[9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* _Rubutawa_ _Ummyn Yusrah_ _Gajeren labari domin nishaɗi_ *Garin Jinjin* _Ƙaramar hukumar Mai Ludaya_ _Yammaci lis!_ _Fadar mai unguwa_ 1 Mai unguwa ne zaune kan kujerarsa, yayin da sauran jama ar fada ke kewaye da shi kan wata ƙatuwar tabarmar ana ta hira da mai da zance. Tunda suka doso fadar idon mai unguwa ke kanta. Kanta ɗauke da tiren talla, kunkumin nan an ɗaureshi tamau da gyale, ga fuskarka ta sha kwalliya da fauda buda jaka. Masifa kawai ta ke ta zubawa har bakinta na kumfa. "Karime Wallah gobe sai na ci uwar Indo, hegiya kucaka ta rasa wa za ta yi zance da shi sai Hamusu rabun raina! Ke alƙur an ji nake kamar na kifar da kayan tallar nan na je na ragargaji tsinanniya." "Yo ke Abuwa tun yaushe na ke gaya miki ki rabu da tsinanniya? Shegen kwashe-kwashe irin naki yasa ki ka kwaso mai ƙwatar miki masoyi. Yo ni ban isheki ƙawance ba ne?" Kallon sama da ƙasa ta yi mata ta keɓe baki "Taɓ! Kin manta ita ɗin ƴar waye? Ƴar gidan mai unguwa ce fa! Duk sati ranar juma'a sai mun je cin hinkafa gidansu. Ke ko sau ɗaya aka taɓa dafata gidanku. Shima albarkacin yayanku ya bi doguwar mota ya yi kabo-kabo zuwa burni ya auno muku ita." Cikin yanayin jin haushi ta ce "Shegiya kwaɗayayya, ai ke wallahi kin ji jiki. Dama tunda naga kin liƙe mata nasan da biyu ne, shiyasa duk ranar juma a kike korata idan na biyo miki yawon juma a. Har kike wani cewa sau ɗaya kika taɓa ci a gidan mu. Ke sau nawa na ci a gidanku?" "Ko sau ɗaya. Amma ai kina zuwa kwaɗayin tuwan biski da miyar ja." "Aikin banza! Abunda sai a share mako uku ko hudu ma ba ai ba, duk ranar ko da a ka yi ƴar hali ki ke yi mun, kin yi ta haɗe fuska kenan kuna kumbura kamar Fanken Dudu na bakin kasuwa." "Kam bala i! Nice Fanken Dudun Yasin sai na hau kan gandar bakinki na yi luguden leɓe, yar jakar ub..." Ta sauƙe tiren tallan dafaffiyar gyaɗar ta ta nufota gadan-gadan za ta cafko ta, da sauri ta matsa can gefe tana faɗin "Idan na tsaya kenan za ki yi luguden ko? Ai wallahi ke da Indo ne sai na faɗa mata kwaɗayi ki ke zuwa yi gidansu." _Ya a ci gaba?_😃 [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* _Rubutawa_ _Ummyn Yusrah_ _Godiya mai yawa da Addu'o'inku_ 3 "Kai! Kun raba mana hankali, maganar wa za mu ɗauka cikinku?" Ɗaya daga cikin jama ar ya daka musu tsawa. "Cewa ta yi Inno Mai Ƙosai." "Ƙarya ta ke yi, ita ta fara cewa Talatuwa mai Tafasa." Sarkin fada ya ce "Yau naga shashanci gurin yara. To ai abun alfahari ne a san mutum asan sana a tasa, naga duk faɗin unguwar nan da Inno Mai Ƙosai ake ƙiranta, ita kuma Talatuwa mai Tafasa. Duk ai sana ar tasu ta gado ne, shine har kuke husuma a kai don an ƙira sunansa?" Liman da ke zaune gefen hannun damar mai gari ya zuba ma yaran ido, ya kaɗe idonshi guɗa ɗaya na dama, yana nunasu da yatsa ƴar manuniya da ke hannun dama ya ce "Wai wannan kam ba Abuwa bace ƴar gidan Ilu mai Amalanke?" Sarkin fada ya amsa yana mai jijjiga kai kamar riƙaƙen gadangare "Ita ce fa! Ai fitinaniyar yarinya ce. Waccar kuma Karime ce ƴar gidan Mudi mai jaki." "Ikon Allah! To, mai Ilun yake jira da bai sallamata ba? Duba fa, duk ta ƙere sa anninta a girma." "Man liman ai yariyar saurin girma ne da ita kamar wani kaji da na gani a can Binni, cikin garin Jinjin, wai kajin turawa, can garin yahudu da nasara a ke kawo su, haka nan suke gaɓa-gaɓa. Girma ba hankali." "To, ai kam gara ya miƙata, tun kafin a fara sata cikin waƙa. Wannan ai abun kunya ne ma a gareshi. Ƴa ta kai har wannan lokacin." "Ai kam! Sa ar fa Huwaila ce ta wajena. Yanzu suke shiga shekara na sha uku, amma kaga ita Huwaila ai bata kai ta ba, nan da mako biyu ne ma za a kai ta ɗaki." "Ikon Allah!" Duk ka-ce-na-ce ɗin da ake Mai Unguwa nashi ido, don ya ma rasa ta cewa. Hasalima tunanin shi daban ne. "Ke me ya haɗa ku da Indo ƴar gidan Mai Unguwar?" Ɗago kai ta yi sai hawaye sharrrr! "Ba komai." "Da gani ba ki da gaskiya, domin duk wani mai saurin kuka rashin gaskiya ne da shi." "A a, dama... Dam...!" "Dama me? Ke Karime, me ya haɗa su da Indon?" Gyara zama ta yi, kamar dama jira take. Nan ta ɗauko zance tun daga tushe har zuwa ƙarshe. Salallami gurin ya ɗauka da. Sarkin fada ya ce "Ikon Allah! Ke kuma haka Allah ya yo ki da kwaɗayin hinkahwa? Yo in ba gidan Mai Unguwar ba, ina ake dafa ta? Shima dai albarkacin dangantakar da ke tsakaninsu da kansilan yankin Mai Auduga ne yake kawo mishi shi, wataran a turo ƴar Kwafarati wataran ƴar Hausa. Shine har za ki ɗarsa rayinki a kai? Ikon Allah." "Kwankwatsi ƙarya ta ke yi mini. Ba haka nan bane." "Rufe mana baki ja irar yarinya kawa..." Mai Unguwa ne ya katseshi yana faɗin "Ku barsu haka nan, ku kuma kada na kuma jin kun yi hayaniya a tsakaninku. Maza tashi ku tai." Jiki na rawa duk suka miƙe, kowa ta sunkuci kayan tallarta. Canza hanya su ka yi, sai da su ka daina hango fadar Mai Unguwa Abuwa ta ce "Yasin da an dokeni kanki zan rama." "Yo ko da ba a dokeki ɗin ba ai kin ɓare baki kamar ɓaure kina ta sharɓar kuka, Tuɓu luɓus kawai, mai kama da kazar masu jajayen kunnuwa." Tana kaiwa nan ta sa gudu. "Hegiya da ƙafa kamar Mazarin tsire. Za mu haɗu da dare a dandali." _Ummyn Yusrah_ [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* _Rubutawa_ _Ummyn Yusrah_ _To, ga ci gaban._ 2 "Idan kin fasa faɗa mata kin raina Talatuwa mai Tafasa!" "Ko kuma Inno mai Ƙosai ba!" "Kam bala in can! Innar tawa?" "Ita dai, ai uwa ba ta fi uwa ba." Har zuƙowa ta yi, itama Karime ta dire kwanon tallarta . "Zo mana! Kada ki ganki haka gaɓa-gaɓa ki ɗauka tsoron ki na ke, Aradu idan ban kwasheki na laftaki a ƙar ba." "Kai! Kai!! Kai!! Kai!!! Kunga ƴan nema, me ya haɗaku kuma?" Abuwa da takaici ya gama cikata, na rashin luguɗen leɓen da ba ta samu ta yi a kan gadar Bakin Karime ba ta ce. "Ƙiran sunan Inna ta ta yi." Tana faɗa tana hararar Karimen, kamar wacce idanunta zai zazzago ƙasa don harara. Ga wani ƙarin takaicin ma da ta ƙirata da sunan da ta fi tsana (Gaɓa-gaɓa.) "Ƙarya ta ke yi Baban Lanti. Ita ta fara ƙiran sunan uwata." "Ya isa, ku wuce mu je, tun ɗazu Mai unguwa ke hango hayaniyar da ku ke, da ya ke ku ba ku san zuru ba sai an tanka shine ku ka ci gaba ko? Za ku yi bayani ne." Jin Mai unguwa ne ya turo ƙiransu duk hanjin cikinsu ya kaɗa, tsoronsu ɗaya kada ya ƙira musu tsabga, don wannan baƙin mugun idan ya riƙe mutum da dorinar nan tashi ba ƙaramin jibgar mutum ya ke ba. Nan suka bar kayan tallar suka ranƙaya gaban mai unguwa. Ɗan aiken ya gurfana gaban Mai Unguwa yana mai dunƙule yatsun hannunshi na dama, yayin da ya ɗaga babbar yatsarshi yana mai jinjina wa Mai Unguwar yana faɗin "Ranka shi daɗe! ga yaran nan na taho da su." Ya ƙarashe maganar yana mai nuna su Abuwa da Karime da ke durƙushe can a ƙasa, duk sun yi tsuru-tsuru, kamar wanda su ka kar uwar Mai Unguwa. Sai da ya ɗan ɗau lokaci kafi ya fara magana cikin isa da mulki "Menene ya faru ku ke ta sa insa a tsakaninku tun ɗazu?" Shiru su ka yi ba amsa Tsawa mahukuncin fadar ya daka musu yana mai nuna su da miƙaƙƙiyar doninarshi ya ce, "Ba Magana a ke yi maku ba ne? Ko nan ma rashin kunyar za ku yi mana? Ahir ku kula, fada ku ke." "A...A...Ab!" "Ta ce me? Kin bi kin ishemu da in ina." "Cewa ta yi wai Indon gidan Mai Unguwa ta..." "Ƙarya ta ke kwarankwatsa. Sunan Innata ta ƙira." "Ƙarya ta ke, ita fa fara ƙiran sunan tawa uwar." Duk suka karaɗe wajen da hayaniya, da wannan ta ɗauko zance sai wannan ta katse, musamman ma Abuwa da ta ke tsoron tonon tonon asirinta. _Mu haɗe a gaba_ [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* _Rubutawa_ _Ummyn Yusrah_ _Tsangayar Marubuta da ke fuskar littafi ina miƙo jinjina da fatar alkairi gareku._ 4 Da ɗai-ɗai mutanen da ke fadar Mai Unguwa suke tafiya, har ya rage saura Mai Unguwa da sarkin fada. Sunkuyowa yayi da kanshi saitin fuskarka Sarkin fadan. "Kai! Wannan yarinyar ƴar gidan Ilu mai Amalanke nan fa kalar mu ce." Zaro ido ya yi, cike mamaki ya ce "Ranka shi daɗe! Wannan ai ta yi ƙarama, duka-duka nawa take." "Ka ji shashanci! Ita Abullen ba za ta zauna ba ne idan an kai ta ɗaki ko me ka ke nufi Kallamu?" "Ahh! Zama kai, daram ma kuwa. Kawai dai gani na yi ta ƙawar Indo ce ta wajenka kuma ƴar autar gidan ka." Ɗagowa ya yi, ya na ƙare ma Sarkin fada kallo "Ahir ka iyar ma bakinka. Ka je ka sami Ilun ka gaya mishi idan bai bada ita Abuwar ba ina ciki." "An gama ranka shi daɗe!" Har ya fara tafiya sai kuma ya dawo ya durƙusa yana jinjina "Amma yallaɓai kana ga ita yarinyar za ta yarda?" Murmusawa ya yi har sai da jajayen haƙoranshi da suka gama rinewa da goro suka bayyana. "Yarda kam ai ta riga ta yi an gama. Kai dai je ka sanar ma Ilun. Ita da ke zuwa cin hinkahwa duk sati, ta samu a sati sau biyu ko uku ai kaga ta more, domin da zarar an yi auren nan za a dawo da girka ta sau biyu ko uku a sati don in samu ta zauna." Shima dariyar ya yi ya ce "Kuma fa haka ne yallaɓai! Na wuce ma, da zarar na yi sallar magariba zan wuce can ɗin." "To, madalla. A dawo lafiya." "A ah! Yau kuma mutanen fadar Mai Unguwa ne a gidan namu?" Malam Ilu mai Amalanke ya faɗa lokacin da ya fito ƙofar gida bayan ɗan aike ya sanar ana nemanshi a ƙofar gida. "Ranka shi daɗe nine da magaribar fari." Juyawa ya yi ya kalli gabas da yamma kudu da arewa "In ce dai Sarkin fada makuwa ya yi ko?" "Makuwa kuma? Mai ka gani?" "Ji na yi ka ƙirani da sunan manya." "Au! Wai da na ce Ranka ya daɗe? Ai ka dace da hakan ne. Ko za mu samu waje na musamman, domin muhimmin saƙo ne ke tafe da ni." "To! Allah dai yasa lafiya ba?" "Lafiya lau ma, sai alkairi." "To Madalla. Ina zuwa." Gida ya shiga ya ɗauko tabarma ya shimfiɗa a ƙarƙashin bishiyar darbejiyan da ke can gaba da gidan. Bayan sun zauna, suka sake gaisawa gami da tambayar lafiyar iyalan da kuma harƙoƙinsu. Shiru ne ya gifta tsakani, kafin Sarkin fada ya katse shirun da faɗin. "Mai Unguwa ne ya tasani ya ce in zo takanas ta kano, ƙafa da ƙafa in sameka in sanar kuma in yi maka albishir cewar idan ba a yi ma Abulle miji ba yana riƙo. Ya gani yana so." Ilu ya faɗaɗa fara arsa ya ce "Ikon Allah! Banda Mai Unguwa da abunshi ai Abulle ƴar shi ce, ko an bada ita ya ce ya mata miji ai da gudu za a ƙarɓo ta. Wa ma zai ƙi haɗa zuri a da jinin Mai Unguwa? Wanne ɗa ne ko jika za a ba Abullen daga ciki?" "A ah! Ɗa ko jika kuma? Ba ko ɗaya daga ciki." "To, wane ne daga cikin dangin nashi?" Yana maganar fuskarshi fal annuri. "Da alama dai ba ka fahimci maganar tawa ba. Shi Mai Unguwar ne ya gani ya ke so, ya kuma buƙaci a bashi auren ita Abullen." Cak! Numfashin shi da tunaninshi ya tsaya na wucin gadi. Jin shirun da ya yi ba amsa yasa Sarkin fada gyaran murya ya ce "Malam Ilu na tare da ni kuwa?" "Ina tare da kai Sarkin fada." "To, me ka ce ne?" "Anya ko Abulle ta wajena ka ke magana kuwa?" "Ita ɗin ce dai, ai duk faɗin unguwar nan tamu ta Mai ludaya ita ake ƙira da Abulle ko Abuwa. Sai Zebu ƴar gidan Iro mai tumaki sai kuma Zinaru ƴar gidan Audu gurgu. Dukda sunayen nasu guda ne Zenabu amma ai da Inkiyar da ake ƙiran kowa." "To, amma ai ita Abuwar ba wata babba har can ba ne. Ina laifin Ma ƙaramin ɗan shi Mado da Indo ƙawar ita Abuwar ke bi ko dai wani daga cikin jikokinshi. Amma shi da kanshi ai ya girme mata nesa ba kusa ba." "To, shi aure ina ruwan hi da wani girma da tsufa ko shekaru? Zaman lafiya da kwanciyar hankali ake nema ai. Kada ka manta abunda ka ce, ba wanda zai ƙi haɗa zuri a da mai gari." 'Da ne da na fahimci maganar a baibai.' "Haka ne. Yanzu a yi haƙuri aɗan bani lokaci in tuntuɓi ƴan uwana da uwar ƴar da ita ƴar, duk abunda muka yanke zan zo har fadar Mai Unguwar in sanar muku." "To, ba damuwa. Muna jira, fatan ba za a ɗau lokaci mai tsawo ba?" "Da ikon Allah." "To, Allah yasa mu ji alheri. Na barka lafiya. A gaida Iyalan da ita Abullen a ce mai unguwa yana miƙo gaisuwa." _Ummyn Yusrah_ [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* _Ummyn yusrah_ _A ƙara yawan feji, a ƙara yawan feji. Duka-duka labarin fa bai wuce feji ɗaya ba idan na ƙara, ban son ya ƙare ne yasa na ke ta yi muku shi kaɗan-kaɗan domin nishaɗinku. Kawai a ci-gaba da gahi kawai._ 5 Naɗe tabarmar ya yi ya nufi cikin gida ranshi ɓace, tunda ya shiga gidan ma bai iya zama ba. Jingina ya yi da zanar da aka zagayeshi da ɗakin. Inno da ta fito daga daki hannunta ɗauke da tire na kwano, an jere kwano tuwo da miya na ci ka duba da kofin ruwa shima na ci ka duban akai tana ƙoƙarin ƙiran ƙanin Abulle ya zo ya kai ma Babansu waje ta ganshi tsaye ƙiƙam kamar wani soja. Da sauri ta sunkuya ta a jiye kayan abinci ta matso ta ɗan rage tsawo tana tambayeshi "Lafiya kuwa Malam ka shigo ko ƴar gyaran muryar nan babu?" Tsaki ya ja kafin ya bata amsa, murya cike da takaici "Ina fa lafiya Inno?" Karɓar tabarmar ta yi ta shimfida musu. "Malam ka zauna." Zaman ya yi domin yana da buƙatar yin hakan, wannan baƙon al amarin da ya kawo mishi ziyarar bazata yasa ya ji jikinshi duk a mace ba wani kuzari. Ji ya ke yi ma kamar ba ƙasusuwa a jikinshi. "Hankali dai Malam! Wannan irin zama haka kamar tumar ƴan bori ai sai ka ji rauni." "Yo, Inno ai na gode ma da na iya yin hakan. Gaba ɗaya fa ƙafafuwana yadda ki ka san an miƙe sanda haka na ke jinsu." Kare ma zaman da ya yi kallo ta yi, ya jingina bayan shi da bukkar ɗakin nasu, yayin da ya miƙe ƙafafuwan shi ƴan sirara masu kama da maburgin miya. "Niko in ce Malam tsere ya yi da agaribar farin nan dai ko, ko in ce lisha i tunda lokaci ya yi, don ma wajen namu sai ai sallar ma mutum bai ji ba." "In da tseren na yi ai da na ji daɗi da wannan mummunan labari da ya riskeni a farkon dare." Gyara zama ta yi "Tofa! Wannan wani irin labari ne haka? Allah yasa dai ba Baffa Jafaru na burni cikin garin Jinjin ba ne ya riga mu gidan gaskiya?" "Ji wani mugun alkaba i a nan? Wan nawa ki ke yi ma fatan mutuwa a wannan tsakani? To li ilafi tsakanin shi da ke." Tsuke baki ta yi ta koma gefe. Tsawon shuɗaɗun mintunan da ba su gaza goma ba ya ce "Habba! Ai hakan ma ba zai yiwu ba." Bayan ya gama jero tsaki ya furta hakan. "Malam wai me ke faruwa ne kam?" "Me ke faruwa ku? Bayan turo ssrkin fada da mai Unguwa ya yi kan cewar idan ba a yi ma Abulle miji ba yana kamu." Zaro ido waje ta yi ta haɗa hannayenta biyu ta sauƙe su kan ƙirjinta da ƙarfi tana faɗin "Na shiga uku! Wai wani Mai Unguwar?" "Mai Unguwa namu dai na mai ludaya." "Da kanshi ko dai ma jikinshi ko ɗan shi?" "To, wai Abuwa tamu ko dai Abu na gida Baba Ɗan Azumi da mijinta ya mutu kwanaki?" "Kin ji ki da wani batu! Ita Abullen nawa ke garemu?" "Ɗaya ke gare mu a gidan nan. Amma a dangi sun yi huɗu." "To, ta gidan nan yake magana." "Ji wani budurwar zuciya ana. Kuma shi tsofai-tsofai da shi, uban wane kakan wance ya rasa wa zai aura sai Abuwa? Ince dai ba ka amsa mishi ba." "Ina fa, na dai ce su bani nan da mako guda zan sanar da ƴan uwana. Duk hukuncin da aka yanke zan sanar da shi." "Gara hakan ai. Kafin nan cikin manemanta ta cire gwani sai a ce musu an ba da ita kawai." "Yauwa, hakan za a yi. Ku zauna da ita ki ji waye gwanin nata." "To, Malam." "Barin je in yi sallar lisha i, har an ida a masallaci ina nan." "To, a dawo lafiya." Ummyn yusrah [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HWA* _Ummyn Yusrah_ _7_ Duk suka nufi gida rai bai so haka ba, don basu samu sun raba raini da Abulle ba. A cewarsu tsoro ta ji tunda har ta k'i zuwa dandalin. Itama ta nufi gida rai b'ace na rashin samun biyar buk'atar ta, don ta gama tsara yadda za ta luguɗen tsuntsayen kan Karime, tunda ta gaggaya mata magana. Don tasan halin Karime da son gulma da neman shiga, duk yanda aka yi ta je ta sanar ma Indo abun da ya faru. Kuma tabbas tasan tare za su zo, gashi iya zaman da suka yi a hanyar zuwa dandali ba wak'iyarsu. Haka ta nufi gidan rai b'ace, tana shiga ba tare da sallama ba ta yanki hanyar bukkar d'akinta. "Ke Abulle zo nan." Juyowa ta yi tana tura baki, ta dawo ta durƙusa kusa da Inno ba tare da ta ce komai ba. "Me ya haɗaki da Indo 'yar gidan mai unguwa?" "Ba komai." "K'arya ki ke yi, za ki gayamin ko sai na sassab'a miki." Sake turo baki gaba ta yi tana mai matsawa baya, don tasan abu mai sauk'ine Inno ta sauk'e mata wannan busheshshen hannun nata. "Da gaske ba komai fa Inno." "Amma ai an ce kun je fad'a ne." "Lahhhh! In ji wani munafukin?" "In ji ni." "A a!" Tana mai gyad'a kai. "Ahir d'inki wallahi na kuma jin, ko a ce mun kin je gidan mai unguwa wallahi sai na tara miki gajiya. Ɓacemun da gani shashasha kawai." Wuf! Ta mik'e kamar tana jira, ta nufi d'aki zuciyarta fal tunanin me Inno take nufi da har zata hanata zuwa gidan mai unguwa? Kenan sun yi ban kwana da 'yar sati kenan ko kuwa? Taɓ! Da sake wai an ma mai zani ɗaya sata. Washegari Mai Unguwa da sarkin fada. Bayan 'yan zaman fadan sun watse ne mai unguwa ya ke tambayar Sarkin fadan. "Kai! Wai yaya ne zancenmu?" "Ai yallaɓai wannan fa inaga so yake ya hanamu. Bai wani bani k'wararren amsa ba, cewa ya yi in je zai zo har fadan idan sun zanta da shak'ik'anshi." Shafe fuskarshi ya yi, tare da tsefe gashin gemunshi da ya gama zamewa fari. "Ba komai, mu bishi a hankali, kasan 'yar shi ce. Mu da muke nema muke da hak'uri da k'ask'antar da kai. Yanzu dai abun da za a yi ita 'yarinyar zaka yi k'ok'arin shawo mana kanta." "Yallaɓoi shi da ke k'ark'ashinmu ai shi zai bimu ba mu za mu bishi ba." "Kai! Wa ya fad'a maka? Ai inda aka san darajar goro, nan ake nema masa ganye. Mu jira dai muji me Baba Ilun zai ce." Cike da mamaki sarkin fada ya d'ago kanshi, ya kafe 'yan k'ananan idanuwanshi ya sauk'esu kan mai unguwar ya ce, "Am fad'o daga dabino, an fad'a rijiya. Yallaɓoi Ilune fa!" "Eh, shi dai." "Ikon Allah! Wai na kwance ya fad'i." Cike da mamaki Mai Unguwa ya bishi da kallo yana fad'in, "Wanda ya cika, ai ya mallakeka kai da iyalanka. Tunda naga d'iyar shi ina so ai dole in girmamashi." Yana karkad'a kai ya ce "Um! Haka ne." Nan suka ci gaba da zantawa. Tafe take hannunta rik'e da ganyen rama, ta sayo a kasuwa za ta gida, sai ga Sarkin fada. Wangale baki ya yi yana fad'in, "A a! Kaga manyan mata, kalan manyan mutane. Ina aka fito kuma?" Cikin jin kunya ta durk'usa k'asa tana sunkuyar da kai, ta ce "Baba sarki ina wuni?" "Lafiya lau Abulle. Abulle ta mai unguwa." Kunya ce ta sake kamata jin ya k'irata da Abulle ta Mai Unguwa, tasan tsokanar ta yake kan yadda aka ritsasu a fadar Mai Unguwa. Mik'ewa ta yi za ta tafi, ya ce "Za a je gida ne?" "Eh." "To, a gaida Malam Ilu kuma ki fad'a mishi ina tuni da sak'onnan." "To." Kawai ta ce ta yi gaba. _Ummyn Yusrah_ [9/5, 10:15 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HWA* _Ummyn Yusrah_ _Ina mai baku hak'urin rashin jina da ku ka yi na 'yan kwanaki, jiki da jini._ _6_ "Kai Muntari, wai Ina Abulle ta yi ne tun ɗazu bata ɗau tallan Gyaɗar nan ta tafi dandali ba." "Inno, wata Abuwar? Sai dai ki tura mata da shi can. Don tun da aka ida sallar magariba suka fice ita da Saratun gidan Shawai wai za su dandali faɗa." "La ilaha illallahu! Faɗa dai? Ita da wa." "Da Indon gidan Mai Unguwa." "Na shiga magana! Yi maza ka je ka yo k'iranta tun kafin ta jawo mana magana a gari." A guje ya fice, ya d'au hanyar dandali. Abulle ne da Saratu ke tsaye a kan hanyar zuwa dandali, jiran isowar Indo kawai suke yi, sai dai shiru har yanzun ba alamar zuwansu da tawagarta. "Sarai! Anya ko Indo zata zo yau kuwa?" "Yo, nima shi nake tunani, har yanzu banga ɓullowarsu ba." "To, ya za a yi?" "Binta zamu yi har gida, mu yi kamar mun biyo mata zuwa dandali, idan ta fito mu tari mu tara mata gajiya, mu fitar mata da jini da majina, daga baka har hanci." "Ke! Kina hauka ko? To Yasin ba dani zaki je ba. Kin san wannan me sharb'eb'iyar dorinar idan ya rik'emu sai d'an burinmu." "Haka fa! To kawai mu yi jiranta." "Ke nifa ba Indon ce damuwata a yanzu ba." "Hamusu ko?" "Hamusu? Hamuso. Ni baya gabana ma yanzu, don naga idonshi rawa ya ke yi, baya tsayuwa waje guda. Yaje can su k'arata da Indon." "Kuma don iskanci shine kika tsaidamu kan hanya kamar wasu ram-santi na cikin garin Jinjin." Dariya Abuwa ta tuntsire da shi, har da durk'usawa k'asa tana fad'in. "Sarai meye kuma wani rafsanti?" Tsaki ta ja tana hararar Abuwar, "Matsalata da ke k'auyanci. Ram-santi ake cewa dallah. Lokacin zuwanmu cikin garin Jinjin bikin 'yar gidan Baffana Tallene muka wuce wasu da kayan sarki tsaye a kan kwalta suna bincike, dana tambayi su kuma su waye? nagansu da kaya daban ba irin na holis d'in da suke zuwa kama mai laifi bane a garin Mai ludaya ba. Shine aka ce mun wai Ram-santi sunansu." Cike da mamaki Abuwa ta ce, "Yo shi cikin Jinjin ai komai gani ake, Allah dai ya kai ni nima inga yarda take." "Amin dai, inda kuna da dangi a can." Kallon sama da k'asa gami da yatsina fusa ta bita da shi, "Mu a suwa da zamu yi dangi a birni? Ku da ke da dangi ai shiyasa naga kullum k'afarku na can, dad'in abun dai k'auye dai tushen birni ne, idan aka bi diddigi su Baffa a cikin k'auyen mai ludaya za a bankad'osu." Ta k'arashe maganar tana mai d'auke kanta daga kan Saratun. "Ikon Allah! Daga magana kuma sai cibi ya zama k'ari? To, Allah ya baki hak'uri. Kinga tafiyata." Ta k'arashe maganar tana kunce mayafinta da ta d'aure a k'ugunta shirin fad'a. "Sauk'a lafiya, agaida na gaba." Sak'e-sak'e tashiga ya azuciyarta, na takoma gida ne? Ko tawuce dandali? Idan kuma ta je dandalin ba wani burgewa abun za ta gani ba. Har ta juya zata yi gida, sai kuma ta sake juyowa ta nufi hanyar dandalin. Tana gab da isa ne ta ji an k'wala mata k'ira, ko bata juyo ba ta shaida muryar mai k'iran nata. Juyowa ta yi don ganin dalilin k'iran nata. Hasken farin watan da ya haskaka duniya ne, ya hasko mata fuskar Muntari da yake ta zuba haki dalilin gudun da ya ci. Tsaki ta ja kafin ta ce, "Lafiya ka ke k'wala min uwar k'ira a daren nan?" "Inno ce ta ce in zo in k'iraki, na manta na tsaya yin Langa dasu Sabitu. Sai da naga wucewar Saratu na tuna Aradu." "Jeka da Allah ina zuwa." Ta juya zata tafi. "Alk'ur an ta ce ki zo yanzu-yanzu." Juyowa ta yi ta zabga mishi harara sannan ta d'au hanyar gida. Indo da Karime da k'awayensu guda biyu da suka iso Dandalin tun da magribar fari suna jiran zuwan Abulle shiru ba labarinta, yasa suka fara taraddadin zuwan nata. "Karime anya ko Abulle zata zo?" "Tsaf zata zo in dai Abulle ce, kinsanta bata fashin zuwa dandali sai da dalili mai k'arfi, balle kuma yau a cike take, mu jira muga zuwanta." "Ke nifa tunda kika zo gida ki ka gayan zancen nan nake tsuma, Allah-Allah nake ta iso. Aradu in sunkuya na kwashi k'afarta ku bita da duka." "Ke, ni kayan tallana nake tunani a gidanku." "Yanzu kika tuno da tallan naki?" Inji d'aya k'awar tasu. "Lantana ai ina nan hankalina na can ne, tun fa rana dana fita ban koma gida ba." "Ni fa kunga tafiyata ma zan yi." "Ke Sahura ai dama ruwan ciki ne da ke." "Hu umm! Ku ji Indon nan? Kuma dare ya yi sai in yi ta zaman jiran gawon shanu ko? To, ba da ni ba. Sai kun zo." Ta juya ta yi tafiyar ta. Karime ta ce "Kai, mu tafinku muna, gobe za ta fito ne, sai mun kwashi 'yan kallo." Duk suka amsa da, "Mu je." _Ummyn Yusrah_ [9/11, 9:31 AM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *© UMMYN YUSRAH* *8* Da dare, Abulle suna zaune a kan tabarmar da suka shimfiɗa a ƙarƙashin barandar ɗakin Inno, suna cikin tuwon dare. Wani kafcecen loma Abullen ta yanko, ta iza shi cikin bakinta, ji ka ke ya ba da sautin "Muƙutt!" Sanadiyar haɗiyar da ta yi masa ba tare da ta tsaya taunawa ba. Haka ta yi ta wurga lomomin nan, tana haɗiɗɗiyar su, ba tare da ta tsaya ɓata lokaci wajen taune su ba. Ga zufar da ta gama wanke mata fuska, wanda har ɗiga ya ke a ƙasa. Inno da ke can gefe kan kujerar tsuguno, ta ɗago fitilar ƙwan da ke gefen ta ta haska fuskar Abullen, a daidai lokacin da ta yanko wani tiƙeken loma ta zazzaro idanuwanta waje masu kama da ƙwan zabbi, tana shirin wurgashi baka, ganin hasken fitilar yasa ta tsagaitawa tana mai kallon Innon da ta saki baki tana binta da idanuwanta kafin ta ce. "Ikon Allah! Wai ke a rayuwarki ba ki iya cin abinci cikin nutsuwa ba ne? Ki duba dai ki gani, ke ɗaya ke ci amma Allah-Allah ki ke ya ƙare, kamar wata mai warwaso kina tsoron kada a ƙwashe a barki hannu rabbana." Turo baki ta yi gaba ta yi tana faɗin, "Inno! Nifa a hankali na ke cikin abincina." "Hoɗijam! A hakan?" Ta tambayeta. "Eh." Ta bata amsa a taƙaice gami da wurga lomar da ta ke ta juya shi a hannunta. "Ummmhh! Lallai da aiki. Da alama gidan Sarkin noma za a wurgaki, domin wannan irin ci naki ba dai gidan rago ba." Ta faɗa a lokacin da ta ke ajiye fitilar da ke hannunta a ƙasa. "Shiyasa kullum ki ke ta hawa kamar farashi ai, daidai da sakan guda ba ki fatan bakin ki ya zauna shiru, ko da yaushe yana cikin motsi hayayam-hayayam. Ki sama ma kan ki lafiya tun wuri ina gaya miki, ba ko wani namiji ne zai iya da wannan cin naki ba ina gaya miki." Ta ƙarashe maganar tana mai ci gaba da saƙar hular da ta ke yi da ƙwarashi. "Inno! Shima fa cin nan lafiya ne aradu, idan mutum ba ya lafiya ina ya ga wani bakin cikin abinci, Allah duk randa aka kai ni gidan da ba abinci kullum gida zan riƙa turo da ƙwarya ta ana yi mun zubi, gara ma tun da wuri kada ku cire ƙwaryata ku barni a layi." Tana maganar ne tana lashe hannunta da ta gama damalmale shi da miya, tana gamawa ta kuma rarumo kwanon tuwon ta hau suɗewa. Inno ta ce, "Wannan ai an yi, ba a yi ba kenan. An sai da akuya, ta dawo kuma tana ci mana danga." Ba ta kula ta ba sai ma ci gaba da ta yi da suɗe kwanon, wanda baya buƙatar wani ruwa da omo wajen wanke shi, domin yawun Abullen ya wanke shi tas. "Ko da yake shi gwanin naki ma Hamusu rago ne, tunda tun zamanin ƙuruciya da aka bashi gwaji a kan kaza ya gaza riƙe ta, duk da yake ita ɗin dabba ce, ina kuma ga an bashi ɗan mutum?" "Taɓ! To ni me ruwana da wani Hamusu kuma? Can, su ƙarata da Indo ƴar gidan mai unguwa ni na wuce ajinsa" "Iyee! Zamani. Kukam dai yaran yau sai dai abarku, kina gabana ko kunya ba ki ji." "Yo, to Inno naga dai zancen nan ke ki ka fara yowa ita, ni ko na ɗora." "Uhmmm! Haka ne." "Inno shi kiwon kazar kuma ta me cece ne da na ji kin ce an ba shi Hamusun ya kasa riƙon ta?" Kallon ta ta yi, kafin ta ce, "Ita wannan kazar da ki ka ga ana ba duk wani ɗa namiji da ke wannan ƙauyen kiwo, ana bashi ne don gwajin yadda zai iya riƙe iyali. Idan aka ga yana kula da ita wannan kazar sosai, to a hankali za a bashi tunkiya, kinsan ita tunkiya uwar tamɓele ce, idan nan ma aka ga ba laifi, sai a yi mishi canji zuwa rago, da haka dai har zuwa kan saniya, idan aka ga ya iya kiwo to anan ne za a bashi mata. Idan kuma shiririta ya sa a gaba to sai dai a wurgashi gona kuma ya yi ta fama." Baki ta saki tana jin jawabin Inno har ta dire, ita ma ta jefo mata tambaya da faɗin, " Kuma Inno shi wannan gwagwarmayar duk mutum ɗin na ƙarami ne zai yi shi? Kuma dama ba su noma ne sai sun gaza riƙon dabba?" Ummyn yusrah [9/13, 4:57 PM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ *9* "Suna yi mana, idan yaro ya kai munzali kuma sai a yi mishi auren ladan noma." Cewar Inno. Keɓe baki Abullen ta yi ta ce, "Hu'umm! Sun ji daɗinsu." Shigowa gidan ya yi, ba ko sallama sai ma bambamin faɗa da ya ke ta yi har ya iso inda suke zaune, ya ja ya tsaya. Bayan shi ya yi ma masauƙi da garun ginin jar ƙasar da ke bayan shi, yana huci da huro iska daga cikin bakin shi, ya harɗe hannayeshi bisa ƙirjinshi yayin da ya ɗago ƙafarshi ɗaya ya dogare ta jikin garun, ɗayar kuma tana ajiye a ƙasa. "Barka da shigowa Malam! Yanzu na ke neman Muntari ya kai muku abincinku waje, baya nan, ina ga ya fita dandali wasa ne." Tsaki ya ja, ya ce, "Wa ke batun abinci kuma." "To, mai kuma ya faru? Na ji ka shigo kana ta bambamin faɗa." "Sarkin fada ne ya bi duk ya matsamin da zancen auren nan wallahi, ba dama ya ganni, duk ya bi ya hanani sukuni." Jin an ambaci Sarkin fada yasa Abulle ta zaburo tana faɗin, "Walle ɗazu ma ya aikoni, wai ko yana maka tuni ko me na dai manta." Inno ta galla mata harara, "Ina kuka haɗu da shi? Ko binshi fadar ki ka yi?" Zaro ido ta yi alamar tsoro, "Walle Inno a hanya muka haɗu, da na je sayo rama a kasuwa ina dawowa." "To, dama da kin ganshi kafin ya hangoki, ki maza ki sake hanya, kin ji na faɗa miki." "Inno!" "Innon gidanku." Ta yi mata daƙuwa da yatsunta biyar. "To, Malam yanzu meye abun yi?" Ƙarasowa ya yi, ya zauna a gefen tabarmar da Abullen ke zaune. Da sauri ta tashi ta koma ƙasa ta zauna. "Ni kaina na rasa ta cewa, da ina tunanin in ce mata cikin manemanta ta fidda gwani kawai, idan na je sai in sanar musu tana da gwaninta dama a hannu." Cewar Ilun mahaifin Abulle. "Hakan ma ya yi, ke cikin maneman naki waye gwaninki?" Ta jefa ma Abulle tambayar. "Ni... Ni... Ba kowa." "Ba kowa ki kace?" "Ba kowa Inno." "Umm! To kaji Malam. Da alama rabon mai unguwar ne." "Ke Inno! Hauka nake zan ɗau Abulle in ba sa ar kakana?" "To Malam, idan rabon shi ce fa?" "Bama rabon shi ba ne." "U um fa Malam! Kasan fa rabo ajali ne, ba mu san me Allah ke nufi kan hakan ba. Idan dai ita Abullen tana so ai shikennan." Jinjina kai ya yi, kafin ya ce, "Kuma fa kin kashen jiki, kince Allah a lamarin dole in saduda tunda ita ɗin ma bata da wani tsayayye." "Ke Abulle! Mai Unguwa ne ya turo Sarkin fada cewar yana son aurenki, me kika ce?" Sai yanzu ta gane kan wa suke zancen su, domin da duk a baibai take fuskantar zancen nasu. 'Wai yau ni Mai Unguwa ke son aure? Lallai ina da sa a.' Zancen zuciyarta kenan, kafin ta sake dulmuya wata duniyar tunanin. Hangota ta yi a gidan Mai Unguwa, an dire mata wani ƙaton kwanon kaya shaƙe da dafaffiyar shinkafa 'yar gwamnati mai santsi da miyar ja, ga kuma ƙatuwar kaza a kai, gefe kuma ga babban kwanon sha cike da sassanyar ruwan ranar ƙasa. Sake kallon ƙeta ta yi ma hinkahwar a karo na ba adadi, tana kuma tuna irin cin walaƙancin da za ta yi mishi. Sake ware ɗaurin zaninta ta yi don yayi sako-sako gudun kada cikin nata ya yi saurin cika, ta kalmashe ƙafafunta waje guda, ta zura hannunta ciki ta gauraya gefe guda, ta ciko hannunta ta kai shi zuwa bakinta. "Kingani ko Inno! Na gaya miki yarinyar nan ba son auren nan za ta yi ba, gashi ko amsa bata bamu ba." Maganar da mahaifinta ya yi, shi ya hanata jin ɗanɗanon hinkahwar da ta shaƙe hannunta da shi, maganar ce kuma ta yi silar dawo da ita daga duniyar tunanin da ta afka. Ta ji takaicin rashin ɗanɗana girkin, sai dai duk ranar da Allah ya kai damo ga harawa ba ƙaramin ɓarna za ta tafka ba, cin huce haushi za ta yi mishi. Murmushi ta yi, wanda sautinshi ya fito, "Kin gani ko Inno? Kuka fa ta ke yi, gara a janye maganar nan idan yaso a jira har ta samu gwani." Cewar Malam Ilu. Salallami Inno ta sanya tare da tafa hannayenta, ta iza ɗaya a haɓarta ɗayan kuma ta ɗago fitilar dake ajiye ta haska fuskar Abullen da shi. Kallo suka bita da shi, fuskokinsu fal mamaki. Madadin suga hawaye ya wanke fuskarta, murmushi ne ke ta bayyana a fuskarta, idanunta kuma a rufe. "Ke Abulle! Lafiyar ki kuwa?" Inno ta tambayeta. Da sauri ta buɗe idon ta sunkuyar da kai alamar kunya ganin yadda iyayen nata suka tsatstsareta da ido. A guje ta bar wajen ta nufi ɗakin kwananta, zuciyarta cike da farin cikin nesa ta kusan zuwa kusa. "Shikennan ai Malam, abu ya zo gidan sauƙi, alamu sun nuna ta yi na am da zancen. Sai ka yi maza ka sanar da su kai ma ka sami lafiya." "Ai kamar yanzu ma kuwa ba sai an kai gobe ba." "Sai kuma mu toshe kunnuwanmu, don za mu sha surutu gurin jama ar garin nan." "Yo Inno! Idan sun yi ma ai za su bari, da yardar yarinya ai aka yi, ba dole aka yi mata ba." "Haka ne kam." Ya miƙe yana faɗin, "Barin je in sanar ma Sarkin fadan." "To, a dawo lafiya." Tunda aka sanar ma Sarkin fada bai yi wata-wata ba, a daren ya isar ma Mai Unguwa. Washegari Mai Unguwa ya turo wakilanshi neman auren Abulle, da sadakinta dubu ɗari. Take aka sallama musu aka kuma sanya musu mako biyu mai zuwa aure. Kafin kyaftu da Bismillah, zance ya karaɗe illahirin unguwar su Abulle, ya karaɗe garin mai ludaya da ƙauyukan dake maƙwaftaka da su. Tsegumi ne kawai ke yawo ta ko ina, ga uwar Indo ma ta ɗaga hankali a gidan Mai Unguwa. "Kai dai ba ka taɓa rabo da abun kunya, ka rasa wacce za ka aura sai ɗiyar cikinka. Allah wadai wallahi, girma dai ya faɗi." Cewar Tabawa. Kallo Mai Unguwa ya bita da shi, kafin ya ce "Abun kunya? Ai mu gaba muka bashi ba baya ba, in dai ta nan hanyar ne. Yaya ina ƙoƙarin raya sunnar Ma aiki Rasulullahi, kuma ki ke neman jifata da wasu kalaman da basu dace ba?" Harara ta zabga mishi, "Wani raya sunnar? Ka rasa lokacin da zaka rayar sai da duk furfura ta gama baibaye ka, mutuwa yau ko gobe, amma ka ke wani ƙiran raya sunna." "Kai Tabawa! Ni da ke ba wanda ya san gawan fari, har yau ba za ki rage kishi ba. Yarinyar nan dai naga ƙarama ce, ba ruwanta, bata san komai ba. Don Allah ki sassauta kishin nan naki a kanta, kinga Lami kam ko a jikinta, bata wani nuna damuwar ta ba." Gyara zama ta yi ta ce, "Lami daban Tabawa daban. Yo ita dama ɗaga hankalin me za ta yi? Taga jiya taga yau, abu tun zamanin ƙuruciya kuke tare, tun auren saurayi da budurwa, ta riga ta ci lokacinta ai, tunda ko ni nan ma ta haifeni few da aniya, balle kuma wata can wai ita Abuwa. Har ka ke wani ƙirinta da yarinya, ƙarshen yarinta inga Inno ta sanya majanyi ta goyata a baya, ta kuma ɗauki bulumboti ta liƙa mata a baki sai in yarda." Ganin da gaske take, zancen nata ba na ƙare ba, yasa ya miƙe yana gyara zaman rawaninshi ya saiti hanyar fita yana faɗin, "Ni dai na faɗa miki, ki sa ma ranki salama ki yi fatan a zauna lafiya kawai don kin san bani son fitina a gidana." Yana kaiwa nan yasa kai ya fice. Tana huci tana faɗin, "Za ma ka dawo ne ka samen, da rawani kamar an naɗa gammo." Yana fita Indo ta faɗo ɗakin kamar wacce aka hankaɗo. Gallamata harara Tabawa ta yi tana faɗin, "Ba ki iya tafiya a hankali ba ko? Kin wani faɗomin ɗaki kamar wacce kare ya biyo." "Yi haƙuri Tabawa! Mutane ne suka ishen a gari, wai me yasa za a bar Baba ya auri waccar yarinyar? Wasu sunce don yana mai unguwa ne ya sa zai yi musu fin ƙarfi, wasu suce sayen ta yi yi, wasu ma cewa suke wa..." Tsawa ta daka mata, "Koma me suka ce, ba ke kike jajiɓo ta ba? Inda ba ki talla mishi ita ba ina zai ganta? Na ji kuma ance saurayinta da suka daɗe tare ya yi ƙaura ya dawo wajenki, kinga da ta tashi huce haushin ta sai ta huce kan mahaifinki. Kinga nan da kwanaki goma ta zama kihiyar uwarki kenan. Sai ki shirya tarbar sabuwar uwa." Ranta ɓace ta ce, "Allah ya satura! Ko rabin-rabin uwata ba ta kai ba, na san kuma kwaɗayin hinkahwa ne zai kawo ta Yasin za ta ga walaƙanci." Masifa ta rufeta da shi har bakin da ya gama rinewa da goro yana fidda kumfa, inda ana bada aron baki, da ba abun da zai hana Tabawa ta yo aro yau. Haushin kaza kenan. Ummyn Yusrah [9/22, 3:52 PM] Ummyn Yusrah🧕🏻: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* *(HWA)* _UMMYN YUSRAH_ _A ƙara haƙuri dai._ _10_ "Yi maza ki je gidan Goshi ta baki daddawar nan, kafin ki dawo na gama daka kukar sai a haɗa musu waje guda ki tafi, kinga rana na tafiya, kada dare ya riskeku, ga hanyar ba kyau ne da ita ba." Cewar Inno da take ta tiƙar busheshshen ganyen kukan da ta zuba a turmi, babban burin ta ta mai dashi gari. "To Inno!" Ta fice daga gidan ta nufi gidan Goshi mai Daddawa. "Abulle! Abulle!! Abulle!!!" Tun daga nesa yake ta ƙwala mata ƙira, sosai ta jishi ta ƙi juyawa Ganin ƙiran nashi ba na ƙare ba ne, yasa ta juyo a fusace tana hararar shi. "Wai lafiya kake yi min irin wannan ƙira kamar wani tsohon makaho ko wacce ta sace maka ɗan taure?" Ƙarasowa ya yi yana dariya ya ce, "Yo Abulle don na ƙwala miƙi ƙira haka ai ba laifi ba ne, tun ranar nake so mu haɗu mu tattauna amma kin ƙi kulani." Kallonshi take mai haɗe da harara, "Kam me zan saurareka? Cemaka aka yi ina da lokacinka? Ka dai san ni ba sa arka ba ce ko?" Cike da mamaki ya hangame baki kamar wani gaɓo yana kallonta kafin ya ce, "Nine fa" Ta yatsina fuska tana faɗin"Kaine wa?" "Hamusu rabun ran Abulle." Ya ƙarashe maganar cikin yanayin shauƙin so, har yana wani jijjiga jiki irin na jin daɗin nan. "Hamusun Indo dai! Ai ni yanzu na wuci saninka." "Ni ɗin?" "Kai ɗin fa." Ta juya ta fara tafiya, ko mai ta tuno sai kuma ta juyo ta yi mishi kallon sama da ƙasa. "A je a bi wani sarkin, ba da ni ba, auren talaka." Ta juya ta yi gaba. "Dakata! Kada ki yi ƙoƙarin jifana da duwatsu, ina mai shawartarki da ki adanasu ki gina gida da su domin nasan duk daren daɗewa zai yi miki amfani. Sannan kada ki yi kuskuren ƙonani da wuta domin da shi muke kunna fitilun da ke haskaka duk wani gida da ke faɗin kyauyen nan. Duk ranar da ki ka kuskura ki ka yi wannan gangancin ina mai tabbatar miki da cewar za ki dawwama cikin duhu." Yana kaiwa nan ya juya cikin ɓacin rai, "Matsalar ka ce wannan kuma, mayaudari kawai." Ta ja dogon tsaki ta wuce aikanta. "Kinsan da tafiya a gabanki amma ki ka sami waje ki ka zauna ko Abulle?" "Inno da na same ta a gida ai ba zan zauna ba, hegiyar yawo ne da Goshin nan kamar wacce ta ci ƙafar kare." "Ni tafi ki je ki shirya, shegen iyayin tsiya, kin san hanyar Mai Rangwangwan ba kyau ne da shi ba. Idan ku ka yi dare ku kuka sani, don ma mai babur ɗin ɗan garin ne da ya sauƙeki gida zai wuce da sai dai ki zauna sai gobe kuma." "Inno to a bari mana gobon na tafi." "Ungo nan." Ta watso mata yatsun hannunta biyar. "An ƙi a barwa goben. Dududu bikin saura kwana goma ne, idan kin je gidan Kawun naku Talle ki ka dawo Jinjin za mu tafi can gidan Kawun ku na burni, nan ma ki kwana biyu ki zo ki bi gidajen dangi na kurkusa suma ki musu sallama." Murna ne ya rufeta da ta ji batun tafiya Jinjin, itama za ta je burni ta ga yadda yake. Ruwa ta dauka a bokiti ta je ta watsa, tana fitowa ta sa kaya, yau ba batun kwalliya, kayanta kulle a cikin ɗankwali, sai wani ƙaramin buhu da aka sa mata dankalin hausa, kuka da daddawa. Sallama ta yi ma Inno, bayan ta gargaɗeta ta kuma ja mata kunnen ta kula ta kuma dawo akan lokaci. Muntari ya ɗaukar mata buhun kukan, suka nufi tasha wajen mai mashin ɗin da aka jima da yi mishi magana. Tana isa ba ɓata lokaci ya suri Abulle da wata mata suka ɗau hanya. Gam Abulle ta riƙe ƙarfen jikin mashin ɗin, domin idan ba haka ba a yadda suke cafke a kan hanyar nan za a iya tsintota a ƙasa idan aka daka wani tsallen. Taimakon ta ɗaya a tsakiya take, ba don haka ba, abun ba dama ne. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _11_ Kwananta biyu a Mai Rangwangwan ta dawo, cike da ɗoki da murnar zuwa birni. Har gida ta je ta sanar ma Sarai itama za ta birni gidan Baffanta Jafaru don haka gara a daina yi musu yanga, don ba a fi su tsumma ba, balle a baɗa musu ƙwarƙwata. Kwananta ɗaya a Mai ludaya washe gari suka ɗau haramar barin gari zuwa babban birnin Jinjin. Tsarabar 'yan Maraya daban da ta ƙauye, domin su ba daddawa ba kuka. Kabeji ce da kayan miya, sai kuma manyan kaji guda biyu. "Inno! Su mutanen Jinjin ɗin ba su cin kuka da daddawa ne? Naga nasu tsarabar daban da ta Mai Rangwangwan." Abulle ta tambayi Inno, ganin yadda aka bambanta tsarabarsu "Ke, tuwon girma ai miyarsa nama. Su can me za su yi da wani kuka da daddawa? Tuwon ma ai sai su shafe mako huɗu ma ko fiye da hakan ba su yi shi ba." Cikin mamaki da sakin baki ta ce, "To Inno me suke ci kuma?" "Ohho! Idan mun je kya gani." Tsuke bakinta ta yi har suka tattari shirginsu suka ɗau wanya. Kalle-kalle kam Abulle ta yi shi, mussaman ma da suka fara shigowa cikin birnin, ga kwalta shimfiɗe kamar tabarma, ƙarafunan wutar layi a tsaye kan hanya, jere reras kamar an dasa bishiyoyi. "Ikon Allah! Kayan burni daban da na ƙauye." Abulle ta faɗa a bayyane. Kallo wasu daga cikin mutanen cikin motan suka bita da shi, don daga dukkan alamu ita ɗin sabon shiga ce a zuwa Maraya. Amai ko ta yi shi yafi sau biyar, tun tana wanke jikinta da shi har aka bata tallafin leda. Har cikin tasha aka sauƙesu, anan ne fa taga tarin jama a, sai kaiwa da komowa a ke yi, kowa na sabgar gabanshi. Abulle kam banda kallo ba abun da ta sa a gaba. Idan Inno ta yi gaba, sai ta sake dawowa baya ta jawo hannun Abulle idan ta ga wani abun. Wani lokacin ma tuntuɓe take yi ko ta yi karo da wani abun tsabar kallo. Haka dai har suka tsare adaidaita zuwa unguwar su Baffa Jafarun. Nan ma dai mamakin ne cike da Abulle ganin mashin mai ƙafa uku, ga kuma gidaje harda masu hawa-hawa. Wani akan wani. 'Ikon Allah! Na zaune bai ga gari ba.' Zancen da Abulle ta yi a zuciyarta kenan. Tafiya dai-tafiya dai, har suka iso inda za su, suka biya mai adaidaita, ya ƙara wuta. Buga get ɗin ƙofar gidan suka yi, da sauri mai gadin ya zo ya buɗe musu ƙofar. Ganin Inno da ya yi ne yasa shi wangale baki yana faɗin, "Maraba lale da mutanen Mai ludaya. Yau kune a garin namu?" "Maraba dai Ɗayyabu! Gamu kamar an jefomu." "Sannunku, ku shiga mana." Ya faɗa yana ɗaukar wasu daga cikin kayan da suka zo da shi ya yi gaba. "Inno kin san shi ne?" "Farin sani ma kuwa, a Mai ludaya yake shima, ɗan gidan Malam Datta mai katako." "Au! Na ɗauka ai tsabar zuwan da kike ne ya sanki." "Yo ni yaushe ma nake zuwa? Rabon da garin nan tun ina goyon Muntari da muka zo yi ma Baffanku barka da dawowa daga Makka." Haka suka ƙarasa har cikin gidan Inno na yi mata bayani, ita kam inda za a shaƙeta ma ba ta san ɓaɓatun da Inno take yi ba, don gaba ɗaya hankalinta ya tafi ga kallon tsari da haɗuwar da gidan ya yi. Zuciyarta ke yi mata tambayar, 'Wai dama suna da dangi masu kuɗi kuma 'yan burni shine ba su taɓa zuwa ba?' Ita dai a saninta da wayonta sau biyu ma ta taɓa ganin Baffan nata a ƙauyensu, sai dai Babanta ya zo ko kuma ya yi musu aike daga nan. Suna ƙoƙarin shiga falon, Ɗayyabu kuma na fitowa. Ya ce, "Inno wannan kamar Abuwa?" "Ita ce." "Ikon Allah! Girma dai ba wuya, ta girma abunta." Ya faɗa yana riƙe haɓa. "Girma kam ai ba wuya Ɗayyabu, musamman ma na 'ya mace. Yanzu ma sallamar Baffanni take zata gidan aure." "Ikon Allah! Ashe dai zamu Mai ludaya kwanan nan." Ya wuce yane 'yan zantuttuka, su kuma suka shiga. Sanyi da ƙamhi ne ya ziyarci sassan jikinsu da hancinsu. Abu guda ne ya faɗo ma Abulle, tunowa da ta yi da ɗakin Inno mai tsamin ƙuli. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _12_ Tunowa da tayi da ɗakin Inno mai ɗankaren tsamin ƙuli da wasu tarkace. Da sallama suka ƙarasa cikin falon, Hajiya da yaranta biyu suna zaune kan kujera suna kallo. Da fara a Hajiya Sabuwa ke yi musu Maraba da zuwa, a ƙasa ƙaramar kafet ɗin da aka ɗaura kan tayis ɗin falon suka zube. Inno na amsa maraban da take yi musu yayin da imanin Abulle ya gama tafiya ga kallon kayan alantun da ke falon. 'Yan gaishe-gaishe suka yi, nan Hajiya Sabuwa ta shiga tambayar jama ar gida. Dungurin Abulle ta yi tana faɗin, "Kekam mene ne haka? Saki iya gaisuwa ba ne?" A firgice ta dawo hayyacinta, tana faɗin, "Ina kwana?" "Ita kika gani ma, ai ga manyan masu hankalin da suka fita ma basu iya gaisuwar ba balle kuma ita." Kallon su Inno suka yi suna mai daɗin, "Sannunku da zuwa. Kun zo lafiya?" Daga nan basu kuma ɗorawa ba, suka cigaba da abun da suke yi. Don su a zatonsu irin baƙi masu zuwa neman aikin nanne ne suka zo. "Ke Lubna! Tafi ki kawo ma baƙi ruwa, Kai kuma Afreen ka ɗauko musu lemo." Kowa ya tafi ɗauko abun da aka aike shi. 'Lubina! Ji wani suna kamar na makarai don Allah, ga wani ma wai a firij. Idan kana raye a duniya dai kaga abu.' Zancen zucin Abulle. "Inno ina fatan dai anan za a bar min ɗiyata ta kwana biyu ko?" Hajiya Sabuwa ta tambaya. "Hajiya ai itace silar zuwan tawa ma, nan zan barta ta kwana biyu, ni yau zan koma. Bikinta ya zo saura mako guda tazo yi muku sallama." "Amma ko kin kyauta wallahi, dama ba ta taɓa zuwa nan ba." "Hajiya, kuma ai ba zuwan kuke yi ba, ko yaran nan ma ku ɗan riƙa kai su suga dangi abun ya gagara, tayaya za su yi zumunci a tsakansu?" "Wallahi ni kaina ina son su je, sai dai makaranta ba su da lokaci, ga kuma halin Alhaji bayaso su matsa ko ina." "Makaranta ko ai ba zai hana su zumunci ba, naga ai suna ɗan samun hutu, ko mako guda suka je suka yi ai za su ga danginsu. Alhaji kam kada a yi mishi sharri, don kin san halin mazan namu idan ba ke mace kin sasu a hanya ba ba yadda za a yi su ce miki jeki, ke mace ke ya kamata ki riƙa yi masa nuni da hakan tunda ki ga shi ba mazauni ba ne." "Haka ne kam wallahi, don idan ka biye tasu zumuncin ma ba za a yi shi ba." "A to, gara dai a riƙa ƙoƙartawa. Kada wataran a haɗu a hanya ba a san juna ba." Dariya suka sa. "Inno ai ba za a yi haka ba ma, ga biki ya zo, sati za muyi a Mai ludaya da yaddar Allah." "Allah ya yaddar mana." "Amin dan na biyur Rahmanti." Ruwan gora mai sanyi aka kawo musu da kofi, ga kuma lemon kwalba, guda biyu mai ja da baƙi. "Ke Lubna zo ki zuba musu mana kin ja kin zauna, wannan ƙanwarki ce Zainab 'yar gidan Baffanku Ilu da mahaifiyarta." Hajiya ta ke gabatar ma yaran nata da su Abuwa. Kallo yarinyar ta bisu da shi, tana mai taɓe baki, na ganin yadda suke a jigace kuma wai ace danginsu, danginma na kut da kut! Ƙanin mahaifinta." Ruwan ta zuba musu a kofi, lemon kuma ta buɗe musu murafen ta koma ta zauna. Tunda aka dire musu, Abulle ke Allah-Allah lemon kwalbar nan ya ziyarci bakinta ya gangara maƙoshinta har ya zuwa tumbinta, don tana ganin mutane ranar kasuwan garinsu suna sha da burodi ko da bisko ko fanke. Ana buɗewa kuwa ta kai ma baƙin nan sura, kai kawai ta kafa ta fara kwanƙwaɗa. Zirrrr! Shine sautin da ta ji a kan harshenta, da sauri ta cire a bakin nata, sai da ta ɗan tsaya kafin ta kuma kwankwaɗa, ai ke ta cire a bakinta. Wani gyatsane ya taho mai haɗe da iska, gaba ɗaya ta yamutse fuska tamkar tsohuwar da ta shekara dari a duniya. Idanunta ya ciko da ƙwalla, azabar gas ya ratsa har cikin ƙwaƙwalwar kanta. "Wayyo Allah na shiga uku! Inno kaina, hancina." Shine abunda Abulle ke faɗi. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* *(HWA)* _Ummyn Yusrah_ _13_ "Sannu Zainab! Ai coke gas ce da ita, ba a yi mata shan garaje." Faɗin Hajiya Sabuwa, lokacin da ta taso tana riƙe Abuwar. Sauran yaran kuwa dariya suke ta zabga mata, Inno dake gefe sai jero mata sannu take. Wani sabon gyatsa ta sake yi mai tafe da hawaye, ta ce, "Yau naga bone! Inno wannan ko ba itace giyar nan da ake faɗa ba kuwa?" Gaba ɗaya suka sake sa dariya, idan ka ɗauke Inno daga cikin masu dariyar, don ita ta taɓa shan jar sau biyu a rayuwarta. "Ke wa ya faɗamiki wannan ne giyar? Tataccen lemo ne aka haɗa shi da wasu sinadaran." Lubna ta bata amsa. "Taɓ! To nikam ba zan kuma sha ba alƙur an. Wannan abun sai ta iya yin ajalin mutum. Fuuuuuu! Fa na ji ta hauro min aka." Duk suka sake sanya dariya. "Inno amma dai za ki yi sallar azahar ki ci abinci kafin ki tafi ko?" "Eh, kinsan motar garin namu ƙarfe biyu take tashi, kafin na yi sallan sai in wuce." "To, Allah ya kai mu." "Amin." Nan suka ci gaba da hirarsu, Afrin, Lubna da Abulle kuwa duk imanimsu na ga tibi. Ƙiran sallar azahar yasa duk suka watse daga falon, ɗakin sauƙar baƙi aka kai su Inno. Nan suka yi sallah, Abulle ko addu ar kirki babu ta miƙe ta nufi falon, don dama bata so aka dagata kan kallon ba. Ba kowa a falon, sai ƙaton tibin da ke ta faman aiki. Zama ta yi, ta kuma baza idanunta, kan kwalbar. Tashar turawa take kallo, wani tsamurarren bature sai zabga surutu yake, ita dai ba ji take ba nata ido. A hankali-a hankali taga yana ta tahowa yana kuma nuni da hannunshi tamkar mai nunata. Ganin yana shirin faso kwalbar ya fito ne yasa Abulle fasa wani uban ƙara. A kiɗime ta zabura, duk ta gigice ta rasa ina ta dosa? Ta ma rasa inda za ta gudu ta tsira kafin aljanin tibin ya gama fitowa ya risketa. Shiko gadan-gadan yake ƙara matsowa, a waige-waigen da take na neman yanyar tsira ne ta hango hanyar da zai sadata da ɗakunan gida. A guje ta ɗiba, yayin da mutanen gidan suma suka fito a guje don ganin ihun me take yi? Karo suka yi da Hajiya, take ta sake sake ihu ta hau roƙo da magiya gami da bada haƙuri. "Ke wai lafiyarki ne?" Hajiyar ta tambayeta, karkarwa ta shiga yi tana magiyar kada ya cutar da ita tasan shi namiji ne ya koma muryar mata, ta tuba ya mata rai, yau ma zata bar gidan ta fasa yin kwana biyun. Cike da mamaki Hajiya ta ce, "Abin Allah! Budurwa da ciki; Gwauro da yaye. Inno 'yar taki na tare da ƙwanƙwamai ne?" Ihu ta sake kurmawa tana faɗin, "Don Allah kada ku cutar da Inno! Tare za mu tattara duk mu tafi. Mun tuba ku yi mana rai, har abada ba zamu kuma Jinjin ba." Duk suka yi tsuru-tsuru suna kallon ikon Allah. "Ina fa wani ƙwanƙwamai! Rashin kunya ne kawai, mace ta auri mace." "Na shiga uku! Muryar Innon ma ɗaukewa ku ka yi." Ta sake zabura. Janyota Inno ta yi tana faɗin, "Wai wani iya shege ne haka ƙauri da kare? Mu ne zaki mayar aljannu? Zaki buɗe idanuwan ko sai na kwakwkwaɗa miki mari?" Da sauri ta ware idanunta, taga jama an gidan duk tsaye suna kallon ikon Allah. Juyawa ta yi ta kuma kallon tibin, sai taga wasu masu jajayen kunnuwane ke ta tiƙar rawa. 'Ikon Allah! Wai na kwance ya faɗi. Ko ina ma mutumin ya nufa ne ohho.' Ta tamabiyi zuciyarta. "Tambayar ki ake, me ya faru kike kurma mana ihu a cikin gida?" In ji Inno. "Wani mutumi na gani yana ta ƙoƙarin fitowa a cikin kwalbar can, yana ta zuwa inda nake." Duk suka sa dariyar ƙauyancin Abulle. "Kedai akwai shashanci, tayaya mutum zai fito daga cikin tibi har yakamaki? Sai kace wani almara? Allah ya shiryeki. Inno muje ku ci abinci kada ki rasa moto tunda kinƙi kwana, kuma kince ba za ki jira Alhajin ba." "Gaskiya kam!" Duk suka nufi wajen da aka tanadar musu abincin. 'Ikon Allah! Shima wajen cin abincin har da wajenshi? To ko dai nan ne aljannar duniyar?' Tana daɗi a zuciyarta tana ƙare ma wajen kallo. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* *(HWA)* _Ummyn Yusrah_ _Ku yi haƙuri, idona ke ciwo._ _14_ Tunda Abulle ta yi ido biyu da shinkafar da ke cikin kulan da ake ta zuzzubashi kan faranti take haɗiyar yawu, inda tare yawun nan ake a ƙiyasi zai iya kaiwa durom biyu. Iya zaƙuwa ta yi shi, sai dai sam Lubna bata lura da hakan ba, sai wani yanga take wajen zuba abincin, wani abun mamakin ma sai ɗigashi take tamkar za a ba yaron goye. Domin duka-duka baya wuce rabin farantin. Ganin abun nata ba na ƙare ba ne, yasa Abulle hangame baki alamar hamma. "To mai cikin zani! Idan kika haƙura yanzu za ki ci." Kallon Innon ta yi, ta kuma maida hankalinta kan ƙwaryar shinkafar, tana kuma jin kamar ta wafce kular ta afka miya ta hau loda ma cikin ta. "Ka ji Inno! Ai ta ma yi ƙoƙari, tun karin safe gashi har wajen daya da rabi ace bata buƙaci abinci ba? A kinsan da kamar wuya, idan ke kin iya daurewa ai ita da yaranta ba za ta iya ba." Kallon Lubna ta yi ta ce, "Ke ki yi ki ba mutane abinci da Allah. Kina abu kamar mai karyayyen hannu." Ta gama zubawa ta zuba miya da ya sha namar kaji, ga kuma ruwan lemo a kofuna da kuma ruwan gora duk a wajen. "Ina kos lo ɗin kuma? Ko gaya za mu ci abincin? Hajiya ta watso mata tambaya. Da sauri ta miƙe ta nufi hanyar kicin. 'Gosulo? Gaya? To duk wannan miya da ya rufe hinkahwar ta mene ne da za a ƙirashi da gaya? Mene ne kuma gosulon Ohho!' Abulle ta gama tunanin zuci, lokacin da ta kai hannunta cikin farantin abincin tana shirin gauraya. "A a, Zainab! Ba ga cokali a cikin abincin ba?" Hajiya ta tambayeta. "Hajiya da hannun yafi ɗebuwa ne, tattara ɗaya za ka yi ya cike hannu, cokali kuwa sai ka yi ta fafutukar tattarowa. Idan ma akai rashin sa a wajen juyewa a baki, duk sai ya zube, kinga ai gara in sa hannuna da Allah ya min ba hannun bature ba." Ta faɗa tana afa shinkafar a bakinta. "To, ki jira a kawo kos lo ɗin mana, ai ya fi daɗin ci da shi." 'Uhmm! Ke kika ma san wani gosulo. Ni burina in gama a ƙaramin.' Ta faɗa a zuciyarta. A fili kuma ta yi yaƙe, ta tsame hannu a farantin tana zaman jiran zuwan gosulo. Takaici ne ya rufe Abulle lokacin da gosuln ya iso. 'Shegen sanabe! A ƙira abu da kwaɗon kabeji an wani lauyance masa suna wai gosulo. Koda yake ma naga an yi haɗe-haɗe, barin ji shi kuma ya yake, don in shiga gidan Mai Unguwa da sabon salo da sabon tsari. Na shigo Jinjin na waye.' Wani murmushi ta yi, da ta tuno da gidan Sahibi Mai Unguwa. "Nikam in ce ko dai Abulle ta ƙoshi ne? Kin bar abinci kin tafi karanto wasiƙar jaki." Kallon Inno ta yi ba tare da ta amsa ta ba, ta hau laftar shinkafa da gosulo. Sosai ta ci, don abun ya kai mata karo. Ya mata daɗi sosai, sai da kowa ya tashi ya bar Abulle a wajen tana ta lodar abinci kamar jaka. Salamar da Inno suke yi da Hajiya Sabuwa ce ta ankarar da ita, ashe har tafiyar Innon ya tashi. Ba shiri ta baro wajen cin abincin ta taho gun su Innon. "Hajiya don Allah kada ku bar Abulle ta wuce sati biyu don akwai gidajen da za ta je sallama idan ta dawo." "In Sha Allahu ba za ta wuce kwanakin ba. Lado direba zai kawota har gida." "Allah ya kai mu lokacin." "To, Allah ya tsare hanya ya kaiku lafiya, sai mun zo kenan." Inno ta amsa da amin. Sai da suka iso bakin get, Ɗayyabu ya ɗauki kayan da Hajiyar ta sallameta da shi suka nufi bakin hanya neman abun hawar da zai kai ta tashe. Tana ta addu ar samun abun hawa don biyu ma ta wuce har da minti ishirin. Allah kiyaye ya yi mata, tare da alƙawarin zuwa ɗaurin Abulle idan lokacin ya zo. A lokacin da ta shige cikin adaidaita bayan ta mishi bayanin inda zai kai ta. **** Sai daf! Magriba Inno suka isa Mai Ludaya. Mai mashin na sauƙeta a ƙofar gida, yara na ganinta rugo da gudu, suna ihu da murnar dawowar Inno kamar wacce ta shekara da tafiya. 2019 *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* (*HWA*) _Ummyn Yusrah_ _Ina miƙo saƙon godiya a gareku masoyana na tayani murna lashe gasar gajerun labarai da muka yi, wanda labarina mai suna Rashin Kula ya zo na ɗaya. Na gode sosai Allah ya bar zumunci._ _Haɗin Allah da Hazaƙa banda kalmar da zan iya faɗi a gareku, sai dai fatan alkairi da ƙaruwar so da ƙaunar juna da kuma ƙarin haɗin kai da zaman lafiya. Na gode sosai._ _15_ Tura ƙofar gidan ta yi, yaran suka ɗebi kayan da ta zo da shi suka shigar ciki. "Inno! Inno!! Inno!!!" Da sauri ta ɗago daga sunkuyon da ta yi da niyyar cire ɗan kwaɗon da aka maƙala a jikin ƙofar. "Wannan wani irin ƙirane Muntari? Na hanaka irin hakan amma ba ka ji ko?" Ƙarasowa ya yi yana haki ya ce, "Inno kin san meye?" Bai jira amssrta ba ya ci gaba da faɗin, "Wai Hamusu ne ya ɓata, yau kwana uku kenan ba a ganshi ba." "Ya ɓata!" Ta faɗa cikin mamaki. "Ya ɓata fa ka ce?" "Eh, an nemeshi ba a sameshi ba." "Yo allura ne shi da za ai ɓata a rasashi? Wataƙila dai ya yi tafiya ne ba a sani ba dai ko?" "Wallahi ɓata ya yi Inno, Baba Marka ma fa yau sau biyu tana zuwa gidan nan bata samun kowa, ta ce idan kika dawo za ta zo." Cikin yanayi na jimami da zancen Muntari ta buɗe ƙofar ta shiga ɗakin, zuciyarta na ta tufka da warwara. Kaya kawai ta ajiye, ta fito ta nufi ɗakin girki don haɗa musu abincin dare, duk da kasancewar dare ya yi. Tana tsaka da haɗa wuta a murhu ta ji ƙarar buɗe ƙofar gidan tare da sallama. Fitowa ta yi, tare da amsawa. "Inna Talle ke ce tafe?" Inno ta tambaye tana mai isa gurin da tabarma ke jingine ta shimfida musu. Wacce aka ƙira da Inna Tallen ta amsa da, "Gani tafe, na taki sa a. Zuwana sau uku yau bakyanan wai kin je Jinjin." Ta faɗa tana ƙara dogara sandar da ke riƙe a hannunta na dama, na hagun kuma riƙe da kafaɗar yaron da ya rakota. "Bismillah Inna! ku zauna. Na je raka yarinyar nan ne gidan Baffanta, kinsan abun ya matso." Hawayen da ya gangaro a idanunta da ke rufe ta sanya hannunta na hagu ta goge. "Iro je ka yi wasa wajen yara, idan na gama zan yi ƙiranka mu koma." Ta faɗa ma ɗan jagoran tana, lokacin da ta zauna akan tabarmar. A guje ya ɗiba kamar dama jira yake yi. Zama Inno ta yi daga can gefe ta gaida Inna Tallen. Shiru ne ya ratsa wajen na ɗan lokaci kafin ta ce, "Sai kuma kika ji ɓatan Hamusu?" "I, ɗazu ina dawowa Muntari yake faɗamin. Na ɗauka ma shirmene kawai irin na yara." Sake share hawayen tayi, "Na rasa Hamusu! Na rasa shi, shine mun ɗa daya tilo da ke ɗawainiya da ni. Tunda aka ba Mai Unguwa yarinyar nan hankalinshi ya tashi, ya kasa sukuni." Ta tsagaita tana mai jan zuciya, da alamar jin ciwon lamarin. "Hamusu ya kasa samun nutsuwa, kullum cikin kuka yake. Babbar ma abum da ya dameshi ya ce sam Abulle ta ƙi ta tsaya ta saurareshi ya yi mata cikakken bayanin dalilil zuwanshi gurin 'yar gidan Mai Unguwa." Sake dakatawa ta yi, tana sheshsheƙar kuka. "Tun lokacin da ya zo min da zancen samun saɓaninsu da ita, da kuma ƙin saurareshi na ce ya bari in zo in yi muku bayani, amma ya hanani. Ya ce, yasan halin Abulle, fushi kawai ta ke yi, nan ba da jimawa ba za ta sauƙo." Shiru ta yi, da alama hutawa take yi, gami da jimamin lamarin. "Ikon Allah! Amma kuma Inna duk an bincika yanda ya kamata kuwa?" Bata bata amsar tambayar ta ba, sai ma ci gaba da ta yi da zancen ta. "Haka muka haƙura zuwa hucewar tata. Duk da haka yana ci-gaba da bibiyarta da bata haƙuri a duk inda suka haɗu. Ba mu kwatsam sai muka ji labarin cewar anba Mai Unguwa Abulle." Tunowa da ta yi na halin da ɗan nata ya shiga ne ya sanya ta kuma tsagaitawa. *** Tunda aka yi mata bayanin cewar ba wani mutumin da zai fito ta cikin akwatin talabijin ɗin ta saduda, don har hannunta aka iza bisa ƙwalbar don ta tabbatar. Idanunta da duk wani imani nata ta tattara ta bar ma kwalbar, masu jajayen kunnuwane ke ta kaiwa da komowa daga mazan har matan. Ita dai mamaki take yi, ganin kowa tsaf-tsaf! Tambayar kanta ma take anya ko suna yin dotti kuwa? Daga jikinsu har cikin garin nasu ba wani dauɗa kamar na garinsu. Zabura ta yi kamar an tsikareta, yayin da cikinta ya sake murɗawa a karo na ba adadi. Zuwa yanzu kam, ta kai magaryar tiƙewa domin kuwa ba abinda take buƙata baya ga kai ma banɗaki ziyara. A guje ta miƙe ta nufi ɗakin da aka saƙesu da Inno ɗazu, ta shige banɗaki. Yadda Allah ya taimaketa ma, ɗazu kafin tafiyar Inno ta gwada mata randar kashi, ba don haka ba, da sai dai ta sauƙeshi a ƙasa. Tana shiga ko kamar an buɗe bakin famfo, ga azabar murɗewar ciki. A iya tunaninta dai tasan ba ta ci komai ba. A wahale ta fito, hannunta na dama riƙe da ciki, na hagun kuma riƙe da ƙwanƙwasonta. Zuwa yanzu duk ta gama laushi, don ta zaga ba adadi. Tun tana tafiya da ƙafafunta har ta dawo yi a durƙushe, ta sake dawowa da rarrafe. Ƙarshe ma mazauni kawai ta nema a cikin banɗakin domin abun ya ci tura. 2019 *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* *NA* *Ummyn Yusrah* _Alhamdulillah! Ido da sauƙi, ras nake kallonku_ _16_ Jin shirun ya yi yawa ne yasa Hajiya Sabuwa ta tura Lubna ta dubota. Tun daga ƙofar ɗakin ta ji iska ya canza, tana kutsa kai ta ji hanjin cikinta ya fara hautsinewa, take zuciyarta ta tashi da gudu ta fice tana yunƙirin amai. Fallon ta dawo tana faɗin, "Mami! Kin ji ɗakin baƙin can kuwa? Wallahi wari kamar mushen jaki." Kallonta ta yi tana faɗin, "Me ya mutu a ciki to? Ina ita Zainab ɗin take." "Nikam ban ganta a ciki ba, ina sa kai na fito don wallahi mutum ya ɗauki tsawon lokaci a ciki zai iya tsintar kanshi a gadon asibiti." "Ungo nan." Ta ware yatsun hannunta alamar zagi. "Kuma shine ba za ki shiga ki duba ko lafiya ba, kin ji yanayin wajen amma ki ka barta anan?" Tsaki ta ja, ta miƙe. "Baki da hankali." Ɗakin ta nufa, tana kunna kai itama ta ci karo da baƙon al'amari. Ba shiri ta ware ɗankwalin da ke kanta ta toshe hancinta hannu bibbiyu. Ba Abulle babi dalilinta. 'Ina ta shiga? Warin meye haka a ɗakin nan?' Ta tambayi kanta. Har ta juya za ta fita sai kuma ta nufi banɗaki ko za ta ji motsinta. Jin shiru ba alamar motsin mutum yasa Hajiya kai hannu ta ƙwanƙwasa ƙofar. Shiru ta ji ba magana, ta sake ƙwanƙwasa shiru, kawai sai ta tura. Abulle ta hango zaune kan randar ta, duk jiki ba ƙwari. Yafutota ta yi da hannu, da yake idanunta na jikin ƙofar, duk bugawar nan da take tana jin ta, kawai kuzari ne bata da shi, duk gwuiwoyinta sun mutu. Da ƙyar ta samu ta iya miƙewa, da taimakon bango ta samu isowa kusa da Hajiyar. Riƙeta ta yi suka fito daga ɗakin gaba ɗaya, don tanason ta yi mata magana tana tsoron buɗe bakinta ta shaƙo wari, yanzun ma ba don ƙamshin turaren da ke jikin ɗankwalin ba da abun ba dama ne. Tana jin warin, amma ba can ba. Suna barin wajen ta buɗe hancin, ta ja wani dogon numfashi ta shaƙi iska mai ni'ima. "Sannu Zainab! Me ya sameki haka, lokaci ɗaya duk kin fita hayyacinki?" Suna tafiya tana tambayarta. Ba bakin magana Abulle, gayu yau ansha wuya, an yi ma gosulo ɗiban karen mahaukaciya shi kuma ya yi mata lalata. Kan kujerar falon ta yi mata masauƙi, tana yi mata sannu. "Hajiya wannan yarinyar anya ba asibiti za a kai ta ba kuwa? Dubi yadda idanunta ya dawo kamar na kifin nan Kafi zuru lokaci ɗaya." Cewar Afreen. "Ai banma san me ke damunta ba, daga zuwa yau kuma sai ciwo? Me ke damunki Zainab? Ki yi magana idan na zuwa asibiti ne sai a tafi." Hajiya ta tambayeta. "Mami! Anya ba Salad ɗin da ta ci bane da yawa wa ɓata mata ciki?" Kallo Abulle ta bi Lubna da shi mai haɗe da harara, da ƙyar take faɗin, "Ni...kuma? Yaushe na ci wani salati? Wancan wancan kwaɗon da kuka cikashi da wasu shirgin ya waren ciki. " Dariya suka sa dukansu. Iya wuya ta kai don haushi, wato ma ba tsusaya mata za su yi ba, dariya za su yi mata don rashin tausayi. Juya kai ta yi ta a basu baya. " Wai salati?" Ta sa dariya. "Salad fa aka ce miki, ba salati ba." 'Koma dai mene ne ku kusa sani.' "Ke Lubna ya isheki! Yanzu me ke damunki Zainab?" "Ba komai." Ta faɗa ba tare da ta juyo ba. "Riƙeta Lubna ku je ɗakinki, ta yi wanka, Afreen ya kaiku Jinjin sifeshiyal hosfitan ko ruwa ne sai su ɗaura mata su bata magani ko zata ɗan ji ƙarfin jikinta." "Mami! Ɗakina kuma? Kada ta je ta..." "Zan ɗaura miki mari. Riƙeta ku je. Kai ƙaramin Asabe ta je ta tsaftace can ɗakin." Haka ta kamata tana yatsina fuska suka tafi. *** Inna Talle ta cigaba da magana. "Ya shiga tashin hankali mara iyaka, haka na yi ta bashi baki ina bashi haƙuri kan cewar idan Allah ya nufa Abulle matarshi ce sai ƙaddara ta bashi ita, idan kuma ba matarshi bace ya yi haƙuri tun can haka Allah ya nufa, ya yi addu'ar zaɓi na gari. Ganin yadda nima na shiga damuwa a 'yan tsakanin nan ne yasa ya daina tunƙarata da zancen, ganin haka yasa nima na kwantar da hankali na." Shiru ya sake ratsa tsakani. Inno kan na tsugunne kan ƙafafunta da suka gama yi mata tsami, ta kasa magana sai sauraro kawai. "Lokacin da Abulle ta fara zaga gidajen sallamar tafiya gidan aure lokacin ne muka tabbatar da ta fita rabonmu. Ranar ya zo ya ce mun sun haɗu da Abulle ta faɗa mishi maganganu marasa daɗi, ya kuma samu labarin tafiyarta Rangwangwan a ranar tunda ya fita ban ƙara jin motsin shi ba har yau, duk wanda na tambaya sai ya ce ya ganshi da kaya a leda ya ce za shi garin Dagal aike wajen kawunshi. Ashe tafiyar kenan..." Kuka ya ci ƙarfinta. "Shi ɗaya ke gareni, shike tallafamin saboda lalurata ta rashin ido, yau anwayi gari na rasashi, kukuma taku ɗiyar tana tare da ku..." Ta sake rushewa da kuka. Hamusu ya yi hijira a soyayya. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Gwiwoyina a ƙasa, hannayena bisa kunnuwana ina neman afwa._ _17_ "Inna Talle ki yi haƙuri! Bansan komai game da wannan lamari ba, kwanaki dai Muntari ya faɗamin Abulle sun tafi faɗa a dandali ita da Indo, tun a lokacin na sa aka ƙirata na haneta da hakan. Ta kuma yi min bayanin dalilin faɗan cewar shi Hamusun yana zuwa gurinta, tun daga lokacin ban kuma bi ta kan zancen ba. Ko auren nan da za a yi mata da amincewar ta ba wai dole za a yi mata ba." Sharce majina Inna Talle ta yi daga hancinta, bakin zaninta ta sa ta goggoge hancin kafin ta ce, "Allah ya sauwaƙe wahala, tsohuwa taga kwananta ya yi kusa. Ba nema tsakanin Indo da Hamusu, shi ɗin dai wakili ne kawai. Wanda aka cuta, ai shi ake ba haƙuri. Haƙuri kam ai ya zama dole." "Wakili? Na wa kenan Inna?" "Ɗan gidan kawunshi Saluhu dake Dagal ne ya ganta yake kamu, to shine fa shi Hamusun ke isar mata da saƙo idan ya je garin. Ya yi ƙoƙarin ya sanar ma ita Abullen amma ta ƙi sauraronshi." Haɓa Inno ta kama cike da mamaki da saurin yanke hukunci irin na Abullen. "Amma ko Abulle ta yi wauta! Ban san dalilinta na ƙin tsayawa ta saurari jawabin Hamusun ba." "Mai hankali ai shi kan ba kaza ruwa da damina." "Karuwa ai bata kiwon kaza. Ki yi haƙuri za mu magantu da mahaifin nata idan ya dawo, da yardar Allah kuma za mu tayaki cigiyarshi. Ko ba Abulle ai Hamusu ɗa ne a wajenmu." Sandarta ta fara lalube, tana ɗauka ta muƙe tana faɗin, "Uhmmm! Allah ya jishshemu alheri." "Amun. Inno ta amsa. Har ƙofar gida ta yi ma Inna Talle jagora, anan ta ƙira ɗan rakiyar nata ya zo suka tafi, itama ta koma ta cigaba da aikinta. Ba dare bayan dawowar Malam Ilu, ya yi mata banganjiya da tambayar yadda ta baro mutanen Jinjin da Yayanshi, ta sanar da shi duk suna lafiya, amma basu gamu da Yayan ba ya tafi aiki. Ta faɗa mishi irin sha tara ta arziƙin da Hajiya ta yi mata. Godiya ya yi gami da yaba ma matar Yayan nashi na halin ƙwarai da son kyautata ma jama'a. "Ohh! Niko Malam ka ji wani batu kuma?" Ta faɗa tana kama haɓa. Kallonta ya yi, ya ce, "Batu akan me fa?" "Batun ɓatan Hamusu ɗan gidan Inna Talle jikan Yawale mai Gurguzu." "I, wallahi, duk gari ya ɗauka. Ko ina ka gifta zancen ake." "Allah sarki! Na tausaya ma halin da Inna ke ciki. Ɗazu bayan dawowata har ta ɗan ɗau lokaci ma anan muna magana kan Abulle da shi Hamusun." "Allah sarki! Abun ai akwai al ajabi, yaro dare ɗaya ya ɓace ɓat! Kamar wanda aka yi ma kurciya? Wannan abu da mamaki." "Wallahi kuwa, ta sanar mun da komai, ashe shi Hamusun ba neman 'yar gidan Mai Unguwa yake ba, ɗan gidan kawunshi yake zuwa ma aike wurinta, da Abulle tagansu tare shine fa ta hau dokin zuciya, ya yi ƙoƙarin sanar da ita gaskiyar magana ta ƙi bashi haɗin kai. Da ya bita ta ƙi sauraronshi shine ya gudu wai ba zai iya ganin auren Abulle da wani ba." "Ka ji shirmen banza! Duk tarin matan garin nan na Mai Ludaya ba zai zaɓi wata ba sai Abuwa? Wannan ai shashanci ne, dama can ya yi niyyar shiga bariki ne kawai. Ba wai rashin auren nata ba. Bana ma son sake jin zancen daga bakinki, tun wuri ki haƙa rami anan ki birne shi, kafin gari ya ɗauka." "To, amma Malam maihaifiyar shi yaron fa? Tana cikin wani..." "Dakata don Allah!" Ya faɗa yana daga mata hannu. "Na faɗa miki ki yi gum da bakinki, ki tayata da addu'a Allah ya bayyanashi kawai. Domin matuƙar zancen nan ya baza gari to, ina mai tabbatar miki fita ma sai ya gagaremu, ki barmu dai mu ji da wanda ake yi mana yanzun muka toshe kunnuwanmu." Cikin marairaice fuska ta ce, "Shi ke nan. Allah ya bayyana shi, ya yi mishi zaɓi da mafi alkairi." "Faƙat! Amin." Ya kaɗe 'yar shararshi ya fice daga gidan. **** _Fadar Mai Unguwa_ "Sarkin fada! Yanzu ya kake ganin za a tsara lamarin bikin nan? So nake a yi biki na kece raini." Kallon Mai Unguwa ya yi, da yake ta mamula gole a bakinshi. "Ranka shi daɗe! Ai kasa a je cikin garin Jinjin a lafto shinkafa a zo a dafa a bi gida-gida ana rabashi, matuƙar akayi hakan to fa ina mai tabbatar maka da cewar wannan biki zai kafa tarihi matuƙa a cikin garin nan da kewayenshi." Wangale baki ya yi, irin a dole yana dariya ɗin nan, ga haƙoran gaba, sama da ƙasa guda huɗu duk babu. "Sarkin fada shi yasa nake son zama da kai. Ga ka ƙarami sai iya tsari wallahi." "Ai Ranka shi daɗe, na fi kowa san kasance a zaman fadar nan." Murmushi Mai Unguwa ya yi, ya ce, "Zama waje uku suna da amfani. Zama a makaranta, zama a mahauta, da zama a fada. Zama a makaranta ko ba ka yi karatu ba, idan ak yi abun addini ka ji. A mahauta in an fiɗa, ko fince ka yi. A fada kuwa za ka ƙaru da maganar tsofaffi don nan ne matattarar magana." "Gaskiya ne! Ina ƙaruwa kam sosai a fadar nan." Nan suka ci gaba da tattaunawa. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _UMMYN YUSRAH_ _18_ Leda biyu na ruwa Abulle ta sha da kuma allurai biyu bayan dogun artabu da akasha wajen sa mata ruwan da tsira mata alluran. Ba kunya ba tsoron Allah ta zage ta yi ta zabga kururuwa tamkar wacce za a zare ma rai. Sai wajen ƙarfe ɗaya saura na dare aka sallemesu. Shima dalilin matsawar da Lubna ta yi ma likitan, don ba zata iya kwana a asibitin ba. Itama Abulle tunda ruwa ya ratsata, jijiyoyin jikinta ya saki, ta ji ta ƙagu su koma gida, don ta gaji da kwanciya a gado mai tafiya. Ko yaya aka ɗan muskuta sai kaga gadon ya matsa. Kamar ba ita ce ɗazu aka sha gwagwarmaya wajen sanya ruwan ba. Gari ya yi shiru, kai ka ce ba wani ɗan adam da ya wuni yana zirga-zirga a wajen. Tituna ma ɗai-ɗaikun ababen hawa ne ke giftawa. Ba ka jin motsin komai sai kukan kwaɗi da wasu ƙwarin. Ƙofofin gidaje ma a rufe, haka ma shaguna, sai dai a wasu ƙofofin gidajen da yake mallakin gidan almajirai, zaka iya hangosu shimfiɗe kan tabarma suna ta sheƙa barci. Wasu kuma a ƙofar shagunan mutane. Tunda suka fara tafiya waje ɗaya ne kawai suka ga mai shayi, da wasu tsirarun mutane da basu wuce uku ba. Dare kenan! Mahutar bawa. Kowa ya bar gida-gida ya barshi. Hakan ce ta kasance. Hamusu ma yana ɗaya daga cikin mutanen da ke ƙawance a ƙofar wani shago, a tsakiyar bencin da aka tokare ƙofar shagon bayan an rufeshi da kwaɗo. *** Tun ranar da suka yi sa'insa da Abulle ya tattara kayanshi ya bar mahaifarshi, ya fita neman kuɗi don huce takaicin abunda Abulle ta yi mishi. Yana da yaƙinin kuɗi ta bi, shi yasa ta amince da auren Mai Unguwa. Inda yana da su da yanzu suna tare. Ya shigo cikin garin Jinjin ba tare da yasan kowa ba, hasalima karo na farko kenan a tarihin rayuwarshi da ya taɓa zuwa. Sosai yaga bambanci da garinsu. Kowa a nan harƙar gabanshi yake yi, idan zaka wuni baka sami ɗigon ruwa ka jiƙa maƙoshinka ba, ba mai baka, basu damu da kai ɗin baƙo ba ne, ya saba gani a garinsu idan aka yi baƙo an rinƙa ina asaka da shi kenan. Kwananshi biyu yana garari a cikin tasha, ganin 'yan kuɗaɗenshi na shirin gangarawa su barshi, yasa ya nemi mafita daga wajen wani da suke kwana kullum a tsakiyar motocin da ake ajesu idan dare ya yi. Gauta yake kasawa a tire ya yi ta yawo kan tituna yana sayarwa. Shine sana ar da Hamusu ya fara yi. Yau kwananshi biyu kenan da fara sana ar, sai dai yanzu ya bar cikin tasha ya dawo kwana ƙofar wani shago. Har ya fara tunanin canza sana ar, domin yau ba ƙaramin galabaita ya yi da zafin rana ba. Sai dai kuma ba ya da wani ishashshen jarin da zai kama wani sana ar. Juyi kawai yake yi, sam! Barci ya ƙi ya ɗaukeshi sai ma wasiƙar jakin da yake ta karanta. "Allah sarki Inna ta! Ko yanzu a wani hali kike? Ki yi haƙuri na tafi na barki ba tare da izininki ba, na tafi na barki ba tare da tunanin lalular makanta da kike fama da shi ba. Ban yi hakan domin in sanya ki a damuwa ba, sai don sama wa zuciyata mafita, Inna ba zan iya zama cikin Mai ludaya a ɗaura wa macen da nake so aure da wani ba, zuciyata ba zata gaza ganin hakan ba Inna! Ki fahimceni, zan dawo gareki nan ba da daɗewa ba, zan dawo, zan dawo..." Maganar da yake yi kenan a hankali cikin sautin kuka, zuciyarshi kuma na ƙuna. *** Barci sosai Abulle ta sha akan lafiyyayen gadon da ya sha shimfiɗi, ba kamar gadonta da aka yi shi da yayi aka ɗinkeshi da buhu ba. "Ke wai ba za ki tashi ba ne?" Lubna ta faɗa tana ɗaka mata duka a sangalalin ƙafafunta. Tashi ta yi tana miƙa, tana hararar Lubnan da gefen ido, don ba ta so tashi yanzu ba. "Lafiya kika tsareni da ido? Ko baki gama warwarewa ba ne?" 'Wannan baiwar Allah akwai buhun masifa! Inaga da ita ke da gidan ma ko wuni ɗaya ba zan yi ba.' Ta faɗa a zuciyarta, a fili kuma ta ce, "Ras nake! Allah na tuba ma ai inaga na fiki lafiya." Ta ƙarashe maganar tana sauƙa daga kan gadon. Zaro ido Lubna ta yi, "Me kika ce?" Ta tambayeta. "Cewa na yi, ai yanzu ko garin nan aka ce in zagaye da gudu zan iya." Tsaki ta yi, ta koma ta kwanta a cikin kujerar da ke cikin ɗakin. "Ina kuma za ki je? Banɗaki za ki shiga, akwai sabon burosh da makilin na ajiye miki." 'Buroshi? Makel? Su kuma suwaye hakan?' Ta tambayi zuciyarta yayin da ta nufi ƙofar banɗakin. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Na_ _Ummyn Yusrah_ _Hhhhhh! Sosai Abulle ta ce in miƙo gaisuwarta ga masoyanta, musamman,_ _Abu Hisham_ _Yayana Almu_ _Kamala Minna_ _Beauty Queen_ _Mai Dambu_ _Heenart Nijar_ _Queen Beelart_ _19_ Duk dube-dubenta ta yi bata fahimci komai ba, don banɗakin cike yake da shirgi. Taɓe baki ta yi, ta ce, "Shima banɗaki sai an yi mishi jere tsabar samun waje. Wannan kwalayen idan na samu na jeresu a kan sif ɗina ba ƙaramin kyauwu za su yi ba." Ta ƙarashe maganar tana murmushi. "Ce miki a kayi ana magana a toilet ne kam." Daga can ta ji Lubna na mata magani. "Ohho miki kuma! Ni na san wani tulat ne." Ta faɗa a hankali, sannan ta ɗauro alwala ta fito. "Kawai ki goge baki ki yi alwala shine ki ka zauna surutu?" Turo baki ta yi da yatsina fuska, haɗe da hararar ta ta gefe don ta tsani masifa, da alama wannan mai farar fuska kamar shinkafar ba za su zauna inuwa ɗaya da ita ba. "Yo, naga dai alwalar haɗe take da wanke baki, kuma duk na yi. Sallah zan yi yanzu." "Kina nufin ba ki yi burosh ɗin ba?" Yadda ta zaburo kai ka ce ashariya Abullen ta yi mata "Magana ta gaskiya ma ni ban sansu ba." Ta bata amsa tana sanya hijabin da ta gani kan sallayar ta tada iƙama. Shiru ta yi ganin ta fara sallah, zuciyarta cike da tunanin wai ba tasan man goge baki ba. To su da me suke wanke bakin? "Ina kwana?" Shine kalmar da ya katse mata tunanin. Kallonta ta yi, tana naɗe hijabin. "Ba dai kin idar da sallar ba ne?" Itama kallon ta ta yi, "Na idar mana." "Malam raka a biyu fa za ki yi, ba ɗaya ba." Kallon rashin fahimta ta yi mata. "To, ai biyun na yi." "A hakan? Kafin kiftawar ido da buɗewa har kin dungura kin tashi! Da aiki. Wannan shi ake ƙira 'yar mubi ba yawa sai lada." Yatsina fuska ta yi, 'Koma 'yar waye ke kika sani.' Ƙofa ta nufa da niyyar fita, tambayar da ta jefo mata yasa ta tsayawa. "Na ce ina za ki je." Ta sake maimaita mata tambayar. "Zuwa gaida masu gidan, in kuma ci abinci." "Ba ki goge bakin ba ne za ki ci abinci?" Cikin jin haushi yasa ta ce, "Wani burushi da makel da kike faɗa ma ni ban sansu ba." Fuska cike da mamaki da kuma don darawa da sunan da ta ƙira abun goge bakin ta ce, "To, da me kuke wanke bakin a can?" "Gawayi da gihiri muke dangwala a jikin soson buhu mu yi ta gogawa a haƙoran. Nan gidan ko ban ga alamar murhu ba balle in samu." Bata ce komai ba ta miƙe ta nufi banɗakin, sai da ta kai ƙofa sannan ta sa hannu ta yafutota. Makilin ɗin ta matsa a jikin burunshin ta miƙa mata, "Ki dirje duk wani lungu da saƙo na cikin bakinki har kan harshenki." Tana gamawa ta fice ta bar Abulle a banɗakin. "Wannan akwai shegen iyayi, in da ita ke da gidan inaga ko wuni guda ba zan yi ba za ta korani gi..." "Wai waya faɗa miki ana magana a banɗaki." Shiru ta yi, ba amsa. Ta ɗau tsawon lokaci tana tunanin yadda za ta zura wannan abun cikin bakinta, tsoro ma take kada kifiyoyin robar su caccake mata dadashi. Lakatar man goge haƙoran ta yi, wani yaji-yaji, zaƙi-zaƙi ne ya gauraye mata baki. Tas ta shanye makilin ɗin kan burushin ta sake ɗauko, gudar makilin ɗin ta rinƙa matsowa tana sha tana jan yaji, idan ta ja sai ta ji iska mai sanyi yana hura mata cikin baki. "Mazauni kika samu a ciki ne kam?" Lubna ta watso mata tambaya daga can. Zabura ta yi, "Gani zuwa." Da sauri ta zura magogin cikin bakinta. Ta dai yi yadda ya samu ta ɗauraye bakin ta sake tatso man ta lashe kafin ta fito. "Au! Duk wannan zaman naki ba wanka kike yi ba?" "Wanka kuma da sassafen nan kamar wacce ta yi fitsarin kwance? Jiya ma ai na yi wanka kafin mu taho nan." "Ikon Allah! Kenan acan ba kullum kuke wanka ba?" 'Wanka kullum! Wa yaga ƙwaɗi.' A fili kuma ta ce, "Ina muka ga ruwan da za mu yi wanka kullum." "Uhmmm! Je ki." Ta fice, don dama ta gaji da yawan tambayoyin nan kamar a gaban alƙali. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _20_ Ta jima zaune a falon ba kowa sai Lantana mai aiki da ke share-share da goge-goge da kuma tibi da ke ta aiki shi ɗayanshi. Gajiya da zaman ta yi, ga kuma yunwa da ya dameta. "Baba! Don Allah an gama abun karyawa ne?" Ta tambayi Lantana dake goge tibi. "Abinci a yanzu ƙarfe takwas da rabi? Ai da sauran lokaci 'yannan, da yake yau duk suna gida sai ƙarfe goma ko sha ɗaya za su fito karyawa. Ki koma ki kwanta ko ki je ɗakin girki ki samu wani abun ki ɗan taɓa." Langwabar da kai ta yi, ta kwantar kan hannun kujerar tana faɗin, "Na shiga uku! Wallahi zan iya mutuwa da yunwa idan na kai wannan lokacin." Kallo Lantana ta bita da shi, ta ce, "Ki shiga ki sami Saude mai girki ta baki ko ruwan shayi mana." To, kawai ta ce, ta miƙe jiki ba ƙarfi. "Sannu da aiki Inna!" Juyowa ta yi ta kalli mai yi mata sannun. "A'a! Baƙuwarmu har kin tashi ne?" "Uhmmm! Ina kwana." "Lafiya, yaya jikinki?" "Da sauƙi. Dan Allah akwai abinci? Yunwa nake ji." Ta faɗa kamar zata yi kuka. "Wai! Gashi yanzu nake ɗaurawa. Ko in haɗa miki shayi ne?" "Eh." Ta amsa da sauri. Tana tsaye a wajen ta haɗa mata a wani ƙaramin kofi ta miƙo mata. Karɓa ta yi tana godiya a fili, a zuciyarta kuma haushi ne ya gama rufeta. 'Wannan ne wai abunda zai riƙe ni har wani lokaci? Alƙur'an fitsari ɗaya zan yi in zubar da shi.' Kafa kai ta yi ta kurɓe. 'Da wannan gara ruwa ma wallahi, ban ji komai ba nikam.' "Ga kofin na gode." Ta fito tana tunano ɗumamen tuwon dawa da kokon Inno! Da yanzu a gida take da ta manta da ta karya, da yanzu a gidansu ne miyar tuwon rana ne a kan wuta. Amma anan wai yanzu ne ma ake ɗaura girkin safe, ba za ta iya ba. Gara ma goben ta yi ta koma gida, kafin yunwa ya mata illah. Falon ta koma ta zauna ta fara kallo, sai dai sam bata jin daɗin kallon. Ɗaki ta nufa, ta tarar da Lubna har ta yi barci. Tsaki ta ja a hankali, a zuci kuma ta ce. 'Barcin asara.' Ganin ba abunda za ta yi yasa ta koma kan kujerar cikin ɗakin ta kwanta, hannunta riƙe da ciki. Juyi kawai take na rashin sabo da kwanciyar, ga kuma uwar yunwa. Ji take kamar ta ƙwala ihu ko duk mutanen gidan zasu tashi. Idan ba iskanci ba, ace duk barcin da aka yi da dare bai ishe mutum ba, sai ya sake komawa. Ba ta fatan ma tayi dogon zama a irin wannan wajen da yunwa zai yi ajalinta. Turo ƙofar ɗakin aka yi, Hajiya ce ta sha ado kamar zata gidan biki. Jin buɗe ƙofar yasa Abulle ɗagowa. "A'a! Ashe ɗiyar tawa ta tashi? Yaya jikin naki?" "Na jima da tashi, na ji sauƙi. Ina kwana?" "Lafiya, yaya ƙarfin jikin naki?" "Da sauƙi." Ta bata amsa a fili. A zuci kuma ta ce, 'Ina wani ƙarfin jiki, ban sanya ma ciki komai ba.' "Allah ya ƙara sauƙi." "Amin." Har ta juya zata fita, ta juyo ta ce, "Ki tashi Auntynki ku zo ku ci abinci, ga Babanki ma ki zo ku gaisa, jiya mun je asibiti da shi kina barci." "To." Ta bata amsa, ta je har gaban gadon ta miƙa hannu ta bubbuga ƙafafunta. Idanuwanta ta buɗe, ganin ta tashi yasa ta faɗa mata saƙon Hajiya. "Na ji ta. Ki je sai na yi wanka." 'Sannu kifi.' Ta miƙe tabar ɗakin. Fitowarta ma ba kowa a falon. Tunani take ina shi mai gidan yake da zata gaisheshi? Ita ba ko ina ta sani a cikin gidan ba. Kicin ta shiga ta tambayi su Lantana, ita ta fito ta nuna mata wani ƙofa da zai kaita har ɓangaren Alhajin. Dogon lungune da ya sha sumuntin bature, (Tayis) samɓal ta miƙe ta fara tafiya tana kalle-kalle zuciyarta fal tunanin irin kayan more rayuwa da ke gidan, su kuma suna can cikin karmami. Ba tayi aune ba, sai ji ta yi santsi ya kwasheta ya timata da kasa, take ta baje a wajen ta yi zaman 'yan biri, sakamakon goge wajen da aka yi bai gama bushewa ba. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _21_ Rintse idanunta ta yi, har da ɗan guntun hawaye,ta shiga shashshafa kunkuminta da ta buge a da jikin garu. Sai da ta ɗau tsawon mintuna goma a zaune kafin ta shiga yin rarrafe zuwa wajen su Hajiyar. Bata yarda ta miƙe ba, sai da ta isa wani babban ƙofa sannan ta tashi tsaye, 'Aljannar duniya! Gida a cikin gida.' Shine abunda ta faɗa a zuciyarta lokacin da ta kutsa kai cikin babban falon, sallama ta yi gami da kalle-kalle. "Shigo mana Zainab." Hajiya dake zaune kan daya daga cikin kujerun falon ta faɗa bayan ta amsa sallamar. A hankali take tafiya don gudun sake afkawa gidan jiya. Tana jefa ƙafarta kan tattausan kafet ɗin da ke baje tsakiyar kujerun ta yi saurin janyewa, don laushin ya yi yawa, tsore take kada ta kuma jefa kafar ya lume da ita. Da sauri ta tsugunna a wajen, tana faɗin, "Ina kwana Baffa!" "Lafiya lau, ɗiyata ashe ta jirma. Taso a ƙasa ki hau kujera ki zauna." Yaƙe ta yi, ta ce, "A'a! Nan ma ya yi." "Ki saki jikinki, nan ma gidanku ne, maza taso." Kamar ta kurma ihu haka ta ke ji, gani take kamar lumewa ƙasa za ta yi idan ta sake hawa kan wannan abu mai gashin. Ƙara matsowa ta yi, ba tare da ta hau kan kafet ɗin ba. "Ke dai Zainab akwai ƙauyanci! Ace mutum da gidansu ya riƙa abu kamar wani baƙo." Cewar Hajiya. Dariya Alhajin ya yi, ya ce, "Za ta ware ne ai, sai a hankali. Yaya jikin naki?Kin ci abinci dai ko?" "A'a, yanzu zamu ci." "To, maza a je a karya, kafin a zo a bani labarin Mai Ludaya." Da sauri ta miƙe, ta fita. Tana fitowa ta gurfana ta hau rarrafe. "Ke! Meye haka?" Taji tambaya daga sama, ba tare da ta ji tahowar mai tambayar ba, da yake kanta na sunkuye a ƙasa. Ganin Afreen yasa ta magana. "Sulewa na yi ɗazu." Dariya ya saka, ya ce, "Sai ki riƙa tafiya kina kula." Ya wuce ya barta. 'Ji mugu! Ba ma sannu zai min ba sai wani in kula! Kulo.' Ta ci gaba da rarrafawa har ta baro wajen, ta iso babban falo. Tana zuwa ƙofar wajen ta miƙe, ta shiga. Wajen da suka ci abinci jiya ta wuce ta tarar an ajiye musu komai na karyawa, sai dai ba kowa a wajen. Daga zamanta zuwa yanzu ta yi tsaki ya fi a ƙirga. Ga dai kwanukan abinci, amma ba masu cin. Ga yunwa, ga takaicin rashin zuwan masu gidan. Ganin ta ɗau lokaci tana jiransu ba su zo ba, yasa ta fara kokuwa da kula. Duk wani dabara da za ta yi don ya buɗu ta yi, amma ya ƙi buɗewa. Ganin haka yasa ta haƙura ta koma ta cigaba da zaman jira. A tare suka fito daga gefen Baffan suna kwasar dariya. Kallonsu Abulle ta yi, take ta ji wani takaici ya ƙara rufeta. Ji ta yi kamar ta je ta shaƙesu. Har suka iso wajen suna dariya. "Ba ki ci abincin ba?" Afreen ya tambayeta. Kallon takaici ta yi mishi, 'Banci ba ɗan rainin hankali, da uwar kai kamar Umarun kiyashi.' A fili kuma ta ce, "Uhmmm!" "Me yasa?" A kufule ta ce, "Ban iya buɗe kwanukan ba." Buɗe mata ya yi, ya bata faranti ta ɗibi dankali da ƙwan. 'Ikon Allah! Wannan uwar mai ai sai yasa mutum ya yi lisu.' Jida tayi yanda zai isheta, ya haɗa mata shayi ya miƙo mata da biredi. Godiya ta yi mishi. Ta kalli Lubna da tun zamanta a wajen take danne-dannen waya. 'Albasa dai ba tai halin ruwa ba. A haka dai za a ƙare.' Ledan burodin ta buɗe ta yagoshi, ta dunƙule ta dauko kofin da ya haɗa mata shayin ta danna a ciki. Hannu ta sa ta kwaso jiƙaƙƙen burodin, ta hangame baki za ta tura, hakan ya yi daidai da sauƙe kofin shayin da Lubna ta yi daga bakinta. Kamar ance ɗaga kanki! Sai ko ta yi ido biyu da kwamacalan Abulle. Furzo da ruwan shayin ta yi, tana faɗin. "A uzu billahi! Wannan wani irin azanta ne don Allah." Ta miƙe da shirin barin wajen. "Sista ba dai kin ƙoshi ba?" Afreen ya tambayeta. Juyowa ta yi tana faɗin, "So kake in yi amai ne? Dubi wani gwale fa da yarinyar nan ke yi." Ta juya ta bar wajen. Gallamata harara Abulle ta yi. 'Har da wani korar A'uzun ta, irin ga sheɗaniyar nan. Idan kin ga dama har yauma ta nannaɗe kada ki kuma cin abinci. Har wani Sitta ko sittin ne kai ka ji wajen.' Ta ci gaba da ba cikinta hakkinshi. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _22_ Afreen ruwan shayi kawai ya haɗa ya sha da wainar ƙai ya miƙe ya bar wajen. Kallo ta bishi da shi mai cike da mamaki, har yaushe wannan ɗan ruwan shayin zai ɗauki mutum? Ga abinci nan a wadace ba za su sake su ci ba sai a dangwala a tashi. Shi ya sa ko kaɗan ma ba su da wani ƙiba, wannan kyakykyawar iska aka yi zai iya awon gaba da su. Juyowa ta yi ta ci gaba da cin abincinta, tana mamakin yawan abincin da aka ajiye ba masu ci. Wannan kam almubazzaranci ne. Wataƙila don ba su san wahalar noma ba ne shi ya sa suke haka. Tattaro sauran sayyayyen dankali da ƙwan da ya rage akan farantin ta yi, ta haɗe waje guda ta dunƙule ta kai baki, tana tauna daɗi na shigarta. Bakinta cike, ta ce, "U'uhum! Garin daɗi na nesa, wani ya zo Jinjin bai ga moto ba. Su Inno ana can ana gwagwarmaya da ɗumame." Ta kurɓi ruwan shayin. Ba ta bar wajen ba, sai da ta tabbatar da cikinta ya gama cika gaba da baya. Juyi kawai ta ke yi a kujerar falon, tun tana iya zama har ta gaji ta kwanta, gashi kwanciyar ma duk ya isheta. Wannan wani irin gida ne haka? Ba fita ba aikin komai, duk jikin mutum ya yi ta ciwo. Sai aikin zuba ma kwalba ido kana ganin masu jajayen kunnuwa na ta gwalaɓen magana. Tsaki ta ja, Lubna da ke zaune kan kujera tana danne-danne a waya ta ɗago ta kalleta ta sake mai da kai ga waya. Ba tare da ta ɗago ba, ta ce' "Ke! Ki ɗauko min ruwa a firij." Waiga-waige ta shiga yi, ba ta ga kowa ba. Kenan ma da ita, ita ce Ke! Lallai wannan rainin hankalinta ya wuce inda take tsammani. Juyawa ta yi ta bata baya. "Wai ba ki ji me na ce ba ne?" Ta yi tambayar. Shiru ba amsa. "Zainab! Wani salon iskanci ne haka? Ina yi miki magana, kin yi banza da ni." Jin ta ƙira sunanta yasa ta juyowa tana faɗin, "Ji nayi kin ce ke! A iya sanina Inno da Baffa Zenabe Abu suka raɗamin wanda wasu ke ƙirana da, Abuwa, Abulle. A garin Jinjin kuma Zenabu, kinga ko ai ba lallai in san da ni ki ke yi ba." Kallon mamaki ta bita da shi. Lallai yarinyar nan bata da kunya. "Idan ba da ke nake yi ba, da wa nake yi? Za ki tashi ko sai na ɓaɓɓallaki." Kallon sama da ƙasa ta yi mata, ta ƙare mata kallo tsaf! 'Wai ɓallawa? Allah na tuba ai ko dusa nake ci wuce nan. Yasin damƙa ɗaya na yi miki sai kin gane kurenki. Renon dawa ce ni.' A fili kuma ta ce, "Zan karɓo miki da gudu ma." Ta miƙe ta bar falon. **** Inna Talle da 'yan uwanta sun yi cigiyar Hamusu har sun fara gajiya ba labarinshi. Yau kwana biyar kenan da tafiyarshi. Tun tana kukan fili har ta dawo na zuci. An shaida mata ya tafi garin Jinjin, lokacin da ta sa a yi mata cigiya a tasha. Duk wanda ta ji zai je garin Jinjin, saƙonta baya wuce a sanar ma Hamusu ya dawo gida. Duk wanda ya dawo, ce mata yake bai ganshi ba. Sosai ta tashi hankalinta, lokaci guda duk ta zabge ta fita hayyacinta. Ganin halin da take ciki ne, yasa Wani ƙaninta Garbati ya tafi da ita garinsu Ɗan kurma. Ƙauye ne sosai, ga ƙauyanci har ya fi na Mai Ludaya. Tafiyar awa goma za ka yi daga Mai Ludaya, zuwa Ɗan kurma. Su Inno shirye-shirye ake ta yi, ba ji ba gani. Haka ma gidan Mai Unguwa ana ta shirin tarbar sabuwar amarya. Yayin da galibin 'ya'ya da jikokin Mai Unguwa ke ji kamar su kamashi da ranshi su jefashi cikin tukunya, su gangama mai wuta ya mutu ko su cakuɗa mishi abincinshi da shinkafar ɓera ya mutu kowa ma ya huta. A fadar Mai Unguwa ma, tawagar ta kasu biyu. Tawagar da ta fi rinjaye, suna tawagar ƙin auren Abulle da Mai Unguwan, tawagar amincewa kuwa! Ba su fi a ƙirga ba. *** A hankali take tafiya a kan simintin bature, gudun kaiwa kasa irin na ɗazu, har ta isa ƙofar ɗakin. Buga ƙofar ta shiga yi. Daga ciki aka tambaya da waye? "Nice Abulle." Tasowa ya yi ya buɗe ƙofar. "Yaya ne?" Ya tambayeta. "Cewa aka yi in karɓo ruwan sha a wajenka." Kallon rashin fahimta ya yi mata, "Ruwa a wajena kuma? Duk gidan nan ace ba ruwa sai an aiko ki wajena? Waye a aikoki?" Taɓe baki ta yi itama, tana tunanin kinibibi irin na waccar mai kama da takardar. Ace duk ruwan gidan ya gagareta sha, a na wajen Afirij! "Uhmmm! Nima shi nagani. Akwai ruwa a gidan amma wai in karɓo mata a wajenka." Tsaki ya yi, ya ce "Wai waye ne?" "Labano mana?" "Labano kuma? Waye haka?" Ya yi tambayar cikin rashin fahimta. Kallon rashin fahimta itama ta yi mishi. "Labano ta gidan nan mana. Ko akwai wata ne." Dariya ne ya kufce mishi, da ya gane ashe Lubna take nufi. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Ku yi haƙuri da jina shiru, zazzaɓi ya riƙe ni. Amma sauƙi sosai, masu yi mini addu ar samun sauƙi ina godiya._ _Masu yi min magana ba amsa a private ko cikin group ba amsa ku yi hakuri don Allah, na ɗan yi fama da matsalar network ne._ _Afwan! Sunan garin su Inna Talle Kurmawa ba ɗan kurma ba._ _23_ Dariya yake ta ƙyaƙyatawa, ita kuwa ta gama ƙuluwa, haushi duk ya cikata. Ba abin da ta tsana kamar a tasata gaba ai ta doka dariya ba dalili. Juyawa ta yi cikin fushi zata tafi, da sauri ya biyota yana ƙiranta. "Zainab!" Tsayawa ta yi kafin ta juyo, fuskarta a haɗe. "Meye?" "Yi haƙuri! Da fari ban fahimci wa kike nufi ba." Keɓe baki ta yi, irin kai ka sani ɗin nan. "Je ki, ki ce mata zan kawo mata kin ji." Juyawa ta yi ta ci gaba da tafiyarta ba tare da ta bashi amsa ba. Ganin ta shigo ba ruwa a hannunta yasa ta tambaya. "Ina ruwan da nace ki ɗauko min?" "Ya ce in je zai kawo." Kallon rashin fahimta ta yi mata. "Shi wa?" "A firij!" Tsaki ta ja sannan ta ce, "Kin taɓa ganin Fridge ya yi ƙafa ne? Ko kuma ya yi baki da har zai ce miki jeki zan kawo?" Kallonta ta yi, ta ce "Dama A Firij ɗin kurma ne? Naga kullum yana magan..." Kafin ta ƙarasa maganar sai gashi ya shigo, yana faɗin. "Aunty Labano ga ruwan." "Yauwa, gashi nan ma kin ji yana magana." Cewar Abulle Yamutsa fuska ta yi, "Meye kuma wani Labano?" "Ba ki san Labano ba?" Ya tambayeta lokacin da ya ke zama kan kujerar. "Ban sani ba." "Sabon sunanki ne da Zainab ta raɗa miki yau." Tsaki ta ja cikin jin haushi. Harara ta galla ma Abulle, tana faɗin, "Wannan bata da saiti, don iskanci sunan nawa ne zata ƙira da sunan wani ƙasa." Dariya shikam ya sake kwashewa da shi. "Ke kin cika masifa wallahi, yarinyar da bata iya ba, don ta kuskure ai gyara za a yi mata ba wai a yi mata masifa ba." "Koma dai meye ku kuka sani. Dallah ni bani ruwana." Ta faɗa tana faucewa. 'Kya ji da shi dai masifatu, Allah yaso gobe ma zan bar muku gidan ki ci kanki. Cewar Abulle ta juya ta fita. "Wai gurinka ta je karɓar ruwan ne?" "Dama ba wajena kika aikota ba?" "Duk ruwan da ke gidan nan in kasa sha sa sha sai na wajenka? A Fridge fa nace ta ɗauki min." "To, ai wajen a Firij ɗin ta je karɓo miki." "Ban gane ba?" "Suna na ne fa A Firij ɗin wai." Dariya ta sa, shima ya tayata, kowa yana ƙiran sabon sunan kowa. Bakin get ta nufa wajen Ɗayyabu mai gadi. Yana hangota ya wangale baki yana dariya don yasan yau, zai sha labarin Mai Ludaya har ya ƙoshi. "Abulle! Abulle! Abulle mutan Mai Ludaya. Sai kuma gaki a Jinjin." Ya faɗa yana tura mata farar kujerar roba. Bayan ta zauna ya ce, "Yaya kika ji Jinjin ɗin?" "Ba daɗi." Zaro ido ya yi, "Ba daɗi kuma? Birni ne fa!" "To, ina daɗi anan don Allah? An jibge mutum waje guda kamar kayan wanki, daga barci sai kafa ma kwalba ido." Dariya ya yi, "Wato dai kin fi gane ki yi ta jeka ka dawo ko?" "Iy mana! Zama waje ɗaya ai haɗari ne." "Gaskiya kam, musamman ma ga wanda bai saba ba." "A, to. Ni waje ma nake son leƙawa." "A yi haka kuwa? Ke da kike baƙuwa idan na barki kika fita ai ba kanta." "Yasin ba nisan zan ba, yanzu zan dawo." "To, ai rana ya yi, ki bari zuwa anjima yanzu za a yi sallar azahar ne." "Dan Allah Baba Ɗayyabu ka bari na leƙa, yanzu zan dawo." Jin ta girmamashi yasa ya ce, "To, iyakarki bakin layin nan, yanzu ki dawo." "Yauware, Na gode." Ƙaramin ƙofar da ke jikin jet ɗin ya buɗe mata, har waje ya fito ya nuna mata hanyar ƙarshen layin, tana zuwa kuma ta juyo ta dawo. Godiya ta yi, ta ɗau hanya. Sunkuyawa ta yi, ta tsinci duwatsu, tana tafe tana ciccilasu sama. Ta zo wucewa wajen wani masallaci dake jikin wani gida taga wani mai saida gauta, a tsugunne. Har ta wuce sai kuma ta dawo. "Malam nawa kahin gautar?" "Hansin da ta dari." Ta nuna ɗaya tiren da ba mai ita, "Su kuma wa innan ɗin fa?" "Duk kuɗinsu ɗaya, mai ita ya zaga makewayi ne, yanzu zai fito amma." "Ni na naira Ahirin nake so." Ta kwanto a bakin zaninta. "To, kawo mana sai in ɗiba miki, da gani ai kema tamu ce daga gida kike." Dariya ta yi, ta ce "Kai ma ɗan Mai Ludaya ɗin ne?" "A'a, a Bugawa nake." "Taɓ! Ban taɓa ji ba." "Nima ban taɓa jin naku ba." Ya faɗa lokacin da yake miƙa mata. Sai da ta ƙirga, ta ce "Ƙwara fa huɗu ne?" "Iy!" "Taɓ! Can kam sai dai mu je mu tsinko, nan kuma ɗan wannan wai Ahirin hu um!" Ta faɗa tana tafiya. Tana barin wajen sai ga Hamusu ya fito daga magewayi. "Ai kawai mu yi alwala kawai mu yi sallah sai mu wuce." Cewar Hamusu. "Kawai ba." Abokin tafiyar tashi ya bashi amsa. A yi haƙuri da kura-kuran ciki, ban bibiyaba. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _24_ Tana tafe tana cin gautarta har ta isa bakin hanya, sai da ta tsaya ta kalli motoci da babura masu wucewa sannan ta juyo. Ci gaba da wurga duwatsunta sama ta yi tana cafkewa. Wani gini ta hango da aka fara ba a gama ba aka mai dashi wajen zuba shara. Hango kwalayen sabulai da robobin mai da kwalaben turaruka da ta yi kan bolan yasa ta nufi wajen. Leda ta nema babba ta karkaɗe, Allah ya taimaketa bai yage sosai ba, ta hau tsintar kwalayen sabulu mai hoton mata da robobin mai da kwalaben turaren da basu fashe ba. A ranta tana hango yanda zata jeresu a cikin kwabet ɗinta. Ta tsinci na tsinta ta bar na bari, ta ɗauko ta nufo hanyar gida. "Lahhhh! Mai gauta har yanzu kana nan?" Ta faɗa lokacin da ta zo giftawa wajenshi a ƙofar wani gida. "Iy, wallahi. Mai gidan nan ne ya ce mu zo mu zubar mai da hyara, ɗan uwana ya shiga ciki zai ɗauko." "Lahhhh! Aiko zan jirashi ko zan sam wasu kwalayen." "Yanzu zai fito kuwa." Suna tsaye sai ga Ɗayyabu da saurinshi. "Abulle! Zo yanzu Alhaji ya dawo sallah yake tambayar ina kike na ce kin fita sai faɗa yake, me ya sa na barki ki ka fita." "Allah sarki Baba Ɗayyabu! Yanzu fa zan dawo. So nake a fito da sharar gidan nan sai in ƙara wasu. Kagama wanda na samu a wancan jujin." Ta faɗa tana ƙoƙarin buɗe ledar shirgin. "Taho mu tafi, ki zubar da wannan sharar don ba yarda za a yi ki shiga da shi gida ba." "Abunfa jeren ɗaki ne." Ta faɗa tana zaro ido. "Mu je, nan ai su basu amfani da shi. Ana gamawa da shi sai bola." Ya faɗa lokacin da ya tasa ƙeyarta. "Hu umm! Nikam ina so, zan ajiye a wajenka, gobe idan zan tafi sai in ɗau abuna. Har Sarai ma zan ɗibar ma wasu itama ta jera a ɗakinta tunda ta kusa aure itama." "Oh! Mutanenmu akwai son jere. Har yanzu dai ba a barta ba?" "Tana nan, ku ai nan sai dai ku aje ƙaton kwalba da kujeru muko cika ɗaki ake da jere mai kyau." "Ci gaba ai aka samu." Ta taɓe baki "Amma dai anjima zaka barni na dawo na sake ɗiban wasu ko?" Zaro ido ya yi, "Rufamin asiri, so kike Alhaji ya sallame ni a aiki." "A'a." "To, ki haƙura da wanda kika samu." Suna shiga ta ɓoye a cikin wani ɗan lungu da ke gefen ɗakin Ɗayyabu, ta nufi cikin gida. Duk a falo ta samesu zaune kan kujera. "A'a! Ɗiyata har kin fara gane gari ne kika fita yawo?" Alhaji ya faɗa yana miƙo mata hannu. Zama ta yi a ƙasa can nesa ta ce, "Gajiya na yi da zaman shine na fita." "Nan ai ɓata za ki yi, zuwa yamma yayanki zai fita da ke sai kiga gari ko?" Da murna ta ce, "To, Baffa!" "Ɗan gidan wanene angon ne? Na manta ban tambayi Ilu ba." Sunkuyar da kainta ƙasa ta yi, ta kamo bakin mayafinta rufe rabin fuskarta sannan ta ɗago fuskar ta buɗe ido ɗaya ta ce, "Mai Unguwar yankinmu ne." Ta ƙarashe faɗa cikin jin kunya, ta duƙar da kai. Dariya suka sanya, Hajiya Sabuwa ta ce, "Da alama ana ji da maigidan nan! Wannan irin jin kunya haka?" Ta kaɗa kai ba tare da ta sake dagowa ba. Alhaji ya sake tambayarta. "Wani yaro ne ɗaya daga cikin gidan? Ko cikin jikokin gidan ne?" Ɗagowa ta yi, fuskarta na nuna alamar rashin jin daɗin tambayar, har da 'yar ƙaramar harararta. "Mai Unguwa fa nace Baffa!" Gyara zama ya yi sosai don bai fahimci wani Mai Unguwar take nufi ba. "Mai Unguwar Yankin mai Ludaya ƙarama kike nufi kokuma yaronshi da ake cema Mai Unguwa?" Kaɗa kai ta yi ba tare da ta bashi amsa ba. "Ban fahimta ba, ki buɗe baki ki yi min bayani." "Baba Mai Unguwa Rabi..." Bata kai ga karasawa ba, ta miƙe a guje ta yi ɗaki. Hannu ya shiga tafawa yana salati yana sanar da Ubangiji. Su kuma yaran sai dariyar Abullen suke yi. "Alhaji lafiya kake ta jero salati?" Hajiya Sabuwa ta tambayeshi "Ina fa lafiya?" "Me ya faru?" "Ban taɓa sanin cewar Ilu baya da hankali ba sai yanzu. Kin san wa zai aura ma yarinyar nan kuwa?" Girgizar kai ta yi, kafin ta amsa "A'a." Tsaki ya ja cikin ɓacin rai kafin ya ce, "Tsoho ne fa da ya kusa ba shekaru ɗari baya." Kirji ta buga ta ce, "Mun shiga uku! Shi ko Ilu me ya yi mishi daɗi haka da zai ɗau 'yar jaririyar 'ya ya ba wannan tsoho?" "Rashin tunani da rashin hankali mana." "Gaskiya Alhaji gara tun wuri asan abun yi. Ni kam da haƙura aka yi da auren nan ta yi zamanta anan, a sama mata makaranta." "Hakan ma za a yi, ba sai sun ga ƙafarta a goben bama." "A, to. Ai wannan abu da cutarwa. Duka-duka Zainab ɗin nawa take da har za a yi mata aure?" "Kin san mutanenmu ai, yanzu idan kin je can ma za ki samu ana ƙorafin girmanta." _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _25_ "Lallai akwai su da yi ma yaro auren wuri." "Ai ba auren wurin ne ma damuwa ba, da ya zaɓa mata tsaranta ai ba damuwa. Amma a ce ya ɗauki yarinya ya danƙata hannu tsoho ai abun bai yi ba." "Kuma fa kaga ita yarinyar kamar tana son shi, ji wani sunne kai da take ta yi ita a dole kunyar nan." "Koma menene ita dai ta sani na riga na gama magana." Ya kalli Afreen ya ce, "Anjima ka kaita taga gari, kasan su basu saba zama waje ɗaya ba, tanan za a ɗauke hankalinta." "To, Daddy! Amma ka faɗa ma Labano ta daina kyararta." Hajiya ta ce, "Waye kuma Labano?" Dariya yake yana nuna Lubna da hannu "Wai Lubnan ce ta dawo Labano? Wannan suna daga ina kuma?" "Daga wajen Zainab, wannan ai kafin ta saitu sai ansha fama. Daddy wai kai ma haka ka yi ne farkon zuwanka Jinjin?" Filon dake kan kujera ya ɗauka ya jifeshi da shi yana faɗin, "Ka ci gidanku! Kana raina mana 'yan gari ko? Can zan kai ku ku yi wata ɗaya ku saba da 'yan uwa." Afreen har da murnarshi "Eh, wallahi Daddy ina son zuwa ƙauye." Labano kuwa yamutsa fuska ta yi, ta turo baki tana faɗin "Daddy har wata ɗaya? Ni dai ba za ni ba. Sai dai ko Afirij." Duk suka sa dariya, Hajiya ta kalli Alhaji "Ni ko Lubna za a ba Mai Unguwar tunda ta girmi Zainab ɗin?" Kwaɓe fuska ta yi, kamar zata yi kuka, ta ce "Mommy!" Sai kuma ta miƙe ta nufi hanyar ɗaki. Afreen da ke ta kwasar dariya harda kwanciya kan kujera ya ce, "Labano ta Mai Unguwa! Kuma fa za su dace sosai Mommy." Juyowa ta yi, ta jefomishi remote ɗin tibin da ke hannunta. "Wayyo Allah matar Mai Unguwa zata yi min illah." Ya sake ƙular da ita, Daddy ya ce "Ya isheka, zo abunki 'yar Daddy ba mai yi miki wannan aikin ina raye." Da gudu ta shige ɗaki abunta. "Sai ki je ki rarrasheta, kin santa ai idan ta kumbura sai an nemi allurar da za a soka mata ta sace." "Ai Lubna ban san wace irin yarinya ba ce, bata son mutane ko kaɗan ga ta da ƙin 'yan ƙauye, ko don ba ta zuwa ne yasa hakan?" "Zata daina ne, yanzu duk lokacin da aka yi hutu zan riƙa kai su akai-akai." "Gaskiya ya kamata kam." Ta kalli Afreen da tun ɗazu ke kwasar dariya ta ce, "Kai kuma abun na ya samu ko? Ba a taɓa ganin dauriyarka sai ta ɓaci. Tashi ka je ka shirya idan zaku fita ku sauƙeni gidan Suwaiba in dubata da jaririyarta." Ciki ya shige ya bar su suna ci gaba da tattaunawa. Sai ƙarfe uku aka gama abincin rana, lokacin duk yunya ya addabi Abulle, tun tana shan ruwa yana riƙe mata ciki har ya dawo da ta sha jimawa sai banɗaki. **** "Daga ɗauko shara ka je ka zauna, wata yarinya ta yi ta jiran zuwanka zai ta tsinci kwalin sabulu ta yi jere baka fito ba." "Bari kawai Ɗalliti, na yi zaton sharan kaɗan ne ashe da yawa, na yi tunanin in ce ka shigo sai naga gara ka zauna ko za mu sami masu saye kada mu ɓata lokaci a waje ɗaya mu zo kuma bamu sami komai ba." "Gaskiya! Kuma ka yi farar dabara don ina nan mutane biyu ma sun zo sun saya." "Kaga ai da yanzu ciniki ya wuceemu, don ma naga layin nan ba ba irin layin masu sayen gauta bane." "Yo, Hamisu gautar abinci ne da mutane zasu yi ta jidarshi? Ina jibi idan na tafi gida in zan dawo zan nimo wasu 'yan kuɗaɗen in sake jarraba wani sana ar." "Allah ya kai mu. Barin kai wannan ɗin idan na dawo sai ka shiga kaima ka ɗebo." "To, ba damuwa." Ya tura baron zuwa wajen da ake tara shara. "Na yi tunanin fa kai zaka zaga da gautarnan, ni sai in ƙarasa kwashe sharar kawai." Hamisu ya faɗa ma abokinshi lokacin da ya dawo daga kai shara. "Allah ko? To inaga kuma za a yi fa! Kada mu taru mu zauna waje ɗaya." Ya faɗa lokacin da ya ɗaura tirenshi a kai, ya miƙo hannunshi Hamisu ya ɗoramishi nashi tiren. Har ya yi gaba ya juyo ya ce, "Idan ka gama kawai mu haɗu wajen Goshi mai abinci." "To, ba damuwa." *Ummyn Yusrah* *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Ina taya Haziƙan Marubuta murnar kammala littafinsu, mai suna TA FI BAGARUWA IYA JIMA. Zeety, Ummyn Yusra, Beauty Queen. Allah ya kara hazaƙa ya ƙaro kaifin ƙwaƙwalwa._ _Ruƙaiya Haroun (Maman Nour) ina tayaki murnar kammala littafinki mai suna RUƊANIN RAYUWA (Ƙalubalenmu a yau) Allah ya kara hazaƙa da fikra._ _26_ Bayan sun ci abinci, sun yi sallar la asar ne, Abulle ta je ta tsalo wanka. Kwalliya sosai ta yi cikin atamfarta riga da zani da ɗankwali mai kalar koriya da ruwan ɗorawa. Ta shafe fuskarta da fauda, ta ɗauko ƙwalli ta yi ɗigo uku a saman goshinta, biyu a ƙasa ɗaya a sama. Haka ta yi a gefen kumatunta na hagu da dama da kuma ƙasan haɓarta. Ta sanya jan jambaki a leɓenta ta sa kwalli a cikin idanunta. Sabon silifas ɗinta mai soso ta sa ta sanya hijabinta, sai gata ta fito cas! Kamar ranar sallah. Ta fi minti goma tana kallon madubi, tana ƙare ma kanta kallo, domin ita kanta ta san yau ta yi kyau! Idan ta juya furkarta gefe ta yi fari da idonta, sai ta sake juyawa ɗaya gefen ta sake fari da idanun. Tana yi kuma tana murmusawa. "Na shiga uku! Wannan wani irin hauka ne? Kin gama ƙwaɓa fuskarki wai ke kin yi ado, kuma kina nufin a haka za ki bimu? Gara ma ki koma banɗaki ki je ki wanke fuskar nan wallahi idan ba haka ba sai dai ki zauna." Lubna ta faɗa lokacin da ta fito daga wanka. Kallo ta yi mata, irin mai nuna amar kin taƙura min ɗin nan, 'Ba ke aka ce ki fita da ni ba, kama albarkacin Hajiya ne ta ce ki shirya ku je gidan barkar haihuwa.' "Afirij zan bi ai! Ke kuma Hajiya za ki bi." Ɗagowa ta yi daga shafa man da ta fara, ta yi mata kallo na sakan biyu, kafin ta ce, "Owo! Shine baza ki goge fuskar ba kenan? Ki barshi to don Allah, zamu ga wa za ki bi. Mara kunya kawai. Ana magana kina ba mutane amsa." Cike da haushi ta nufi bayan gidan ta wanke fuskarta. Tana fitowa ta nufi hanyar fita. "Zo nan." Lubna ta ce da ita, har ta kara gaba sai kuma ta juyo ta dawo. Kaya ta miƙo mata ta ce, "Ki cire na jikinki, ki sa wannan." Murmushin takaici ta yi, zuciyarta na faɗin 'A rashin sani, baƙo ya sha ruwan wanka. Ki bi a hankali, idan na bauɗe sai kin raina kanki Labano, sai kin san Abullen Inno ba baya bane.' Karɓar kayan ta yi, ta cire nata ta sa. Doguwar riga ne, da ɗan mayafinshi. Ta rasa yadda zata yi da mayafin, don santsi ne da shi, kawai sai ta tattaro ta ɗaure a wuya. Ta yi waje. **** "Kai! Na aikatu sosai yau, amma na fanshe gumina fa." Hamisu ya faɗa lokacin da suke zaune a ƙarƙashin biya. "Gaskiya kam! Nima da na gama zagawa, na je gurin Goshi na ci abinci na jima sosai a wajen kafin ka zo." "Bari ka gani Ɗalliti!" Ya faɗa yana ciro kuɗin da ke cikin aljihun rigarshi. "Ka gansu." Ya nuna mishi ɗari biyar-biyar guda uku. "Dubu ɗaya da ɗari biyar ya bani, da abinci mai yawa. Ya kuma ce duk bayan kwana biyu in rinƙa zuwa ina zubar da shara da share musu harabar gidan sabida furannin da ke zuba." Ya kare maganar yana kunce wani baƙin leda da ya taho da shi. "Ga naka abincin, ni na ci na ƙoshi a can." "Kai mutumina!" Cewar Ɗalliti, lokacin da yake miƙa ma Hamisu hannu suka tafa, fuskarshi cike da annuri ya ci gaba da faɗin. "Ka ce dai mun shiga wannan layin a sa a?" "Ba laifi, mun taki babbar sa a. Ya kasuwar taka?" "Ba laifi, na ɗan taɓa ciniki." "Mun gode Allah!" Janyo ledar abincin ya yi, ya wurga wani ƙaton yankin nama a bakinshi, sannan ya ce, "Niko Hamisu me zai hana mu kama ɗaki a gidan Malam Bukar, zai fi mana sauƙi da kwanan ƙofar shagunan mutane ko cikin rumfar kasuwa ko? Kaga kullum Da u, cikin kai mana hari suke, sai ka yi nisa cikin barci wani ƙaton ya mirginaka ya kwashe abunda da wuni kana nema." Ajiyar zuciya Hamisu ya yi, da godiya ga Allah da ya haɗashi da abokin ƙwarai, mai son ci gabanshi. Bai da ƙyashi ko hassada. "Kuma fa ka kawo shawara mai kyau wallahi. Amma kana ga zamu iya biyan kuɗin?" "In Allah ya yarda zamu iya. Dubu huɗu ne fa a wata guda, kasan ɗakunan ba wani fasali ne da su ba." Dariya Hamisu ya yi, ya ce, "Allah na tuba! Wa ke duba wani fasali Ɗanliti? In dai asiri ya rufu ai shi ke nan." "Haka ne kuma." Ya faɗa yana ciro kuɗi daga cikin ramin zariyar wandonshi. "Ga dubu biyu nan, ka kawo na wajenka mu haɗa sai ya bimu bashin ɗari biyar ko?" "Kawo dubu guda a wajenka ka gani." Ya karɓa, ya haɗa da na aikinshi, ya ciro wata tsohuwar dubu ɗaya a ramin zariyar shi shima ya haɗa. "Kaga sun cika dubu uku da ɗari biyar, ka adana dubun kaga tafiya ce jibi a gabanka, ba lallai ka sake samun wasu kuɗaɗen kamar wannan a gobe ba." "Ikon Allah! To, ai na gama shirye-shiryena, na sai musu omo, sabulu, manshafawa, da farin magi. Burodi kawai dama ya rage in saya." "To, ka gani ai. Ko mu hakura har ka je ka dawo?" "A a! Daga yanzu ai duk aikin da ya samu yi za mu yi. Kaga tanan zamu riƙa samun wasu kuɗaɗen." "Allah ya taimakemu, yanzu ina muka dosa?" " 'Yan kura za mu, mu yi haya kagani mu ɗebi ruwa mu shigar unguwannin da suke da ƙarancin ruwa ka gani." "Hhhhhh! 'Yan Garuwa kenan?" "Ƙwarai!" Ya faɗa yana wanke hannunshi da guntun fiya watan da ya sha. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _27_ Kai tsaye fallo ta dawo ta zauna, zuciyarta sai ƙuna yake yi mata. Walaƙanci na ɗaya daga cikin abinda ta tsana, sai dai ta lura wannan Lubnar mutuwar 'yar walaƙanci ne. Amma, ba komai. Gobe i yanzu ma ta yi nisa da garin. " 'Yammatan mai ludaya an sha kyau." Bata ɗago kai ba, murmushi kawai ta yi. Sai dai idan ka dubeta zaka iya hango ɓacin rai maƙale a fuskarta." "Yaya ba ki yafa mayafin ba, kika tukuikuyeshi a wuya?" Afreen dake tsaye ya sake tambayarta. "Ƙauyanci mana. Kasan ko yaya baƙauye yake sai ya nuna halin nashi." Lubna ta faɗa lokacin da ta iso falon tana ɗaura ɗankwali. Kallon takaici bita da shi. Yanzu kam ta gama gano tsanarta ce ƙarara a fuskar Lubna. "Hummm! Na gode Allah ina da tushe ba a kwararo aka tsintoni ba. Ki sani ko yaya mutum yake daraja ce da shi. Ɗan adam ba abun walaƙantawa bane. Idan ma kin yi haƙuri, gobe iyanzu babu ni a gidan nan." Harzuƙowa ta yi, ta nufota gadan-gadan tana faɗin, "Iye! Ashe rashin kunyar naki har ya kai haka ne? Har kin kai ki faɗamin magana?" Afreen da ya tare ta ne ya ce, "Haba Anti Lubna! Abin da kike yi mata bai dace ba wallahi." Kallonshi ta yi rai ɓace ta ce, "To, mara kunya! Sai ka koyamin abin da ya dace." Tana kaiwa nan ta ja tsaki kan kujera ta zauna. Ya juya da niyyar yi ma Abulle magana yaga bata nan. Da sauri ya nufi ɗakin Lubna. Ji alamar motsin tafiyar mutum yasa ta yi saurin sanya bayan hannunta ta goge hawayen da ya wanke mata fuska. Shigowa ɗakin ya yi, ganin ta canza kaya yasa shi tambayarta. "Ya naga kin canza kaya kuma mu da zamu fita?" Ba tare da ta ɗago kai ta kalleshi ba ta ce, "Ku je kawai." "Me ya sa? Ya sake tambayarta "Akwai abin da zan yi ne." "Ban yarda ba! Abin da Anti Lubna ta yi miki ne ya ɓata miki rai ko? Ki yi haƙuri kada abun ya dameki, rashin fahimtar juna yasa hakan da zarar kun kun fahimci juna komai zai daidaita ki yi..." Bai kai ga ƙarashe maganar ba muryar Lubna ta katseshi tana faɗin, "Kai! Dallah ka zo, ka bar mutane tsaye a waje suna jiranka ka zo nan ka yi zamanka. Idan ba za ka kai mu ba ka bani makullin." Tana kaiwa nan ta juya. "Ki yi haƙuri kin ji? ki sako mayafinki ki zo mu tafi. Muna jiranki." Ya fita. Yana fita ta yamutsa fuska, ta ce "Ko maton ubana Ilu ne, ba zuwa zan yi ba. Idan kun gaji da jira sai ku yi gaba." Jakar kayanta ta janyo ta zazzage kayan ciki duka, ta shiga ɗaukarsu da ɗai-ɗai tana sake naɗesu, duk da a naɗen suke. "Wallahi Mommy mu tafi, ta sanfa ita muke jira don iskanci ta je ta yi zamanta. Sama da minti goma muna zaman jiranta." Lubna dake zaune a bayan moto kusa da Hajiya ta faɗa. "Fita ki je ki dubota. Meyuwa wani abun ya tsaida ita ko batasan mun fito ba." Cikin yanayin shagwaɓa Lubna ta kalli Hajiyar ta ce, "Mommy!" Itama kallonta ta yi, fuskarta ba alamar wasa ta ce, "Eh!" Ganin yanayin Hajiyar yasa ta fita da sauri badon ta so ba. A sonta a aiki Afreen. Tana zaune a ƙasa, ta jingina bayanta da gado. Ta gama naɗe kayanta ta mayar cikin jaka, hotunan da ta ciro take kallo, wasu da ƙawaye, wasu 'yan uwa, wasu kuma ita da Hamusu. Jin motsin tafiya yasa ta yi saurin turasu ƙasan gadon ta rarumo jakarta tana ƙoƙarin jan zif ɗin ne aka buɗo ƙofar. Fuskarta ba annuri ta leƙo ta ce, "Malama ke fa muke jira, kin wani nemi waje kin zauna." "Ku je, ba zani ba." Ta bata amsa "Ya fi miki." Ta juya ta fita, ita kuma ta janyo hutunanta ta mayar cikin jaka ta zuge zif ɗin ta ɗauka ta koma ɗakin da tun farko aka yi musu masauƙi ita da Inno. "Ina Zainab ɗin?" Hajiya ta tambayeta ganin ta shigo tana jan ƙofa zata rufe Fuskarta a sake ta ce, "Kanta ke ciwo ashe, na ce ta zo mu tafi, ta ce ba zata iya ba, shine na bata magani ta sha ta kwanta." "Subhanallah! Ta sha maganin ta kwanta dai ko?" "Eh!" "Mu je mu dawo da wuri sai in dubata." "Gaskiya kam, ta riga ta kwanta kada ki je yanzu ta tashi ciwon kan ya ƙaru." Hannu ta miƙa daga baya ta zare abin sauraron sautin da Afreen ya toshe kunnuwanshi da shi, ta ce "Mu je ko?" Ta faɗa tana ɗaga mishi gira "Ina Zainab ɗin kuma?" Ya tambaya lokacin da ya juyo. Harara ta zabga mishi, "Kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta." Kai kawai ya gyaɗa, don yasan kwanan zancen, sai dai bai ɗauka yarinyar na da zuciya har haka ba. Zama ya gyara, sannan ya ja suka tafi. *Ummyn Yusrah* *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Matso kusa ku ji! Ko kuna da labarin shahararren kamfanin nan mai suna *RANDAWA MEDIA CONCEPT* kuwa? Kamfani ne ɗaya tamkar da dubu. Aiki cikin aminci, inganci, rangwame da kuma rahusa. Ku dai kawai ku tuntuɓemu ta wannan number domin samin biyan buƙata cikin sauƙi 08062176520. Ga kaɗan daga cikin aiyukanmu_ _1. Waƙar biki, suna, siyasa, ring tone da sunanki/ka, waƙe masoynka/ki, miji ko mata._ _2. Calendar da sticker biki, suna sauƙar karatu, ko dai na wani abun._ _3. Tallata haja ko wakar ma aikata ko company._ da dai sauransu _Kai tsaye ku tuntuɓemu ta numbermu dake sama don samun aiki cikin rangwame da rahusa, sai kun zo._ _28_ Ada baya tana son zuwa cikin garin Jinjin, sai dai a yanzu da take cikinsa duk ta ji ya fita mata a rai. Ta tsani garin gaba ɗayanta, ko kaɗan ba zata iya rayuwa cikinta ba. Gara ta koma inda ta fi wayo, gurin da aka san kimarta da darajarta. Sai daf magriba Hajiya suka dawo. Kai tsaye ɗakin Lubna suka nufa dukansu, bata ciki, har banɗaki tasa Lubna ta duba bata ciki. "Ina ta shiga to? Kika ce ta kwanta ɗazu, shigowarmu kum bata falo." Hajiya ta tambayi Lubna da ta yi tsuru-tsuru da ita. Cike da tsoro ta ce, "A nan fa na barta tana kwance." Ta faɗa tana nuna gefen gado "Barin dubata ko tana kicin ne." Ta fice da sauri ta nufi kicin ɗin, duk tsoronta kada Hajiya ta ji abinda ta yi mata. Tana fita Hajiya da Afreen suka bi bayanta. "Ba ta kicin ɗin." Lubna ta faɗa lokacin da ta sami su Hajiya tsaye a tsakiyar falo. "Ba ta kicin? To, kodai sake fita ta yi ne irin na ɗazu? Kai Afreen tambayo Ɗayyabu, ke kuma duba ɗakin baƙin can." Hajiya ta basu umurni Da sauri dukansu suka fita. Tana buɗe ƙofar ɗakin kuwa ta ganta kwance, "Har kin tsoratamu, mun duba ɗaki bakyanan ashe nan kika dawo." Ba tare da ta ɗago ba, ta ce "Eh!" "Ki zo Mommy tana nemanki to." Bata amsa ba, kuma bata tashi ba. "Na ce, Mommy tana ƙiranki." Kaɗa kai ta yi, ganin har yanzu tana kwance yasa ta keɓe baki ta juya zuwa falon. Zaune ta samesu yanzu a kan kujera, Afreen ya sanar mata saƙon Ɗayyabu cewar Abulle bata fita ba. "Tana kwance a can, ta ce tana zuwa." Sai da ta ɗau lokaci kafin ta fito, ta tsugunna can gefe. "Shigo mana ki zauna, kin koma can gefe kin raɓe kamar wata baƙuwa." Ƙara matsowa kaɗan ta yi, "Ke dai akwai baƙunta Zainab! Ace mutum da gidansu ba zai saki jiki ba, sai ki ta ɗari-ɗari. Ko ba ki jin daɗin zama da mu ne?" Girgizar kai ta yi, "To mene ne?" "Ba komai." Ta faɗa a hankali "To, ki saki jikinki kin ji?" "To." Murmushi ta yi, "Yaya kan naki? Lubna ta ce kanki na ciwo, ta baki magani. Fatan kin ji sauƙi." Kai ta ɗaga ta kalli Lubna, a zuciyarta kuwa cewa ta yi, 'Makira.' A fili kuma ta ce "Na ji sauƙi." "To, Allah ya ƙara sauƙi." Ƙiran sallar da aka fara ne yasa suka watse. Ko da aka fito cin abincin dare ma, kaɗan Abulle ta ci, don gaba ɗaya tunaninta da hankalinta ya koma gida. Duk zaman gidan ya isheta. *** Ba laifi, yau kasuwa ta buɗe ma su Hamusu sosai, har takai ga sun haɗa kuɗin ɗaki, sun kuma biya an basu. Yanzu zasu yi barci cikin salama. *** Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin a kayi daga waje, daga bisani ya ce, "In shigo?" Kanta na kan waya tana kishingiɗe a kan gado ta ce, "A a, ka yi ta tsayuwa." Buɗe ƙofar ya yi ya shigo, ya janyo kujerar da ke gaban madubi ya aje kisa da gadon sannan ya ce, "Ina abokiyar zaman taki?" Keɓe baki ta yi, ta ce "Ohho mata ba! Can ɗakin naga ta koma." Girgiza kai ya yi, kafin ya fara magana. "Anti Lubna dama magana nake so mu yi." Sai sannan ta ɗago kai ta kalleshi "Ina jinka." "Daddy da Mommy suna son Zainab ta zauna a gidan nan, sai dai kuma abinda kike yi mata naga bata jin daɗinshi. A tunanina zaki jata a jiki ki yi farin ciki da murnar samun 'yar uwa, sai kuma naga akasin hakan. Don Allah Anti Lubna ki sassauta mata ko zata ji daɗin zama da m..." "Dakata! Mara kunya. Tazarar shekaru nawa ne tsakani na da kai?" Ta katseshi ba tare da ya kai ga ƙarshen maganarshi ba. Mamaki ne ya kamashi jin ta ambato shekaru, bai ga zancen da ya yi da har zai kai ga hakan ba. "Biyar!" Ya bata amsa "Ok! Ashe kana sane, kana da shekara ishirin ina da ishirin da biyar. Kenan kaga ba kai zaka gwadamin yadda zan yi rayuwa ta ba, idan ba zaka iya ganina a haka ba ka kau da ido." Baki kawai ya saki cike da mamaki, daga bisani ya miƙe ya bar mata ɗakin don baida ta cewa. A yi haƙuri da kura-kuran da ke ciki, ban bibiyaba gaskiya. *Ummyn Yusrah* *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _29_ Yana fita ta miƙe ta ja tsaki, ta sa ma ƙofar makulli ta rufe. Dawowa ta yi ta fara rage kayan da ke jikinta don shirin kwanciya. Abun hannunta ne ɗaya ya gangara zuwa ƙasan gado garin cirewa. Tsaki ta ja, da nuna alamar gajiya sannan ta sunkuya da niyyar cirowa. Ba ta ganshi ba, ya yi nisa, sai wani farin takarda ta ci karo da shi. Hannu ta miƙa ta ciro. *** Yana fita kai tsaye ya nufi ɗakin da Abulle take, da sallama ya shiga yana faɗin "Ba dai har amaryar mai unguwa ta yi barci ba?" Tashi ta yi daga kwanciyar da ta yi tana faɗin, "Tuni na kwanta, barci ya ƙi zuwa." Dariya ya yi "To, yaya za a yi ya zo, bayan lokacin yinshi bai yi ba." "Ai so nake in tashi da wuri." "Ai ko ba ki kwanta da wuri ba, gidan nan ba a makara. Dolen mutum ya tashi ya yi sallar asuba da zarar lokaci ya yi, idan ya idar sai ya koma." 'Ya koma barcin asara ba.' Ta faɗa a zuciyarta "Mu je falo akwai film ɗin da za a sa." Kallonshi ta yi, ta ce "Fin? Meye kuma wannan?" Dariya ya yi, "Ba fa fin na ce ba. Film!" Dariyar da yake ne ya fara ƙular da ita, "Uhmmm! Koma dai mene ne, ni barci zan yi, so nake gobe in tashi da wuri in shirya." Ta jingina da gadon fuskarta na bayyanar da murmushi ta ce, "Gobe kamar wannan lokacin ina gida." Kallonta ya yi, "Nan ma ai gida ne, mu da muke so ki zauna ko 'yar diplomar nan ki yi ki karanto mana engineering." Zaro ido ta yi, "In zauna a ina? Yasin a a! Kuma waye shi gudulomar da injimiyarum ɗin?" Dariya ne ya kamashi har da riƙe ciki "Ba fa guduloma ba! Diploma na ce da engineering, ina nufin ki zauna ki yi karatu anan har a kai ki jami a." A tsarace ta ce, "A ina ɗin? Yasin ba ni zama. Har wani jami a ma zani? Taɓ! Ashema so ake mutanen Mai ludaya su ƙirani da 'yar iska. Hu'umm! Ba da ni ba aradu." Yau wannan yarinyar zata kasheshi da dariya, da zantukanta masu cike da shirme. "Yau kam nan kuka tare da hirar ne?" Hajiya ta katseshi lokacin da ta shigo ɗakin "Yau mun ba falo hutu Mommy! Hirar nan ɗin ma ya fi na falon daɗi." Ya ba Hajiya amsa "Ai kam naga alama! Tun ɗazu nake jiyo dauriyarka. Zainab yaya kayin naki?" "Na ji sauƙi Memi." "Ankuma!" Afreen ya faɗa "Don Allah Mommy ki ji, Diploma fa na ce mata da engineering, ita kuma wai guduloma da injimiyarum. Ance Mommy ta ce Memi." Kaɗan ya rage itama ta yi dariya, sai dai ta gimtse. "To, ai bata iya ba ne. A hankali zata koya." Har ta juya zata fita sai kuma ta juyo tana tambayar, "Ina Lubnar kuma?" Take fuskar Abulle ya canza "Ta kwanta." Afreen ya bata amsa lokacin da ya lura da sauyin da ya gani a fuskar Abulle. Matse baki ta yi, ta juya ta yi gaba. Tasan halin 'yar tata na rashin son hayaniya, hala sun dameta ta korosu nan. Shi kanshi ya sani mai zama inuwa ɗaya da Lubna sai ya shirya, ko kaɗan bata iya zama da mutane ba. "Zainab! Nasan bakya jin daɗin zama da Aunty Lubna. Haka halayyata yake, duk mai zama da ita sai ya yi haƙuri..." "Idan zaman ya zama dole ma mutum ba." Ta katseshi "Haka ne kam! Ɗazu nima na shiga mu yi magana kan yanda take yi miki, ko saurarata bata yi ba. Sai ma wani maganar shekaru da ta fara jeromin." Ya faɗa yana jan ƙaramin tsaki. Da alama maganar ta konashi "A rayuwa ai ba a duba yawan shekaru, abinda aka aikata a tsahon shekarun ake dubawa." "Haka ne kam, na yi iya ƙoƙarina don ganin na saitata amma abun ya gagara." Ya faɗa cikin damuwa "Abune mawuyaci ka iya canza mutum lokaci ɗaya akan wata ɗabi a tashi." "Haka ne kam! Na tabbata inda hakan na da tasiri da Aunty Lubna ta daɗe da canzawa. Sai dai hakan ya riga ya zama ɗabi arta. Ki tayata da addu'a sannan ki yi mata uzuri Allah ya bata ikon canzawa." "Uhmmm! Amin." *** Saida ta juyo taga hoto ne ashe. Ƙurama hoton idanu ta yi, kabanta na dukan uku-uku ganin kyakkyawan matashin saurayin da ke jikin hoton tare da Abulle. _Goron Jumma a_ _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _30_ Ga saurayi har saurayi, sai dai da gani ƙauyanci ya gama yi mishi ƙawanya. Da zai samu ya goge, ba ƙaramin nagartaccen namiji za a yi a wajen ba. Wurgi ta yi da hoton kan durowar da ke gefen gadonta, da niyyar idan gari ya waye zata ba mai shi. Sai dai maimakon ya zauna kan durowar sai ya faɗa bayanshi. Bata bi ta kanshi ba, gado ta haye ta ja bargo ta rufu. Ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita. *** Duk wani rarrashi da magiyar da Afreen ya ma Abulle kan ta koma ɗakin Lubna ƙi sauraronshi, sai ma tsalle da ta daka ta ce ita da ɗakin Lubna sai a ƙiyama, ta barmata shi bari na har abada kuwa. Tana iya jure komai amma banda walaƙanci Ƙarshe dai haƙura ya yi ya barta, nan itama ta bi lafiyar gado cike da ɗokin gobe tana garinsu. Daren yau ya mata nisa, ta yi barci har ta gaji gari ya ƙi wayewa. Tun tana juyi har dai ta tashi ta zauna. Agogon bangon da ke manne a jikin bangon ɗakin ta ƙura ma ido, gashi dai sai aiki yake yi, amma ita sam bata fahimtar me yake aikatawar, don ba iyawa ta yi ba. Ita dai kawai bin ɗan dogon tsinken da ke ta zagaye a ciki take da kallo. Daga bisani ta keɓe baki ta ce, "Agogo kenan! Sarkin aiki." Da ta gaji da zaman sai ta sake jawo jakar kayanta ta sake zazzagesu tana kuma yi musu sabon naɗi tare da shiryasu cikin jaka. Sai da ta gama tas! Ta sake ciro hotunan nan tana sake ƙare musu kallo. Wasu ta yi dariya, wasu kuma haka kawai sai su bata tausayi. Mussaman ma wanda suka yi a wani sallah ita da Inno, Ilu da ƙaninta Muntari. Duk sunci kwalliyar sallah. Ilu da Inno zaune a kan kujera, Abulle da Muntari kuma zaune a ƙasa a gabansu. Kuka ne ya ƙwace mata wanda bata san dalilin yinshi ba. Sosai take kewar iyaye 'yan uwa da illahirin mutanen Mai Ludaya. Haka nan kawai take jin wani irin janji a jikinta dama yanayinta. Ita kanta tana mamakin yanda aka yi Lubna ke cin bulus da yawa a kanta. Duk da kasancewarta mai tsoro, bata lamunci rashin mutunci da raini ba. Da zarar ka ce mata kule zata ce cas! Share hawayenta ta yi, ta ci gaba da kallon hatunan. Sosai ta kura ma hoton idanu. Tsaye suke a bakin gona ita da Hamusu, yana sanye da rigarshi 'yar shara mai ruwan bula da na yadi da farin wando, ita kuma tana sanye da atamfarta riga da zani da ɗankwali mai kalar ruwan ƙasa da baƙi yayin da ta tamke kunkuminta da gyalenta. Dukkanninsu rake suke sha. An ɗauki hoton ne daidai lokacin da suka kai raken bakunansu da niyyar gutsura. Ta daɗe tana ƙare ma hoton kallo, ƙirjinta na dukan sha uku-uku. Yau ce rana ta farko da ta fara nadama da da-na-sanin biye ma banzar zuciyarta wajen rabuwa da rabun ranta Hamusu! wanda a baya ko a mafarki basu taɓa tunanin hakan ba. Yau ce rana ta farko da tayi Allah wadai da ƙin tsayawa ta saurari uzurinshi, sabida baƙin kishi irin nata. Yau ne kuma ta tuna irin gangancin da ta yi na amincewa da auren Mai Unguwa sabida tsantsar ƙwaɗayi irin nata. Inama tana da halin hana faruwar auren nan nata da Mai Unguwa? Bakin alƙalami ya riga ya bushe. Ta yi ganganci tun a karon farko, a yanzu bata isa ta je da zance fasuwar auren ba, don tasan hakan babban abun kunya ne, abune kuma da zai iya taɓa kima da darajar gidansu. Abune da zai kafa tarihi tun daga iyaye har jikokin-jikoki a gari. Domin abun kunya ne a saka auren mutum a ce an fasa. Gaba ɗaya gari da maƙota sai zance ya zaga kuma gidan sai ya shiga cikin tarihin garin. Tunowa ta yi da ranar da zata tafi Mairangwangan ya biyota yana yi mata magiyar ta tsaya ta saurareshi, amma ta ƙi, sai ma maganganu da ta gaggayamishi wacce ya gaza haƙuri shima ya mayar mata. Duk da kasancewarshi mai haƙuri sai da ta kai shi maƙura. Ta sake ɗauko wani hoto da suka yi a yammacin biyun sallah. Tarin samari ne da 'yammatan garin, sun taru sun yi layi, mata sun tsaya a ɓangaren gabas, maza kuma yamma, dukkanninsu suna kallon juna. Tafi aka fara tare da waƙa. 'Yammata a dandali da samari a dandali. Kowa nata shaggali, yau ranar tamu ce Abulle zo ki rausaya, Hamusu ne gwaninki ke. Kowa ya san dashi, kema kin tsayar dashi. An ɗaukeshi ne daidai lokacin da ta fito tsakiyar fili tana rawa, kai a ƙasa Hamusu ya fito yana tayata takawa. Kuka ne mai ƙarfi ya ƙwace mata, da sauri ta toshe bakinta da hannayenta duka biyun, ta miƙe samɓal a ƙasa tana kuka mara sauti. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _To, me ma zance muku ne? Kawai dai na gode. Duk da nasan kalmar godiya ta yi ƙaranci a gareku masoya wannan labari._ _31_ Ƙauyen Mai Ludaya A wannan daren da Abulle ke kewar mutanen garin Mai Ludaya, a garesu su shaida kawo kayan auren Abulle da Mai Unguwa suka yi. Yau gidan nasu tun safe ba saka tsinke, hidima kawai ake yi, kai ka ce yau take ranar ɗaurin aure. Da dare bayan sallar isha i ne, jama ar garin mai Ludaya suka shaida kawowar fantimoti mai taya babba guda ɗaya, irin na 'yan burni, na auren Abulle da Mai Unguwa. Atamfarta guda biyar, shadda ɗaya, mayafai biyu, takalmin ado biyu, silifas ɗin roba ɗaya, sai jakarta guda ɗaya irin ta wanzamai. Sai kayan kwalliya da sauran tarkace. Duk inda ka gilma ji kake 'Abulle ta yi goshi.' wasu kuma cewa suke, 'Dama ƙaɗayi yasa suka ba Mai Unguwarta.' Zantuka dai iri-iri. **** Rayuwa ta fara canza ma Hamusu. Daga kwana a rumfar shagunan mutane zuwa kwana a ɗakin haya. Kwance suke a kan tabarmar Ɗalliti, shikam ya jima da barci, Hamusu ko sai juyi kawai yake yi, tunani fal! Zuciyatasa. Gajiya ya yi da kwanciyar ya miƙe ya nufi ledar kayanshi ya ciro wani riga ya warwareta. Hotunansu ne ya bayyana, ya ɗauka ya shiga kallo da ɗai-ɗai tamkar yau ya fara ganinsu, duk da mafi yawan hotunan shi da Abullenshi ne. Ji yake kamar ya yi fiffike ya isa garin Mai Ludaya, ya je ya gano Abulle ko zai sami sassaucin ƙuna da raɗaɗin da zuciyarshi ke yi mishi. **** A hankali sautin kukanta ke fita, zuciyarta ƙuna take, ga kuma shauƙin son Hamusu da ya addabeta a yau. Lallai tayi ganganci da ta biye ma son zuciyarta, akan kwaɗayin Shinkafa ta guje ma masoyinta. Me ya sa tun a lokacin bata gane irin gangancin da tayi ba? Me ya sa bata tsaya sunyi fito-na-fito da Indo ba, ta ƙwace masoyinta. Sake rushewa da kuka ta yi, a hankali ta fara waƙa, 'Rabuwa da masoyi ba daɗi, wannan cuta ce a zuciya.' 'Zan yi bankwana da kai, ka zamemin rabin jikina.' 'Zuciyata taka ce, kasance mai tallafawa.' Rayuwata na yi zurfi, kaunarka ce ke sani nishaɗi.' 'Mun yi bankwana da kai, yau gashi raina yana ta ƙuna.' Ta ƙarashe waƙar tana mai tsananta kukanta, ga zuciyarta da ya yi mata nauyi da zafi. Inda da yanda zata yi a wannan daren, da ba abinda zai hanata tafiya garinsu ta gano abun ƙaunarta ko zata sami sassauci daga ƙuna da raɗaɗin da take ji. Ta yi gangancin da batasan hanyar da zata gyarota ba, ba wanda zata iya fuskarshi da zancen canza akalar aurenta daga kan Mai Unguwa zuwa kan Hamusu. Lallai ta makaro, makara mara amfani ma kuwa. Batasan tsawon lokacin da ta ɗauka a cikin wannan yanayin ba, sai da sanyin asuba ya fara ratsata ne, barci ya yi awon gaba da ita. A firgice ta tashi, cikin tsoro da fargaba ta shiga ƙare ma ɗakin kallo. Take mafarkinta ya dawo mata, nan ta shiga tunanin me ke faruwa a gidansu? Me ya sa mutane suka taru da yawa haka? Kodai mutuwa aka yi ne? Da sauri wata zuciyar ta tunatar da ita taron aurenta ake. Ita har ta manta da wani aure ma. Tunanin Hamusu shi ne a ranta. Cikin sanyin jiki ta tashi ta nufi banɗaki. Hasken ranar da ya shigo ta tagar banɗakin ne ya tabbatar mata da rana ta yi batama sani ba, tana ta sheƙa barci. 'Wannan gida ko ina a rufe, ina ma mutum zai gane rana ta yi idan ba fita ya yi ba.' Alwala ta yi ta fito ta duddungura, tana gamawa ta tattara duk wani shirgi nata a ɗakin ta fito falo. Tsaki ta ja, haushi duk ya rufeta ganin ba kowa a falon. Zama ta yi, ta ajiye jakarta a gefe don tasan zaman jira zata sha tunda masu gidan basu tashi a barci ba. Ita a nata ra ayin ma, zuwa yanzu ta yi nisa a hanya. _Ku yi haƙuri da wannan_ _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _To, me ma zance muku ne? Kawai dai na gode. Duk da nasan kalmar godiya ta yi ƙaranci a gareku masoya wannan labari._ _31_ Ƙauyen Mai Ludaya A wannan daren da Abulle ke kewar mutanen garin Mai Ludaya, a garesu su shaida kawo kayan auren Abulle da Mai Unguwa suka yi. Yau gidan nasu tun safe ba saka tsinke, hidima kawai ake yi, kai ka ce yau take ranar ɗaurin aure. Da dare bayan sallar isha i ne, jama ar garin mai Ludaya suka shaida kawowar fantimoti mai taya babba guda ɗaya, irin na 'yan burni, na auren Abulle da Mai Unguwa. Atamfarta guda biyar, shadda ɗaya, mayafai biyu, takalmin ado biyu, silifas ɗin roba ɗaya, sai jakarta guda ɗaya irin ta wanzamai. Sai kayan kwalliya da sauran tarkace. Duk inda ka gilma ji kake 'Abulle ta yi goshi.' wasu kuma cewa suke, 'Dama ƙaɗayi yasa suka ba Mai Unguwarta.' Zantuka dai iri-iri. **** Rayuwa ta fara canza ma Hamusu. Daga kwana a rumfar shagunan mutane zuwa kwana a ɗakin haya. Kwance suke a kan tabarmar Ɗalliti, shikam ya jima da barci, Hamusu ko sai juyi kawai yake yi, tunani fal! Zuciyatasa. Gajiya ya yi da kwanciyar ya miƙe ya nufi ledar kayanshi ya ciro wani riga ya warwareta. Hotunansu ne ya bayyana, ya ɗauka ya shiga kallo da ɗai-ɗai tamkar yau ya fara ganinsu, duk da mafi yawan hotunan shi da Abullenshi ne. Ji yake kamar ya yi fiffike ya isa garin Mai Ludaya, ya je ya gano Abulle ko zai sami sassaucin ƙuna da raɗaɗin da zuciyarshi ke yi mishi. **** A hankali sautin kukanta ke fita, zuciyarta ƙuna take, ga kuma shauƙin son Hamusu da ya addabeta a yau. Lallai tayi ganganci da ta biye ma son zuciyarta, akan kwaɗayin Shinkafa ta guje ma masoyinta. Me ya sa tun a lokacin bata gane irin gangancin da tayi ba? Me ya sa bata tsaya sunyi fito-na-fito da Indo ba, ta ƙwace masoyinta. Sake rushewa da kuka ta yi, a hankali ta fara waƙa, 'Rabuwa da masoyi ba daɗi, wannan cuta ce a zuciya.' 'Zan yi bankwana da kai, ka zamemin rabin jikina.' 'Zuciyata taka ce, kasance mai tallafawa.' Rayuwata na yi zurfi, kaunarka ce ke sani nishaɗi.' 'Mun yi bankwana da kai, yau gashi raina yana ta ƙuna.' Ta ƙarashe waƙar tana mai tsananta kukanta, ga zuciyarta da ya yi mata nauyi da zafi. Inda da yanda zata yi a wannan daren, da ba abinda zai hanata tafiya garinsu ta gano abun ƙaunarta ko zata sami sassauci daga ƙuna da raɗaɗin da take ji. Ta yi gangancin da batasan hanyar da zata gyarota ba, ba wanda zata iya fuskarshi da zancen canza akalar aurenta daga kan Mai Unguwa zuwa kan Hamusu. Lallai ta makaro, makara mara amfani ma kuwa. Batasan tsawon lokacin da ta ɗauka a cikin wannan yanayin ba, sai da sanyin asuba ya fara ratsata ne, barci ya yi awon gaba da ita. A firgice ta tashi, cikin tsoro da fargaba ta shiga ƙare ma ɗakin kallo. Take mafarkinta ya dawo mata, nan ta shiga tunanin me ke faruwa a gidansu? Me ya sa mutane suka taru da yawa haka? Kodai mutuwa aka yi ne? Da sauri wata zuciyar ta tunatar da ita taron aurenta ake. Ita har ta manta da wani aure ma. Tunanin Hamusu shi ne a ranta. Cikin sanyin jiki ta tashi ta nufi banɗaki. Hasken ranar da ya shigo ta tagar banɗakin ne ya tabbatar mata da rana ta yi batama sani ba, tana ta sheƙa barci. 'Wannan gida ko ina a rufe, ina ma mutum zai gane rana ta yi idan ba fita ya yi ba.' Alwala ta yi ta fito ta duddungura, tana gamawa ta tattara duk wani shirgi nata a ɗakin ta fito falo. Tsaki ta ja, haushi duk ya rufeta ganin ba kowa a falon. Zama ta yi, ta ajiye jakarta a gefe don tasan zaman jira zata sha tunda masu gidan basu tashi a barci ba. Ita a nata ra ayin ma, zuwa yanzu ta yi nisa a hanya. _Ku yi haƙuri da wannan_ _Ummyn Yusrah_ [11/17, 9:36 AM] Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _32_ Gajiya tayi da zaman jira, ga barci da hamma duk sun dameta, dole ta sake komawa ɗakin da ta baro ɗazu don ta ɗan taɓa ko kaɗan ne, tunda daren jiya bata samu ta yi ba. Gashi gani take yau da gayya mutanen gidan suka ƙi tashi da wuri. Tana kwanciya ba jimawa barcin da ta ci bashinsa ya yi awon gaba da ita. Sosai take barcinta hankali kwance, tare da daɗaɗan mafarkai. "Zainab! Zainab!!" Cikin barci ta ji ana ƙiran sunanta a hankali, tare da bubbuga mata kafa. Buɗe idanu tayi, Hajiya da ke tsaye, ta ce, "Wannan barci haka kamar wacce ta kwana bata yi barci ba? Sau biyu Afreen na zuwa dubaki ba ki tashi ba, gashi har an yi sallar azahar baki ko karya ba." Zaro ido ta yi, tana faɗin, "An yi sallan Azahar? Na shiga uku! Shi ke nan na rasa moto." Cikin rashin fahimta Hajiya ta kalleta, tare da tambaya. "Moton me kika rasa kuma?" Kuka tasa tana faɗin, "Moton Mai Ludaya!" 'Tirƙashi! Na manta ban sanarmata da zaman ta ya dawo nan ba.' A fili kuma murshi ta yi, ta ce "Ai na zo in tasheki ki shirya ganin baki tashi ba yasa na barki." Kuka itakam take yi, don tasan yanzu ta rasa moto, kwana ya sake kamata. "Tashi mu je ki wanke baki, ki zo ki ci abinci, zan tura Tukur direba ya je tasha ya duba ko sunanan. Kin ga kafin ya dawo kin shirya ko?" Cikin murna da farin ciki ta miƙe tana faɗin "To!" Ta nufi banɗaki. Ficewa daga ɗakin Hajiya ta yi, zuciyarta cike da tunanin yanda zaman nasu da Abulle zai kasance. Cikin sauri take yin komai, abincin ma kasa shiga ya yi cikinta, haka ta ci kaɗan ta koma falo jiran dawowan Tukur direba. Har yammaci babu Tukur babu dalilinshi, ga Hajiya ma ta ƙi fitowa daga ɓangaren Alhaji, Afreen da Lubna kuma sun fita tun safe. Ganin magriba ya gabato yasa ta ja jakar kayanta ta koma ɗaki. Kwanciya ta yi, sai kuka. Sai bayan Isha Lubna suka dawo, ɗakinta ta wuce, Afreen kuma ya yi ɗakin Abulle yana ƙwalamata ƙira. Yana buɗe ƙofar ya hangota zaune a ƙasa ta kifa kanta da jikin gado, sai kuka take yi. A hankali ya tako har cikin ɗakin, ya zauna a gefen gadon. "Zainab!" Ya ƙira sunanta, bata amsa ba kuma bata ɗago ba, domin duk gidan haushinsu take ji. Da gangan suka ƙi tashinta har lokaci ya ƙure. "Zainab! Me aka yi miki kike kuka?" Ya tambayeta. Kai ta girgiza mishi, "Me ya sa ki kuka to?" A hankali ta ce "Ba komai." "Ban yarda ba. Ki faɗamin kin ji?" Ɗagowa ta yi, idanunta sun rine sun yi ja ta ce, "Ni gida zan tafi." Murmushi ya yi, "Don za ki tafi gida sai ki zauna ki yi ta kuka?" "To, ai yau aka ce zan koma." Dariya magar ya bashi, "Ai Daddy ya ce anan za ki zauna, ke da garinku sai dai ki kai ziyara ko baki son zam..." Zaburar da ta yi, ta miƙe ne, ya hanashi ƙarasa maganar. "Me haka?" Ya tambayeta tare da miƙewa tsaye. Kuka tasa, "Wallahi ni kam gida zan tafi gobe, ko ba asani ba sai na gudu, ba zan zauna ba. Au Inno da Baba cewa suka yi in yi kwana biyu in dawo. Haka kawai a wani ce in zauna! Alƙur an gobe guduwa zan yi." Ta faɗa tana mai ƙara rushewa da kuka. Duk rarrashin da yake yi mata, kamar zugata yake yi, ganin ta ƙi ta yi shiru yasa shi fita ya nufi ɓangaren Daddy. Tare ya samesu, ya sanar da su abinda ke faruwa. "Je ka ƙiramin ita." Daddy ya faɗa. Da sauri ya koma ya ƙirata. Tare suka taho tana sharar ƙwalla. Suna isowa ta ja burki daga bakin kafet ɗin. "Zainab!" Daddy ya ƙirata yana kallon fuskarta. "Me ya sa kike kuka? Ba ki son zama da mu ne?" Kai ta girgiza, "To, banason kukan nan, anan za ki ci gaba da zama, zan samo miki makaranta ki fara zuwa." Hawaye ne ya sake gangaro mata ta goge, cikin rawar murya ta ce, "Baf... fa! Sau... Ra...kwana biyar a..." Ta kasa ƙarasawa. Hajiya ta ce, "A yi miki aure ko? Zainab ai karantun ya fi, idan kika ƙara girma kinga sai ki yi auren ko" Bata amsa ba, kanta na kasa, sai Daddy da ya cigaba da cewa, "Ni na rasa ma rashin hankali irin na Ilu! Ya rasa wa zai ba Mai Unguwa sai wannan 'yar. Wannan da hukumar kare hakkin ɗan Adam zasu ji sai sun kamashi." "Ni da aki zancen auren na ɗauka ma tsaranta ne." "Ina fa! Ke Zainab, tashi ki je, Allah ya yi miki albarka kin ji." A hanzarce ta miƙe ba tare da ta amsa addu ar ba. Afreen kam murna yake, kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha, ya bi bayanta yana ƙiranta. Ko kulashi ba ta yi ba, saima shigewa ɗaki ta yi ta rufe da makulli. Bugu yake a hankali yana faɗin, "Baby filis ki buɗe za mu yi magana kin ji?" "Daga ciki ta ce, ka je can ka sami Baby, ni ba yarinaya bace. Kuma tafiya gobe kamar na yi ta ne." _Ummyn Yusrah_ [11/17, 9:36 AM] Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Jamila K Mashi na gode sosai da cover, ga kyautan shafi gareki in ji Abullen Gayu, Allah ya bar zumunci._ _33_ Ganin taƙi buɗewa ne, ya ce. "Ki fito to, mu je mu ci abinci." "Ba zan ci ba." Ta bashi amsa daga ciki, Cikin sanyi jiki ya juya, yasan faɗa kawai take yi, ba wani gudun da zata iya tunda ba sanin garin ta yi ba. "Amma Alhaji ka sanar da shi Ilun kuwa?" Hajiya ta tambayeshi, "Idan zan yi iko da abin Ilu sai na nemi izininshi? Da ita da shi duk abun iko na ne don haka ba sai na roƙeshi da ya bar mun ita ba." "Amma Alha...!" Ya katseta, "Amma me? Don Allah ki bar zancen nan, na riga na yanke hukunci." "Shi ke nan!" "Tunda gobe Litinin ne, kisa Afreen ya dubo makarantar da za a sata." "To, Allah ya kai mu." Tana son magana, sai dai ba hali, tasan halin mijin nata. Abu ƙaɗan ne zai tunzurashi. *** Inno ce ta fito daga cikin kicin hannunta ɗauke da tire an jere kwanukan abinci a kai, ta ajiye a kan tabarmar da ke shimfiɗe a jefen ɗakin kwanansu. "Muntari! Zo ka miƙa masu Malam abincin nan a waje." Muntari da ya yanko lomar tuwo zai kai baki, ya ce "Allah sarki Inno! Abinci fa nake ci." "Kaga ɗan nema! Tun ɗazu ka iza ƙwano a gaba sai juya gaya kake cikin miya ka kasa cinyewa, kamar wanda aka aje ma abincin gari guda." "Inno da zafi ne fa." "Sai ka ajiye, ka zo ka miƙa musu." Tasowa ya yi, yana suɗe hannu, yana ƙunƙuni. Ta ɗaura mishi kenan, su ka ji an bugu ƙofar gidan. Cikin sauri yake tafiya tamkar mai shirin tashi sama. "Inno! Abullen ta dawo kuwa?" Ya tambaya lokacin da ya iso wajen su Innon. "Shiru dai Malam! Ina tunanin Alhaji ne ya tsaida ita, amma duk rintsi ai gobe nasan zata taho, ko kuma su taho gaba ɗaya goben." "Allah ya kai mu. Ina salula ta? Ki fitomin da ita, da safe sai in je can bayan gari wajen da ake zamun zaren sadarwa in ƙira Yayan don in tabbatar." Ta tafi ta ɗauko mishi a cikin fantimoti, ta miƙa mishi ya yi waje. Muntari kuma ya dawo daga kai musu abinci ya koma kan ƙwaryarsa, ya ɗora daga inda ya tsaya. *** Duk yanda yaso rabuwa da ita ya kasa, ya yi sintirin zuwa ɗakin nata ya fi a ƙirga ta ƙi ta buɗe. "Shi ke nan, tunda kin ƙi buɗewa barin je in faɗa ma Daddy kin ce baza ki zauna ba. Kuma cikin dare za ki gudu." Jin alamar tafiya ya sa ta taso da sauri ta buɗe, ya turo ƙofar yana dariya, "Matsoraciya kawai." Tsaki ta ja a hankali ta zabga mai harara. Tahowa ya yi, yana faɗin, "Lallai ma yarinyar nan! Ni kike yi ma tsaki da harara? Sai na yanke wannan bakin na kuma soke idanun da allura." Ganin ya nufota yasa ta fara yi mai magiya, "Don Allah Yaya ka yi haƙuri, ai dai ka san ba da kai nake yi ba ko?" Tana maganar tana zaro idanu, tare da karkaɗa hannaye alamar kar ya ƙaraso. "Idan ba da ni ki ke yi ba da waye? Mu biyu ne ai kawai a ɗakin." "Nima ban sani ba, kawai dai ji na yi ya fito." "To, kada ki sake yi min tsaki, ba kyau. Idan kika sake sai na murɗe bakin." Rufe bakin ta yi, "Bazan sake ba Allah." Dariya ya yi, ya tsaya, "Matsoraciya! Wuce mu je ki ci abinci." "Ni na ƙoshi." Ta faɗa tana share idanu. "Me kika ci?" "Ba komai." "To, wuce." "Allah Yaya na ƙoshi." "Yau kuma Yaya? Ina Afrij ɗin?" Ya faɗa yana kallonta, bata amsa shi ba, ya juya alamar tafiya, "Barin je in ce ma Daddy kin fasa tafiya goben. Dama na riƙe shi ya barki ki tafi, tunda kin ƙi cin abinci shi ke nan." Da gudu ta biyoshi, "Don Allah Yaya kada ka faɗa, mu je zanci ka ji." Kallonta ya yi, tana share idanu fuska sake, kamar ba ita ce mai kuka yanzu ba. Girgizar kai ya yi, tare da murmushi, ya nuna mata hanyar fita "Wuce mu je." Har wajen cin abincin suka isa. Anan suka iske Lubna tana cin abinci. Kai ta ɗaga kalle su ta matse baki, ta sake mai da kai ƙasa ta ci gaba da cin abincinta ba tare da ta tanka musu ba. _Ummyn Yusra_ [11/18, 8:29 AM] B²: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Mmn Nour da Beauty Queen kwament ɗinku na ƙara tunzurani, hanani dakatawa da rubutu yake, ku riƙa yi min sese-sese in samu in ƙarasa. Ina matuƙar godiya, Allah ya bar zumunci._ _34_ Ko kaɗan ba ta jin daɗin hanjin baturen (taliya) da take ci, duk da haɗuwarshi da ɗanɗanonshi, jinshi take yi kamar maɗaci. Kaɗan ta ci, ta miƙe za ta tafi. "Ina kuma za ki je?" Afreen ya tambayeta. "Ni fa na ƙoshi ne." Kallonta ya yi, "Kin ƙoshi? Tafiyarki ba gobe ba." Ya faɗa yana miƙewa, Harara Lubna ta bisu da shi, ta ja dogon tsaki. "Kai meye naka a ciki don ta ƙi ci? Cikin ta ne, idan ta ci ruwanta in ta ƙi ci ruwanta. Yunwa ai ba ƙanwar gyatumar mutum ba ce." Tana gama faɗa ta bar wajen. Kallo suka bi ta da shi har ta ɓace. Afreen ya ce, "Shareta dallah! Ki cinye wannan yanzu, barin je in samu Daddy zai ban aike ko za ki rakani?" "Yaya don Allah to ka roƙarmin shi ka ji?" "Idan kin ci abinci da yawa ba." Yana barin wajen itama ta koma ɗaki ta sa makulli, zuciya fal! tunanin hanyar da za ta bi gobe ta gudu gida, don ta ga Afreen tsokanarta kawai yake yi. Tunda ya je Daddy ya ba shi aika, bai dawo ba sai wajen goma da rabi, har ya nufi ɗakin sai kuma ya juyo don ya san yanzu kam ta yi barci. Haka nan ya koma ɗakinshi ba don ya so ba, so ya yi su sha hira, ya kuma rarrasheta ta yarda ta zauna. **** Ƙauyen Kurmawa "Kun san Allah! Idan har ba ku nemomin Hamusu ba, gobe za ku wayi gari ku rasani." Cewar Inna Talle da ke ƙwance jiki ba baɗi, ƙaninta da matanshi biyu zaune a ɗakin. "Yaya Talle ki yi haƙuri, gobe Salele zai je can Mai Ludayan ya ji ko shi Hamusun ya dawo, idan kuma bai dawo ba sai ya wuce can Jinjin ɗin." "Wani Salelen? Ina tunda kuka zo kuka ɓoyeni a wannan ƙungurmin jejin ban sake jin labarin Mai Ludayan ba. Da barina kuka yi a can ni ya fiye min wannan waje da sai a shekara ba a ji me ke faruwa a gari ba." "Yaya Talle ki yi haƙuri! Kinga ba lafiya ne da ke ba, ki kwantar da hankalinki, Hamusu zai dawo In Allah iyarda." "Ke Talatu! Wani kwanciyar hankali kuma? Ai idan ba Hamusu na gani ba ba ni da wani kwanciyar hankali." "Ki kwanta goben in Allah i kai mu za a tafi a nemo shi." "Kin tabbata dai ko Delu?" "I, Yaya." "To, Allah I kai mu. Wannan yarinya ta cuceni, ita tana can da iyayenta hankali kwance, ni nan sun bar ni cikin kogin tunani." Ta faɗa tana gyara kwanciyarta gami da sharar ƙwalla. "Ai haƙuri Yaya, za a nemo shi." "To, Hi ke nan ai, amma sai Allah ya sakamin duk wanda ke da hannu kan ɓacewar ɗan nan." "Ai Haƙuri dai Yaya! Ai haƙuri." Shi ne kawai kalmar da suke binta da shi. *** Duk yadda ya so ya yi barci abun ya gagara, juyi kawai yake yi, ga kuma kewar Ɗanliti da ya tafi yau garinsu, ga kuma kewar sahiba Abulle da Innarshi. Wunin yau duk bai ji daɗin shi ba, ga kuma daren ma ba daɗi, zai yi ƙoƙari ya tara kuɗin moto ko a ɓoye ya ga Innar shi ya dawo, don ko kaɗan ba ya fatan haɗuwa da wani da zai ba shi labarin auren Abulle. Gudun hakan ya sa ya daina zuwa tashar da zai haɗu da 'yan garinsu. Amma kuma dole ya je ya ga halin da Inna Talle ke ciki, yana ji a jikinshi tana cikin wani hali. A haka har ɓarawo ya yi awon gaba da shi. Bai jima da barci ba, ya tashi a firgice sakamakon wani irin mummunan marfarki da ya yi. Mummunan mafarki, kai! Tunda gani ya yi an taru ana ɗaurin auren Abullen shi. Zama ya yi dirshan, ya cusa kanshi tsakanin cinyoyinshi ya shiga rabzar kuka mara sauti, haɗe da ƙunan zuciya. Duk da bai kasance mawaƙi ba, dalilin soyayyar Abulle ya tsinci kanshi da jero wasu baituka. Ƙaunata taki ce, ina jiranki masoya. Duk rintsi duk wuya, ƙaunarmu na nan ba rabewa. Munyi nisa yau da juna, amma a zuci muna a tare. Ya sake rushewa da kuka. *** Yau ma dai haka Abulle ta tashi da shirin tafiya, duk da an sanar da ita ba tafiyar, sai dai tana ji a ranta ba abin da zai hanata tafiya a yau. Kawai zancen su suke yi, ai dai tana da Murtala taƙwas a bakin zaninta kuɗin adawo lafiya da mutane suka ba ta lokacin da za su taho da Inno. Shi za ta yi kuɗin babur daga nan zuwa tasha, idan ta isa ta san masu moton za su ɗauketa, idan ta hau babur daga Tasko ta shiga mai Ludaya za ta karɓi kuɗin su gurin Inno ta kawo musu. Murmushi ta yi da ta gama wannan tunanin. 'Tashar ina za ki ce a kai ki to?' Zuciyarta ta tambayeta 'Ɗayyabu!' lta ce amsar da ta sake samu, wajenshi kawai za ta iya samun kwatancen tashar da kuma inda za ta sami moto, don ba za ta iya gane hanya ba idan ta fita, ta dai san titi. Cikin farin ciki ta miƙe ta nufi ƙofar get. _Ummyn Yusrah_ [11/19, 6:57 PM] Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Wannan shafin gaba ɗaya sadauƙarwa ne gareku 'yan *Hazaƙa writer's association* Allah ya ƙara muƙu hazaƙa, basira, da ɗaukaka mafi daraja. Ina alfahari da ku kamar yadda Abulle ke alfahari da kasancewarta amarya a gidan mai unguwa._ _35_ "Innar Abu!" Ilu da ya fito cikin shirin fita ya ƙirata. Da sauri ta fito daga ɗaki, ta ɗan rusuna can gefe. "Zan wuce, so nake kafin rana ta hudo na dawo, kin san kuma yau litini Yaya zai fita da wuri, gara in sanar mishi ya turota da wuri sabida yanayi na hanya." "Da wannan kam! Adawo lafiya, idan an samesu a gaishesu." Ya fice, itama ta koma ɗaki ta cigaba da gyara, don zuwa anjima gidan nasu zai cika, yau za a zo wanke-wanken amarya. "Malam Ilu! Malam Ilu!!" Daga can nesa ake ta ƙwalamasa ƙira, tsayawa ya yi, har mai ƙiran nasa ya iso, suka miƙa ma juna hannu alamar gaisuwa. "Malam Ilu ina zuwa haka, kake ta zuba sauri ka nufi wajen gari?" "Wallahi so nake in je wajen zaren sadarwan nan in ƙira Yayan Jinjin, kasan yarinyar nan ta je yi musu sallama, jiya muka yi zata dawo, na ji shiru shine zan lalubosu ta salular nan." "Ayya! Biki ya ammatso. Nima nan itace na je ɗebowa, idan na kai musu zan wuce jana'izar ɗan gidan Ɗan Asabe." "Ashsha! Rashi aka yi ne a gidan bani da labari?" Malam Ilu ya tambaya "I, wallahi. Jiya yaron nan Hudu da abokinshi sun tafi biki can Guwal, suna dawowa cikin talatainin dare suka sami haɗari a daidai tudun mun tsira." Sallallami ya shiga yi, yana faɗin, "Wannan waje ba kyau ko kaɗan. Allah ya jiƙansu, ai sai mu je, idan an kai su na dawo in yi ƙiran. Ban ji labarin mutuwar ba, sai yanzu." Ya faɗa lokacin da suka rankaya cikin gari. *** Tunda ya dawo daga sallar asuba yake ƙawance, tubka da warwara kawai yake, ga kuma wani irin yanayi da yake ji a jinkisa wanda ya kasa gane na mene ne? ga rana har ta hudo. Haka nan ya miƙe jiki ba ƙwari, ya ɗauraye ƙafafuwansa ya mulkesu da mai ya ɗau tiren gautarsa ya rufo ƙofar ɗakin nasu, ya nufi kasuwa gurin da suke sari. Zuciyarsa cike da tunanin Innarsa ko awani hali take. *** Cikin wayo da dabara, ta yi ta tambayar Ɗayyabu tashan da ake shiga motar zuwa Mai ludaya, ba tare da ya kawo komai a ransa ba ya sanar da ita, har ma da abubuwan da bata tambayesa ba. Suna zaune Daddy ya zo wuce wajen aiki, Afreen ma ya fita. Ganin haka yasa ta miƙe ta nufi cikin gidan. Ba kowa a falon, da sauri ta nufi ɗakin da take ta ɗauko jakar kayanta. Tana shirin fita daga ɗakin Lubna ta leƙo. Kallon sama da ƙasa ta yi mata, a razane ta yar da jakar. (Abinka da mara gaskiya.) "Ki zo inji Hajiya." Ta faɗa ta juya Haushi da baƙin ciki ne ya dirar mata lokaci guda. Naushin jakar tayi da ƙafarta ta yi waje. **** Ya kai kusan minti ishirin a wajen yana kai komo a wajen, neman zaren da zai sadasa da Baffa, shiru ba labari. Ƙarshe dai sai da ya hau kan bishiya ya ɗaga wayar sama na ɗan lokaci kafin abinda yake nema ya samu. Magana ya shiga yi tamkar wanda ya tara bataliya guda, yake da burin kowa ya ji abinda yake faɗa. Fuskarsa kawai zaka kalla ka tabbatar da cewar saƙon da yake son isarwa bai sami karɓu ba. Bai kai ga ƙare maganar ba, daga can aka datse wayar, haka ya sauƙo ya nufi gida jiki ba ƙwari tare da tunanin yanda zai tunƙari Mai Unguwa da zancen da kuma yanda mutanen gari za su tasasu a gaba. Turus! ya ja ya tsaya lokacin da ya iso ƙofar gida, take fuskarsa ta bayyanar da alamar mamaki. **** Hajiya dake zaune a falo tana ta rarrashin Abulle da ta cire damuwa ta kuma saki jikinta wayar ta da ke jefenta akan kujera ya fara ruri, dagawa tayi, ganin sunan Alhaji yasa ta yin murmushi, ta latsa koren madanni ta kara a kunnenta. "To, gani zuwa." Amsar da ta bayar kenan ta miƙe, tana tunanin me kuma ya dawo da Alhaji gida a wannan lokacin, ƙarfe sha ɗaya na safe. Miƙewa tayi, tana faɗin, "Bari je Daddynku ne ya dawo, zan zo yau a bani labarin garin Mai Ludaya da Mai Unguwa." Tana wucewa Abulle ta bi bayanta da harara, don duk maganar da take yi ba fahimta take ba. Yare ɗaya ne kawai a yanzu zata iya ganewa shi ne 'Shirya ki tafi gida.' ga dukkan alama kuma basu shirya hakan ba. 'Ki gudu kawai ba tare da kin tsaya ɗaukar jaka ba.' Tana kai nan ta miƙe ta nufi hanyar waje, cikin sa a kuwa taga ba Ɗayyabu mai gadi a wajen. A wankali ta buɗe ƙaramar ƙofar da ke jikin get ɗin ta fita. Tana fita kuwa ta sa gudu iya ƙarfinta. *** A tsaye ta sameshi a falon, rai ɓace. "Alhaji! Lafiya kuwa?" Ta tambayesa lokacin da ta ƙarasa shigowa. Juyowa ya yi ya kalleta. "Ina yarinyar nan?" "Wacce? Lubna?" "Zainab!" "Au! Yanzu na barota a falo." "Ta shirya, yanzu Tukur zai zo ya maida ita, ya je shan mai ne." Ido ta zaro, ta ce "Lafiya Alhaji?" "Ke dai ki yi abinda nace kawai." _Kun makaro, sai dai ku tura jakar kayan abulle._ _Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _37_ "Don Allah Alhaji me ke faruwa ne? Ka sanar da ni mana." Ta faɗa tana kallon fuskarsa, Zama ya yi, yana girgiza kai cikin takaici, sannan ya zauna. "Da na ɗauka ina da iko da 'ya'yan Ilu a matsayinsa na ɗan uwana, sai dai yau ya gwadamin akasin hakan." "Alhaji ban fahimta ba fa! Don Allah ka sanar da ni, me ke faruwa." "Wai har ni Ilu zai ƙira ya ce in turo yarinyar nan gida?" Zama ta yi, tare da jan numfashi. A tunaninta ma wani gagarumin al'amari ne, sai dai sanin halin mijin nata na mai da ƙaramin abu ya zama babba ya sa ta ce, "Alhaji! Wannan ai ba abun tashin hankali da ɓacin rai ba ne, shi ya sa na ce tun farko a sanar da su zaman nata." Wani irin kallo ya watso mata mai cike da jin haushi, "Wannan ne ba abin tashin hankali ba? Ina yi mishi bayanin zata zauna a nan ta yi karatu, yana faɗamin an riga an sa mata rana, idan aka fasa hakan zai iya shafar kima da mutunci na gidanmu, sabida rashin wayewa irin na mutanenmu. Ki je ki sallameta, ko ɗaurin auren ma ba zan je ba. 'yarsa ce ya yi duk yadda ya so da ita." Ido ta zaro, "A dai yi haƙuri abi komai a hankali. Ya kamata ka karɓi uzurinsa, idan ya so, sai ka je can ɗin ka yi masa bayani yadda zai fahimta, idan ya so, sai a sami shi Mai Unguwar ya janye batun auren, inaga hakan zai fi." "Ba inda za ni." Ya faɗa yana ciro waya a aljihu, danne-danne ya yi, kafin ya kara a kunne. "Kan ina?" Abinda ya faɗa kenan, ya ɗan tsaya jim! Kafin ya sake magana. "Ka dawo kawai an fasa zancen karatun, yanzu Tukur zai kai ta gida." Ya katse wayar, ya sa hannu a aljihu ya ciro kuɗi. "Ga dubu goma nan ki bata, idan zaku tafi sai in baku kuɗin da za a yi hidima da shi." "Amma Alhaji sai naga kamar ka yi saurin yanke hukunci, da dai an je can ɗin an yi musu bayani in..." Dakatar da ita ya yi, "Bana son wani dogon zance, kema idan kinga ba ki da ra ayin zuwa sai ki zauna." Miƙewa tayi, ta bar falon gaba ɗaya, don ta san yanzu sai ya dawo kanta. Sam bata ji daɗin yadda ya yi saurin yanke hukunci ba. Ɗaki ta nufa, manyan kwalaye ta ciro guda uku, ɗaya setin kula mai huɗu, ɗaya kuma, setin kofuna da jug ɗayan kuma setin tukwane. Tana cikin jeresu a cikin wani buhu ne, Afreen ya shigo, hankali a tashe. "Mommy wai da gaske Zainab tafiya zata yi?" Ɗagowa ta yi, fuskarta da alamar rashin jin daɗin tafiyar nata, ta ce "Hummm! Haka Daddynku ya ce." "Mommy to me ya sa?" "Ka sanshi ai, da maida ƙaramin abu ya zama babba. Yanzu haka ya yi ma maganar Babanku rashin fahimta ne, ya hau dokin zuciya." Zama ya yi a bakin gado, "Daddy Ho! Me Baban ya ce ne Mommy?" Nan ta labarta masa yadda aka yi. Matsowa ya yi kusa da ita, ya riƙo hannunta yana faɗin, "Mommy don Allah ki roƙe sa ya barta, idan ta koma tsohon nan zasu aura mata, kinga kuma da ƙuruciyarta za a cutar da ita. Don Allah Mommy!" Ya ƙarasa maganar tamkar mai shirin yin kuka. "Afreen! Da da yadda zan yi in hana da na yi, sai dai babu, Alhaji ya riga a tirje, sai dai mu yi haƙuri. Idan yaso ko gobe ne sai mu shirya mu tafi, daga can mu rokesu ko Allah zai sa su yarda." "Allah yasa." **** Manyan buhunan biyu aka sauƙe da kwandon kayan miyu, tumatur biyu, tattasai biyu, attaruhu ɗaya, da ƙaramin buhun albasa, da jarkar manja a ƙofar gidan Ilu. Ana gama sauƙewa, sarkin fadar Mai Unguwa ya biya masu amalanken kuɗinsu suka juya. Ilu da ya yi mutuwan tsaye don mamaki ne yasa ya yi saurin ƙarasawa wajen, ganin Sarkin fadan na neman ɗan aika zuwa cikin gidan. Yana isowa, Sarkin fada ya fara, "Ranka shi daɗe! Kaga uban Abu, sirikin babban mutum. Kaga zuriya masu rabo da babbar sa a! Mai Unguwa aiko ni, ya ce ga shinkafa a yi ta dafa ma jama'ar garin Mai Ludaya da maƙwaftanta kowa ya shaida, bikin da ba a taɓa yin irinsa ba, ba kuma za a taɓa yi ba." Gaba ɗaya Ilu ya rasa bakin magana, domin bai san me zai ce ba a yanzun. Yana buƙatar kaɗaicewa don samun damar tunanon mafita. Yaƙe ya yi, wanda ya fi kuka ciwo. Hannu ya sa a aljihu ya ciro naira dubi, gudan ɗari biyar, sai gudan ɗari biyu, sai gudan ɗari, sauran duk gudan goma ne da ishirin, sai hamsin. "Gashi ka zo yau ban fita ba balle in ba da na goro, ga wannan ba yawa, a yi haƙuri. Tukwuici na musamman na zuwa da izinin Allah." Karɓa ya yi ya jujjuya su alamar sun yi kaɗan, kafin ya cusa magoginsa a baki ya goge haƙorarsa ya furzar da tukar kafin ya ce, "To, ai shi ke nan, tunda dai mai yawar na hanya, ai ba damuwa. Idan an shiga a gaida gimbiyar." "Zata ji." Cikin zaƙuwa ya amsa masa, don ya zaƙu ya tafi. Yana tafiya ya nemo majiya karfi suka tayashi kwansar kaya. Kafin ka ce me, zance ya zaga gari, irin kayan abincin da Mai Unguwa ya tura gidansu Abulle. _Ummyn Yusrah_ [11/22, 9:13 PM] Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _An sami kuskuren lamba a shafin da ya gabata. 36 ne aka sa 37._ _37_ Fitowa ta yi daga maɓoyarta, wanda ta ɓoye lokacin da ta hango motar Afreen ya shigo layin. Waige-waige ta shiga yi, daga bisani ta juya ta cigaba da zuba sauri tamkar mai shirin tashi sama. Wani nannauyar ajiyar zuciya ta yi, lokacin da ta iso bakin titi. Kallon yadda ababen hawa ke kai kawo kawai take yi, ta rasa ta ina zata fara tsaran abun hawa, ga jikinta dake ta kaɗawa tamkar mazari **** Mommy! Yanzu ina take?" Kallonsa ta yi, "Tana falo ai, can na barta." "Shigowata banganta ba, wataƙila ko don ban kula bane. Barin dubata." Ya miƙe ya fita. Kai tsaye falon ya nufa, bai ganta ba, ya nufi ɗaki, bata ciki, sai jakarta da ke ajiye a tsakar ɗakin. Tunaninsa ne ya bashi, tana banɗaki, me yiwa ta na wanka ne. Hakan ya sanya ya koma ɗakin Mommyn suka ci gaba da tattaunawa yanda zasu yi don ganin an fasa auren Abullen idan sun je goben. *** Duk kayan da aka shigo da shi, ɗaki ɗaya aka tarasu. Cikin sanyin jiki Ilu ke yin komai. Ganin mutane sun fara taruwa a gidan ne, ya buƙaci da su keɓe a ɗakinsa da Inno don jin yadda suka yi. "Malam me ya faru ne? Duk naga jikinka ya yi sanyi. Ba dai wani abin ne ya sami mutanen Jinjin ɗin ba?" Inno ta tambayesa lokacin da ta shigo ɗakin ta ganshi zaune ya taƙure, fuskarsa kuma na bayyanar da alamar damuwa. "Bari kawai! Yaya ya ce Abulle ba za ta dawo ba, yanzu haka makaranta zai sa ta." "Malam! Auren fa?" "Na yi masa maganar, sai dai ya ƙi ya saurareni, ya kuma karɓi uzurina." Ƙirjinta ta buga da hannayenta duka biyun tana mai kallon sa. "Yaya kam, nema yake ya ja mana abun magana a gari." "Na ma rasa ta cewa nikam." "Yanzu Malam meye abun yi?" Cikin yanayin damuwa ya ce, " Ni kaina ban san ta ina zan fara ba. Ga kuma kaya da Mai Unguwa ya turo da shi, a yi amfani da shi wajen shagalin buki. Ban san ta ina zan fara sanar da shi zancen Yaya ba! Ban san da wani ido zan kalli jama'ar garin nan ba. Ta dalili hakan duk wani kima da daraja ta zuri'armu zai iya shafa." Don numfashi ta ja, "To, Malam! Ko dai komawa za ka yi ne ka gwada ƙiran ita Hajiyar ta lallaɓa Yayan ya barta ta dawo?" Miƙewa ya yi, yana zura takalmarsa a ƙafa, yana faɗin, "Haka ma za a yi, barin je yanzu. Ku cigaba da shirye-shirye kada ki nuna wani alama da mutane za su gane akwai matsala." "To, a dawo lafiya. Allah yasa a dace." "Amun." Yamsa ya fita, itama ta koma suka ci gaba da aikinsu. *** Ko kaɗan baya jin daɗin tallar yau, badon kuɗin mota da yake son tarawa a yau gobe ya wuce gida ba, da ba abinda zai sa ya fito. A haka yake yake bin tituna, idan ya ga lungu ya shiga, sai dai cikin da sauƙi. Gidan Alhajin da ya zubar ma shara ne ya faɗomasa. Cikin azama ya ɗau hanyar Unguwar zuciyarsa cike da fatan samun nasara. **** "Ina Zainab ɗin?" Mommy ta tambayi Afreen lokacin da ta fito, ta gansa zaune a falo. "Ban sameta a falo ba, na leƙa ɗakinta bata ciki, ina tunanin wanka ta shiga." Ya bata amsa "Wani irin wanka ne haka har yanzu? Alhaji ya fara magana, ta shirya kafin Tukur ya maida shi wajen aiki ya zo ya kaita, ya dawo." Ta yi maganar tana tafiya ɗakin don ganin irin wankar da Zainab ke yi, wanda ya hanata fitowa har yanzu. Shima ɗakin Lubna ya nufa, kwance ya sameta, tana daddana waya. Bayan ya shiga ne, ya zauna kan kujerar. "Yau dai mutumiyarki zata tafi ki huta." Ya faɗa yana dariya, Ɗagowa ta yi, tana yi masa kallon rashin fahimta. "Wace mutumiyata kuma?" "Zainab!" "Tafiya kuma? Daddy ai ya ce zata yi karatu anan ko? Ba ɗazu ka fita duba makarantar da za a sata ba?" Ta jero masa tambayoyin, kallonta ya yi, ya ce, "Kinsan Daddy ai! Abu kaɗan ke harzuƙasa." "Me aka yi to?" Nan ya faɗamata abinda Mommy ta faɗamasa. Karo na farko kenan da ta ji batason tafiyar Abulle, zata je ta roƙi Daddy ko zai yi haƙuri, ya je ya ba Mai Unguwa haƙuri ya haƙura da auren zuwa wani lokaci. _Ummyn Yusrah_ [11/22, 9:14 PM] Ummyn Yusrah🧚🏼‍♀: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _38_ "Ina kuma zaki je, kin barni a zaune?" Ya tambayeta, lokacin da yaga ta ɗau hanyar fita daga ɗakin ba tare da ta yi masa magana ba. "Zan sami Daddy ne." Abinda ta ce kenan, ta yi gaba ba tare da ta jira taji me zai ce ba. Keɓe baki ya yi, ya ɗage kafaɗunsa fili ya ce, "A dawo lafiya. Shalelen Daddy." Yana shirin miƙewa ne Mommy ta shigo, "Zainab fa bata ɗaki, na duba banɗaki ma bata nan." Cikin mamaki ya ce, "Bata ciki kuma? Ni dana ga bata ɗakin na yi zaton banɗaki ta shiga." "Bata nan kam, zo ka duba ko tana kicin. Barin sanar ma Daddynku tana shiryawa." Ta juya, shima ya fice zuwa kicin. *** Yana tsaye, ya kara waya a kunnensa, yana sarma Tukur da ya ƙirasa yana sanar masa ya iso, ne ta shigo. Sauƙe wayar ya yi, ya kalleta "Mamana yaya aka yi?" Ƙarasawa kusa da shi ta yi, ta riƙo hannayensa duk biyun, ta ce "Daddy! Don Allah kada ka bar Zainab ta..." Cire hannunsa ɗaya ya yi daga nata, ya ɗaga mata alamar ta dakata yasa ta katse zanceta ba tare da ta kai aya ba. "Idan dai kan wannan zancen kika zo, to na riga na rufe shafinsa. Idan kuma da makasudin zuwan naki, ki sanar da ni, zan koma wajen aiki ne." Girgiza kan da ta yi, ya yi daidai da gangarowar hawaye daga idanunta. "Kuka kuma Mamana? Indai zaki bita maza ki shirya ku tafi, idan an yi bikin sai ku dawo." Yana kaiwa nan ya yi waje, don baiso ta matsamasa ya santa da naci. Cikin sanyi jiki ta bar falon zuwa wajen su Mommy da ke ta neman Abulle. Duk wani saƙo da lungu na gidan sun bincika ba ita ba dalilinta. Har Ɗayyabu suka tambaya ko ta fita, ya sanar da su bata fita ba, ɗazu dai sun jima da ita anan daga bisani ta tashi ta koma ciki. Abu wasa-wasa, sai gashi yana neman zamewa gaske. Suna tsaye cirko-cirko tamkar zakarun da suka ƙoshi suna neman abokan gwabzawa ne a harabar gidan, cikin tashin hankali, ƙira ya shigo wayar Mommy. Sunan da ta gani ne, yasa gabanta ya yi mummunar bugawa. Sau biyu tana tsinkewa taƙi ɗagawa, tunaninta idan ta ɗaga ya tambayeta 'yarsa ta ce masa me? Bata shirya wannan amsar ba a yanzu, domin batasan wani irin ruɗani zasu shiga ba, domin a yanzu ma tasan cikinta suke, tunda har taga ƙanin mijin nata ya ƙirata. **** Ya yi tsaki ya fi a ƙirga. Gashi dai wayar na ƙara, amma anƙi ɗagawa, tunaninsa kada dai itama Hajiyar irin amsar Yayan nashi take son sanar da shi. Tunda ga alama ya nuna, ya ƙirata ta ƙi ɗagawa. Saƙowa ya yi, daga kan bishiyar, ya zube a ƙasa, ya jingina da jikin itacen bishiyar. Zuciyarsa ce ke rayamasa, anya ba zai gudu ya bar garin ba? Ya gudu ya je ina? Ita Innon kuma yaya zata yi idan ta ji labarin ya gudu. Gaskiya bai yi mata adalci ba, a ce babu shi babu Abulle, amma kuma fa yana tunanin irin badaƙalar da za a kwasa a garin, gara kawai ya gudu, idan ƙura ta lafa ya dawo. Idan yaso Inna za ji da su. Yana gama tunanin ne ya miƙe, ya ƙara cusa ƙafarsa cikin ƙwaftarsa tamkar mai shirin zuwa kiwon shanu." Ya yanki jeji, ya hau tafiya. ***** "Garbati! Ina fatan ka tura Salele ya tafi duba ɗan nan? Duk hankali na yana garesa." Inna Talle ta tambaya, lokacin da ta dogaro sandarta ta fito daga cikin ɗakin da aka yi mata masauƙi. "A'a! Yaya, keda ba ki da lafiya kuma sai fi fito? Da dai kin zauna waje ɗaya ne, kinga jikin naki duk ba ƙwari" Dalu da ta taho da sauri ta riƙe Innar ce take magana. " Indai ba Hamusu na gani a gabana ba ai zama bai ganni ba. Gara kawai in fita in nemo ɗana da kaina, tunda naga ku baku damu da batar nasa ba. Da ɗanku ne ya bata, cikinku ba mai zama a gidan nan." "Yaya ki yi haƙuri, ana iya bakin ƙoƙari wajen nemosa, za a gansa nan bada daɗewa ba." "Zaki sake ni, ko sai na dokeki da sandar nan? Kuna nan zaune ku ci ku sha hankali ƙwance ne zaki ce ana ƙoƙari? Ina shi mijin naku? Kai Garbati! Ka zo ka maidani Mai Ludaya kokuwa?" "Ki yi haƙuri, ya tafi kai Salele can Mai Ludayan, daga can zai wuce Jinjin ɗin." "Au! Sun tafi?" "Eh, sun tafi." "To ai shi ke nan, yanzu kam zan ɗan sami nutsuwa. Allah yasa a dace." "Amin Yaya, mu je ki kwanta." "Ke ni barni! Kwanciya kamar wata ruwa. Barni a waje sha iska." "To, mu je ga tabarma can sai..." "Wannan ai iskanci ne! Hatsin ne aka bar yara suke wasa da shi?" Garbati ya fara sababi lokacin da ya shigo gidan. Da sauri Delu ta fara bubbuga hannunta a baki, alamar ya yi shiru. Ai kamar ta ƙara tunzurasa "Lallai Delu baki da mutunci! Ina magana kina yi min nuni da in yi shiru? Wato ga sakarai ko?" Ya nufota kamar zai kai mata duka. "Wa nake ji kamar Muryar Garbati?" Da sauri Delu ta ce, "Iy! Shi ne." "Har sun dawo ne?" "Eh, da yake fitar wuri suka yi, zuwa mai Ludayan shi yasa suka dawo da wuri." Sai yanzu ya fahimci kan me ake zancen. "Eh, Yaya na dawo, da yake mun fita da wuri." "To sannu da dawowa." Ya juya, yana tunanin nacin Yayar tasa. _Ilu mai amalanke Allah ya tsare hanya_ _Ummyn Yusrah_ [11/23, 3:07 PM] B²: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _39_ Ta daɗe sosai a titin, tana tunanin yadda za ta yi ta tsare abin hawa, daga bisani ta sanya hannu ta tsare mai mashin, ganin da ta yi mutane da yawa haka suke yi. Domin a tsayuwar da ta yi mutane da yawa sun tsare kuma sun tafi. Da ƙyar ta iya tuna sunan tashar da mai mashin ɗin zai kai ta. Ganin da ya yi mata, wata kala ya sa ya cajeta murtala biyar. Ba ta damu ba, babban burinta kawai ta ganta cikin motar da zai kaita gida. Suna barin wajen, Hamusu yana yankowa, ya nufi gidan Alhaji Shitu domin aiwatar da aikinsa. Ya yi sa a kuwa akwai aiki, don haka ajiye tirensa ya yi, ya sunkuya aiki ba tare da ɓata lokaci ba. **** "Lahhhh! Alƙur'an na yi mantuwa cikin jakata." Abulle ta faɗa lokacin da suka yi nisa da tafiya. Bai kulata ba, sai ma wuta da ya ƙara ma mashin ɗin. "Malam don Allah ka maidani, na yi mantuwa ne." Ta faɗa ganin da ta yi, bai da alamar tsayawa. Masifa ya hauta da shi, "Idan na kai ki sai kin ƙaramin kuɗi, haka kuke, tsabar son abin duniya irin na iyayenku, sai suyi ta turoku birni yin aiki, don ku tara musu abin duniya, ko duba irin rayuwar da za ku faɗa ciki basu yi, abin duniyar kawai shi ne burinsu. Ke da gani ma gudowa kika yi daga gidan aikin naki ba a sani ba." Takaici ne ya kamata, meye nashi a ciki idan ma hasashen nasa haka ne? "Nawa zan ƙara maka to?" Ta tambayesa don ba ta son jan wani zance. "Mu je tukunna in ga inda zan ajiyeki, sai mu fara sabon ciniki." "Wajen da ka ɗaukoni, wajen za ka ajiye ni." "Yauwa, Ko ke fa! Gara dai ki koma, idan ya so, sai a mai dake gaban iyayeki a mutunce ai ya fi." "Yau na ga ikon Allah! Ni fa ba aikatau na zo yi ba." Ta ba shi amsa. "Ƙarya kike!" Ya faɗa har yana wani zabura akan mashin ɗin. "Idan ba aikatau ba, to menene? Ko aure za a yi miki, kika gudu?" 'Sai ka yi kuma, ni ba danginka ba, ka wani daddage. Da zan iya gane unguwar ma sauƙa zan yi in hau wani, don dai kawai kai ka ɗaukoni shi ya sa.' Ta faɗa a zuciyarta. Har suka isa inda ya ɗauketa, ba ta kuma ce masa komai ba. Haka ya yi ta zuba tamkar injin markaɗe har suka iso wajen da ya ɗauketa. Yana sauƙeta ta ba shi murtala shida. Mita ya shiga yi, daga bisani ya ja mashin ɗin ya yi gaba. **** Ɗayyabu ne ya turo ƙofar gidan ya shigo duk jikinsa ba ƙwari. "Ya ya, ka sameta kuwa?" Afreen ya tambayesa cikin zaƙuwa. "Wallahi na duba, har bakin hanya ko mai kama da ita bangani ba." Shiru ne ya gifta na wani lokaci, kowa saƙar zuci yake. "Mommy ko za a faɗa ma Daddy?" Lubna ta faɗa hankalinta a tashe. Kallonta Mommyn ta yi, "Kada mu yi gaggawar sanar da shi, yanzu Afreen da Ɗayyabu za su fita su sake dubata ko Allah zai sa a dace." "Allah yasa a ganta, In Allah ya yadda ba za ta ɓace ba." "Allah yasa Mommy!" Ta faɗa tana kwantar da kanta a kafaɗar Mommyn "Ɗayyabu kuma ka ce baka ji fitarta ba?" Hajiya ta sake tambayarsa. "Gaskiya banga fitarta ba, ina zaune a nan tun safe, sai kuma banɗaki da na shiga, bayan nan ban je ko ina ba." Ya bata amsa. "Ku je da Afreen ku sake dubata to." Afreen kam ya ma kasa magana, gaba ɗaya jin lamarin yake kamar almara. Lokacin da take faɗamasa ko ba a sani ba sai ta gudu, ya ɗauka kawai faɗa take, ashe zancen gaskiya ne. Lallai kowa ya raina mai labari, in kaga mai gudu shi ne. **** Har ya ɗau hanyar fita daga gari, sai kuma zuciyarsa ta yi ta tunatar masa da rashin adalcin da yake shirin aikatawa. Gara yakoma ya sake ƙiran Hajiyar, wataƙila ta ɗauka sai ya yi mata bayani. **** "Kai Afreen! Ka ko ji abinda nake cewa kuwa?" Mommy ta taɓa shi, kafin ya dawo daga dogon hanyar da zuciyarsa ta ɗauka, na tunani. "Na'am!" Kallonsa ta yi, "Na ce ka ji me na ce kuwa? Ku je da Ɗayyabu ku sake dubo..." Ƙiran da ya shigo wayarta ne ya yi silar katsewar maganar da take. Ba yadda ta iya, dole yanzu ta ɗaga wayar tasa. Sai da ta tattaro duk wata natsuwarta kafin ta ɗaga, gudun kada ya fahimci wani abun daga gareta. A daidai lokacin da suke jimamin ɓatan 'yarsa. Bayan gaisuwa ba tare da ya jira komai ba, ya fara wassafomata bayani da yadda suka yi da Yayan nasa, da kuma yadda lamarin zai shafi Ahalinsu. Sosai ta fahimce shi, ta kuma basa haƙuri, ta sanar da shi cewar, za ta dawo yau, yanzu haka ma shiryawa take. Daɗi ne ya rufesa, nan ya shiga yi mata godiya, da fatan isowarta lafiya ya datse ƙiran, ya nufi cikin gari, yana mai farin ciki. "Ku je ko? Allah yasa a d..." Turo ƙofa da shigowar Abulle ne ya yi sanadin tsaida maganar tata, ba tare da ta kai aya ba. Duk suka juya, ganin Abullen ce ya sa suka ɗunguma gareta, har suna rige-rigen isa gareta. Wani irin razana da faɗuwar gaba ne ya ziyarceta a lokacin da ta buɗo ƙofar ta yi tozali da mutanen gidan, tsaye cirko-cirko a harabar gidan. Ba don sun ganta ba, da juyawa za ta yi ta gudu, ta yafe ɗaukar hotunan da ya dawo da ita. _Ummyn Yusrah_ [11/25, 8:20 AM] B²: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Ashe haka Abulle ta yi kasuwa? Ina tayata murna, ta ce a yi ma duk mai bibiyarta godiya, a kuma ƙara haƙuri da ita na rashin ganinta a kan lokaci._ _Maman Nour, Beauty Queen, Abu Hisham, Yayana. Taku gaisuwa da godiyar daban ce, har kullum Abulle ba za ta taɓa gajiyawa wajen miƙo saƙon godiyarta gareku ba, koda kuwa za ta cinye shafin nan ne, sai dai za ta taƙaita saboda masoyanta. Amma tabbas tana tare da ku a kodayaushe, tana kuma jin daɗin kwament ɗinku. Mun gode ni da ita. Saura in ji ance kalan dangi.😏 sins shis ma kozin sista ehe!_ _40_ Har wajen da take suka ƙaraso, suna tambayarta ina ta je. Ba ta basu amsa ba, sai da Mommy ta sake tambayarta, "Zainab ina kika je? Duk kin tashi hankalinmu." Hawayen da ke shirin gangarowa kan ƙuncinta ta goge, ta ce "Gida zan tafi." Duk suka kalleta, Afreen ya ce, "Gida? Kin san hanya ne? Kina da kuɗin mota ne?" Kai ta gyaɗa, Mommy ta riƙota, "Zo mu je, yanzu Tukur zai zo ya kaiki dama. Alhaji ya mayar wajen aiki, ki yi sauri ki shirya maza kafin ya iso." Da murna ta shiga ɗaki, jakar kayanta ta ɗauko, ta dawo falo wajen su Mommy da ke tattaunawa ita da Afreen. Lubna kam sai ido, don ko da Abulle ta dawo ma ba ta tanka mata ba. Mommy ta kalleta ta ce, "Yau sai gida ko?" Dariya ta yi, ta gyaɗa kai. "Muma goben muna hanya In Sha Allahu, idan an je a gaida mutanen gidan." "To!" ta ce, don ɗokima ba zai iya barinta ta yi dogon magana ba. "Afreen duba Tukur ɗin, idan ya iso yazo ya fita da kayan su tafi ka da su yi dare a hanya." Jiki a sanyaye ya fita, ba jimawa ya dawo, "Ta fito, ya iso, motar tana bakin get." Da sauri ta suri jakarta. Afreen ya ce, "Ohh! Wannan saurin fa? Kamar kin gaji da mu?" Dariya ta yi, Mommy ta ba ta saƙon kuɗin da Daddy ya bada, ta yi mata addu'a da fatan alkairi, itama ta yi godiya suka fita. Suna tsaye a jikin mota ya kalleta ya ce, "I miss You!" "Almisyu?" Ta tambayesa, "Yeah! I really miss you." Kallon rashin fahimta ta yi masa, ganin hakan ya sa ya fahimci ba ta gane abinda yake nufi ba. "Cewa na yi, idan kika tafi zanyi kewarki sosai." Murmushi ta yi, "To, ka zo mu tafi mana." "Na so hakan, sai dai ina da uzuri. Amma zamu zo da su Mommy gobe ko jibi aure." Jin an ambaci aure, ya sa yanayinta ya canza, ƙirjinta ya shiga bugawa. Haka kawai ta ji sam ba ta son auren nan, tana son komawa Mai Ludaya ne don ta ga Hamusu da mutanen cikinta ba don ayi aurenta da Mai Unguwa ba. Kallonta ya yi cikin kulawa, ya ɗaga mata gira ya ce, "Ya aka yi? Ko a fasa tafiyar ne?" Kai ta girgiza ba tare da ta ba shi amsa ba, sai ma hawayen da take gogewa. "Kukan fa? Barin je in faɗa ma Mommy a fasa tafiyar kawai." Ya juya zai tafi, da sauri ta riƙo rigarsa ta ce, "Don Allah Yaya Afreen ka yi haƙuri! Na daina." Juyowa ya yi, "To, me ya sa ki kuka?" "Nima ban sani ba, kawai dai bana jin daɗi ne." "To, ki daina kuka, ki yi ta karanta Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Za ki ji daidai." Kai ta gyaɗa ta ce, "Na gode." Hira suka ci gaba da yi, har Tukur ya fito da kaya ya sa a but, ya shiga gaban motar. Suna sallama da Afreen ne Lubna ta fito, jikinta ya yi sanyi, duk ta ji ba daɗi, haka kawai ta ji ba ta son tafiyar Abulle. Kusa da su ta iso tana faɗin, "Da gaske tafiya za ki yi?" Kallonta ta yi, ta keɓe baki, zuciyarta na faɗin 'Ji wani kinibibi! Ko meye damuwarta da tafiyata?' A fili kuma ta ce, "Eh, zan koma ƙauyenmu inda nafi wayo, inda aka san kimata da darajata." Duk sai ta ji ba daɗi, da kalaman Abullen. Hannayenta duka biyu ta riƙo, tana murmushi ta ce, "Ki yi haƙuri." "Allah ya kara mana duka." "Me fa?" "Haƙurin." Duk suka sa dariya Lubna ta ce, "Zamu zo, jibi. Me za a ajiye ma..." "Tsareta kuka yi ashe? Sai ta rasa mashin ko?" Mommy ta katse Lubna, daga maganar da take yi lokacin da ta fito. Juyowa suka yi su duka, za su yi magana, Mommy ta ce, "Shiga ku tafi, so suke ki rasa mashin ɗin da zai ƙarasa dake ko?" Jin zancen rasa mashin ya sa ta daka tsalle ta shige cikin motar. Duk suka sa mata dariya, Afreen ya rufe ƙofar ya leƙo ta taga, ya ce, "Allah ya kai ku lafiya, sai mun zo." "Amin." Ta amsa ya matsa ya rufo ƙofar. Motarsu ta ɗaga. Hannu suke ɗaga mata, itama haka har tana leƙowa ta taga. Sai da motar ta ɓace ma ganinsu kafin suka juya cikin gida zukatansu cike da kewa da rashin jin daɗin tafiyarta . _Ummyn Yusrah_ [11/25, 2:25 PM] B²: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Tsangayawa kuma ga naku. Tsangayar Marubuta da ke Fuskanr littafi (Facebook). Ina godiya, ga kyautar shafi gareku musamman Umman Maryam. Na gode._ _41_ Koda Malam Ilu ya isa gida bai iya shiga ba, don a cike yake da mata, sai kai kawo ake, ga wasu manyan tukwanen girki da aka ɗaurasu kan murhu. A zauren gidan ya tsaya, ya tura aka yi ƙiran Inno. Da sauri ta nufo wajen har tana tuntuɓe, don tunda ya fita hankalinta ke tashe. "Malam ya ya kuka yi?" Ta faɗa lokacin da ta iso, idanunta akan fuskarsa. Kallonta ya yi, lokaci ɗaya duk ta canza, hakan kuma ba zai rasa nasaba da zancen rashin dawowar Abulle da ya yi mata ɗazu ba. Da shima ya tafi da taraddadi. "Malam an dace kuwa?" Ta sake tambayarsa. Dogon numfashi ya ja. "Eh, mun yi magana da Hajiyar tana hanya." Itama numfashin ta ja, na jin daɗi, "Alhamdulillah! Yanzu hankali ya kwanta." "Suma goben za su iso, a gyara musu ɗakin da Muntari yake kwana ko?" "To, Allah ya kai mu, ita kuma Allah ya dawo da ita lafiya." "Amin, barin fita." "To, a dawo lafiya." Ya fita, itama ta koma bakin aiki. **** Gudu kawai yake shararawa, domin yana sauƙeta zai juyo, rediyo ne ke ta aiki, Abulle kuma ta afka kogin tunanin yadda za ta je ta sami Hamusunta har barci ya ɗauketa. "Hajiya Zainabu! Mun iso." Tukur direba ya faɗa lokacin da suka iso tashar garin Guwal, anan ne ake hawa mashin ɗin da zai kai mutum Mai Ludaya, don mota ba ta shiga. Miƙa ta yi, fuskarta na bayyanar da farin ciki. Gari ɗaya za ta wuce yanzu ta isa garinsu. Tafiyar kwana uku, ji take tamkar ta shekara uku. Lallai bahaushe ya yi gaskiya da ya ce, 'Kowa ya bar gida, gida ya barshi.' Tana tsaye ya gama fito mata da kayanta, Mai mashin ya tafi ya ƙira mata, ita kuma ta tafi kanti sayen oyoyo ma yara da kuɗin da Afreen ya ba ta, idan ta ga abu a hanya ta saya. Biredi manya ta saya guda biyu, sai bisko da minti mai kan ɓarawo (Lollipop). Ta samu, har mai mashin ya iso, sun tsadance da Tukur ya biyasa. Mutum biyu suke ɗauka a mashin ɗaya, sai dai yau ba zai yiwu ba domin kayanta ya tare wajen. Jakar kayanta aka sa a gaba, sai babban buhun kayan kicin ɗin da Mommy ta ba ta aka ɗaureshi tamau a baya, ita kuma ta hau tsakiya, ledar oyoyonta na hannunta. Godiya ta yi ma Tukur sosai, ta kuma ba shi sautu wajen Ɗayyabu ya taho mata da kayan jerenta da ta ɓoye, wanda ɗoki ya sa ta manta da su idan za su taho aure. Addu'ar Allah ya kare hanya suka yi ma juna. Sai da ya tabbatar da tafiyarsu kafin shima ya shiga mota ya juya lokacin ƙarfe biyar saura. **** Yau aiki sosai Hamusu ya yi, bai sami Alhajin ba sai Hajiya. Har wankin labulaye ya yi, bayan share harabar gidan da kuma zubar da shara. Ya ci ya sha ya yi hani'an. Nan ta ce ya riƙa zuwa kullum yana yin aiki, a wata ana biyansa ya fi tallar da ya ke yi. Ya ji daɗi sosai, sai dai ya sanar mata gobe zai je gida ya duba mahaifiyarsa zai yi kwana biyu, idan ya dawo sai ya fara zuwa. Da zai tafi, ta yi masa sha tara ta arziƙi ta kuma yi masa kyakkyawar sallama ya tafi yana farin ciki, yadda abin ya zo masa da sauƙi. Duk gajiyar da ya ke ji take ta washe. Ga kuɗin moto harda kyautar kaya ya kai ma mutanen ƙauye. Sosai ya jinjina karamcin mutanen gidan, ya kuma yi alƙawarin yana zuwa kwana biyu zai dawo don bayason a yi bikin abar ƙaunarsa yana garin. A haka ya isa ɗakinsu ya hau shirin tafiya. **** Tafiya kawai suke, ba ka jin komai sai ƙaran mashin, da kuma karo da suke yi da duwatsu. "Kai! Hanyar nan tamu sam ba kyau. Kodayaushe cikin sayen sabuwar taya da gyaran babur muke." Idirisu mai mashin ya faɗa lokacin da suka shige cikin yashi. "Hakan ma ai kamar da sauƙi ko?" Ta tambaya, ba tare da jiran amsa ba ta ɗora. "Na ga lokacin damina wajen ya fi haka lalacewa." "Iy! Da sauƙi kam za a ce, mun maƙale fa ina ga sai kin sauƙa mun tura." Sauka ta yi, suka hau turi. Da ƙyar ya fita, ga shi hanyar yau kamar an yi ruwa an ɗauke, ba mutane ko kaɗan, duk da wajen ba ya rabo da masu shiga ko fita daga ƙauyukansu. Amma yau shiru. Hawa ta yi suka ci-gaba da tafiya, wani sanyi ta ji ya ziyarci zuciyarta lokacin da ta hango Tudun mun tsira. Wajen wani ƙaton tudu ne, da gangara shi ya sa ake ƙira da Tudun mun tsira. Ba ko wani mai abin hawa ke iya hayewa da mutum ba, masu tsoro idan sun zo wajen sauƙa suke, wasu kuma haka suke hayewa a dari. Kariyar Ubangiji kawai ke kai mutane ƙasa lafiya. Yanzu haka an fara aikin rage tudun, saboda yawan hatsarin da ke afkuwa a wajen, aiki ne na ƙarfi da ƙarfe da mutanen ƙauyukan ke yi, don rage afkuwar hatsarurrukan. Suna isowa Idirisu ya ƙure ma mashin ɗin gudu, a ɗari ya haura. Haurawar ta sa ta yi daidai da cakar wani dutse, take duk suka yi sama, mashin da kayan da ke ɗaure suka hantsila can gefe, hakama Idirisu da jakar kayan Abulle. Ledan oyoyon Abulle da ya yi sama, shima ya watse a hankali abinda ke ciki suke dawowa ƙasa. Abulle kuma da ta yi sama, ta faɗo ƙasa yayin da kanta ya cakku da wani tsinin dutse ya nitse can. _Ummyn Yusrah_ [11/26, 7:53 AM] B²: *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _42_ Ihu ta ƙwala mai karfi sakamakon azaba, raɗaɗi, da zafin da ya ziyarceta. A razane wasu tsuntsaye saman wata ƙatuwar bishaya suka tashi Furrrr! Dalilin tsorata da suka yi da ƙarar da ta yi. Lokaci guda jikinta ya hau karkarwa, numfashinta ya shiga kaiwa da komowa, zuwa wani lokaci ya tsaya cak! Idirisu kam,tunda ya wurgu ya faɗi bai san meke faruwa ba. Tsawon mintuna kusan ishirin ba wanda ya ɓullo ta wajen. Mudi mai Jaki ne ya taho a kan keke, yana tafe yana waƙe, ya taho daga cikin garin Mai Ludaya, zai je ƙauyen da ke gaba da su. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!" Shine kalmar da yake ta maimaita lokacin da ya yi ido biyu da abinda ya faru. Da sauri ya sauƙo daga kan keken nasa, ya ƙarasa garesu, duk cikinsu babu mai motsi. Da sauri ya juya ya hau kan keken nasa ya koma cikin gari, bakinsa na maimaita 'Innalillahi wa innalillahir raji'un!' Gudu kawai yake ba ƙaƙƙautawa, yana isa cikin gari, kai tsaye gidan Mai Unguwarsu ya nufa. Wurgi ya yi da keken ya rugo da gudu, ya gurfana a gaban Mai Unguwa, har lokacin bakinsa bai daina furta kalmar nan ba. Jiki na rawa ya ce, "Rankashidaɗe! Akwai matsala. Wallahi akwai matsala." Duk mutanen dake wajen kallonsa suke. Cikin muryar tsufa da sarauta Mai Unguwa ya ce, "Subhanallahi! Wace irin matsala kuma Mudi?" "Haɗari rankashidaɗe! Haɗari wallahi a daidai tudun mun tsira. Lamarin babu kyan gani, gaba ɗayansu babu mai numfashi." Duk wajen ya dau salati, Mai Unguwa ne ya ba da umurnin a samo amalanke a kwashi mutanen a kaisu asibitin dake garin don duba halin da suke ciki. Malam Ilu da suka taho da abokinsa yi ma Mai Unguwa godiyar kayan abinci da aka kawo musu, ya miƙe cikin sauri don ɗauko ta sa amalanken. Haka kawai yake jin mummunar faɗuwar gaba, tunaninsa Allah ya sa Abulle su wuce lafiya. **** Hamusu da tunda ya gama shirya kayansa ya miƙe akan tabarma. Lokaci guda, gabansa ya tsananta bugawa, sosai ya ji jikinsa ya mutu, tunanin garinsu ya faɗo masa a rai. Tabbas akwai abinda ke faruwa. Sai dai bai san ko ga wanene ba, amma koma dai menene, abun na da nasaba da shi. Domin sauda yawa idan wani abu zai faru da shi, walau na farin ciki ne ko akasin hakan yana ji a jikinshi. Wannan alamar yana jinta ba abu mai daɗi ne ke faruwa ba. "Inna! Ina hanya gobe, na sani yanzu kina cikin mummunar yanayi. Ina zuwa gareki Innata ka da ki tafi ki barni." Nan ya yi ta sambatu har yana sharar hawaye. **** Gaba ɗaya mutanen sun tsorata da yadda suka ga hatsarin. Dukkanninsu babu alamar rai a tare da su. Cikin sauri aka cicciɓo Idirisu aka sanya a amalanke, aka yi gaba da shi, aka kamo Abulle, wacce saida aka janyota da ƙarfi kafin aka rabata da kakkaifar dutsen da ya shige kanta. Anan ne fa Malam Ilu ya yi ido biyu da ɗiyarsa Abulle. Jikinsa ne ya shiga kaɗawa kamar mazari, bakinsa na faɗin, "Innalillahi! Abuwa ce ta wajena. Ita ce!!wallahi ita ce!" Abinda yake faɗa kenan. Sai yanzu suka kula, domin da fari hankalinsu a tashe yake, basu kula da ko suwaye ba. "Ku taimakamin don Allah! Ku taimakamin a kaita asibiti, wayyo Allah!" Cikin sauri aka sanyata cikin amalanken da Ilu ke riƙe da shi, duk ya ruɗe ya fita hayyacinsa sai sambatu yake, jikinsa sai rawa yake. Ganin ya kasa tura amalanken ne aka karɓa, da gudu aka nufi hukumar kiwon lafiya a matakin farko na garin. Sauran jama'ar suka biyosu a baya da kayansu da kuma mashin ɗin. Babu likita, sai wata ma'aikaciyar jinya guda ɗaya da aka samu. Ta dai dubasu, ta tabbatar musu da cikawar Abulle, shi kuma Idirisu buguwa ya yi, shi ya haddasa masa dogon suma, zai farfaɗo, ta sanya masa karin ruwa ta yi masa allurai. Kasantuwar rashin aikin da ma'aikatan ke yi ya sa ba a wani tsaya dogon bincike da wasu ababen da ya dace ma'aikatan asibiti su yi ba. Akan yi kwana biyu ko fiye da hakan ma ba tare da an buɗe asibitin ba, yanzun ma sa a suka yi, ma'aikaciyar ta zo karɓar haihuwar 'yar uwarta. Ba Malam Ilu kawai ba, duk wani mutum da ke wajen sai da ya girgiza da jin mutuwar Abulle, shi kam ya gama yin mutuwar zaune. Tashi guda ya nemi juriya da jarumtarsa ya rasa. Hawaye ke gangarowa kan ƙuncinsa. Haƙuri da ban baki aka shiga ba shi, nan suka tura gawar Abulle zuwa gida, shi kuma Idirisu aka tura gidansu don sanar ma iyayensa. *** Shiru falon ya yi, tibin ma dake aiki rage muryarsa aka yi. Afreen da Lubna dake zaune duk kewar Abulle ta damesu, zaman kwana uku kawai suka yi da ita, yau da ta tafi sai suke ji kamar sun ɗabi shekaru mai tsawo da ita. Lallai sabo turken wawa ne. Lubna ce ta kalli Afreen cikin sigar tsokana ta ce, "Afiriji! Ɗan ɗauko min ruwa a na'urar sanyaya ruwa." Kallonta ya yi, ya langaɓar da kai, "Anti Labano ruwa ya ƙare." Take duk suka sa dariya. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _43_ Tafiya kawai suke, ko kaɗan Malam Ilu bai san inda yake jefa ƙafarsa ba. Badon riƙe hannunsa da ake yi ba ma da kamar wuya ya iya tafiyar. Har yanzu bai gaskata mutuwar Zainabunsa ba, ya fi dangantata da dogon suma kamar dai yadda aka ce Idirisu ya yi, ko shakka babu wannan matar bata san aikinta ba. Tayaya za a ce, daga taɓa tsintsiyar hannu da dokin wuya sai a ce mutum ya mutu? Wannan ma ai ƙaryane da rashin sanin makamar aiki. Ga yarinya sai murmushi take dokawa amma a ce ta mutu! Hakan ba zai yiwu ba, suna kai ta gida zai je ya ƙira Hajiya ya sanar mata da abinda ke faruwa ko za a turo musu mota ya jirasu a Guwal su kaita asibitin Jinjin a dubata da kyau. *** Cikin tashin hankali ya isa ƙofar gidan Mai Unguwa, lokacin har an yi sallar isha. Yaro ya aika a yi masa ƙiran Mai Unguwa. Koda ya fito ya sanarmasa cewar ance bai dawo daga masallaci ba, don haka kai tsaye masallacin ya nufa. Sauri yake rafkawa haɗe da maganganu shi ɗaya tamkar sabon kamun hauka. "Sarkin fada! Lafiya kake kuwa? Kana tafe kana ta sambatu ko kallon gabanka baka yi." Mai Unguwa ya faɗa lokacin da ya taho yana haska hanya da tafkekiyar tocilarsa ta ƙarfe tamkar irin na masu gadin nan, sun zo zasu yi karo da juna. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Sannunmu fa!! Sannunmu da haƙuri. Ita kuma sa i ya yi. U'uhumm! Abun gwanin tausai." Ya faɗa yana goge fuska. Kallon rashin fahimtar zancen da yake Mai Unguwa ya bisa da shi. "Ban fahimci zancen nan naka ba Sarkin fada, me kake faɗa ne?" "U'uhumm! Mun yi rashi babba wallahi. Da an sani aka barta a gida bata je ko ina ba, da duk hakan bata faru ba." Yanzu kam ransa ya kai maƙura wajen ɓaci, tafiya ya fara yi yana faɗin, "Shashancin banza da hofi kawai! Yaya zaka tareni a kan hanya ka fara yi mini zance mara kan gado? Badon na yi maka farar sani ba, da sai ince ka fara shaye-shaye irin na 'ya'yan zamanin nan ne." "Sai haƙuri Ranka shi daɗe! Abin ne da nauyin faɗa." Ya ɗago kansa da tun ɗazu ke sunkuye zai sake magana, ya ga ba Mai unguwa, bai ma san tafiyarsa ba don lokacin da suka tsaya ya kashe tocilar. Waigawa ya yi, ya hangosa yana tafiya yana mita. Da sauri ya bi bayansa yana faɗin, a yi haƙuri ranka shi daɗe! Tuba nake, na yi kuskure." Bai kulasa ba, har suka iso gida, ganin zai shiga ne ya sa shi saurin cewa, "Ranka shi daɗe! Sai haƙuri, daga wajen haɗarin ɗazun nan nake, al amarin ba kyan gani." Dakatawa yi yi, ya juyo yana faɗin, "Shi ne tuntuni ka tsaya kake wani ƙumbiya-ƙumbiya?" "Ya zama dole ai, sosai na firgita da lamarin. Shi mai tuƙin nasa da sauƙi, doguwar suma ya yi, sai kuma buguwa da raunuka a wasu sassa na jikinsa. Ita kuma yarinyar ta bugu sosai a tsakiyar kayi, har kana hango ƙoƙon kanta, jini kuwa a wajen tamkar kwata (wajen yanka dabbobi), tun daga Tudun mun tsira har muka shigo gari zuwa cikin asibitin nan jini ne ke malala, ga kuma wasu raunuka a jikinta. Mun kai su duka an dubasu, shi yana raye ita kuma an naɗe kan da bandeji sun tafi gida shi ne na nufo nan, don in sanar maka Allah ya yi mata cikawa." Ya ƙarashe maganar yana share idanun da ba alamar hawaye. "Ashsha! Ashsha!! Abu bai yi daɗi ba. Wannan hanya tamu, Allah ya kawo mana wanda zai gyaramana shi. Kansila Akilu ya ce zai yi maganar gyaran nan ka ji shi shiru ga masu aikin sa kai ɗin ma kwana biyu sun dakata. Sun sake tone waje sun tafi." "Ai jiya da yau abin ba kyau, Allah dai ya taƙaita." "Amun dai, sukuma Allah ya jiƙayinsu." Har ya juya zai shiga gida, Sarkin fada ya ce, "Umm! Ranka shi daɗe yarinyar nan ce fa ta rasu." "Wacce yarinya kenan?" Ya faɗa yana sake gyara tsayuwarsa. "Amm! Um!! Ta..." Katsesa ya yi, "Wannan inda-indar na mene ne Sarkin fada? Kai tsaye ka faɗama duk kasa gabana sai faɗi yake yi." Sai da ya ɗan yi jim! Sannan ya ce, "War wajen Ilu Mai Amalanke ce." A razane ya ce, "Wacce kenan?" " 'Yar tasa ai ɗaya ce, Abulle ce, wacce ake shirin aurama ita nan da kwana huɗu, ta je bankwana ma Baffanta a hanyar..." "Riƙeni Sarkin fada! Riƙeni, bana gani, zan faɗi." Shi ne kalmar da ta katse Sarkin fada daga dogon sharhin da yake yi. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _44_ Gida ya cika maƙil, ba ka jin komai sai hayaniya da ƙarar taunar shinkafa. Yau wuni aka yi, ana ɗaurawa da saukewa, buhun shikafa mai cin kwano ɗari ya kusa karewa, bai fi saura mudu goma ba. Wasu ma tun yau suka naɗo tsummokinsu; suka taso ƙeyar 'ya'yansu daga nan har a gama biki. Suna tsaka da hayaniya ne suka ji ana, "Hanya, hanya." Ana turo amalanke. Wasu kuma sai rafka salati suke. Hankalin wasu matan ya koma kan masu shigowar, wasu kuma kallo ɗaya suka yi, suka kau da kai don ka da hankalinsu ya raja'a wajen su juyo suga daron shinkafa wayam. Umma Sakina, ƙanwar Inno da ke ta kurɓar miyar ja a bakin murhu ce ta taho hannunta riƙe da ludayi tana tambayar me ke faruwa. "Ina za a saka ta ne Malam Ilu?" Mai turo Amalanke ya tambaya, "Ba ajiyeta za a yi ba, ruwa za a sake watsa mata za ta farfaɗo." Ilu da ke kiɗime ya faɗa. "Wai menene a nan ɗin ne kam? Ana tambaya kun yi hiru?" Umma Sakina ta sake tambaya, bayan ta kurɓe jar miyar dake cikin ludayin ta lashe bakinta. Kallonta Malam Ilu ya yi ya ce, "Ina Inno?" "Tana ɗaka tana sallar ihya i." "Dama yar..." "A'a, Malam Ilu!" Malam Mudi ya dakatar da shi, gefe ya ja shi, "Malam Ilu kasan taron mata ne, ba a gaggawar faɗa, yanzu sai su cika gida da kururuwa." "Malam Mudi ba ta mutu ba fa, doguwar suma kawai ta yi, zan ƙira Yaya yanzu ya turo moto mu kaita can asibitin Jinjin a dubata da kyau." Malam Kallah ya ce, "Haba Malam Ilu! Rai fa guɗa ɗaya ce a jikin ɗan Adam, ko duk asibitin duniyar nan za ka kai ta ba za ta dawo ba, domin ba wanda ya isa ya ɗagata, tunda ran da ke jikinta ya riga ya fita. Don Allah ka sa ma ranka haƙuri da juriya, idan ka riga ka karaya ita mahaifiyar yarinyar kuma ta yi ya ya? Kasan fa su mata rauni ga..." "Wayyo Allah mun shiga uku! Yau me zan gani?" Umma Sakina da ta buɗe gawar Abulle da aka rufe da zani ne, ta haska da fitilar da ta ɗauka a ƙasa ne ta kurma wannan ihun,wanda ya yi sanadin katse maganar da Malam Kallah ke yi ma Ilu. Cikin sauri suka iso wajen, "Habba baiwar Allah! Wannan ihu kuma na menene?" Ba ta basu amsa ba, sai ɗiba ta yi da gudu zuwa ɗakin Inno hannu a ka, tana rusa ihu tana shi ke nan mun mutu mun lalace. Tana isa ta daka tsalle, ta yi zaman 'yan bori, hannunta da ke kai ta sauƙe ta waresu, ta karkaɗa ta buga a ƙafarta gami da tattaro zaninta zuwa guiwarta, ta sake ɗaga su ta watsa kan cinyarta tana faɗin, "Shi ke nan Yaya! Ta tafi ta barmu, mun yi rashi, wayyo Allah." Ta juya ta fyace hanci ta ci gaba da shissheƙar kuka, a daidai lokacin ne matar liman ta sallame sallar da take ta juyo ga Sakina da ke ta zuba maganganu. "Haba baiwar Allah! Da hankalinki kike ta janyo muku alkaba'i? Ko menene ya faru ai salati ya kamata ki yi kururuwa da ihu ba." Hanci ta ja, ta share idanunta sannan ta ce, "Malama ko ke aka yi miki irin wannan mutuwar bazatan sai kin yi kuka, don haka babu ruwanki." Tana gama faɗi ta ci gaba da kukanta, Inno da tun ɗazu take ta rafka sallah ba iyaka ta yi saurin sallamewa, don tunda ta ga shiru Abulle ba ta dawo ba zuciyarta ke ta wasu muggan saƙe-saƙe. Ko da ta ji ihun Sakina ba ƙaramin tsorata ta yi ba, sai dai ta san shirme irin nata da maida ƙaramin abu ya zama babba ya sa ba ta kula ta ba, sai da ta ji martanin da ta mayarma matar Liman ne ya sa ta yi saurin sallamewa. "Kina hauka ne? Malamar kike maida ma irin wannan martanin don ba ki da mutunci." Inno ta faɗa lokacin da take kallon ƙanwar tata, "Au! Bayanta ma za ki bi kenan? Sai ki fita kiga me nake yi ma kukan ai." Ta faɗa tana ƙara sautin kukanta. Inno ta buɗe baki za ta yi magana, Lami matar Liman ta hanata. A waje kuwa cire gawar suka yi, aka saka a ɗakin da aka gyara ma mutanen Jinjin, aka janyo ƙofar aka rufe, suka fita da Ilu ana ta tausarsa da basa haƙuri. Cikin gida kuwa ya kaure da koke-koke da sallallami, don wasu sunga abin da ya faru ta dalilin buɗewar da Sakina ta yi. Jin hargowar ta yawaita ne, yasa Inno da mutanen da ke ɗakin suka fito don ganin abinda ke faruwa. _Ummyn Yusrah_ _45_ "Wai me ke faruwa ne?" Inno ta tambaya cikin fargaba. Kallo suka bi ta da shi, domin tsoron sanar da ita suke yi, sai nuni da ɗakin kawai suka yi mata. Jikin ƙofar ta nufa, malama na biye da ita har ta buɗe suka shiga, ƙaramar tocilan da ke hannun malama ta haska musu, ganin abu suka yi rufe a kan tabarma. Sarawar kai da faɗuwar gaba ne ya dirar ma Inno a lokaci guda, sakamakon ganin zanin Abulle da ta yi an rufe abu kamar mutum da shi. Ba ta iya ƙarasawa wajen ba sanadiyyar ƙafarta da ta kasa ɗaguwa, ga kuma jikinta da ya hau kaɗawa, tamkar wacce ta yi wanka da sassanyar ruwa da sassafe a lokacin damina. Cikin sanyin jiki malama ta ƙarasa wajen, ta tsugunna. A hankali ta kai hannunta ta yane zanin, ta haska saitin fuskar Abulle. "Innalillahi wa innalillahir raji'un!" Ita ce kalmar da ta faɗa, cikin sauri ta saki zanin. Ta taso, juyowa ta yi zuwa ga Inno wacce tunda ta yi ido biyu da Abullenta rufe haka ta san ba ta raye, yatsar hannunta na dama kawai ta ke ta nunawa wajen gawar, bakinta na motsi sai dai ta kasa furta kalma ko guda, har malama ta iso gareta ba ta sani ba, domin jinta, ganinta da komai na ta ya ɗauke, sai nuni kawai da gauraya harshe cikin baki. "Inno! Lafiya kuwa? Mu je ko?" Ta faɗa a lokacin da ta dafata. Nannauyar ajiyar zuciya ta saki, sannan ta buɗe baki za ta kwaɗa ihu. Da sauri malama sanya hannu ta toshe mata baki, tana faɗin, "Me kike shirin aikatawa? Ihu ma mamaci? Wannan ba ɗabi'a ce ta musulmai ba, addu'a ce kawai soyayya da gatan da za ki yi mata a yanzu ba ihu ko kuka ba. Ki sani wanda ya fimu sonta ya riga ya karɓi abinsa, don haka ki sa ma ranki salama ki yi ta rakata da addu'o'i ki kuma yafe ta, sai ki ga Allah ya kawo miki sauƙin lamarin." Haka nan ta yi ta tausarta, da ba ta haƙuri. Da taimakon addu'ar da take yi ne ta fara jin sassauci a zuciyarta, ta kuma yi alƙawarin ba za ta bari koda ɗigo ɗaya na hawayenta ya sauƙa ba, da sunan yi ma Abulle kuka. Haka shi ma Malam Ilu, ya samu salama dalilin tausa da kuma addu'ar da yake yi, ganin haka ya sa duk suka yi haramar gabatar da salloli biyu da ya hau kansu. Bayan idarwa ne, Ilu ya nufi cikin kasuwa da salularsa don sanar da su Hajiya. *** Hajiya da ke zaune a falon Alhaji, ta na yi masa bayanin yadda tafiyar ta su za ta kasance gobe ne wayarta ta fara tsuwwa. Ɗagawa ta yi, cike da mamakin ganin lambar Ilu a daren nan, har wayar ta katse ba ta ɗaga ba. Ƙiran ya sake shigowa, kallon wayar ta tsaya yi, zuciyarta cike da saƙe-saƙen ko lafiya? Kodai Abulle ba ta isa gida ba ne ha... "Ba ƙiranki a ke yi ba?" Alhaji ya katse mata tunanin da ta ke yi. Fuskar wayar ta ɗago ta nuna masa, ganin sunan Ilu yas a ya ɗaga kafaɗa ya mai da kallonsa ga tibi. Haka nan ta tsinci kanta cikin faɗuwar gaba, ɗagawa ta yi, haɗi da sallama. Bayan wasu 'yan daƙiƙu, ta miƙe tamkar wacce aka tsikara ma allura. Cikin rawar murya da tsiyayar hawaye a idanunta ta shiga faɗin, "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!" Kalmar da ta ke ta furtawa kenan har ya katse waya. Ganin yadda hankalinta ya tashi, ga kuma zubar hawayen da take yi ne ya sa Alhaji tambayrta ko lafiya? Jiki a sanyaye ta zauna kan kujerar tana sharar ƙwalla, ta ce, "Shi ken an Alhaji! Zainab ta tafi ta barm..." "Don ta tafi shi ne kike wannan kukan? Ina dai ya ce miki ta isa? Ai shi ke nan." Ya maida kansa ga kallon da ya ke, kallon mamaki ta yi masa, bai bari ya ji ƙarshen zancenta ba, ya yi gaggawar katseta, ya iya maida ƙaramin abu ya zama babba. "A hanyarsu ta komawa, suka yi hatsari, mai mashin ɗin yana asibiti, ita kuma Allah ya karɓi abinsa, ya raba gardama a tsakaninmu, da mu da su duk mun huta, kai ma ka huta, ba ka yi niyyar zuwa aurenta ba, ga shi za ka je jana'izarta." Tunda ta fara maganar ya ke kallon bakinta, kansa ya yi masa nauyi, bai gama fuskantar me take cewa ba. "Me kike faɗa ne? Ban fahimci ko ɗaya daga cikin abinda kike cewa ba." Ɗago idanunta da ke ta zubar da hawaye ta yi ta kallesa, "Baka fahimta ba?" Kai ya ɗaga mata. "Zainab ɗin da kake ta fushi akan tafiyarta, har ka ƙi saurarar uzurin mahaifinta Allah ya karɓi abinsa, sun yi hatsari a hanya ta rasu." Tun kafin ta kai ga ƙarshen maganar, ya sanya hannunsa biyu ya riƙe kansa yana salallami. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _46_ Girgiza kai kawai yake, yana faɗin, "Me na aikata ne? Me ya sa ban tsaya na saurari uzurinka ba ƙanina? Har na yi gaggawar yanke hukunci. Komai ya faru ni ne sila kanina, da wani ido zan kalleka a matsayin wanda ya yi sanadin mutuwar 'yarka?" Ɗago kai ya yi, ya kalli Hajiya da rinannun idanunsa, "Hajiya! Wallahi ni ne silar mutuwarta, a yau na tsani halina na rashin uzuri da saurin zartar da hukunci, ba tare da jin sahihin zance ba. Da ban yi haka ba, da yanzu tana raye." Ganin yana neman sakin layi ne, ya sa ta dawo kusa da shi ta zauna. Ta ce, "Ka yi haƙuri Alhaji, ka saita natsuwarka. Kwananta ne ya ƙare, ko da ba ta tafi ba, dole Allah zai karɓi abinsa tunda kwananta ya riga ya ƙare, ka sa ma ranka cewa, Allah ne ya kaddara ta nan ne ajalinta." Sosai take ta nusar da shi, sai dai ko kaɗan bai yarda da hakan ba, ya san shi ne sanadin mutuwarta, da bai biye ma zuciyarsa ba, da hakan bai faru ba. Da taimakon addu'a, ya samu sassauci a zuciyarsa. Kallon Hajiya ya yi, ya ce, "Ki duba lambar Tukur direba, ki sanar masa ya zo da asuba mu wuce, ki sanar ma yaran nan su shirya da wuri ka da su ɓata mana lokaci." "To" kawai ta ce. Ta nufi falon, sai da ta yi ƙoƙarin saita kanta kafin ta shiga, hira suke suna ta ƙyaƙyatawa, jin hirar ya sa ta ɗan dakata, "Kin san me? Cewa na yi mata ta zauna ta yi karatu, ko engineering ta y..." Dariyar da ta taho mishi ce ya sa shi dakatawa, kafin ya ci gaba. "Kin san me ta ce?" Kai ta gyaɗa Cikin dariya, "Wai Injimiyarum!" Tare suka sake fashewa da dariya, sai da ta ɗan tsagaita sannan ta ce, "To, kai ma sai ka haɗa ta da wani injimiyarum! Ina laifin ma asibiti ko banki ta sami kuɗi ta dawo da suwit Mai Unguwar ta birni." "Banki kam! Da yake kuɗin kwasowa za ku yi ta yi ko?" "Yo wa ya sani?" "Ke." Ya faɗa da dariya. "Kai dai Afirij." "Ko kuma Labano ba." Duk suka sake sa dariya, Hajiya da ke ƙofar falon ta share ƙwallar da ta gangaro mata, tana tunanin irin yanayin da yaran za su ji, idan suka ji labarin mutuwarta. Sallama ta yi, ta shiga falon, masauƙi ta yi kan kujera, tana kallonsu, suma ita suke kallo. Domin duk ƙoƙarin da ta yi wajen ɓoye damuwarta, sun gano damuwa maƙale a fuskarta. Murmushi ta ƙaƙaro, ta ce, "Hira a ke yi ne?" Lubna murmushi ta yi Afreen ne ya amsa, "Zainab ta tafi ta barmu da kewa Mommy. Goben za mu ta fi da wuri ko?" Ya faɗa yana kollon Momyn, yana rausayar da kai. Murmushin ƙarfin hali ta sake yi, ta ce, "Abinda ya kawo ni kenan." Ɗaga hannunsa na dama ya yi, ya dunƙule yatsun ya karkaɗa ya ce, "Yauwa Momyna!" Ya ƙarasa faɗa yana kwanciya kan cinyarta. Harara Lubna ta watso mai, ƙaramin filon dake kan kujerar ta ɗauka ta jefo masa, ta ce, "Dubesa goɗai-goɗai da shi, ya wani mimmiƙe, Allah Mommy zai karya miki cinya." Gwalo ya yi mata, ya ce, "Gara ni ai, ke kullum kina kwance jikinta kamar wata kyanwa, ni ko sai idan autancin ya motsa." "Ji! Wai auta. Tuff!!" Ta tofar da yawu. "Ya son ranki Labano?" Ya fana yana ƙanƙame Momyn. "Raina fes! Ban ji komai ba yaro." Dariya duk suka sa, Mommy kam na jinsu. Ganin hirar ta su ba mai ƙarewa ba ce, ya sa ta ce, "Ya isa, yanzu dai ku je ku kwanta, gobe da asuba za mu wuce." Tare suka tambayeta, suna zaro idanu, "Da asuba Mommy?" "Eh, harda Dadynku." Da sauri Afreen ya miƙe, ya sanya hannayensa duk biyu ya dafa ƙafafunta, ya na kallon fuskarta ya ce, "Mommy ya yarda zai je ya ba Baba Ilu haƙuri, ya bar mana Zainab ne?" Idanunta suka cicciko, da sauri ta miƙe, ta juya tana tafiya, tana faɗin, "Ku shirya da wuri, kun san Daddynku, ba zai tsaya jira ba, ku ɗebi kaya kuma don zamu kwan biyu." Tana gama faɗi ta fice, hawayen da ta maƙale suka gangaro. Tana fita, Afreen ya yi ɗan ƙaran farin ciki, da sauri suka nufi ɗakunansu domin shiryawa. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ni Marubuci sarkin aiki, ni ke rayawa da kashewa, ni ne mai rushe dauloli in na so kuma in maido su, alkalamina ne alkali, mai shari'a ne mai yankewa, duk a rubuce nake yin wannan, sai ku tayani gurin aikawa, al'ummata bar kokwanto, duk kimata ba Marubuta._ #Wakar kare martabar Marubuta# _Ummyn Yusrah_ _47_ Gidan da ya cika da kwaramniya ɗazu, a yanzu shi ne ya dawo gidan jimami da koke - koke. Da yawan mutanen da suka naɗo tsummokinsu da niyyar zama sai bayan biki, a daren suka tattara suka gudu. Duk wanda aka ce ya kwana da gawar Abulle, sai ya ce bari ya je gida ya dawo, ba ka ƙara ganinsa. Ciki kuwa, har da Umma Sakina. Inno da ƙanwar mahaifiyarta ne a ɗakin, sai marigayiya. Sallah kawai Inno ke yi wanda idan aka ce ta ƙirga, ba za ta iya sanin adadinsu ba, ita dai kawai yi take haɗi da addu'a da kuma nema mata gafarar Ubangiji. A haka ta shafe tsawon daren nan tana ibada, shi ma Ilu hakan take a garesa. *** Kallo ɗaya za ka yi ma Mommy da Daddy, ka gane cewar ba su samu isasshen barci ba, duba da yanayin idanunsu da suka canza launi, da kuma rashin kuzari, ga kuma fuskokinsu da ke nuna alamar damuwa. Sun fi minti goma zaune cikin mota, suna jiran Lubna ta fito, sai dai shiru. "Kai! Fita ka je ka faɗa mata, idan ba za ta fito ba za mu tafi." Mommy ta faɗa ma Afreen Kafin ya kai ga cikin gidan, sai ga ta ta fito da sauri. "Ke fa muke jira, kin je kin zauna." "Mu je dalla!" Alhaji da direba a gaba, Mommy da su Lubna a baya, suka ɗau hanyar Mai Ludaya. *** Cikin shigarsa na riga 'yar shara na yadi da wando ya fito, hannunsa riƙe da ledar Viva, wanda ya sa kayansa kala ɗaya, sai burodi da ya sai ma Innarsa Talle. Rufo ƙofar ɗakin na su ya yi, ya nufin wurin mai gidan hayansu, ya kai masa makullin ɗakin, akan zai je gida kwana biyu zai yi ya yawo. Suka yi sallama ya nufi hanyar titi, domin samun abin hawar da zai kai sa tasha. Ya yi tafiya sosai, don har ya bar unguwar da ya ke bai sami abin hawa ba, kasantuwar gari bai gama wayewa ba, ga kuma lokaci na sanyi. Sauri ya ƙara, dalilin hango wani mai abin hawa da ya yi can nesa da shi, hawa titi ya yi da niyyar tsallakawa, sai dai, bai yi aune ba ya ji shi a sararin samaniya yana shawagi, daga bisani kuma ya ji an jefosa ƙasa tim! Ɗan ƙara ya saki, na zafin da ya ji. Mai mashin ɗin da ya bugesa kuwa, ganin ba kowa ya sa ya ƙara wuta ya gudu. Yunƙurawa Hamusu ya yi da niyyar tashi, sai me? Ji ya yi, ƙafarsa ta dama ta riƙe ya kasa miƙewa. Ya yi ya taka ƙafa, ta ƙi, kawai sai ya koma ya kwanta, ya rufe idanu. Hawaye mai zafi ya gangaro masa ta gefen idanu, magana ya fara shi ɗaya. "Me ya ke shirin faruwa da ni? Allah ka kawo min agaji, Innata ki yafeni, alhaƙinƙi ne ya fara kamani, ina shirin zuwa gareki, ƙaddara ta hana Inna! Gani a yashe kan titi babu mataimaki, na gudu domin ƙin ganin auren Abulle, yanzu gani ina son dawowa gareki amma ba hali, rayuwata Inna! Rayuwata za ta shiga garari." Sharrr! Hawaye ya sake zirarowa daga idanunsa. Ƙararrawar sanarwa ake ta kaɗa masa daga cikin moton, domin ya matsa sai dai ko gezau ya ƙi yi, sai ma gyara kwanciya ya yi, fatansa kawai motar ta bi ta kansa ya mutu ko ya huta, don ya san nan gaba sakayyar ba ta ma mahaifiyarsa rai da ya yi, sai tafi haka. Cikin damuwa mai motan ya juyo ya kalli matar da ke kwance a kujerar baya, hannunta riƙe da ciki, sai murƙususu ta ke yi, ya ce, "Sannu! Yanzu zamu isa asibitin, wani ne kwance a kan hanya, ina ga irin masu shaye-shayen nan ne ya sha ya yi tatul, ya zo ya kwanta kan hanya. Barin fita in samesa, sannu." Ya ƙarasa faɗa, yana fita daga cikin moton. "Haba Malam! Ka gama shaye - shayenka, ka rasa ina za ka yi masauƙi sai tsakiyar hanya? Don Allah ka matsa in wuce, tare nake da majinyaciya, ko kuma in jaka ta ƙarfi." Mutumin da ke tsaye kan shi ya yi maganar, yana ƙoƙarin sunkuyawa ya janyoshi, ganin ba shi da niyyar tashi. Hakan ya sa Hamusu buɗe idanun da ke ta zubar da hawaye. Yau shi ake ƙira da ɗan maye, shi da ko sigari bai taɓa sha ba, yau an ce da shi ɗan maye. "Don Allah ka taimaka ka bi ta kaina ka wuce, a yanzu rayuwata ba ta da wani sauran amfani, na roƙeka da kaima ka bi ta kaina ka takeni ka gudu, kamar yadda mai mashin ɗin nan ya bugeni ya gudu. Don Allah ka taimakeni, idan na zauna haka ban san wa zai tallafi rayuwata ba, na sani sai dai in ƙare rayuwata a kan titi, amma babu mai cetona a garin nan, tunda duk na fuskacin ɗabi'u da halayyarku na son kai da rashin taimako duk ɗaya ne. Ka taimaka don Allah." Ya ƙarasa maganar yana haɗa hannayensa biyu, yana roƙon mutumin. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _Badiyya Adam (Beauty Queen) har kullum ba zan gajiya da miƙo saƙon godiyata a gareki ba, godiya mai tarin yawa, Allah ya saka da alkairi, ya ƙara miki lafiya._ _48_ Tausayin shi ne ya mamaye illahirin zuciyar mutumin, domin cikin maganar da ya yi, ya fuskanci yana neman taimako a yanzu, ya kuma fahimci bankesa da mashin aka yi aka gudu, ba wai shaye - shaye ya yi ya kwanta a kan hanya ba, kamar yadda ya faɗa. "Zan iya taimakonka?" Mutumin ya faɗa. Da sauri Hamusu ya buɗe idanu ya kallesa. Kai ya gyaɗa ya miƙa masa hannu, ya ce, "Ka yarda da ni, ka kuma sani cewar halayya da dabi'u sun bambanta, ba duka aka taru aka zama ɗaya ba. Ka daina yi ma mutane kuɗin goro, duk rintsi duk wuya sai an ɗebe tsakuwa a cikin ƙasa, domin kowa da halinsa. Asibiti zan kai matata da ta kwana ba lafiya, shi ya sa kaganni da sassafe, me yiwa wannan ita ce silar haɗuwarmu, Allah ne ya ƙaddara ni zan taimakeka, ba don haka ba, a gida zan yi mata komai, ni likita ne a babban asibitin garin nan." Yana gama magana ya juya zuwa moto, har yanzu tana nan cikin mawuyacin hali. Buɗe ƙofar bayan ya yi, ya sunkuyo daidai fuskarta. "Ƙalbi mu tafi don Allah! Zan mutu, cikina." Ta faɗa cikin raunanniyar muryarta. "Yi haƙuri, yanzu za mu tafi, wani aka bige da mashin aka gudu, shi ne zan taimaka masa sai mu tafi tare ko?" Kai kawai ta ɗaga, ba tare da ta iya yi masa magana ba. Da sauri ya koma gun Hamusu ya kamosa, da taimakonsa suka kai ga moto, domin da alama ƙafarsa ta dama akwai matsala. Yana sanyasa ya figi motar suka yi gaba. **** Tukur direba gudu kawai yake tsulawa, domin Daddy ya sanar da shi yana son su isa da wuri domin su sami jana'izar. Afreen da Lubna sai zuba hira suke, da kuma ɗokin ganin Abulle. "Ku kam kun ishemu da surutu, addu'a a ke yi idan ana tafiya ba hira ba." Mommy da ke ta jan carbi ta faɗa musu. Duk suka ɗinke bakinsu, suka koma kallon yadda hanya ta ke, sai jefi-jefi suke magana. Tunda suka fara karo da duwatsu akan hanya bakinsu ya mutu. Kafin su isa Guwal duk sun yi laushi, sakamakon karo da duwatsu da shiga gargadar da suke yi. Abinka da ba sabon ba. Suna isa suka sami mashina, lokacin har tara ta gota. **** Jama'a ne tun daga waje har cikin gida, domin tun a daren labarin rasuwar Abulle ya riski da yawan mutanen garin. Mai Unguwa ma da tunda ya ji saƙon rasuwar, masassara ta kamasa ya rarrafo don sallatar masoyiyarsa da kuma rakata makwancinta. **** Har ƙofar gida masu mashinan suka sauƙesu. Daddy na sauƙa ya nufi dandazon jama'ar, Afreen da Lubna kallon mamaki suke yi ma juna na ganin taron jama'a. "Za ka sallamesu su koma bakin aikinsu ne, ko za ka tsaya kallon juna?" Mommy ta faɗa ma Afreen, ganin bai shirya sallamar masu mashinan ba. Da sauri ya ciro dubu ɗaya ya basu, kowa ɗari biyar-biyar don Tukur ya tsaya zai yi sayayyar kayan abinci ya taho da shi. Da sauri ya biyo bayan su Mommy, da ta tasa Lubna a gaba. "Mommy dama yau ne ɗaurin auren?" Ya tambaya lokacin da ya iso garesu. Kallonsa ta yi ba tare da ta ba shi amsa ba, sai ma cewa ta yi, "Ka sami Daddy a can, mu zamu shiga ciki." Tana kaiwa nan ta riƙe hannun Lubna, suka raɓe gefen mutanen suka shige ciki, shi kam ya kasa fahimtar komai, ga dai mutane da yawa a wajen, wasu sai alwala suke wanda ya kasa fahimtar ta mecece? Ga wasu kuma sai goge idanu suke, da alama kuka su ke yi, me ke faruwa ne wai? Ɗaurin aure ne ko rasuwa? Dam!! Kirjinsa ya buga, take kuma ya shiga harbawa da sauri - sauri, tunowa da ya yi, mai mashin ɗin da ya hau, ya gwada masa inda aka yi hatsari jiya, har ma yarinyar ta mutu, ga jini kaca-kaca a wajen duk ya bushe. 'Abulle!' shi ne sunan da mai mashin ɗin ya ambata, wanda ko kusa bai alaƙanta mutuwar da Zainab ɗinsu ba, domin su da Zainab suke ƙiranta. Kenan dai ita ce ta yi hatsari ta mutu? Kai! Ƙarya ne, ba mutuwa ta yi ba. Bai san sanda hawaye ya fara zirarowa daga cikin idanunsa ba, ya kuma kasa motsawa a wajen, don isa ga Daddy ya amsa masa tambayoyin da zuciyarsa ke yi masa. **** "Ayya! Ayya!! Abulle!! An yi taron biki ashe taron mutuwa ne, kina ta zaga dangi sallamar tafiya gidan miji, ashe sallama da duniya ce gabaɗaya, Allah sarki 'yannan, Allah ya jiƙanki ya sa mutuwa hutu ce, ya ba iyayenki da 'yan uwanki haƙurin jure wannan rashi naki, Allah ya y..." Kuka ne ya hana matar ƙarashe maganarta. Maganar da ta doki dodon kunnen Lubna kennan, daidai lokacin da suka shigo gidan. Turus! Ta ja ta tsaya tana girgiza kai gami da kallon Mommy. Janta ta yi sai dai ƙam! ta ƙame a wajen, ta kasa motsawa, sai hawaye da ke rige-rigen sauƙowa daga cikin idanunta. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ _49_ Wani irin kallo mai wuyar fassara, ta bi yamutsattsiyar tsohuwar da ke ta mamular goro a bakinta ta yi, ta kuwa sake maimaita magartata wanda ta ji a bazata. Kallonta ta maida kan Mommy da ta ke riƙe da hannunta, kallon yanayinta, ya sa wani sashe na zuciyarta ta fara yarda da abinda ta ji daga shigowarta gidan. "Mommy da gaske ne abinda kunnuwane suka jiyo daga shigowata? Da gaske ne taron mutuwar Abulle a ke ba taron bikinta ba?" Ta tambayi Mommyn a daidai lokacin da idanunta suka fara tsiyayar da ƙwalla. "Mu shiga ciki, kinga nan kan hanya ne, mutane na wucewa." Mommyn ta faɗa, a lokacin da ta dauke idanunta daga kanta, ba tare da ta ba ta amsar tambayoyinta ba. "Mommy ki amsa mun tambayata." Mannata ta yi da jikinta. Ta ce, "Yi haƙuri, mu shiga ciki tukunna." Tafiyar kawai take, amma sam, ba ta ganin gabanta, balle ta ga masu yi ma Mommy gaisuwa da barka da zuwa. Shigarsu cikin gidan, ya yi daidai da fito da ita daga ɗakin da aka gama shiryata, aka sanyata cikin makara za a fita da ita a yi mata sallah a kaita makwanci. "Ku dakata da ita Hajiya su yi mata addu'a." Umma Sakina da take ta sharar ƙwalla ta faɗa. Tsugunnawa su ka yi a gaban gawar, Mummy ta yi mata addu'a, sannan ta buɗe zanin da aka rufeta da shi. Fuskarnan a sake tamkar mai murmushi. "Mummy! Wallahi ba ta mutu ba. Kalleta, kalleta fa. Allah murmushi take yi, wallahi ba mutuwa ta yi ba, ki ce su cireta a cikin abun nan, tana raye wallahi, ƙarya suke yi. Barci kawai ta ke yi, ki ce su kai ta ɗaki, ba ta mutu ba." Lubna da ke ƙankame da hannun Mommy ke faɗin haka, lokacin da ta leƙa ta ga fuskar Abulle. Ganin tana neman fita hayyacinta, ya sa ta ƙarasa zama daga tsugunnon da ta yi, ta janyota gaba ɗaya ta kife kanta a jikinta, hannunta ɗaya ta yi musu alamar su tafi da ita. "Lubna!!" Ta ƙira sunanta a saitin kunnenta. Ta ɗora da faɗin, "Ki tattaro natsuwarki, kin dai san mamaci baya buƙatar kuka ko? Addu'a za ki yi mata, kin ji ko?" "Mutuwa? Mutuwa fa kika ce Mommy? Ki duba fa ki gani, ba ta mutu ba, ba yanzu za ta mutu ba, ki tasheta barci take yi." Ta faɗa cikin matsanancin kuka, a lokacin da ta ɗago kanta tana kallon Mommy. "Lubna! Gudu ga harbabbe ai ɓata lokaci ne. Kwananta ya riga ya ƙare, wanda ya fimu sonta ya riga ya karɓi abinsa. Gata ɗaya za ki mata a yanzu, shi ne addu'a kin ji ko?" Bakinta na rawa tana girgiza kai, hawayenta ta kasa tsayar da su. Ta ce, "Mommy ba za ta mutu ba, sai ta yafemin abinda na yi mata. Ba ta mutu ba ko Mommy? Ki ce tana raye Mommy, tana raye ba ta mutu ba." "Na ce ki saita tunaninki waje ɗaya ko? Ki kalli yadda kika tara mana mutane, ki tashi mu shiga ɗaki." Mummy ta ce a kausashe, ganin Lubna ba ta da shirin yin yadda ta ce. "To! Ki ce su cireta cikin abin nan, ta tashi mu shiga ɗaki, kuma tare za mu koma da ita ko?" Ta ƙarasa maganar tana juyawa don ganin gawar. Idanu ta shiga rarrabawa gani babu ita babu dalilinta, sai tarin mutanen da suka taru suke ta sharar hawaye. Cikin tashin hankali ta juyo. "Mommy! Ina take?" "Mu je tana ciki." Ta faɗa tana miƙewa, don idan ba haka ta yi mata ba, ba za ta miƙe ba. **** Ɗakin taimakon gaggawa aka shiga da Badiyya, matar Likita Kamal da kuma Hamusu. An ba shi duk wani taimako da ya kamata, an kuma tabbatar da komai daidai, buguwa ce kawai da ya yi, zai ji sauƙi nan ba da daɗewa ba. Zai kwana biyu kafin a sallamesa. Ita kam Badiyya tunda ta sha ruwa da magungunana ta ware. *** "Kunsan Allah! Yau banga wanda zai hanani shiga duniya nemo tilon ɗana ba. Ina dalili kullum ku yi ta rainamin hankali? Kuna yi mini daɗin baki cewar kun tura Salele, ina ce shi Salelen kullum yana cikin gidan nan yana shawaginsa? Idan na rasa ido na rasa ji ne? Wallahi idan ba ka zo ka mai dani Mai Ludaya ba sai na ci mutuncinka. Ka fada min nan ɗin wace uwar nake tsinanawa? Me nake ɗauka, baya ga kulleni da kuke a ɗaki, kamar gidan kaso." Inna Talle ne da ta fito ta yi tsaye a tsakar gidan ke ta zuba ruwan masifa. Baki cike da kumfa tana hargagi, ga shi babu idanu. Kande dake tsaye cikin rashin sanin mafita ta ce, "Yaya ki yi haƙuri don Allah! Malam yana iya bakin ƙoƙari wajen nemo yaron na..." Cikin harzuƙa ta katseta. "Ke Kande! Kin rufemin baki ko sai na sheƙa miki mari. Munafukar mata, kullum da na yi magana ki wani fiffiƙe ki gwadamin yana ƙoƙari akan hakan. Gwadamin ƙoƙarin, na ce gwadamin ƙoƙarin." Gefe ta yi tana murmushi, jin za ta sheka mata mari kamar mai idanuwa. "Allah ya baki haƙuri." "Kema ya baki idan da daɗi, mara kunya kawai." Sum-sum, ta wuce ta bar wajen. Dama ita ɗaya ta rage a gidan, sauran duk sun ta fi jeji. "Ina nan, ina jiran dawowarsu, ba inda zan je gara yau a yi ta ƙare, idan da Salele ne ya ɓata da tuni kun ja mayafi kun shiga duniya nemansa. Ni kun barni kullum cikin zullumi da tunanin nawa ɗan." Ta sake gyara tsayuwarta, don zaman jiran dawowar mutanen gona. _Ummyn Yusrah_ *ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITERS ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ *K'arshe* _50_ Kowa ya tuba don wuya, ba lada. Inna Talle dai tun tana iya tsayuwa, har ƙafarta ta gaza ɗaukarta ta nemi waje ta zauna, daga zaunen ma gyangyaɗi take hakan ya sa ta ja tsufanta ta yi ɗaki don sanya haƙarƙarinta a makwanci, har lokacin ba wanda ya dawo. **** Tun daga yi mata sallah, zuwa kai ta makwancinta, zuwa yanzu da suke zaune ƙofar gida karɓar gaisuwa, gani ya ke, al'amarin tamkar almara, gani ya ke ba ta mutu ba. Idanu kawai ya zuba ma saitin ƙofar gidan, tamkar za ta fito, su zauna ta yi masa hirar shirmen nan nata. Addu'ar da ya ke, Allah ya sa ya farka daga wannan mummunar mafarkin da ya ke tun ɗazu. Ga shi nan dai zaune kamar mutum-mutumi, abu ne mawuyaci ka iya gane halin da ya ke ciki. Baya ga fitar numfashi da kiftawar idanunsa, babu wani abu da ke motsawa a jikinsa. "Haba Afreen! Kada ka bari tunani ya shige ka..." Daddy da ya matso kusa da Afreen ne ya yi masa magana, ganin hawayen da ya ziraro daga idanunsa zuwa kan fuskarsa ne ya sa ya katse maganar. Shiru ya yi na ɗan lokaci ya ci gaba. "Haƙuri da juriya shi ya kama ce ka, ka yi mata addu'a Afreen! Shi ta fi buƙata, ba kuka ba." "Me ya sa Daddy? Me ya sa tun a can ba ku sanar mana ba? Me ya sa kuka yi mana bazata? Ka fi kowa sanin wani hali Aunty Lubna za ta iya shiga a wannan lokacin. Na tabbatar idan ni na daure a matsayina na Namiji, ka sani ita ba lallai ta iya jurewa hakan ba. Da tun a can kuka sanar mana da komai, na san za ku taushe ta kafin mu zo..." Kuka ne ya ƙwace masa. Rungumosa ya yi jikinsa ya shiga bubbuga bayansa, yana magana. "Gudun faruwar hakan ya sa muka ƙi sanar da ku, domin mun san shaƙuwar da ke tsakaninku zai iya jefa ku cikin wani hali. Ka yi ƙoƙarin riƙe kanka, ka ga taron mutanen nan duk kai su ke kallo. Ka shiga ciki ka duba wani hali su ke ciki." Ɗago kan da zai yi, su ka yi ido biyu da Sarkin fada da ke ta galla masa harara, shi a dole yana taya Mai Unguwa kishi, gani ya ke kamar saurayinta ne. "Zan shiga, ba yanzu ba. Daddy waye wancan da ya kima rawani, tamkar kullin kayan wanki?" Ya tambaya yana kallon saitin da tawagar mai Unguwa ke zaune. "Sarkin fada ne, wancan ɗayan kuma shi ne Mai Unguwa." Daddy ya ba shi amsa. "Banza girman kato, ƙaramin mai hankali ya fishi. Idan ba zalunci ba, kamar wannan a ce shi za a ba Zainab? Ga shi ma Ubangiji ya karɓi abarsa. Shi ma Baba Ilun ko makancewa ya yi ne Ohho!" Cewar Afreen da shi ma ke ta aike musu da saƙon harara, ga kuma wani kululun takaici da ya gama tokare masa maƙoshi, ji ya ke, kamar ya tashi ya je ya shaƙo wuyan tsoho mai budurwar zuciyar nan, domin shi ne sila. Da bai ballo zancen aure ba, da yanzu tana raye. "Ranka shi daɗe! Anya ba za mu bar wajen nan ba? Sai ƙus-ƙus ake yi, kuma da alama duk kai su ke kallo, gani su ke duk kai ne sanadin komai, da ba a daga zancen aure ba da hakan bai faru ba." Cewar Sarkin fada, da ya dawo da fuskarsa ga mai unguwa, bayan sake aika ma Afreen da wani mugun harara. Kansu na haɗe ya ke maganar cikin murya ƙasa-ƙasa. "Allah ko? Gara mu zo mu tafi, nima duk a tsarge nake, ga kuma masassarar nan da ta dameni sosai." "Mu yi musu sallama kawai mu wuce, tun kafin a fara aiko mana da makaman ƙare dangi ta ido. Ka ga wancan matashin da ke saiti na? Wannan da gani taƙadari ne, ina ga kuma saurayinta ne. Ja'iri mai kama da ƙosai." "Na hangosa, sai saƙonni ya ke aikon ta ido. Sallamesu sai mu wuce." Sallama su ka yi, bayan Sarkin fada ya sanar da su cewar, masassara ta dami mai unguwa sakamakon faruwar wannan al'amari. ***** "Kinga ni ko? Na ce ki sassauta kukan nan kada ya ja miki zazzaɓi, amma tamkar zugaki na ke, dubi yadda kike ta ɓarin sanyi, kamar wacce aka izama shokin." "Hajiya a bi ta a hankali, kin san irin wannan sabo na kwana kaɗan ya fi shiga jiki, ga kuma mutuwa ta farat ɗaya, dole abun ya dameta." Inno da ke jan carbi ta yi magana ganin yadda Mommy ke yi ma Lubna da ke kuɗunɗune faɗa. "Sai a ka ce ta yi ta kuka? Ashe ba za ta sanya ma ranta haƙuri ba? Duk wata shaƙuwa da suka yi, ya kai shaƙuwar da kuka yi ke da kika haifeta? Yanzu ina za a samu asibiti nan kusa?" "Babu kam! Asibitin ɗaya ne, kuma ba ma'aikata. Akwai saiwa ai, idan za ta iya sha sai a kawo mata, a yi haƙuri a bi ta a hankali." Da ƙyar aka samu ta sha maganin, ta koma ta kwanta. *** "Ni fa ina ga kamar ƙafar nan akwai karaya, ba za a kai sa wajen Malam Ɗahe ya duba ba kuwa? Kwanansa biyu fa kenan da dawowa gida, bayan ya kwana ɗaya a asibiti. Ƙafar za ta yi masa tsami." Cewar Badiyya da ke kallon Kamal, lokacin da suka shigo duba Hamusu, a ɗaya daga cikin ɗakunan dake gidan wanda suka yi masa masauƙi. "Na yi tunanin hakan, na ga har yanzu ba ya taka ƙafar. Barin shirya sai in kai sa." Ficewa su ka yi, ya ta fi shiryawa. Hamusu da tun lokacin da aka ambaci karaya, ya ji damuwa ta ziyarcesa, fatansa kawai Allah ya sa buguwa ne ba karayar da suka ambata ba. Domin ko kwana biyu baya fatan ya kara a cikin garin nan, ba don rashin tafiyarsa ba ma, da tunda suka daukosa daga asibiti zai ce su saukesa a tasha. Sai dai rashin kuɗin moto da ba ya da shi a yanzu, shi zai taka masa burki, domin a cikin jakar kayansa ya sanya kuɗin, tunda kuma lamarin ya faru bai bi ta kansu ba, ta ransa kawai ya ke yi. Yanzu koda ya sami lafiya ma, dole sai ya nemi kuɗin moto. Ga shi duk jarinsa ya haɗa cikin jakar, tunowa da ya yi da gidan Alhaji Sama'ila ya sa ya ɗan ji sanyi, amma da kunya ya koma a yanzu ya ce musu ga tsautsayin da ya afka masa, tunda sun sallamesa. Wataƙila ma su ce ƙarya ya yi musu dama. Haka ya yi ta saƙe-saƙe, har likita ya fito, ya kamasa ya miƙe, ya saƙalo hannunsa ta wuya, ƙafa ɗayar a ƙasa, ɗayar kuma ya ɗangaleta, domin bai isa taka ta ba, tsananin raɗaɗi da azabar zafi ta ke yi masa. Badiyya da ke tsaye jikin motar ce ta yi saurin buɗe musu ƙofar baya, ya zaunar da shi, sannan ya zaga ya shiga, ta yi musu fatan alkairi ta koma ciki suma su ka tafi. Sosai ya azabtu wajen Malam Ɗahe mai ɗori, karaya ce a cinya, kuma ta yi tsami sosai. Gida suka nufa, bayan an gama da su. "Yaya! Don Allah, tsawon wani lokaci zan yi kafin a kwance mun wannan ɗaurin?" Hamusu ya tambayi Kamal, ganin zai fita daga ɗakin. Juyowa ya yi, ya ce, "Malam dai ya ce, wata huɗu, ko uku, idan har jikinka na da kyau. Zai riƙa turo yaronsa yana duba ka." Hawaye ne ya wanke masa fuska lokaci guda, yaraf! Ya koma ya kwanta. "Ka yi haƙuri Khamis! In Sha Allah kamar yau ne, za ka sami lafiya, ka koma garinku. Kada ka sanya ma kanka damuwa, ka sake janyo wata cutar." Yana kaiwa nan ya fice. "Wata huɗu ko uku?" Ya tambayi kansa. Ya dora da cewa, "Inna! Ƙaddara ta yi sanadin rashin haɗuwarmu a lokacin da na so. Wani hali kike a yanzu? Wa ke yi miki jagora akan dukkanin lamuranki? Wayyo Allah na!!" Ya faɗa cikin ɗaga murya. *** Kallo ɗaya za ka yi ma Inno ka san ta faɗa sosai, duk da ba ta nuna damuwarta a fili, damuwar a cikin ranta ta ke, ba ta kuma samun kanta cikin yanayi na rashin jin daɗi ba, sai da ta ga jama'a na ta tafiya gidajensu, kasantuwar an yi addu'ar kwana uku. Lubna kam, har yanzu tana cikin jimami haka ma Afreen, sai dai shi ta wajensa da sauƙi. "Hajiya kuma yanzu tafiyar za ku yi?" Inno ta tambayi Mommy da ke ta shirya kayansu a jaka. "Za mu tafi Inno, amma In Sha Allah za mu riƙa zuwa akai - akai wannan lokacin, babu jinkiri irin na baya." "Allah yasa!" "Amin. Akwai dai sauran kayan abinci nan da yawa ko?" "Eh, kinsan sun ce a maida na wajen Mai Unguwan nan." "Ya kamata, tunda ba auren aka yi ba, ba amfanin a ci gaba da yi musu amfani da wani abunsu, duk wasu kaya ma da yake na su, ya kamata a mayar musu." "Shi ke nan! Hakan za a yi." Inno ta amsa a sanyaye. Har waje aka rako su, ana yi musu fatan Allah ya kai su lafiya ya tsare hanya. "Wai ina Lubnar ta tsaya ne? Mun fito da ita fa, ta kuma komawa ciki, ko so take mu yi dare ne? Kai Muntari! Je ka ce ta fito mu tafi." Da gudu Muntari ya koma cikin gidan. A tsakar gida ya tarar da ita, ta durƙushe sai rabzar kuka take yi. "Aunty, Hajiyar Jinjin ta ce ki fito ku tafi ke ake jira." "Anti! Ki zo ku ta fi ke ake jira." Ya sake maimaita a karo na biyu. Jajayen idanunta da ke ta sauƙar da ruwan hawaye, tamkar indararo ta ɗago ta kallesa. A hankali ta ce, "Je ka ce su tafi, ba za ni ba." Kallon ta ya yi, sannan ya fita a guje. "Ina take?" Inno ta tambayesa. "Cewa ta yi wai su tafi ba za ta ba." Kallon juna su ka shiga yi, "Kamar ya ya mu je ba za ta ba?"Afreen ya tambaya. "Haka ta ce." Muntari ya amsa mishi. "Me ta ke yi?" Ya sake tambayar Muntari. "Kuke ta ke ta yi, tana tsakar gida ma." Duk suka sauka daga kan mashin ɗin suka yi cikin gidan, tare da sauran mutanen da su ka yi musu rajiya, anan suka sameta durkushe sai zabga kuka ta ke yi. Har gabanta Daddy ya ƙaraso, ya ɗagota. "Mamana me ke faruwa ne?" Kai ta ɗago ta kallesa, "Daddy! Don Allah ku tafi ku barni anan. Ku barni in koyi zama da mutane, in koyi sanin daraja da kima ta ɗan Adam, ku tafi ku barni in gyara hallayata da ɗabi'ata, ko nima zan iya rayuwa cikin mutane, in daina keɓe kaina waje ɗaya a kodayaushe, na roƙeku Daddy kada ku ce a'a, don Allah. Mommy! Zainab ta yi gaskiya, ban san komai ba game da zamantakewa cikin mutane, ku amince mun don Allah." Ta ƙarasa maganar tana durƙusawa kan gwiwoyinta; Ta haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo a garesu. Matsanancin tausayinta ya rufe illahirin mutanen da ke wajen. Kukan da ya ƙwace ma Inno ne ya sa ta juya da sauri ta nufi ɗakinta, don ta san da kamar wuya, gurguwa da auren nesa. Zai so zamanta shi ma, kamar yadda ta ce za ta gyara rayuwarta, shi ma yana fatan rabuwa da tasa mummunar ɗabi'ar saurin fushi da rashin yi ma mutane uzuri. Ɗagota ya yi, ya rungumeta a jikinsa, ya shiga shafa kanta a hankali. Saitin kunnenta ya kai bakinsa, "Za ki iya zama a nan?" Kai ta ɗaga "Za ki iya rayuwa a cikin garin nan?" Ta sake kaɗa kai. "Share idanunki, ki yi min alƙawarin kin daina wannan kukan daga yau, ki kuma saki ranki, zan barki anan na wani lokaci." Ɗagowa ta yi, ta matse idanunta, hawaye ya gangaro, ta sanya bayan hannunta ta goge, ta kalli Daddyn tana kuka mai haɗe da dariya a lokaci ɗaya. "Kalla!"Ya faɗa, yana taɓa kumatunta. "Ga wani hawayen na fitowa, da alama ba ki shirya zama ba." Da sauri, ta sanya hannayenta biyu, ta goge fuskar tana faɗin, "Na daina Daddy! Na daina, ka ga ma na goge ko?" Murmushi ya yi, ya kaɗa mata kai, ta rungumesa tana faɗin, "Na gode Daddy! Na gode sosai." Kallon Hajiya da Afreen da ke kallonsu tun ɗazu ya yi, suna jira su ji hukuncin da Daddyn zai yanke, da ma sauran jama'ar da ke wajen. Mommy da ke ta addu'ar, Allah ya sa ya amince ya bar ta,ya ga ta marairaice kamar za ta yi kuka, domin tana son ɗiyar tata ta zauna, ta koyi rayuwa cikin mutane, ta rage saurin fushi da ƙyamar mutane. Gira Alhaji ya ɗaga mata, alamar tambaya. Murmushin da ta yi masa ya fahimci ta amince, domin shi ma yana tantamar kada ta yi masa turjiya, don yana so ya barta ɗin ko da na sati biyu ne, ta ɗan ɗebe ma su Ilu kewar rashin 'yarsu da suka yi. Kallon Ilu ya yi, "Ga diyarku, mu za mu wuce, kada dare ya yi mana." Wani farin ciki ne ya ziyarci Ilu na irin karamcin da ya yi masa, "Amma Yaya! Kana ganin za ta iya rayuwa anan kuwa? Babu wasu ababe na more rayuwa da ta saba da su, kada kuma ta taƙura." Karaf ta cafke, "Zan iya Baba." "To, ai shi ke nan. Inno ta sami mai yi mata wanke - wanke da shara." Dariya duk suka yi. Sakin Daddyn ta yi, ta je ta shige jikin Mommy ta ƙanƙameta tamkar mai shirin komawa ciki, ta ce, "Na gode sosai Mommy!" Murmushi ta yi mata, "Ba komai, Allah ya yi miki albarka, ki kuma kula da kan ki, ki kare kima da darajarki ta 'ya mace, kamar yadda na ke umurtarki da shi kodayaushe." "Zan yi Mommy! Zan yi In Sha Allah." Afreen da ke tsaye a gefen Mommy ne ya dafa bayanta ya ce, "A sake mun Mommy haka, kada a ɓallata don an yi sabuwar Mommy a barni in shiga uku." Sake Mommyn ta yi, ta juyo ta rungumesa tana kuka, ta ce, "Almisyu ɗan'uwa!" Hawaye ne ya sako daga idonsa ya ce, "Ai rili mis u mai sista." Da gudu Muntari ya isa wajen Inno, ya sanar mata, sai ga ta da saurinta ta fito tana goge ido, zuciyarta fal! Farin ciki, ta yi musu godiya sosai tare da alƙawarin kula musu da 'yar su, yadda ya kamata idan Allah ya yarda. "Za ku saki juna mu tafi ko kuwa?" Mommy ta ce, ganin Lubna da Afreen ba su da niyyar barin juna. Sakinta ya yi, ya juya. Har ƙofar gida suka raka su, aka sauƙe ma Lubna kayanta, nan aka sake neman yafiyar juna, suka hau sai hanyar Jinjin. Sai da suka ɓace ma ganinsu, sannan suka shige gida. Dis is jos da biginin! Rayuwa daga Jinjin zuwa Mai Ludaya. Ko ya Rayuwar za ta kasance? Ya rayuwar Hamusu a Jinjin? Ya Inna Talle a Kurmawa? Ina labarin Mai Unguwa? Ku dakaceni cikin littafi na biyu mai suna *RAYUWAR LUBNA* (Cigaban Abulle) Nan ba da daɗewa ba. Godiya ta musamman ga: Badiyya Adam Yayana Almu Abu Hisham Ummu Mahmoud Da ɗaukacin masu bibiyar wannan labarin. Sannunku da jimurin bibiyar wannan labari, duk da tsaiko da aka yi ta samu, hakan bai sa kun nuna gajiyawarku ba. Na gode sosai Allah ya saka da alkairi Kura - kuran da ke ciki, Allah ya yafemin. *ALHAMDULILLAH!* 16/12/2019 _Ummyn Yusrah_*ABULLE TA MAI UNGUWA* *HAZAƘA WRITERS ASSOCIATION* _Ummyn Yusrah_ *K'arshe* _50_ Kowa ya tuba don wuya, ba lada. Inna Talle dai tun tana iya tsayuwa, har ƙafarta ta gaza ɗaukarta ta nemi waje ta zauna, daga zaunen ma gyangyaɗi take hakan ya sa ta ja tsufanta ta yi ɗaki don sanya haƙarƙarinta a makwanci, har lokacin ba wanda ya dawo. **** Tun daga yi mata sallah, zuwa kai ta makwancinta, zuwa yanzu da suke zaune ƙofar gida karɓar gaisuwa, gani ya ke, al'amarin tamkar almara, gani ya ke ba ta mutu ba. Idanu kawai ya zuba ma saitin ƙofar gidan, tamkar za ta fito, su zauna ta yi masa hirar shirmen nan nata. Addu'ar da ya ke, Allah ya sa ya farka daga wannan mummunar mafarkin da ya ke tun ɗazu. Ga shi nan dai zaune kamar mutum-mutumi, abu ne mawuyaci ka iya gane halin da ya ke ciki. Baya ga fitar numfashi da kiftawar idanunsa, babu wani abu da ke motsawa a jikinsa. "Haba Afreen! Kada ka bari tunani ya shige ka..." Daddy da ya matso kusa da Afreen ne ya yi masa magana, ganin hawayen da ya ziraro daga idanunsa zuwa kan fuskarsa ne ya sa ya katse maganar. Shiru ya yi na ɗan lokaci ya ci gaba. "Haƙuri da juriya shi ya kama ce ka, ka yi mata addu'a Afreen! Shi ta fi buƙata, ba kuka ba." "Me ya sa Daddy? Me ya sa tun a can ba ku sanar mana ba? Me ya sa kuka yi mana bazata? Ka fi kowa sanin wani hali Aunty Lubna za ta iya shiga a wannan lokacin. Na tabbatar idan ni na daure a matsayina na Namiji, ka sani ita ba lallai ta iya jurewa hakan ba. Da tun a can kuka sanar mana da komai, na san za ku taushe ta kafin mu zo..." Kuka ne ya ƙwace masa. Rungumosa ya yi jikinsa ya shiga bubbuga bayansa, yana magana. "Gudun faruwar hakan ya sa muka ƙi sanar da ku, domin mun san shaƙuwar da ke tsakaninku zai iya jefa ku cikin wani hali. Ka yi ƙoƙarin riƙe kanka, ka ga taron mutanen nan duk kai su ke kallo. Ka shiga ciki ka duba wani hali su ke ciki." Ɗago kan da zai yi, su ka yi ido biyu da Sarkin fada da ke ta galla masa harara, shi a dole yana taya Mai Unguwa kishi, gani ya ke kamar saurayinta ne. "Zan shiga, ba yanzu ba. Daddy waye wancan da ya kima rawani, tamkar kullin kayan wanki?" Ya tambaya yana kallon saitin da tawagar mai Unguwa ke zaune. "Sarkin fada ne, wancan ɗayan kuma shi ne Mai Unguwa." Daddy ya ba shi amsa. "Banza girman kato, ƙaramin mai hankali ya fishi. Idan ba zalunci ba, kamar wannan a ce shi za a ba Zainab? Ga shi ma Ubangiji ya karɓi abarsa. Shi ma Baba Ilun ko makancewa ya yi ne Ohho!" Cewar Afreen da shi ma ke ta aike musu da saƙon harara, ga kuma wani kululun takaici da ya gama tokare masa maƙoshi, ji ya ke, kamar ya tashi ya je ya shaƙo wuyan tsoho mai budurwar zuciyar nan, domin shi ne sila. Da bai ballo zancen aure ba, da yanzu tana raye. "Ranka shi daɗe! Anya ba za mu bar wajen nan ba? Sai ƙus-ƙus ake yi, kuma da alama duk kai su ke kallo, gani su ke duk kai ne sanadin komai, da ba a daga zancen aure ba da hakan bai faru ba." Cewar Sarkin fada, da ya dawo da fuskarsa ga mai unguwa, bayan sake aika ma Afreen da wani mugun harara. Kansu na haɗe ya ke maganar cikin murya ƙasa-ƙasa. "Allah ko? Gara mu zo mu tafi, nima duk a tsarge nake, ga kuma masassarar nan da ta dameni sosai." "Mu yi musu sallama kawai mu wuce, tun kafin a fara aiko mana da makaman ƙare dangi ta ido. Ka ga wancan matashin da ke saiti na? Wannan da gani taƙadari ne, ina ga kuma saurayinta ne. Ja'iri mai kama da ƙosai." "Na hangosa, sai saƙonni ya ke aikon ta ido. Sallamesu sai mu wuce." Sallama su ka yi, bayan Sarkin fada ya sanar da su cewar, masassara ta dami mai unguwa sakamakon faruwar wannan al'amari. ***** "Kinga ni ko? Na ce ki sassauta kukan nan kada ya ja miki zazzaɓi, amma tamkar zugaki na ke, dubi yadda kike ta ɓarin sanyi, kamar wacce aka izama shokin." "Hajiya a bi ta a hankali, kin san irin wannan sabo na kwana kaɗan ya fi shiga jiki, ga kuma mutuwa ta farat ɗaya, dole abun ya dameta." Inno da ke jan carbi ta yi magana ganin yadda Mommy ke yi ma Lubna da ke kuɗunɗune faɗa. "Sai a ka ce ta yi ta kuka? Ashe ba za ta sanya ma ranta haƙuri ba? Duk wata shaƙuwa da suka yi, ya kai shaƙuwar da kuka yi ke da kika haifeta? Yanzu ina za a samu asibiti nan kusa?" "Babu kam! Asibitin ɗaya ne, kuma ba ma'aikata. Akwai saiwa ai, idan za ta iya sha sai a kawo mata, a yi haƙuri a bi ta a hankali." Da ƙyar aka samu ta sha maganin, ta koma ta kwanta. *** "Ni fa ina ga kamar ƙafar nan akwai karaya, ba za a kai sa wajen Malam Ɗahe ya duba ba kuwa? Kwanansa biyu fa kenan da dawowa gida, bayan ya kwana ɗaya a asibiti. Ƙafar za ta yi masa tsami." Cewar Badiyya da ke kallon Kamal, lokacin da suka shigo duba Hamusu, a ɗaya daga cikin ɗakunan dake gidan wanda suka yi masa masauƙi. "Na yi tunanin hakan, na ga har yanzu ba ya taka ƙafar. Barin shirya sai in kai sa." Ficewa su ka yi, ya ta fi shiryawa. Hamusu da tun lokacin da aka ambaci karaya, ya ji damuwa ta ziyarcesa, fatansa kawai Allah ya sa buguwa ne ba karayar da suka ambata ba. Domin ko kwana biyu baya fatan ya kara a cikin garin nan, ba don rashin tafiyarsa ba ma, da tunda suka daukosa daga asibiti zai ce su saukesa a tasha. Sai dai rashin kuɗin moto da ba ya da shi a yanzu, shi zai taka masa burki, domin a cikin jakar kayansa ya sanya kuɗin, tunda kuma lamarin ya faru bai bi ta kansu ba, ta ransa kawai ya ke yi. Yanzu koda ya sami lafiya ma, dole sai ya nemi kuɗin moto. Ga shi duk jarinsa ya haɗa cikin jakar, tunowa da ya yi da gidan Alhaji Sama'ila ya sa ya ɗan ji sanyi, amma da kunya ya koma a yanzu ya ce musu ga tsautsayin da ya afka masa, tunda sun sallamesa. Wataƙila ma su ce ƙarya ya yi musu dama. Haka ya yi ta saƙe-saƙe, har likita ya fito, ya kamasa ya miƙe, ya saƙalo hannunsa ta wuya, ƙafa ɗayar a ƙasa, ɗayar kuma ya ɗangaleta, domin bai isa taka ta ba, tsananin raɗaɗi da azabar zafi ta ke yi masa. Badiyya da ke tsaye jikin motar ce ta yi saurin buɗe musu ƙofar baya, ya zaunar da shi, sannan ya zaga ya shiga, ta yi musu fatan alkairi ta koma ciki suma su ka tafi. Sosai ya azabtu wajen Malam Ɗahe mai ɗori, karaya ce a cinya, kuma ta yi tsami sosai. Gida suka nufa, bayan an gama da su. "Yaya! Don Allah, tsawon wani lokaci zan yi kafin a kwance mun wannan ɗaurin?" Hamusu ya tambayi Kamal, ganin zai fita daga ɗakin. Juyowa ya yi, ya ce, "Malam dai ya ce, wata huɗu, ko uku, idan har jikinka na da kyau. Zai riƙa turo yaronsa yana duba ka." Hawaye ne ya wanke masa fuska lokaci guda, yaraf! Ya koma ya kwanta. "Ka yi haƙuri Khamis! In Sha Allah kamar yau ne, za ka sami lafiya, ka koma garinku. Kada ka sanya ma kanka damuwa, ka sake janyo wata cutar." Yana kaiwa nan ya fice. "Wata huɗu ko uku?" Ya tambayi kansa. Ya dora da cewa, "Inna! Ƙaddara ta yi sanadin rashin haɗuwarmu a lokacin da na so. Wani hali kike a yanzu? Wa ke yi miki jagora akan dukkanin lamuranki? Wayyo Allah na!!" Ya faɗa cikin ɗaga murya. *** Kallo ɗaya za ka yi ma Inno ka san ta faɗa sosai, duk da ba ta nuna damuwarta a fili, damuwar a cikin ranta ta ke, ba ta kuma samun kanta cikin yanayi na rashin jin daɗi ba, sai da ta ga jama'a na ta tafiya gidajensu, kasantuwar an yi addu'ar kwana uku. Lubna kam, har yanzu tana cikin jimami haka ma Afreen, sai dai shi ta wajensa da sauƙi. "Hajiya kuma yanzu tafiyar za ku yi?" Inno ta tambayi Mommy da ke ta shirya kayansu a jaka. "Za mu tafi Inno, amma In Sha Allah za mu riƙa zuwa akai - akai wannan lokacin, babu jinkiri irin na baya." "Allah yasa!" "Amin. Akwai dai sauran kayan abinci nan da yawa ko?" "Eh, kinsan sun ce a maida na wajen Mai Unguwan nan." "Ya kamata, tunda ba auren aka yi ba, ba amfanin a ci gaba da yi musu amfani da wani abunsu, duk wasu kaya ma da yake na su, ya kamata a mayar musu." "Shi ke nan! Hakan za a yi." Inno ta amsa a sanyaye. Har waje aka rako su, ana yi musu fatan Allah ya kai su lafiya ya tsare hanya. "Wai ina Lubnar ta tsaya ne? Mun fito da ita fa, ta kuma komawa ciki, ko so take mu yi dare ne? Kai Muntari! Je ka ce ta fito mu tafi." Da gudu Muntari ya koma cikin gidan. A tsakar gida ya tarar da ita, ta durƙushe sai rabzar kuka take yi. "Aunty, Hajiyar Jinjin ta ce ki fito ku tafi ke ake jira." "Anti! Ki zo ku ta fi ke ake jira." Ya sake maimaita a karo na biyu. Jajayen idanunta da ke ta sauƙar da ruwan hawaye, tamkar indararo ta ɗago ta kallesa. A hankali ta ce, "Je ka ce su tafi, ba za ni ba." Kallon ta ya yi, sannan ya fita a guje. "Ina take?" Inno ta tambayesa. "Cewa ta yi wai su tafi ba za ta ba." Kallon juna su ka shiga yi, "Kamar ya ya mu je ba za ta ba?"Afreen ya tambaya. "Haka ta ce." Muntari ya amsa mishi. "Me ta ke yi?" Ya sake tambayar Muntari. "Kuke ta ke ta yi, tana tsakar gida ma." Duk suka sauka daga kan mashin ɗin suka yi cikin gidan, tare da sauran mutanen da su ka yi musu rajiya, anan suka sameta durkushe sai zabga kuka ta ke yi. Har gabanta Daddy ya ƙaraso, ya ɗagota. "Mamana me ke faruwa ne?" Kai ta ɗago ta kallesa, "Daddy! Don Allah ku tafi ku barni anan. Ku barni in koyi zama da mutane, in koyi sanin daraja da kima ta ɗan Adam, ku tafi ku barni in gyara hallayata da ɗabi'ata, ko nima zan iya rayuwa cikin mutane, in daina keɓe kaina waje ɗaya a kodayaushe, na roƙeku Daddy kada ku ce a'a, don Allah. Mommy! Zainab ta yi gaskiya, ban san komai ba game da zamantakewa cikin mutane, ku amince mun don Allah." Ta ƙarasa maganar tana durƙusawa kan gwiwoyinta; Ta haɗe hannayenta waje ɗaya alamar roƙo a garesu. Matsanancin tausayinta ya rufe illahirin mutanen da ke wajen. Kukan da ya ƙwace ma Inno ne ya sa ta juya da sauri ta nufi ɗakinta, don ta san da kamar wuya, gurguwa da auren nesa. Zai so zamanta shi ma, kamar yadda ta ce za ta gyara rayuwarta, shi ma yana fatan rabuwa da tasa mummunar ɗabi'ar saurin fushi da rashin yi ma mutane uzuri. Ɗagota ya yi, ya rungumeta a jikinsa, ya shiga shafa kanta a hankali. Saitin kunnenta ya kai bakinsa, "Za ki iya zama a nan?" Kai ta ɗaga "Za ki iya rayuwa a cikin garin nan?" Ta sake kaɗa kai. "Share idanunki, ki yi min alƙawarin kin daina wannan kukan daga yau, ki kuma saki ranki, zan barki anan na wani lokaci." Ɗagowa ta yi, ta matse idanunta, hawaye ya gangaro, ta sanya bayan hannunta ta goge, ta kalli Daddyn tana kuka mai haɗe da dariya a lokaci ɗaya. "Kalla!"Ya faɗa, yana taɓa kumatunta. "Ga wani hawayen na fitowa, da alama ba ki shirya zama ba." Da sauri, ta sanya hannayenta biyu, ta goge fuskar tana faɗin, "Na daina Daddy! Na daina, ka ga ma na goge ko?" Murmushi ya yi, ya kaɗa mata kai, ta rungumesa tana faɗin, "Na gode Daddy! Na gode sosai." Kallon Hajiya da Afreen da ke kallonsu tun ɗazu ya yi, suna jira su ji hukuncin da Daddyn zai yanke, da ma sauran jama'ar da ke wajen. Mommy da ke ta addu'ar, Allah ya sa ya amince ya bar ta,ya ga ta marairaice kamar za ta yi kuka, domin tana son ɗiyar tata ta zauna, ta koyi rayuwa cikin mutane, ta rage saurin fushi da ƙyamar mutane. Gira Alhaji ya ɗaga mata, alamar tambaya. Murmushin da ta yi masa ya fahimci ta amince, domin shi ma yana tantamar kada ta yi masa turjiya, don yana so ya barta ɗin ko da na sati biyu ne, ta ɗan ɗebe ma su Ilu kewar rashin 'yarsu da suka yi. Kallon Ilu ya yi, "Ga diyarku, mu za mu wuce, kada dare ya yi mana." Wani farin ciki ne ya ziyarci Ilu na irin karamcin da ya yi masa, "Amma Yaya! Kana ganin za ta iya rayuwa anan kuwa? Babu wasu ababe na more rayuwa da ta saba da su, kada kuma ta taƙura." Karaf ta cafke, "Zan iya Baba." "To, ai shi ke nan. Inno ta sami mai yi mata wanke - wanke da shara." Dariya duk suka yi. Sakin Daddyn ta yi, ta je ta shige jikin Mommy ta ƙanƙameta tamkar mai shirin komawa ciki, ta ce, "Na gode sosai Mommy!" Murmushi ta yi mata, "Ba komai, Allah ya yi miki albarka, ki kuma kula da kan ki, ki kare kima da darajarki ta 'ya mace, kamar yadda na ke umurtarki da shi kodayaushe." "Zan yi Mommy! Zan yi In Sha Allah." Afreen da ke tsaye a gefen Mommy ne ya dafa bayanta ya ce, "A sake mun Mommy haka, kada a ɓallata don an yi sabuwar Mommy a barni in shiga uku." Sake Mommyn ta yi, ta juyo ta rungumesa tana kuka, ta ce, "Almisyu ɗan'uwa!" Hawaye ne ya sako daga idonsa ya ce, "Ai rili mis u mai sista." Da gudu Muntari ya isa wajen Inno, ya sanar mata, sai ga ta da saurinta ta fito tana goge ido, zuciyarta fal! Farin ciki, ta yi musu godiya sosai tare da alƙawarin kula musu da 'yar su, yadda ya kamata idan Allah ya yarda. "Za ku saki juna mu tafi ko kuwa?" Mommy ta ce, ganin Lubna da Afreen ba su da niyyar barin juna. Sakinta ya yi, ya juya. Har ƙofar gida suka raka su, aka sauƙe ma Lubna kayanta, nan aka sake neman yafiyar juna, suka hau sai hanyar Jinjin. Sai da suka ɓace ma ganinsu, sannan suka shige gida. Dis is jos da biginin! Rayuwa daga Jinjin zuwa Mai Ludaya. Ko ya Rayuwar za ta kasance? Ya rayuwar Hamusu a Jinjin? Ya Inna Talle a Kurmawa? Ina labarin Mai Unguwa? Ku dakaceni cikin littafi na biyu mai suna *RAYUWAR LUBNA* (Cigaban Abulle) Nan ba da daɗewa ba. Godiya ta musamman ga: Badiyya Adam Yayana Almu Abu Hisham Ummu Mahmoud Da ɗaukacin masu bibiyar wannan labarin. Sannunku da jimurin bibiyar wannan labari, duk da tsaiko da aka yi ta samu, hakan bai sa kun nuna gajiyawarku ba. Na gode sosai Allah ya saka da alkairi Kura - kuran da ke ciki, Allah ya yafemin. *ALHAMDULILLAH!* 16/12/2019 _Ummyn Yusrah_