinta cikin mamaki! tace"Asiya masifa kike so ki jawo mana."? Shuru Asiya tayi tana takure jikinta." Gaje ta girgixa kanta tace"Allah ya shiryeki zo ki dauki wannan kwanon abincinki ne a ciki kije dakinki kici." Asiya jiki na kyarma taje ta dauki kwanon dake gaban Gaje ta daga buhun dake kofar dakinta ta shiga, dakin duhu dum'dum! haka ta laluba inda shimfidarta take ta zauna hannu na rawa ta bude kwanon abincin ta duma hannunta, Wayam! babu komai a ciki....Ta dinga lalube kwanon babu towo sai yau'kin miya dake biyo hannunta, Hawaye suka sake kufce mata! miyar ta shiga sud'a tana kuka da adduar Allah ya fitar da ita daga cikin wannan 'kangi na masifa, tana jin babanta da Gaje suna hira ta kasa kunnanta sosai Taji suna ambatar sunan mutumin da tayi masifar tsana a rayuwarta, Alhaji Bawa Mai kalwa! Sunansa kadai taji gabanta faduwa yake yi! ta tsaneshi dan iskan tsoho ne! yafi a 'kirga yana tare ta a rafi yana so yayi lalata da ita, da kyar take tsira daga hannunsa, tunda tagane sai ta sauya hanya ta daina bi ta inda zai ganta, kafin ta dawo daga tunaninta taji babanta na fad'in" Wallahi kuwa Gaje wani hanin ga Allah baiwa ne maigari na tabbatar min da cewar yaronsa ba zai aureta ba sai kawai Alhaji Bawa yace shi zai aureta a take ya bada sadakinsa dubu bakwai ga dubu biyar na bada la'adar dubu biyu a fada." Gaje ta rangwad'a bud'a tana fad'in "Yanzu naji magana Malam kace kwana biyu zamu daina rashin abinci Alhaji Bawa mai kalwa shine ya bada sadakin Asiya kai naji dadin wannan lamari wallahi mutumin nan ya taimakemu sosai da ya rufa mana asiri! Asiya tayi dacan miji." Mai shaniya yasa dariya yana fad'in "Wallahi kuwa ni sai nafi son ma ta auri Alhaji Bawa din kan ta auri Isma'il din, a gaskiya naji dadi kwarai da shawarwarin da kike bani." Cikin makirci tace"Haba Malam Asiya fa 'yata ce kada kaji komai." Asiya tsame hannunta tayi daga cikin kwanon miyar da take lasa, gabanta ya shiga faduwa, jikinta yayi sanyi! Babanta ne ya bada auranta ga Alhaji Bawa, wannan mugun mutumin tsoho mai mugun son kansa, mugu mai zalintar iyalansa, kaf garin babu wanda bai san abinda yake ba, auri saki yake yi 'yaya a gidansa sunfi hamsin ko wanne da uwarsa, me yasa babanta zaiyi mata irin wannan auran? a take zuciyarta tace"Kwadayi ne ya jawo da kuma bin shawarar matarsa gaje! Hawaye ya wanke mata fuska! a fili gaje na nunawa babanta tana kaunarta amma a bayan idonsa tayi ta azabtar da ita, gashi dai yanzu 'kiri-kiri ta bata abincin a gabansa! shi zai dauka da gaske abincin ne ashe ita tasan abinda ke cikin kwanon, bata ta'ba kukan maraici ba irin yau! tabbas da mahaifiyarta na raye ba zata bari ayi mata irin wannan auran ba, 'Dan kwanciya tayi gefan tabarmarta tana kuka da tunanin irin rayuwar da zatayi a gidan Alhaji Bawa da manyan matansa da sukayi jika da ita da kuma garadan samarin 'yayansa. **** Garau! ya tashi a sakamakon shan tablet din da Dr Hisham ya bashi jiya ya dan samu sassauci, ya sauko 'kasa cikin shirin fita ofis, as'usul yana sanye da 'kananun kayan Jins da t_shart mai karamin hannu fara tas da ita da adon heart baki a gaban rigar, sai yayi amfani da f-cap 'baka takalminshi booth baki hannunsa daure da agogon fata shima baki, yayi kyau sosai sai kamshin turare yake yi, kyakykyawar fatarshi tayi luf luf sai daukar ido, take Hafeez ba fari bane amma kalar fatarsa nada wahalar samu dan ko ke mace kikayi dace da irin fatarsa to zakiyi farin ciki kuma kiyi tun 'kaho, yana da wani irin karamin baki mai daukar hankali da siririyar fuska kana yana da manyan idanu maidaidaita masu tsananin daukar hankali, bai da fara'a sosai kuma baya shiga abinda bai shafeshi ba, yana da masifar tsabta da kuma son kamshi, baya kuma ya son raini shiyasa ma bai fiye tara abokai barkatai ba, aminansa Isha'ik da Huzaifa da suka taso tare sukayi komai na rayuwarsu a tare dasu kawai yake sakewa, wannan abotakar tasu har iyayensu sun san da ita......Daning ya samesu suna break fast, tun kafin ya karaso Farhana dake cikin shirin tayi skull take dariya, Tace."Mommy kinga bro yaji sauki gaskiya Dady Dactor Hisham yasan aikinsa." Prof dake goge bakinsa da tissue ya dan kalli Hafeez din dake gyara kujera domin zama, cikin zuciyarsa yace dama ai cutar tashi ta karya ce idan gaskiya ne ai bai ci ace ya warware hakaba." A zahiri kuwa cewa yayi shiyasa ai na kasa rabuwa dashi Hisham yasan aikinsa." Hafeez na zama ya kai mata rankwashi a kanta yana shan kunu yace."Kin zama magulmaciya ko."? Dariya takeyi tace"Allah bro kamar bai kaine jiya kake mur'kususu ba." Yace."Shiyasa naga kina kuka ko." Tace"Tausayi ka bani." Murmushi yayi yana girgiza kansa, ya kalli mahaifin nashi dake sakin murmushi yana kallonsa yace"Dady barka da asubah." Professor Ali yace."Barka dai ka tashi lafiya ya 'karfin jiki."? Yace."Daddy jiki yayi sauki." Mommy tace"Myson ka warware tunda gashi kayi shiri da alama yau ofis zakaje ko."? Yace."Eh Mommy yau Daddy ya zauna zanje na kula masa da companynsa." Professor Ali yayi mirmushi mai kayatarwa yace."Zan zauna a gida amma zuwa karfe goma sha biyu zaka iya ganina domun nazo naga yanda kake huld'a da jama'a da kuma ma'aikatan gurin." Ajiyar zuciya ya sauke yace."To shikkenan Daddy da naso ka huta a gida tau kada kaji shakkar komai zan tafiyar da harkokinka." Professor Yace."Shikkenan xan zauna kamar yanda ka bukata din, amma idan naga kuskure ranka zai 'baci."! Murmushi yayi yace."Insha Allah sai dai a samu cigaba." Mommy ta hada masa break ya soma karyawa suna hira cikin nutsuwa har ya kammala, ya mi'ke a nitse hannu ya mikawa mahaifin nashi sukayi sallama, yace."Mommy sai na dawo." Tace."Myson Allah ya tsare." Yana kokarin fita ya amsa da "ameen Mommy." Farhana na gama break fast tayi musu sallama itama ta wuce skull Farhana na level 1 a jami'ar bayero, jami'ar da mahaifinta ya koyar kenan yanzu shekarunsa bakwai da yin Ritare a jami'ar sai kawai ya bud'e wani katafaran company mai suna *ALIYU ADAHAMA MOTORS AND SPIRE PARTS* Kyawawan motoci da babura kekuna masu kyau da tsada yake saukewa a company shi duk kalar motar da kake so zaka sameta cikin sauki da rahusa, company na dauke da ma'aikata kusan hamsin da suke ci a 'karkashinsa, komai na tafiya cikin tsari da wayewar kai, dan har 'kanun company na zuwa sarin kaya company ya basu cikin sauki da inganci, ma'aikatan company yawancinsu cristan ne da kwarori hausawan cikinsu kadan ne, suna aiki cikin tsari da ilimi dukaninsu da uniporm dinsu mai dauke da sunan company a jiki. Tunda ya shiga cikin company ake bashi girma, ya dinga binsu a hankali a hankali suna gaisawa, kafi ya shiga ofis din mahaifin nashi, yana zama sakatare ya shigo da wasu takardu ya ajiye masa a gabansa, yace."Sir yauwa ka duba takardun sosai agreement ne da company yayi da mutum biyu zasu zo daukar kayan to sun bada rabin kudin.......Kafin ya 'karasa ya d'aga masa hannu yana d'an juyi kan kujerar ya cire c-cap din kanshi ya aje yace."Kaje kawai zan duba koma menene ok."? Sakatare yace."Okey Sir." Fita yayi da sauri. Shi.kuma ya gyara zamanshi a jawo takardun yana dubawa, gashinan kamar dai yanda ya fada din hakane, mutane biyu zasu dauki kaya masu yawa kana kuma zasu bada sauran kudin....Ya ajiye takardun yana cigaba da duba wasu...........Turo 'kofar ofis d'in akayi, ya dan d'aga kansa a hankali yana kallon me shigowa, Titi ce ta shigo ofis din cikin kayan aiki riga iya gwiwa da karamin hannu wuyan rigar mai kwala kirjinta ya matse sosai 'katun-'katun nonowanta duk sunyo waje ta saman rigar ga cinyoyinta sai daukar ido sukeyi dake titi fara ce kal! kuma tana da kyau da diri gajera ce me fad'in 'kugu had'e da mazaunai masu fizgar hankali uwa uba na shanu da sukaso suyi mata yawa, gata da bala'in tsafta da gyara jikinta, Sauri dauke kansa yayi daga kanta gabansa na wani irin fad'uwa! Titi ta 'karaso gurinsa, ta d'an risina "Good morning Sir." Ba tare da ya d'ago kansa ba yace."Morning.'' Cikin turanci tace"Sir kana bukatar Coffe ne."? Ya d'an kalleta yana juyi cikin kujera, Yace."Jeki kawo." Titi ta juya da sauri tana mur'kuda mazaunanta, gigicewa yay da sauri ya mi'ke tsaye! yana safa da marwa a ofis d'in! Titi ta dawo ofis d'in hannunta rike da wani tire dauke coffe din a kai...... A nutse ya koma ya zauna kan kujerarsa, ita kuma ta karasa kusa dashi..."Sir gashi." Tafad'a tana d'an rankwafawa, nonowanta suka fito sosai, ya lumshe idonsa tare da tura lips d'inshi masu duhu a bakinsa, yana bud'e idonsa ya zube a kanta, a take ta fahimci halin da yake ciki domin dai lokaci 'kan'kani duk ya sauya idanunsa sunyi jawur kuma sun d'an risina ga fatar saman goshinsa ta wani tattare.! Mirmushi tayi tace."Sir ko na d'ebe maka kewa ne."? Ya tsira mata idonsa yana kallonta tare da nazarin maganarta, Titi ta zagaya inda yake zaune ta zuba hannayeta a jikinsa tana shashshafa jikinsa tare da sakar masa kesses a fuskarsa, Hannunsa ya d'ora saman nononta ya latsa! ta wani gantsare tana dariya, ya 'kan'kance ido yana tsuke mata 'karamin bakinsa yace."Kin ta'ba yin sex."? Girgiza kanta tayi tana shafa lafiyayyar sumar kanshi tace"No ban ta'bayi ba Sir saboda ina tattalin budurcina nafi so na mallakashi ga mijina amma saboda yanda nake kaunarka zan iya mallaka maka kaina." Wani killer smile yayi ya d'an d'ora fuskarsa saman nonon nata yasa harshe ya lasa a hankali yace."Dai-dai kenan! ni mutum ne mai 'kyan'kyami! kin bani sha'awa sosai kuma tsarin hallitar da Allah yayi miki ya burgini zanso naji yanda kike amma me kika tanadar min."? Titi ta ri'ke kansa dake saman 'kirjinta tana shafa sajensa tace"Sir zan jiyar da kai dad'in da baka ta'ba ji ba."! Ya d'ago kansa yana kallonta da wani irin mirmushi a fuskarsa, yace."Okey tashi tu'be kayan jikinki amma kafin nan jeki murza key a kofa." Titi ta wuce da sauri ta kulle 'kofar ofis d'in, tun daga bakin kofar ta sabu'le rigar, daga ita sai brez da pant ta 'karaso inda yake, suma tana zuwa ta ciresu tayi tik da ita, Gabansa ya wani mi'ke! ya 'kankance idanunsa, yana sauke wata irin zazzafar ajiyar zuciya ya mi'ke! hannunta ya ri'ke suka nufi wata shirgegiyar kujera me kamar gado dake ofis d'in ya kwantar da ita, Titi ta kwanta sosai had'e da bud'e masa kafafunta, blet d'in jikinsa ya shiga kwancewa idanunsa kuri kan brest din titi ya zare wandon joystick dinshi tayi tsalle ta fito, a d'imauce! titi ta mi'ke zaune! ta kama joystick din da hannuwa biyu ta shiga shafawa tana lasa da harshenta, Nishi ya shiga saukewa yana shafa kitson attachment din dake kanta, Sosai Titi Take sucking dinshi yana sakin wani irin ihu! da gurnani, ya d'inga marmatsa nonowanta, yana sake tura mata a bakinta, Kwantar da ita yayi ya hau kanta ya rike joystick d'inshi da hannunsa ya wage kafafunta da karfin gaske yake kokarin shigarta, yana nishi! da cizar lips titi ta daure sosai ta bashi had'in kai har ya rasta jikinta, yana jinsa cikin wata duniya ta daban! ya rasa nutsuwarsa gabakidaya wani irin ci yakewa Titi na fitar hankali. GA DUK MAI BUKATAR KARANTA BOOK D'IN ZAI TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN..... 0542382124.......BINTA UMAR GTBAN.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURO KI SAMENI TA WANNAN NUMBARS........07084653262......ZANYI MIKI BAYANIN YANDA ZAKI TURA *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *DAN ALLAH IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK DIN NAN ZAKIYI BA KADA KI KIRANI KO KI MIN WATA MAGANA* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR* WhatsApp *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* **Free Pege6* Ganin yanda yake hak'arta yana bugunta da wani mugun 'karfi! ya sanya ta sare da al'marin sai ta soma kokirin kwatar kanta ihu!! takeyi azabah ta isheta, ya d'amke mata bakinta da tafin hannunsa guda daya yabi ya ma'kal'kaleta a jikin kujerar yana gurnani had'e da zufa sai sukuwa yake kan yarinyar mutane! Titi taga jaraba da masifa kuka takeyi wiwi tana bashi hakuri da fad'in kada ya yaga ta tsananin azabar da ta takeji a gurin ta sanya ma'kogwaronta bushewa, Hafeez kam! baya ji baya gani ya zama mayan 'karfe a jikin ta, kuka yakeyi yana fad'in "Dady ka cuceni ashe haka wannan al'amari yake da dad'i! Inaaa! sam! wallahi bazai yiwu ba kai kullum kana kwasar dad'i ni ka hanani.'! Sambatun surutan da yake yi kenan yana sake zurkudawa Titi jijiyarsa wacce takejin ta har cikin cikinta. Sakatare ne tsaye a bakin kofar ofis din yana dan dubbugawa da Fadin " Sir ba'kin nan fa sun zo suna jiran su shigo ku tattauna." Shuru yaji yaja kofar yaji a kulle, sai ya koma ya zauna gurin zamanshi yana d'an kallon ba'kin dake zaune kan kujera, yace."Dan Allah kuyi hakuri mybe yana wani uziri ne ko yana toilet amma bari na sake kiran wayarshi." Daya daga cikinsu yace."Wai shin baka fad'a masa zuwan mu bane? duba fa munfi karfin awa guda zaune a gurin nan muna zaman jiransa, shiyasa kwata kwata bana so hurd'a ta had'ani da yaron sam bai iya mu'amulah ba." Sakatare yace.",Afuwa Alhaji wallahi na fada masa ina tunanin dai ko bacci yake yi." Daya mutumin yaja siririn tsaki yana fad'in" Okey bacci yazo yi kenan ba aiki ba, babu shakka watarana yaron nan zai rusa muku company mutukar yallabai zai dinga d'orashi kan harkokinsa." Sakatare dai shiru yayi yana cigaba da trying d'in numbar Hafeez d'in gashi tana shiga amma ya'ki d'agawa! Ya d'an dago kansa yana kallonsu jikinsa yayi sanyi saboda yasan sunji wayar na shiga amma ba'a dauka ba. Alhaji Manu ya mi'ke tsaye ransa a 'bace! ya mi'kawa na kusa dashi hannu yace."Ni ina da abinyi alhaji yaron nan wulakanci yaso yayi mana dama ya an gama magana komai nasa hannu na biya kudi kuma azo a 'bata min rai! a ba kyauta nace a bani ba, saboda haka ni zan tafi harkokina dik sanda yaga dama ya bude ofis din shi ya sani." Alhaji Dantani ya mike shima yana bige babbar rigarsa yace."Nima harkokina na bari nazo domin cika alkawari saboda haka yanzu zan kira Yallabai din shaida masa abinda ke faruwa." Sakatare yace." Kuyi hakuri mana ku dan jira Alhaji." Suka watsa masa wani kallo suka fita daga gurin ransu a mugun 'bace! Sakatare ya koma ya zauna shima nasa ran a 'bace! Lallai babu shakka Hafeez idan haka yace zai dinga yi to kaf sai ya kori costumes dinsu dake rububin zuwa daukar kaya, shin wai me ma yake yi ne a ofis d'in.? Can ya tuno Ai Titi ta shiga ofis din tunda ta shiga kai masa Cofee bata fito ba, yayi jim yana tunani babu shakka biri yayi kama da mutum to amma ai yana zaune a gurin zaiga da idon da Titi zata kalleshi. Professor Hankalinsa yayi masifar tashi da jin bayanin da Alhaji Dantani yayi masa, a hanzarce ya shiga kiran numbar Hafeez sai dai ya kira sau kusan goma bai daga ba, ya sauko 'kasa inda Mommy ke zaune ita da Farhana ya shiga sirfa bala'i ta inda yake shiga batanan yake fita ba, yana fad'a mata irin aika aikar da Hafeez din yaje yayi masa a Company. Mommy hankalinta ya tashi itama ta shiga kiran wayarsa sau ba'adadi bai daga ba. Professor yace."Kinga ni ko? kinga abinda nake fad'a miki ko? Hafeez ni zai kassara ya rusa min harkokina, kamar gaske ya shirya yace in zauna a gida zai kula min da harkokina ashe karya yakeyi muhiman mutane zasu zo a gana dasu ya yayi musu wulakanci yana cin ofis ya'ki sauransu, ai dama na fad'a miki yaron ba zai ta'ba hankali ba."! Murya na rawa Mommy tace."Yallabai kayi hakuri dan Allah ka kwantar da hankalinka kabi komai a tsanake mybe akwai wani abu da yake faruwa, ni nafi zargin ko ciwonsa ne ya dawo ya sanya bai sauraresu kaga ma ko waya ya kasa dauka dan Allah ka kwantar da hankalinka." Ai sai ya shiga bambami! yana fad'in" Ai dama tuntuni nasani duk wani abu da Hafeez keyi kece kike zugashi da har zakice na kwantar da hankalina kwata kwata yaron nan be da gaskiya, aure yake so nayi mishi billahillazi banza masa aure yanzu ba dan baiyi hankalin da zai iya jagoranta wani ba, ni ban haifi d'an da zai sauya min a'kidata ba." Mommy ta soma kuka tana fad'in "Ya zaka ce nice nake sanya shi yayi abinda ya ga dama, nice fa na haifeshi zanfi kowa son ya shiryu, kada kayi masa baki kai mahaifinsa, ne kuma ni banga laifinsa ba dan ya bukaci aure tunda ya kai munzali." Tace."To ke dashi sai ku tursasani nayi abinda kuke so zan gani ni ko ku."!!!! Yana gama maganarsa ya haura sama a mugun fusace! Murya na rawa Farhana tace"Mommy dan Allah ki daina hawaye idan da sabo kin saba da wannan hayaniyar ta Daddy shi komai a laifi yake ni wallahi bana so naga yana miki masifa." Mommy ta girgiza kanta tana share fuska tace"Farhana Daddynku yayi lafiya ai da yafi zafi Kinsan duk mai suna Ali yana da zafi da a'kida." Kafin Farhana tace komai ya sauka, cikin shirin fita, yasha farin gilashi, ko kallonsu baiyi ba ya kama hanya zai fita, Farhana tace"Daddy a dawo lafiya." Ko kallonta baiyi ba ya fita daga palon. Hafeez bai san iyaya a dadin kawowar da yayi a kan Titi ba sosai ya suburbudeta tamkar ba budurwa, sai da ya tabbatar da tayi gamsuwar da yake bukata sannan ya sauka daga kanta, Ita dashi duk sunyi wujiga wujiga, Titi fuskarta duk jirwayen hawaye kwarmin idanunta ya zurma sai kuka takeyi gabanta duk ya tsage! wannan wace irin masifa ce yau ta afka, da kyar ta jawo rigarta ta fara kokarin sakawa, Ya dinga kallonta yana tausaya mata shi kansa yasan ya azabtar da ita sai shima bada son ransa bane! Rigar ya kar'ba ya zura mata yana goge mata hawaye, miryarta na rawa tace"Sir zaka aureni."? Ya dago kansa da sauri yana kallonta, "Zaka aureni."? Ya sake maimaita tambayarta, shuru yay mata yana d'an tsuke 'karamin bakinsa, bashi da tacewa wai 'barawo a hannu mata, Tace" Nasan ba zaka aminci ka aureni ba, yanzu shikkenan na rasa abu mai mahimanci a rayuwata."! Sai kawai ta fashe da kuka." Yaji tausayinta sosai ya dan rungumeta a jikinsa, "Stop Crying bab, ki daina kuka kinji ko! nasan kinyi min adalaci a rayuwa kin farfad'o dani daga fad'awa wani 'kangi kuma nasan wannan abun naki da kika mallaka min mai daraja ne da girma, nayi miki alkawarin daukar dukkanin laluranki zan baki kudi sosai zan sauya miki mota duk abinda kike bukata ki tambayeni zanyi miki mutukar kudi na magani." Girgiza kanta ta shigayi tana goge fuskarta tace"Ni daina nafi so ka aureni." Yaji wani fad'uwar gaba sam! baya so tana wannan furucin D'an had'e rai yayi yace."Baby kin manta addinina da naki ya bambanta bana jin zan iya auranki."! Tace."In dai zaka amince ni zan muslunta saboda kai ina sonka sosai shiyasa ma na mallaka maka jikina." Jim! yay yana nazari yace."okey zanyi tunani kada ki damu, sannan ka bana so kowa yasan mu'amular dake tsakaninmu." Titi tayi murmushi tana jin sanyi a ranta ta amince mutukar zai aureta zata musulunta koda kuwa kaf danginta zasu gujeta.....Tace"Yanzu zanje gida in huta in gasa jikina ne." Mikewa yayi yana fad'in "Bari nayi wanka na fito ko." Ta daga masa kai, tana kallonsa ya shiga toilet a gurguje yay wanka ya fito ya goge jikinsa ya mai da kayansa, Lokacin itama ta dan 'kokarta ta kimtsa jikinta, ya bud'e 'kofar ofis d'in suka fito a tare, wanda yay dai-dai da shigowar Professor gurin.........Kafatanin ma'aikatan dake gurin suka mi'ke suna masa barka da zuwa, hankalinsu duk ya dauke a kansa, hakan ya bawa Titi damar silalewa ta fice da saurin gaske! dama tana ta tunanin ya za'ayi ta fito su ganta, Professor hankalinsa na ofis dinshi bai wani tsaya sauraran su ba, ya nufi ofis d'in Hafeez ya bishi da kallo cikin tsananin rud'u da tashin hankali, a duk sa'ilin da yaga irin wannan fuskar daga gurin mahaifinshi to babu shakka yana cikin tsananin 'bacin rai! Bayansa yabi da sauri! sai suka buga karo, Yace."Daddy da kan........! Kafin ya 'karasa ya wanke shi sa lafiyayyan mari! Allah yasa ba'a gaban jama'a bane cikin ofis din ne. Yana huci! yace."Kayi dai-dai! nace abinda kayi yayi kyau! kuma yayi dai-dai! ashe kai munafiki ne Hafeez."!? Yakarashe maganar yana nunashi da yatsa. Hafeez ya sunkuyar da kansa 'kasa, yana tunanin abinda ya janyo wannan tashin hankalin! da sauri ya d'ago kansa yana kallon mahaifin nasa dan ya tuno komai, saurin mayar da kansa kas yayi ganin yana idanun Mahaifin nasa sukayi jajawur jijiyar kansa tayi rad'a!-rad'a! Professor Ali mugun masifaffan mutum ne.!!!! A hankali yace."Daddy kayi min afuwa dan Allah wallahi tunda na shigo ofis din nan jikina ya sake rikicewa kwanciya nayi bayan na d'an sha magani bacci me nauyi ya daukeni ,sai yanzu na farka naga miss call dinka." Ya nuna shi da yatsa yana fad'in" Bana son rainin hankali Hafeez ni bazan dauki wannan shashancin naka ba wallahi! wato dama bacci kazo kayi min a ofis ba aiki ba? kamar gaske ka dakatar dani da zuwa kace zaka tsaya min kan al'amura sai kazo ka kwanta bacci!? Kullum idan na kiraka, mara hankali da iya mu'amula ka nuna 'bacin ranka, kana shigowa ofis din nan Sakatare ya shaida maka abinda keda akwai, mutanan nan da mutukar mahimanci a garemu kuma tsofaffin abokan cinikayyarmu ne, manyan mutane kaiwa irin wannan wulakancin ka ajiyesu ayi ta kiran wayarka ka'ki d'agawa."!! "Daddy bani da kuzarin d'auka waya a lokacin ni bacci ma fa nake ka dubi yanayi na da kyau ban jima da tashi ba wallahi." Professor yaja wani matsiyacin tsaki ya juya ya nufi kujerar zamanshi wayarsa ya dauko ya shiga laluben numbobin su Alhaji Dantani.....Hafeez ya dan ta'be tsukakken bakinsa a sace ya kalleshi ya d'aga kafad'arsa ya juya ya fita daga ofis d'in, yana fita yaci mur! ya daure fuskarsa sosai Sakatare nata so yayi masa magana yaga babu fuska, sai yaja bakinsa yay shuru yana fadin "A sauka lafiya." Hannu kawai ya daga masa wuce. ***** Washe gari Asiya ta tashi da wani irin ciwon kai mai tsanani hakan bai hanata yin duk wani aikace aikacen da takeyi a gidan ba sai da ta gama ayyukanta tukkuna Gaje ta mi'ko mata wani karamin kofi da ruwan kunu a ciki tsalala! babu sugar. Asiya ta kafa kai kur'ba uku tayi masa ta shanye tasa hannu ta katse ragowar ta sud'e, taje ta d'auraye kofin ta kife a kwando, da sauri ta dauki tulu ta nufi rafi domin jidon ruwa. Sai da ta cika ko ina na gidan da ruwa kana ta ajiye tulun ta zuba ruwa zatayi wanka Gaje ta fito daga daki tana harararta tace"Kina dai da sabulu ko."? Cikin tausayawa kanta tace"Bani dashi." Gaje tace"To sai kiyi da ruwa, dan baxan baki sabulana ba ki 'karar mun dashi gurun gurzar wannan annakiyar daudar ta jikinki." Asiya ta dauki karamin bokiti da ruwa ta shiga bandakin ta wawwatsa a jikinta ta fito tana wani mai'ko kaf daudar dake jikinta ta tashi a sakamakon zubawa jikinta ruwa da tayi, ita kanta tasan tana wari! haka dai ta shiga dakinta ta kwance 'kullin kayanta ta d'auki wani kod'addan lesi wanda take kwalliyar juma'a dashi tana shirin sakawa a jikinta, lalurarta ta tashi, zama tayi ta bude kafafunta ta shiga kartar gabanta da hannu bibbiyu tana lumshe idonta, sai da ta sosa iya son ranta sannan ta hakura aikuwa fatar gurin ta d'auka d'au! ta dinga yi mata zafi da rad'adi! Kuka tasa tana wage kafarta ta kasa saka wando saboda axaba. Mai shaniya ya shigo gidan cike da farin ciki yana fad'in "Gaje kina ina ne? ina Asiya maza ga Alhaji mijinta yazo su gana." Gaje ta fito daga daki tana fadin "Ganinan malam to lale maraba sannunsa da zuwa aikuwa anci sa'a yanzu naga tayi wanka bari na shiga na fada mata ta fito." Gaje ta nufi dakin Asiya tana fadin"Alhaji Bawa attajirin gari ai mu kakarmu ta yanke sa'ka." Tana d'aga buhun d'akin taga Asiya zaune dirshan babu kaya a jikinta ta bud'e kafafunsa tana kuka. Gaje ta rafka salati! wanda ya dawo da Asiyar hankalinta a gigice! ta zabura ta mi'ke tana neman zani ta rufe jikinta, Mai shaniya ya shiga dakin da sauri yana fad'in "Lafiya menene."? Gaje tace" Mallam ni naga abinda nagani! O! duniya ina zaki damu? yarinyar nan da kanta take biyawa kanta bu'kata shigowa nayi naga ta bud'e kafafunta tana 'kwa'kular gabanta wannan wace irin jaraba ce."! Tana kuka wiwi! tace"A'a Baba ba haka bane wallahi gurin ne keyi min zafi shine na bude domin yasha isk......Kafin ta karasa Mai shaniya ya buge mata baki, yana fadin"Karya zatayi miki? ai ni duk abinda akace kinyi bazan musa ba, tunda aure kike so ai shi zanyi miki kada ki jawo min abun kunya." Gaje tace"Shine yafi alkairi a gareta." Yace"Dan ubanki yi maza ki saka kaya Alhaji Bawa na zaure yana jiranki." Da sauri tasa kayanta tana hawaye, suka fita daga dakin Gaje na fadin "Ai halin uwarta ta tsotsa haka Mariya ma tayi tashen jaraba a gidan nan." Mai shaniya dai waje yayi yaje yana d'ebewa Alhaji Bawa Kewa kafin Asiyan ta fito. Pls kuyi Sharing👏🏻 *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCOUNT DIN......0542382124........BINTA UMAR GTBANK.........A TURA SHAIDA TA WANNAN NUMBAR....07084653262.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR....07084653262 ZANYI MIKI BAYANIN YANDA ZAKI BIYA.* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR KARANTA BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK DIN NAN ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBARTA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MAI BUKATAR SHIGA VIP GRUOP SAI YAYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege7* Jikinta a sanyaye ta fito tana 'boye hannayenta cikin wani mayafi data yafe tattararre sai kace abun tatar koko dik ya lalace ya yamutse wasu guraran na jikinsa ma ya yage, Gaje ta bita da wani irin kallo tana murmushi Allah Allah takeyi ayi auran nan tasan matan Alhaji Bawa basu da Imani ga manyan 'yayansa maza duk marasa kunya ne tasan tilas tasha wuya dasu, a hankali take tafiya har ta isa soron kanta a 'kasa, Mai shaniya na ganinta ya washe baki yana fad'in Alaji ai gatanan ta fito." Alaji Bawa ya wani 'kure ta da ido yana washe shegun hakoransa wando suka rine, yace."To to! ai sai ka bamu guri ko." Mai shaniya yayi saurin ficewa daga gidan yana fad'in "Alaji a sauka lafiya." Alaji Bawa bai samu damar amsa masa ba kaf hankalinsa na kan Asiya dake tsaye kanta a 'kasa. Ya matso kusa da ita a hankali yana dariya wacce tayi masifar 'kara masa muni yace."Asiya 'yan matana ina fatan kinji abinda ke faruwa tsakanina dake ko? yau kwanaki biyu kenan mahaifinki ya kar'bi sadakin auranki a hannuna yanzu ke a matsayin matata kike sosai naji dad'in wannan al'amari dama na dade ina sonki dan duk wasu alamu na nuna kuma na tabbata kema kin fahimta." Yakarasa maganarshi yana sake nani'karta, da sauri ta matsa gefe guda tana 'bata rai! Yace."Tauraruwar zuciyata banji kince komai kiyi magana kinji ko ina so naji ta bankin ki." Ta dago kanta a fusace! tana watsa masa manyan fararan idonta tace"Ni bana sonka."! Alaji bawa yayi wani murmushi na takaici yace."Asiya yanzu ai duk maganar so ta kare tunda na bada sadaki saura kwana uku daurin aure ki soni ko kada ki soni be dameni ba, nan gaba kadan nasan zaki soni ki saki jikinki dani na nuna miki zahirin kauna." Kallonsa takeyi tana jin zuciyarta kamar ta fashe! ba ita ba ma tana jin ya haifi babarta 'karewa ma tsofai tsofai dashi yazo yana maganar yara ko kunya baiji ba, dik wani girma da mutuncinsa ya zube a idonta wani irin mugun haushinsa takeji, Tace."Yanzu bakaji kunya ba zaka ce zaka aureni nifa a matsayin jika nake gurinka." Alaji bawa ya shafa gemunsa wanda ke cike da furfura yace"Yaro dai yaro ne Asiya wanene ya fad'a miki ana jin kunya gurin neman aure? ni banji wani kunya ba tunda sinnar ma'aiki nake so na raya, na kuma taimakeki a lokacin da kowa ke gudunki." Tace"Alaji kada kasa na zageka wallahi na tsaneka me zanyi da kai! bana son taimakon ni da na aureka gwara nayi ta zama babu aure kuma wallahi ka sake ka aureni nice ajalinka." Alaji Bawa ya bude bakinsa yana kallonta cike da mamaki yace."Lallai Asiya kuruciya na damunki, ban dauka za'a samu matsala da ta bangaranki ba, to ki bude kunnanki da kyau kiji ni Alaji Bawa sai na aureki wallahi koda kuwa zaki zama ajalina." Asiya ta fashe da kuka tana ji kamar taje ta sha'ke masa wuya Alaji Bawa maye ne wallahi! Ganin tana kuka sai hankalinsa ya tashi ya karasa inda take yana kokarin rungumota tayi gaggawar kaucewa, ya wani had'iyi miyau! yana kallon 'yan nonowanta da suka soma girma ya kai hannunsa zai shafasu da sauri ta buge hannunsa jikinta na wani irin rawa! take kokarin shiga gidan, ya riko gyalenta, wuyanta a shake tilas ta tsaya domun ta gyara wannan damar Alaji Bawa ya samu ya rungumeta ta baya ya zuba dukanin hannuwansa kan nonowanta yana murzawa! Asiya tasa kuka tana tureshi, yana sake ru'kun'kumeta a jikinsa so yake ma ya cusa ta cikin katuwar babbar rigarsa yanda zaiji dad'in ligwigwitata, ita kuma ta'ki bashi dama sai kuka takeyi tana cire hannunsa dake nononta wanda ke mata zafi sakamakon murzawa da yakeyi......Hannunsa guda ta gartsawa cizo aikuwa ya saketa da sauri yana dubawa hannunsa har ya huje ga jini nan ya fito, ta kalleshi taga duk ya wani burkice idanunsa sun sauya, tace"Azzalimin tsoho makiri ta Allah ba taka ba, insha Allah Allah sai ya bimin hakkina."! Tana gama maganarta ta shige gida da sauri! Allah yasa Gaje na 'kuryar dakinta, zama tayi kan shimfidarta ta hada kanta da gwiwa tana wani irin kuka mai tsuma zuciya. Alaji Bawa kuwa kwata'kes! yayi yana kallon Guri guda tsafar shiga rud'u da tashin hankali kamar wannan 'yar ficiciyar yarinyar ce ke zaginsa, lallai dole ya dauki tsatstsauran mataki a kanta tunda bata da kunya, Gaban babbar rigarsa ya kalla yaga yanda katuwar jijiyarsa ta kumburo kamar zata fito waje! Jingina yayi da jikin bango (garu) yana sakin nishi da ajiyar zuciya! wata irin muguwar sha'awar yarinyar ce ke taso masa, dole ne ma a dawo da daurin auran gobe domin ya samu biyan bukatarsa. Fita yayi daga zauran yana baza babbar rigarsa duk dan kada jama'a su fahimci abinda ke faruwa dashi, sai washe baki yake yana amsawa gaisuwar jama'ar dake gasheshi, Yana isa gidansa, ya shiga yana 'bata fuska matayensa da wasu daga cikin 'yayansa suna zaune cikin wata katuwar rumfa mai mugun tsayi da fad'i, dakuna takwas ne a cikin rumfar, kowa jikinsa na rawa yake masa sannu da zuwa, babu wanda ya amsawa a cikinsu sai ya watsa musu harara yake yi, idanunsa yake rarrabawa kan matayen nasa, ko wacce ta sunkuyar da kanta 'kasa gabanta na faduwa babu shakka tunda suka ga mijin nasu ya shigo da irin wannan fuskar to an 'bata masa rai ne! Ya sauke idonsa kan Larai dake bawa d'an 'karamin d'anta nono yace."Larai." da sauri ta d'ago kanta tana kallonsa, "Na sake ki saki uku."! Larai ta fasa wani irin ihu! tana dora hannunta aka tace" Alaji me ya faru? me nayi maka ka sakeni saki har uku! ina zan kai 'yayana."? Ya gya babbar rigarsa yana harararta yace."Sai kin yi min wani abu zan sakeki nine nayi niyyar sakinki saboda zan maye gurbinki da yarinya 'kan'kanuwa Asiya 'yar gidan Mai shaniya, sannan kina maganar 'yaya ki aje min 'yayana ki 'kara gaba dama ke kad'ai kika zo." Larai ta dinga rafsa ihu tana fad'in "Alaji ka cuceni wallahi Allah sai ya saka mun, sai da ka bari na saki jikina da kai na haihu har sau uku sannan zaka rabani da 'yayana."! Alaji Bawa Ya buge babbar rigarsa ya juya zai fita, Hansatu Uwar gidansa itace bata jin shakkarsa sosai saboda ita ko ya saketa bata fita itace kume keda manya 'yaya a gidan tace wallahi ba zata fita ba zaman 'yayanta take haka yayi hakuri ya kyaleta dan Hansatu masifaffiya ce, Tace" Yanzu kai Alaji ko kunya bakaji ba kazo kana fad'in zaka auri jikanyarka dan Wannan yarinyar sai dai kayi jika da ita wallahi Alaji Bawa kaji kunya budurwar zuciyarka na bani mamaki wai wane irin abu kake nema ne yanzu kaci zamaninka kuma kace dole sai kaci na wani."! Yace."Ai Hansatu ba zaki gane ba tunda ke yanzu kin zama galli ga horo har ni zaki cewa mai nake nema yanzu, to bari kiji jin dadi da nutsuwa nake nema shiyasa naje na zab'o yar 'kan'kanuwar yarinya domin in barje gumina dukaninku kun zama taron tsintsiya babu shara ko wacce ta bude kamar bakin rijiya ni kuwa yanzu ne ma nake tashena nake 'kara jina namijin gaske." Yakarasa maganarsa ba tare da yaji kunyar 'yayansa ba dake zaune a gurin. Hansantu tace"To Allah ya kyauta maka ya shiryeka kuma idan zaka shiryu kada kuma ka manta da cewar duk abinda kayi wa dan wani sai anyiwa naka wallahi kaima dai gashinan ka haifa ehee! yanda kake auran 'yayan mutane kana saki kamar ka samu tumakai." Ya wani tura hularsa 'keya yana shafa farin gemunsa yace."Hansatu kanki akeji wai mahaukaci ya fad'a rijiya, ni babu wanda zai hanani jin dad'in rayuwata." Fita yayi ya nufi fada domin ya shaidawa maigari cewar ayi shela a sanar da jama'a gobe ne daurin auransa da Asiya dan ta katifa da ledar daki da labulaye duk zai sha mata baida matsala..... Larai kuwa tana kuka 'yayanta na kuka ta soma hada kayanta su Hansatu na bata hakuri haka ta had'o kayanta cikin ghana masgo ta fito yana fyatar hanci 'yayanta na rirri'keta suna kuka! da kyar su Hansatu suka janyesu ta fita daga gidan cikin bakin ciki da takaicin Alaji Bawa. ***** Hafeez kuwa tun daga ranar da al'amarin nan ya faru Daddynsa ke fushi dashi sosai ya bashi hakuri amma ya'ki hakura ita kanta Mommy sai da tayi masa fad'a irin wanda bata ta'bayi masa irinsa ba, hakuri kawai yake bata yace." Insha Allah hakan ba zai sake faruwa ba. Suna zaune a daining suna karyawa, ya sauko 'kasan palon yana cikin kananun kaya as'usel wando iya gwiwa tree qutar sai t-shart mai karamin hannu ta matse shi sosai kanshi yasha gyara sai kyalli yake yi hade da sajen fuskarshi, a hankali yake karasowa inda suke Professor na ganinsa ya 'bata rai mikewa yayi yana daukar wayoyinsa zai bar gurin dama ya gama break din ya tsaya ne suna magana da Farhana kan karatunta, Hafeez yayi sauri rike hannunshi yana marairaice fuska yace."Daddy wai har yanzu baka hakura ba dan Allah ka daina wannan fushin mana." Professor yace."Ka riga ka gama kaini karshe Hafeez ace kai ba zaka xauna ka kimtsa rayuwarka ba, tun ranar da nayi maka fad'a baka sake zuwa ofis ba wato zuciya kayi kenan." Yace." Daddy naga ka dauki zafi da yawa ne bana son nazo mu sake samun sa'bani gaban mutane shiyasa amma kayi hakuri zan shigo yau." Professor ya d'an ta'be bakinsa yace."Idan kazo kanka kayiwa idan ka zauna ma a gida duk abinda ya shafeka ne ni dai nayi iya abinda zan iya." Hanyar fita ya nufi ya mike da sauri yabi bayanshi yana sake bashi hakuri, da kansa ya bude masa mota ya shiga direbansa ya zauna a mazauninsa yana tsaye har motar ta fita daga gidan sannan ya koma ciki, sam baya son 'bacin ran mahaifin nashi, daining din ya nufa Farhana ta hada mishi break yana tambayarta me yasa bataje skull ba tace"Yau bata da lectures sai gobe, yana break kiran Huzaifa ya shigo wayarshi, suka gaisa Huxaifa yace."Guy yau zanyi tafiya fa zanje can branch dinmu dake legos amma ba zan wani dade ba." Hafeez yace."Okey to my friend Allah ya kiyaye hanya." Huzaifa yace."Guy ka kula min da gida dan Allah da my Wife kwana biyu ma baka zo dinnar ba." Yace."Ba najin dadi kwana biyu shiyasa amma kada ka damu idan na tashi a ofis zan shigo insha Allah." Huzaifa yace."Ayya ai ni mybe ma na sauka a legos dan yanzu shiryawa nakeyi." Yace."Okey zan my friend sai ka dawo kenan." Huzaifa yace."Insha Allah." Kashe wayar sukayi a tare, Hafeez na kur'bar tea yana jin yanda duk tsigar jikinsa ke mi'kewa, kasancewar ya tunano siffofin jikin Safina a take yaji sha'awarta na taso masa, tun ranar da yayi sex da Titi yake jinsa wani sama-sama! daurewa kawai yakeyi saboda bai da mafita Titi na gida tana jinyar kanta ballanta ya kirata ta rage masa zafi, yanzu kuwa dama ce ya samu da zai lalla'ba gidan abokin nashi Ya biya kanshi bukata yanda yake so ba tare da wata fargaba ba, idanunsa ya lumshe yana dan tura lips dinshi a baki ya mi'ke jikinsa a sanyaye zai bar gurun. Mommy tace"Ya ka tashi baka gama break din ba." Yana layi yace."Mommy bana jin zan iya 'karasawa jiri nakeyi da alama ciwona ne zai tashi." Tace"Wai Hafeez wannan wane irin ciwo ne da baya jin magani." Ya kalleta da idanunsa da suka risina yace."Mommy ki tambayi Daddy shi yasan kome ke damuna." Ya juya yana tafiya, tace"To kada dai ka manta kayiwa Daddynku al'kawarin zuwa ofis dan Allah ka daure ka shirya ka tafi." Ya shafa tarin sumar kansa yana dan mutsika goshinsa yace."Mommy koda naje ofis za'a yi abinda bai kamata ba kin san halin daddy bai da hakuri ni kuma ko naje wallahi ba zan wani iya aiki ba a yanda nake jin jikin nan nawa." Mommy tace"To Allah ya sawake amma dai ka kirashi a waya ka fada masa abinda ke faruwa." Murmushin takaici yayi yace."Mommy wallahi bazai yarda ba cewa zaiyi karya nakeyi kawai ki kyaleshi." Mommy tace"Kace kawai yau na shirya tashin hankali a gidan nan dan cewa zaiyu nice na hanaka zuwa." Ta'be 'karamin bakinsa yayi yace."Mommy kada ki saurareshi dan Allah." Mommy ta bude bakinta tana kallonsa cikin mamaki! Sauri sauri yake hayewa sama, ya bude dakinshi ya mai da kofar ya rufe zubewa yayi kan bed yana lumshe idonsa, ajiyar zuciya yake saukewa daki-daki yana matsala pillow da sake rungumeshi a kirjinsa, ya jima jikin wannan halin kafin ya mike da mataccan jiki ya nufi toliet wanka yayi ya fito duk kamaninsa sun sauya Hafeez mugun fitinanne na ina niha! A gurguje ya shiya cikin rigar atampa ja da rashin fari yayi amfani da farin wando jins mai fashashshiyar gwiwa botiran rigar ya saka ya gyara links din hannun rigar ya dauko wani abun wuya ja mai 'kulalai ya saka a wuyansa, agogo ya daura mai kyau da tsada ya fesa turaransa mai kamshi ya dora f_cap dinshi fara kal da ita saman kanshi ya zauna gefan gado yana sanya safa a kafafunshi gabakidaya ya dokanta ds Safina so yake kawai yaje ya dand'anta yaji ita yaya kalar dadinta yake, wani had'addan booth ya saka a kafafunshi mai fari 'kal dashi! Hafeez yayi masifar kyau! sai ka rantse da Allah ba bahaushe bane, duk sanda yayi irin wannan shigar mutane da yawa na shagala gurin kallonshi tanayi masa bala'in kyau! shima sanin da yayi yana kyau yasa yake yawan yin ta, Daddynsa kuwa ya tsani irin shigar duk ranar da yaga yayi irinta bala'i yake masa sosai ya dinga kiransa da kafuri, shi kuwa yayi kunnan uwar shegu dashi Mommy na ganinsa na sakkowa tace"Allah yasa dai ofis din zakaje." Dan ya mutsa fuskarsa yay yace."Eh Zanje amma kafin nan zan danje wani guri." Tace"To Allah ya kiyaye myson ka kula da kanka." Yace."Insha Allah Mommy sai na dawo." Fita yayi cikin wata irin tafiya ta had'ad'dun maza ya nufi parking area wata arniyar Peugeot ya bude ya ya shiga maigadi ya bude masa gate a guje ya fita daga cikin gidan sautin music na tashi ta cikin motar. Pls kuyi sharing *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK DIN NAN ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBARTA KIYI MIN WATA MAGANA* _Muna siyar da less da manya da kananu Materials manya da kananu atampopi manya da kananu shaddodi manya da kananu mayafai masu kyau kalar 'yan birni kayanmu masu kyau ne da sauki! muna bada sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai a ko'ina a kowa ne gari kike za'a kai miki kaya masu sari ku garzayo ku kwashi garabasa hakanan masu siyan da'i-d'ai kuma kada a barku a baya, kayanmu masu kyau ne kuma irin wanda ake yayi zakiyi ficce kiyi zarra cikin 'yan uwanki mata kana kuma kullum maigida na ganinki tamkar sabuwar amarya, Siyan nagari mai da kudi gida_ *Sai kunzo* *IDAN KINA BUKATAR LITTAFIN NAN ZAKI TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.....0542382124.......BINTA* UMAR GTBANK IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA SAI KI SAMENI TA WANNAN NUMBAR.....07084653262.....ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA *MUTANANMU NA NIJAR IDAN KUNA BUKATAR LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.......90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR* WhatsApp *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege8* Koda ya isa gidan Huzaifa maigadi baiyi wani jinkiri ba ya bude masa gate saboda yasan matsayinsa a gurin maigidan, jiki na 'bari ya 'karasa inda yayi parking din motar tashi ya bud'e masa motar yana rankwafawa had'e da fad'in''Yallabai barka da zuwa." Hafeez ya fito daga motar a nutse yace."Barka dai Iliya." Hannunsa na dama ya mi'ka masa ba tare da 'kyankyami ba, Iliya maigadi ya rike hannunsa yana washe baki yace."Sai dai kayi rashin sa'a wallahi d'azu maigidan yayi tafiya kuma ina jin zai kwana biyu." Hafeez yace."Ayya! munyi waya dashi kafin ya tafi kada ka damu nasani zan shiga mu gaisa da madam ne." Malm Iliya yace."To to a fito lafiya ranka shi dad'e." Hafeez ya zura hannu cikin aljuhun jins din dake jikinsa dubu biyar ya mi'ka masa yace."Gashi a siyawa yara sweet." Malam Iliya ya washe hakora yana fad'in "Godiya nake yallabai Allah ya kara arziki." Hafeez yayi gaba ba tare da ya sake cewa komai ba dan 'ka'idarsa ne baya yin kyauta ya tsaya yana amsa godiya duk abinda yayi wa mutum to dan Allah yayi ba dan wata niyya ba ko dan a gode masa. Safna na zaune a parlo taci uwar kwalliya cikin wani material wanda akayiwa wula'kantaccen d'inki wayarta ce a hannunta kana kallonta zaka fahimci ranta a 'bace yake, wannan tafiyar ta Huzaifa ba 'karamin 'bata mata rai tayi ba, tafiya irin wannan bagatatan! babu shiri gashi tayi tayi su tafi tare ya'ki, ita ta riga ta saba da sex duk da Isha'ik sa'i da lokaci yana zuwa idan yayi irin wannan tafiyar yana d'ebe mata kewa amma dai ba kamar Huzaifan ba data saba dashi sosai, yanzu ma wayarta ce a hannunta tana so ta kira Isha'ik d'in ta fad'a mishi yazo da daddare dan gaskiya ba zata iya bacci ba sai an zurkud'a mata, wani masifaffan 'kamshi taji ya doki hacinta, ta dago kanta da sauri saboda tasan mutum d'aya shike amfani da turaran, Shi ta gani tsaye a bakin 'kofar shigowa ya wani 'kureta da shu'uman idanunsa yana sakin wani miskilin murmushi, Ji tayi kamar zata suma dan dad'i, ta mike da sauri tana d'an buga tsalle sassan jikinta suka motsa mussaman nonowanta, da sauri ta 'karasa bakin kofar tana fad'in "Welcom hand some." Hafeez ya d'an d'age mata girarsa guda yana bin ilahirin jikinta da kallo yace."Kinji dad'in ganina ko."? Ta wani lumshe ido tana shashshekar dariya tace"Sosai kuwa Wallahi naji dadi dama kewa duk ta dameni ka shigo ciki mana." 'Dan ma'kale kafad'a yayi yace."Um-um! nan ma ya isa nazo dubaki ne mijinki ya kirani a waya yayi tafiya yau ko."? Safna ta wani marairaice fuska tana shirin yin kuka tace"Eh ya tafi legos zaiyi sati biyu a can shine nace ya dam'ka amanata a hannuka." Murmushi yayi yace."Naji dad'i da kika za'bi amanata kan ta sauran abokanmu.'' Murmushi takeyi tana dan matsawa jikinsa ta rike hannunsa guda daya cikin kasa kasa da murya tace"Amma anan zaka kwana ko."? Dan zare mata ido yay ya girgiza kansa alamun a'a yana ta'be bakinsa. Hannunta ta sanya ta ratsa 'kungunsa tana wani lumshe idonta, jinta a jikinsa ya sanya hankalinsa ya soma tashi, ya daure dai har suka isa cikin palon ya zauna kan kujera yana cire hular kanshi, Cinyarsa ta haye tana shafa had'addan sajen da ya 'kawata kyakkyawar fuskarsa, cikin kasala da muguwar sha'awa tace"Gaskiya kayi min kyau yau sosai! lallai ka amsa sunanka Hand some ko wane dressing kayi yana maka kyau! Allah kana burgeni bakad'an ba." Hafeez dake lumahe idanunsa ya kalleta yace."Nima kina burgeni sosai kina muhimman abubuwan dake jan hankalina a kanki." Kansa ta kamo ta d'ora saman kirjinta ta wani rike sosai ta goga masa nonowanta a fuskarsa tace"Nasan dai har da wad'annnan abubuwan dan na lura duk sanda kazo hankalinka kaf na kansu." Ya d'an d'ago kansa yana kallon manya manyan nonowanta da suke wani sake kumburowa dan har sunfi na Titi girma, ya sauke zazzafa ajiyar zuciya yana wani irin huci! ya kai hannunsa kai yana shafa samansu a sar'ke! yace."Sosai kam wannan ballon naki na masifar gigita min lisaafina." Shashsheka tayi tana sake tsiyaya! ta ban'kare masa kirjinsa sosai ta kai hannunta ta bayanta ta zage zif d'in rigarta a hankali ta soma sabule rigar suka bayyana kan idanunsa, le'bansa ya shiga lasa yana sake d'age gira da kanne ido guda, Da kanshi ya 'balle briziyar nonowan suka bayyana, ya wani gigice sosai ya mi'ke kan kujerar ita kuma ta raba 'kafafunta a kansa tasa masa nononta guda a bakinsa ya shiga tsotsa kuwa kamar mayun wacin zaki! Shid'ewa ne kawai Safna ba tayi ba amma babu shakka tayi masifar kaiwa ma'kura tana kuma masifar jin dad'in yanda Hafeez ke tafiyar da ita, sosai ya iya romantinc duk sun gigice ita a wannan gabar so take kawai taji an soma zurkud'a mata, dan har tayi fatali da kayan jikinta tana kokarin kwance masa blet ya hanata,mi'kewa yayi zaune yana kallonta, ta koma wata iri ya lura kamar ma tafi shi jaraba, Yace."Kiyi hakuri ba zan iya yin wani abu dake ba, ina mutukar jin nauyi ace wani abu ya shiga tsakaninmu kina a matsayin matar abokina." Safna tasa masa kuka tana nani'karsa magiya ta shiga yi masa hawaye na zuba! tace"Wallahi tallahi yau zan iya mutuwa idan bakayi sex dani ba Hafeez na gama kwadaituwa dakai wallahi bakaji yanda gindina ke min 'kyaikyayi ba ka taimaka min dan girman Allah! abokinka babu abinda zaice dan kayi sex dani dadi ma zaiji tunda ku abotarku ta gaskiya ce na tabbata kai ma zakayi masa rana watarana." Tausayi ta bashi sosai ganin yanda take kuka hai'kan! duk ta jigata sai shafa shi takeyi, yace "Nafada miki bazan iya sex dake ba saboda wani dalili nawa, amma zan amince dai mu dinga biyawa kanmu bukata gurin romancing kin amince." a rud'e tace"Eh na amince wallahi nima zan biya maka bukatarka zan jiyar da kai dad'i insha Allah." 'Dan d'age girarsa yayi yana mata wani shu'umin kallo, a d'imauce! ta soma sakar masa kisses masu zafi a jikinsa tana so ta cire mashi blet yana hanata, har yanzu yanajin nauyin abinda zai aikata da matar abokin nashi, duk da ya kasance mutum mai 'kyan'kyami! kan komai amma wannan karon sai yaji kwata kwata baya 'kyamar Safna zai iya sex da ita amma kuma yana jin tsoron abinda zaije ya dawo zai dai dinga ragewa kansa zafi da ita tunda ya lura ta iya salo, tun yana ya mutse ya mutse har dai ya bada kai bori hau nan palon suka lalace gurin biyawa junansu bukata ta hanyoyi daban daban. ***** To kamar yanda Alaji Bawa ya bada sanarwa cewar za'a daura auransa da Asiya hakan ne ta kasance da safiyar laraba mutanan gari suka shaida daurin auran Alaji Bawa da Asiya Mai shanu, nan aka raba goro da alawa a fadar maigari daga gidan Alaji Bawa aka dinga fito da abinci fada maigari ta cika ma'kil da jama'a! bayan 'kura ta lafa Alaji Bawa ya kalli Mai shaniya dake zaune yayi jugum! Alaji Bawa yace."Mai shaniya nasan abinda ke damunka, ka kwantar da hankalinka Asiya zataje gidana ta tarar da komai na daki nasa mata sabuwar katifa da leda da labulaye sababbi saboda haka ka kwantar da hankalinka nasan abinda ke daga maka hankali kenan, sannan nayi mata akwati biyu ta kayan lefe komai da komai akwai a ciki, yau yau d'in nan nake so a kawo min ita gidana." Mai shaniya ya gurfana a gabansa yana godiya da washe baki yace."Alaji Allah yaja da rai ya kara lafiya da nisan kwana babu shakka ina alfahari da wannan auran." Alaji Bawa ya dinga girgid'a 'kafarsa yana 'bantarar goronsa sai wani murmushi yake yana gyara hularsa, Allah Allah yake duhun dare yazo ya samu ya tada komad'arsa da Asiyatu 'yar mai shanu. Mai shaniya na washe baki ya nufi gidansa, lokacin akwai sauran mata 'yan biki a gidan, Baraka da Taburni 'kawayen Gaje sun 'kule, Kuryan daki sai shewa suke suna zancan batsa da watsa dafadukan shinkafa a bakinsu, maishaniya ya shiga gidan cikin farin ciki ya daga labulen dakin yana kallonsu yace."Kaga aminan 'kwarai yau kuna bikin 'yarku ko."? Taburni tasa dariya tana fad'in"Oh ikon Allah wai mai shanu shine ya aurar da 'ya Uban amarya kenan Allah ya sanya alkairi gaskiya munyi farin ciki da wannan auran sosai da sosai yarinya tayi dace Allah yasa gidan zamanta ne." Mai shaniya ya gyara tsayuwarsa yace."Ameen ameen Taburni ai wallahi Alaji bawa mutumin kirki ne sosai yanzu ma yake shaida mun da cewar kada na siya mata komai na kayan daki ya shirya mata dakinta yanzu wanketa zakuyi kawai ku kaita dakin mijinta." Gaje ta rangwada bud'a ayiriri!!!!! "Kai wannan yarinyar da goshi take wallahi Allah dai yasa kada ta bamu kunya." Maishaniya yace."Ameen dai aini Alaji Bawai ya gamanin komai." Tace."Aikuwa dai sai ka fito da kudin sadakin nata dama kayi tanadinsu ne gurin siyan katifa da ledar tsakar daki to tunda an siya mata komai sai ka bani wannan kudin na hannunka duk na biya bashshikan dana ci." Mai shaniya ya d'an kalleta yana so ya musa mata, ganin yanda taci kunu yasa yace."Sai dai na baki dubu uku dan nima ina da uziri zanyi amfani da dubu biyun." Tace"To shikkenan." Hannunsa ya zura a aljihu ya dauko kudin daure a wata leda yaluwa, ya bata dubu uku ya daure dubu biyu ya mayar aljihunsa, ya kalleta yana fad'in "Ina Asiyar take."? Tace" Tana daki tun dazu take kuka anyi rarrashin taki hakura." Yace."Ka jini da 'yar 'kwal uba dama ba aure take so ba kuma anyi mata zata damu mutane da kukan banza." Dakin Asiyar ya nufa a fusace ya daga buhun yana fad'in"Ina kike ne ja'ira kukan me kikeyi." Asiya dake takure a kusurwar dakin ta dago kanta tana kallonsa da idanunta da sukayi jawur saboda kuka tace"Gani Baba." Yace."Kin nuna kina son aure anyi miki kuma zaki dingai wa mutane kuka." Kanta ta sunkuyar tace"Kayi hakuri Baba." Yace."To kada naji kada nagani wallahi Alaji Bawa babban mutum ne kinyi dacen da ba kowace mace tayi irinsa ba a kauyen nan, babu abinda bai miki ba na kayan daki akwai akwatin nan ki a gurinsa yace idan an kaiki zai baki, kiyi masa ladabi da biyyaya duk abinda ya umarceki dashi ki aikata bana son gardama Asiya ki zauna a dakin mijinki wanda ya taimaki rayuwarki." Tana kuka wiwi tace"To Baba." Maishaniya ya danji tausayinta kadan amma be nuna ba yana kokarin fita yace."Bayan sallahr la'asar ki shirya tsaf iyayenki su Taburni zasu kaiki dakin mijinki Allah ya sanya alkairi" Fita yay daga dakin, Ta kwanta kasa tana kuka da kiran mutuwa ita me zatayi da wannan tsohon azzalimun mutumin tasan idan an kaita gidansa zaice zai ta'bata ita kuma wallahi ba zata yarda yayi komai da ita, komai zai faru sai da ya faru tasan abunda ke rud'arsa kenan itama yayi mata ciki ta haihu ya saketa, to bazata bari ya keta mata martaba da mutunci ba, shawarwarin da takeyi kenan da zuciyarta. Pls Kuyi Sharing👏🏻 _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege9* Taburni ce ta d'aga buhun dakin nata tana fad'in"Ina amaryar Alaji Bawa takene? maza tashi kiyi wanka ki kimtsa jikinki dan yanzu la'asar d'in ta kusa." Asiya ta d'ago kanta dake dukufe tana kallon Taburni dake tsaye bakin 'kofa, Ganin yanda take hawaye ne ya sanya Taburni hangame bakinta ta rike ha'barta cikin mamaki tace"Ikon Allah sai kallo Asiya ashe har yanzu kukan kikeyi.''? Gaje da Laritu suka fito daga daki da sauri suka tsaya bakin kofar! Gaje naganin Asiya na kuka sai kawai ta shiga dakin a zuciye ta sha'ke mata wuya ta soma gaura mata mari! tana haki! tace"Bari jikinki ya fada miki dan ubanki sai kiyi kukan da hujja, haba! jama'a! tun dazu sai rarrashinki akeyi kin'ki shuru dan uwar ubanki akanki aka soma aure? shegiya kawai dan ma kin samu Alaji Bawan shine kike wulakanci shi da zai auri fanko mara budurci ai shine zaiyi kuka bake ba."!!! Asiya tana ihu! take fad'in "Dan Allah Baba kiyi hakuri na daina kuka dan Allah kiyi hakuri." Gaje tace"Habawa! ai wallahi sai nayi miki na 'karshe ai kece kika jawowa kanki nafi ki taurin kai dan ubanki."!! Kawai sai ta zauna a kanta ta matse mata wuya ta shiga jibgarta tana fad'in"Dan ubanki kiyi kukan da hujja."!! Taburni tayi saurin shiga dakin tana janye Gaje da fad'in"Ki kyaleta kada kiji mata rauni ki jawo wani aikin daban, ai ba zaki huce abinda tayi miki ba haba! shashashar yarinya kowa nayi mata murna ita tana bakin ciki auran alaji Bawa a cikin 'kauyen nan ai abun alfahari ne." Gaje ta mi'ke tana gyara daurin zaninta sai hakki takeyi tace"Ai bata gaji arziki ba shiyasa take wannan iskancin ko kin mata haka uwarta take mutsiyaciya masu mugun abun fad'a ai ke Asiya da haihuwarki gwara 'barin cikin ki wallahi." Laritu tace"Duk magana dai ta kare ke Asiya tashi jeki yi wanka kizo ki shirya kiyi hakuri ki zauna a dakin mijinki lafiya. Gaje tace"Au! har hakuri kike bata Laritu? tom kada Allah yasa ta zauna a gidan mijinta ta fito wallahi sai nayi mata muguwar iziyar da zata gwammace kid'a d karatu." Asiya ta 'mike jikinta sai rawa yake yi ta fita daga dakin da sauri! ruwa taja a rijiya ta dauki soso da sabulu ta shiga bandakin , tsugunawa tayi ta dinga kuka tana jin dama ta mutu ta huta da wannan masifar, Gaje tazo ta tsaya bakin bandakin tana fad'in "Au! cigaba kikayi da kukan? ba zakiyi maza kiyi wanka ba ki fito.'' Da sauri tace" Wankan nakeyi Baba." Gaje tace wallahi idan bakiyi wasa ba zan shigo bandakin da kaina nayi miki wankan kuma naci ubanki." Asiya tayi saurin cire kayan jikinta ta soma wankan tana sauke ajiyar zuciya alamun taci kuka ta 'koshi. Tana fitowa Gaje ta mika mata sabuwar atamfar leda me yallow da blue sai wani dogon yari da sark'a da man shafawa dangwali ya'ba da jar hoda da jan janbaki tace"Maza shirya jikinki." Asiya ta karbi kayan jiki na rawa ta soma shiryawa Gaje na tsaye tana kallonta tayi kwalliyarta irin ta kauye taji hoda da janbaki, wani mayafi sharara mai kyalli ta mika mata da sabon takalmin dan madina tace"Yafa mayafi kisa takalmi." Asiya ta yafa mayafin ta zura takalmin Laritu da Taburni suka ce masha Allahu amaryar Alaji Bawa ta fito." Asiya ta tsani taji suna kiranta da wannan sunan haushinsu takeji! Gaje ta fito daga dakinta da wata kwalbar turare irin d'an d'uri nan, ta bude ta tsiyaya a hannunta ta shafa mata a jikinta tana fad'in "Kinci albarkacin aure dan Ubanki shiyasa na shafa miki turarena." Taburni da Laritu suka saka dariya suna tafawa." Laritu ce ta rike hannunta suka fita daga gidan, 'Yan matan 'kyauye dake zazzauna a 'kofar gidan suna jiran a fito da amarya suka mi'ke ko wacce taci kwalliya da uwar d'amara! suka soma rera w'akar *Da baki ce kina so ba da ba'a baki shi ba* Asiya na jinsu suna shewa da dungurin kanta, zuciyarta tamkar ta tsage dan haushi, ita bata ta'ba cewa tana son Alaji Bawa ba amma suna rera mata wa'ka! Alaji Bawa da abokansa na zaune a katuwar tabarma a kofar gidanshi suka hango ayarin amarya! Alaji Bawa ya dinga washe bakinsa ya sake gyara zamansa, Yayi wa na kusa dashi magana" Kaga yanzu yanzu muke maganarsu ashe suna tafe! maza kaje sabuwar kasuwa gurin d'anliti mai balangu kace ya baka kajin nan da nace ya gasa mun su sannan kace ya bad'e su da kuli-kuli sosai." Isuhu ya mike da sauri yana fadin"Angama Alaji." Alaji Bawa idanunsa kan Asiya yana taunar goransa har suka 'karaso inda yake, suka tsaitsaya suna gaisheshi ya dinga amsawa yana le'kan fuskar Asiya dake cikin shararan mayafi, Asiya kam jin muryasa yasa gabanta ya tsananta faduwa, Innalili wa'ina ilaihi raji'un kawai take ambata a zuciyarta.....Yace."Maza maza ku kaita d'akinta zaku ganshi ya fita daban a cikin rumfar dan jiya nasa akayi mata sabon fenti fari da bula" ya mikawa Taburni mukkulin dakin. Taburni tace"To Alaji Allah ya saka da alkairi." Hansantu da sauran matan gidan da yaransu suna zazzaune a tsakar gidan sukaji an rangwada bud'a! ayururi!!!! Ai tuni Yaran suka mi'ke suna ihu da fad'in"Ga amaryar Babanmu ga amaryar babanmu." Lanto taja tsaki tana buga musu tsawa da fad'in "Dan ubanku ku zauna shegu shashashai Asiyar mai shaniyar ce baku sani ba da zaku dinga ihu."! Ai kamar ma bada su take ba tuni sun lullu'be Asiya suna so su cire mata mayafi tana ri'kewa." Laritu tace"Ku zazzauna mana ai sai kun gaji da ganinta kubi komai a hankali." Da kyar suka zauna suna surutu kasa kasa. Su Gaje suka zaunar da Asiya suma suka zauna sai suka shiga gaishe-gaishe! Taburni tace"Hajiya Hansatu kece Uwargida dan haka zamu damka amanar yarinyar nan a hannuki." Hansatu tace"Ke kinga Taburni bana son Iyayi ni babu wata amana da zan karba to kaji." Lanto tace"To ballanta kuma ni." Atika dake sakace hakori tace"Ai kawai kuje ku ajiyata a dakinta amma mu babu wata amana da zamu karba." Gaje tace"Kema dai Taburni wace amana kuma ai yanzu duk an daina yayin wannan! ni banga laifinku ba wallahi, ku cigaba da tsarinku yanda yake gatanan itama matar gidace ta fito tayi aiki da dukkanin abinda kukeyi a gida.....Atika tace"Mutukar ta iya d'aukar Alaji da daddare to ai ta zama matar gida kada ki damu zamu bata aikinta tayi ta kuma kwana da miji." Gaje tace"To yanzu naji magana mu zamu koma." Kafin suce wani abu Alaji Bawa ya shigo hannunsa rike da katuwar leda ya mikawa Taburni yace." To ga kayan siyan baki nan." Taburni ta karba tana fadin "Mungode Alaji." Suka mike suka nufi dakin Asiyan Gaje ta ajiyeta gefan katifa tace"Allah yasa idan ya nemi hakkinsa ki hanashi wallahi naji labari saina nakastaki."!!! Asiya na kuka wiwi ta rike hannuna, Gaje ta fuzge hannunta ta fice daga dakin tana yi wa su Hansatu sallama! ai suna tafiya 'yayan gidan suka cika d'akin suka haye kan katifa suna ta tsalle da ihu!!!!! Asiya ta 'boye fuskarta cikin mayafi duk tana jin ihun su da tsalle-tsallensu tayi shuru gabanta sai faduwa yakeyi har yanzu ta kasa bude fuskarta ballanta ta kalli kalar dakin da aka ajiyeta......."Kai-kai!!! meye haka."? Muryar Alaji Bawa kenan a lokacin da ya shigo dakin ya tadda 'yayansa na tsalle kan shimfidar amarcinsa....Sai suka soma ficewa daga dakin simi-simi! ita kuma Asiya tun sanda ya shigo dakin gabanta ke lugudan duka n daka! sake takure jikinta takeyi tana makyarkyata. Yazo ya zauna kusa da ita yana cire babbar rigar jikinsa sai washe dafaffun hakoransa yakeyi, hannu ya kai zai yaye lullubin kanta ta matsa da sauri! bakinsa ya saki yana kallonta yace."Asiya tauraruwata mekikeyi haka kuma? ki bude min fuskarki mana kyakyawar yarinya yau Allah ya cika min burina gani gaki a daki daya alhamdullhi." Asiya taje ta raku'be a kusurwar d'akin tana watsa masa kallon tsana! Wata iriyar mi'ka yayi yana sakin hamma da 'yar dariya yace"Asiyatu na fuskanci tsoron agon naki kikeyi kizo ki zauna muttauna, yau ranar farin ciki ce a garemu." Taji kamar taje ta sha'ke masa wuya saboda takaici, tsofai tsofai dashi ko kunya bayaji yana abun yara, mikewa yayi ya nufi inda take, da sauri ta nufi hanyar fita daga d'akin Yayi gaggawar janyota ta fada kirjinsa, Ihu!!!! mai 'karfin gaske ta kurma! ai kafin yayi wani yun'kuri yaransa sun cika d'akin suna rarraba idanunsu akansu.......Ransa a 'bace! ya buga musu tsawa da fad'in "Dan ubanku me kuka shigo yi kaga munafukan yara." Lanto ta shigo dakin tana cin magani tace"Haba Alaji wannan wace irin zilama ce ana kawo amarya 'yan kawota ma bai isa ace sun isa gida ba har kake shirin yin wani abu ai ka bari gari yayi duhu mu dai kada ka 'bata mana tarbiyar yara."! Cike da borin kunya yace."Lanto ki shiga hankalinki wallahi haramun na aikata da zaki titsiyeni dakin matata fa na shiga shine saboda gulma da munafurci zaki turo min yara ko? to bari kiji da kyau! babu abinda zai fasa wallahi na samu dai-dai dani dole na mori kuruciyata." Lanto tace"Anji kunya dai wallahi anyi faduwar ba'kar tasa alaji." Sosai yaji ciwon maganarta yace."Lanto daf nake da na sakeki wallahi ni kike gayawa magana gaban amaryata." Lanto ta buga cinya tace"Sai me dan ka sakeni wallahi zama daram a gidan nan domin ba zan tafi na bar 'yayana ba." Tana gama maganarta ta kad'a kan yaran suka fita daga dakin. Alaji Bawa ya maida hankalinsa kan Asiya dake ra'be a jikin bango tana kuka yace."Wallahi duk sanda kika sakeyi min ihu! sai naci ubanki kwarto ne ni da zaki dinga yi min ihu a gida yarana naji! duk son da nake miki wallahi zan 'bata miki rai na kara kusantarki kikayi min ihu! dan kinga ina rarrashinki kike min iskanci banza" Asiya ta gumtse bakinta tana ti'kar kuka da tunanin yanda zata fece daga gidan dan tayi alkawarin ba zata bari wannan wulakantaccen mutumin ya lalata mata rayuwa ba. Babbar rigarsa ya dauka yasa ransa a 'bace ya futa daga dakin, yana jin matan nasa nayi dashi, yayi saurin ficewa daga gidan dan yasan Hansatu na iya kunyata shi gaban yaransa. Asiya zama tayi 'kasan dakin ta had'e kanta da gwiwa tana sauke ajiyar zuciya wai shin ya zatayi ne da rayuwarta ko ta gudu ne? tunanin da takeyi kenan a cikin dakin. Alaji Bawa kam na futa fadar maigari ya nufa yana baza babbar rigarsa, ya zauna jama'a sai gaisheshi sukeyi ya kallesu yana bata rai yace."Ina son zamu tautauna mahimiyyar magana da maigari." Dukaninsu suka mi'ke kowa ya zura takalminsa ya 'kara gaba." Alaji ya soma wassafawa maigari abinda ke da akwai da wulakancin da Lanto tayi masa gaban yaransa, Maigari yace."'Kuruciya ce ke damun yarinyar amma na tabbata yau tasan wanene kai zata daina gudunka kayi 'kokari ka kwanta da ita a yau din nan shikkenan an wuce wuri." Alaji Bawa yace."Ai ko dan na bawa matan nan haushi yau zan kwanta da yarinyar nan a gado d'aya kuma da gayya zan ta sakin ihu! suji sai na cuzguna musu." Maigari ya saki dariya yana gyara zamansa yace."Ina ma nine na samu wannan yarinya ai da sai nayi wata guda ban zauna a fada ba." Alaji Bawa ya saki wata mahaukaciyar dariya yace."Wallahi har ka sake kwadaita min sha'awar yarinyar nan so nake duhu yayi sosai na shiga gidan." Maigari yace."Bari na shiga na dauko maka wani tsumi! da nake kur'ba kullum yana 'kara karfi da guzari! kana kuma kayan aikinka zai 'kara girma da kumburi ai kada ka saurara Alaji ka bugi yarinyar nan yanda zata dinga ihu! matanka suji su tabbatar da cewar baka tsufa ba da sauranka."" Hahahahahaha!!!! Alaji Bawa ya saki mahaukaciyar dariya yace."Maza d'auko min in banka danni kaina ina ji zan iya kwana kan yarinyar nan ina abu d'aya amma dai hausawa nacewa idan kana da kyau to ka kara da wanka." Maigari ya mi'ke yana gyara babbar rigarsa yace."Wannan magana haka take Alaji bari na shiga ciki na dauko maka." Yana shiga ciki Isma'l ya 'karaso gurin, dik ya rame ya lalace saboda rashin abar 'kaunarsa Asiya shi dai Allah ya dora masa masifar sonta da tausayinta, shiyasa kawai yaji yana sha'awar auranta, tun ranar da mahaifinsa ke shaida masa abunda ke faruwa yace shi yaji ya gani yana sonta a haka zai aureta, maigari yace."Ai dole ya hakura tunda Alaji Bawa ya bada sadakinta kawai ya nemi wata yarinyar, to tun daga ranar ya rasa kwamciyar hankalinsa ya saka damuwa a cikin zuciyarsa shiyasa yake ta rama a tsaitsaye! Alaji Bawa ya daga kansa yana kallon Isma'il din dake tsaye a kansa, Yace."Kai baka da d'aa ne zakayi min 'kerere aka." Isma'il yace."Nagartaccen mutum shi ake risinawa ba irinka tsohon banza ba." Alaji Bawa ya bud'e bakinsa yana kallonsa cike da d'umbun mamaki yace."Isma'il ni kake fad'awa wannan maganar?" Yace."Eh Ai ban gama ba, ka saurara da kyau kaji abunda ke tafe dani gurinka, ka daina murna da zumud'i ka aure min masoyita wallahi ka auri gaibu dan komai kulafucinka ba zaka samu wannan abun da kake so ba a jikinta baka son Asiya sha'awarta kakeyi dan da kana sonta da tausayinta ba zakace zaka aureta ba ka rusa mana farin cikinmu Asiya ni take so nima ita nake so gwara tun kafin tafiya tayi nisa ka sakar min matata." Alaji Bawa yace."Anya Ismail baka shaye-shaye kuwa, wannan wace banzar magana ce kakeyi haka? kasan nafi karfin wannan rashin Arzikin naku na 'yayan Zamani! ubanka ma girma yake bani ballanta kai saboda haka ka shiga taitayinka dani kada ka sake kiran Asiya da sunan matarka idan ba hakaba zan dauki tsatstsauran mataki akanka." ! Yakarasa maganar cike da bacin rai! Isma'il na shirin yayi magana Maigari ya fito daga cikin gida hannunsa rike da wata kwarya rufe da fefe! girgiza kansa kawai yayi ya kad'a kansa ya wuce yana jin 'kunar zuciya hakika Alaji Bawa ya yanke masa jindad'in rayuwa tunda ya rabashi da sahibarsa, Alaji Bawa kuwa nunawa yayi maganar arziki sukeyi da Ismail din shiyasa maigari bai damu ba, ya zauna kan kujerarsa yana mika masa kwaryar hannunsa dake cike wasu saiwowi kumfa sai tashi takeyi cikin ruwan tsumin.Alaji bawa ya kafa kansa yana bankar ruwan tsumin sai da yasha fin rabi kana ya ajiye kwaryar a gefe yana wata irin gyatsa! Maigari yace."Yanda ka banki maganin nan nasan yau akwai shagali Alaji." Hahahaha Alaji Bawa ya shiga girgiza kansa yana jin yanda tsigar jikinsa ke tashi, kadan kadan ya soma jin sanyi, sai ya shiga zabura kuma kafin kice me jijiyarsa ta cika tayi fam ta mike tamkar ta saurayi sabon balaga yana jin yanda take harbinsa a jikinsa, kamar wani bugagge yace."Anya kuwa zan iya bari ayi sallah isha'i kuwa wannan maganin ya soma aiki a jikina." Maigari yace."Dama na fada maka ai sha yanzu magani yanzu ne." Alaji Bawa yay shuru yana sauke numfashi, hira suka cigaba dayi sama sama yana daurewa dai so yake yaransa kananu suyi bacci sai ya shiga gidan.......Sai kusan goma da rabi na dare sukayi sallama ya nufi gidansa yana baza babbar riga dan kada jijiyarsa dake mike ta tona masa asiri! Koda ya isa gidan nasa ya tarar 'yayansa duka Sunyi bacci 'yan mata biyu ne ba suyi bacci ba suna tare da iyayensu a tsakar gida suna hira da cin gyada marau!marau! sosai ya shiga mamaki ya akayi yau basu kwanta da wuri ba! 'Kwafa yayi ba tare da yace musu komai ba ya shigesu dakin Asiya ya tura ya shiga. Tun bayan futarsa take ra'be a guri guda ko sallah ta kasayi ballanta taci abincin da aka kawo mata, taci kuka ta koshi sai zabura take ga uban duhu a dakin, da sauraye sai cizonta sukeyi, jin kamar an shigo dakin ya sanya ta mike a zabure ta la'be bayan labule gabanta na dukan uku-uku! Ya kunna hasken fitilar wayarsa 'kirar nokia yana haske dakin hade da sassauta murya yana fad'in "Tauraruwata kina ina ne? shuru tayi tana jinsa tana kuma kallonsa yana haske haske! can ya hango kafafunta ta kasan labule! yana tangadi kamar dan kwaya yaje ya yaye labulayen suka hada ido! Ihu!! zata kurma ya damke bakinta da hannunsa, fincikota yayi ta fad'a tsukakken kirjinsa da yaga jiya da yau! ya matseta sosai yana nishi, yace." Amarya zo kici kazar amarcinki me ku'li 'kuli kafin na kwanta dake dan a tsananin bukace nake." Tunkudeshi ta shiga yi tana kuka wanda baya fita sosai gabanta kuma na wani irin bugawa jin taurin wani abu me tsini dai-dai cinyarta, Yace."To tunda ba zaki ci kazar amarcinki ba to bari ni na kar'bi sadakina." Kawai ya ti'bar da ita kan katifa, ya shiga cire kayansa ya zage tazugensa yayi zigidir!! ta dunga buge buge tana so tayi ihu! ya gumtse mata baki da hannunsa, sai kawai ta shiga yakushinsa a ya mushashshiyar fatar jikinsa, shi kuwa ai tuni ya cire mata rigarta ya kama nonowanta yana ta luguda yana nishi! ya saka hannunsa cikin wandonta, nan Allah ya bata sa'a tayi masa wata wawar bangaza ta sauka daga kan katifar a guje ta dauki rigarta ta nufi kofar fita, a kulle takeyi tayi tayi ta bude ta kasa! sai ta hau diri-diri! lokacin shi kuma ya samu karfin mikewa tsaye ya nufi inda take tana kallon jijiyarsa kamar torchlight a tsaye ya nufo inda take sai ta nufi bakin tagar dakin tana so ta d'ane ta fita, ya wani fincikota da karfi ta fadi kasa! hawa kanta yake shirin yi ta angizashi ta kama, 'katuwar jijiyarshi ta wani murd'eta da mugun karfi! dan har sai da ta cije bakinta!!! A take Alaji Bawa Ya zube a kasan d'akin yana makyarkyata da fad'in "Shikkenan ta kasheni!!! Wayyo!! Hansatu!!! Lanto! Atika!!! kuzo ku kawo agaji!! Yana ihu had'e da bajewa a 'kasan dakin yake wannan maganar......A guje matan gidan suka shigo d'akin, nan suka ga mijinsu a baje a tsakar dakin zigidir yana Ihu! da ri'ke Jijiyarsa sai wata irin zufa! ce ke keto masa.......... Pls kuyi Sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* *🌎MAZANARTA WRITES ASSO* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *PAID BOOK!!* *Free Pege10* "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!!" suka fad'a gabakid'ayansu sukayi kan mijin nasu suna rirri'keshi lokacin shi kuma wata irin kumfa ta soma fitowa daga bakinsa ya dinga zabura idanunsa na kafewa! Hansatu ta fashe da kuka tana fad'in Alaji kagani ko garin zilamarka ka auro wacce zata nakastaka, ke Asiya uban me kikayi masa."!!!? Tafada tana kallon inda Asiyan ke tsaye tana shar'bar kuka gashi babu riga a jikinta sai kare 'kirjinta takeyi!! Lanto tace"Kinga Hansatu babu lokacin magana yanzu Alaji na cikin halin rai da mutuwa kawai a kira Dalladi yazo su yafi asibitin cikin gari dashi dan ni nagane aika aikar da yarinyar nan tayi kuma ni wallahi banga laifinta ba." Atika tace."Wallahi nima haka duba ki gani dan Allah ashe Alaji nada lafiya sosai dubi yanda gabansa ya mike humm! Lanto tace"Lafiyarsa lau dama ai mu ya raina watakila ma yaje yayi shaye shayen maganin karfi ne Allah shi kara." Hansatu ta fita daga dakin da sauri ta tura daya daga cikin yara suje shagon dake waje su kira su Dalladi, ta koma dakin, nan ta tarar da tashin hankali dan Alaji Bawa ya suma ya daina motsi a guje! Lanto taje ta kamfato ruwa a duro tazo ta watsa masa, ya bude ido a gigice yana kurma uban ihu da fad'in ta murd'e min mazakuta zata kasheni Hansatu kina ina ne!? Tace."Gani Alaji." Yace."Lanto da Atika ku suturtani ku kaini asibiti a dubani ni kadai nasan bala'in da nake ciki.'' Atika tace"Zulamarka ce taja wo maka Alaji." Lanto ta janyo wandonsa suka daga shi suna kokarin saka masa wando, babban dansa Dalladi ya shigo kana ganinsa kaga shegen 'kauye le'bansa ba'kikkirin sai warin wiwi yake. "Yane wai me yake damunsa ina tsaka da bacci na an taso ni."!? Alaji Bawa najin maganar d'ansa yace." Dalladi ashe ajalina na aura ban sani ba naga masifa yau! maza jeka samo mota mu tafi asibiti 'Yar iskar yarinyar nan ce ta murd'e mun mazakuta zata kasheni."!!! "Hahahahaha!! Dalladi ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya yana buga bango hade da dukan kasan dakin da kafarsa, yace."Baba kenan wallahi ni kwadayinka na bani mamaki! ka tsufa amma kamar kara tunziraka ake yanzu dan girman Allah ina kai ina wannan yar 'kan'kanuwar yarinyar ai da irinmu matasa masu jini a Jika ta dace." Hansatu tace"Kai bana son shashanci kaje kayi abunda aka saka." Wata dariyar ya kuma saki yana kallon baban nasa da yayi shame shame! yana gumi! sai ya kalli Asiya dake ajiyar zuciya fuskarta duk bushashshen hawaye, lasar lebansa yayi yana kure ta da ido ganin babu riga a jikinta, da sauri ta shiga kare jikinta tana jan tsaki! Waje ya fita yana ayyana abunda zaiyi a kanta. Duk da dare ne hakan be hanashi samo mota ba har kofar gida ya shiga gidan shida dan uwansa suka kama mahaifinsu suka fito dashi, mota suka sakashi Hansatu da Lanto suka shiga suka zauna yace."Kai Nura kuje tare ai nayi me wuyar tunda na samo mota zan koma na kwanta dan bacci nakeji." Nura ya shiga motar ya rike Alaji Bawa dake matagugu direban yaja suka tafi, Dalladi ya koma cikin gidan, la'bewa yayi a wani guri sai da yaji shuru Atika da sauran yaran sun shige daki sunyi bacci ya salalla'ba a hankali ya afka dakin Asiya ya maida kofa ya rufe! Jin alamun an shigo dakin yasa ta mike zumbur ta tsaya kan katifar tana kallon kofar shigowa, alamun mutum take gani yana kusantota, ta takure lokon dakin tana hawaye da makyarkyatar jiki, ganin an kusa cimmata ne yasa, ta duro daga katifar aguje tayi kofar fita daga dakin, Dalladi ya bita ya tade mata kafafu, ta fadi cicci'barta yayi ya nufi katifar ya jefata a kai! Ihu!! ta kurma! Dalladi ya aza mata nauyinsa ya danneta sosai yana rufe mata bakinta, Warin Wiwi ya cika mata hanci gashi ya toshe mata baki hawaye ne kawai ke zurara! zuwa yanzu ta gane ko wanene dan ta lura dama d irin kallon da yake mata d'azu, ta shirya tsaf! za tayi masa abunda tayi wa Ubansa tunda shima d'an iska ne! Dalladi ya shagala sosai yana ta lasar saman nononta jikinsa dik ya saki ya hau sabule wandonsa, aikuwa tayi kukan kura ta tureshi ya fadi kan katifar cikin azama take kokarin dura 'kasa ya ri'ke! 'kugunta! Ta Juyo a zuciye! ta gaura masa mari! lokacin zuciyarta ta riga ta bushe! Dalladi yace."Dan kutumar ubaki ni kika mara! lallai yau sai na yagalgalaki wallahi! sai kawai ya shiga buga kanta jikin bango(garu) yana boll da ita, karkashin kafafunsa ta shiga tayi gaggawar kamo jijiyarsa dake cikin gajeran wando ta murd'e! tana cije bakinta!!! Dalladi! ya rafsa wani Uban Ihu!!! ya silale a gurin yana wata iriyar zabura! a tsorace! ta mik'e tana saka rigarta ta bud'e dakin ta fito.......Atika da ihun! Dalladi ya tada ita ta fito daga dakinta da sauri! ganin Asiya ta fito tana waige waige yasa tace"Ke Asiya menene."? Fashewa tayi da kuka tace"Yana cikin dakin dalladi ne ya shiga yana cire min wando." Atika taja tsaki tace"Dan iska dan na gada gwara shima da kika murd'e masa mazakutur shegu tsinannu shida uban nasa! Asiya tace"Dan Allah ki taimaka min ina so in gudu." Atika tace"Ai guduwar itace tafi miki alkairi dan Allah kika sake Alaji ya dawo to ubanki ma yayi kad'an nasan bashi ma dalladi ya farfad'o sai kin gwammace kid'a da karatu." Asiya na kuka tace"Na sani wallahi! gashi ina jin tsoro na koma gidanmu." Atika tace." Ki shiga duniya kawai." !!! Tana goge fuska tace"Ai ban san wace duniyar zan shiga ba." Atika taja tsaki tace''Ke dallah ni kin dameni idan zaki nemawa kanki mafita shikkenan idan kuma zaki tsaya anan har su dawo su sameki shikkenan ni na tafi na kwanta." Ta shige dakinta tabar ta a tsaye a gurin tana sa'ke-sak'e! jin motsin Dalladi dake dakinta ya sanya ta zabura! da sauri ta fice daga rumfar ta nufi kofar fita cikin duhu ta dinga laluben sakata, ta sanya karfinta sosai tana so ta bud'e kofar takasa, can taji yo muryar Dalladi na fad'in "Duk gidan uban da kika shiga sai na kamo ni zakiyi wa wannan iskanci wallahi sai na 'kwakule miki gindi!!! kema Jiki idan da dad'i."! Yana wata irin tafiya yake wannan maganar yaji jiki sosai dan da 'kyar yake cire kafa.......Ra'bewa tayi dake soron mai girma ne sosai, tana jin motsinsa yana kici kicin bude sakata yana surutai, ya bude ya fita daga gidan, sai da ta tabbatar yayi nisa sannan ta fito da sauri ta dauki hanya, tanayi tana waige-waige ga dare ya tsalla, cikin gonaki ta dinga bi ko tsoro ba taji 'kokari take kawai taga tayi nisa da 'kyauyen nasu na Fanisau!!. Shi kuwa Dalladi can gidan mai shaniya ya nufa sai tam'bele yake yi a hanya da surutai gami da zagin Asiyar ta uwa ta uba! Wani wawan bugu ya dinga yi a kofar gidan maishanu wanda ya sanya suka tashi a gigice! suka fito suna tambayar waye! Dalladi yace." Nine nan Dalladi dan gidan Alaji Bawa." Hannu na rawa Mai shanu ya bud'e kofar, kawai Dalladi ya afka cikin gidan dan har yana ture Gaje da duk hankalinta ya tashi! ciki ya shiga yana d'ure-d'uren ashar! "Wallahi duk inda kuka 'boyeta sai kun fito da ita kamar yanda tayi yun'kurin kisa to muma sai mun dauki mataki a kanta baza mu yarda ba." Mai shanu yaje yana rirrikeshi da tambayar abunda ke faruwa, Dalladi na cije baki yace." Ba wani waye waye! 'Yarka Asiya tayi niyyar kashe mana ubanmu ta hanyar murd'e masa azzakarinsa kawai saboda ya nemi hakkinsa na aure! tayi nufin kasheshi, ni kuma daga zuwana taimakon mahaifina nima ta murd'e mun nawa yanzu haka Babanmu na asibiti cikin halin rai da rayuwa sabida haka idan ya mutu to kome za'ayi a garin nan sai dai ayi dan wallahi baza mu yarda ba." A gigice maishanu ya fito waje kawai sai yaga cincirindo na jama'ar gari suna 'kus-'kus, dan hayaniyar da Dalladi yake yi ta tashi hankalin kowa, labarin abinda ke faruwa a daran ya iske fadar maigari cewar 'yar gidan maishanu xata kashe Alaji Bawa ta hanyar murd'e masa azzakari! Maigari ya sanya wasu daga cikin fada suka tasa 'keyar maishanu domun zuwa a fada, Gaje ta fito tana zabga ihu da fad'in su ba laifinsu bane dan duk wani fad'a da iyaye kewa 'yayansu sunyiwa Asiya kuma suma basu san inda take ba a halin yanzu." Babu wanda ya saurareta shi kuwa Dalladi sai da ya hargitsa gidan kaf yana duba Asiya bai ganta ba ya fito yana surutai Gaje tayi saurin bashi hanya ya wuce, Taburni taja ta suka shiga cikin gidan tana rarrashinta. Shi kuwa Alaji Bawa ai har suka isa asibiti bakinsa bai mutu ba ya ma riga ya zauce dan wata maganar ma bai san yana fad'arta ba, likita ya shiga bashi taimakon gaggawa da kyar aka samu yayi bacci sannan suma su Hansatu hankalinsu ya kwanta. Da asuba Maigari Maishaniya da sauran jama'ar Fada sukayi mota guda suka nufi asibitin cikin garin domin duba jikin Alaji Bawa da yanda yake. A jigaje ta fito bakin titi shuru sai jefi jefin motocin dake wucewa kawai sai ta shiga bin titi tana tafiya tana waige-waige dan duk da ta fito titi hankalinta be kwanta ba tsoro takeji kada wani ya ganta, sai da tayi tafiya sosai gari ya washe ta nemi wani guri 'boyayye ta zauna tana hutawa tana kallon yanda jama'a ke fitowa suna harkokinsu, ga motoci sai zurga zurga sukeyi a kan titi, kwanciya tayi kasan gurin tana sauke ajiyar zuciya, hawaye ya 'kwace mata da wannan wahalalliyar rayuwar da takeyi gwara mutuwarta, bacci ne ya soma fizgarta, taji tsawa! a kanta, "Ke yarinya me kikeyi anan gurin."? Ta tashi firgigit! wata katuwar bayerabiya ce tsaye a kanta baki na rawa tace." Babu komai kwanciya nayi ina hutawa ni na fito daga kyauyen Fanisau ne.'' Madam Simi tace"To nan ba gurin hutawa bane maza tashi ki bar nan."! Duk da tana jin tsoron matar bai hanata karyar da kanta ba tace"Dan Allah ki taimaka min." Madam tace"Oh ya inayi miki magana kina had'ani da Allan ku ni ban san shi ba ki tashi kina 'bata min lokaci zanyi shara in fito da kayan sana'ata." Asiya ta mi'ke tana gyara daurin zaninta kafarta tayi bud'u-bud'u da ita ta kama hanya zata bar gurin, Madam Semi tayi wani tunani tace"Ke zonan xan taimaka miki." Asiya ta dawo da sauri! Madam Semi ta kalleta sosai tace yarinyar kyakykyawa da ita gata bafulatana za'a nemi kudi da ita zan raineta idan ta zama mutum sosai sai ta zama hannun jarina." tace"Zo muje dakina ki bani labarin ki." Hannunta ta rike suka nufi wani d'aki dake can tsallaken titi cikin wata 'yar 'karamar kasuwa, Madam ta bude dakin suka shiga, Katifa ce a kwance a dakin sai koren kafet da labulaye sai jakkunan kaya da kwanunkan cin abinci, cikin yanayin hausarta tace"Bani labarin rayuwarki." Asiya ta soma goge hawaye ta shiga labarta mata rayuwarta da irin bakar wahalar da take sha hannun matar babanta da kuma yanda ta auri Alaji Bawa da irin abinda tayi masa. Madam Semi tace"Kin burgeni da baki bari tsoho nan ya lalata miki rayuwa ba ni zan taimaka miki zamu taimaki juna nan shine dakina dana kama haya Ina siyar da kosai a bakin titi da safe da yamma kuma ina gasa masara, zaki dinga taimka min ni kuma zan siya miki kayan kwalliya sannan kuma dik abinda nace miki kiyi to kiyi bana son gardama."! Asiya na murna tace"Na amince insha Allahu zanyi miki biyayya." Madam tace"Ki kwanta ki huta kinji yanzu bari naje na share gurin sana'ata na fara kada customs suzo zan shigo miki da break fast." Tace."Nagode" Madam Semi ta fita daga dakin da sauri nan ta tarar yaron dake mata hidima har ya share mata gurin ya fito mata da kayayyakin aikinta ya ajiye mata gurin, zama tayi kan kujerarta ta fara sallamar Jama'a..........Asiya bayan fita Semi daga dakin ta sauke ajiyar zuciya tana ganin gwara ta zauna da wannan arniyar kan ta zauna tare da Alaji Bawa da zuriarshi. **** Hafeez da Safna sunyi wata irin 'kullewa, kullum kafin yaje ofis sai yaje gidan sunyi shaid'ancinsu sannan yake tafiya ofis din, idan kuma jarabarsa ta sake ciyo shi a ofis din dai zai kira Titi yace."Tazo ta sameshi, sai su kashe awa uku suna aikin abu d'aya, jama'ar dake aiki a company har sun soma fahimtar wani dangane dashi da Titi, to amma tsoro ya hanasu magana sai dai bayan ido suyi ta 'kus!'kus amma suna ganinsa kowa zai shiga hankalinsa.......Alhamdullhi yanzu al'amuransa sunyi sau'ki tunda yana samun Satisfaction ta kowane 'bangare baga Titi ba baga Safna ba kowacce na kokarin faranta masa, mussaman Safna dake ta so ta janye masa hankalinsa gurin ganin yayi sex da ita shi kuma yana janyewa iyakacinsa da ita romantic ne baya za'kewa sosai dan idan hankalinsa ya tashi sosai shine yake kiran Titi ya biya bukatarsa da ita saboda da ita kawai ya amince itama dan dai shine ya fara saninta kuma yana da ya'kini akan bata neman maza shi kad'ai take mi'kawa jikinta, hidima da facaka da kud'i kuwa babu irin wacce baya yi mata, Hafeez har wata 'kiba yayi yay fresh sosai sabida yana samun abunda yake so, hankalinsa ya kwanta gabad'aya ya daina maganar aure wanda dama haka Professor yake so, sai ya shiga lalla'bashi suka cigaba da gudanar da harkokinsu wanda suke samun cigaba akai sosai yanzu ma shirye shiryen bud'e wani sabon company suke.....Tsakanin Professor da d'ansa Hafeez yanzu akwai jituwa sosai saboda Hafeez din yana kokarin kaucewa 'bacin ran mahaifin nasa. ** Asiya ta samu kulawa sosai a gurin Semi abinci mai kyau take siya mata taci ta koshi bata aikin komai sai kwanciya, Madam ta shiga kasuwa ta siyo mata kayan ganjo riga da siket da dogon wando, Asiya ta dinga jin kunyar saka kayan, ganin kamar masu fitar da tsaraici ne! to ganin ran Madam din ya 'baci yasa ta soma sawa! a ranar Madam yini tayi tana kwarzanta kyawunta tana kuma tunanin irin kud'ad'en da zata samu da ita......Yamma nayi ta dauketa suka nufi wani gurin saloon aka shiga warware cukurkud'add'an gashin kanta dake wani mugun wari! Wanke shi akayi tsaf! aka taje sosai ya mike ya dinga wani uban she'ki gashi baki'kirin! sai daukar ido yake, Katon ribbon akasa mata aka tufke gashin guri guda sai kamshi mayuka yake, Madam ta biya kudin gyaran gashin suka fito, Asiya ta dinga takure jikinta kunya takeji sosai kamar wata kafura gata cikin matsatstsun riga da wando kanta babu dankwali gashi Madam tasa mata wani abu me kyalli a farcenta na kafa da hannuwa, duk da bata zuwa makaranta tasan hakan haramun ne amma saboda gudun 'bacin ran Madam din yasa take hakuri, Watarana ma haka take wuni batayi sallah ba sai ta dai-dai ci madam din ta fita kasuwa ko gurin sana'arta take fitowa taje ta dauro alwala ta dawo dakin tayi sallah a gurguje.......Sun fito bakin titi suna neman abun hawa wata mota henassi mai ruwan zuma ta tsaya a gabansu, 'katon mutum ne mai jikin girma zaune a bayan motar direbansa na jansa. Ya sauke glass din motar yana dariya, cikin turanci suka gaisawa da Madam, Baba Tinde yace."Kwana biyu bakya nema na ko banzo siyan masara ba." Madam tace"A'a oga na dauka kayi tafiya ne."! Baba Tinde yace."Eh nayi tafiya jiya na dawo zan shigo anjima kad'an." Tace."To sai ka shigo." Ya kai idonsa kan Asiya dake 'buya bayan madam tsoronsa takeji sosai ganin har wani shuni yakeyi saboda ba'ki ga fuskarsa tayi taya taya! da zane! Baba Tunde! yace."Madam wannan bab d'in fa she is beautiful girl." Madam ta washe baki dama irinsu Baba Tinde take so su tanka! Tace."Yarinya ta ce Ai." Baba Tinde ya lashi 'katon le'bensa yace."Okey zan shigo anjima mu tattauna." Madam na murna da farin ciki tace"Okey Oga ina sauraranka." Baba tinde ya daga mata hannu ya bawa direbansa umarnin tafiya....Madam murna kawai takeyi tasan yau zata samu kudi sosai tunda ta lura Tinde ya yaba da Yarinyar Babur suka shiga Asiya jikinta yayi sanyi dan irin kallon da Baba Tinde keyi mata yayi kama da irin kallon da Alaji Bawa yake mata jikinta na bata ba alkairi ne zai kawo shi ba...... Pls Kuyi sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege11* Suna komawa gida Madam Semi ta dinga wani lalla'bata motsi kad'an tayi zata tambayeta menene? sai tace babu komai, misalin 'kerfe biyar da rabi na yamma, Madam ta fita bakin titi domin fara sana'arta, Asiya kuwa na d'aki a kwance a katifa lokaci zuwa lokaci gabanta na fad'awa, duk sanda gabanta ya fad'i sai ta ambaci kalmar innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! Gajiya tayi da kwanciyar ta mi'ke a hankali ta isa bakin window dakin ta d'an d'aga labule a hankali tana le'ka waje, can ta hango Madam ita da wasu matasan samari suna tsaye da alama masara zasu siya, ta dinga kallon gurin tana nazarinsa, gabakid'aya babu mutumin arziki gurin yayi kama da bariki kowa nayi abinda yake so, masu d'aki-d'aki ne a jere ya kai hamsin ko wanne da numbarshi kuma ko wanne da mutane a ciki, amma mafi a kasari karuwai ne masu zaman kansu, sai dare yayi kaga maza nata karakaina a gurin, suyi ta shaye-sheye suna wasan banza a gurin babu me cewa dasu dan me hasali ma jami'an tsaron da zasuyi magana sunfi yawa a gurin suma suna zuwa su she'ke ayarsu ne a gurin, Tana kokarin komawa ta zauna motar Baba Tinde tayi parking sai ta dinga bin motar da kallo har direbansa ya bude masa ya fito, gabanta yayi wata mummunar faduwa shaf ta manta da mutumin yace zaizo gurin Madam! Baba Tinde na sanye da rigar atamfa blue da fari da blue d'in wando kansa da hula mai malafa yana ri'ke da wata sanda mai 'kyalli! (kwagiri) yana tura 'katon cikinsa ya nufi rumfar Madam Semi! Direbansa ya jingina jikin motar yana bin gurin da kallo. Madam Semi na hango Tinde sai ta soma washe baki cikin turanci take masa sannu da zuwa tana karkade masa gurin zama! Baba Tinde ya zauna yana murmushi da fad'in "Tun had'uwarmu daku ta d'azu na kasa samun kwanciyar hankali Madam hakika wannan yarinya taki ta dauke mun hankali ina so ki bani ita muje guest house dina mu kwana biyu tare nayi miki alkawarin baki kud'i masu kwari watakila ma ki daina wannan sana'ar da kikeyi." Madam ta saki ajiyar zuciya tace"Kada ka damu Oga zan baka yarinyata saboda na amince da kai ba zaka cutar da ita ba, amma ina so ka dan d'aga mana kafa zanyi magana da yarinyar gobe da yamma sai kazo ka dauketa." Baba Tinde ya d'an bata fuska yace."Madam kin san kuwa yanda na kwadaitu da yarinyar nan kuwa gobe tayi min nisa." Semi tace"Oga yanzu ma kana iya shiga domin ka dan rage damuwa kafin goben ina so in shirya maka itane." Baba Tinde ya washe katon bakinsa yana 'bab'baka dariya yace."Idan naji yarinyar nan zam-zam! kina da gwaggwa'bar kyauta mai tsoka." Madam tace"Zan kuwa baka mamaki! Baba Tinde ya mi'ke yana me zura hannunsa cikin aljihu ya dauko daurin kudi na dubu ashirin ya mika mata yace."Wannan kad'an ne daga cikin alkairan da zanyi miki mutukar na samu yarinyar nan a yanda nake so." Madam ta mike da sauri tana fad'in "Godiya nake oga, muje nayi maka jagora gurin yarinyar.....Tare suka jera suna tafiya Semi sai godiya take masa shi kuma yana sake jaddada mata cewar mutukar ya samu abunda yake bukata a jikin yarinyar to zaiyi mata alkairi ba d'an kad'an ba. Asiya na takure kan katifa gabanta sai faduwa yake yi dan tun bayan zuwan Baba Tinde ta rasa nutsuwarta ta shiga bandaki yakai sau nawa saboda fargarbar abunda ke tafe dashi.......Madam ta shiga dakin tana fad'in " Beby kina ina ne? kinyi ba'ko." Kafin tace wani abu Baba Tinde ya shigo d'akin idanunsa kur!! a kanta, tayi saurin sunkuyar da kanta a kasa, murya na rawa tace"Gani nan Madam." Semi tace"Okey ga Oga nan yazo gurin ki zaku gaisa ina fata dai baki mance maganar da mukayi dake ba ranar da na kar'beki." Murya na rawa tace"Eh ban mance ba." Madam tace"Good! Ta kalli Tinde tana kannare masa ido guda tace"Oga sai ka fito ko.. Yana kokarin zama gefan katifa kusa da Asiyan yace."Thank you Madam." Asiya yana zama kusa da ita ta matsa da sauri ta kasa d'ago kanta ta kalleshi tsabar yanda take jin tsoronsa muninsa yayi yawa gashi ba'kikkirin dashi! Baba Tinde ya sake matsawa jikinta sosai ya kai hannunsa zai rike nata tayi saurin daukewa tana kuka tace"Don Allah kayi hakuri kada kayi min komai ni musulma ce." Baba Tinde ya saki bakinsa yana kallonta tana kuka harda shashsheka! Ilahirin jikinta ya shiga bi da kallo yana lumshe ido yace."Baby daina kuka ki dawo ki zauna nan." Cikin hard'ad'diyar hausarsa yake mata magana yana nuna mata kusa dashi....Ma'kale kafad'a tayi jikinta sai kyarma yakeyi hakan na kara sanyawa sassan jikinta na rawa mussaman madaidaitan nonowanta da suke matse a cikin riga body Hork, Mi'kewa yayi da kyar ya nufi inda take ta buga wani tsalle ta haye katifar ta ma'kure jikinta tana rawar jiki tace"Wallahi ni matar aurece kada ka kusance ni ni musulma ce kai kuma kafuri ne." Baba Tinde ya fusata! sosai ya haura Kan katifar ya jawota da karfi ta fad'a katon kirjinsa sai ta zama kamar tsakuwa, hannu daya yasa ya matseta sosai yana wani irin nishi, hade da d'ora hannunsa kan d'uwawunta da suka matse cikin wani matsatssan wando da ya yi mugun d'ameta, sosai yake shafa mazaunanta yana numfarfashi, ita kuma sai kuka take had'e da buga kanta a kirjinsa tana fad'in"Ina da aure ni musulma ce kai kuma kafuri ne!!!!! Baba Tinde ya dagota rai a bace ya kifa mata mari! yace"Wannan kalmar ta isheni, babu ruwa na da musuluncin ki nawa na sani babu ruwana da auranki ke kika kawo kanki bariki kuma uwar dakinki itace ke iko dake idan kika sakeyi min magana sai naci ubanki." Asiya ta soma makyarkyata tana zubar da hawaye! bakinta yayi gum! dan wani irin mugun tsoronsa ne ya kamata, jikinta duk ya shika sai tayi lamo a jikinsa, ya dauketa kamar 'yar tsana ya ajiye kan katifa ya soma cire mata kayan jikinta, da tayi yun'kurin 'kwacewa daga hannunsa ta kalli 'kwala-'kwalan idanunsa da sukayi jawur duk sai taji jikinta ya mutu tsoro ya shigeta, tana kallo Baba Tinde yayi mata zir! shima ya kwabe kayan jikinsa, rintse idonta tayi tana kiran sunan Allah hawaye sai ambaliya yake a kuncinta, sanda Baba Tinde ya raba 'kafafunsa a kanta tayi nufin 'kwallara 'kara ya had'e bakinsu guri guda ya soma tsotsar harshenta kamar mayuwanci duk hannayensa na kan 'yan 'kananun breast dinta yana murzawa kamar zai tsinke nipples din.......Tana kuka tana saka gwiwarta 'karkashinsa tana so ta bugi jijiyarsa da yake soka mata jikinta, da yaji gwiwarta a gurin zai dauke saboda yasan darajar Kayansa shiyasa yake taka tsantsan da abarsa, Gani tayi jikinsa na narkewa sosai ya danneta nishi ma da kyar takeyi! tayi wani kukan kura kamar mai aljanu! ta tureshi ya fad'i kan katifa a guje ta dauki wando da rigarta ta afka toliet din dake dakin ta zura sakata ta zube kasan toilet din tana kuka!!! Wannan wace irin rayuwa ce ta jefa kanta a ciki, Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! Ya Allah ka futar dani daga wannan masifa da nake ciki." Abunda take fada kenan tana daga hannuwanta sama. Baba Tinde ya jima a zaune kafin ya dawo nutsuwarsa, a fusace! ya shiga mai da kayansa rai a 'bace ya futa daga dakin, Madam na ganinsa ya fito da fuska a murtuke sai tasha jinin jikinta da sauri ta bishi bakin motar tashi tana masa magana, ya tsaya yana kallonta a fusace! Yace."Ashe wannan yarinya bata da mutunci, ko kuwa dama baki fada mata waye ni ba, da har zata dinga kambaba! addininta kan nawa, ni take kira kafuri sannan tana kiran ita tana da aure! To ki ja mata kunne da kyau! kada na sake zuwa tayi mun wannan shirmen dake da ita duk zan hukunta ku." Madam ta soma rarrashinsa tana bashi hakuri, baiko saurareta ba ya shige mota direbansa yaja motar da sauri suka bar gurin. A zuciye Semi ta nufi dakin, tana fad'in" Kina ina munafuka algunguma! ba'kin ciki zakiyi min ko? to wallahi idan baki bi sharad'ai na ba zaki barmin d'aki! 'yar iska kawai kamar Baba Tinde Babban mutum kikewa iskanci."!!! A tsorace ! ta fito daga toilet din jikinta na rawa ta zube gwiwa bibbiyu "Dan Allah Madam kiyi hak.....Kafin ta karasa Semi ta zuba mata lafiyayyan mari! tace" Dan Ubanki dama haka mukayi dake? Asiya ta shiga girgiza kai jikinta na rawa! Tace"To me yasa kika 'ki yarda da Tinde da bukatarsa ba cewa nayi duk abinda yace kiyi kiyi masa ba, ko kina mun bakin cikin abinda zan samu ne."? Tana hawaye tace"A'a Madam bana miki bakin ji wallahi dan Allah kiyi hakuri kada ki koreni dan idan kika koreni bani da inda zanje ni kuma bazan koma garinmu ba." Semi tace"To wallahi kinyi na farko da karshe kika sake 'batawa Tinde rai sai kin barmin d'akina dan kinga ina rarrashinki ne yasa kike min iskanci gobe Tinde zai dawo ki bashi had'in Kai sosai ga dukkanin abinda ya nema daga gareki." Tace"In Allah ya yarda zan amince masa Madam." Semi ta fita daga dakin tana suratai da zaginta....Asiya zama tayi bakin kofar bandakin ta hada kai da gwiwa tana kacon da wannan rayuwa da take cikinta. **** Alaji Bawa ya xama kwarkwar a sakamakon abunda Asiya tayi masa dan likitan dake duba lafiyarsa ya tabbatar musu da cewar 'kwakwalwarsa ta samu matsala dan haka duk lokacin da sukaji yana sambatun surutai shi kadai to su kyaleshi idan ya gaji zai daina, haukan zai dinga zuwa sa'i da lokaci amma kuma idan an tsaya masa da shan magani kan 'ka'ida zai samu sauki!! Jikinsu duk a sanyaye suka dawo gida, dan a cikin motar ma ciwon ya tashi yayi ta sambatu yana tonawa kansa asiri kan irin abubuwan da yake yi na rashin alkairi! Maishanu hankalinsa yayi masifar tashi dan ba 'karamin tozarci da cin mutunci Maigari yayi masa ba, ya sanya jama'ar Fada sukayi masa fata fata! yana goge kwalla ya nufi gidansa zuciyarsa yana nadamar haihuwar Asiya tunda ta jawo masa abun kunya a gari. Washe garin ranar da aka sallamo Alaji Bawa daga asibiti ya shirya tsaf cikin manyan kaya sai kace wani lafiyayyan mutumin arziki ya nufi gidan Maishanu Maishanu na fitowa yaga Alaji Bawa sai gabansa ya yanke ya fad'i! Alaji Bawa ya mi'ka kasa hannunsa yana fad'in "Bani kudin sadakina da na biya, dan banci nanin! ba nanin! ba zata ci ni ba."! Maishanu ya hau diri-diri! yana kallon jama'ar da suka soma taruwa a gurin, yace." Alaji yi hakuri mu shiga daka ciki muyi maganar." Alaji Bawa Yace."Babu inda zan shiga matsiyaciyar 'yarka ta 'karasa ni kud'ina kawai nake bukata ka bani naci nanin! ba nanin ba zata ci ni ba."Ya sake maimata maganarsa, Maishanu yace."Alaji halin da ake ciki yanzu yarinyar nan muma bamu san inda take ba wallahi tun ranar da ta aikata wannan d'anyen aikin muka nemata muka rasa, kayi hakuri dan Allah duk inda ta shiga zan lalubo maka ita ka dauki duk matakin da kake gani yayi maka." Alaji Bawa, ya saki wata katuwar ashariya yace." Waye!! ni idan ka ganni a lahira to kaini akai, wannan matsiyaciyar yarinyar da ta kusa kasheni ta murd'e min ma'karfafata me zanyi da ita na sake ta saki uku."!!! Maishanu yayi salati yana fad'in "Alaji ya zakayi min haka."!? Alaji Bawa ya fusata sosai yace." Wai maishanu ko da hadin bakinka ne 'yarka keso ta kasheni."? Maishanu yace."A'a Alaji." Yace."To maza shiga ka dauko mun kudina." Maishanu yace."Wallahi bani da ko kwabo a cikin gidan nan Alaji kayi hakuri." Alaji Bawa baiyi wata-wata ba ya sha'ki kwalar maishanu yana kuza masa ashariya da fad'in "Dole ne ya bashi dubu bakwai dinsa dan beci nanin! ba nanin! ba za taci shi ba. Da 'kyar jama'a suka 'kwaci maishanu daga hannun Alaji Bawa, wanda yake ta zubaba zagi da wasu irin surutai marasa kan gado sai tonawa kansa asiri yake yi......Babu shiri maishanu ya tafi kasuwar dabbobi ta cikin gari domin ya siyar da saniyarsa guda ya biya Alaji Bawa kudinsa. Washe gari da yamma li'kis! Baba Tinde ya sake zuwa lokaci madam ta shirya Asiya cikin wasu matsiyatan kayan da suka fitar mata da tsaraicinta a fili, gashin kanta tasha gyara da mayuka masu kamshi, ta sanya mata farce irin na kanti sunyi za'ko-za'ko babu kyawun gani, ta fesa mata wani shegen turare mai mugun daukar hankali, har bakin mota ta rakota Asiya sai 'buya take a bayanta duk kunya da tsoron abunda zaije ya dawo ya dameta sai kokarin maida hawayen dake kokarin kufce mata takeyi, Tinde na ganin Asiyar hankalinsa ya tashi mutuka sosai kwalliyarta ta tashi hankalinsa Madam ta bude mata mota ta zauna kusa dashi, sai murmushi take sakar mata wanda ita Asiyan ta gane ko namene, Madam ta daga musu hannu tana fad'in "Oga Baba Tinde a sauka lafiya sai gobe kenan." Baba Tinde yace "Sai gobe da yamma zan dawo miki da ita, za kuma kiji alert idan na samu nutsuwa." Tace"Okey to godiya nake oga." Asiya sai kallonta take tana marairaice fuskarsa, madam taki kallonta sai ma ta matsa daga jikin motar direba yaja suka bar gurin... Pls kuyi sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *_Dan Allah ku daina tambaya ta in turo muku farkon littafin nan, ina ganin tunda nayi typing d'in ai nayi me wuyar duk me bukatar karanta littafin nan daga farko to ta tambaya a gruops ko kuma ta turo kud'inta na tura mata🤗 Sannan masu tambaya ta in inda novls dan Allah su daina bana karatun novls ballanta na ajiyesu a wayata duk me son wani novls din ta shiga gruops ta tambaya, ni bani da novls din kowa sai nawa, ina fatan kun fahimce ni._* *PAID BOOK!* *Free Pege12* Motar na hawa kan kwalta baba Tinde ya juyo yana fuskanta inda take zaune, tayi saurin sunkuyar da kanta kasa gabanta sai faduwa yake yi! bata ankara ba taji saukar hannunsa kan kirjinta, a zabure! ta matsa gefa jikinta ya soma rawa! Baba Tinde ya sha kunu yana kallonta cikin hard'ad'd'iyar hausarsa yace."Idan na kara ta'ba ki kika zabura ko kikayi mun ihu! sai na yanka ki! kud'i na biya antin ki tabani ke dan haka zan kaiki guest house dina nayi abinda nake so dake dan haka ki kiyaye." murya na rawa tace"Dan Allah kada ka cutar dani ni Marainiya ce kada ka lalata mun rayuwata." Baba Tinde ya dauke kansa daga kanta yana me daga wayar da ake masa, kukan zucci takeyi tana tunanin yanda zatayi ta ku'butar da kanta daga hannun wannan azzalimin, tafiya mai tsayi sukayi kafin taga sun shiga wata unguwa me yawan kangwaye da sabbin gine gine da alama unguwar sabuwa ce dan babu jama'a a cikinta sosai, wani katon gate taga sun shiga, ta dinga bin gurin da kallo ginin dake gurin ma abun kallo ne ita dai tunda take bata ta'ba ganin gini mai tsayi irin wannan ba, Baba Tinde ya fito daga motar yana dora sandarsa, kalle kalle yake yi a gurin, kafin ya juya ya kalli direbansa yace."Kaje da motar zan kira ka a waya gobe da safe." Da sauri yace."Okey oga." ya bude motar Yana kallon Asiya dake raku'be ta kasa fitowa sai 'kwalla take gogewa, tausayi ta bashi sosai kasancewar shi d'in bai jima da musulunta ba shiyasa yaji yana kishinta tunda addininsu d'aya, ya lura itama yarinyar ba'a son ranta bane tursasata akayi ga 'karancin shekaru da yana da yanda zaiyi ya taimaka mata to da yayi bashi da hanyar da zai taimaketa, Yace."Madam fito zan tafi da mota." Tana goge hawaye tace"Ka taimaka mun." Ya dan kalli inda Ogansa ke tsaye yace."Bani da hanyar da zan taimake ki Allah ya kubutar dake."! Baba Tinde ya buga masa tsawa da fad'in "Me kakeyi anan." Yace."Madam nake jira ta fito." Asiya ta bude motar ta fito tana takure jikinta, Da sauri shi kuma ya shiga motar ya fita daga gurin, Baba Tinde ya soma matsowa inda take tsaye tana matsawa baya haka suka dinga yi har sai da ya cimmata ya danneta a jikin bango yana shinshineta, a gurin ya dinga shafata yana zura hannunsa a cikin rigarta yana wani irin gurnani! Asiya da 'kyar take iya motsi kasancewar Tinde ya matseta sosai a bango sai ta shiga tari tana tureshi da hannyenta wanda hakan da takeyi kamar 'kara ingizashi takeyi, ya fita daga cikin hayyacinsa a d'imauce ya dauketa a kafada ya nufi cikin gidan da ita, dake benene yasa kafin su hau suka sha artabu dan zillo ta dinga yi tana dukansa tana kuka da rokon shi, shi kuma yana sake matseta sosai yana tallafeta har sai da suka shiga katafaran dakinsa da ya gaji da haduwa, a bed ya jefata ya tsaya yana kallonta fuskar nan tasa a murtuke hakika yarinyar ta kaishi ma'kura sosai ta 'bata masa rai! ya kuma lura tana da taurin kai! ya tsani zai nemi mace ta dinga yi masa ihu! dan haka yanzu zai nunawa yarinyar shi ba'ayin haka dashi. Kayan sa ya kwa'be yayi zigidir haihuwar uwarsa katuwar jijiyar mai kauri da tsayi tana tsaye kamar torchlight ya nufe ta gadan!-gadan!!! Rintse idonta tayi da mugun saurin tana makyarkya! ashe ba taga komai ba gurin Alaji Bawa ashe bai da komai kan Baba Tinde sandar raken Baba Tinde muguwar katuwa ce mai firgita mace wannan duk wacce ta ratsa sai taji i jikinta shiyasa shima yake masifar ji da abarsa......Ihu! ta kurma! mai karfin gaske! wanda takeyi babu wanda ke jinta sabida yanayin gidan da take ciki, tana ihu! da fad'in "Ya Allah ka kawo mun a gaji kada wannan mutumin ya samu galaba a kaina, Ubangiji Allah ka bani rinjaye a kansa, Allah ka ku'butar dani daga hannun ba'kin mugu azzalimi."!! Baba Tinde tunda yaji irin adduoin da takeyi masa sai ya kara fusata sosai! ya jawota ta karfib tsiya ya yage ficiciyar rigar dake jikinta, ya cire breziyar ya jefar da ita a kasa, wandon dake jikinta yake kokarin cire mata ta rike blet din sosai tana kuka fuskarta tayi gaje gaje da hawaye da majina! " kada ka cutar dani ka taimake dan Allah dan annabi kada ka cuceni ni musulmace."!!! Wannan kalma da take yawan nanatawa na masifar bashi haushi , kawai sai yasa 'katon hannuta ya buge mata baki a take kuwa ya fashe abunka da bakin da baya samun kulawa, ta gumtse jini da majinar dake bakinta ta fesa masa a fuska!! Da sauri ya saketa yana ya mutse fuskarsa, Baba Tinde mutum ne shi mai mugun 'kyankyami! wannan abun da tayi masa yay bala'in tunzura masa zuciya, ya bude idonsa da sauri! Wayam! bata gurin! ya juya da saurin gaske can ya hangota bakin kofa tana kici kicin budewa dan har ta saka 'yar ficiciyar rigarta da wandonta, a fusace ya cimmata ya dauki blet ya shiga lafta mata yana zaginta! faduwa tayi kasan dakin tana ihu! da ceton kanta, boll ya dinga yi da ita yana sake lafta mata blet din a jikinta huci! kawai yake yi, taje ta matse jikinta cikin kusurwar dakin tana kuka da had'e hannuwanta guri guda taba bashi hakuri! Imani da tausayi gabadaya ya gushe a tare dashi, ya raba kafarsa a kanta, tana kallon katuwar jijiyarsa na so ta tsukale mata idonta, shahada tayi ta rintse idonta gam! ta cije! bakinta had'e da had'e ha'koranta guri guda, dai-dai lokacin da ya d'aga blet d'in da niyyar dukanta, ita kuma a dai-dai lokacin ta had'a hannuwanta biyu ta kama jijiyarsa da wani mugun karfin gaske ta matseta!!! tana mutsikata cikin tafikan hannayenta!!!!!!! "Oh my god"!!!!!!!! Baba Tinde ya fadin wannan kalmar a take 'kafafunsa suka soma rawa ya kasa tsayuwa dasu, ihu!! kawai yake kurmawa yana ganin dishi dishi a idanunsa, kawai sai saukar fitsarinsa taji a fuskarta kafin ya silale ya fad'i 'kasan d'akin wata kumfa na fitowa daga bakinsa, da mugun saurin gaske ta mike ta tsallake shi jikinta na kyarma ta maida ficiciyar rigarta blet d'in ma bata dauka ba, ta nufi kofar fita daga dakin, tayi tayi ta bude takasa, da sauri taje tana zazzage rigarsa da ya cire ta dauki key din tana duban inda yake kwance yana kyarma!! da daga mata hannu! key din ta zura da sauri ta bude dakin ta fice a guje!! koda ta fita harbar gurun rasa ina zatayi tayi, ga gate din a rufe ta dinga kallon manya manyan katangun gidan babu damar ta haura, can dakin da ta gani daf da bakin gate din ta nufa maigadi na kwance a dakin ya rufe fuskarsa da hula yana jin music ta lalla'ba ta d'auki key d'in dake gabansa, Fitowa tayi ta nufi karamar kofar da kyar ta iya saka key din a jiki dan tsayinta be kai ba sai da tayi d'age gabad'aya karfinta ta had'a guri guda ta murza key din kofar ta bude, da kyar ta tura ta ta dan bude kadan sai ta ra'ba jikinta ta fice da saurin gaske!! Tana fita ta kalli gabas da yamma! ko'ina shuru ga duhun magariba ya gabato ta gane hanyar da suka biyo dan haka ita ta dauka a guje da wani irin gudu tanayi tana waigen bayanta. Wani irin gudu takeyi wanda ita kanta bata san ta iyashi ba addua take kan Allah yasa tana futa titi tasa mu me taimakonta dan tasan ko giyar wake tasha bazata komawa Madam ba watakila ma ta kasheta ga wannan katon arne data kusa kaiwa lahira shima tasan ya kamata sai ya dauki fansa, a kanta!!!! Cikin galabaita da sarewa da al'amarin ta fita titi, lokacin gari yayi duhu sosai dan har anyi sallahr isha'i ma ga titin dama ba sosai jama'a kebi ba dan gabadaya ma motocin haya basa hawa titin masu motar gida sunfi hawa kansa, durkushewa tayi a gefan titi tana fad'in "Ya Allah ka dauki rayuwata na huta da wannan bala'i! Kaico da wannan wahalalliyar rayuwar da nakeyi Allah ka kawo mun agaji."!! Kawai sai ta mike taje ta kwanta tsakiyar titi plate tana fad'in " Akan in aikata zina gwara mota ta takeni na huta dama wannan rayuwar da nake bata da amfani." Rintse idonta tayi tana sauke ajiyar zuciya kalimatusshada kawai takeyi a cikin zuciyarta, can taji 'kugin mota, ta sake rintse idonta tana sake fad'in "La'ila ha'illallahu Muhammadur rasulillahi Salallahu alahi wasalam.""!!!! Kawai taji wani irin cin burki dai-dai kanta, motar tayi wani irin 'kara kuuuuuuuuuuu!!! a razane ta bud'e idonta ta 'kwallara 'karar da tasa gurin ya amsa! Gabakid'ayansu suka fito daga motar cikin tsananin rud'u da tashin hankalin abinda yake shirin faruwa dasu, Professor Mommy Hafeez da Farhana suka kewaye Asiya dake rintse da ido tana sakin 'kara da sake nanata kalmar shahada! Professor yayi maza yace da Mommy taje ta rik'eta a jikinta ta tofa mata addua." Allah sarki Mommy mace mai tausayi babu tunanin komai taje zata rungume Asiya! Hafeez yace."Mommy d'an tsaya." taja ta tsaya tana kallonsa, yace."Haba Daddy a irin wannan gurin da kuma daddare kawai muga yarinya kwance a tsakiyar titi sannan kuma kai tsaye mu tunkareta nifa ina gajin aljana ce ko kuma 'yar 'kunar ba'kin waike mybe ma bomb ne a jikinta wallahi." Maganar da Hafeez d'in yayi tasa dukaninsu suka dawo hayyacinsu, dan Mommy ma dake kusa da Asiya tayi saurin matsawa Farhana na bayanta a 'boye shi kuwa Daddy wayarsa ya kunna yana haske Asiya da ita, Nan Hafeez ya tsira mata idonsa yana nazarinta sosai ganin ma babu riga a jikinta yasa ya sake tabbatarwa cewa aljana ce ga uban gashinta da duk ya barbaje a kafadarta da gefan fuskarta. Daddy yace."Ke yarinya da mutum muke magana koda aljan." Asiya ta d'ago kanta tana kallonsu, sai ta fashe da kuka tace"Me yasa baku takani da mota ba na mutu wallahi na tsani wannan rayuwar da nakeyi, ni mutum ce kamar kowa."!!!Hafeez yace."Karya kikeyi."!! Professor yayi saurin d'aga masa hannu yace."Ya isa Hafeez yarinyar nan daga ni dik inda ta fito ba mai kyau bane, kuma siffar aljan kana ganinta tafuta daban wannan yarinya mutum ce kamar kowa." Asiya tace"Wallahi ni mutum ce ba wata hallita ba wani mutun ne ya sato ni zai yanka ni Allah ya ku'butar dani." Mommy da Farhana dashi kansa Professor din jikinsu yayi sanyi Mommy tace"Allah sarki baiwar Allah tashi muje kinji ko ai ba kwanciya Za kiyi akan titi ba idan kikayi haka kin butulcewa Ubangiji da ya kubutar dake daga hannun azzalimai." Asiya ta yun'kura da 'kyar ta mi'ke tana kare jikinta dan har yanzu babu riga a jikinta sai yagaggiyar rigarta da Baba Tinde ya yaga mata.....Mommy ta rike hannunta tana fad'in "Muje mota sai kiyi mana bayanin a inda kike."? Hafeez yace."Mommy dan tsaya." Ta tsaya tana kallonsa Professor yace."Wai kai Hafeez meye hakane." ? Ba tare da yace masa komai ba ya nufi inda take tsaye, Yace."Ni ban yarda dake ba wallahi sai na duba ki sosai kawai ba zamu shiga mota dake ba bomb ya tashi damu." Yana gama maganarsa ya shiga lalube mata jikinta, rigar da take kare kirjinta da ita ya fizge ya dinga haskata da hasken wayarsa, Professor kuwa naganin iskancin da Hafeez din keyi sai yaja tsaki ya bar gurin, Mommy ce ta dinga kakkare Asiyan tana fadin "Hafeez wai baka da hankali ne zigidir zakayi mata ko me? ." Mommy jikina na bani yarinyar nan 'yar 'kunar ba'kin wake ce ni ban shirya mutuwa yanzu ba."! Farhana ta kunshe baki tana so tayi dariya ta lura Yayan nata da gaske yake. Asiya kuka takeyi tana ture hannunsa dake jikinta tana kare kirjinta take fad'in ''Kabari ka daina ni ba 'yar boko haram bace wallahi bana tare da bomb a jikina." Mommy da abun ya isheta da kanta ta buge hannunsa tana masa fada sosai! Ita kuma Asiyan sai 'buya take a bayanta tana waige-waige bata so Baba Tinde yazo ya sameta a gurin. Ganin bai samu abunda yake zargi ba a jikinta yasa yay gaba yaje ya bude mazauninsa ya zauna, Mommy ta rike hannun Asiyan dake layi suka shiga mota, Hafeez din ne ke driving yaja motar da sauri suka bar gurin. Pls kuyi sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ *Free Pege13* Baba Tinde da rarrafe ya iske inda wayarsa take, ya samu ya d'auko da kyar ya zauna yana rintse idonsa zufa sai kwaranya take da jikinsa, hannunsa na kyarma ya nemi numbar dravar sa Emanuel wanda ya koma Musa, saboda tsabar 'kin musuluncin Baba Tinde yace shi ba zai kirashi da suna Musa ba da sunansa da ya daukeshi aiki zai kirashi wato Emanuel........Emanuel ya daga wayar da sauri ya bude baki zaiyi magana yaji muryar ogan nasa a sha'ke! "Emanuel maza maza!! kazo da mota ka kaini asibiti bani da lafiya."!! Da sauri yace."Okey Oga ganinan." kashe wayar yayi ya dauki key ya futa yana mamakin to me ya samu ogan nashi, sai ya soma tunane tunane ko dai yarinyar nan ce tayi masa wani abun? shi yafi zargin ko wu'ka tasa ta yanke shi dan ta kubutar da kanta be kawo komai ba sai hakan, amma hakika yanda yaji muryar ogan nasa na futa da kyar ya gane yana jin jiki. Kuka takeyi a cikin motar me shashshe'ka duk ta cika musu kunne gashi Mommy da Professor sunyi rarrashin har sun gaji sun zuba mata ido......Hafeez sai tsaki yake ja! wai shin wannan yarinyar wace irin ce sai bata hakuri akeyi ana rarrashinta tabi ta damu mutane da kuka shi wallahi ya tsani kuka kunnensa sai kud'a yake masa. Sitiyarin mota ya buga da kar'fi! dan har sai da motar taso ta kufce daga hannunsa, cikin tsawa! yace"Ke! dallah malama kiyi wa mutane shuru haka duk kin bi kin damu mutane Allah Daddy zan tsayar da motar nan yarinyar nan ta futa ni wallahi ta cika mun kunne."!! Asiya tayi saurin saka hannunta a baki ta rufe hawaye na sake kwaranya a fuskarsa rayuwarta kawai take tunani da kuma tunanin shin wad'annan mutanan da suka dauketa mutanan arziki ne ko kuwa.! Gashi ganin farko da tayiwa me wannan maganar take jin wani bala'in tsoronsa duk da a cikin duhu ta kalli fuskarsa ta gane bai da fara'a kuma masifaffe ne ko ga yanayin maganarsa ma......Mommy tace"Kana dai jin yanda muke ta bata baki takasa yin shuru ni wallahi tausayi take bani kukan da takeyi zaisa ta samu sassaucin abinda ke damunta." Yace."Mommy mu kuma sai akace ta shiga hakkinmu kawai daga taimako sai ta sa mana damuwa da ciwon kai! kowa da kika gani a duniyar nan yana da damuwa hakuri yake." Professor Yace."Ya isa malam ai tayi shuru masifar sai ta 'kare."! Hafeez shuru yay yana d'an jan tsaki 'kasa-'kasa.....Asiya gum! tayi da bakinta tana rarraba idonta a motar 'kamshin turaransu duk ya cika mata hanci gefe guda kuma tana tunanin Baba Tinde ita kanta tasan ba tayi masa da sau'ki ba! ai tunda ta gane lagon maza to kuwa duk wanda zai kawo mata wargi tasan abunda za tayi ta ku'butar da kanta, tana cikin wannan tunanin suka isa gidan, maigadi ya bud'e katon gate din gidan motar ta kutsa kai ciki, ko ina haske dal dal ga wasu shuke shuke sunyi shar shar dasu, wata katuwar rumfa taga sun nufa sai kace katin siyar da motoci zuciyarta ta sake tsinkewa, Hafeez yayi parking din motar , Bilya mai musu hidima da gida shine yazo ya budewa Prof motar ya futo yana fad'in Yallabai sannuku da zuwa, ya aka baro su Baba Inna wuro."? Professor yana zare glass din dake idonsa yace."Duk sunanan kalau Baba ma tace zata zo insha Allah." Bilya yace." Allah ya kawota lafiya, Ya juya yana wa Mommy barka da zuwa, ya dan risina Yace."Hafeez an dawo lafiya." Yana 'kokarin barin gurin yace."Lafiya lau muka dawo Baba Ina wuro tace zata zo gidan nan saboda kai wai dik kafi masu aikin gidan kirki da mutunci." Bilya ya washe baki yana fad'in "Kai naji dadi wallahi Allah ya kawota lafiya." Hafeez wucewa yay ya bar gurun, Bilya ya kalli Farhana da Asiya wacce take ta ra'bewa tana 'buya bayan Farhana yace." 'Yar fara ba'kuwa mukayi kenan! amma kuma ba tayi kama da 'yar 'kauyen Falgore ba." Farhana tace''Bilya dad'ina da kai cika baki kai komai sai kace 'kauyen Falgore kaima d'an 'kauye ne dan har gwara falgore kan garinku, kuma sai na fad'awa Inna Wuro cewar kullum kana kushe garinsu kaga daga nan sai ta daina zumud'in zuwa gurunka."Bilya yace."Afuwa Faratu dan Allah kada ki fad'a mata ai ni dake bata 'bace." Farhana tace"To kada na sake jin kayi maganar Falgore! Yace."Insha Allah ba zan sake ba." Ta kalli Asiya dake kallonsu, tace."Muje ko."! Asiya tabi bayanta zigwi zigwi gabanta sai fad'uwa yake girman gidan Professor yayi masifar bata mamaki bata ta'ba zaton zata tako kafafunta irin gidan ba, sai da suka shiga parlon ma ta sake sarewa, haske ko ina da wani kamshi maidadi da sanyi-sanyi maishiga jiki, ta dinga kallon tankamemen palon mai dauke da matattakalar bene uku, 'kasan sa palo uku kowanne da shirga shirgan kujeru hade da labuye to mach, ga wani dogon abu da tagani mai kujeru guda goma sha biyu ko wane 'bari shida shida ne, tsakiyar gurin daga sama wata fitila ce take futar da wani haske mai kyalkyali, kayan abinci ne reras kan daining table d'in.....Prof mutum ne shi mai tsananin sha'awar ta'adun india shiyasa da ya tashi yin ginin gidansa ya tsara komai irin nasu, gidan Professor tamkar gidan hamshakin maikudin india gidan prof tamkar gidan (Amita bachan) saboda yanda aka kashe masa kudi akayi masa tsari mai kyau da burgewa.....Asiya wata irin atishawa ta soma saki, sanyi Ac ya soma ratsata, Mommy tace"Farhana kuje dakinki tayi wanka ki bata kaya tasa sai ku sauko muci abinci tasha magani da safe sai mu zauna da ita." Farhana tace"To Mommy.'' Tace."Muje ko." Asiya ta dinga d'ararewa tana jin tsoron hawa matattakalar benan gani take kamar zata zame ta fad'i, ties d'in sai daukar ido yake tana kallon kanta a jiki gani takeyi ma kamar glass ne! Farhana tayi nisa da hawa ta tsaya tana kallonta tace"Ki hawo mana kin tsaya ko bakiji abunda Mommy tace ba." Cike da tsoro tace"Tsoro nakeji." Farhana ta tsaya tana kallonta cike da mamaki, tagane da gaske dai tsoron takeji sai ta sauko ta kama hannunta tace "Muje na ri'ke ki ba zaki fad'i ba." Suka soma hawa benan, Asiya sai ri'ke hannun Farhana take tana rintse idonta, da kyar suka hau biyar Asiya ta tsaya 'kafafunta na rawa, sai hawaye shaaaaa! tace''Yanzu idan na hau waye zai sauko dani naga ko rabi bamu hau ba ni wallahi tsoro nakeji." Ta bawa Farhana tausayi da dariya amma bata dara ba tace"Haba 'kawata babu fa wuya dandai baki saba bane kuma ta inda kika hau tanan zaki sauko da kanki." Asiya ta shiga share hawaye tana sha'kar majina itafa ta rantse ba zata hau wannan abu me tsayin ba!!! Cikin d'amammiyar vest da short nickar yake saukowa daga benan shi, can ya hango su suna artabu, ya d'an tsaya yana kallonsu na minti uku nan ya gane kan abunda suke, Yace."Ke Farhana meye wai." ? Farhana tace"Yawwa big bro wai kaga tun dazu ta'ki hawa sama wai ita tsoro takeji har da kuka." Abun yaso ya bashi mamaki! da kuma yayi tunani sai ya kauda mamaki, a d'azu kallo guda yay wa yarinyar ya gane 'yar 'kauye ce sosai da kuma yanayin yanda take maganarda He da he duk da cewar ba sosai take ba, amma mutumin birni dana 'kauye ya fita daban. Inda suke ya nufa cikin wata iriyar tafiya yana wani cilla hannu da d'an d'aga kafa, ya karasa yana kallonta, Asiya ta risinar da kanta da sauri gabanta na bala'in fad'uwa, duk sanda za taga namiji da gajeran wando sai ta tuna Alaji Bawa da Baba Tinde, Yace."Ke! meye haka? dallah!! hau kada kiyi mana 'kauyanci anan."!!! Kasa kallonsa tayi gabanta sai bugawa yake yi.......Cikin tsawa yace."Ko bakiji abunda nace ba."!! Da sauri ta ri'ke hannun Farhana suka cigaba da hawa benan, yasa hannu kan tarin sumarsa dake bala'in ci masa kud'i yana sosawa, yana bin bayanta da kallo, gabakidaya rigar kamar ba jikinta take ba dik bayanta a bud'e ga wandon dake jikinta ya wani matseta sosai ya fito mata da zahirin hallitarta, wawar ajiyar zuciya ya sauke! yana jan tsaki! ya nufi daining ya zauna, wunya yake ji sosai dan tunda sukaje Falgore bai saka komai a cikinsa ba sai fura da nono itama sai da Inna wuro ta takura masa yasha, yana kallon su Mommy da Professor suna ta ciye ciyen gargajiya (Zogale rama da yad'iya dinkin! da 'kuli-'kuli) ko sha'awa basu bashi ba shi mamaki ma yake yi yanda suke ta cin ganyayyaki sai sunje cikinsu ya rud'e! duk ranar da sukaje Falgore da yunwa yake dawowa Inna wuro tayi ta masa masifa da 'korafi kan shi yafiye iyayi da tsirfa. Bubbud'e kwanukan abincin ya shigayi a hankali ya soma zubawa a plate, yana d'an ya mutsa fuskarsa, ya zuba iya yanda yake so, abincin ya d'ebo a cokali zai kai bakinsa, ya ajiye yana jan tsaki! 'kasa yay da kansa yana murza goshinsa, yarinyar nan ta tsokano shi sosai dan tun a mota yake daurewa , shifa ko yaya idan zai kalli wani 'bangare na jikin mace hankalinsa mugun tashi yake, shiyasa sam ne fiya kallon indian film ba dan wataran ma idan ya shigo yaga suna kallon india baya zama, idan kallon rungume rungume da tsotse tsotse yake so ya gwammace ya kalli bf mai gabadaya, yasan idan ya kalli Bf wani sa'in yakan iya samun satisfaction amma indian film babu abinda suka iya sai dai su tayarwa da mutan hankali, yanzu ma to kallon wasu 'bangarori na jikin Asiya ya sanya masa kasala gami da tsananin sha'awa, dole kuwa ya nemawa kansa mafita, dan ba zai zauna ya mutu cikin dare ba.....Kujerar da yake zaune ya tura baya ya mi'ke yana jan tsaki, benanshi ya nufa, ya dauko key, yana sakkowa Mommy Da Prof suma suna sakkowa, diriricewa yayi yaso ya fice kafin su sauko, Professor yace."Ina zakaje na ganka da key."? Ya dan dafe kansa cikin basarwa yace."Wallahi Daddy muna shigowa Isha'k ya kirani a waya wai yana airport ya sauka naje na dauko shi." Prof yace."Bashi da direba ne? ko kaina ka zama direbansa ban sani ba."? Dariya yay yace."No! Daddy kasan fa yanda muke da Friends d'ina, Isha'k nada direba kawai dai yana so ni naje na daukoshi ne." Prof ya kalli a gogon dake daure a hannunsa yace"Yanzu tara da rabi na dare idan ka futa sai lokacin da muka ganka ko."? Cikin d'an 'bacin rai! yace."Haba Daddy ya kake wannan maganar ne? nifa ba yaro bane daddy ina daukoshi na ajeshi gidansa zai dawo gida." Mommy tace"Dan Allah kada ka le'ka Club dan ni wannan shigar dake jikinka tasa jikina yay sanyi." Yace."Mommy babu fa inda zani dan Allah ku kwantar da hankalinku." Professor baice komai ba ya nufi gurin cin abincin, Mommy tace"Myson bazan bar palo ba sai naga shigowarka." Shareta yay ya futa daga palon wai kamarsa ake wa wannan abun an saka masa ido sosai sai kace wani karamin yaro za'ace masa ga lokacin da zai dawo idan ya fita mtsssw! yaja wani matsiyacin tsaki lokacin da yake juya kan motarsa da niyyar fita daga gidan. Asiya wanka tayi da ruwan d'umi ta gasa jikinta sosai ta fito,daga toilet din ta zauna gefan bed tana kalle kalle a dakin, daki sai kace aljannar duniya dubi wani irin gado kamar jirgi, ko a bandakin ma hauka iri iri ta dingayi kafin tayi wanka ta futo, Farhana ta mi'ka mata wata atamfa nicham me ja da 'baki d'inki doguwar riga mai madauri a baya, dinkin irin me brestcop ne kuma da yake Farhana bata da da wani girman jiki sosai sai rigar ta shige Asiya, dan har Asiyan ta fita kumari da 'baragen girma shiyasa rigar ta dan kamata daga kirjinta, Farhana ta busar mata da gashinta ta gyara mata ta daure mata shi guri guda, tace "Kiyi sallah bari nayi wanka sai mu sauka kasa." Farhana na shiga toilet Asiya ta tsaya jikin mirror tana ta kallon kanta da kanta, hannunta ta dora kan fuskarta tana shafawa, gani tayi kamar ba ita ba, sosai take dudduba jikinta, Jin motsin fitowar Farhana daga toilet ya sanya tayi maza taje ta hau kan dadduma ta dauki hijab ta zura ta tada sallah. Farhana ta fito ta shirya a gurguje itama ta hau kan dadduma ta tayar da sallah! Suna idar da sallahr suka sauka 'kasa, wannan karon Farhana ba tasha wahala da ita ba, ta sauka amma cikin tsoro da d'ari-d'ari!!!!!!!!! Sai da ya hau kwalta sosai sannan ya kira wayar Safna, lokacin suna tare da Isha'ik! dan dama Safna tunda taji Hafeez yace mata zasuje kauye da famliys dinsa sai kawai ta gayyaci Isha'ik yazo ya d'ebe mata kewa, Safna nacan wata duniyar Hafeez na kiran waya bata sani ba, yaso ta d'aga wayar tasa, domin ya shaida mata zuwansa, dan ya soma shan jinin jikinsa da irin kallon da maigadin Huzaifa ke masa, dama yaso ta d'aga wayar ne yace ta fito ta sameshi a mota a bayan layinsu, in yaso cikin motar ma zasu iya komai......Isha'k ya kira to da yake shi wayarsa na kusa dashi, sai a kasa mu ya dauka, shima a sha'ke yake magana dan lokacin Safna ce a kansa ta ri'ke wuta sosai tana bugunsa, Yace."Ya akayi ne my friend. "? Hafeez yace." Guy yane naji ka sama-sama ko dai har ka hau network ne."! Isha'k ya lashi le'bansa yana shan yaji tare da d'an shafa kirjin Safna da hannunsa wanda baya aiki dashi, yace."E....Kai ma ka...sani guy ina nan gidan Huzaifa Safna ta ri'ke wutaaaa."! Hafeez yaji wani iri a tare dashi! Okey ashe dama tana tare da Isha'k ne shiyasa ta'ki d'aukar wayarsa, ta'be bakinsa yay ransa ya 'baci sosai, a take yaji wani irin kishin Isha'k d'in, Yace."Okey sai da safe kenan dan yanzu kome zan ce maka ba zaka gane ba." Isha'k yace."Sosai ma kuwa kabari da safe zan shig........! kafin ya'karasa maganar, yaji yo ihun!!! Safna tana fad'in "Zan kawo ahhhh! Oh my god!!! Ahhhh!!!!."""""" 'Kit!!! yakashe wayar ya jefar da ita kusa dashi, babu shakka Safna zata san tayi da d'an halak!! Sai da ya dawo nutsuwarsa tukkuna ya kunna motar, kai tsaye, hanyar gidan Isha'k d'in ya nufa, tunda yana tare me d'ebe masa kewa, to shima bari yaje gurin matarsa ta d'ebe masa, kewarsa, tunda Isha'k yayi masa tayi kan matarsa Fadila bai ta'ba sha'awar zuwa gidabshi ba, sai yau yaji yana sha'awar zuwa domin daga Safna d'in harshi Isha'k din sun 'bata masa rai sosai, shiyasa ya yanke shawarar zuwa gidansa gurin matarsa Fadila ta biya masa bukatarsa. _'Yar uwa kiyi maza ki garzayo kizo ki biya kudin littafin nan, na kusa gama free pege, littafin DA WATA A 'KASA Yanzu ma a ka fara kada ki sake ayi babu ke #300 kacal ta biya miki bukata_ Pls Kuyi sharing. _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *DEDICATED TO:* *HAUWA S ZARIA* *MMN USWAN* ('Kawar Rufin Asiri) *ALLAH YA BARMU TARE YA 'KARA ZUMUNCI DA 'KAUNTA TA TSAKANI DA ALLAH* *Free Pege14* Hafeez na isa gidan Isha'ik maigadi ya bud'e masa gate ya shiga da motarsa cikin gidan ya samu yay parking ya futo daga motar, maigadi ya iske inda yake cike da ladabi ya d'an risina yana gaishe, Hafeez ya amsa yana kokarin shiga cikin gidan, maigadin yace."Yallabai d'in kuwa baya nan dan na dauka shine ma lokacin da ka shigo." Yace."Eh nasani ai." Da sauri maigadin yace."Afuwa maigida." Hafeez yaja tsaki yay gaba ya tsani sa'ido irin na mutane wallahi, Hafeez na shigewa maigadin yayi tsuru yana mamakin wannan al'amari, shi dai tunda abun nan ke faruwa bai ta'ba ganin Hafeez din yazo gidan da daddare ba, yafi ganin d'ayan Huzaifa shine yake zuwa a kai-akai gidan, to kwana biyu ne bai ga yazo ba, abunda ke bashi mamaki me yasa idan zasu zo sai maigidan baya nan, kuma idan sun shiga ciki su dade sosai dan watarana ma har sai yayi bacci ya farka tukkuna zaiji futowarsa, zama yayi kan kujerarsa yana tunanin al'amarin, babu shakka abunda ke kawo su gidan ba abune mai kyau ba, kuma a yanda ya fahimta shine da sanin maigidan komai ke faruwa. Fadila na can cikin bedroom ta kwanta bacci yana fizgarta dan tayi kiran wayar Isha'k din har gaji bai dauka ba sai kawai ta hakura ta kyaleshi ta kwanta tasan dama ya saba shigowa gida cikin talatainin dare, Masifaffan 'kamshin turaran da take so ne ya ba'kunci hancinta, tayi saurin mi'kewa zaune tana kallon ba'kin 'kofar shigowa, Hafeez ta gani tsaye a bakin kofa da irin shigar da take masifar so hannunsa guda cikin aljihun wandon dake jikinsa, ajiyar zuciya ta sauke, ta mike cikin 'yar iskar figalalliyar rigar baccinta tana wata irin tafiya da karkad'a jiki ta nufi inda yake tsaye......Cike da barikanci ya bud'e mata hannuwansa, yana sakar mata shu'umin murmushi, a guje taje ta rungumeshi tana shafa wuyansa da tarin sumar kansa, Dan cirota yayi daga jikinsa yana kanne mata ido daya yace."Bab yau Kinyi mamakin ganina a gidanki."? Fadila tayi wani murmushi tana shafa sajen fuskarsa tace"Wallahi nayi mamaki guy sai da na cire rai daga kanka sannan kazo in da nake aikam zan jiyar da kai dad'in da baka taba jin irinsa ba." Cike da zumud'i yace."Da gaske kike baby."? Ta wani ja nishi tana shafa faffadan kirjinsa tace."Da gaske nake wallahi kai dai kawai ka saki jikinka." Yace."Idan mijinki ya dawo fa." Ta'be bakinta tayi tace"Ba zai shigo yanzu sai wajejan uku ko da asuba yana gidan Huzaifa." Hafeez ya sauke ajiyar zuciya yaja hannunta suka nufi bed, dorata yayi a cinyarsa yana tsirawa nononta ido yace."Nifa ba zuwa nayi inyi sex dake ba, kawai ina so kiyi mun wasa na samu satisfaction kin gane." Fadila ta d'an 'bata fuska tana tura masa brest dinta dai-dai bakinsa tace"Uhmm!uhmm! gaskiya ni na kwad'aitu da kai kuma ni bana gane romatinc dole sai an shigeni nake samun gamsuwa. Yace."Ban shirya wannan ba yanzu idan kin saki jikinki zaki samu gamsuwar da baki ta'ba samu ba dani, zan miki abinda mijinki bai ta'ba yi miki irinshi ba." Ajiyar zuciya ta sauke, ta shiga sa'bule rigar jikinta, ya tsira mata idonsa har tayi zurrr! gaskiya nononta ya bashi sha'awa sosai duk da basu cika girma da yawa ba amma tsarinsu da cikarsu ya burgeshi ga nippls din masu kauri da girma. Harshe yasa ya d'an lashi saman nipple din ta wani gantsare tana tura masa breast din a bakinsa, kansa ta dam'ka! tana shan yaji! ahhhhh!! tafad'a lokacin da taji ya soma tsotsar nonon nata yana murza dayan, ta dinga shashshafa kansa da sassan wuyansa, a gigige ta tunkudashi ya kwanta plate kan bed din, sauka tayi ta soma cire masa kayan jikinsa, Cike da za'kuwa, ta kama joystick d'inshi da ta wani irin mi'kewa ta cika tayi fam har ta soma kawo ruwa, a bakinta tasa ta soma sucking dinsa ya mi'ke zaune da sauri ya kamo kanta yana tura mata a bakinta gurnani yake yana wani irin abu da bakinsa, Fadila ta dinga yi masa salo salo wanda ya kusa sa shi zaucewa, ihu! ya shiga yi jikinsa na sake shikawa bakinta ta cire ta kama da hannunta tana ja hade da hura iskar bakinta a gurin, a gigice ya kamota ya kwantar da ita, kan bed din, kafafunta ya bude ya turmutsa babban yatsansa a viginal dinta Ihu! ta saki mai tafe da shashheka ta sake wargaje kafafunta ruwan ni'ima na gudana a kasanta Hafeez ya dinga 'kwa'kuleta! da hannunsa yana shan nononta guda, Fadila ta dinga sambatu tana sake rirrikeshi, "Wow! ahhh! kayi da kyau!! ka caccaka!!!! sosai ahhhh!! irin sambatun da take kenan tana shashshafa jikinsa, Hafeez duk wata fitinar dake kan Fadila sai da yayi maganinta tsaf! ya gamsar da ita ba tare da ya ratsa jikinta ba, Fadila ta dinga kallonsa tana mamakin baiwar da Allah yayi masa, ko kusa ko alama ba zaka hadashi da Mijinta Isha'k da Huzaifa ba domin su da suke cinta kullum bata ta'ba samun satisfaction irin na yau ba, da d'an yatsa Hafeez ya gamsar da ita gamsuwa irin wacce bata ta'bayi ba, Dan haka itama sai ta shiga yi masa nata salon wanda ya sanyashi kusan mutuwa, sai kusan uku da rabi na dare suka saurara da shaid'ancinsu, Hafeez yayi niyar tafiya a wannan daran ta hanashi tace ya bari ayi sallah......aikuwa ana shiga massalaci ya fito daga gidan, wanda yay dai-dai da shigowar Isha'ik da mota.....Sai ya tsaya har Isha'ik din yayi parking ya fito, kwata kwata babu alamun mamaki a tare da Isha'ik shi dadi ma yaji da yaga Hafeez din a gidansa, cafkewa sukayi sukai gaisuwa irin tasu Isha'k yace."Guy Ashe nan kayo ni dama jiya nagane inda ka dosa ka saba zuwa gurin Safna duk dare shiyasa jiya nayi maka hakan nasan ba zakayi iya hakuri ba tilas ka nemawa kanka Mafita." Hafeez yay dan murmushi yana kallonshi yace."Eh man ai kaima ka sani gashinan Ai ta ri'ke wuta sai yanzu ta barni na fito. Isha'k yasa dariya ya bashi hannu suka tafa yace."Guy Fadila nada sirri sosai kai dai kawai ka saki jikinka kaji dad'in duniya." Hafeez yace."Wannan shine magana." Tafawa suka sakeyi suna dariya, Hafeez yace."Zan wuce gida yanzu kasan halin Daddy fad'a ne zan sha idan na koma." Isha'k yace."Hooo! Daddy kace har yanzu yana nan dai da halinsa." Hafeez na ta'be bakinsa ya nufi motarsa yana fad'in "Daddy ne fa me zai fasa." Isha'k yace."Okey mybe anjima zan shigo idan ban shigo ba sai mu had'u a Club da daddare." Yace."Okey shikeenan." Motarsa ya shiga ya kunna Isha'k ya daga masa hannu, maigadi ya bude masa gate ya futa daga gidan. maigadi naganin Isha'k ya shiga gidansa sai ya nemi guri ya zauna yana mamaki da al'ajabin al'amarin ya dauka idan Isha'k din ya dawo yaga abokinsa a gidansa zai dauki mataki sai yaga akasin hakan, sai ma murna yake da farin ciki tabbas wannan al'amari dake faruwa akwai abun mamaki a cikinsa. Yana 'kokarin shiga da motarsa cikin gidan, Professor ya fito daga massalacin dake jikin gidansa, dan haka sai maigadi ya bar gate din a bude Professor ya shiga gidan ransa a 'bace! dan da kyar ma ya amsa gaisuwar da maigadin ke yi masa. Hafeez ya fito daga cikin motarsa cike da nishadi kawai sai sukayi ido hud'u da maifin nasa, gabansa ya yanke ya yafad'i! saurin sunkuyar da kansa 'kasa yayi Yace."Daddy barka da asubah." Ba tare da ya amsa ba yace." Hafeez sai yanzu ka shigo ko.''? Sai ya hau inda inda "Daddy Wall......Kafin ya 'karasa Professor ya daga masa hannu! " Bana bukatar jin komai daga bakinka." Yana fad'ar haka sai ya wuce ciki, Jikinsa babu kuzari yabi bayansa, bai ta'ba tsammanin zasuyi arangama da Daddyn nasa ba. Yana tsaye tsakiyar parlon hannunsa goye a bayansa kana ganinsa kasan yana cikin tsananin 'bacin rai! Hafeez din na shigow ya rufeshi da ruwan bala'i! cak! ya tsaya bakin 'kofar shigowa yana sunkuyar da kansa kamar wani mai gaskiya......"Dube ka Hafeez dubi sutturar dake jikinka wando iya cinya da matsiyaciyar rigar da take 'kokarin yagewa a jikinka, bana jin ma kayi sallah asubahi yanzu, shin wai me kake so ka zama ne ? ko ka kafurta ne bamu sani ba? duka wannan d'abi'un da kakeyi bana d'an musulmi bane, wato saboda na'ki nayi maka aure shine ka tsirarwa kanka yawon dare ko? ni kake so ka tozarta a idon duniya kana so ka watsa mun kasa a ido ko Hafeez kana so na futa zakka a cikin abokaina idan an hangoni a dinga nuna ni ga uban gafalalle nan! To bari kaji wallahi tallahi sai na dauki tsatsauran mataki a kanka mutukar baka sauya halayarka ba."!!!! Hafeez da tunda Professor ya fara bala'in bai d'ago kansa ba sai bayan da ya gama sannan ya d'ago kansa duk ya muzanta, kawai sai ya ga gabad'aya su Mommy Farhana da Asiya sun zuba masa ido, idan ba idonsa ke masa gizo ba sai yaga kamar Mommynsa ma hawaye take sharewa, hankali a tashe ya nufi inda take......Hannu ta d'aga masa alamu kada ya karaso ta nemi guri ta zauna tana matse hawaye.....murya a sha'ke! Yace."Mommy dan girman Allah ki daina mun kuka kina so na lalace ko."! A tsawace! Professor yace."Lalacewa wace iri kake magana yanzu? wallahi ka sake ka sanya mata hawan jini ko ciwon zuciya sai nayi sharia da kai dan ni tafi min kai sau dubu kaje kana sharholiyarka ita nan ka barta da rashin bacci wallahi ka kiyayi hakkinta dake kanka. Hafeez yace."Wai Daddy me yasa kake kausasa! kalamanka akaina ne? nifa idan kana mun haka sai naga kamar da wani abun a 'kasa, kuma ni ba abunda kake zargi naje nayi ba, Daddy gabad'aya baka yarda da gask.......Kafin ya 'karasa Professor ya wanke shi da mari mai zafi!! Yana tsuma! yace"Dan ubanka me kake nufi da wannan maganar.'? Mommy tasa kuka tace"Yallabai ka rabu dashi ni wallahi lamarin yaron nan ya soma bani tsoro wannan maganar da yake yi irin ta mashaya ce mybe yasha wani abune ka kyaleshi kawai Allah ya shiryeshi." Professor yaja tsaki ya haye sama yana cigaba da zazzaga masifa had'e da zagin Hafeez din tare da ai bata shi, Hafeez ya dago kansa idonsa yayi wani irin jaaa!! Farhana sai kuka take sosai yayin da Asiya ke masa wani irin kallo tayi kur!! da idanunta a kansa, Ransa yayi bala'in 'baci! cikin tsawa! yace."Dan ubanki me kike kallo a jikina? idan baki dauke wannan shegun idanun naki ba sai na karya ki."!!! Asiya tayi saurin dauke kanta taje ta zauna kusa da Da Mommy jikinta duk yayi sanyi lallai Hafeez ta'kadiri ne iyayansa na masa fad'a yana mayar musu da magana gaskiya abun ya bata mamaki!!! Mommy tace"Ka daina wani huci!! wallahi ka sake ka daki yarinyar nan to za kaga 'bacin rai na, yawon dare kuma kaje kayi tayi kada ka daina." Sosai maganarta ta bashi mamaki wato yarinyar har ta samu matsayi me girma a gurin Mommy irin haka?? Jinjina kansa yayi ya nufe inda take zaune gwiwa biyu ya durkusa ya riko hannayeta ya wani koma kalar tausayi yace."Mommy zubar hawayenki babban bala'i da masifa ne a gareni Mommy me yayi zafi!! har da zaki dinga kuka! me nayi wanda zai daga miki hankali kawai saboda ban kwana a gida ba shikkenan duk sai ku tashi hankalinku? Ni fa ba yaro bane Mommy yaci ace kun bani 'yanci na, dan naje Club nayi rayuwa da abokaina ba laifi bane Mommy bana neman mata kuma bana shan abun da zai bugar dani! naji kina maganar ko bana cikin hayyacina wallahi Mommy ban sha komai ba, kuma in dai zuwa Club ne ke saki 'bacin rai da kuka to na daina, amma ki cewa Daddy ya daina zagina yana aibata ni wallahi wannan masifar tashi bata bani tsoro da zan koma yanda yake so da tuni na koma, kuma ina masa ladabi da biyyaya dai-dai gwargwado me kuma yake so nayi masa sai zagina yake gaban yara harda wata bare, Gaskiya Mommy hakuri na ya soma 'karewa da abunda da Daddy yake mun." Asiya sakin bakinta tayi tana kallon ikon Allah ta'b! da itace take wannan rashin kunyar tasan Gaje kasheta ne kawai ba zatayi ba, gaskiya tana mugun mamakin rashin tarbiyarsa da yanda yake magana da Iyayensa kamar wasu sa'aninsa....Ganin ya dago kansa ne ya sanya tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa! Mommy tace"Hafeez duk wani abu da Daddynku ke maka wallahi kaine ka jawo kasan halinsa mutum ne me zafi me yasa ba zaka dinga kiyaye fushinsa ba, jiya fa cewa kayi zakaje dauko Isha'ik daga airport shikkenan kuma sai mukaji ka shuru, nan parlo na kwana zaman jiranka ko kadan ban rintsa ba fargaba da damuwa duk sun dame ni! Hafeez jikina na bani kana aikata mummunar d'abiar nan, tun daga sanda ka kwanta ciwo Daddynku ya tabbatar mun da abunda ke damunka, kuma tun daga wannan lokacin naga ka daina maganar auren da kakeyi jikina na bani cewar kana samun satisfaction ta wani 'ban........Kafin ta 'karasa maganar ya katseta ta hanyar bugawa su Farhana tsawa! jikinsa na kyarma Yace."Ke! Farhana ja wannan 'yar iskar mai shegen kallon tsiya ku bar nan ko yanzu naci ubanki."!! Farhana ta mi'ke da sauri! dan gaskiya tana jin tsoron 'bacin ran Hafeez din shima haka yake masifaffe dan ta wani gefan ya dauko halin Daddynsu, amma dai Professor ya fishi masifa.......Yana wani irin gumi! Yace."Mommy kina irin wannan maganar gaban yara me kikeso su dauke ni! ? billahil-azim Mommy ni ba fasi'ki bane!! Mommy meye riba ta idan na aikata fasi'kanci nasan fa sai anyi da matata ko 'yata kamar yanda Annabi ya fad'a! Mommy ki daina mun wannan zargin dan Allah! tun da daddy ya hanani aure yanzu gabakid'aya ma naji auran ya fice mun a rai zan iya 'kare rayuwa ta a haka ba tare da mace ba." Ganin yanda yake rantsuwa da karyar da kai yasa jikinta yayi sanyi , dama ta fada masa hakane domin ta gano shin gaskiya ne abinda take zarginsa dashi ko kuwa? dan hausawa na cewa (Mara gaskiya ko ruwa gumi yake) sai taga shi duk ya nuna alamun gaskiya a maganarsa sai rantsuwa yake mata. Tace"myson naji dad'i sosai da baka fad'a wannan harkar ba, kuma naji kana cewa kai ba zakayi aure ba, baka isa ba aure kamar kayi ka gama mu jira lokaci dai, kamar yanda Daddynku yace sai ka cika shakara talatin zakayi aure ai kamar yau ne tunda saura shakara biyu dan haka sai ka fara neman matar aure." Yace."Mommy ni kawai ji nayi auran ma ya fita a kaina amma zanyi tunani kan hakan." Tace"Myson na yafe ka maka ubangiji Allah yayi maka albarka ya shirya min kai." Ya amsa da ameen." Yana rintse hannunta cikin nasa, tace"Ka hau sama ka bawa Daddynku hakuri kasan dai halinsa maganar har yanzu bata wuce ba a gurinsa, kaje ka bashi hakuri kace ba zaka sake ba." Ya d'an ya mutsa fuska yace."Mommy ni wallahi bana son zuwa gurinsa nasan har yanzu bai huce ba gwara idan ya sakko ma had'u gurin breakfast sai na bashi hakuri! Tace."A'a nafi so dai kaje yanzu duk wani abu da zaiyi maka ka jure ka ta'boshi ne." Ya mi'ke tare da fad'in"Shikkenan Mommy inama daddy me saurin fahimta ne irinki da naji dadi wallahi." Mommy tayi murmushi tana binsa da kallo yana hawa steps da nufi zuwa gurin Daddyn nasa...... Kuyi sharing pls👏🏻 _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *PAID BOOK!* *Free Pege15* Koda ya shiga dakin Professor na zaune kan sofa 'kafarsa d'aya kan d'aya yana girgizata fuskar nan tasa a mugun had'e! yana ganin Hafeez din ya shigo dakin ya daga masa hannu!! "Futa ka bani wuri."! Yafada da kaushashshiyar murya! Hafeez 'kin futa yayi, kai a kasa ya isa inda yake zaune, tsugunawa yayi gabansa ya ri'ke 'kafarsa a hankali yace." Daddy kayi hakuri dan Allah." Shuru yayi masa bai tanka masa ba, Hafeez ya cigaba da karyar da kai yana fad'in."Insha Allah haka ba zata sake faruwa ba Daddy jiyan ma akasi a kasamu amma ba zan sake ba."Professor ya sauke ajiyar zuciya zuciyarsa tayi masa sanyi kadan don ganin yanda Hafeez din ya nuna nadamarsa yana bashi hakuri da rantsuwar ba zai sake ba, Yace."Hafeez kana so ka kunyata ni cikin abokaina ko."? Ya girgixa kansa, Prof yace."Duk cikin 'yayan abokaina waye ka gani da irin wannan halayen naka." ? Yace."Babu Daddy." Yafadi hakane dik don ya kwantarwa da daddyn hankali amma mafi akasari ma da 'yayan abokan nashi suke sharholiyarsu ba zai gane bane......Ya cigaba da cewa "Daddy ka daina zagina addua zakayi min kuma insha Allah ba zanyi lalacewar da kake gudu ba, amma ina jin ciwon zagin da kake mun Daddy ka rufe idonka kamar ba jininka ba."!! Prof ya sauke ajiyar zuciya yana kallonsa yace." Me yasa kasan halina baka kiyaye 'bacin raina.''? Yace."Daddy duk dan adam ajizi ne nima ban san zan kwana a waje ba wallahi." Yace."Ban hanaka shiga cikin abokan ka ba amma ka dinga kiyaye da wanda zaka dinga mu'amula, wannan abun da ya faru yasa na soma zarginka kan wasu abubuwa da kayi mun guda biyu, a iya sanin da nayi maka nasan *Sigari* kawai kake sha, to amma wata magana da kayi mun tasa na soma zargin ko ka fara shan giya da sauran kayan maye shin hakane ko ba hakaba."Yakarasa maganar yana kallonsa cike da tuhuma!! Sunkuyar da kansa yayi 'kasa yana shirya kalaman da zai kwaci kansa, Eh tabban yana shan Sigari dan le'banshi ma mutum ya kalla zai gane amma kuma baya shan kayan maye kamar yanda iyayen nasa suke zargi, Ya dago kansa a nutse yace."Daddy ina shan sigari kaima ka sani amma wallahi bana shan giya da yawancin abubuwan da kake zargina dasu itama sigarin kullum addua nake Allah ya yaye mun." Prof Yace." Yanzu dai gashi kana ta rantsuwa da Allah ka daina ba zaka sake ba ba za'ayi sati biyu cikakke ba zaka manta da rantsuwar da kayi ka cigaba da abinda kake." Yace."Haba daddy ka dinga kyautata zatonka a kaina mana." Prof yaja tsaki yace."Hafeez Kaine fa ka iya ladabin karya da rantsuwa ni tuntuni na dawo daga rakiyarka." Murmushi yayi ya rike hannunsa yace."Daddy zakayi mamakin abinda zan zama nan gaba kadan kaida ka cigaba da yi mun addua kasan duk abinda nake yi akwai kuruciya a tare dani tunda kace ni d'in yaro ne har yanzu ban mallaki hankalinka kaina ba." Prof ya kai masa rankwashi aka yana dariya yace."Kana so ka fada mun magana kenan."? Hafeez ya dinga kyalkyala dariya yace."No daddy tuna maka nayi kaga ko yanzu nasa ka dariya." Girgiza kai ya shiga yi yace."Allah yayi maka albarka yasa ka zama kintsantsan mutum kamar yanda nake bukata." Hafeez ya sauke ajiyar zuciya ya rungumeshi sosai yana fad'in"Ameen Daddyna Allah ya kara maka hakurin jure hali na." Tare suka sauka 'kasa, Hafeez ya hau benansa domin yin wanka dan ma Allah yasa ya tsarkake jikinsa gidan Isha'ik yayi sallah asubahi bai da nauyin komai a kansa. ***** Emanuel da maigadin guest house din ne suka cicci'bo BabaTinde suka saka shi a mota suka kaishi asibiti mafi kusa dasu, dan yanda suka ga jikin nasa yayi masifar daga musu hankali, yanda yake rirrike joystick dinsa yana ihu! shine ya tabbatar musu da cewar yarinyar da ya dauko ce tayi masa babbar illah! gashi ta gudu! ta barshi cikin tsananin azabah da wahala! Cikin gaggawa Dr ya zurkud'a masa allurar bacci dan ana shiga dashi asibitin ya cika musu kunne da ihu! da katuwar muryarsa kamar ana buga ganga........Wani magani Dr din ya dauko ya cire daga kwalinsa maganin kamar cream yake, ya shiga shafawa Tinde kan mazakutarsa da ta wani lankwashe ta lan'kwame kamar ba itace ke 'kokarin tsokanewa Asiya ido ba, shi kansa Dr yayi mamakin yanda mazakutar Baba Tinde ta koma sai kace lagwanin risho! lallai babu shakka yana cikin gagari dan kallo guda yayi mata ya gane da kyar in zaka sake aiki. **** "Haba Asiya yaci ace kin daina wannan kukan da kikeyi bashi da amfani kwata kwata, daga tambayarki wane gari kike sai ki fashe da kuka kin kasa yi mana gamshshan bayanin da zai sanya mu san ke wacece sannan kuma mu had'aki da danginki." Mommy ce ke wannan maganar lokacin da suke zaune a palo bayan sun gama breakfast ......Asiya taja majina tana shashsheka tace"Hajiya ni na manta sunan garinmu wallahi kuma idan na koma kasheni zasuyi."? Cike da mamaki Mommy da Farhana suke kallonta. Mommy tace"Kashe ki zasuyi kamar yaya? Asiya ina so ki bani ta'kaitaccen labarin ki." Asiya kuka ya kufce mata tace"Ni marainiya ce tunda na taso ban san mahaifiyata ba sai matar babana Gaje, itace uwar ri'kona, Tana bani wahala sosai duka zagi ba irin wanda ba tayi mun, katsam! babana ya bada aurena ga wani tsohon mutum a kauyenmu wanda kowa yasan halinsa mugune kuma auri saki yake yi, amma haka babana ya daukeni ya kaini gidansa, a daran ranar babban d'ansa ya shigo dakina zaiyi mun fyad'e! shine na.......Kasa k'arasawa tayi kuka ya kufce mata! Mommy tace''Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! to ina mijin naki ya shiga har d'ansa ya samu damar shiga dakinki." Asiya ta shar'be majina tace"Ya fita bayan yayi mun dukan mutuwa kawai saboda na'ki amincewa dashi, to wannan damar d'ansa ya samu ya shigo dakin, wanda da kyar na kwaci kaina daga hannunsa, na fito daga gidan, ban nufi gidanmu ba saboda nasan idan naje sai Gaje ta dake ni kawai sai na dinga gudu har na fito wani titi da ban san na ina bane! nan cikin wata tasha na had'u da wata 'kabila ba musulma bace, tace zata taimaka mun amma sai nabi umarninta nace na amince dan a lokacin wanda zai taimakeni nake nema! kwana biyu da nayi a hannunta nagane ba mutuniyar kirki bace, ta dinga bani wasu kaya masu futar da tsaraici ina sakawa sannan kuma ta hanani yin addinina bana sallah sai na fakaici ta fita gurin sana'arta sannan...akwai ranar da muka dawo daga gurin gyaran gashi wani 'Kabilan mutum irinta ya tare mu nan ya nuna mata yana sona tun daga irin kallon da yake mun na gane mutumin banza ne, washe gari yazo ya daukeni ya bata ma'kudan kudi, can wani gida ya kaini yana so ya lalatani ni kuma Allah ya bani sa'a a kansa na.........Kasa 'karasawa tayi ta sunkuyar da kanta tana wani irin kuka mai tsuma zuciya!! Prof da Hafeez dik sun sauko daga sama kuma a kunnansu Asiya ta 'karasa labarinta, Mommy tace"Kai amma gaskiya wasu mutanan basu da imani wallahi! Yanzu kamar wannan yarinyar me ta sani a rayuwa da za'ayi mata aure, Farhana ma ina tunanin ta girmeta dan dai kawai tana da girman jikine! amma gaskiya labarin nan naki ya sosa mun rai wallahi na tsani auran da mutanan 'kauye sukewa yaransu da 'karancin shekaru." Prof ya sauke ajiyar zuciya yace."Daina kuka Asiyatu kinji ko ni zan zame miki uwa da uba kuma insha Allah duk ranar da kika tuna garinku da kaina zan kaiki gurin mahaifinki sannan nasa shi ya warware auran da yayi miki tunda bakya so, nagode Allah ma da yasa baki aikatawa mijin naki wani mummunan aikin ba, dan duk irin hakane ke janyowa kaji ance yarinya ta fada rijiya ko kuma ta kashe mijinta da makami Allah ya kyauta.".......Asiya tace"Dan Allah kada kuce zaku mayar dani gidanmu wallahi Gaje kasheni za tayi." Mommy tace."Kwantar da hankali ba zamu mai dake ba." Farhana ta dan riketa a jikinta tana bata baki......Hafeez kam ta'be bakinsa yay ya wuce daining yana fad'in "Allah ya kyauta." Da 'kyar Mommy ta rarrasheta tayi shuru tana Fad'in "Tunda bakya son komawa garinku zamu kyaleki ki zauna tare damu tsayin lokacin da zaki dawo nutsuwarki nasan lokacin zakiyi tunanin komawa gaban iyayenki ki daina kuka kina tayar mana da hankali kinji ko mu zamu ri'ke ki tsakani da Allah ki kwantar da hankalinki Allah kuma ya sanya iyaye masu irin wannan halin su gane su daina yiwa 'yayansu auran dole." Farhana ta amsa da "ameen Mommy." Professor da Hafeez tare suka fita Ofis Hafeez sai wani ladabi yake masa kamar mutumin kirki shi kuma Professor din sai murna yake da fatan Allah yasa adduarsa ce ta soma tasiri a kansa. Sati biyu da faruwar al'amarin Hafeez ya d'aukewa Safna wuta ko kiransa tayi a waya baya dagawa, Safna duk hankalinta ya tashi Hafeez ya saba mata da salon soyayyarsa mai wahalar samu, shi kuwa nasa 'bangaran so yake ya yakice al'amarin daga rayuwarsa ya san mugun zunubi yake kwasarwa kansa duk da baya za'kewa kan abun da yake yi din amma yasan yin zina da matar aure ba karamin haramun bane ga uban Zunubi shiyasa ya gwammace yayi da Titi ita da bata da nauyin kowa a kanta amma wannan aika-akair da yake yi yana jin tsoron ranar da asirinsa zai tuno gurin Daddy yasan me rabasu sai Allah shiyasa kawai yake so yayi wa kansa fad'a......To bama Safna kad'ai ba ita kanta Fadila ta bud'e wuta sosai dan tunda ya d'and'ana mata zumarsa a bakinta ta kasa hakuri kullum cikin kiran wayarsa take da turo masa pictures dinta tsirara, duk dan taja hankalinsa zuwa a gareta, sai dai kawai ya kalli pictures din yayi dariya idan kuma ta tsokano shi sai ya kira Titi a waya, a ofis din zasuyi su gama ba tare da wani ya sani ba.......Sannan kuma ya d'an rage zuwa gidan Huzaifa yin lunching dan duk ranar da yaje gidan sai Safna ta kusa sashi a masifa, da muguwar sha'awa yake dawowa gida gashi ya riga yayi wa iyayensa al'kawari kan cewar ya daina fitar dare, duk inda goma tayi yana gida tare da iyayensa......Zuwa wannan lokacin Asiya ta zama yar gida ta saba sosai dasu, tana sakin jikinta mutukar Hafeez baya gidan, idan kuwa ya dawo komai a sanyaye takeyi bata so ta kalleshi saboda irin kallon wulakacin da yake mata, yau tsayin sati biyu da zuwanta gidan, magana ba ta sake had'asu ba, sai kallo da ido idan ta gaisheshi in ya ga dama ya amsa idan kuma 'yan wulakancin na kusa yayi mata banza, hakuri take yi kawai ga wata masifa dake damunta, haka kawai take jin wani mugun sonsa a cikin zuciyarta duk sanda ta ganshi ko taji muryarsa sai gabanta yayi wani irin fad'uwa, innalilihi kawai take ambata ta samu sa'ida, shi kam watarana ma mantawa yake da ita idan ba sakkowa yayi ya ganta ba........Farhana bata zama a gida sosai saboda jarrabawar da sukeyi, duk ranar da take gida haka suke zaman karatu ita da Asiya, sosai take da 'kwa'kwalwa dan har Mommy wani sa'in tana mamakin kafin basirarta yarinyar da bata ta'ba shiga aji ba amma cikin sati biyu kacal ta iya rubuta sunanta ta kuma iya hausa sosai ta rubuta ta karanta, sai dai rubutun nata sai mai fahinta ne zai gane, amma dai duk da haka mutanan gidan sun yaba da basirarta banda mutum daya wato Hafeez! watarana idan ya sakko yaga suna ta karatun tsaki yake ja yace."Ke Farhana wahalar da kanki kike a banza yarinyar nan sam bata ganewa, sai kawai ya lailayo wata kalmar mai mugun wuya da turanci cikin tsawa zaice ke! me wannan kalmar take nufi.'? Asiya tayi shuru tana diri-diri sam bata gane komai ba dan bata zo gurin ba, Sai yaja tsaki ya bar gurin yana fad'in " 'Ba'kauyiya kawai wai ance da ita Ya sunan shugaban 'kasa ta kasa fad'a." Mommy tace"To ai komai sai a hankali ba kaga hausa kawai ta iya ba, ai ma tayi kokari wallahi. Dariya kawai yake yi ya wuce ya bar gurin yana fad'in"Mommy ke kike ganin kafin basirarta ni ban ganta ba." Sai bayan ya fita ne Mommy zata bata hakuri dan ta lura dik sanda yayi mata irin wannan iskancin ranta na 'baci! dan wataran ma har hawaye take sharewa............. ***** "Asalamu alaikum." Taburni ce tayi sallama gidan maishanu kanta dauke da 'kullin kaya.....Gaje dake zaune kan kujera 'yar tsuguno ta rafka uban tagumi ta amsa da "Wa'alaikisalam.'' Taburni ta karaso cikin gidan tana fad'in." Ke kuwa Gaje me ya dame ki kika zabga irin wannan tagumi haka."!? Gaje ta sauke ajiyar zuciya tace"Taburni zauna kedai abokin kuka shi ake gayawa mutuwa." Taburni ta nemi guri ta zauna tana sauke kayan dake kulle a kanta. Gaje tace"Taburni masifar cikin garin ta isheni wallahi, tun ranar da Asiya tasa 'kafa ta bar garin nan na rasa kwanciyar hankali babu dama na futa sai jama'ar gari su hau zagina har da masu jifa da fad'in" Wai na cuce Marainiya hakkinta sai ya kamani tunda ta gudu yanzu ba'asan inda take ba, wallahi haka zakiga yara na bina suna jifana hade da rera mun wa'ka kwata-kwata zaman fadar maigari ta gagari mashaniya kullum yana gida ya zabga tagumi duk mun rasa meke mana dad'i, ga uwa uban babban a kunyar da Asiya ta aikata kan Alaji Bawa da d'ansa Dalladi duk jama'ar gari sun san saboda wannan abun da tayi masa ne ya zama kwar!kwar yau da lafiya gobe babu, Dalladi da sauran 'yayansa sun dauki al'kawarin kan idonsu idon Asiya sai sun ga bayanta tunda tayi sanadiyar da mahaifinsu ya zama mahaukaci, kinji halin da muke ciki Taburni Dalladi jiya yazo gidanan yace."Daga nan zuwa Sati d'aya idan bamu nemo inda Asiya take ba to kuwa sai sun cinna mana wuta a gida, kinga kuwa dole hankalina ya tashi, gashi duk sun kame shaniyoyinmu sun dauresu, yanzu haka abinda zamuci babu a gidan Taburni tace"Kai! wannan yarinya bata kyauta ba wallahi! Ja'ira mara mutunci ni da ina tausayinta ashe shegiyar kanta ce, tunda har tasan ta murd'ewa namiji ma'karkafa! ai dole mutum yayi takatsantsan da ita dan ke da kike mace ma zata iya yi miki lahani ta wata sigar ta daban!!! Watakila yanzu ai ta zama 'yar gari dan ga irinsu nan muna gani a birni idan munje dauko kaya haka zaki dinga ganinsu suna yawo kan titi da sunan karuwanci! ai wannan yarinyar ta cuci kanta wallahi da wannan rayuwa data za'bawa kanta ai gwara zamanta gidan Alaji Bawa yafi mata alkairi da ta shiga burni tayi sana'ar iskanci." Gaje tace"Humm! ai 'yar na gada ce dole tayi tunda itama uwarta ai sai da tagama yawon iskancinta na siyar da nono da manshanu a kasuwanni sannan shi maishanun ya kwaso ya kawo gidansa, kinga duk abinda Asiya zatayi yanzu sai muce uwarta ta gado." Taburni tace"To yanzu ke wace shawara kika yankewa kanki."? Gaje tace"Nace da maishanu mu shirya muje can Falgore garin su ita Mariyar mu duba mu gani ko can Asiyan ta nufa, yace shi ba zai iya gane cikin 'kauyen ba dan zuwansa biyu kauyen ko daurin auransa da Mariyar anan garin akayi, su kuma dangin nata hegu tsinnanu tun bayan mutuwar Mariyar basu sake zuwa duba Asiyan ba har yau d'in nan da nake miki magana akai.Taburni tace"Babu shakka Gaje kuna cikin matsala dake da maishanu ina jajanta muku Allah yaye muku wannan ibtila'in, kinga ni Burni zan tafi dama kin san duk karshen wata nake zuwa, to rashin kudin mota yasa na kwana biyu banje ba idan naje zan shiga kasuwar rimi na samo tsummokara masu kyau! ke zan fara kawowa ki za'ba dan wannan karon har Gidan da yayata Ladidi take aikin aikatau zanje ko Allah yasa na samo abun arziki a gidan." Gaje tace"Taburni wannan masifa tasa naji sha'awar binki burni wallahi don ina fargabar ranar dasu Dalladi zasu zo su 'kona mana gida, idan mun rasa mufuta dole mu tattara namu namu mu gudu daga garin." Taburni ta mike tana fad'in "Ba za'ayi haka ba Gaje yanzu kafin na tafi tasha bari naje gidan Alaji Bawa gurun Hajara mahaifiyar Dalladi in rarrasheta ta bashi hakuri insha Allah komai zai zo da sauki." Gaje ta mike da sauri tana fad'in "Yawwa 'kawar rufin asiri bari na dauko mayafina muje tare dan dama tuntuni nake so naje gidan tsoro ya hanani." Daki ta shiga ta dauko mayafi ta yafa suka dauki hanyar gidan Alaji Bawa mai kalwa. Pls kuyi sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ ```Barkan mu da juma'a My fans Kada ku manta da salatin Annabi da karanta abinda ya sawwa'ka daga cikin suratul khafi.``` *DEDICATED TO:* *My doghter* *ZAINAB KHABIR ISHA'K* (Ina miki fatan alkairi har'karshen rayuwarki nagode 'kwarai da alkairin ki a gareni) *Free Pege16* Tun daga soron gidan suka soma jiyo hayaniyar Alaji Bawa, ya dage sai d'ure-d'uren ashar yake yi yana d'aga muryarsa, Gaje tace''Taburni anya kuwa zan iya shiga gidan nan da alama haukan ne ya motsawa maigidan kada na shiga na fito da rauni." Taburni tace" Ki dai daure mu shiga tare babu abinda zai faru." shahada sukayi suka kutsa kansu cikin gidan suna rafka sallama. Alaji Bawa na zaune kan wata kujera ya d'ora 'kafa d'aya kan 'daya sai zazzagawa Hajara masifa yake yi yana fad'in ta tattara nata ya nata ya saketa ta bar masa gidansa, yayin da ita kuma take cewa babu inda zataje zama daram kamar kujera take a gidan dole a zauna da ita. Yace."Aure zanyi kuma a dakinki nake so na jiye amaryata, saboda haka wallahi ko kinfi 'koda naci sai kin bar mun gida." Hajara tasa dariya tana tafa hannuwa tace"Lallai Alaji wato baka daddara ba kenan zaka sake jajibowa kanka wata wahalar ko." Yace."Hajara na fad'a muku fa baku isa ku hanani na more kuruciyata ba da kudina da komai sai na auri yarinya shakaf wacce tafi 'yar iskar yarinyar nan da taso ta sabautani, to da ita da ku duk bukatarku ba zata biya lafiyata lau sumul garau! idan an ajiye mun mata dubu sai na gama dasu! dan yanda nake jin karfi da kuzari a jikina wane dan shekara goma sha bakwai!! Hahahahaha! Kan ubancan! Yarinyar nan Asiya taso ta kassara mun rayuwata billahil-azim duk sanda ta dawo garin nan sai na kashetaaa."!!! Ya'karasa maganar yana buga hannun kujerar da yake zaune. Gaje da Taburni tsoro ya kamasu dan su duk abunda ake fad'a dangane da haukan Alaji Bawa basu dauka shiriricewar ta kai haka ba, daga shi sai gajeran wando a gidan kuma gaban yaransa yake wannan kwakyariyar!!! Sukayi sallama suna sunkuyar da kansu kasa, mussaman Hajara da bata so ya shaida ta sai sunkuyar da kai takeyi tana so tayi wuf! ta fad'a rumfar su Hajara.....Yace."Ku ku dakata anan su waye ku da zaku shigo mun gida babu notice." Taburni tace."Mune Alaji munzo duba jikinka ne."? Yace."Dan ubanku! waye ya fad'a muku bani da lafiya? ni lafiyata lau na fahimci jama'ar garin nan sun mai dani shashasha! ko wacce munafuka sai ta lullu'bo mayafi tace tazo dubani, to nagaji yanzu zan nuna muku ni lafiyayye ne."! Sai kawai ya mi'ke tsaye da sauri yayi kansu yana 'kokarin cire gajeran wandonsa, A guje!! Su Gaje suka fad'a rumfar suna fad'in "Subahanallahi."!! Lanto da Hajara suka fito daga d'akunansu suna salati, lokacin Alaji Bawa ya shigo rumfar da sa'bulallan wando wanda ya tsaya iya gwiwarsa. Allah sarki jijiyarsa ta wani lanjare sai jale jale takeyi, Fad'i yake" Dan ubaku!! ku kalla ku gani! da kyau! ni lafiyayye ne lafiyata lau."!!! Gaje da Taburni suka soma neman hanyar tserewa suna salati da sallalami, yayin da Hajara da Lanto sukayi kan mijin nasu suna so su mayar masa da wandonsa yana buge hannunsu, kai tsaye Inda Gaje take yake kokarin nufa. Gaje ta tsorata sosai da sosai, da gudu ta tunkud'e Taburni tayi waje a guje!!! ko takalminta bata dauka ba, sai da tayi nisa sosai ta samu ta zauna tana hutawa can ta hango Taburni ta yanko a guje!! hannunta ri'ke da 'kullin kayanta da ya soma kwancewa.........Tana zuwa ta zube a gurin tana nishi!!!! Gaje tace"Wannan wace irin masifa ce Taburni da gaske dai Alaji Bawa ya haukace."!! Taburni tace"Ga zahiri kin gani Gaje, wannan haukan na Alaji Bawa me lasisi ne wallahi da ya samu nasarar kama wata daga cikinmu to da ban san abinda zai faru ba." Gaje tayi sauri ta kalli hanya tace"Tashi mu tafi dama tunda muka doso layin jikina ke bani wani abun zai faru." Taburni ta gyara d'aurin kayanta ta d'ora a kanta suka d'auki hanya fakam!fakam! sunayi suna waiwayen bayansu da tunanin abunda ya faru. ***** Yau ta kasance Lahadi ranar huta ce ga Professor ga iyalinsa, ranar hutu ce kuma ga ma'aikatansa, yana zaune a palo cikin kayan shan iska idanunsa sakaye da farin gilashi hannunsa rike da jarida yana dubawa yana d'an duban inda su Farhana da Asiya ke zaune suna karatu, Mommy ta sauko daga sama cikin kwalliya tana sanye da jar atamfa java wacce akayi mata dinki zamani ya fito da kuruciyarta, Mommy macace mai tsafta da gayu shiyasa kullum Mijinta ke kara kaunarta, Ta zauna kusa dashi tana fad'in "Yallabai barka da hutawa." Ya kalleta a nutse yace."Barka dai dama so nake ki sakko muyi wata magana." Tace."To gani na sakko ina jinka." Professor ya aje jaridar hannunsa ya mai da hankalinsa kanta a nutse yace."Shawara na yanke kan yarinyar nan Asiyatu, ina ganin zan nema mata makaranta ta soma zuwa, muga abinda Allah zaiyi nan gaba yarinyar na bani tausayi kwarai kuma na amince sosai da abinda tafad'a shine dalilin da ya sanya ni naji ina sha'awar tsayawa kan lamuranta. Mommy tayi ajiyar zuciya tana kallon mijin nata tace"Wallahi kamar ka shiga zuciyata Yallabai sakkowar nan da nayi dama da maganar a bakina sai gashi ka rigani furtawa, Yarinyar nada brain ('kwa'kwalwa) tana burgeni sosai wallahi daga zarar Farhana ta d'ora mata karatu zata dauke a kanta, yanzu ina mai tabbatar maka da cewar koda secondary aka ajiyeta ba zata sha wahala ba sosai." Prof yace."Nima ina hankalce da abinda sukeyi kwarai naji dadi sosai da Farhana ke bata kulawa kema Allah ya saka miki da alkairi domin kin cancanci yabo da godiya, Insha Allahu da kaina zan kaita makarantar *Kuntau* za'ayi mata interview zamu gane wani level ya kamata a ajiyeta." Mommy tace"To alhamdullhi Na tabbata ba zata bamu kunya ba.'' Professor ya kalli parlon da suke karatun yace."Farhana ku zo nan keda Asiyatu." Duka suka mike sukaje suka zauna kasan kafet......Yace."Farhana Allah yayi miki albarka, abinda ya dace 'Dan uwanki yayi ke kina yin sa ina alfahari dake my dota." Tana murmushi tace."Nagode Daddy." Ya dan shafa kanta yace."Allah yayi miki albarka." Mommy ta amsa da ameen." Asiya ya kalla dake zaune kanta a kasa yace."Asiyatu zan kaiki makaranta kina so." ? Da sauri ta kalleshi fuskarta ta cika da farin ciki da annusuwa tace."Eh ina so Daddy." Yace."Kinyi min al'kawari idan kika kammala makaranta zaki fad'a mun ina ne garinku."? Kanta ta d'aga gabanta na fad'uwa, kwata kwata ta tsani a dinga tuna mata da garinsu, ko sha'awar komawa bata yi. Prof ya cigaba da cewa. Naga kina da saurin fahintar karatu insha Allah zan kaiki makarantar da 'kwa'kwalwarki zata sake bud'ewa sosai fanni biyu zaki zauna boko da arabic ina so ki iya karatun al'kur'ani da sauran littafai! dik da naga Farhana na koya miki nasan idan kin shiga makarantar ba zaki sha wahala sosai ba." Taji wani irin farin ciki tace"Nagode Daddy Allah ubangiji ya saka maka da alkairi, babu shakka kamar yanda kafada cewar zaka zama uwa da ubana hakane Daddy gashi kana yi mun abunda iyayewa kewa 'yayansu bani da abinda zance sai dai nace Allah yaja da rai yasa a gama lafiya." Professor da Mommy da ita Farhana sunji dadi sosai da adduar da Asiya tayi, Yace."Kada ki damu kinji ko, idan kin dawo daga makaranta duk abunda ya shige miki duhu ki tambayi Farhana ko Mommynku idan ina gida irin wannan rana ki tambayeni insha Allah mai tambaya yana saurin gane abu. Tace"To shikkenan Daddy nagode." Ladidi mai aiki ce ta fito daga wata 'kofa me murfi biyu da alama kicin ne a nutse cikin ladabi ta karaso gurunsu, zubewa tayi gaban Prof tana gaisheshi ya amsa da kulawa yana kokarin mikewa ya bar gurin, Ladidi ta gaishe da Mommy a nutse tace"Nace yau me za'a girka ne a gidan naga Yallabai na gida." Mommy tace"Semo zaki tu'ka masa da miyar agusi mu kuma kiyi mana jollop na macaroni da dankali." Ladidi ta mi'ke a hanzarce tace"To Uwar d'akina insha Allah yanzu zan kammala komai." Kicin ta nufa da sauri.....Asiya ta dauke kanta daga kallon Ladidi tunani takeyi kamar tasan fuskarta amma kuma ta kasa tuna a ina ta santa. Cikin dreesing din da Professor yayi masifar tsana! ya sakko daga benansa yana duba rantsatstsan agogon hannunsa......Tunda ta hango saukowarsa gabanta ke wani irin fad'uwa! anya wannan musulmi ne kuwa? Yana sanye da rigar atamfa fara mai ratsin blue black da dogon wando na jins blue black!! Rigar 'karama ce ta d'an kamashi, tana da dogon hannu wanda akayi masa wani irin ado da links masu tsada da she'ki! wuyan rigar daga sama kad'an an d'an tsagashi, sai wata sar'ka dake rataye a wuyansa mai manyan duwatsu jajaye sai walwali sukeyi, kansa sanye da hula me malafa! fara 'kal!'kal! da ita, kafafunsa sanye da bakin takalmi helf cover sai shaning yake yi, cikin wata irin tafiya ya karaso inda suke, Kanta ta sunkuyar 'kasa gabanta na fad'uwa! Tana ji Farhana na gaisheshi yana amsawa, ta d'an saci kallonsa "Ina kwana." Ta furta muryarta na d'an rawa." A yatsine ya d'an kalleta ya kauda kansa tare da fad'in "Lafiya." Shuru tayi sam ba taji dad'in yanayin yanda ya amsa gaisuwarta ba, Mommy ta kalleshi tana d'an jinjina kai tace"Sai ina kuma? kai ranar hutun ma ba zaka zauna a gida ka huta ba, kayo wata kwalliya da ko kyau ba tayi maka ba wai kai nan kayi gayu mtssss." !! Ya d'an bata fuska yana fad'in "Haba Mommy ya kike hakane! wannan drassing din fa nawa na mussaman ne! ba kowa ne yake kyau! ba idan yayi irin wannan shigar, Mommy mu kam abun har ya zame mana jiki mutane so sukeyi muyi su kallemu suna daukar selpie damu saboda burgewa Mommy idan kinga irin 'yan matan da zanyi yau d'in nan sai kinyi mamaki wallahi." Farhana ta 'kunshe bakinta tana so tayi dariya ya kai mata rankwashi a fuska yana 'bata rai!! Hannu ta d'aga tace" Sorry *B-B* Mommy kam baki ta ta'be! tace"Kaine dai kake ganin kayi kyau myson amma ni banga ni ba suma 'yan matan da suke rububinka kyalkyala banza ke rud'arsu, dan haka ni maza ka tafi kada Daddynku ya sakko kasan abunda zai biyo baya mutukar ya ganka da wannan kayan tashin hankali ne ya dingi yi kenan." 'Dan zabura!! yayi dan har yana takewa Asiya hannunta da sauri ta janye hannunta tana d'an dubawa had'e da ya mutsa fuskarta, yasan sarai hannunta ya taka! ko kallonta baiyi ba ballanta ya bata hakuri ya cigaba da magana da Mommy, ."Mommy dama be futa."? Harararsa tayi tace"Dama yana fita irin wannan ranar ne."? Kansa ya dafe yace."Oh! my god! Hanyar futa ya nufa yana d'an d'aga 'kafafunsa yana ajiyesu da 'karfi! a 'kasa! irin dai tafiyar da nigogi keyi a gogon dake daure a hannunsa yake dubawa yana fad'in "Mommy sai na dawo." Tace."Allah ya tsare." amin." Yafada a takaice ya fice daga parlon, parking spece ya nufa, Bilya yayi maza yaje yana karkade masa motarsa sai da ya karasa gurin yace."Biliya yau ba da wannan motar zan fita ba." Sabuwar Motarsa sawa key ya shiga ya zauna Biliya yace."Allah ya tsare maigida." Hannu ya daga masa ya figi motar maigadi ya bude masa gate ya fice daga gidan.........Club ya nufa wanda ya kwana biyu bai le'ka ba, Yau suna bikin wani abokinsu me suna jonny cristan ne, dan haka suka shirya party sosai yau za'a raba dare ana cashewa za'ayi abunda ake so za'aji dad'in duniya iya son rai. Hafeez na isa Club gayu sukayi caaaa! a kanshi da wanda ya sani dama wanda bai sani ba kowa 'kokarinsa yayi hannu dashi ya kuma yi selpie dashi kamar dai yanda ya fad'awa Mommy haka d'in ne ya faru 'Yan mata zankad'a-zankad'a masu ji da kyau! da wayewa ke kawo masa farmaki! nan ya zauna tare dasu Huzaifa yana kallonsu suna ta shawagi a gabansa, cikin sutturun da dasu gwara babu, tuni hankalinsa ya tashi, ya dauki sigari da leghtar ya kunna ya soma busa haya'ki!!! Can ya hango wata bab had'addiya mai kayan mata gaba da baya a filin rawa tana wata irin rawa!!! Nonowanta sai tsalle sukeyi tana yi kuma tana fito dasu tana lasa da harshenta wanda ke manna da wani abu mai'kalli, cike da barikanci take rawar tana jawo duk namijin da yayi mata, kasa jurewa yayi sai kawai su Huzaifa suka ga ya mi'ke! ya nufi filin rawar! a take aka bashi guri ya dinga wata irin tafiya yana cigaba da fesar da haya'kin sigarin dake hannunsu, Yarinyar na hangoshi tayi wani d'an tsalle! tana kar'kada nono dama duk abinda takeyi saboda shi takeyi to bukatarta ta biya taja ra'ayinsa, Yana karasowa inda take ya jefer da guntuwar sigarin hannunsa, ya kamo 'kugunta ita kuma ta ri'ke wuyansa suka soma yin wata irin fitinanniyar rawa! Kafin kice kwabo kid'a a sauya gayu sai ihu suke gurin ya karad'e da hayaniya, 'Yan matan dake gurin kuwa sun cika da kishi da ba'kin cikin samun nasarar da Linda tayi akan wannan had'addan guy da ludayinsa yake kan dawo..... Pls kuyi sharing👏🏻 _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *Free Pege 17_18* Jonny dashi da amaryasa suka mi'ke daga gurin zamansu cike da nishadi suka nufi gurun rawar, Suna isa Jonny ya fara watsawa Hafeez 'yan dubu dubu sabbi kar-kar dasu! Ishak da Huzaifa suka karaso gurin cikin nishadi da farin ciki abokinsu ya fitar dasu kunya, manya wayoyinsu suka dauko suka soma daukar hotunan Hafeez din shida Ashanty da suke wata irib rawa suna tattaba jikinsu, Aikuwa ganin Huzaifa da Ishak na vdo da pictures sai jama'ar dake gurin suma suka soma daukar vdo da wayoyinsu, sai sannan Hafeez ya ankara yay saurin sakin yarinyar ya fita daga gurin dan saboda baya son a sashi a bakin duniya, yasan tunda vdo da pictures dinsa suka fita to babu shakka duniya sai zata gani, Yana zama ishak da Huzaifa suka karaso gurin cike da farin ciki Ishak yace."Guy kalli vdo nan kagani gaskiya abun ya 'kayatar da yawa wallahi yau kayi masifar burgeni dan banta'ba sanin haka ka iya rawa ba." Hafeez ya karbi wayar yana dubawa, murmushi yayi dan shima abun ya burgeshi sosai, to amma sam baya so vdo ko pictures dinsa su fita har wani nasa ya gani! Yace."Ishak pls kagoge vdo nan dan Allah." Huzaifa dake sake duba pictures din yace."Dalili."? Goshinsa ya dan murza ya tsuke karamin bakinsa a miskalance yace."Bana so vdo ya futa wallahi saboda kasan halin maihafina yana da zafi! kaga dai wannan abun da nayi ba wani abu bane na laifi kawai naji dad'i ne na lokaci 'kan'kani! amma idan ya gani zan iya shiga 'bacin rai wallahi." Ishak ya girgiza kansa yana mamakin maganarsa yace." Gaskiya Hafeez dad dinka yana takura maka wallahi! haba abun is to much!! Kada fa kayi tunanin bamu san shine ya hanaka aure ba, kullum kana b'oye mana tuntuni mungane cewar shine ya hanaka aure shiyasa muka amince maka da matayenmu domun mu taimaki kanmu gabadaya amma dai komai abunsa sai munyi aure mun mori matarmu wallahi." Huzaifa ya bashi hannu suka tafa! yana dariya yace."Kai ni Bab din nan ma da sukayi rawa yanzu wallahi ita nake kwadayin ya aura Hafeez kunyi masifar dacewa da bab d'in nan wallahi."! Huzaifa ya karashe maganarsa yana d'an dukan kafad'arsa......Hafeez kallonsu kawai yake yi ya ma rasa abinda zai ce musu, wato sunan suna jira yayi aure su ramawa kura aniyarta lallai akwai 'kalubale a gaba, shi dai yasan cikin matansu babu wacce ya ta'ba yin sex da ita 'ballanta suce wani abu amma yanzu ba zai ce musu komai ba zai cigaba da tafiya kan tsarinsu sai a gaba zai nuna musu nasa tsarin!!! Ya kalli Ishak yana 'kokarin bagarar da maganar Huzaifa yace."Malam ka goge vdo nan dan Allah." Huzaifa yace."Wai me yasa kake cewa mu goge vdo wani abu kayi wanda ya shallake hankali da tunani! ni wallahi duk wanda zaiyi magana kan vdo ka da yarinyar nan ba zai dameni ba dan banga abinda da kayi ba wanda za'a saka a bakin duniya, wanda suka san meye duniyar ne zasu sha'awar abun kana kuma suji ka burgesu.'' Yace."Ishak! Daddy nake tsoro wallahi." Huzaifa yace."Kasan dai mu abokan juna ne masu rufin asiri bata yarda za'ayi mu futar da wannan vdo duniya tagani." Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya 'kurawa Ashanty ido wacce take kokarin karasowa inda suke....Tana zuwa ta zauna kusa dashi tana shashshafa kirjinsa had'e da kiss dinsa a kumatu! Lumshe idonsa yayi yana jin yanda take 'kara kunnashi! anya kuwa zai iya kauda kansa daga kan yarinyar kuwa.....Lumshe idonsa yake yana d'an kai hancinsa jikinta yana shanshanata kamshin turaranta ya tafi da imaninsa, a take ya soma tatta'ba jikinta yana d'an lasar lips dinsa.....Ishak da Huzaifa gurin suka bari ganin Hafeez din ya hau network sai suma sukaje suka samu bebis d'insu suka soma biyan bukatar junansu. Hafeez yayi masifar yabawa da bajintar Ashanty dan sosai ta kusa sashi ya mutu saboda salon da take masa bai ta'ba cin karo dashi ba, sai da ya samu cikakken satisfaction ta hanyar romantic tare da ita, sannan ya kar'bi accnt numbar dinta da alkawarin zai tura mata 1millon saboda jin dadin da yayi da ita, Ashanty ta dinga tsalle da murna bayan shigar Hafeez din wanka, tayi alkawarin makalewa guy din domin ta kowane fanni yayi gashi ya iya love ga kudi ga aji da kasaita gaskiya zata rike wuta sosai a kansa. Sai da ya saka kayansa ya dauki agogonsa yana dubawa yaga karfe d'aya na dare! A fili yace."Shikkenan na mutu."! Ashanty ta karaso kusa dashi ta rugumeshi ta baya tana shanshana shi tace."Baby wane irin mutuwa kuma ko baka manta da abun dazu ba." tafada tana d'ora hannunta kan joystick dinsa, ture ta yayi da hanzari ya fita daga dakin, kallo ta bishi dashi tana lasar lips dinta.....Yana fita yaga gurin kamar rana haske dal dal jama'ar yanzu sunfi na d'azu yawa gurin ya cika makil! sai ciye ciye ake ana cashewa! Wayarsa ya dauko ya nemi numbar Ishak, tana ta ringing bai dauka ba, tsaki! yaja yay gaggawar fita daga gurin, yasan Huzaifa da Ishak na can tare da mata, ko ya neme su a yanzu ba zai gansu ba, shi kuma yanzu gabakidaya hankalinsa yayi gida, yana gudun masifar dake jiransa........Yana kokarin shiga da motarsa cikin gidan Kiran wayar Safna ya shigo wayarsa, da sauri ya dauki wayar ya kashe ya ajiyeta, parking yayi ya fito a gurguje ya nufi cikin gidan........Fitilar palo ya gani a kunne gabansa ya fad'i! sai ya hau rarraba idonsa a katafaran palon Can kan kujerar da Prof ke zama ya hango gilashinsa da wani karamin littafi a ajiye!!! da alama bai jima da barin gurin ba, kuma tunda ya ga fitilar palon a kunne yasan xai dawo." Da wani mugun sauri ya soma hawa steps din yana had'awa bibbiyu uku uku! yay saurin bude dakinsa ya shiga ya maida kofar ya rufe! ajiyar zuciya ya sauke ya wuce ciki ya zauna kan sofa ya soma cire takalminsa yana mamakin bin'kwakwafi irin na mahaifin nasa yasan shi yake jira ya dawo ya ci masa mutumnci shi kuwa ya shirya karyar da zai masa idan Allah ya kaimu gobe.....Bayan shigar Hafeez Professor ya dawo palon ya zauna jiran gawon shannu, yau yayi alkawarin 'kure 'karyar Hafeez d'in shiyasa ya shirya kwana a palon yaga karfe nawa zai shigo cikin gidan. To har asubahi Professor na zaune daram! a palo ba tare da ya gyangyad'a koda sau d'aya ba, yana zaune yana kallon hanya da kallon agogo, har sai da yaji massalatai zasu tada kiran sallah asubah ya hakura ya mike ya hau sama ya dauro alwala ya sakko domun zuwa massalaci, Yana fita suka gaisa da maigadi nan yace dashi kada ya sake ya bude gate bayan futarsa. Maigadi yace insha Allah."Fita yayi ta karamar kofa ya nufi massalacin yana tunanin halin yaron nasa, addua ce magani kawai amma almarin na hafeez yanzu ya daina bashi mamaki! abinda yasa yace kada maigadi ya bude gate saboda yasan Hafeez din zai fakaice da lokacin shiga massalaci ya shigo gidan kamar yanda ya saba." Koda ya fito daga massalacin bai shiga cikin gidan ba sai ya zauna kujerar maigadi yana saka idonsa a hanyar shigowa yana dakon shigowar Hafeez d'in, Har gari yayi haske babu labarin Hafeez a cikin gidan, ransa a tsananin 'bace ya mi'ke ya nufi ciki, Hafeez bai ta'ba 'bata masa rai ba irin yau!! Yana shiga palon Hafeez na kokarin sakkowa daga benansa cikin jallabiya milk color da carbi a hannunsa sai kace wani mumini." Professor sakin bakinsa yayi kawai yana kallonsa har ya sakko ya karaso kusa dashi." Daddy barka da asubah."Yafada a kamilance yana mika masa hannunsa na dama. Jiki a sanyaye Prof ya mika masa nasa hannun sukayi musabaha da juna, yace."Hafeez dama kana cikin gidan nan."? Cikin dakewa yace."Eh Daddy wani abunne ya faru."!? Prof ya dinga kallonsa yana girgiza kansa, gabakidaya kansa ya daure sosai yana mamakin ta ina Hafeez din ya shigo ba tare da ya ganshi ba. Yace."Tun misalin goma na daran jiya nake zaune a palon nan har karfe biyar na asubahi banga gilmawar k'waro guda ba ballanta naga shigowarka ina so kasanar dani ta ina ka shigo mun gida ko ka amso sa'a ne gurin malamai sun baka layar zana." Hafeez ya fashe da dariya!! da yana kallon Daddyn nasa sosai ya bashi dariya da maganarsa wai layar zana to shi ina zashi a bashi sa'a shima malamin kansa ne!! Yace."Daddy wallahi ka bani dariya wace irin sa'a kuma? kace kai dai kawai ka zauna ne a palo kana so ka tarfa ni! kaga ta inda zan shigo! Allah sarki my Dad d'ina! Tuntuni na shigo gidan tun misalin takwas saura lokacin duk kun shiga sallahr isha'i! da yake ciwona ya d'an motsa mun yasa ban sakko naci abinci ba, ina hawa benena na samu nayi wanka yasha maltina sai kawai nasha magani na kwanta, bacci ya daukeni ban farkaba sai bayan an idar da sallah asubahi shine dalilin da ya sanya ma ban samu zuwa massalaci sallah ba." Prof jikinsa yayi sanyi da jin maganganun Hafeez d'in! fuskarsa ya saki yana kallonsa a nutse yace."Dazu bayan hawa ta sama Mommy ka ke shaida mun ka fita raina ya baci saboda nasan yau Sunday ranar hutu ce dan me yasa kai ba zaka zauna ka huta a gida ba, nan take shaida mun cewar kana da bikin abokin ka kace da ita can zakaje, wannan dalilin ne ta sanya na gamsu da uzirinka, to ganin goma na dare tayi baka shigo gida ba ya sanya na zauna zaman jiran shigowarka ashe tuntuni ka shigo bamu sani ba." Hafeez ya dan lankwasar da kansa yana kallon mahaifin nasa cike da tausayinsa, Daddy ya damu dashi sosai wai shin wannnan abin da yake nunawa a kansa so ne ko takurawa ce? Bashi da mai bashi amsa dole sai shi Daddyn sa, Yace."Daddy wani lokacin idan nagana kana tattalina da kulawa dani wallahi har tausayi kake bani Allah ya bani ikon yi maka biyayya Daddyna.! Prof yayi murmushi yana sake jin kaunar d'an nasa yace."Ameen yarona ina so inga ka zama kamilin mutum cikkake managarci."! Hafeez ya rungumeshi sosai yana sake tsinkewa da a'lamarin mahaifinsa.....Palo suka nufa hannunsu cikin na juna. **** Baba Tinde sai da ya kwashe tsayin sati biyu a kwance a asibiti sannan ya soma gane waye a kansa, Ya rame sosai matarsa mai suna Lara itace ke jinyarsa da 'yan samarin 'yayansu duk maza! Lara duk taji bayanin da dr yayi mata kan lalurar mijinta sosai taji mamaki! akan abinda Dr d'in yace dangane da joystick d'in Mijin nata, wai da kyar in zata dinga kuzari da karfi kamar yanda take aiki ada! Lara ta tambayeshi dalili nan ya warware mata komai, dan Dr din sai da ya zauna da Emanuel da maigadi ya tambayesu dallah dallah dangane da abunda ya faru da ogon nasu, babu batun 'kunbiya'kunbiya suka warware masa zare da abawa cewar yarinya ya dauko domin yaji dadi da ita ita kuma ta murde masa mazakuta."! Dr dake mai zuciyar imani ne kuma dama yana cikin likitocin dake ya'ki da masu aikata har zinace zinace da fyade ga 'kananun yara, Sai yaji masifar dad'i da abinda Asiya ta aikata ga Tinde Allah yasa hakan ya zama izina ga mutane masu irin wannan d'abiar. Lara hankalinta ya tashi sosai! dan ita kaf rayuwarta idan ba tayi sex kullum ba to ba tajin dadi Baba Tinde ya saba mata sosai kuma tana masifar jin dad'insa dan yana da katuwar jijiyar dake ratsata sosai shiyasa take kishi sosai da duk macan da zata rabeshi, hankalinta a tashe ta iske shi gadon da yake kwance ta hau sirfa masa masifa da bala'i!! Baba Tinde ya kalleta cikin tsananin takaici da muguwar damuwa da nadama yace."Lara baki kaini fa jin ciwo da takaicin wannan al'amari ba, dan bakiji yanda zuciyata take mun zafi ba!! Addua kawai nakeyi na samu lafiya na nemi yarinyar nan ita da Wacce tayi sanadiyar haduwata da ita na dauki alkawari sai na dauresu muddun rai! bana yafiya kuma bana manta ranar daukar fansa! yarinyar nan ta cuceni tunda sauran kuruciyata."Murya na rawa ya karasa maganar ta inda zaka san yana cikin halin damuwa gami da tsananin bala'i!!!! Lara tace"Ba wani ne ya jawo komai ba sai kai! meye banayi maka na zamantakewa duk kokarina sai ka nemi matan waje! ai gashinan ta cuceka dan ni ba zan zauna da kai a haka ba, zan tafi yanzu ka boyoni da takardar sakina, yara ne dama sun girma sai su zauna suyi jiyyarka." Tana gama maganarsa ta kad'a kanta ta fice daga dakin, Baba Tinde ya shiga girgiza kansa yayin da wata irin zazzafar kwalla ta sauka akan kuncinsa......Kwafa! yayi yana cin laya a kan Asiyatu 'Yar maishanu! ***** Alhamdullhi Asiya an zama 'yan makaranta, tun safe i dan drvar ya kaita ya ajiye a skull sai misalin shida na yamma zaije ya daukota, dan abinci ma shike komawa ya kai mata, karfe biyu sun tashi daga boko sai su shiga isilamiyya, sosai ta maida hankalinta kan karatu sai dai takasa sakewa da kowa a makarantar abinda ya kaita kawai takeyi. Bata samun zama a gida sai asabar da lahadi shima da yamma ne dan da safe suna zuwa islamiyyar dake bakin titi ita da Farhana, karfe hud'u da rabi ake tashi! Tayi kyau sosai ta sake 'kiba, dake macace mai gam'ba! gami da 'baragen jiki!! Hasken fatarta ya dawo duk datti da kirci da dauda babu shi duk sati suke zuwa wanki kai da kafa! fatar ta kamar ka matsa jini yayi tsartuwa! sai dai har yanzu idan ciwonta ya tashi takan 'buya a d'aki!! tayi susarta yanda ranta yake so, duk ranar data kwarjane!! fatarta kuwa zama take taci kuka ta koshi! ta sauya pant ta fito tana wawware kafafunta..............Yau ma tun safe! 'kyaikyayin ya taso mata gashi suna zaune gabadayansu a palo har mutuminta ana hira, sai mutsu mutsu takeyi, a hankali ta dan zura hannunta cikin sket dinta ta shiga sosawa tana lumshe idonta, d'an sake bud'e kafafunta tayi ta cigaba da sosawa idonta a rufe!! Mommy da Farhana hankalinsu na kan tv suna kallon maimaicin shirin DADIN KOWA! Hafeez dake ba gwanin kallon hausa film bane ya yun'kura zai mi'ke kawai idanunsa suka sauka a kanta! tana ta sosawa tana lasar leps dinsa!! Cike da mamaki ya tsaya yana kallonta, me yarinyar nan take sosawa a cikin wandonta? tambayar kansa yake! Cikin wata irin tsawa! Yace."Ke!!!! a furgice ta bud'e idonta! fit! ta zare hannunta daga cikin sket dinta tana kallonsa, ya tsirawa idonta ido yaga sunyi jaa!! al'amarin yayi masifar girgiza shi, shin me yarinyar nan ta sani a duniyar nan da har take zura hannu a wando!! Mommy tace"Wannan wane irin abune kawai zaka razana yarinya da tsawa!! Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, kawai ya girgiza kansa ba tare da yace komai ba ya fice daga gidan yana mamakin abun a cikin ransa......Asiya kuwa kunya ce sosai ta rufe ta tasan ya ganta tana susa, yanzu da wane idon zata kalleshi, jikinta sanyi yayi sosai tana adduar Allah ya yaye mata wannan masifaffan ciwo dake damunta. Bayan kwana biyu da faruwar al'amarin Asiya ta dinga 'kauracewa had'uwarta da Hafeez dan Allahn da ya hallice ta ya hallice a matsayin mace mai kunya kallon da yayi mata a lokacin shine ya tabbatar mata da cewar kamar yana zarginta da wani abun.....Shi kam Hafeez ya manta ma da abun da ya faru sai dai in yaji maganarta da Farhana ko yaga gilmawarta yake tunawa, sai dai kawai ya girgixa kansa...........Yana zaune a palo shi kadai wayarsa ce a hannusa yana latsawa, Ta fito daga kicin hannunta ri'ke da wani jug irin mai daukar sanyi da zafi nan lemo ne a ciki Mommy tace mata ta kai dannig dake yau ana azumin tashua da ashura duka gidan azumi sukeyi shiyasa ma shida Daddyn suka dawo gida da wuri domin su sha ruwa. A tsorace! ta nufi danning hannunta rike da jug din tafiyarta sai hard'ewa takeyi, duk sanda zata hada ido dashi duk wani kuzari nata takan nemeshi ta rasa! Ya dauke kansa daga kan wayar hannunsa ya bita da kallo tana tafiya, faffad'an hips d'inta dake juyawa cikin siket din atamfar dake jikinta shi ya tsirawa ido! lokaci kankani yaji jikinsa ya saki! gabadaya wata masifaffiyar sha'awa na yunkuro masa, yarinyar zatayi zurfi da ni'ima!! abinda zuciyarsa ke raya masa kenan! ya lashi lips dinsa na kasa, yana sake kureta da idonsa, tabbas duk macen dake da tsayi da fad'in kwankwaso tana da sirrin da ba kowace mace keda irinsa ba, yarinyar tayi duk da cewar bata gama cika mace ba! Ji yayi aziminsa na 'kokarin karyewa!!! a gigice! yace."Ke!! Ta juyo tana kallonsa jikinta na rawa! Harararta tayi yace."Dallah wuce ki bawa mutane guri kazama kawai." !! Da sauri ta juya baya tana tafiya! Cikin gaggawa ya sunkuyar da kansa kasa, yana jin yanda joystick dinsa ta soma mi'kewa, shikkenan zata sanya ni ishirwar banza an kusa shan ruwa, azimi na zai karye! mtssssw? yaja tsaki me karfi ya mike da sauri ya haye sama! kwanciya yayi kan sofa yana hada zufa! sai kokarin korar shaidan yake daga jikinsa yana adduar Allah yasa Aziminsa ya tsira! Alarm din kiran sallah yaji, ya sauke ajiyar zuciya yana furta kalmar "Alhamdullhi! mikewa yayi ya nufi toilet domun yin bursh gami da alwala. Suna dawowa daga massalaci suka zauna katafaran gurin cin abincin nasu, Ganin aikin yana so yayi wa Mommy yawa ya sanya ta mike a nutse ta soma taimaka mata! Yace." Ke! zauna dallah bama son kazanta kullum hannunki a wando kina susa sannnan ki ta'ba mana abinci." Mommy ta kalleshi tana so tayi magana Prof ya karaso gurin, Asiya kuwa jin abinda yace ya 'bata mata rai sosai! hararasa tayi ta cigaba da zuzzuba musu lemo a cups ba tare data bi umarninsa ba, tana kallo kowa ya dauki lemon yana sha bandashi, sai ma ya jawo lemon kwali ya bud'e da kansa ya tsiyaya ya shiga shan abinsa.......Taji zafin abun amma bata nuna ba kawai ta share ta bar abun tagane idan tace zata saka damuwa da 'bacin ran Hafeez d'in to ciwo zai iya kamata, shiyasa duk sanda yayi mata abu take 'kokarin watsar dashi a gurin, sai ta nuna masa ma bataji haushi ba. Koda ya kammala cin abincinsa a daining din maza yayi ya bar gurin domin zamansa a gurin tare da yarinyar kan 'kissama masa abubuwa da yawa, shiyasa ma har ya gama cin abincinsa bai sake kallon inda take zaune ba. Yayi ta dubarar so ya fita a daran Professor ya kafa ya tsare a palon tilas ya hakura ya zauna kusa dashi suna hira ya fahimci zamansa tare da dashi din ya faranta ransa, addua yayi cikin zuciyarsa kan Allah ya bashi ikon yiwa mahaifin nasa biyayya. Washe gari da wuri suka tafi ofis saboda suna da bakin da zasu zo daukar kaya daga legos, dan haka bakawai a ofis tayi musu.....Farhana da Asiya ko wacce ta sakko cikin shirin makaranta, suka zauna suna karyawa suna hira, Mommy ta sauko suka gaisa sukayi mata sallama suka tafi, sai da direba ya soma ajiye Asiya a makarantarsu sannan ya wuce da Farhana jami'ar da take karatu wato b.u.k. Da yamma Ladadi mai aiki na shirye-shiryen tafiya gida sai ga Taburni kanwarta ta dira a gidan, Mommy tayi mata barka da zuwa, Taburni dama ta saba zuwa gidan ta gurfana gaban Mommy tana kwasar gaisuwa Mommy tace"Taburni kwana biyu kin yada mu ko bakya zuwa daukar kaya ne a kasuwa." Taburni tace"Wallahi hajiya al'amura ne sukayi yawa sosai gari babu kudi ga matsaltsalon nan da ake ta fama dasu na cutar corona shine dalilin da ya sanya na zauna a gida nace idan kura ta lafa sai na shigo." Mommy tace"Aikuwa kinxo a sa'a akwai kayan dana ajiye miki su." Taburni ta washe baki tana kallom yayarta Ladidi dake zaune tana murmushi tace"Ladadi ki tayani godiya gurin Hajiya kinji abin arziki ko." Ladadi tace"Hajiya Allah ya saka da alkairi kullum dai bakya gajiya da alkairi." Mommy tayi murmushi ba tare da tace komai ba ta mike ta nufi sama. Taburni da Ladadi suka shiga 'kus-kus! a palon suna kalle kalle mussaman dai Taburnin dan ita Ladadi komai na gidan ba bakonta bane. Motarsu Hafeez na shigowa gidan, ko gama parking direba baiyi ba suma suka shigo cikin mota 'Dalha direba na tukasu. Parking yayi da sauri ya fito yana wa Professor barka da zuwa, Farhana da Asiya suka karaso gurin suna masa barka da zuwa, Hafeez dake cikin mota ya bude ya fito yana dan kallansu, Farhana tace"Bro ya aiki." Yace."Alhmdullhi baby."Gaba yayi yana dan murza goshinsa, Asiya ta bishi da kallo 'kasa-'kasa tana jin tashin tsigar jiki, a kullum kauna da sonsa karuwa suke a cikin zuciyarta Suna tafiya domin shiga cikin gidan Professor yace."Ya akayi kuka dawo gida a tare alhalin ko wanne da makarantarsa." Farhana tace."Mun tashi daga lecture karfe uku da na kira Dalha nace yazo ya daukeni to ganin mu biyo ta titin rijiyar zaki yasa nace kawai ya samu guri yayi parking mu jira Asiya ta fito tunda a lokacin an kusa tashinsu." Yace."Hakan nada kyau! Professor ne a gaba sai Farhana Asiya ita a bayansu.....Su Taburni na ganin maigidan sai zuka sunkuyar da kansu suna gaisheshi Professor ya shiga amsawa yana kokarin hawa sama, Taburni na d'ago kanta kawai sai taga Asiya na kokorin wuce wa dan ita bata gane ta bama. Cikin gigita gami da razana! Taburni tace."Asiya!!!!! Da sauri Asiya ta kalleta a take ta shaida ko wacece a gabanta!! Sai jikinta ya soma rawa! jakar littafan ta ta fadi a gurin......Taburni ta d'aga hannunta wanda ke wani irin karkarwa tace"Asiya bayan kin gama ta'addacin! dama nan kika gudo kika samu gurbin zama a gidan mutane."!!!! Wannan maganar tayi dai-dai da sakkowar Hafeez da Mommy daga sama, kawai sai suka tsaya suna kallon Asiya dake wani irin kuka! jikinta sai rawa yake yi shikkenan kashinta ya bushe tunda Taburni ta ga inda take........Taburni ta dinga tafa hannuwa tana salati da sallalami! Mommy tace"Taburni kin santa ne? Taburni ta zabura! tana kallon Mommy din tace"Farin sani kuwa Hajiya! Wannan yarinyar 'yar mijin aminyata ce Gaje dake can garinmu, wattani uku kenan da yi mata aure da wani bawan Allah, a daran ranar da aka kaita gidan mutumin ta murd'e masa azzakari! bata hakura haka ba ta kama azzakarin babban d'ansa shima ta murd'e! ta gudo ta barsu cikin halin rai da rayuwa, Hajiya yanzu zancen da nake miki Alaji Bawa ya zama shashasha ya shiririce duk saboda wannab ta'adancin da yarinyar nan ta aikata masa, dan gwara yaron nasa ba taci galaba a kansa ba sosai shi lafiyarsa lau! yanzu dai suna can suna nemanta da al'kawarin mutukar sun kamata sai sun sabauta mata rayuwa kamar yanda ta sabauta rayuwar ubansu."!! Wannan magana tayi masifar bawa Mommy tsoro da mamaki!! ta dinga kallon Asiya ta ma rasa me zata ce ita kuwa Asiya kuka takeyi mai gunji, hawaye yayi kaca kaca a fuskarta......Hafeez dariya kawai yake yi ya kama hanyar futa yana mamakin al'amarin babu shakka idan kana 'kauye zaka sha kallo! kamar yarinyar nan gallafiri da ita har tasan ta ri'ke ma'karfafar mutum! abun ya dinga bashi dariya da mamaki! babu shashasha! sai wand'anda zasu tsaya har ta samu galaba a kansu, yana ganin idan shine tayi yunkurin yi masa wannan ta'addancin zai kamata ne ya wargaje mata kafafu, ya samu Ta'barya mai kauri da tsayi ya zurkud'a mata a gabanta sosai zai dinga buga mata ta'baryar har sai yaga jini na tsartuwa sannan zai kyaleta. Tsaki yaja yana girgiza kansa ya fice daga palon. Pls kuyi sharing _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *DA WATA A 'KASA!!* Writing By *BINTA UMAR ABBALE🍒* ~~~~~~~ *🌎Manazarta Writers Asso* _'Kungiyar Masu Nazari da aiki da Ilimi._ ~~~~~~~ *YA SHAFI👏🏻* *YA KAFI👏🏻* *YA MU'AFI👏🏻* *Last Free Pege19_20* Mommy tace"Asiya abinda Taburni take fad'a gaskiya ne dama abinda kika aikata kenan a garinku kika gudo."Asiya ta shiga girgiza kanta hawaye na zuba a fuskarta ta zube kasan kafet tana cigaba da girgiza kanta hade da wanin irin kuka me ban tausayi. Taburni tace"Haba hajiya ai mara gaskiya ko a ruwa gumi yake yi baki ga yanda ta razana na lokacin da ta ganni wallahi dik abinda na fada dangane da ita gaskiya ne." Jiki a sanyaye Mommy ta nemi guri ta zauna tana kallon Asiyan da mamakin abinda ta aikata. Prof ne ya sakko daga sama yaga Asiya durkushe tana kuka su kuma sun zuba mata ido. Cikin 'bacin rai yace."Me yake faruwa ne? naga Asiyatu na kuka kuna kallonta." Mommy ta kalleshi a nutse tace"Yallabai zo ka zauna kaji aikin da Asiya tayi a garinsu ashe 'kauyan su Taburni take." Prof ya zauna kusa da ita yana kallon Taburni fuskarsa babu yabo babu fallasa shi sam baya son gutsiri tsoma irin na mutane, Yace."Taburni kin san wannan yarinyar ashe, masha Allah dama haka muke so muga wanda yake da ala'ka da ita."Prof ya warware wa Taburni yanda akayi suka tsinci Asiya da yanda suka dinga fama da ita ta sanar dasu daga wane gari take ta'ki. Taburni tace"Alhaji Wannan yarinyar ai ba zata so ta koma cikin garin Fanisau ba saboda tasan mummunan aikin data tafka a garin, kisan kai ne kawai yarinyar nan ba tayi ba amma tayi sanadiyar shiriricewar Alaji Bawa mutumin da ya rufa mata asiri ya aureta a lokacin da kowa ya guje ta.'' Nan Taburni ta warware wa Prof zare da abawa abunda ya faru wanda ya saka Asiyan guduwa domin ta tsira da ranta. Prof shima abin ya daure masa kai sosai ya jima yana kallon Asiyan kafin ya girgiza kansa ya kalli Taburni a nutse yace."Yanzu ya jikin mutumin da wannan al'amarin ya faru dashi." (Yana nufin Alaji Bawa) Taburni tace" To jiki dai za'a ce da sau'ki Alhaji amma al'amarin na Alaji Bawa kullum 'kara gaba yake yi." Prof Yace."Allah ya bashi lafiya, yanzu tunda mun san inda Asiya take da iyayenta insha Allah zamu shirya zuwa garin tare da ita domin mu sadata da iyayenta da shi mijin nata ta nemi afuwarsu gabakid'aya amma ha'kik'anin gaskiya abinda tayi ba dai-dai bane, sha'anin 'kuruciya ne kawai Allah ya kyauta." Suka amsa da ameen." Asiya da rarrafe tazo ta ri'ke kafafun Prof tana kuka take fad'in Daddy kayi mun rai dan girman Allah kada kace zaka mai dani garinmu wallahi kasheni zasuyi ni bana son Alaji Bawa ni ba mijina bane, Daddy idan kuka mai dani garinmu karatuna fa? kada ka manta kaifa kayi mun al'kawari cewar zaka zama uwa da ubana daddy ka cika al'kawarin daka dauka ni bani da iyaye sai ku." Prof ya dinga kallonta cike da tausayi yace."Asiya dole ne muje dake garinku mahaifinki shike da iko dake bayan shi ga nauyi aure a kanki tilas muje mu zauna dasu domin mu san abinyi." Taburni tace"Ai tuntuni ya saketa saki uku." Prof yace."Subahannalahi." Taburni ta cigaba da cewa "Yana fitowa daga asibiti yaje har 'kofar gidan maishanu yay sallama dashi ya mika masa takardar sakinta." Prof yace."To alhmdullhi naji dadi faruwar wannan al'amari yanzu zamuje ta nemi gafarar mahaifinta bisa bujirewa umarninsa da tayi, sannan kuma da kaina zan kaita fadar maigari na sanya a kira shi tsohon mijin nata tabashi hakuri kan abinda ta aikata masa." Taburni tace"To hakan yayi Alhaji Allah ya kiyaye gaba." Asiya gefe ta koma tana goge fuskarta, wani irin haushin Taburni take ji, Cikin 'bacin rai! Mommy ta shiga yi wa Asiya fad'a kan abinda ta aikata Asiya na kuka tace"Mommy bana sonsa ne shiyasa naji ba zan iya amince masa ba, dan a lokacin ma ji nake kamar na caka masa wu'ka! na kasheshi na huta." Prof yace."Subahannallahi! Ya kalli Mommy yana 'kokarin mi'kewa yace."Maganar nan ta isa haka tunda dai anyi abun ya wuce sai a bari! 'kuruciya ce kawai ta d'ebeta a lokacin, dama kuma irin wannan abun ake gudu ga auran dole ga wad'anda basa so, naji dad'i da al'amarin ya tsaya iya haka bata aikata abinda take fad'a ba yanzu." Jiki a sanyaye tace."Shikkenan Allah ya kyauta ya kiyaye gaba." Ya kalli Taburni yace."Ranar asabar zamuje can garin naku sai kiyi mana jagora." Taburni tace"To Alhaji dama ranar zan koma gida sai mu tafi tare daku." Bece komai ba ya fita daga palon.....Mommy ta mi'kawa Taburni kaya cikin manya manyan ledoji guda biyu tace"Kije da wannan insha Allah ranar Asabar idan kinzo zaki tarar da wasu na had'a miki." Taburni ta dinga godiya kamar zatayi sujjada Ladidi yayarta na taya ta......Sallama sukayi wa Mommy suka mi'ke tare Da yake dama Ladadi ba a gidan take kwana ba tana da karamin gidanta da Prof ke biya mata kudin haya can tsallaken layinsu idan tazo tun misalin shida da rabi na safe bata tafiya sai ta gama komai da duk abunda suke bukata. ***** Madam Semi zuwanta biyu asibiti tana duba Baba Tinde, sosai ta tausaya masa kuma ta shiga data sanin taimakon Asiyan da tayi ganin tana nema ta jawo mata masifa, kuka ta dinga yi tana bashi hakuri Baba Tinde kuwa jinta kawai yake yana kallonta yana so kawai ya samu sau'ki ya kame 'yar iska yasa ayi ta azabtar da ita har sai ta fada masa ina ta 'boye yarinyar dan duk bai yarda da irin maganganun da take masa na cewar bata da ala'ka da Asiyan bayan kuma had'uwarsu ta farko ta tabbatar masa da cewar 'yarta ce, yana ganin cikin maganarta babu shakka akwai lauje cikin nad'i yana ganin ta shirya wannan makircin ne duk domin taci kud'insa. ***** Hafeez kam duk sanda zai tuna al'amarin dariya yake yi sosai dan sai da ya kasa 'boye maganar ya fadawa su Huzaifa labarin Asiya da yanda suka tsinceta da kuma abinda ta aikata a garinsu wanda ya zama silar guduwarta, To suma mamaki! sukayi sosai da sosai lokaci guda sukaji suna sha'awar ganin yarinyar ido da ido saboda yanda al'amarin ya girgiza su, Hafeez yace kuma kada ku dauka babba ce Farhana ma ta girmeta sai tafi Farhana girman jiki, duka bata fi 15yeras ba, amma wai itake aikata wannan aikin." Yana dariya yake maganar.Ishak Yace."Babu shakka yarinyar nan 'yar daba ce ko a can 'kyauyen nasu ma, amma nan idan tace zata aikata wannan iskancin ubanta za'aci wallahi! Ni sai naji ma ina sha'awarta wallahi so nake inga zata iya aikata wannan d'anyan aikin akaina, wallahi sai naci ubanta sai na yagalgala ta na cinyeta tsaf! sai na d'aukarwa mutumin da tayi wa wannan iskancin fansa. Huzaifa yace."Kai! ni kuma wallahi tsoranta nakeji haka kawai ina d'an jin d'adina ta kassarani, duk hukuncin da zanyi mata bazan huce ba kaima kayi taka tsantsan." Cikin rashin damuwa da kulawa Hafeez yace." Guy kana da damar da zaka nuna mata kai d'in namiji ne dan wallahi nima taba ni haushi sosai tsanar da nake mata ta sake ninnkuwa saboda martabarmu data ta'ba. Ishak yace."Kaine ai zaka had'ani da ita xanje da sigar ina sonta da aure daga nan na shigar da kaina sosai sannan naci ubanta sai na 'kwa'kuleta wallahi kuma na d'aure mata baki! mu har a gaya mana duniya." Hafeez yace."sai an kwana biyu zamu tsara yanda za'ayi." Da wannan shawarar suka rufe maganar da sukeyi suka shiga wata. Asiya komai takeyi cikin rashin jin dadi takeyin sa duk lokacin data tuna zasuje gida sai gabanta ya fad'i dan har 'buya take taci kukanta ta 'koshi! Mommy da Farhana ma sun fahimci sauyawarta, Prof da yaga tana salo salo ya shiga rarrashinta da fad'in Idan sunje zai nemi alfarma gurun babanta kan ya barta a hannunsa har ta kammala makaranta, wannan maganar ce ta sanya ta sakin jikinta ta shiga walwala da mutane. **** Ranar Asabar ranar Tafiya babu yanda Prof beyi da Hafeez ba kan ya shirya aje dashi ya 'ke'kashe ido yace ba zai je ba, haka Prof ya hakura ya kyaleshi suka tafi suka bar masa gidan shi kad'ai! Damar da ya samu kenan ya kira Titi a waya yace tazo gida ta sameshi, dan ko ofis beje ba so yake yau ya ra'kashe sosai tunda masu takura masa basa gidan, dama baya son yana neman Titi a ofis saboda rashin sakewa da kuma saka idon mutane....Titi tazo gidan suka haye benansa suka bud'e shafin iskanci kala kala, Yanda suke mu'amula da juna ke kyace masu aure ne. Tunda suka shiga garin Fanisau! Asiya take kuka a mota, sam bata kaunar ta sake yin tozali da wad'annan mutane guda uku Alaji Bawa Gaje da kuma Dalladi, har ta k'are rayuwarta ta duniya ba zata ta'ba mantawa dasu ba. Kai tsaye fadar maigari suka nufa Taburni ce keta nunawa Dalha hanya har suka isa fadar, Dalha ya samu wani fili yayi parking din motar, Maigari da mu'karrabansa na can bakin wata 'katuwar bishiya a zazzaune kan tabarma suka ga katuwar mota mai kyau da daukar ido tayi parking, ai sai maigari ya soma washe baki yana adduar Allah yasa wani mai kudin ne ya shigo siyan gonaki da filaye yasan dole ya samu kudi masu yawa.....Prof ne ya soma fitowa sannan suka fito gabakid'ayansu, Asiya sai 'buya take bayan Prof jikinta na rawa. Kai tsaye fadar maigari suka nufa. Maigari Halilu na ganin Professor na tunkaro in da suke sai kawai ya mike tsaye yana gyara babbar rigarsa sai dashare bakinsa yake, jama'ar fadar suka bishi da kallo cike da mamaki! sun rasa me yasa maigarin garin nasu yake haka duk sanda yaga 'bako ya shigo garin ya fahimci mai kud'i ne sai ya watsar da mulkin nasa a maimakon ya zauna a hakimce a kan kujerarsa azo a gaisheshi tunda garinsa aka zo A'a shine yake mi'kewa da gaggawa yana mi'ka gaisuwarsa, maigari Halilu baya nuna mulkinsa a ko'ina sai a iyakacin cikin garinsa. "Alhaji sannunku da zuwa sannu sannu ai tun daga nesa na hango zuwanku nasan babu shakka muhummin a'lamari ne ke tafe daku." maigari ne yake wannan maganar yana ta faman gyara babbar rigarsa. Prof ya mika masa hannu suka gaisa yana fadin"Kwarai kuwa muhimin abu ne ke tafe damu shiyasa ma kai tsaye nace mu nufo fada dan ta inda aka hau tanan ake sauka." Maigari yace."Babu shakka maganarka haka take Alhaji ku zauna ga gurin zama nan.." Prof ya nunawa su Mommy gefen doguwar tabarmar da babu kowa akai yace su zauna. duk suka bi layi suka zazzauna Asiya kanta a cikin hijab sai 'boyewa take. Gaishe gaishe aka shigayi kafin gurin yayi tsit! kowa ya zubawa Prof ido yana son yaji karin bayani....Prof yace."To Alhamdullhi ni sunana Prof Aliyu Nasir Adahama mamalakin Adahama motors and spire parts, Ina zaune a wannan jahar wato kano wataranar alhamis da ta wuce nida iyalina mun dawo daga ziyara muka tsinci wannan yarinyar kan titi kwance..........Prof ya shiga warware musu abunda ya faru komai bai rage ba sai da ya fada musu, kana kuma ya sanya Asiya ta bude fuskarta, a take suka zabura ganin Asiyatu 'yar gidan maishanu yarinyar da suke nema ruwa a jallo. Maigari ya bude bakinsa zai magana Prof ya tareshi ta hanyar daga masa hannu yace."Ranka shi dade ban tari numfashinka ba." Maigari yayi shuru yana muzurai ya had'e da watsawa Asiya harara. Prof yace."Nasan kana so kayi min bayani kan irin abunda ta aikata wanda yayi sanadiyar guduwarta daga garin, to na samu labarin komai daga bakin waccan baiwar Allahn data kasance 'Kanwa ga mai aikin gidana Ladidi, Aranar da taje duba 'Yar uwarta tayi tozali da Asiya a gidan nan take shaida mana duk abunda ya faru a baya, wannan dalilin ne ma ya sanya nace mu sauka a fada domin a warware matsalar yanzu ina so yallabai ya tura a kira mahaifin yarinyar nan da tsohon mijin nata." Maigari ya tashi na kusa dashi yace maza-maza yaje gidan maishanu ya tawo masa dashi, ya kalli wanda yake gefan hagunsa shima yace dashi yayi maza maza yaje gidan Alaji Bawa yace yazo fada zasu tattauna magana..............Mintuna goma wanda aka tura kiran maishanu ya dawo ya zube gaban maigari yace."Allah ya taimake ka na samu labari daga bakin Ma'kotan maishanu cewar yau kwanansa biyu da barin garin nan shida iyalinsa." Maigari ya zabura yana kallon dan aiken yace."Maishanu ne ya bar garina ba tare dana sani ba."? Maga takarda yace"Ranka ya dade shin ka manta abubuwan dake faruwa kenan, 'Yayan Alaji Bawa sun dauki alkawarin 'kona gidan maishanu har in dai basu dauki fansar abunda 'yarsa tayiwa ubansu ba, ina kyautata zaton wannan dalilin ne ya sanya maishanu yanke wannan hukuncin." maigari yayi shuru yana zullumi! Asiya kuka takeyi sosai tana kaunar babanata tasan wani abu n duk bayin kansa bane Gaje ce ke zugashi. Prof yace."amma abu baiyi dadi ba wallahi naso na samu mahaifin yarinyar nan mun tattauna dash........Kafin ya 'karasa maganarsa suka soma jiyo d'ure-d'uren ashar! d'in Alaji Bawa tun daga nesa suka hango tawowarsu shida d'an aiken yana sanye da babbar riga kawai da gajeran wando a ciki, kafafunsa babu takalmi yana tafiya yana nuni da hannunsa sai zage-zage yake yi......."Haka kawai ina zaune a gida ina hutawa za'ace nazo akwai mahimiyar magana ni akwai wata magana data dameni a yanzu burina kawai naga Asiyatu na rama abinda tayi mun, shegiya tsinnanniyar yarinya sai naci ubanki 'yar butan uwa."!!!! Asiya kanta tasa cikin hijab tana makyarkyata had'e da nanikar jikin Mommy wacce take a tsure! sai zare ido suke ita da Farhana. Prof ya dinga kallon Alaji Bawa tsoho d'an kimanin shekaru saba'in da wanin abun sabida tsabar zulama da son zuciya shine zai auri yarinya kamar wannan 'yar 15years wani abu sai kyauye. Alaji Bawa ya zauna yana kallon maigari da fad'in"Bani goro naci tukkuna kafin wata magana ta biyo baya dan na lura da ba'kin fuska dake zaune a gurin." Da sauri maigari ya mika masa wani katon goro ya kar'ba ya rabashi biyu ya soma taunawa yana tsotse ruwan......Prof ya zuba masa ido kawai yana kallonsa, Alaji bawa ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya yana kallon Prof din yace."Alaji kamar nasan wannan fuskar taka shekaru saba'in da suka wuce kamar munyi akin dukan manda'ko da kai."! Prof ya fashe dariya yana kallonsa yace "Anya kuwa ni ne Alaji."? Alaji bawa yana tauna goro yana murmushi kamar wani mai hanakali yace." Gaskiya kuna kama da wanda na sani." Fada tayi shuru maigari yana ta tunanin ta ina zai fara.....Alaji Bawa ya k'ure Farhana da ido yana kallonta yana lasar busassan lebansa, Farhana gabanta sai faduwa yake. Wata mahaukaciyar dariya ya saki! yace."Yau nayi sabuwar amarya gata can 'yar fara kyakykyawa tamkar ba indiya hahahahahaha! jama'a ku shida an d'aura aurena.'"!!! Ba Farhana kad'ai ce ta shiga rudani ba har da Mommy da take data sanin zuwa, ta tsani ganin abinda zai daga mata hankali.....Gani sukayi Alaji Bawa ya mi'ke yana tattare babbar rigarsa sama yana nufar inda Farhana ke zaune da fad'in "Kyakkyawar amaryata zo muje gida mana." A guje! Taburni ta mike dan bata manta abunda ya faru ba lokacin da sukaje gidasa. Prof ne yayi gaggawar rike masa hannu yana fad'in "Alaji zauna mana mu tattauna abinda ya tara mu." Fuzge hannunsa yayi ya cigaba da tattare babbar rigarsa yana so ya sab'ule gajeran wandon jikinsa......Taburni tace"Gwara fa kuyi wani abu akai dan wallahi yanzu zaiyi zigidir." Da sauri Maigari da Professor suka shiga rirrikeshi yayin da yake kokarin fizgewa daga hannunsu dole sai yaje inda Farhana take......Mommy ta mike da saurin gaske ta kama hannun Farhana suka bar gurin. Asiya ta mike zata bisu Prof ya hanata kusa dashi ya zaunar da ita jikinta sai b'ari! yake......Da kyar! Maigari da wasu daga cikin fadar suka zaunar dashi ya zauna yana muzurai da neman inda Farhana take. Sai da ya soma dawowa hayyacinsa tukkuna maigari ya shiga warware masa abinda ke faruwa ya zabura da karfi yake fad'in "Ina mutsiyaciyar yarinyar take yau sai na kasheta."!!! Prof yay gaggawar kare Asiya wacce Alaji bawa ya kaima mata wani mugun duka da hannunsa, Prof yace." Hakuri zakayi dan shine abinda ya cancanta wannan yarinya ba ta aikata maka wannan abu dan ta illata ka ba tsautsayi ne."! da fadin wannan magana ta Prof sai kawai Alaji Bawa ya rikice ya hargitse sosai ya shiga sambatu gami da kunzume kunzumen ashar!! Prof ya mike yana kallon maigari yace."Mu zamu koma ranka shi dade babu halin barin yarinyar nan a garin nan tunda iyayenta basa ciki zan dunga aike sa'i da lokaci insha Allah duk ranar da aka samu labarin inda iyayenta suke to sai a sanar damu, saboda haka yanzu ka tura akwai kaya mota akwashe muku saduwar alkairi." Maigari ya mike yana godiya sai washe hakora yake ta'b! shi zuwan yarinyar ma yayi masa amfani ga kudi ga kayan abinci.....Alaji Bawa ya mike a zabure! zai bi bayansu, da sauri maigari yasa mutane suka rirrikeshi! Allah sarki Alaji Bawa laushi yayi abunka da jikin girma sai kawai yayi lakas ya kwanta a gurin bacci ya daukeshi bakinsa yayi dagaje dagaje! da ti'kar goro. Asiya suna shiga mota ta sauke ajiyar zuciya, hankalinta ya kwanta tunda sun fito daga garin lafiya yansu babban abunda yafi damunta shine sanin ina mahaifinta ya shiga, duk abinda ya faru dashi tasan itace sila tinda ta kasa yi masa biyyaya, hawaye ta share tana jin wani irin kunci a cikin zuciyarta, babu shakka Gaje ta cutar mata da rayuwarta. Kallonsu Mommy takeyi ita da Farhana suna ta labarin abinda ya faru, Farhana tace"Daddy wallahi naji tsoro sosai kai Allah ya bashi lafiya tsoho dashi abin ya bani tausayi wallahi." Prof yace."Al'amarin akwai abun tausayi dama, amma kuma komai idan kun duba yana tafiya ne da kaddara kada ku dinga zargin ko Asiyatu ce tayi sanadiyar saka masa wannan lalurar, kaddara ce kawai kuma ita da tasan haka zata faru da bata aikata abinda ta aikata masa, da ace ta kasheshi ai gwara hakan da tayi Allah y rufa asiri." Asiya na kuka tace"Daddy wallahi tsautsayi ne nima ban dauka haka zata kasance ba Allah ubangiji ya bashi lafiya." Prof da Mommy suka amsa da ameen suna jin wani irin tausayinta, Mommy tace"Ko dan gaba Asiya kada ki sake kwantanta irin wannan abun ga wani hakan ba dai-dai bane kuma idan baki sani ba ki sani wannan gurin shine mahad'ar ransu kinga akwai matsala kenan ki kiyaye." Tace."Insha Allahu Mommy." Bayan kwana biyu da dawowarsu gida Asiya ta dan samu nutsuwa sai dai jefi jefe takan tuna mahaifinta ta share hawaye tayi masa adduar kan Allah ya tsareshi a duk inda yake..............A gajiye ta shigo gida misalin karfe biyu na rana yau alamis babu islamiyya sai boko palo ta zauna jikinta a sanye ta cire hijab din wuyanta ta zauna tana lumshe idonta, susa ta dinga yi tun a cikin mota al'amarin ya tsananta mata kwana biyu dan kusan kullum sai ciwon nata ya tashi, ganin palon babu kowa tasan Mommy na sama Farhana kuma bata dawo ba Prof da Hafeez suna ofis, sai kawai ta dan zage tazugen wandon makarantar jikinta ta zura hannunta a hankali ta soma sosawa tana lumshe idonta, duk sanda take susar wani irin dadi takeji sai bayan ta gama ne kuma sai zafi ya biyo baya............A hankali a hankali yake sakkowa daga sama cikin shirin fita dake ya dan tashi da ciwon kai ne shiyasa basu fita tare da Daddy ba yace zai sha magani ya kwanta idan yaji dama dama zai biyo bayansa, alhmdullhi ya samu sauki shiyasa ya shirya domin tafiya ofis din......Kallonta yake yi idanunta a rufe ruf! tana ta aikin susa duk ta bude kafafunta da alama ta manta a inda take......Ya karaso kusa da ita ya tsaya hannunsa duka cikin aljihu....Inuwar mutum da ta gani a kanta itace ta sanya ta bude idonta da sukayi mata nauyi sukayi jawur dasu.....Zabura! tayi tayi saurin zare hannunta tana kallonsa.....Ya d'ora kafarsa guda kan kujerar inda take zaune yana kallonta da murtukakkiyar fuska yace."Ke! kazama wai shin me kike sosawa ne a wandonki!? Kullum baki da aiki sai susa hannunki a wando saboda tsabar kazanta, da kin san kina bukatar mijin ki me yasa kika aikata abinda kikayi! sai kuma kizo mana gida kina mana susar wando dan ubanki! ko an fada miki nan gidan karuwai ne."!!! Jikinta na rawa tace"A'a bana sosa komai wallahi."! yace."Karya nayi miki."!? girgiza kanta ta shiga yi tana Allah Allah ya matsa daga kanta 'kamshin turaransa duk ya kashe mata jikinta...Yace."To maza ki nuna mun abinda ke miki 'kyaikyayi a wandon ki ni nasan da wanda zan had'aki ya sosa miki." Kuka ta soma yi tana girgiza masa kanta, Yace."Kamar ki har kin iya murd'ewa mutum Joystick saboda ta'addanci ke idan akayi miki haka zakiji dadi." ? Girgixa kanta ta shiga yi, Ya dan murza goshinsa yana kallon kirjinta da suka kumburo ta saman rigar ta dan botiran sun cire ya lashi le'bansa masu duhu! yace."Wallahi daga yau sai yau na sake ganinki kina susar nan sai na kamaki na 'bude ki kin nuna mun abinda kike sosawa na gaji da ganin wannan iskancin." Tana kuka tace" Nima ban san sanda nakeyi na mybe kuma bani da lafiya ne." Ya shiga watsa mata wani irin kallo yarinyar nan 'yar rainin hankali ce! Yace."Koma dai menene ke kika sani ni dai na fada miki na sake ganinki kina susa to sai kin nuna mun abunda kike sosawa." Daga kanta tayi alaman ta yarda.....Ya dauke kafarsa yana jan tsaki ya kama hanya zai fita.....Kallo tabishi dashi tana jin wata irin faduwar gaba, Yana dab da fita Prof ya shigo cikin gidan, kallon fuskarsa kawai ya nuna masa akwai tashin hankali, da sauri ya ja baya yana fadin "Daddy lafiya ka dawo gida da irin wannan lokacin gani na shirya zan tafi ofis din." Prof yayi masa wani irin kallo mara dad'i da nuni ga na gaji da al'amarinka. Hafeez ya sunkuyar da kansa kasa jikinsa yayi sanyi babu shakka akwai abinda ke faruwa. Prof ya shige ciki Yabi bayansa, Asiya tace"Daddy sannu da zuwa."Hannu kawai ya daga mata yace "Je ki kira min mommynku." Tana kokarin hawa sama Mommy ta sakko, ganin Prof din sai tasha jinin jikinta. Tana zama ya mika mata wayarsa ba tare da yace mata komai na, Mommy ta shiga duba wayar a take wani irin gumi ya tsinke mata cikin sauri ta dago kanta tana kallon Hafeez dake tsaye take yaga kwalla ta cika kwarmin idonta, da sauri! yaje yana le'ka wayar, gabansa yayi wani mummunan faduwa! shikkenan asirinsa ya tuno pictures dinsa ne da ashanty lokacin da suke rawa a Club suna tsotsar bakin junansa wasu hotonan sun nuna fitsara a fili dan akwai wanda suka nuna gashinan hannunsa kan d'uwawunta wani kuma kan nononta!! Murya na rawa Mommy tace"Hafezz wannan wace yarinya ce kuke wannan shaid'aicin da ita."!? Shuru yayi ya rasa me zaice shima gumi kawai yake yi......Mommy ta buga masa tsawa, Yace."Mommy kada kiyi kuka dan Allah." Pror yaji kamar ya sha'keshi! kallonsa kawai yayi ya girgiza kansa zuciyarsa nayi masa wani irin d'aci!! Mommy dai sai da hawayen nan suka zuba ta goge da sauri ta kalli Prof tace"Yallabai a ina ka samo wannan pictures din." Ya jima kafin yayi magana, yace."Ina zaune a ofis Alaji danliti yazo ya nuna mun, yace shima ya pictures din na yawo a media yarinyar da suka aikata hakan ce ta d'ora a Instagram da twttar." Mommy tace"Shikkenan kuma yansu bamu san irin zagin da muka sha ba daga bakin jama'a wanda suka sanmu da wanda basu sanmu ba, muna iya bakin kokarinmu Allah ya sani." Prof ya goge gumin goshinsa, yace ki kwantar da hankalinki na yanke hukunci na karshe." Ya kalli Hafeez din dake tsaye kamar gunki! Yace."Sati biyu kacal na baka ka fito da matar aure idan sattikan suka wuce baka fito da mata ba to zakaji daurin auranka da duk wacce nayi ra'ayi.'' Yana gama maganarsa ya mike ya bar gurin, Mommy ma tabi bayansa, Asiya dake tsaye itama simi simi ta bar gurin, duk taga abinda ke cikin wayar shiyasa jikinta yayi sanyi sosai tana jin wani irin masifaffan kishi na taso mata, yarinyar yabi da kallo cikin rashin kwarin jiki ya zube kan kujera yana janyo numfashi! da kyar! *Daga nan zuwa sati biyu na baka sati biyu ka fito da matar aure idan kuma baka fito da ita ba to zan had'a ka da duk wacce nayi ra'ayi* wannan maganar itace ke tayi masa amsa kuwwa a kunne...........! *TIR'KASHI!!!!!* *KADA KU MANTA A YANZU DAI BABU AJANDAR AURE A TARE DA HAFEEZ A LOKACIN DA YA NEMA BA'AYI MASA BA SAI YANZU DAMA YACE LOKACIN DA DADDY NASA YASO YAYI AURAN SHI KUMA A LOKACIN ZAI NUNA MASA IRIIN NASA TAURIN KAN! YANZU BABU AURE A TSARIN SA TUNDA YA GANE AKWAI INDA ZAIJE YA BIYA BUKATARSA AKWAI GAGARIMAR MATSALA MUTUKAR MAHAIFIN NASA YAYI MASA KUTSE A CIKIN RAYUWARSA, TA HANYAR HAD'ASHI AURE DA WACCE YAYI RA'AYI KAMAR YANDA YA FAD'A* *SHIN YA ZATA KASANCE IDAN BABA TINDE YA WARKE KADA KU MANTA DAI YA DAUKI ALKAWARI KAN SAI YA DAUKI FANSAR ABINDA ASIYA TAYI MASA* *BUKATAR ISHAK ZATA BIYA KAN ASIYA? SANNAN KUMA SHIN HAFEEZ ZAI AMINCE DA TSARIN MU'AMULANTAR MATAYEN SU DA SUKEYI KAMAR NASU KO KUWA? HAFEEZ ZAI AMINCEWA HUZAIFA DA ISHAK SU KUSANCI MATARSA KO KUWA?* *'DARI UKU KACAL TA BIYA MIKI BUKATA KI KARANTA BOOK DIN NAN CIKIN SALAMA DA KWANCIYAR HANKALI* *KADA KIKA SAKE A BAKI LABARIN WANNAN LITTAFIN AKWAI GWARAMA DA BADAKALA A GABA YANZU AKA FARA LABARIN YAR UWA KADA KI SAKE AYI BABU KE* _Muna Siyar da less manya da 'kananu materials manya da 'kananu atamfofi manya da 'kananu shaddodi masu kyau da 'karko mayafai 'yan yayi masu kyau da 'karko, muna bayar da sari kuma muna siyar da d'ai-d'ai ko ina muna tura kayanmu, Ina kuke masu sari daku masu siyan da'i -d'ai ku maza ku garzayo ku samu naku ba yabon kai ba kayanmu nada kyau! kuma ba kowa ke da irinsu ba, akwai sar'ko'ki da agogona ko wane iri idan kina bukatar sari ko siyan d'aya sai kiyi magana 'yar uwa anayi dakai gwara ba'ayi dakai! ko ina kike zamu tura miki kaya_ *Sai kunzo* *IDAN KIN SAN BA SIYAN BOOK ZAKIYI BA KADA KI DAUKI NUMBAR TA KIYI MIN WATA MAGANA* *GA MASU BUKATAR BOOK DIN ZASU TURA #300 TA WANNAN ACCONT DIN.......0542382124......BINTA UMAR GTBANK.......IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA TO KIYI MIN MAGANA DA WANNAN NUMBAR TA WSP......07084653262......ZAN FADA MIKI YANDA ZAKI BIYA* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA DA BUKATAR BOOK DIN TO ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS..........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE* *IDAN KINA BUKATAR SHIGA VIP GRUOP KIYI MIN MAGANA TA WSP DA WANNAN NUMBAR* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*