*🌈 IDAN BA KE 🌈* _True Life story_ arewanovels.com.ng Jimeta/Yola Njoɓoli Rugar Rome Gudu Saniyar take tana bin ta a baya itama, hannunta riƙe da sanda na korar Nagge, tamkar wanda suke wasan tsere haka Saniyar ke gudu a cikin jejin ita ma bata fasa bin ta ba, sauran Naggen suna gefe guda ko wacce na cin ciyayi wanda bisa kuskure tana can tana bin Saniya ɗaya tilo, sauran Naggen suka faɗa cikin gonar wani manomi, a yunwace suka rufarwa albarkatun gonar. Cikin siririyar muryarta mai nuni da Yarintar ta, da kuma nuna cewa ita ɗin zallar bafullatanar Yola ce ƴar Usul. "Waru! Waru! Waru" shi ne abin da yarinyar ke ta nanatawa cikin hausarta ta Fulani, yayinda Saniyar tuni tai mata nisa cikin gajiya wa da bin Saniyar ta tsaya a wajan wata gaɓar ruwa tana riƙe ƙugunta ta ce "Bone, lalashewa ta samu Nagge Aradu" da sauri kuma ta ɗauki sandar tana ƙara yin kan Saniyar ganin ta tsaya da gudun da take, cikin sa'a ta cimmata tana zuwa ta kama ƙahonta tare da ƙifƙifta idanunta alamar zallar fitsarar dake tattare da ita "d'ume ngid'd'a?" Ma'ana "me kake so?" Kallon ta Saniyar ta yi sai kuma ta kaɗa jela tare da zubewa a wajan ta shiga shura ƙafafuwa kamar zata mutu, cikin tsoro haɗi da razani HALISA ta ce "Jomirawo ka taimakeni" ta faɗa tana kallon Saniyar wacce tai male-male a ƙasa ga wani ruwa mai kama da jini na fitowa ta ƙasanta, kuka Halisa ta sanya domin idan Saniyar ta mutu a nan wajan ta shiga uku, itama watan mutuwarta ya kama. Tsayar da kukan tai kafin ta fara duba cikin jeji babu kowa sai ita, ga wani kwantaccen baƙin hadari dake ƙasa wanda a koda yaushe zai iya tashi. Juyawa tayi ta nufi wajan wata bishiya inda ta hangi ƙaramar igiya a jiki, tana zuwa jikin bishiyar ta zame hular Fulanin dake kanta, nan da nan sumar kanta ta sauka wacce take jajir babu alamar baƙi ko ɗaya, gashin ba wani cika ne dashi ba, kawai tsayin gashi gareta, domin har fatar tsakiyar kanta ana iya ganowa. cikin sayin jikinta ta fara jan igiyar tana ƙoƙarin kunce igiyar gaba ɗaya daga jikin reshen bishiyar, kamar daga sama taji saukar wani abu mai sanyin gaske zuwa kafaɗunta. Cak ta tsaya tana sauraren yadda abin ke tafiya sululuuuu a jikinta har ya gama sauka, hannunta ta miƙa da nufin kama abin da ya sakko mata domin bata da tsoro ko kaɗan, cikin rashin sa'a hannunta ya sauka saman ƙaton kan maciji wanda yake kwance a jikinta, wani santsi-santsi ta ji a jikin macijin ga wani sanyi sosai dake ratsa fatar jikinta, bata gama yadda da abin da zuciyarta ke ayyana mata ba, a hankali ta juya wani ihu ta kurma wanda ya yi daidai da ɗaukewar numfashinta, baya tayi zata faɗi kafin ta kai zuwa ƙasa macijin ya yi wata girgiza cikin sakanni ya juye zuwa wani saurayi wanda jikinsa ya ke sanye da wasu haɗaɗɗun kayan sarauta na farin saƙi, fari ne tas amma kamar Fatar mace haka fatar hannunsa da sauran jikinsa suke gaba ɗaya gashi ya kwanta luff. Zubewa ya yi a ƙasa ta faɗo jikinsa idanunsa a kan fuskarta, ya jima yana kallonta kafin cikin izza da nutsuwa ya ce "kin tsoratani, kin tsorata kanki Danejo, banyi niyyar zuwar maki ba yanzu" Danejo sunan da ƴan rugar Rome suke faɗawa Halisa ke nan. Sai da ya gama Kallon ta sosai, kallon da ya jima bai mata ba tun tana zanin goyo matsayin Jaririya. Ɗaukanta ya yi ya nufi inda Naggen suke yana zuwa ya tarar da wannan Saniyar dake Shure Shure ta haihu, ashe daman ciwon haihuwa ke damunta. Halisa ya kalla yana sakin Murmushi kafin ya zaro harshesa waje sai ga wani zobe ya bayyana, cikin sauri ya saka mata zoben mai ɗauke da tambarin wata masarauta, kafin ya yi Girgiza sai ga shi ya sauya kama, kamarsa a fuska na nan, amma kayan jikinsa sun sauya sun koma irin kayan Fulani sak komai da komai, goya Danejo ya yi a bayansa, ya ɗauki jaririn Saniyar cikin nutsuwa ya fara kaɗa Naggen zuwa Rugar Rome. Kamar ƙifatawar idanu haka ya ƙaraso Rugar.. Iskar dake kaɗawa na alamar tashin hadarin ya sanya matashin ɗaga kansa sama, yana kallon yadda gajimare ke haɗa kansa. A nutse kuma ya fara bin Rugar Rome da kallo ba wata babba bace, amma Ubangiji ya albarkaci rugar da dabbobi musamman Nagge, gasu manyan gwanin sha'awa yawancinsu jajaye ne kafin ka samu farar saniya zaka daɗe. Wasu sun dawo daka kiwo wasu kuma na hanya sbd rashin yawaitar mutane da babu a rugar, daidai wajan wata bukka ya Ƙarasa yana gyara riƙon da ya yi wa Jaririyar Saniyar kafin ya ce "Sannunmu dai" ya faɗa a taushashe jin shiru ya sanya ya ƙara buɗe muryarsa mai sanyi ya ce "Afuwanku dai" daga cikin bukkar wata ƙaramar murya ta amsa da faɗin "Waye nan?" Ta faɗi hakan tana fitowa, lokacin da Idanunta ya sauka acikin ƙwayar matashin gabanta taji ya faɗi saboda yadda taga ƙwayar idanunsa, gane cewa kamar ta tsorata da yanayinsa ya sanya ya lumshe idanunsa kaɗan tare da buɗewa ya ce "Ga ɗan uwanki na kawo shi, arado bashi da lafiya ne can na ganosa yashe a jeji ba rai, har naggenku ya samu zuri'a" yana faɗin hakan ya ajjiye Jaririyar Saniyar a ƙasa wacce take jajir da ita Kuma ƙatuwa. Shatu dai binsa take da Idanunta domin bata taɓa ganin mai kama dashi a rugar ba sai yau, kallon da yaga yai yawa ne yasa ya ce "Shai a mata magani" a hankali ya sauke Halisa Dajeno ya kwantar a ƙasa a nan gaban bukkar kamar zai juya ya tafi sai kuma ya ƙurawa zoben hannunta idanu wanda yake sheƙi sosai ga tambarin masarauta nan ya fito sosai a jikinsa, a ransa yake ji kamar bai dace daya mallaka mata wannan zoben ba, amma bashi da wani zaɓi dole ya bata ta haka ne kawai zai lalubota a duk sanda ta ɓace masa, tun tana ciki yake fama da rainonta lokacin haihuwarta ne kawai bai sani ba. Ba tare da ya ƙara cewa komai ba ya juya da sauri ya fara tafiya tare da shankwana, yana barin wajan ya ƙara yin girgiza wata iska mai daɗi da guguwa ta mamaye gaba ɗaya cikin Rugar Rome. Nan take ya koma asalin macijinsa kamar yadda ya bayyana a farko, yana iya komawa duk suffar da yaga dama cikin ƙaramin lokaci amma zama maciji yafi masa daɗi sbd yawaitar macije dake cikin jejin daya zagaye Rugar Rome, a haka ya sulale tare da komawa cikin jejin. Iskar dake kaɗawa ce tai sanadiyyar farkawar Dajeno daga barcin dolen da macijin ya sanyata a ruɗe ta miƙe tana dafe kanta dake mata ciwo sosai cikin sanyin murya ta ce. "Miyyati Allah" Shatu dake gefen Dajeno tana ɗaure Naggen a garken dake dab da bukkar ta ce "Nassu, ka shigo" Shiru Danejo tai kamar zata tuna wani abu sai kuma tai saurin ware manyan idanunta ta ce "Shai Shatu ina Dadana ya tashi daga barci hoo?" Shatu ta ce "E, yana ta kiranka baka dawo ba, ciwonsa ya tashi yana ta masa zafi" da sauri Danejo ta faɗa cikin bukkar Idanunta ya sauka akan Dada (her mother) tana kwance a rufeta da wani farin zani jikinta sai rawa yake, fara ce matar sosai amma yanayin jikinta kamar ta shekara 60 nan kuma ba tafi shekaru 50 ba idan ma ta cika. "Shannu shannu Dadana" Idanu Dada ta buɗe da ƙyar ta ce "Zakiyi Albarka Halisa ki riƙe gaskiya da amana ki zama mai haƙuri ki daina saurin fushi da rashin kunya" Kallo juna sukai da Shatu da Halisa wacce akafi sani da Dajeno "Dada me yasa kake shaiwa haka?" Dada ta kalli Shatu kana ta juya ta kama Hannun Dajeno ta haɗa dana Shatu ta ce "Meyasa ba zance haka ba? Shatu kece ƙarama Halisa ita ce babba amma zafin zuciya ne da ita, rauninta akai na yake, kuma dole na tafi na barta" da sauri Shatu ta kalli Dada tana faɗin "Ina zaka Dada kuma?bayan Rugar Rome ina muke dashi" Dada ta numfasa ta ce "Babu da inda yafi wannan Rugar, zan tafi zuwa ga Mahaliccin daya samar da Rugar Romen, ciwon nan ba zai barni ba kuɗin amanata ce musamman ke Halisa" Dajeno kasa cewa komai tai sai ƙurawa Dada fararen idanunta da tayi zuciyarta cike da fargaba. "Dadana ba zaki mutu ba, idan kin mutu wa muke dashi a nan rugar wazai dinga kulawa damu?" Dajeno ta ƙare maganar cikin sanyin murya gaba ɗaya jikinta yai sanyi sosai. Shiru kawai Dada tai can kuma ta ce "Hamma Yabi ya dawo?" "A'a birni da nisa Dadana yace gobe zai kai ki can asibitin birnin". Jinjina kai Dada tai Dajeno ta miƙe bayan ta ce Shatu ta kula da Dada yanzu zata wajan Sarkin ruga ta amso magani. Cikin sanyin jikin nan nata take tafiya kanta a ƙasa domin bata fiya kallon mutane ba, a yadda jikin Danejo yake da sanyi zaka ɗauka babu ruwan ta, musamman da fuskarta yai kala dana salihai amma zafi da zuciya gareta, ga kuma taurin kai da naci akan abu, idan tace zatai to tabbas zatai, amma idan tace A'a babu wanda ya isa juyata ko Dada sai dai ta zuba mata Idanu. Abin birgewa ga rayuwar Halisa Dajeno tana da saurin yafiya, da kuma tausayi da kuma kawaici. Cikin tafiyar nutsuwa ta Ƙarasa gaban wata bukka wacce tafi ko wacce bukka kyau da girma a cikin Rugar Rome. "Shai shai Mene haka kamar makauniya ina kwaɗa miki shandan nan Aradu" da sauri Danejo ta ɗaga idanunta ta kalli Gwaggo Niyabi wacce ke zaune tana kaɗa audiga, murguɗa baki tai ba tare data ce komai ba, jin tai shiru yasa Gwaggo faɗin "Ko njid'ud'a?" "Magani za'a bawa Dadana" Gwaggo Niyabi ta ce "To baya nan" shiru tai kamar zatai Mgn sai kuma ta juya sai da tayi nisa kaɗan Gwaggo Niyabi ta ce "Yaka Dajeno waru" tsaye Dajeno tai domin ba shiri suke da Gwaggo ba, Murmushi Gwaggo tai sosai kafin ta numfasa ta ce "Idan kinje ki tambayi Dada waye mahaifinki, mene yasa daya rasu bata bar Rugar Rome ba, ta tafi danginta ko dangin mijinta" da mamaki Danejo ta ce "To bayan Baffa ya rasu mene na tambayarsa, ki daina maganar Uwayena" Gwaggo ta miƙe tana kallon Danejo "To ana gab da kurarku a Rugar Rome, domin bama son mara gurbi" harara Danejo ta watsa mata ta ce "Miyidi saro'am" ma'ana ina son iyayena "Kalleki mai ƙaton baki da ƙwalaƙwalan idanu" tana faɗin hakan ta kwasa da gudu zuwa bukkarsu. Da ƙyar suka samu zazzaɓi Dada ya sauka tasha paracetamol sai 12 na dare ta samu barci. Shatu ma barci take kusa da Dada a hankali Danejo ta miƙe daga kwancan da take har yanzu fararen kayan Fulani ne sanye a jikinta, hula ta ɗauka ta rufe kanta a nutse ta fita daga cikin bukkar kai tsaye garken shanun dake dab da bukkar ta nufa, wanda aka kunna musu wuta tana ci kaɗan kaɗan. Gobe da sassafe take son tafiya tallan kindirmon. ƙwarya ta ɗauka ta tsuguna tare da kama nonon jikin wata Nagge ta fara tatsa gaba ɗaya hankalinta baya jikinta sai a lokacin maganar Gwaggo Niyabi ta faɗo mata, a haka ta gama tatsar nonon acikin ƙwayar ta ajjiye can gefe guda a bukkar tasu. Gari na waye ba tare da yin wanka ba ta shasshafa ruwa ƙafa duk lam'a ta dungura sallah. Dada na gefe tana kallon yadda take sallah tana son tuna wani abu amma ta kasa har zuciyarta take jin kamar yadda Danejo ke sallah ba haka ake yi ba, amma ta kasa ganewa da kuma tuna yadda ake?. "Ina Hamma Yabi?" Danejo ta kalli Dada tace "Mi naddi mo (na kira shi)". Jinjina kai Dada tai, Danejo sai kallon Dada take kamar zatai shiru sai kuma tace "Dada waye Baffa?" Da sauri Dada ta juya gabanta na faɗuwa sosai na rashin amsar tambayar Danejo tace "Kamarya Halisa? Baffa mahaifinku ne kuma ya rasu mene?" "Na sani Dada, ina dangin Baffana suke me yasa muke zaune a Rugar Rome?" A hargitse Dada ta ɗaga hannunta tare da ɗauke Danejo da mari sai kuma ta fashe da kuka ta ce "Wacce masifa ce wannan kika koya Dajeno? Bance miki nice Dangin uwa dana uba a gareku ba? Ban gaya miki ba Halisa?" Hawaye na sauka a fuskar Halisa ta ce "Kiyi haƙuri Dadana ba zan sake ba, ban san mene yasa nai miki wannan tambayar ba" kasa magana Dada tai saboda hakin daya fara cin ƙarfin ta, zuciyarta na bugawa da ƙarfi Danejo na ƙwala ihu ta shiga kiran sunan Hamma Yabi wanda ke garken shanu, tattara Dada Hamma Yabi yai zuwa wani ƙaramin asibiti dake gefen Rugar, suna zuwa kusan sune na farko amma abin mmki sai kwasar wasu ake ana barinsu sbd cin hancin da suke bawa Nurse's ɗin, har lokacin tashi yai ba'a samu damar duba Dada ba a haka suka dawo gida. Yola South Abti America Babbar makaranta ce Wacce ta kasance Private school tun daga primary school har zuwa University makarantar dake da ita, Abti America mallakin mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na yanzu Atiku Abubakar ce. Makarantar na cikin Yola South ko ace Yola town duk ɗaya. Makaranta ce wacce sai ɗan wane da wane suke zuwanta duk wanda ka gani a ciki to ka tabbatar ubansa ya mallaki arziƙi ba dukiya ba. Adamawa/jimeta. Yola shi ne babban birnin jihar Adamawa. Yola South ana kiranshi da Yola town acan fadar lamiɗon Adamawa yake ma'ana gidan sarauta (LAMIƊO'S PALACE). Yola North, jimeta kenan. Acan fadar gwamnati yake, jimeta yafi kyau haɗuwa da tsari fiye da Yola South. Manyan abubuwa gaba ɗaya acan Yola North wato jimeta suke. Babu wani nisa tsakanin Yola South da Yola North/jimeta hasali ma roundabout ne ya raba tsakaninsu, akwai wani roundabout mai ƙwayoyin ƙwaryar nono da ludayi a kai muna ana kiransa da Yola roundabout, akan hanyar express yake daga shi sai wata ƙofa, to wannan ƙofar shine da zarar ka shigeta ka shiga yola kenan, sunan ƙofar “JIPPAJAM” da kuma “JAƁƁAMA” Ma'anar Jippajam shi ne Ka sauka lafiya. Wannan idan kazo fita kenan ta cikin yola zaka ganshi, idan shiga garin zakayi kuma za ka ga an rubuta Jaɓɓama ma'ana Sannu da zuwa. Njoɓoli wani ƙauye ne sosai dake cikin ƙauyukan dake zagaye da Yola south wato yola town,ƙauyen yawancinsu fulani ne makiyaya,amma akwai manoma ma, babu nisa da cikin gari, sannan suna da tashar mota mai tafiya ƙauyen a cikin yola. Wannan kenan. Tana tafe hannunta riƙe da sanda tana kaɗawa, a hankali bakinta ke motsawa tana karanta 1,2,3-10 cikin fillatancin karatunta bai nisa ba, babu arabi ba boko kuma ba za'a kirata da jahila ba,ita dai gata nan ne dai, ba wanka sosai ma'ana ba tsafta. Go'a 1 D'id'i 2 Tati 3 Nay 4 juy 5 Je go'o 6 haka ta dinga maimaitawa har ta ƙarasa can nesa da gate ɗin makarantar Abti America. Ajjiye ƙwayar kanta tai tare da neman waje ta zauna tana jira a tashi duk da cewa ba'a talla amma sbd ƙarancin masu sai da kindirmo yasa ake siyan nono a wajanta sosai. Tana zaune wata mota baƙa ta taho da gudu gadan-gadan zata take Danejo cikin tsoro da firgita har tana ture ƙwayar nonon Danejo ta miƙe tsaye tare da fasa ihu tana ƙanƙame jikinta idanunta rufe sbd gaba ɗaya motar kanta tayo da alama giyar motarce ta ƙwace. Motar na gab da taka Dajeno ba zato taji an saka hannu tare da yin sama da ita... 😌🫣 let's see yadda zaku amshi labarin HALISA DAJENO wanda ya faru a gaske bawai fiction story bane.*🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta *_Arewabooks@Nimcyluv_* 2. Ihu Danejo ta fasa lokacin da taji an saka hannu tare da yin sama da ita cikin muryarta ta Fulani ta ce "Mi boni Dada'am mi nasti tati hande mi mayi" gaba ɗaya ta tsorata ta ɗauka motar za tabi ta kanta. Jin an direta gefe guda ya sanya ta buɗe idanunta a hankali a tsaye ta gansa nesa da ita kaɗan hannunsa harɗe a ƙirji yana ƙare mata kallo tare da nazartar yanayinta. Kasa daina kallonsa Danejo tai sbd yanayin shigar jikinsa wani farin yadi ne a jikin nasa amma yai baƙiƙƙirin sbd dauɗar daya haɗa gaba ɗaya yadin ya yayyage har ana iya ganin farar fatar jikinsa, sumar kansa rabi furfura rabi baƙa. Ajjiyar zuciya ta sauke da sauri kuma ta juya sbd ƙarar motar da taji sai a lokacin lura da shegewar motar cikin Abti America. Ƙugu ta riƙe tana fari da manyan idanunta cike da tsiwa ta ce "Shai mutum ya tsaya yaga yadda ake tijara aradu ina iya fasa gilahin moto ɗin" daga bayanta taji murya mai sanyi ta daki kunnenta ance "Zaki biya?" Juyawa tai ta kallesa mutumin ɗazo ne dai wanda ya taimaketa kafin motar ta bigeta, harara ta banka masa ta ce "Kai Almajiri Sukajo meye ruwanka dani? Ina ruwanka idan moto ya takani, da kayanka duk a yage" ta faɗa tana murguɗa masa baki. A hankali ya nanata kalmar “Sukajo” a ransa idan ya fahimta Sukajo na nufin “Saurayi” Girgiza kai kawai yai ba tare da yace mata komai ba ya juya zai bar wajan. Da sauri ta sha gabansa tana faɗin "hani inbano ina ka kai mini kindirmon shaniyata? Waye ya tittila a tumbinsa?" Juyawa yai tare da kallon ƙwayar nonon babu komai a ciki sbd tuni ta zubar da nonon dalilin tsoran da taji, amma ta kasa fahimtar ita ta zubar ɗin. Yana dai tsaye bai ce komai ba can kuma ya kalli cikin idanunta da sauri ta ɗauke nata idanun tana murguɗa masa baki cikin ƙasa da murya ya ce "Siya akai ai" baki ta buɗe ita ai ba taga wanda yazo ya siya ɗin ba kuma gaba ɗaya nonon aka siya kenan? "Ina kuɗin to ɗan Almajiri mai yagaggun kaya?" Da hannu ya nuna mata ƙasan ƙwayar yana rufe idanu da buɗewa ya ce "Gasu can" ta durƙusa ta ɗaga ƙwayar sai ga kuɗi da gudar dubu ɗaya da ɗari biyar guda biyu sai ƴan ɗari guda goma. Zaro idanu tai waje jikinta na rawa ta ce "Kai ɗan Almajiri mai ƙarya wannan kuɗin duk na kindirmona ne? Ai aradu kuɗin yai yawa" hannunsa dake harɗe a ƙirji ya wara tare da ɗaga kafaɗa ya ce "haka suka bayar ai" "su waye?" Shiru yai mata yana ƙoƙarin juyawa ta ce "Mene wannan a ƙafarka?" Zaro idanu waje yai tare da yin baya ganin tana ƙoƙarin zuwa inda yake yasa yai saurin faɗin "ke fillo bayanki" juyawa tai da sauri amma babu kowa a wajan tsaki taja tana kakkaɓe zanin jikinta ta ce "Mai ƙarya dai ɗan wuta" ta ƙare zancan tana ɗago kanta babu Almajirin kamar yadda ta raɗa masa suna babu ko inuwarsa sai wani farin Zomo data gani kyakkyawa dashi ya ƙura mata idanu, itama kafesa tai da idanu kamar zata kamasa sai kuma ta ɗauki ƙwayarta ta nufi bakin hanya inda zata samu motar da zata kaita Njoɓoli. Da idanu Zomon ya bita har tayi nisa sosai yana kallon sanda ta samu abin hawa, girgiza yai yana kaɗa kunnuwansa sai gashi ya koma mutumin ɗazo wanda take ce masa Almajiri mai yagaggun kaya. Murmushi yai mai kyau a kuma fili ya furta "Danejona" Da gudu motar mai ƙirar Toyota Rav 4 ta Ƙarasa shiga cikin compound na Abti American University Yola (AUN). A hankali akai parking motar a tsakanin jerin motocin da suke cikin harabar. Buɗe murfin motar tai cikin faɗa faɗa ta ce "No! I mean I lost my eye sight for a while, my Mom slapped me and i was very shouked da marin, Sbd kawai wancan banzan ya kai ƙarata gida i hate him wallah ai babu dole cikin aure ko? I'm 29 years mene ya sa za ana damuna akan wani aure?" Yanayin yadda take maganar kaɗai zai sanya kasan ranta ya ɓaci har buga kan motar take sbd zafin zuciya tsaki tai ta ce "No am okay nazo ganin Zahrah ne, i will catch you later" kashe wayar tai baki ɗaya tana fitowa daga cikin motar tunawa da yadda Yarinyar ɗazo da yadda ta firgita ya sanya tai Murmushi tana nufar hanyar wani office. Office ɗin ba kowa sai some of things da suke saman table zama tai tana danna number Zahrah. Zahrah na tsaye cikin hall ɗin da take lecturing wayarta tai ringing ta san babu wanda zai kirata at this time sai Surayyerh da sauri ta kalli students ɗin dake hall tana faɗin "Ok guys Conservation biology has two central goals 1. to evaluate human impacts on biological diversity and 2. to develop practical approaches to prevent the extinction of species (Soulé 1986, Wilson 1992)" tana faɗin hakan tace "You get it?" Gaba ɗaya suka ce "Yes Maaa" jinjina kai tai tana taɓe baki idanunta akan wani matashi da sauri kuma ta juya hannunta riƙe da Ink pen ta nufi wajan bord da sauri ta shiga rubuta. “What is Bachelor of Science in Conservation Biology?" Dake tana ɗaukar su course ɗin Conservation Biology Under Faculty of Sciences ne. Shiru duk sukai suka kasa bata amsa hakan yasa Zahrah sakin tsaki a file ta ce "Is an assignment, ba zan wasting time ɗina wajan yi muku explanation ba, i have so much work to do bye" wani daga cikin students ɗin ne ya miƙe yana dariya tare da ƙwaiƙwayar yadda Zahrah ke tafiya ya tsaya gaban ɗaliban ya ce "I have so much work to do bye... Big Maaaa The arrogant one I hate this woman. But i like her style" gaba ɗaya Students ɗin suka saka dry ba kuma kowa ke ƙaunar Zahrah ba, wulaƙanci da disga mutane ya mata yawa, kuma idan ta shiga hall babu wanda ya isa ya shiga ga bada Assignment da shegen text da Attendance. Zahrah na fita ta nufi Office a nutse take tafiya cikin takun isa da gadara tana sanye cikin wata atamfa Amarya collection mai tsada ɗinkin riga da skert ya kama jikinta sosai, idanunta sanye cikin farin cat eyes wanda ya ɗan haska ɓakar fatar jikinta she's classes and educated ƴar wanka ce ga tsafta da tarin ilimi. Ƙafarta dake sanye cikin Derby shoes ta tura cikin office ɗin tana ya tsona fuska ta ajjiye handbag ɗin L.v akan kujera idanunta akan Surayyerh ta ce "Lafiya dai?" Surayyerh taja tsaki ta ce "ina lafiya? Can you imagine yau Mom ce ta mareni sbd wancan banzan?" Buɗe idanu Zahrah tai kamar ba zatai Mgn ba sai kuma tace "mene abin damuwa?" "Zahrah mari fa? Wallahi ba zan ƙara ɗauka ba idan aka sake marina, Look at me am 29 going to 30 ace Mom bata bar marina ba?" Girgiza kai kawai Zahrah tai ba tare da ta ce komai ba. "Ina magana Kinyi shiru, wannan miskilancin naki na tsana fa" "uban me kike son nace maki Surayyerh? Your mother has been slapped you sbd kinyi kuskure sai nace bata kyauta ba? Babu abin da zaki iya sbd Uwa ce dole ki hqr" Zahrah ta faɗa cikin ɓacin rai. "i can't bazan iya jurewa ba" cewar Surayyerh "ok zaki rama kenan? Are you going to beat your mother?" Surayyerh ta girgiza kai cikin damuwa ta ce "A'a kawai zan faɗa mata kada ta kuskura ta sake marina, Nasan Uwa tace kuma sai tai ta dokana akan wanne dalili, ɓacin rana nake gudu" Kallon Surayyerh kawai Zahrah keyi kafin taja numfashi ta ce "Ina cikin damuwa Surayyerh na fara tsorata fa" Surayyerh ta ce "Damuwa akan me?" Hannu Zahrah ta ɗora akan cikinta ta ce "Am pregnant Surayyerh ina da ciki wata uku, kuma na gaji da zubar da ciki wallahi" zare idanu Surayyerh tai tana faɗin "Pregnant? ciki na huɗu kenan fa Zahrah? Kina da hankali kuwa? Wannan karan dole ki yafe cikin kin manta mai Dr yace miki ko?" Ajjiyar zuciya Zahrah ta sauke kafin ta kalli Surayyerh da kyau ta ce "I'm not ready for this, kin san ba aure gareni ba, idan na bar cikin na haihu me zance a gida? Me zan faɗawa Mimi? daman Kullum cikin faɗan naƙi aure take wai na girma da yawa, karatun boko ya buɗe min idanu yanzu kusan shekaruna 31 ne Surayyerh" Surayyerh ta numfasa ta ce "Me kike jira? Ki kira Deen mana kuyi magana ya turo iyaye kuyi aure, Mimi nada gaskiya Kinyi primary, secondary, N.c.e, degree, kinyi masters to what are you waiting for wanda ya shige kiyi aure, haba ai ta boko ai ta boko nifa idan yanzu ne wlh ba zan wata boko ba, shekara 31 ana abu ɗaya sai zallar iskanci kawai da kike kina zubar da ciki a banza, sai kin gama zubar da ƙwayayen da Ubangiji ya baki matsayin zuri'a a banza wlh" Tsaki Zahrah tai "wani lokacin wlh ke Mahaukaciya ce, ni kike tunanin zan iya auren Deen yanzu? Inda a yanzu nasan rayuwa nai boko naje ƙasashe kala-kala da ace ko secondary schl ban rufa ba shi ne zan iya auren Deen amma yanzu kam i can't, zanje hospital a cire cikin, da kike maganar haihuwa waye ya faɗa miki daman ina son raya da haihuwa da yawa ne? Abeg ta shi muje Madam am not in the mood" Surayyerh ita dai mamakin Zahrah take bata, ta rasa ita da Zahrah waye yafi laifi, ita tana ganin mahaifiyarta na takura mata domin har kusan zaginta take a zuciya, ta hanata jin daɗin rayuwa komai sai ta ce wai taji tsoran Allah, ita kuma Zahrah iyayenta sun sake mata duk abin da zatai babu me cewa dan me gidansu gidan boko ne a waye suke gaba ɗaya, hakan yasa Zahrah keta aikata alfasha hankali kwance. "Kinzo da mota ne?" Surayyerh na miƙewa tsaye ta ce "E, kefa?" Zahrah ta ce "A'a, ba zan iya driving ba wannan cikin duk ya sauyani muje kiyi dropping nawa gida" "ok let's go" Fita sukai Zahrah da Surayyerh aminai ne duk faɗan da za suyi har abada babu mai ji, su gama fushi su shirya. Mota suka shiga Surayyerh na driving Zahrah na gefe a haka suka bar cikin Abti America. Da idanu Dada take bin kuɗin da Danejo take bata, a sanyaye ta ce "Duk wannan?" "E, Dadana ɗan Almajirin mai yagaggun kaya ne yace mini aradu duk kindirmo ake siya dasu, kuɗin da yawa" Dada ta jinjina kai ba tare da tace komai domin magana bai dameta ba, tun bayan rasuwar Baffansu Danejo ta zama shiru-shiru sanadin hakan ciwonta ya sake yin tsamari. "Dadana nawa ce wannan?" Danejo ta tambaya tana nunawa Dada gudar dubu ɗaya, girgiza kai Dada tai bayan ta tsurawa dubu ɗayar idanu ta ce "Ban san sunanta ba, ki bari Hamma Yabi ya zo sai ki tambayeshi ko?" Miƙewa Danejo tai ta ce "Bari naje wajan Shatu na tayata irga Naggenmu" fita tai a hanya taci karo da Hamma Yabi, da sauri Hamma Yabi ya kama hannun Danejo ya shiga duba Funa, Fobbina, Wayla, Hirna. Ma'ana Gabas, Kudu, Arewa, da Yamma, ganin ba kowa yasa Hamma Yabi faɗin "Mun shigesu Danejo, gobe ake bikin gasar wasa da maciji, wanda Sarkin ruga yake sawa, kuma yau za'a zaɓi wanda za'ai wasan dashi" fararen idanunta ta juya sosai cikin rashin damuwa ta ce "Hamma mene abin damuwa, ni Dadana kawai nakeso ta samu lafiya ina ta mafarki wani kala" girgiza kai Hamma Yabi yai kaifn ya kama Danejo sosai ya ce "Baka iya wasa da Mashiji ba Danejo, kuma Sarkin ruga zai iya zaɓarki matsayin wacce zatai wasan, idan baki iya ba Mashijin zai iya saranki ki mutu murus, ko baki mutu ba idan baki iya ba Sarkin ruga zai iya korar mutum daga cikin Rugar Rome" cike da tsoro Danejo ta zaro idanu waje ta ce "Mi boni Hamma Yabi yaya zanyi?" "Yanzu shai mu jira muga wa za'a zaɓa, kije ki ɗauki kindirmo mai man shanu ki bawa Dada gobe zamu koma ashibiti" kai ta ɗaga alamar to Hamma Yabi ya nufi cikin jejin nemo wani sassaƙen magani ita kuma ta nufi wajan garke a nan ta samu Shatu ta kama bakinta a nonon Nagge tana ta sha hankali ƙwance. Zama tai kan wani Leggal (Icce amma kututture) samun kanta tayi da tunani wanne kalar Mashiji za'ai wasan dashi? Meyasa idan taje Birni take ganin wasu mutanan ba irinsu ba komai nasu daban ne, meyesa birni ta banbanta da Rugar Rome?. Ajjiyar zuciya ta sauke tana murza yatsun hannunta da sauri takai dubanta zuwa ga ƙadamin yatsarta idanunta ya sauka akan zoben dake maƙale da yatsar da tsananin mamaki take kallon hannu yaushe wannan abun ya zo hannunta? Mene sunansa ita bata taɓa ganin abu mai kama da zobe ba sai yanzu, ga wani zane a tsakiyar zoben kamar tambarin abu amma bata san ko mene ba, ƙoƙarin zare zoben take amma ta kasa hakan yasa dole ta hqr. Suna zaune a garken suka ji ana shelar Sarkin ruga yana neman jama'ar Rugar Rome baki ɗaya. Da Shatu da Halisa suka kalli juna zuciyarsu cike da zullumi amma Danejo tai ta maza ta kama hannun Shatu suka nufi wajan. A tsaye suka samu mutane wasu na sanye da fararen kaya na Fulani wasu kuma Kuraye yawancin su gaba ɗaya farare ne, amma sam babu cikakken addini ga rashin tsafta. Sarkin ruga ya gyara tsaiwa yana faɗin "Kamar yadda kowa ya sani, a gobe ne zamu gabatar da gasar wasan Mashiji, za'a zaɓi mutum ɗaya ya buga wasa da ƙaton Mashiji kamar yadda muka saba, idan mutum ya kashe Mashiji akwai kyautar Nagge da kuma ƙwayar nono guda hamsin, idan Mashiji ya kashe mutum Shi kenan wasa ya zo ƙarhe, idan mutum bai mutu kuma za'a kuresa daga Rugar Rome baki ɗaya, don haka yanzu zamu fito da alƙalin wasa ya zo ya zamu wanda za'ai wasan da shi" Shatu ta ƙankame hannun Danejo ita ko kalmar Mashijin bata so taji an faɗa balle ta gansa a gabanta. Dajeno kam shiru tai kanta a ƙasa tunani fal ranta domin gaba ɗaya ma hankalinta baya wajan. Alƙalin wasa ya fara zagaye mutane har ya shige kan Danejo gama dubawa yai sannan ya gyara murya ya ce "Mun zaɓi Halisa Dajeno Rome a matsayin wacce zata fafata da ƙaton Mashijin mu a gobe.... #Sarautar marubuta #True life story*🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta *_Arewabooks@Nimcyluv_* 3. "Na shiga uku ta ya ya zan iya wasa da maciji? Wallahi kashe ni zai yi" Danejo ta faɗa a fili cike da tsora wanda ya sanya har ta kusan sakin fitsari gaba ɗaya ta firgita. Shatu ta ce "Ki faɗa masa ba zaki iya ba a zaɓi wata, idan Mashijin ya kashe ki na shiga uku na lalashe aradu" da sauri Danejo ta fito tsakiyar fili idanunta akan Alƙalin wasan muryarta na rawa ta ce "A yi mini afuwa Alƙalin wasan ba zan iya wasa da maciji ba aradu sarata zai yi" Alƙalin wasan ya kalli Danejo sosai, shi ya ɗan jima bai ganta ba, ta ƙara girma da wayo sosai ta zama ƴar budurwa irin girman ƙauyen nan dai. Sai rashin tsafta da addini dake ɗawainiyya da ita duk da ana ƙoƙarin ganin an magance hakan a cikin Rugar Rome. Murmushi alƙalin wasan ya sake yi cikin kulawa ya ce "Zaki iya mana? Ai Baffanki ya ƙware wajan iya sarrafa maciji, a wasan ƙarshe kuma macijin ya zama silar mutuwarsa, ki yi wasan ko dan ƙarasa cikawa Baffanki burinsa na zama gwarzo a Rugar Rome. Tabbas zaki iya Halisa Dajeno Rome" girgiza kai tai da sauri idanunta cike da hawaye ta ce "Ba zan iya wasa da maciji ba, mene ya sa sai ni? Baffana daban ni daban kalleni ƙarama ga maza nan da yawa a zaɓi wani daga ci" Sarkin rugar yai saurin faɗin "Ke aka zaɓa, kuma dole kiyi domin ba zamu taɓa sauya ra'ayinmu ba, ya zame miki wajibi muddin kina cikin Rugar Rome" a tsorace Shatu ta ce "Hande en boni, yau mun shiga uku" kasa cewa komai Danejo tai domin gani take kamar ma ta mutu ne lokaci kawai take jira. Da sauri ta juya idanunta cike da hawaye ta nufi cikin bukkarsu zuciyarta cike da zullumi da kuma fargabar abin da zai je ya dawo. A haka ta shiga cikin bukkar Idanunta akan Dada wacce take kwance cikin halin ciwo, domin a kullum ciwon nata ƙara tsanani yake. "Dada Alƙalin wasan ya zaɓi Danejo matsayin wacce zatai wasa da maciji a gobe" da sauri Dada tana jan numfashi ta kalli Danejo cikin damuwa ta ce "Mene ya sa baki cewa masa ba zaki iya ba?" Shatu tai saurin faɗin "Sarkin ruga ya ce wai dole tayi domin cika muradin Baffanmu" Dada ta miƙawa Danejo hannunta cikin kulawa ta ce "Waye yace muku Baffanku wasan maciji shi ne burinsa?" Danejo ta kasa magana sai ajjiyar zuciya take saukewa Shatu ce tai ƙarfin halin cewa "Sarkin ruga ne ya faɗa" Murmushin taƙaici Dada tai bata taɓa ganin zalunci irin haka ba, ta rasa me suka tsarewa Sarkin ruga da yake shirin ƙarar dasu ta hanyar kashesu da maciji wanda wasu suka tabbatar macijin tsafi ne. Cikin ƙonar zuci ta ce "Baffannku bai taɓa sha'awar yin wasa maciji ba, halima babu wannan al'adar ta wasa da maciji a Rugar Rome, daga baya Sarkin ruga ya samar da ita, bayan ya samar da ita ya zaɓi Baffanku matsayin wanda za'ai wasan dashi" shiru tai sbd tarin daya sarƙe mata numfashi, da sauri Shatu ta ɗauki ruwa ta bata, numfashi ta sauke kafin ta ce "Bisa dole Baffanku ya amince, yasha wahala kafin ya kashe macijn bayan ya samu raunuka wanda ya sa ya kwanta jinya, da shekara ta zagayo aka ƙara zaɓar Baffanku abin mamaki shi ne babu bambanci tsakanin macijin shekarar data shige da kuma wanda aka fito da shi, Baffanku ya tsorata, gashi idan ya ce ba zai ba to za'a kuresa daga Rugar Rome, tun daga wannan shekarar Baffanku ke gabatar da wasan Maciji, har zuwa shekarar da maciji ya kashe shi wanda kuma anyi hakan ne domin aga bayansa. a ruɗe Danejo ta ce "Kenan kashe Baffa akai Dada?" Dada ta girgiza kai ta ce "Ba zance ba, bani da hujja akan haka koma mene hukuncin na wajan Allah". Danejo taja numfashi cike da raunin murya na rashin sanin mafita zuciyarta cike da tarin zullumi ta kalli Dada ta Shatu ta ce "Dada ba zan iya ba, ina jin tsoro" "Halisa idan ba kiyi korarki za su yi daga cikin Rugar Rome, ni kuma ba zan jure hakan ba, Ubangiji na tare dake. Dole kiyi wasan imma ki mutu ko kiyi rai Kinji ko?" Kafin Danejo tai magana Hamma Yabi ya shigo da sauri idanunsa akan Danejo yana faɗin "Tashi mu tafi Danejo daman nasan bayanki suke son gani kamar yadda suka kashe Baffa" kallo Hamma Yabi Danejo tai idanunta ya kumbura sbd kuka ta ce "Hamma ina zamu?" Muryarsa na rawa ya ɗaga ta tsaye ya ce "Zanje na ɓoyeki sai an gama wasan zaki dawo, zan nuna ban san idan kike ba" Dada tai saurin cewa "A'a Yabi, kada ai haka kamar Halisa tare damu, idan ta tafi to Shatu ce zata maye gurbinta kasan haka ai" zama yai sosai ya ce "Yanzu haka zamu zauna? Ke baki da lafiya ita kuma muna kallo maciji ya kashe ta?" "Akwai Allah" Dada ta bashi amsa tana rufe idanunta. Halisa kasa bacci tai ga yunwa ga tsoro can cikin dare ta tuna ai ha tayi sallar issha ba, da sauri ta fito daga bukkar gaba ɗaya rugar shiru babu kowa sai wutar da aka kunnawa ko wanne garke dake ci hankali. Can bayan bukkarsu ta nufa tai tsari a wajan tai alwala babu ko shafar kai ta kwararan ruwan ta dawo. Sallar ma dungure tai Fatiha kawai ta iya cikakkiyar babu gyara. Yadda taga rana haka dare, dab da Asuba ta nufi garke tare da tatsar nono, tana gamawa ta Ajjiye. Gari na fara haske bayan tai sallah ta kaɗa shannun zuwa cikin jeji. Har zuwa lokacin bata da nutsuwa ita a yanzu ba wasan majin ya dameta ba, illar rashin lafiyar Dada idan har macijin ya kasheta waye zaici gaba da kula da Dada? Zama tai a gefen wani dutse ta shiga rusa kuka da iya ƙarfinta. Commissioners Quarter's Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi, wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan. A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce "Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba, wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa, naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai" Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok" cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna" marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce "Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah". Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa. Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne? Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya, wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce "Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi kan juna. 🫣Bala'i🚶🏽‍♀️kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu ƙari👌🏾. Muje zuwa #Sarautar marubuta #True life story*🌈 IDAN BA KE 🌈* Nimcyluv sarauta _*Arewabooks@Nimcyluv*_ 4. A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin. Sarkin ruga ya kalli tarin jama'ar da suke wajan hadda Shatu da Hamma Yabi, da sauran mutanan rugar kafin ya numfasa ya ce "Lokaci ya yi ake a kawo mana Halisa Dajeno Rome cikin fili, domin su fafata da maziji yau ranar tace" Wani mai suna Giɗaɗo ya rusuna tare da faɗin "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya kalli Hamma Yabi tare da faɗin "Maza jeka kawo ɗiyar taku, tana ɓata mana lokaci" Hamma Yabi ya ce "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi bukkarsu tun daga nesa ya hangeta kwance a bakin bukkar inda Prince ya kwantar da ita tana barci. Cikin sassarfa ya ƙara yana faɗin "Assha Subuhanallahi barci a ƙasa Danejo" ya faɗa yana ɗagota tare da jijjigata sosai, da sauri ya buɗe idanunta tana zabura "Hamma Yabi yaushe na dawo nan?" Kallonta yai ya ce "Kina nufin baki san lokacin da kika kwanta a nan ba?" Girgiza kai tai ta ce "Aradun Allah ban shina ba, kawai naji iska mai daɗi ta lulluɓeni wani barci yazo mini daga nan ban san komai ba" Girgiza kai yai yana kama Hannunta ya ce "Danejo ƙurushiya, maza muje sarkin ruga na jiranmu" dafe ƙirji tai cike da tsoro ta ce "Na shiga uku na lalashe, Kur'ani na manta yanzu hamma yabi shikenan mutuwa zan, zan mutu na bar Dada? Zan mutu banyi karatu na zama babbar mace ba? Don Allah kada na mutu yanzu bana son wasan nan" rirriƙeta Hamma Yabi yai sosai ya ce "Ma zaki mutu ba Danejo, sai na kai ki burni Kinyi karatu kin zama babbar mace abar ƙwatance, sai kin zama mace ta farko wacce zata kawo sauyi cikin Rugar Rome, ki daina kuka kinji" kai ta ɗaga masa kafin da sauri ta ce "Kuma zan zama wannan mutumin na jikin bango?" Zare idanu Yabi yai kafin ya ce "Wannan gwamna ne fa" murɗa baki tai cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai irinsa nake son zama" Yabi ya dungure mata kai ya ce "Aradu ƙarya kike, ina zaki iya yin siyasa tayaya zaki zama gwamna daman mata na zama gwamna ne?" Banza tai masa bai ƙara ce mata komai ba ya jata zuwa filin da za'a gabatar da wasan. Giɗaɗo dake tsaye shi da Sarkin ruga suna jiran zuwan Hamma Yabi da Danejo ya ce "Me ya sa ka zaɓi Danejo kasan ba zata iya wasan ba" murmushi Sarkin ruga yai kafin ya ce "Ina son ganin bayanta ne, kuma a hankali zan ƙarar da zuri'ar Manga a cikin Rugar nan, wannan macijin na tsafi ne hatta mutuwar Manga ni na shiryarta"... "Amma me Manga yai maka haka?" Cewar Giɗaɗo. Sarkin ruga ya ce "Sirri ne.." kaifin su ƙara magana Hamma Yabi ya ƙaraso hannunsa riƙe da Danejo wacce ta ƙanƙamesa sosai jikinta na rawa da ɓari. Alƙalin wasan ya ce "Yawwa yanzu zamu fara, Danejo ta shigo cikin fili jama'a ku buɗe idanunku da kyau yau za kuga wasa wanda baku taɓa ganin irinsa ba" Halisa Dajeno Rome na tsakiyar fili ko kuka ta kasa a wannan lokacin ta tsaya ne kawai tana jiran taga ta inda mutuwa zata zo mata, domin abune mai wahalar gaske ace yau ta rayu ko ta tsira da ranta. Sarkin ruga ya bada umarnin a fito da Macijin, da sauri Alƙalin wasan ya nufi bukkar da macijin yake. Yana kwance sharkaf yau lamo a ƙasa tare da yin gammo da jikinsa, wani irin zabura yai tare da fasa kansa a lokacin da alƙalin wasa ya shigo cikin bukkar, ƙuri yai masa da idanu yana ƙare masa kallo. Ko me ya tuna Ohhu a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar ya koma ya kwanta, shi kansa Alƙalin wasan ya tsorata jikinsa na rawa yasa hannu ya ɗauki Macijin da ƙyar sbd nauyin da yake da shi. Tun da Halisa Danejo Rome ta saka idanunta akan macijin taji gabanta ya faɗi, jikinta ya ɗauki rawa hawaye suka fara sintiri a saman Fuskarta, bata taɓa ganin maciji mai girman wannan ba, tama rasa wacce kalar addu'a zatai duk da ba wani abu ta iya sosai ba. Alƙalin wasan ya ajjiye macijin nesa da Halisa, aka fara kallon kallo tsakanin Danejo da Macijin, an shafe tsayin wasu daƙiƙo aka rasa waye zai fara kaiwa wani hari tsakanin Danejo da Maciji Prince?. Zaro idanu tai waje ganin ya fara warware tare da yin tsayi sululuuuu kuma ya nufo inda take, tana ja baya yana biyota har ya ƙaraso dab da ƙafarta tare da tsorawa zoben hannunta idanu. Juya tai tana neman inda zata gudu can idanunta ya sauka akan wani ƙaton dutse. Da sauri ta ɗauka tare da riƙewa a hannunta, ganin haka yasa Macijin bin ƙafafuwanta suuu haka ya dinga sufa a jikinta, har ya naɗeta ciff kansa daidai Fuskarta yana tsora mata idanu tare da kallon cikin idanunta. Jirkinta na ɓari ta ɗaga dutsen tare da kwaɗa masa a tsakiyar kansa, wani kalar ihun azaba macijin yai yana fasa kai kamar zai sarata, sai kuma ya saki kansa tare da ɗorasa saman ƙirjinsa gaba ɗaya naman Macijin rawar azaba yake, kansa tuni ya fashe ya fara zubar da jini. Ganin nasarar da Halisa Danejo Rome ta fara samu yasa Hamma Yabi da Shatu tare da sauran jama'ar Rugar Rome suka fasa ihun murna, Sarkin ruga da Alƙalin wasan hankali tashe suka kalli juna tare da faɗin "Me ya samu macijin nan? Ki dai asiri akaiwa Yarinyar nan?". Halisa a tsorace Macijin a tsorace amma a haka cikin dakiyar zuciya ta ƙara ɗaga dutsen a karo na biyu ta ƙara bugawa Maciji, Innalillahi a wannan lokaci kururuwar da Macijin yai sai da kowa na wajan yaji, jini ya sake ɓalle masa a hankali ya sulale ƙasa baya ko motsi alamar ya mutu... ajjiyar zuciya ta sauke haka kurum taji kuka ya ƙwace mata, durƙushewa tai a wajan ta shiga rera kuka tausayin macijin ya kamata musamman yadda taga jini na zuba a jikinsa, Hamma Yabi ya ƙaraso wajan Halisa Dajeno Rome tare da ɗagata yana dariya ya ce "Danejon Dada kin kashe macijin, kin kashe sa bana faɗa miki cewa ba zaki mutu ba? Zamu samu ƙwayar nono da Nagge masu yawa" ƙanƙame Hamma Yabi tai cikin kuka ta ce "Bana so Hamma Yabi, mu bar nan wajan kaina juyawa yake, bana son ganin jinin nan kaji" hannunta ya kama sukai gefe guda. Cike da taƙaici Sarkin ruga yake bin Macijin da kallo bai taɓa tunanin haka ce zata kasance ba, cike da baƙin ciki ya amshi wani sanda ya shiga kwarɗawa macijin aka tun macijin na motsi har ya daina jikinsa yai face face da jini tare da raunuka. "Ka ɗauke sa ku cillar a gefen gaɓar ruwa wani abin yai kalace dashi" Giɗaɗo da Alƙalin wasan suka ɗauki Macijin tare da nufar cikin jeji da shi. Suna zuwa suka cillar gefe guda da sauri suka juya cikin Rugar Rome. Sanyin gaɓar ruwan daya ratsa cikinsa ya sanya ya fara Girgiza yana juyi tare da murmurɗe jinsa gefe guda, wani kalar ihu yake mai nuni da azabar da yake ciki, ya daɗe cikin wannan halin kafin yai Girgiza tare da rikiɗewa ya dawo siffarsa yadda yake fitowa a mutum ba Aljani ba, yana kwance sambal gefen ruwan Farar Alkyabbar jikinsa duk ta ɓaci da jini. A hankali ya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa inda yake zubar da jini, runste idanun yai sosai cikin ƙasa da murya ya ce "Ya Allah" yana nan ƙwance yaji iska ta mamayesa baki ɗaya kafin kace wani abu iskar ta ɗaukesa zuwa sama. Duk farin cikin dasu Shatu suke ciki banda Danejo rasa abin da yake mata daɗi tai, gashi jinin Dada ya matsa ga tunanin dake wanzuwa a cikin zuciyarta. Dada ta kalli Shatu ta ce "Farin ciki za kiyi Halisa ba damuwa ba, da tuni an rabani dake Allah bai ba, akwai ƙaddarorin da suke biye dake, amma duk wahala duk tsanani waya rana zaki zama abar ƙwatance tabbas zaki samu miji wanda zai kula da maraicinki" Danejo ta ce "Dadana nifa ba marainiyya bace, ina dake ga Hamma Yabi ga kuma Shatu" jinjina kai Dada tai idanunta akan zoben hannunsa Halisa ta ce "Ina kika samu wannan Halisa?" Girgiza kai tai cikin damuwa ta ce "Ban sani ba Dada, kawai na gansa a hannuna"... "Bana son ƙarya fa" da sauri Halisa ta ce "Da gaske nake miki, kalli kiga" ta faɗa tana nuna mata tambarin zoben, Dada ji tayi kansa ya sara idanunta akan Zoben da sauri ta riƙe kanta tare da rufe idanunta, kamar mai son tuna wani abu babu abin da take gani a cikin idanunta sai tambarin masarauta dake manne cikin zoben. Ganin yadda Dada ta rirriƙeta kanta ya sa Hamma Yabi fita da gudu ta tatso mata kindirmo mai zafi, da taimakon Halisa Dajeno Rome suka bawa Dada kindirmon nan da nan zufa ga shiga saukar mata bacci ya ɗauke ta. Juyawa Halisa tai ta kalli Shatu dake barci a nutse ta kalli Hamma Yabi ta ce "Hamma yaushe Dada zata samu lafiya ne? Kullum a ƙwance take ina tsoran na rasa ta aradu" Hamma Yabi ya kama hannun Danejo ya ce "Ba zaki rasa Dada ba, gobe zan koma asiti bamu da kuɗin kai ta asibitin burni" Da sauri Danejon ta ce "A siyar da Nagge to" zare ido Hamma Yabi yai ya ce "Aradu ƙarya ne, Uban waye zai taɓa Nagge ai mu dasu mutu karaba" ba tace masa komai ta miƙe tsaye tare da yin waje lokacin rana ta faɗi, can gefe ta nema ta zauna ita ɗaya sai tunani take a haka har akai magariba tana zaune, ganin duhu ya fara yasa ta miƙe tare da zagayawa bayan bukka ta kwaɓe kayan jikinta, halittar jikinta ta tsorawa idanu, musamman ƙirjinta tana mamakin abun mene amfaninsu a jikinta? Ita a gareta basu da wani abu kullum sai dai su ƙara girma. Ruwa ta sheƙa babu ko sabulu tana gamawa tai alwala, wasu kayan fulanin ta ɗauka farare ta saka tare da Ajjiye waɗan can, da sauri tai sallah tana gamawa taci tsiran da Hamma Yabi ya kawo musu, tana ci ta kwanta barci domin da wuri take son zuwa kiwo ta dawo ta tafi tallan kindirmo. Ciki zafin nama Prince ya saka hannu tare da ɗauke Safwan da mari ya ce "Ka fita a sabgata, kaje ka faɗawa Sarki halin da nake ciki ya ɗaukeni, kuma kasan yana gab da rabani da matata wanda ba zan iya jure hakan ba sam" Safwan ya kalli Prince cike da mamaki ya ce "Ban taɓa ganin mai taurin kai a duniyar Aljanu irinka ba Prince, cutar da yarinyar nan kake fa, babu haɗi tsakanin mutum da Aljani na faɗa maka, abin kunyane ka rasa wacce zaka so sai Bil adam? Allah zai saka mata fa" banza Prince yai da Safwan a wannan lokacin rabinsa na mutum rabi kuma na siffar Aljani da sauri ya juya zai tashi sama Safwan ya ce "Ina zaka? Ba dai wajanta ba?" Prince ya ce "Ba zan iya yin wasu daƙiƙo ba, ba tare da naga matata ba, da matata nake son kwana a yau ɗin nan" yana faɗin haka ya ɓace ɓat kai tsaye Rugar Rome ya nufa. Halisa juya cikin barci taji wani sanyi na ratsa mata jiki, ga wani mafarki da ke ƙafafuwanta sai motsawa suke amma ta kasa koda motsi bada ji take kamar ana danneta. Can dai ta farka a firgice Innalillahi a ruɗe ta fara kallon inda take, tana kwance tsakiyar dokar daji ba gida gaba ba gida baya... Waye ya kawo Halisa Dajeno Rome cikin dokar daji?... #Sarautar marubuta #true life story*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* https://wa.me/+2348119237616 5.. A zabure ta miƙe tsaye tana ƙarewa cikin dokar dajin kallo, babu abin da ya bata mamaki irin yadda taga an sauya mata kayan jikinta, daga na Fulani zuwa na wasu saƙi farare masu kyan gaske. Jikinta na rawa sbd tsoro da tarin fargabar dake ratsa dukkan wasu lunguna na ƙofofin zuciyarta ta shiga ƙarewa jikinta kallo. Idan hankalinta yai dubu to ya tashi ta ƙara razana da halin da take ciki a yanzu, domin ba iya kayan jikinta da aka sauya mata ne kaɗai ya bata mamaki ba, zanan jan lallen data gani kwance a hannunta shi ne ya ƙara ta hanyar mata da hankali, ga sumar kanta da akai mata wasu irin kalba manyan gwanin sha'awa ita bata taɓa ganin kanta yai irin wannan kyan ba sai yau. Waye ya kawota nan Meke shirin faruwa da rayuwarta ne, ina Dadarta?. Ƙare wa cikin dajin tai babu ko hanyar da zata bi ta nufi Rugarsu, daɗin daɗawa ita kanta bata san a inda take ba, wacce kalar rayuwa ce haka? Daga yin barci kuma sai mutum ya farka ya gansa a tsakiyar daji? Bayan tasan a bukkar Dada tai barci. Tafiya ta shagayi idan ta kalli gabas da Arewa, guda da yamma sai ta saki kuka tare da faɗin "Na lalashe jama'a ina nake ina rugar rume tayi, ina Dadata, ina Shatu, ina Hamma Yabi duk kuna ina wayyooo Hande en boni, Yettore jaumirawo" ta faɗa ɗora hannunta aka tare da sakin kuka, ta fiya kawai cikin dokar dajin tun tana kuka har tai shiru sai idanunta da take rarraba wa a ciki dajin. Kukan da tayi da kuma gudun data jima tana yi sune suka taru suka haifar mata da wata gajiya wacce ta sanya ko idanunta bata iya buɗewa sosai sbd yadda kanta ke juyawa da kuma yunwar data keji, lokaci zuwa lokaci tana buɗe idanunta tare da zubawa zanan lallen hannunta idanu, tana cikin wannan hali ta ƙaraso wani waje wanda yake da rana sosai hakan yasa Danejo ta wahala fiye da zaton mutum, ga ƙishin da take ji. Daurewa tai taci gaba da tafiya sai dai duk yadda takai da daurewa ta kasa bata san lokacin da jiri ya kwashe ta ba, tai baya luuu zata kifa da sauri aka tareta ana faɗin "Subuhanallahi" mutumin ya faɗa a taushashe yana mai riƙe Danejo wacce ta faɗo jikinsa babu numfashi alamar ta soma kenan. Kyakkyawan idanunta mai ɗauke da kuriyar ƙwayar ido su ya ware akan Danejo yana mai ƙara jin nutsuwa na saukar masa a jikinsa, a hankali a kuma dukkan wata ƙaunarta ta shiga nunkuwa a zuciyar Prince Bilal. Yanzu ne zai samu cikakken lokacin kasancewa da ita, irin kasancewar nan ta har abada domin baya jin akwai mutumin daya isa ya raba shi da Matar Danejo a cikin wannan Dajin, zai zauna da ita zai rayuwa da ita, tai ta haifa masa yara, ya kuma yi alƙawarin ba zata taɓa sanin shi aljani bane, zaici gaba da zuwar mata a suffar Balarabe kamar dai suffar wani Sheikh ɗin Malami. Ɗaukarta ya yi a hannunsa zuwa gaɓar wani ruwa, jallabiyar jikinsa ta sauka har ƙasa tare da rufe masa ƙofatonsa, a haka ya Ƙarasa tare da kwantar da ita a gefen ruwan wajan da yake da ɗan danshi danshi musamman daya lura da jigatar da tai duk da cewa duk wani abu da take akan idanunsa ne. Yana kwantar da ita ya zauna gefenta idanunsa na juyawa tare da sauya launi zuwa wata kalar, hankalinsa ya karkata gaba ɗaya zuwa cikinta idan yake hango ɗansa dake maƙale a mararta hakan sai cike da farin ciki Prince ya saki Murmushi bakin na rawa ya ce. "Ubangiji ya saka mini sonkiwa zuciyata, tun kina cikin mahaifiyarki, zanci gaba da sonki ba zanyi saken da za a rabani dake ba, kamar yadda aka rabani da mahaifiyarki tun tana asalin inda take rayuwa" shafa cikin nata yai idanunsa na tsiyyayar da wani ruwa ya ce "Babu alaƙa tsakanin mutane da Aljanu, amma naji a wannan karan dama Ubangiji a suffar mutane ya halittoni, mene yasa bakwa iya ganinmu a suffarmu ta zahiri sai dai mu muganku? Ina son ki matata Danejo,ina gab da ɗaukeki zuwa duniyarmu" dariya ya saka gaba ɗaya wajan ya ɗauki rawa da Girgiza can kuma ya ɓace da wajan. Acan Rugar Rome kowa gari na wayewa suka saba Danejo na tashi zuwa garken Nagge ƙara tatsar nono, hakan yasa Dada bata damu ba sbd ganin Danejon bata cikin bukkar sai Shatu dake kwance a gefe tana barci, Hamma Yabi ya fita tun sassafe zuwa asibitin dake gefen Rugar Rome domin samawa Dada layi. Yana tsaye a a ɗan wajan da mutane suke tsayawa gaba ɗaya mutanan ba sufi mutum goma ba, suna zuwa kamar mutum biyar zai koma ya ɗakko Dada. Wani Likita ne hannunsu riƙe da waya yana dubawa ya raɓa ta gefen Hamma Yabi ya shiga office, Fuskarsa ɗauke da fara'a ya kalli mutumin dake cikin office ɗin ya ce "Dr Hamza na ganka a zaune ina patients ɗin?" Dr Hamza ya dubi Dr Iliya yana ƙara ware idanunsa ya ce "Patients suna can waje, bani da time na duba su serious,idan zaka shekara kana duban jama'ar Rugar nan ba zaka taɓa samunsu da cikakkiyar lafiya ba, ƙazanta ita take ƙara lalata musu lafiyar jikinsu na gaji wallahi, sai Shegen son shanunsu amma basu san yadda zasu kula da lafiyar jikinsu ba" Dr Iliya yaja kujera tare da zama sosai yana faɗin "Ai Dr Hamza sai haƙuri, kasan cikin karkara musamman ruga haka ba komai suka sani ba, kai dai barsu da arziƙinsu wato Nagge su kawai suka sani" Dr Hamza ya ce "Let's leave this matter, it is not in front of me" ya faɗa yana duba wani file, "I got the message you want to see me up, lafiya dai kake mini kiran gaggawa haka?" Dr Iliya ya tambayi Dr Hamza cike da jin don abin dake faruwa. Gyara zama Dr Hamza ya yi kafin ya ce "The government has given free medicine to the people of Ruga, maganin da gwamnati ta bayar suna da yawa, akwai maganin Suger, Hawan jini, Maleriya, da sauran maganin cuccutikan, yawwa sai maganin sikila irin folic acid, Paludrine, Peniciillin V,Hydroxyurea. Anfi kawo maganin Sickler sbd yawaitar samunta da ake cikin karkara, shiyasa nace a kiraka" cikin jin Daɗi Dr Iliya ya ce "Masha Allah yanzu yaya za'ai kenan?" Wani kallo Dr ya Hamza yaiwa Dr Iliya kafin ya ce "Ya kowa za'ai? Kasan Rugar nan ko an basu magani a banza, basu san important ɗinsa ba, so that zamu kwashi 88% a cikin 100 mu siyar mu raba kuɗin, kai ba kana da chamist ba? Sai ka zuba kawai acikin chamist ɗin naka" cike da gamsuwa Dr Iliya ya ce "that's good, amma gwamnati ƙoƙari sosai fa, banda haka wannan maganin sunfi ƙarfin miliyan 3 da wani abu fa,ana kula yanzu da ɓangaren lafiya sosai da masu juna biyu, anywhere zuwa dare zan zo da mota na ɗauki rabona" Sallama sukai tare da fitowa a tare ganin hakan yasa Hamma Yabi saurin kallon Dr Hamza ya ce "Aradun Allah na shafe awanni a nan gashi muna ta jira" a faɗace Dr Hamza ya ce "Wai kai fillon nan wani irin banza ne bagidaje ne kai? You doesn't know anything akan asibiti ka addabi mutane da wautarku ta Fulani, mu bamu da wasu kayan aiki cikin Asibitin nan kana kallo da idanunka ai, dan haka kada ka sake zuwa idan an kawo kayan aiki zamu sanar get out" jiki babu ƙwari Hamma Yabi ya koma cikin Rugar Rome, yana zuwa ya sake tarar da wani tashin hankalin babu Danejo gaba ɗaya acikin Rugar, sanadin hakan yasa jikin Dada ƙara rikicewa abu kamar wasa duk inda suke tunanin ganin Danejo babu ita sam har kusan kwana biyu. Tunda ya kwantar da ita a gaɓar ruwan har gari ya waye ta kwana a wajan, wani daren ya yi ta sake kwana, kwana biyu kenan amma bata motsa ba. Bata kuma da ranar tashi sai lokacin da Ubangiji ya nufa ko kuma ya tsara. A can cikin barci ta fara mafarki gata da namiji suna kasancewa waje guda, wani abu mai kama dana auratayya na gilmawa a tsakaninsu. Numfashi ta sauke tana motsa ƙafafuwanta zuwa cinyoyinta da suke mata zafi, tana jin kamar an daddaneta a firgice ta farka tana kurma ihu tare da kiran sunan Dada, ba addu'a babu komai. Cikin tsoro ta fara bin jikinta da kallo babu komai lafiyarta ƙalau domin ba wani sauyi da taji. Ajjiyar zuciya ta sauke a bayyane tare da kifa kanta a tsakanin cinyoyinta ta shiga rera kuka, kenan haka rayuwarta zata ƙare cikin dokar dajin ko yaya ne? ya akai ta tsinci kanta a dajin gaba ɗaya ta rasa amsar tambayoyin zuciyarta. A hankali ta fara jin dariya na karaɗe wajan, tare da surutu ƙasa ƙasa. Miƙewa ta yi da sauri ta shiga duba inda take jiyo sautin dryar a haka ta ƙaraso jikin wata ƙatuwar bishiya, cike da tsoro da kuma tarin zullumi ta ɗaga kansa zuwa saman bishiyar idanunta ya sauka akan wani ganyen bishiya dake lilo shi ɗaya, sai ka ɗauka iska ke kaɗa shi amma abin mamaki shi kaɗai ne yake lilo daga cikin sauran ganyen bishiyar. Prince Bill wanda a yanzu ya rikiɗe zuwa suffarsa ta asalin aljani yana kwance saman ganyen yana karkaɗa ƙafarsa wacce ita ce take sanya ganyen bishiyar motsawa, Danejo dai kallon ganyen take cike da mamaki tana tsaye taci mangoro ya faɗo kanta abinka da mai jin yunwa da sauri ta ɗauki mangoron babu Bisimillah ta shiga sha idanunta na lumshewa sbd daɗi. Daga bayanta taci ance. "Kisha a hankali da wasu da yawa idan kina buƙata" juyawa tai da sauri baki buɗe take kallon mai maganar, iya tsoro da razani ta shiga domin bata taɓa ganin halitta irin wannan ba, mangoron ta saka tare fasa wani Ihu ta ɗaga ƙafa zata gudu yai saurin riƙe hannunta. Share🥰🥰🥰*🌈IDAN BA KE 🌈* 6.... *_Arewabooks@Nimcyluv_* "Na shiga uku Aljani Balarabe" Danejo ta faɗa a ruɗe tana ƙoƙarin kwace Hannunta daya riƙe cikin nasa. A nutse Prince ya ware idanunsa sosai a kanta yana Mmkin Yadda duk ta ruɗe kamar taga mugun abu. "Me ya baki tsoro" murguɗa masa baki tai tana suɗe hannunta dake ɗauke da ruwan mangoron ba tare data ce komai ba. Prince ya saki tattausan murmushi mai kyau da tsari yana binta da kallo musamman idan ya tuna abubuwa da suke faruwa a tsakaninsu, sai yaji nutsuwa ta kamasa. Hannunsu ta make ta ce "Sakeni haka kurum kai mini ciki, bayan Dada ta ce ba kyau namiji ya taɓa mace" ta ƙare Maganar tana binsa da kallo, sai a lokacin da a shiga ƙarewa tsarin hallitar jikinsa da kallo, fari ne tas kamar ka taɓa shi jine ya fito, yana da faɗin ƙirji fuskarsa mai cike da ilhama, ga wani gudun saje wanda ya kewaye fuskarsa zuwa ƙasa wajan gemunsa, fuskarsa mai faɗi ce babu wani abu da zai bamban tasa da jinsin larabawa. Prince ya saketa yana mai faɗin "Ciki na nawa kuma?" Zuciyarta na bugawa sosai ta ce "Me kace?" Ya girgiza mata kai yana ware hannun shi ya ce "Babu komai Danejo" zare ido tai tana dafe ƙirji sosai a tsorace ta ce "Kasan sunana? don Allah kasan rugarmu wallahi ɓata nayi ka taimaka kaji ɗan Balarabe" idanunsa ya ɗaga sama tare da daidaita juyawar launin idanunsa ganin yana neman rikiɗe masa, jikinta duk rawa yake tai saurin cakumarsa tare da rirriƙesa wanda yai sanadiyar fitowar wata jela a bayansa, sbd ko yaya ya samu kusanci da ita, baya iya zama a zallar mutum, dole sai wani sashi na jikinsa ya juye zuwa na aljani. "Ukkkkk heee" ya faɗa cikin kumburarriyar wacce ta amsa kuuwa cikin kunan Danejo. Gaba ɗaya rikicewa tai ganin yadda take neman maƙalesa baki ɗaya saboda tsoro da fargaba har take shirin bayyanar da kofatonsa yasa yai saurin riƙo Fuskarta tare da hura mata iska a fuska. Ƙuri tai masa da idanu a rarrabe ta shiga faɗin "Ka kaini wajan Dadata kaji, bana son zama a nan tsoro na keji Da...da...ta.." ta kasa ƙarasa maganar sbd idanunta da suka ruf wani barci mai nauyi ya ɗauketa. Fuskarta yabi da ido yana hango lokacin da yake tare da mahaifiyarta, duk yadda ya nunawa Dada so da ƙauna amma haka wani mugun babban Malami ya raba shi da ita, ba shi da niyyar cutar da Dada kawai ƙauna ce tasa yake tare da ita, yai ihun tare da magiya amma haka Malamin ya fatatakesa daga cikin Dada bayan ya ƙona shi. Wannan dalilin ya sa yai jinya sosai har bai san inda Dada tai ba sai kwatsam ya ganta lokacin tana ɗauke da cikin Danejo, tun daga wannan lokacin ya ɗauki son duniya ya ɗora akan Danejo, ya manta da batun Dada ɗan tayin dake cikinta kawai yake muradin yaga ya zo duniya. Sauke numfashi yai yana binta da idanunsa daya gama rikiɗewa har wani hayaƙi yake fiddawa, hannunta ya riƙo ya kama yatsan dake ɗauke da zoben daya saka mata ya jima yana kallonta kafin ya saketa zuwa ƙasa ya kwantar. Tsakiyar dajin ya koma yana Girgiza da surutai cikin ƙaramin lokacin ya koma asalin suffarsa ta aljani yana wani ihu da gurnani kafin kace wani abu ya gama haukata dajin can kuma ya ɓace ɓat. Yamma Yabi ne da Shatu tare da Sarkin ruga da kuma Giɗaɗo kwance a gaban Dada wacce take cikin halin rayuwa ko mutuwa, bata san inda kanta yake ba, sunan Halisa Dajeno Rome ne kawai a bakinta. Giɗaɗo ya ce "A jiƙa wannan maganin a bata" da sauri Hamma Yabi ya amsa tare da jiƙawa da taimakon Shatu ya ɗaga Dada suka ɗora mata maganin, wani shaƙuwa tai jikinta ya shiga jijjiga can kuma ta kwanta shakaf barci ya ɗauketa. "Na shiga uku na lalashe Hamma Dada ta mutu wayyo yanzu yaya za mu yi Dada ki tashi" idanun Hamma Yabi na taruwa da ruwan hawaye ya kama Shatu tare da riƙeta ya ce "Assha Assha Shatu Dada nada rai, daina kuka yaro barci Dada tai" kuka kawai Shatu take, duk da ƙarancin shekarunta amma ta fahimci cewa Dada ita ce cikon farin cikin su, tare da jin daɗinsu. Sarkin ruga ya sauke ajjiyar zuciya ya ce "Allah shi bata lafiya, Aradu tana gab da mutuwa" jin kalmar Sarkin ruga yasa Shatu ƙara sakin kuka tana jijjiga Dada tare da faɗin ta tashi kada ta mutu ta barsu cikin ƙuncin rayuwa. Cike da takaicin kalamar Sarkin ruga Hamma Yabi ya bisa da kallo yana addu'ar Ubangiji shi ya ɗauki rayuwarsa yabar Dada a duniya ko dan farin cikin Shatu da Halisa. "Ba a samu labarin Danejo ba har yanzu?" Girgiza kai Hamma Yabi yai yace "Aradu ta ɓace babu ita kaf cikin ruga da kuma daji" cikin tausayawa Giɗaɗo ya ce "Wayyo Allah shi baiyyanata" "Kawai iskanci ta tafi, amma ina ne Danejo bata sani ba cikin ruga da dajin ba har kiwo take zuwa ba?" Da sauri Hamma Yabi ya ce "Danejo ba zatai iskanci ba, domin bata san shi ba" fita duk sukai daga cikin bukkar. Hamma Yabi ya dubi Shatu da barci ya ɗauketa a jikinsa a hankali ya kwantar da ita, tare da fita daga cikin bukkar. Yana fita ya shiga irga Nagge wanda ya zama al'adarsa kullum tunaninsa za a iya sace musu Nagge shi ya sa a rana sai ya irgasu sau biyar. Kai tsaye asibiti ya nufa lokacin ana zubawa Dr Iliya magani a cikin mota. Saukar ruwan ruwan sama ne ya haddasa farkawar ta daga barci, da sauri ta miƙe tsaye jirkinta na rawar ɗari sbd gaba ruwan ya gama yi mata doka, ganin bata da wata mafita ya sa ta fara ƙoƙarin ɗaga ƙafarta Innalillahi sai a lokacin ta lura ashe a kan wani ƙaton dutse mai tsayin gaske take, ita kanta bata iya hango ƙasan dutsen, a hankali ta koma tare da zama saman dutsen "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wacce kalar rayuwa ce take ciki haka? kenan akan dutsen ta kwana? ina ne nan kuma kwananta nawa? ta haukace ne ko mene? Anya ita ce ba wata Danejon bace daman?" Wani raunataccen kuka ta saka kuka take da dukkan ƙarfinta kenan ita da Rugarsu har abada ina za taga Dadarta? Kuka take sosai na rashin mafita ga rayuwarta ga ruwan sama na dukanta, yunwa take ji sosai, hannunta ta tara ruwa ya shiga sauka a hannun cikin sauri ta shiga shan ruwa sai daya isheta sosai sannan ta koma ta kwanta barci ya ƙara ɗauketa saman dutsen. "Ke! Ke! Baiwar Allah" aka shiga kiran sunanta wanda yasa ta buɗe idanunta da sauri tare da fatan Allah ya sanya a cikin Rugar Rome take, wasu fatake ta gani su wajan biyar tsaye a kanta ko wanne hannunsa riƙe da abu. Sai a lokacin ta lura ashe a kwance take saman wani ya shi saɓanin ɗazo da take kan dutse. Idanunta take rattabawa tare da binsu da ido ganin ba wanda ta sani yasa ta mayar da kanta ƙasa "Baiwar Allah wace ke daga ina kike? Kin san ina ne nan a Maiduguri kike fa?" Da sauri ta kalli mai maganar sai bata ce komai ba. Wani daga ciki ya ce "Ko bata magana ne? Kamar bafulatana" "Akwai abin da ke damunta Allah kaɗai ya sani" cewar wani, yin duniya sukai tai magana ko ta faɗi garin da take amma tai shiru kamar an kulle mata baki dole suka barta bayan sun yi mata fatan alkairi. "Danejo" aka kira sunan a taushashe sautin Muryarsa da taji yasa tai saurin Miƙewa yana tsaye kamar kullum sanye da fararen kaya ga tarin nutsuwa da ilhama a tattare da shi. da sauri ta nufesa kamar zata riƙesa sai kuma ya tsaya dab dashi tana sakin kuka tare da faɗin "Ɗan Balarabe ka kaiki gida kaji, tsoro na keji ina son nasan halin da Dadata ke ciki" Prince ya sake mata murmushi yana faɗin "Waya kawoki nan?" Hannu ta watsa alamar bata sani ba da sauri ta ce "Amma ka sanni ko? naji ka iya kiran sunana do Allah ka kaini wajan Dadata" yana kama hannunta ya ce "Ban san inda kike ba, Danejo kuma sunan matata ne ina iya kiran sunan kowa da ita" da fararen idanunta ta kallesa ba tace komai ba, sai hawayen dake suntiri a cikin idanun nata. Hannunta ya riƙe yana janta da Shira tun tana kuka harta daina, tana zaune taga ya kawo mata naman kaji da yawa da kuma kayan marmari ƙin cin komai tai sai da ya fara mata wasa yana bata labarin abin dry sannan ta saki jiki taci kayan marmarin. "Zan kaiki gida" da sauri ta ce "Da gaske kake Balarabe?" Kai ya ɗaga mata yana faɗin "E, Matata" turo baki tai ta ce "Ni ba matarka ce ba" ya ce "Daman ba dake nake ba" kamar ba zatai Magana ba sai ta ce "Yaushe zaka kaini wajan Dada" yana riƙo hannunta ya ce "Ko yaushe, amma kiyi mini Al'ƙawarin na dinga zuwa ina koya miki karatu, kuma kiyi al'ƙawarin zamu zama ƙawaye a duk sanda na buƙace ki, kizo gareni ba zan cutar dake ba na rantse da Ubangiji al'arshi, ba zan bari kuma kowa ya cutar dake ba" tunda ya fara magana take kallonsa cikin rashin sani ya ce "Kuma Dadata zata samu lafiya?" Shiru yai mata an riga anyi masa iyaka da mahaifiyarta, babu abin da zai iya a gareta, sai dai ya sanya Safwan yai wani abu akai. "Uhm ni kayi magana mana" ta faɗa tana jijjiga hannunsa kai ya ɗaga mata ya ce "E, kina zuwa ya kiga ta samu lafiya" Murmushi tai Wanda ya bayyanar da kyanta a hankali ya dinga ɗauke mata tunani harta manta da batun gida sulalewa tai ta kwanta saman ƙafarsa barci ya ɗauketa. ISLAMIC UNIVERSITY OF MADINA. _Jami'ar Musulunci ta Madinah_ masarautar Saudi Arabiya ta kafa jami'ar bisa umarnin sarauta a shekarar 1961 a tsattsarkan birnin Musulunci na Madina. Koda yake wasu sun danganta akidar Salafiyya da bude jami'ar, ana ganinta a matsayin rashin fahimta sakamakon halayyar da cibiyar ta ke da ita ga kowane akida. Jami'ar ta sami takardar shaidar digiri na jami'a ba tare da banbanta ta ba daga Hukumar Kula da Ilimin Kimiya da Nazari a watan Afrilun 2017. Jami'a ce mai tsarin gaske musamman Ɓangaren Addini. Ga nagartattun Malamai, da yawan ɗaliban na son karatu a jami'o'in Saudi Arabia sbd dalilai masu yawa. Manyan jami'o'in Saudi Arabia an basu shaidar yabo a bangaren ilimin kimiyya. Wasu daga cikin jami'o'in Saudi Arabia suna cikin manyan jami'o'i a duniya dangane da cibiyoyin bincike. Jami'o'in Saudiyya suna ba da kyakkyawan yanayin binciken ilimin, ta hanyar ingantattun cibiyoyin bincike. Yankunan ilimi da al'adu iri daban daban a jami'oin Saudiyya. Akwai daliban duniya daga sama da kasashe 165 da ke karatu yanzu haka a jami’o’in Saudiyya. Baya ga manyan masana ilimi da ma’aikata da ke aiki a waɗannan jami’o’in. Jami'o'in Saudiyya suna ba da cikakkiyar kulawa mai kyau ga ɗalibanta da kuma malamanta. ire-iren wannan manyan dalilai yasa akeso da burin karatu a jami'o'in Saudi Arabia. Da sauri ya fito daga ɓangaren hall ɗin da aka ɗauki darasin Islamic Studies and History. Kansa a ƙasa ya tatatare hannayensa cikin milk ɗin Arabian jallabiya daya saka sai wani ƙaramin baƙin hirami da yai rawani dashi, ɗaya hiramin kuma ya ɗora saman kafaɗarsa. Wasu matasa ne manyan suke take masa baya hadda wasu securities. Yanayin yadda yake tafiyar kaɗai zai tabbatar maka babu sassauci a zuciyarsa, idanunsa yai jajur bai taɓa shiga ta shin hankali na yau ba, yana zuwa bakin wata farar mota jikin Umar-khan na rawa ya buɗe masa murfin bayan motar ya shiga, Malamin na shiga mota, Umar-khan ya shiga gaban motar bayan driver ya shiga. Da sauri Driver yai wa motar key ganin haka yasa Saif-Wazir ya shiga wata motar kai tsaye daga cikin University ɗin Prince muhammad bin abdul'aziz international airport suka nufa. Ta cikin madubin motar Umar-khan yabi Sheikh Aliyu Haydar wanda ke bayan motar da kallo, ya jingina da jikin Kujera sai huci yake fitarwa, ya rirriƙe Jallabiyar jikinsa da hannu bibbiyu, gumi na tsastsafo masa ta tsakiyar goshinsa sbd yadda zuciyarsa ke masa zafi da ta fasa. Girgiza kai Umar-khan yai cike da tausayin yanayin yadda Sheikh Aliyu Haydar ke gabatar da rayuwarsa. Juyawa yai yaci gaba da kallon yadda driver ke sharara gudu, har suka ƙaraso filin tashi da saukar jirgin, The plane is ready to take off. Tun daga bakin wajan securities ɗin suka firfito tare da mamaye motar Sheikh, Umar-khan ya buɗe murfin motar ciki. Sauri Sheikh Aliyu Haydar ya fito a wannan lokacin ma kansa a ƙasa, yana hawa strains ɗin jirgin Saif-Wazir na biye dashi, sai Umar-khan wanda ya ɗan tsaya yana amsa kiran Father. Cikin damuwa Umar-khan ya ce "Kayi haƙuri Father, Sheikh ba zai taɓa aikata hakan ba, zargi ne kawai ake masa, yanzu jirginmu zai tashi be patient Father" tsaki Father yai ta cikin wayar kafin ya kashe. Yana shiga jirgin aka bawa Pilot daman keta hazo, a hankali jirgin ke zagayawa a ƙasan kwalta ya jima a haka kafin ya kete zuwa sararin samaniya. Jeniyar motocine suka tabbatar da Father Sheikh Aliyu Haydar ya ƙaraso gida Nigeria, da sauri ya miƙe daga zaunan da yake yana zaga haɗaɗɗan parlon gidan, tare da jiran shigowar Sheikh ɗin. Da mamaki Umar-khan ke bin ƴan jaridu da kallo, daga na gidan Redio, T.v, media. Abin har yai tsamari haka yana da tabbaci Sheikh ba zai taɓa aikata abin da ake tuhumarsa ba, zargi ne kawai. A nutse ya sakko da ƙafarsa daga cikin motar kai tsaye ƙofar shiga cikin gidan nasu ya nufa, Umarninka da Saif-Wazir na karesa daga ɗaukan da ƴan Jaridu suke masa. Sako ƙafar da Sheikh Aliyu Haydar yai cikin parlon yai daidai da lokacin da Father yake sauke masa wani lafiyayyan mari wanda yasa Umar-khan saurin juyawa ya fita, domin ba zai iya jure ganin ana cin zarafin babban mutum akan idanunsa ba kamar Sheikh Aliyu Haydar, Saif-Wazir Hawayen da yake maƙalewa ne suka sakko masa, da sauri ya karawaw Umar-khan baya. Cikin faɗa da tsawa Father ya ce "Ka kyauta Aliyu Haydar, ashe wannan dalilin ya hanaka auren tsayin shekaru talatin da huɗu? Ka yaudareni kaci amanar Musulmai kana fakewa da karatun addininka kana lalata yaran mutane a makarantar Jami'ar Madina?" Har wannan lokacin kan Sheikh a sunkuye yake banda cukurkuɗe Jallabiyar jikinsa da yake da hannu babu abin da yake. Father ya girgiza idanunsa cike da hawaye ya ce "Ba shakka biri yai kama da mutum, tunda nake baka taɓa zuwa wajena kace Father na zaɓi yarinya ina son aurenta ba,You betrayed me Aliyu, you deceived me as your father" Ya faɗa yana saukewa Sheikh wani marin cikin tsawa ya ce "Talk Aliyu, kayi magana ka amsa mini Sheikh..!!!" Father ya faɗa yana Girgiza kafaɗar Sheikh. Ɗago kai Sheikh yai bakinsa na rawa laɓɓansa na karkarwa alamar yana son cewa wani abu, amma sam ya gagara sbd rashin iya magana da bai ba. "Ban damu da duk yadda zakai magana ba Aliyu, a yanzu ba zanwa ƙinƙinarka uzuri ba ka bani amsa da gaske wata kaiwa ciki?" Shaaa hawaye ya sauka fuskarsa Sheikh sbd yadda yake son furta wani abu ya kasa. Matsawa ya yi kusa da Father yana buga hannunsa a cinya a hankali hannu na rawa ya miƙa tare da kama kwalar rigar Father, idan ya ɓalle bottle ɗin gaban rigar Father sai ya mayar rufe, da ƙarfi ya buga ƙafarsa yana riƙe wuyan Father hawaye ba zubu masa cikin ƙinƙina ya ce. "Ya....ya.... ya Allah..." Ya ƙare mgnar cikin ƙinƙina yana mai buga ƙafarsa a ƙasa. Share as so much as you can💋... Not Edited👏🏻 #Sarautar marubuta #True life story*🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Arewabooks@Nimcyluv*_ Follow my account👇🏾 https://arewabooks.com/u/nimcyluv 7... "Heeeyyy..faaa..Father,babb babu uhmuuu macen dana taɓa laaahhh latawa" a wahale ya Ƙarasa maganar sbd zafin ƙinƙinar dake cinsa take basa wahala, yana buga ƙafa a ƙasa tare runste idanunsa zuciyarsa na maza zafi da raɗaɗi sosai na cin zarafi da sharrin da ake son yi masa, amma ko kaɗan fuskarsa bata nuna damuwar da yake ciki ba, ƙinƙinar ita ke azabtar da zuciyarsa wacce take kassara dukkan wani mafarki nasa. Hannun Sheikh dake wuyan Father ya ture cikin ɗaga murya ya ce "Ok ƙarya za ayi maka kenan Sheikh? Mutane dubu nawa ne a makarantar ba ace sune suka aikata haka sai kai? Kasan halin da ake ciki yanzu gidan Jaridu na gab da sakin labaran? Mata nawa ka lalata, mata nawa kai wa ciki?" Cikin zafin maganganun Father Sheikh ya ƙara runste idanunsa kansa ma sara masa, shiru kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba. Father ya yi tsaki yana juyawa zuwa upstairs har lokacin bai dai na faɗa ba. "Kaje ka kare kanka daga zargi Aliyu, at anytime jami'an tsaro na iya zuwa, You are accused of a serious crime, we have no evidence to defend you in court" "Wanne Irin Court Father? Laifin Aliyu har ya yi girman da za a kaisa court? Wallahi babu mai kai mini ɗana Court" Hajiya Maryam wacce suke kira da Mother ta ƙare maganar tana sakkowa daga upstairs, domin lokacin da motocin su Sheikh suka shigo Sallah take. Father ya Kalli Hajiya Maryam tare da nuna Sheikh wanne yake ta damƙi Jallabiyar jikinsa. sam bai damu da duk zargin da za a yi masa ba, idan ƙaddararsa ce ta zo da haka babu yadda za ayi ya goje mata. "Sai ki tilasta masa ya yi magana, na faɗa masa ya nutsu ya ajjiye ƙinƙinarsa a gefe ya bani bayani, amma yaƙi, kina tunanin iyayen yaran zasu ɗaga masa ƙafa ne akan laifin fyaɗe da ya yiwa yaransu? Sbd kasancewarsa Malami kuma mamallakin S.A.H BANK..? ki Ajjiye son da ki ke masa a matsayin ɗanki, ki kwatantanta adalci tsakaninsa da sauran yaran daya lalata Maryam" Cikin faɗa Mother ta ce "Look Aliyu, idan kai ba zaka iya ƙwatarwa ɗan ka ƴanci ba, zan shiga ko'ina domin ganin an wanke Sheikh daga zargin da ake masa, ba abin kunya bane ace wai kai ne mai bada goyon baya akan Aliyu Haydar ya aikata hakan?" Father wanda Hajiya Maryam ta kira da Aliyu dake sunansa aka sakawa Sheikh ya yi Murmushin ta kaici. "Idan taƙamar maki Lawyer ce, kada ki manta su ma yaran Gwamnati na iya ɗaukar musu lauyoyi, dake da gwamnati sai ku zuba muga, kada ki manta daga can Madina aka zo da zan can, an kai maganar state C.i.d idan jami'an Nigeria bata ɗauki mataki ba, na Madina zasu ɗauka suna gab da bashi takardar kora daga aiki" yana faɗin hakan ya haura sama cike da baƙin cikin abin da Sheikh Aliyu Haydar ya ja musu a cikin Alhhali. Mother ta bi bayan Father da kallo, tana mamakin rashin ko'in kula da Father yake nunawa Sheikh kamar ba ɗan cikin sa ba. Juyawa tayi tare da kallon Sheikh da har yanzu kansa yake ƙasa tasan he never talk domin damar maganar bata damesa ba, sbd ƙinƙinar da Ubangiji ya jarabce shi da ita. Tana ƙoƙarin yi masa magana ya juya da sauri zai bar parlourn sbd raunin daya hango cikin ƙwayar idanun mahaifiyar ta shi. Yana saka kansa zai bar parlourn Umar-khan ya shigo da sauri jikinsa na rawa ya ce. "Innalillahi wacce irin masifa ke shirin tunkaro Mother?" Mother na ɓoye damuwar ranta ganin yadda Umar-khan ya firgita ta ce "Me ne ya faru Umar-khan?" Idanunsa akan Sheikh wanda ya ɗan jinkirta da fitar Umar-khan ya ce "Na rasa tayaya ƴan Jaridu suka samu wannan labarin, gaba ɗaya sun cika gidan nan da waje baki ɗaya, duk yadda securities sukai ƙoƙarin hana faruwar hakan amma abu ya gagara" Sheikh na jin haka ya juya alakar tafiyarsa zuwa haɗaɗɗan sashinsa dake cikin gidan nasu. Mother ta bi bayansa da kallo kafin ta juya ta kalli Umar-khan tace "Na jima banga mutum mai taurin kai da tsayayyiyar zuciyar irin Sheikh ba, duk abin da za ayi masa ba zai taɓa cewa komai ba" Umar-khan yaja numfashi yana mai ƙara gasgata zan can Mother, domin babu wanda bai san Sheikh da kafiya ba. "Yanzu ya za mu yi Mother? Al'amarin nan ya shige tunaninmu, ba tsammaci haka ba" Mother ta zauna kujera tana tunani ta ce "Zan shigar da ƙara Court, da kai da Saif-Wazir kuji da ƴan jaridu subar ƙofar gidan nan Immediately" "Court Mother? Waye zai tsaya masa? bakya tunanin shiga Court ɗin kamar latata rayuwar Sheikh ne?" A taƙaice Mother tana danna waya ta ce "Hakan ne mafita Umar-khan, batun lawyer ni ce zan tsayawa ɗa na da kai na" "but Mother" hannu ta ɗaga masa cikin sakin murya ta ce "Umar-khan...!!! Stop asking to much" jinjina kai yai ya fita yana jinjina girman yadda abin ya lalace cikin ƙanƙanin lokaci haka. Sheikh na shiga bedroom ɗinsa yaja numfashi sbd wani sassayan ƙamshin turarensa na ROJA daya daki hancinsa wanda ya jima da zama abokin hirar ɗakin. Ƙamshin daya haifar masa sauƙi a zuciyarsa, kasa zama ya yi ya shiga kaiwa da komowa a tsakiyar bedroom ɗin, tunani fal ransa wacce yarinya ya lalata? ba mace ɗaya ba har mata da yawa, kuma harda ciki? Bayan tunda yake maganar minti 20 bata taɓa haɗa shi da mace ba, idan ka ɗauke mother. Bai taɓa jin sha'awar mace ba, duk daɗin muryar mace bai taɓa ji ba, kamar an saka masa tsanar mata haka yake ji a ransa balle a wayi gari yau wata ta birgesa ba. Yinin ranar a sashinsa yake, Mother ba tai tunanin zuwa wajansa ba, ta san ba zai taɓa saurararta ba, koda Maimoon ta nufi part ɗinsa ɗauke da try na dinner yadda taje haka ta dawo, bugun duniya yaƙi buɗewa haka ta juya tana mai jin tausayin yayan nata. Mother dake zaune a Parlourn Father dake cikin sashinsa ta gyara zama ta ce "I couldn't believe what was happening,Aliyu is your son, you gave birth to him. Me ya sa ka yarda a ranka zai aikata hakan?" A nutse Father ya ɗaga kansa ya kalli Mother kafin ya ce "na fiki sanin ɗana ne, tunda akan idanuna ki kai Labour ɗinsa, amma hakan baya nufin zan saka masa Idanu, sai yanzu na fara tunanin tsayin shekarun da Aliyu ya kwashe a wannan duniyar ba tare da tunanin yin aure ba, kamar ko wanne namiji, nasan Aliyu nada lafiya balle nace, ke shaida ce how many times da zan kira Aliyu nace ya fitar da matar aure ya ce na bashi shekara ɗaya ko wata kaza? He is thirty-three years old now, but to this day there is no thought of marriage in his mind. Ni da kai na, na fara shakku da tantama idan ba lalata yaran mutane yake" wani irin ɗaci Mother taji a ƙasan zuciyarta, wanda ya sa ta fara ladamar yarda da Mijin nata da tayi. Magana ɗaya zai yi a janye Case ɗin amma yaƙi infact bai damu da matsalar ɗan nasa ba. Miƙewa tsaye ta yi tana kallonsa idanunta na sauyawa amma ta hana kanta zubar da hawaye ta ce. "Court zata tantance mai gaskiya, kuma zata wanke Sheikh daga sharrin da ake masa" tana faɗin hakan tai waje cikin ƙonar zuciya. Bayanta yabi da kallo yana faɗin "If you give evidence that Aliyu is innocent, zan tsaya wajan karɓar masa haƙƙinsa Maryam" sosai kalamansa suka daki kunnanta amma ta share. Tana zuwa parlour ta samu yaranta zaune sun zabga tagumi "Maimoon zugi driving nawa, Zeefa ke da Fattoumah ku zauna, I'll be back 10:00 ki tabbatar kunyi alwala tare da sallah kun kwanta barci, kada na dawo naga kuna kallo ok" Fattoumah ta ce "Mother ina zaki? Yaa Lee har yanzu bai fito ba fa?" Mother ta ce "Kada ki takura Sheikh, idan kika takurasa sai ya shaƙeƙi tas kafin ya baki amsa, You better be careful, bye my babies"... "Bye Mother" fita sukai har lokacin wasu ƴan jaridun na ɓoye suna jiran ganin motar Sheikh ta fito. Maimoon na fita taja motar da gudu ta ɗauki hanyar da zata kaita Maiduguri road. Tafiya kawai Danejo take babu takalmi kalbar kanta duk ta hargitse duk wanda ya ganta a wannan lokacin babu tantama zai kirata da mahaukaciya wacce ta jima cikin ciwon haukan. Tafi futu futu baya hayyacinta baki ɗaya,ita kanta ba zata taɓa tuna kwanakin data shafe tana tafiya ba, kuma abin mamaki ko gajiya ba tayi duk wanda ya ganta tambayar duniya idan zai mata ba zata taɓa kallon inda yake ba, balle kuma ta bashi amsa. Cikin ikon Allah ta samu kanta a gefen Rugar Rome inda take zuwa kiwo, tana zuwa nan ta yanke jiki ta faɗi babu numfashi. A hankali jikinta ya shiga Girgiza wani hayaƙi nafitowa ta jikinta a hankali hayaƙin ya cure waje guda, a haka ya rikiɗe zuwa suffar Prince.. idanunsa na kanta yana ƙoƙarin zuwa inda take yaji an daka masa tsawa wacce ya sanya ya tsaya da zuwa inda take, ko ba a faɗawa Prince ba ya san wane yake masa wannan tsawar domin shi kaɗai ya isa ya yi masa tsawa ya saurara. "Ka Saurara Prince, kada ka kuskure ka taɓa Bil'adama ɗin nan" Prince ya juya idanuna ya sauka akan mahaifina wanda yake cikin suffar mutane cike da kamala. "Matata ce Abba, ina da ikon taɓa ta a lokacin da nasu kada ka hanani aikata hakan" Wanda aka kira da Abba ya kalli Prince ya ce "Ban san yaushe ka zama mai son zuciya ba, zuciyoyi nawa zaka baƙantawa? yanzu bayan wannan ƴar tayin kaje ka saka bawan Allah cikin masifa me ya yi maka?" Prince yana huci ya ce "Abba wannan bawan Allan shi ke shirin rabani da farin cikina, na jima da sanin haka shi ya sa na fara yin abin da ya dace, kashe sa naso yi ma.." Abba ya kalli Prince da mmki kafin ya ce "Shi ne daidai da rayuwarta, shi ne Bil-adam shike da ikon kasancewa da ita, ba kai ba da kake Hallitar Ubangiji ta ban ƙasa ina rabaka da son zuciya, koda muke aljanu hakan bai zama lasisin da zamu cutar da wata hallita dake duniya ba, ko me zakai ba zaka taɓa iya cutar da shi ba" A hargitse Prince jiki na rawa yana rikiɗewa zuwa suffar aljanu ya kalli Safwan ya ce "Kai ne ka faɗa masa abin da na aikata ko? Kai ke ko?" Kafin Safwan ya yi magana Prince ya ɗaga sa zuwa sama tare da buga ƙasa da jikin dutse yana ƙoƙarin sake ɗaga Safwan, Abba yai wata kururuwa hakan yasa Prince yin kururuwa shima lokaci guda suka koma aljanu... 08119237616...*🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Zaku samu cikakken labarin a Arewabooks, kuyi searching sunan littafin ko username Arewabooks@Nimcyluv*_ 8.... Ihu da kururuwa Prince ya din ga yi, sbd tsananin azabar da Abba ya ganawa masa. Cikin wata kakkausar murya wacce take nuna cewa ko a cikin Aljanu shi ɗin nada banne, kuma taƙadiri ne. "Akan aurena dake kan Halisa banƙi na kashe kowa na illata shi ba, daga ci hadda kai Abba, ba ruwana da kasancewar ka mahaifina, kada ka rabani da Danejona zakai babban kuskure zanyi ɓarna a duniya" Bakin Abba na fitar da hayaƙi kamar zai kunna wuta a ciki ya ɗaga hannunsa sama gaba ɗaya ya naɗe Prince cikin wata sarƙa da yana bakinsa ɗauke da addu'ar neman samun nasara akan Prince ɗin. Duk ihun da yake bai hana Abba ya sarƙafesa cikin yanar ba idanunshi ya yi wata kala. Cikin ɗaga murya mai amo! Ya ce "Na raba aurenka da Halisa, babu kai ba ita, kuma a yanzu zan cire cikin dake jikinta mara imani mai muguwar zuciya" yana faɗin haka ya yi girgiza tare da ɓatar da Prince ɗin baki ɗaya daga wajan. A hankali Abba wanda Asalin sunansa ya kasance MURWAS ya sauke numfashi, tare da juyawa ya kalli Halisa dake kwance a ƙasa tana barci, juyawa ya sakeyi ya kalli Safwan dake kwance shi ma. Cikin nutsuwa wacce ba zata addabi dabbobin dajin ba ya yi Girgiza tare da rikiɗewa ya koma suffar mutane sak. Hannuna ya ya ɗauki Halisa Dajeno Rome da sauri ya nufi cikin Rugar Rome zuciyarsa fal farin ciki ganin yau ya raba ɗansa Bilal da Bil-adam. Babu kowa cikin rugar kamar an share hakan yasa ya fara bin bukkokin Rugar da kallo kamar daga sama Hamma Yabi ya fito daga cikin ruga zufa na yanko masa hannunsa riƙe da ƙwarya maganin gaba ɗaya tunaninsa ya yafi wani wajan bai lura da mutumin dake tsaye yana binsa da kallo ba. "Jamɓanduna" Abba ya faɗa yana kallon Hamma Yabi dake ƙoƙarin yin gaba, tsayawa ya yi yana duba mutumin da ya ce masa Ina kwana, cike da mamaki ya ce "Jamni tawon" ma'ana lafiya. Abba ya jinjina kai ba tare da ya ce komai ba, jikin Hamma Yabi na rawa ya amshi Danejo daga hannun Abba kafin ya ce "Ikon Allah, ina kasa meta? Tsayin mako guda ta ɓace mana ba ita ba labarinta, shai Allahamdulillah" Murmushi mai sanyi Abba ya yi cikin nutsuwa ya ce "Ayyah ni ma yanzu ina iyu a cikin ruwan na ganta kwance gefen ruwan" cikin nuna jin daɗi da manta halin da Dada ke ciki wanda duk rashin Danejo ya haifar da haka ya ce "Shannu, wallahi shannunka kaji" kai kawai Abba ya ɗaga yana ƙarewa yanayin rugar kallo kafin ya juya bayan sun yi Sallama da Hamma Yabi yabar wajan. Yana fita ya ɓace a wajan baki ɗaya. Dada na kwance bakinta na fitar da wani ruwa kamar dafara Shatu na gefe tana kuka tamkar ranta zai fita. A cikin wannan halin Hamma Yabi ya shigo cikin bukkar hannunsa ɗauke da Danejo wacce har yanzu take bacci. Jikin Shatu na rawa ta miƙe fuskarta cike da hawayen halin da mahaifiyarsu ke ciki, amma hakan bai hana Fuskarta baiyyanar da farin cikin da zuciyarta ke ciki ba na ganin Yayarta Danejo. Bakinta na rawa ta ce "Hamma ina ka samu Danejo, da gaske ita ce yanzu Dada zata tashi naji daɗi sosai" bai ce komai ba ya kwantar da Danejo gefen Dada idanunsa akanta ya ce "Maza kawo mini ruwa" Shatu ta miƙe da sauri tare da nufar tulo ta tsiyayi ruwan mai ɗan sanyi, tana bashi ya shiga shafawa Danejo yana kiran sunanta. A hankali ta sauke ajjiyar zuciya tana buɗe ido a nutse. "Danejo"... "Halisa" Shatu da Hamma suka kira sunanta lokaci guda,a sanyaye cikin sanyin jikinta kamar kullum ta shiga binsu da idanu. "Kin farka?" Kalmar Hamma ta sanya ta lumshe idanunta kana ta buɗe a hankali tana sake binsa da kallo kafin ta yunƙura zuwa zaune "Naga kuna ta kallona kamar za a cini ɗaya?" Murmushi Hamma ya yi ya ce "Munji daɗin ganinki Danejo, mako guda kenan mun rasaki kin ɓace daga idanunmu" da Mmki take kallonsa ɓata? Mako guda? Taje ina? Ita gani tayi kamar barci take mai ɗauke da mafarkai kala-kala. Shiru tayi tana ƙara sauke numfashi tare da fara tunanin maganar Hamma Yabi. "Hankalinmu ya tashi, Kullum Dada cikin kiran sunanki take, gashi yanzu ko buɗe ido ba tayi jikinta ya tashi ina tsoro kada mu rasa Dada kamar yadda muka rasa Baffa" ambaton sunan Dada ya saka Danejo saurin juyawa zuwa gefenta manyan idanunta ta buɗe "Dadata" ta furta a ruɗe ganin yadda Dada ta ƙanƙame jiki, idanunta na kafewa kamar mai shirin mutuwa cikin muryar kuka ta ce "Na lalashe ni Danejo Dadata kada ki barni kada ki mutu do Allah,Kada kibi Baffana" sai girgizata take amma ina Dada ko motsi ba tayi. Da sauri Hamma ya fita zuwa bakin hanya tare da samu abin hawa yana zuwa suka ɗauki Dada a mota zuwa asibiti, asibitin babu jama'a sosai. Dr Hamza na zaune a Office gabansa cike da kuɗi ya kalli Dr Iliya ya ce "Kawo maganin nan ya yi mana rawa sosai, na ƙara tura saƙo zuwa ɓangaren lafiya akan magungunan da suka bayar ya ƙare, sbd cututtukan da suke damun jama'ar rugar, ina saka ran cikin satin nan za a kawo maganin" Dr Iliya ya numfasa yana jinjina kai kafin ya ce "That's good. Amma da gaske maganin ya ƙare ne?".. "No ba wani ƙare wa da ya yi, har yanzu ban bawa ko mutum ɗaya ba" cikin fahimta Dr Iliya ya kalli Dr Hamza yana faɗin "huh! za a kawo maganin sauro kyauta ma a raba, sbd yawaitar Maleriya" "Na samu Information ɗin hakan, amma idan an kawo gidan sauron, asibitin nan za a Ajjiye mu zamu raba, so za a bawa Kowa akan 1500 each one" waro ido waje Dr Iliya ya yi kafin ya ce "baka ganin zamu iya samun matsala, tunda kyauta gwamnati ta bayar?" Ɗaga hannu Dr Hamza ya yi yana dakatar da Dr Iliya da faɗin "Hakan shi ne ribarmu, ba za mu yi musu bauta ba kamar wasu bayi, they have to pay" Kafin Iliya ya yi magana Hamma Yabi ya faɗo office ɗin da sauri cikin tsawa Dr Hamza ya ce "Malam ya haka zaka faɗo kamar wani mahaukaci? Me ya sa duk fulanin nan baku da ilimin zaman rayuwa ne, baku san yadda ake mu'amala ba?" Hamma baya gane zancan nasu ya ce "Don Allah ka taimaki Dadarmu, kada ta mutu cikin wannan halin ita kaɗai ta rage mana, sau wajan goma ina zuwa" "Idan munje kanta lafiya zamu bata kenan? Ko zamu hanata mutuwa? Zan maka last warning Kada na sake ganin ƙafarka cikin asibitin nan, na faɗa maka bamu da maganin ko ɗaya me kake so nayi maka? Haba kuna yi mana adalci mu likitoci sai an bimu a hankali mai ya sa zan zuciyarku ya yi yawa ne?" kasa magana Hamma yai sbd Hawayen daya cika masa idanu me ya sa su Fulani ake musu kallon mahaukata wanda basu san me suke ba? Akwai wani bambanci a jikinsu wanda ya bambanta su da sauran jama'a ne? Juyawa ya yi yana zuriyarsa babu daɗi. Danejo na ganinsa ta ce "Hamma ya naga ka daɗe, numfashi Dadata zai gudu ka taimaka, ina masu bada lafiya ɗin?" A hankali ya kama hannunta ya riƙe yana shafa kanta dake ɗauke da suma mai kyau can ƙasa ya ce "Muje gida, ba zamu ƙara zuwa asibitin nan ba, Allah ya a bamu Kuɗi mu kaita asibitin burni" shiru kawai tayi tana kallonsa tare da son fahimtar abin da yake nufi a haka suka koma gida jiki babu daɗi, kwana sukai ba su yi bacci ba, Shatu kawai ta runsta sbd ƙarancin shekarunta. A daren Danejo ta sanyawa ranta zata sai da nono iya iyawarta ta tara kuɗi masu yawa akai Dada asibiti. Hakan yasa ta tashi da asuba ta tatsi kindirmo a ƙwayar gari na fara haske ta nufi cikin burni wajan Abti America. Mother ce ke sakkowa daga upstairs kunnanta maƙale da waya idanunta sanye cikin farin glasses ta fito a Barrister Maryam ɗinta sak. A hankali ta ce "Na riga nayi reporting case ɗin, idan ba a samu good evedance ba akan wanda suka kawo ƙarar Aliyuna, kai tsaye zan maka ko wacce ƴar banza a court dama kawai nake jira" daga cikin wayar aka ja numfashi tace "Barrister Maryam kasa aje court,idan akaje to kin bawa duniya damar zata fahimci halin da ake ciki,abi komai a sannu" ɓayayyiyar ajjiyar zuciya Mother ta sauke idanunta na sauka akan Zeefa da Fattoumah "Ok za mu yi magana bari naje wajansa Allah ya sa ya yi magana, al'amarin Sheikh na bani tsoro yana bani mamaki" ƙara tattaunawa sukai kafin sukai sallama. "sannu da sakkowa mother" idanunta akan Plasma ɗin da suke kallo ta ce "Fattoumah sau nawa zan ce bana son kuna kallon zee world ne? Ashe ban isa daku ba ko?" A sanyaye Fattoumah ta ce "We're sorry Mother ba zamu sake ba" zama tayi ta ce "Change the channel immediately Mamana" Sauya channel Fattoumah ta yi zuwa Aljazeera tana faɗin "Ok Mother" kallonsu ta yi sosai ta ce "Where's Maimoon and Auta?" Zeefa ta bata amsa da "She's inside the kitchen, Auta barci take" Mother ta ce "Bana son barcin yamma taso mini ita" tana faɗin ta miƙe tare da nufar kitchen daga bakin ƙofa ta tsaya tana kallon Maimoon dake haɗa coffee ta ce "Ina Lunch ɗin Sheikh?"... "Gashi a tray mother bari na kai masa" tsareta tayi da idanu ta ce "Bani nan" tray ɗin lunch ta bawa Mother tana ci-gaba da aikin gabanta. Haɗaɗɗan part ɗinsa ta nufa tun daga nesa ƙirar arar Sheikh Muhammad didat ta ratsa cikin kunnuwanta da Mmkin fal fuskar Mother ganin ƙofar shiga parlournsa a buɗe. Ƙamshin air-cod ya ratsa cikin hancinta. Tana shiga idanunta ya sauka akan Umar-khan dake zaune gabansa ɗauke da system yana duba wani abu, ganin Mother ya sa Umar-khan saurin miƙewa tsaye ya ce "Sannu da zuwa Mother" "Yawwa Umar-khan ina Aliyun?" Hanyar da zata sadaka da bedroom ɗin Sheikh ya kalla yana faɗin "a Parlour na samesa lokacin da nazo, ina fara yi masa magana akan wannan case ɗin ya tashi ya shige bedroom har yanzu bai fito ba" jinjina kai tayi ta nufi bedroom ɗin, babu abin da bedroom ɗin yake sai ƙamshin turarensa ROJA wanda ya a jima da kama ɗakin duk da cewa bai fiye rayuwa a cikin gidan iyayen nasa ba, yafi rayuwa a Madina idan yana ƙasa Nigeria kuma yafi rayuwa a gidan Hakimi. ba kowa nan ma a bedroom ɗin sai tsarin ɗakin da Mother tabi da kallo wanda a kullum yake Sauya mata, komai na ɗakin fari ne tas, ɓangaren clothes, shoes, perfumes. Komai daban yake. Juyawa tayi zuwa parlourn tana faɗin "Umar-khan Aliyu baya nan fa? Ko dai ya tafi gidan Hakimi?" Umar-khan yai shiru ya ce "Bashi da ikon fita, kamar kullum ƴan jaridu na waje ta ko'ina maybe yana Library ɗinsa" sai a lokacin ta tuna da Library tana zuwa ciki ta samesa zaune akan wata ƙyakkyawar kujera wacce take juya kanta da kanta ya rufe idanunsa, sumar kansa ta ɗan bayyana sbd yanayin naɗin rawanin nasa wanda ya yi da farin hirami. Hannunsa harɗe a ƙirji. Zama tayi kujerar dake kusa dashi tana kama hannunsa ta ce "Abbana Babana" ajjiyar zuciya Sheikh Aliyu Haydar ya sauke sbd jin sunan da Mother's ta kirasa da shi amma ya kasa buɗe idanunshi domin baya son ta fahimci halin da idanunsa ke ciki wanda sune kaɗai suke fallasa raunin zuciyarsa. "Buɗe idanunka mu yi magana Babana, ba zan taɓa bari kayi gidan yari ba, zan tabbatar da kai a matsayin mai gsky ba zaka wulaƙanta ba" nan ma shiru ya yi mata bai ce komai ba kamar yadda ta tsammata. Hawayen da take maƙalewa ne ya kwance mata wanda ya zuba a tafin hannun Sheikh. Da sauri ya ƙankame hannunsu dake riƙe da nata yana buɗe idanunsa a hankali wanda suka sauya daka rinewar da sukai. Fararen idanun nasa ya ɗora akanta ganin hawaye a Fuskarta ya ƙara sashi cikin damuwa amma sam hakan bai bayyana a garesa ba. "Kayi magana Babana rashin maganarka shike sawa a dinga tunanin baka da gasky, zuciyata ba zata jure ganinka haka ba" Kallonta yake har lokacin bai ce komai ba. Ganin bashi da niyyar magana yasa Mother fashewa da kuka sosai tana miƙe tsaye da sauri ya riƙe hannunta gam! Yana miƙewa tsaye jallabiya ce jikinsa mai kyau da tsada ga laushi da tsantsi. Kai ya fara Girgiza mata yana matse hannunta sosai babu abin da Sheikh yake ƙauna sama da mahaifiyarsa sai Father daga su Hakimi sune duniyarsa. Hannunsa mother ta riƙe ta ce "Try to speak Sheikh ban damu ba nasan zan fahimce ka, zamu Court bani da wani proof da zan kareka, mene gasky?" Riƙe hannun Mother Sheikh ya yi tare da fara buga ƙafa yana ƙoƙarin buɗe bakinsa. Ganin haka yasa Mother taimaka masa wajan riƙe hannunsa tana faɗin "Ahha say something, speak Babana, say it" hannunta duk biyun ya kama ya riƙe yana runtse idanunsa sai buga ƙafa yake tuni hawaye ya fara cika idanunsa. "Yee... Ƙaƙƙƙaaa... M...mmm" kai ta ɗaga masa tana shafa kansa a fisge bayan ya buga ƙafarsa da ƙasa yana saka hannun Mother a bakinsa ya ce "Babbbban akaita ba, bbbb ba zan taɓa yin yin yin haka ba mother" yana faɗin hakan yana ƙara saka hannun Mother a bakinsa duk ya jiƙa mata hannu da yawunsa mai ƙamshi a ƙoƙarinsa na ganin ya yi magana daidai waya baiwa ta Sheikh idan koyarwa zai yana samu maganarsa ta fita yake fara karatu cikin sauri baya tsayawa sai ya gama yana gamawa baya ƙara cewa komai yake fita daga hall. Wani irin rauni ya kama zuciyar Mother tausayi da ƙaunar Sheikh ya ƙara wanzuwa a zuciyarta wacce irin larura ce haka wacce bata barin har babban mutum? Zare hannunta ya yi domin har ransa bai san lokacin daya saka hannunta a baki ba a hankali ya juya zai bar wajan da sauri mother tana goge hawaye ta ce "Aliyu" cak ya tsaya tana ƙoƙarin magana Umar-khan ya shigo wajan da sauri gaba ɗaya suka bisa da kallo Umar-khan ya ce "Sheikh na shirya mota a ƙofar baya, yanzu zamu bar gidan nan jami'ai na hanyar zuwa nan zasu kamaka" ko motsawa Sheikh bai ba shi dai ya san ba zai taɓa hana abin da Ubangiji ya tsara afkuwa ba. "Jeka Aliyu ka bisu su fitar dakai Sheikh" Mother ta faɗa tana jan hannunsu ganin haka yasa ya bita har zuwa bakin wata sabuwar mota shiga ya yi. Drivern yaja, Umar-khan shima ya shiga mota, Saif-Wazir ya shiga wata motar. Motar ƙarshe kuma Ishaq-hakim ya shiga kai tsaye suka nufi wata hanya ta daban. Sbd gujewa haɗuwa da jami'an da kuma ƴan jaridu, kasancewar duk sunyi connecting wayoyinsu dana juna yasa Umar-khan gyara bluetooth na kunansa ya ce "Saif-Wazir" Saif ya amsa da "Ina kan layi" haka Ishaq-hakim da kuma Drivern Sheikh. Cikin jin daɗi Umar-khan ya ce "Saif-Wazir idan mun isa Shatalelen gidan gwamna kabi hanyar Amado bello way" Saif-Wazir ya ce "Noted bro" Umar-khan ya ce "Ishaq-hakim kabi hanyar Asibitin nasarawa, Drivern Sheikh Kabi hanyar ƙofar nasarawa,ni kuma zanbi hanyar kasuwar tarauni, gaba ɗaya hanyoyin zasu haɗamu a titin Dawaki roud zamu sauka gidan Hakimi.." haka duk suka amince suna zuwa Shatalelen gidan gwamna ko wacce mota ta ɗauki hanyarta suka ɗauke tunanin jami'an tsaron daka hanyar da zasu bi, Sheikh na bayan mota ya zubawa ikon Allah idanu a haka suka ƙarasa Dawaki roud motocin suka haɗu waje guda kai tsaye suka ƙarasa gidan Hakimi. Sheikh na fito da ƙafarsa waje aka riƙe hannuna tare da saka masa sarƙa kamar daga sama yaji ance "You are under arrest..... 08119237616.*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* _*E.O.W*_ 9... "You're under arrest?" Umar-khan daya fito daga cikin mota ya ƙara maimaita kalmar ɗan sandan wanda ya yi ɓadda kama cikin kayan gida. Ɗan sandan ya kalli Umar-khan fuska ba walwala ya ce "As you heard" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Shi ne kalaman da Saif-Wazir ya faɗa domin Umar-khan kasa motsawa ya yi idanunsa a ƙasa baya taɓa jin zai iya haɗa idanu da babban mutum kamar Sheikh Aliyu Haydar cikin wannan halin. "Yallaɓai kayi mana afuwa mu shiga ciki mu tattauna, ba sai an tafi da Yaa Lee police station ba please" Wanda aka kira da Yallaɓai ɗin ya ce "Stop interfering with our work, because we know our work well, kuma wane ya faɗa maka police station zamu kai Aliyu Haydar Aliyu? State C.i.d zamu" da tsoro sosai akan fuskar Saif-Wazir ya ce "C.i.d? Wajan da ake ajjiye manyan masu aikata criminals, ƴan fashi,ƴan daba, Kidnappers Sheikh bai dace da wannan wajan ba, don Allah kada ko taɓa mana martabarsa.....," Ishaq-hakim ya katse Saif-Wazir da faɗin "har yanzu ba a tabbatar da abin da ake tunanin ya yi ba, zargi ne kawai" Wani daga cikin ma'aikatan ya ce "Say whatever you want to say,We must arrest Sheikh Aliyu Haydar Aliyu" cikin zafin zuwa Ishaq-hakim ya kalli ɗan sandan yana nu nasa da hannu ya ce "Idan ta ƙamar kai uniform ne a jikinka mu kuma mune da garin, wallahi idan ya tabbata Sheikh bashi da laifi sai munyi Shari'a da kai" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi babban gate ɗin shiga gidan Hakimi, kasancewar daman a ƙofar gidan suke. Sheikh dai na tsaye tamkar ba akan sa ake wannan muƙabalar ba, ya tsorawa hannunsa dake maƙale da ankwa ido shi kaɗai zai iya fasalta halin da zuciyarsa ke ciki sai kuma Abba Hakimi dake iya fahimtar raunin zuciyar Sheikh ɗin lokaci guda. Suna ƙoƙarin saka Sheikh cikin wata baƙar mota mai kyau wacce babu wanda zai iya ganin Sheikh ɗin a ciki gyarar muryar Abba Hakimi ta karaɗe wajan. Cikin mutuntawa da tarin ladabi duk jama'ar wajan suka sunkuyar da kansu ƙasa. A hankali Sheikh ya ɗago kansa tare da sauke ganinsa akan Abban nasa Hakimi, raunin idanun Sheikh ya bayyana sakamakon zuwan Hakimi wanda shi kaɗai ya fahimci hakan, shi kansa ya kasa yiwa Sheikh ɗin gwaggwaran kallo, idan akwai abin da Hakimi ya keso a rayuwa bai shige Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ba, son da yake masa ko ƴar ƴan cininsa su Ishaq-hakim ba ya yi wa soyayya ce ta musamman tun Sheikh na zanin goyo. Zame ido Abba hikima ya yi daga kan Sheikh yana mayar wa kan jami'an tsaron da suke jiran suji mai zai ce, domin su basu da wani laifi akan aikinsu suke komai, ko da basu aikata hakan ba, gwamnatin ƙasar Madina zata ɗauki mataki, matakin da zaiwa kowa ciwo da zafi a zuciya. "Zaku iya tafiya da shi" Abba Hakimi ya furta a nutse yana shafa sumar Sheikh tare da ɗaukan hiraminsa ya fara naɗa masa sabon rawani. Da sauri Ishaq-hakim ya ce "Abba ta ya ya zaka bari a tafi da Yaa Lee? Kai ne wanda nake tunanin zaka dakar dasu daha tafiya da shi?" Murmushi mai laushi Abba Hakimi ya yi yana ɓoye damuwar ransa kafin ya ce "Mulki daban, hukuma daban Ishaq-hakim a barsu suyi aikinsu muma muyi namu" Umar-khan juyawa ya yi tare da shiga mota ya kifa kansa jikin Kujera ba zai iya zuba idanu a gabansa a tafi da Sheikh ba. Saif-Wazir idanunsa ya yi jajur gaba ɗaya yanayin baya yi masa daɗi. "Aliyuna" Abba Hakimi ya kira sunan a taushashe yana kallon Abban nasa, cikin kulawa ya ce "Kayi haƙuri, ƙarya fure take bata ƴaƴa, lashakka gaskiya zatai halinta ka ɗauka kai ni kana daga cikin bayin da Ubangiji zai gwada imaninsu" ƙanƙame hannun Abba Hakimi Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya yi, hakan ya tabbatar wa da Abba Hakimi Sheikh ya amince da zan can nasa. Sakin hannunsa ya yi gaba ɗaya jikin jami'an tsaron ya yi sanyi bisa dole suka saka Sheikh cikin mota tare da tafiya da shi. "Ishaq-hakim kawo mota, zuwa wajan Aliyu da Barrister Maryam" jinjina kai kawai Ishaq-hakim ɗin ya yi, tare da buɗewa Abba Hakimi bayan mota ya shiga, Saif-Wazir da Umar-khan suka bi bayan motar su Sheikh domin suji inda zan can zai tsaya. Mother na tsaye ta kasa zama sai number ɗaya daga cikin samarin take gwadawa amma basa ɗagawa, hankalinta ya ƙara tashi fiye da ko yaushe tunanin abin da ya samu Sheikh ya wanzu a zuciyarta. Upstairs tayi da sauri kai tsaye part ɗin Father ta nufa yana zaune a ƙawataccen parlournsa mai kyau, hannunsa riƙe da jarida cikin baƙin ciki yake karanta inda aka saki zan can Sheikh tare da photonsa,gaba Al'amarin ya wanzu a duniya dama media baki ɗaya. Shigowar mother ya sanya Father Kallonta yana jiran jin abin da zata faɗa wannan karan. "Barrister Maryam lafiya ki kai mini tsaye?" Da mmki ta dubesa sosai kafin ta ce "lafiya kake tambaya? Wai me Aliyu ya yi maka da baka kula da al'amarinsa ne?" Hannu ya ɗaga mata ya ce "Saurara Barrister Maryam ni na aiki Aliyu ya aikata hakan? ko da izinina ya ke lalata yaran jama'a yana musu fyaɗe?At Aliyu's age, I will not be surprised at all that he did, ba a shaidar ɗan yau Maryam da ace yana da mata babu mai zarginsa da aikata haka" tarin mamaki da ya gama cika Mother ya sanya ta kasa cewa komai sai kallon Father kawai da take "Aliyu ɗan ka na cikinka kake wa wannan shaidar, shaidar iyaye ita ce shaidar Allah fa, banda na san kai ne mijina kai ka samar da Aliyu da babu abin da zai sanya nace ba kai ka haife shi ba, amma kaje lokaci ne zaka fahimta idan baka son sa muna son shi" kai kawai ya girgiza mata yana faɗin "Zaki iya zuwa ki nemi Mahaifinsa a waje, tunda kina tantama" kafin Mother tayi magana Fattoumah ta shigo Parlourn kallon iyayen nata tayi ganin kamar hayaniya suke, fahimtar hakan yasa Mother yin murmushi ta ce "Mamana ya akai? Ban hanaku zuwa waje ba without permission zan fara bulala fa" marairaice fuska tayi ta ce "Am sorry mother ina ta sallama tun ɗazo" kallon yadda Fattoumah ta tsare Father da ido mother tai cikin sauri ta ce "Ya akai to?" Da sauri ta ce "Abba Hakimi yana Parlour kizo ke da Father" tana faɗin hakan ta juya da sauri tana jin Father na faɗin "Fatimah.. Zarahh..!!" Amma tai banza da shi, Fattoumah irin yaran nan ne masu riƙo da kuma kishin iyayensu mata gaba ɗaya taji abin da Father yake faɗa akan Sheikh. Fita Mother tai tana sakkowa fuskarta ɗauke da fara'a tasan tun da taga Abba Hakimi to Sheikh yana can gida cikin kwanciyar hankali. A ƙasa ta zauna tana gaida shi ya amsa a nutse kafin ya yi magana Father ya fito shi ma ya zauna saman Kujera ya ce "Sannu da hanya Abba Hakimi" kai kawai ya jinjina idanunsa akan Fattoumah yana faɗin "Matar zo nan mana ke dawa haka?" Turo baki tayi idanunta na sauyawa ta ce "Mijin me ya sa Father baya son Yaa Lee?" Sa mamaki Hakimi ya kalli Father yana faɗin "Aliyu ya akai haka? Me ya sa kake barin raya su san abin da ke zuciyarka ne?" Father ya ce "Abba Hakimi ta ya ya zan ƙi ɗana? Shirman Fatimah ne" da sauri Fattoumah ta ce "Da gaske nake Mijin,ina jin yana faɗawa mother wai a nemo mahaifin Yaa Lee kuma ai ba kyau ƙarya" surutun Fattoumah ya jijjiga Mother bata taɓa haifar yarinyar mai kaifin bakin Fattoumah ba. "shige ki bamu waje Mamana kafin ranki ya ɓaci laɓe kike mana kenan?" Turo baki Fattoumah tayi tace "Mother kawai ki nemowa Yaa Lee Abbansa wanda zai so shi tunda father baya son sa" Abba Hakimi da Mother suka kalli juna da sauri kuma suka janye idanunsu ko wanne tunani fal ransa. Tsawa Mother ta yiwa Fattoumah ta tafi ɗakinu Maimoon tana sakin kuka ta fara bori a ƙasan carpet. A nutse Abba Hakimi ya kalli Mother ya ce "Aliyu yana state c.i.d Barrister Maryam" a ruɗe Mother ta Kalli Hakimi hankali tashe take faɗin "An kama Babana? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wallahi sharri ne ba gaskiya ba, kuma zan tabbata da hakan" Hakimi ya ce "Samu nutsuwa Barrister Maryam, mu duka ba zamu ja da ikon Allah ba, kuma da hujjar kare Aliyu, shi ya sa nazo naji ko ya faɗa muku wani abun?" Father ya yi dariyar baƙin ciki ya ce "Wannan ne zai magana? Ko ya yi bata da wani amfani me zamu fahimta banda, A...Aaaa...ƙikkkk... Yeee gaba ɗaya Aliyu bashi da amfani a rayuwarmu, naji baƙin cikin samunsa Matsayin ɗa namiji" wani baƙin ciki ya tukare zuciyar Mother idanunta na cika da hawaye ta ce "Sai yanzu na fahimta larurar Aliyu ta sanya kake ƙinsa? Ubangiji ya ɗora masa shi nake roƙa kuma ya ye masa" Abba Hakimi ya numfasa kalam Father sun bashi mmki a haka ya share ya ce "kayi babban kuskure Aliyu, kuma Sheikh abin Alfaharin duk wani ɗan Kano dama Najeriya ne, muhimmancin bai tsaya iya ƙasar shi ba, har ƙasa mai tsarki.. Allah ya kyauta wata rana zaka gane gaskiya lokacin da za kaji kunya" juyawa kan Mother yai ya ce "Akwai abin da ya faɗa miki ne, ina son shigar da maganar zuwa court ne" Mother ta ce "Yana cikin ƙoƙarin fahimtar dani suka taho wajanka ya faɗa mini bashi ya aikata ba, kuma ni ma na shigar da ƙara ni zan tsaya masa tare da Barrister Zainab" wayar Mother ce ta fara ringing ganin sunan Umar-khan ya sanya ta ɗauka cikin sauri ta miƙe tana faɗin "Ohhh ok on our way" kashe wayar tayi idanunta akan Abba Hakimi ta ce "Umar-khan ya ce muzo yanzu al'amarin ya shige tunani" da sauri ta nufi ɗaki tare da ɗakko mayafi da key car. Abba Hakimi da Mother suka nufi state c.i.d hankali a tashe Maimoon da Zeefa da Fattoumah sai kuka suke a rayuwa suna ƙaunar yayan nasu duk da babu wata jituwa a tsakaninsu. Ko abinci suka kasa ci sai sallah kawai da suke suna addu'ar Allah ya kuɓutar da Sheikh ɗin. Hankali kwance Father yake zaune yana waya da babban amininsa ko da wasa bai masa magana akan matsalar da suke ciki ba, duk da cewa al'amarin ya gama zaga ko'ina a faɗin Nigeria. A kiɗime Mother take bin su Saif-Wazir da kallo ganin yadda idanunshi ya yi jajur alamar kuka suka sha. "Ina Babana ina Aliyu mai ya faru da shi?" Shiru Saif-Wazir ya yi mata, ta juya kan Umar-khan ta riƙe wuyansa sosai cikin faɗa ta ce "Where's my son Umar-khan? Ina Aliyuna?" Umar-khan ya yi ƙasa da idanun shi ba tare da ya ce komai ba. Sakin Umar-khan tayi ta nufi wajan Ishaq-hakim ta ce "Ishaq-hakim faɗa mini gsky ina Aliyu me akace yana da gsky ko? Ba aikata abin da ake zarginsa ba?" Hannunsa ya ɗaga tare da nuna mata wani waje da sauri ta juya Idanunta ya sauka akan Sheikh Aliyu Haydar Aliyu wanda aka cire masa Jallabiyar jikinsa aka ɗauresa da Sarƙa tun daga wuyansa hannunsa zuwa ƙafarsa farar fatar jikinsa tayi jajir bakin Ishaq-hakim na rawa ya ce "Mother Sheikh ya amsa laifin da ake zarginsa ya tabbatar shi ne ya lalata ƴan matan hadda ciki..... _*IDAN BA KE...* labari ne da kuka daɗe ba kuci karo da irinsa ba, ƙaddarar labarin akan soyayya ne mai tsayawa a zuciya da saka shauƙi a zuƙatan masu karatu..... Tsammaci abin da baka tsammani salo na musamman🫣💋 08119237616._*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 10.... Kasa magana Mother tayi sai Ishaq-hakim da tabi da kallo tana son gasgata abin da yake faɗa. "Ta ya ya Sheikh zai amsa laifi fyaɗe? Laifin da duk duniya ta san ba zai iya aikatawa ba?" Ta faɗa a fili tana sakin wani raunataccen kuka mai tsayawa a zuciya ba zata iya kallon Sheikh cikin sarƙa a ɗaure ba, kamar wani ɗan fashi ko Kidnapper. Umar-khan ne ya kama Mother wacce take ƙoƙarin zubewa a wajan sbd kukan da take idanunsu ya yi jajur ya ce "Ki daina kuka Mother, wata kila Sheikh ya amsa laifin ne sbd rashin mafita, mu duka abin ya zo mana cikin wani sabon yanayi wanda bamu taɓa riskar kanmu ciki ba, Ubangiji ka ɗai ya san gaskiya kuma shi muke roƙa ya fidda Sheikh Aliyu daga cikin wannan jarrabawar" gaba ɗaya zuciyar Mother ta karaya tunaninta ya tsaya cak duk inda take neman wata hujja ta kare ɗan nata babu. Da hannu bibbiyu ta riƙe Umar-khan ta ce "Kai ne kake tare da Babana Umar-khan, ka taimaka mini nasan kasan Aliyu ba zai iya aikata hakan ba, yana tsare imaninsa yana amsar rayuwa a duk yadda ta zo masa" Umar-khan ya mayar da hawayen dake cika idanunsa kafin ya zaunar da Mother ya ce "Be patient Mother, muyi addu'a kawai amma da ace zan iya bada shaida, da iya abin da zan faɗa ya isa ya wanke Sheikh daga cikin zargi" "That's enough, this is not a place to make noise" Wani daga cikin jami'an tsaron ya faɗa yana daka musu tsawa. Sai a lokacin Abba Hakimi ya yi ajjiyar zuciya domin shi ma Al'amarin ya girgiza shi fiye da tunanin kowa, zuciyarsa shi zafi take masa sosai. A nutse ya juya ya kalli Ishaq-hakim ya ce "Ka mayar da Barrister Maryam gida yanzu, ka ce ina buƙatar ganin Aliyu immediately" da girmamawa Ishaq-hakim ya amsawa mahaifin nasa, idanunshi akan Mother yana jiran ta miƙe. Cikin kuka ta kalli Abba Hakimi ta ce "Ina son nayi magana da Aliyu Please Hakimi" Kafin Abba Hakimi ya bata amsa wani daga cikin Jami'an tsaron ya ce. "No way Madam" tana share hawaye ta ce "Don girman ka bani 2 minutes nayi magana da ɗa na, ina son tambayarsa, tare da kwantar da hankalin shi" cutting nata out ya yi da faɗin. "Isn't necessary Maaah..." A ƙagauce Abba Hakimi ya ce "take her out Ishaq-hakim" Mother na kuka sosai tana kiran sunan Sheikh Aliyu aka fitar da ita waje, Aliyu shi ne rauninta ka kaf cikin yaranta tafi ƙaunarsa duk abin da Mother ta mallaka daga cikin dukiyar iyayenta Aliyu ta bawa, She owned all her property for him, Lands, houses, companies, all signed in the name of Aliyu's property. Su Mother na fita Abba Hakimi ya kalli jami'an tsaron cikin murya mai taushi ya ce "Kun samu hujja mai ƙarfi da kuka kama mini ɗa na?" Ɗaya ya sunkuyar da kai cikin girmamawa ya ce "Har yanzu bamu da hujja, amma a duk bin ciken da mukai Sheikh ƙara shiga ciki yake, yaƙi buɗe baki ya yi magana, gwamnatin Madina da universityn ƙasar sun matsa akan kwana biyu suka bayar idan ƙasa Nigeria bata ɗauki mataki ba, zasu ɗauka da kansu domin su irin wannan cases ɗin kai tsaye suke bincike kuma hukuncin kisa ne" runtse idanu Abba Hakimi hukuncin kisan ya daki zuciyarsa ainun. Umar-khan da bakinsa ke rawa tun ɗazo sbd masifa ya ce "Ita kanta gwamnatin Madinan idan bata da hujja dole ta haƙura, ina masu kawo ƙarar? Daga ina wannan zan can ya fito? Ina ƴan matan da akaiwa fyaɗen suke?" "Stop raising your voice, we are working on our system, nan ba Court bace" Umar-khan zai sake magana Abba Hakimi ya yi gyara murya kafin ya ce "Ka bari abu komai a nutse, shi ya sa na mai da Barrister Maryam gida" Saif-Wazir dai na tsaye duk yadda suka so a basu Sheikh su yi magana hanawa akai. Kuma a gobe za a kaisa court domin fara gabatar da Shari'a tun da case ɗin ya zo da hargitsi. Haka suka komai gida zuciyoyin kowa babu daɗi. Sheikh na zaune daga shi sai single da wani farin trousers mai laushi tunda yake a duniya babu wanda ya taɓa ganin tsari da zubin halittarsa sai yanzu, an tuzarta shi tuzarcim daya har zuƙa kuturwar zuciyarsa, shi kaɗai sai tsuma yake shi da ko sauro baya so baya ƙaunar yaga baiwar halittar da tsaraicin jikinsa, yana tsarkake jikinsa domin sirrinsa ne, amma yau da wanda ya dace da wanda bai dace ko wanne tom and jerry gani yake abin ya yi masa zafi ainun. Dalilin daya sanya ya amsa laifin kenan ba tare daya shirya hakan ba. Mother na komawa gida ta samu Fattoumah na zaune ita ɗaya a Parlour da sauri Fattoumah ta ce "Mother ina Yaa Lee? Ba zai dawo ba?" Murmushi mother ta yi tana ɓoye damuwar ranta ta ce "Ya dawo mana Manana, yan gidan Abba Hakimi where's your sisters?" Da hannu ta nuna mata part ɗinsu, Mother ya kama hannunta suka shiga ciki. Yaran duk suna zaune sanye da hijabi sunyi shiru bayan sunci kuka sun ƙoshi, cikin faɗa ta ce "Maimoon, Zeefa what's this? Kuna da hankali zaku shigo ɗaki kuyita kuka kamar anyi mutuwa, Depression kuke son ya kamaku ko mene?" Gaba ɗaya suka miƙe tsaye jikinsu na rawa za su yi magana ta ɗaga musu hannu ta ce "Ku fita a nan wajan, maza aje a kunna kallo ayi" fita gaba ɗaya sukai jiki babu ƙwari mother ta bisu da kallo tausayin su na kamata tasan duk sanadin Aliyu Haydar suka shiga wannan damuwar. Kuma ita idan har ƴar halak ce ba zata sake zuwa wajan Father ba akan maganar Sheikh Aliyu ɗin ba. Tana fitowa daga cikin bedroom ɗin upstairs ta haura zuwa nata bedroom ɗin wayarta ta ɗauka ta shiga kiran Barrister Zainab akan gobe zasu shiga Court sun daɗe suna waya kafin ta kira Yaya Halima anan ta kwantar mata da hankali ta ce ita ma ta nan zuwa dan sunyi nisa ne. Har Mother ta miƙe da sauri kuma ta koma ta zauna domin gaba ɗaya ta manta da batun Jadda cikin sauri ta danna numberta wayar ta jima tana ringing kafin a ɗaga a fusace akace "Allah dai yai gutsi gutsi da duk wanda yake addabata wannan masifar har ina, ba lallai mutum yaga Annabi ba" A hankali Mother ta ce "Jadda ni ce Maryam" Jadda ta ce "Wata abace Maryam kuma? daga wacce duniya mena haɗa dake?" Shiru Mother can kuma ta ce "Mahaifiyar Sheikh Aliyu" Jadda ta zabga salati da duk ƙarfinta ta ce "Yanzu Maryam cewa nayi ban gane ki ba? Masifar gaisuwa ce bana so, Ina shi Aliyu yana can Madina ɗin ne?" Mother ta ce "Baki san meke faruwa da shi ba?" Jadda dake kishin giɗe tayi saurin Miƙewa zaune tana faɗin "Allah ya isa, dake Maryam da shi Aliyu Allah dai ya isa wani abu ne ya samu Sheikh bani da labari?" Kafin Mother tai mgn father ya ƙwace wayar tare da kashewa baki ɗaya ya kalli Mother ya ce. "Yanzu Barrister akan wannan maganar zaki haɗani da Mahaifiyata? Su kike ta tsine mini tunda kin san bakinta ba shi da tsarki wajan sakin magana da kwasa ta" banza tai masa ba tare da ta ce komai ba, yana ƙoƙarin sake magana ta miƙe tsaye tana faɗin "Idan ka gama ka ajjiye mini wayata, I have something to do with my phone" tana faɗa ta shige toilet domin zuciyarta a kusa dake da shi. da idanu ya bita kana ya ajjiye wayar yana mmkin halin mata a wasu lokutan. Gari na waye Barrister Zainab ta zo suka fita zuwa State C.i.d ita da Mother abin mamaki gaba ɗaya ƴan jaridu sun cika gidan Redio, da t.v kowa yana jiran a fito da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu. Cikin nutsuwa Barrister Zainab dake driving ta kalli mutanan ta ce "Am still wondering ta ya ya zan can nan ya shiga kunnuwan Al'umma" Murmushin taƙaici kawai Mother ta yi wai duk akan Innocent son ɗinta ake wannan tururuwar kamar wanda ya kashe mutum?. "Allah ya kyauta, mutane akwai su da son gulma musamman ƴan jarida wallahi" I.d card ɗinta wanda ke nuna ita cikakkiyar lawyer ce mai zaman kanta ta nuna kana aka basu damar shiga, tun kafin Barrister Zainab ta yi parking idanun Mother ya sauka akan Sheikh wanda aka fito dashi cikin wata ƙatuwar sarƙa tare da wasu manyan ƴan fashi, wani abu ya tsaya mata wanda bata taɓa jin irinsa ba, ko hawaye ta kasa a wannan lokacin. Da sauri ta fita haka ma Barrister Zainab ɗin, ana ƙoƙarin saka Sheikh Aliyu cikin mota wata mota ta shigo da gudu cikin haraba wajan hakan ya sa duk suka daka ta. Wani babban jami'in tsaro ne tare da Abba Hakimi suka fito daga cikin motar sai wata matashiyar budurwa wacce Fuskarta ta kumbura sosai sbd kuka. I.G ya kalli jami'an tsaron cikin tsawa ya ce "Maza a cire sarƙar nan, a bawa Sheikh Aliyu Haydar Aliyu kayansa ya saka, He's Innocent ya fita daga jikin zargi, Wannan matar ita ce wacce ta shirya komai, she's the reason behind, She is the one who harmed Aliyu" Gaba ɗaya kallon budurwar sukai wacce take kuka kamar ranta zai fita. A karo na farko Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya ɗago idanunshi tare da sauke su akan budurwar wani irin lallausan murmushi ya sauke wanda ya kusan ɗauke hankali jama'a tare da basu mamaki, hatta Mother tai mamakin ganin murmushi a fuskar Aliyun. Cikin ƙaramin lokaci aka sakawa Sheikh wata jallabiya mai kama da Alkyabba tare da wani farin hirami nan da nan kamalarsa ta fito haibarsa ta cika Idanun kowa. I.G ya bada umarnin a kama budurwa Sheikh ya yi gyara murya yana tafiya a nutse cike da kamala tsayawa yai daidai inda budurwar take, for the first time a tsayin rayuwarsa daya tsaya gaban mace kana ya juya ya kalli I.G sanin cewa ba zai iya taɓa jikin I.G ba yasa ya kama hannun Abba Hakimi ya riƙe da kyau yana runtse idanunshi, ƙafarsa ya ɗaga ya buga a ƙasa cikin In-ina ya ce "Aahhhh ahhha abarta, dooo.. do.. domin ba ba ba....ba a faɗa da Aljani. Not Edited 08119237616 🫰🏽kai tsaye ga mai buƙatar littafin.*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 11..... Abba Hakima ya kalli Sheikh a nutse yana mai sakin murmushi shi ma, tare da juyawa ya kalli budurwar wacce taƙi yarda ta kalli inda Sheikh ɗin yake, tun daga sama zuwa ƙasa Abba Hakimi ya ƙare mata kallo kafin ya ce "A'uzu bi wajhillahil karim, Wabi kalimaatil lahillati la yujawizuhunna barran wala fajiran, wabi asma'illahil husna kulliha, ma alimtu minha wa malam a'alam min sharri ma yanzilu minas sama'i, wa zara'a fil'ardhi, wa min sharri ma yakhruju minha, wa min fitnatillaili wan nahari, wa min ɗawariƙil laili wan nahari, illa ɗariƙan yadruƙu bikhairin ya Rahamanu. Wa min sharri kulli dàabbatin Rabbi akhizun bi nasiyatuha inna Rabbi ala siraɗin mustaƙim" jikin budurwar ne ya fara rawa sosai, tsoran Abba Hakimi da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu suka cika mata zuciya, bata son su cutar da ita tunda ita bata zo da nufin hakan ba, kuma daman Ubangiji ya ɗora mata tsoran Sheikh ɗin tun ba yanzu ba, tana jin girma da nauyinsa tare da shakkar sa kwarjininsa yafi komai dagula mata lissafi. Idan ka ɗauke Abba Hakimi, No one understands the words of Sheikh Aliyu. "No!!!" Sheikh Aliyu Haydar ya furta a nutse yana riƙe hannun Abba Hakimi wanda bakinsa ya kasa yin shiru da addu'ar da yake, dalilin hakan yasa budurwar ta nemi birkicewa wanda kuma daga Abba Hakimi sai Sheikh ɗin ne kawai suke ganin hakan. Shiru ya yi da addu'ar yana kallonta kafin ya juya ya kalli Sheikh fuskarsa ɗauke da annuri irin na cikakkun dadtawan nan ya ce. "Yaushe Aliyu ya samu abokai haka bani da labari" a wannan karan Sheikh bai murmushi ba sai rirriƙe hannun Abba Hakimi da ya yi yana lumshe idanunsa tare da buɗewa alamar "Bai san yadda akai hakan ya faru ba" riƙe hannu Sheikh ɗin kai tsaye Abba Hakimi ya yi domin kai tsaye ya fahimci karatun idanun na Sheikh. I.G dake tsaye shi da Barrister Maryam yana bata haƙuri ya ce. "I'm sorry, action was taken without investigation, we were wrong" kasa riƙe kanta mother ta yi cikin losing control ta ce. "You have defamed Sheikh's name, all those who respect him have now stopped, Sbd Kuskuren ku my son is innocent na riga dana faɗa muku, but you refused to understand me" Bar Zainab ta numfasa cikin rashin jin daɗi ta ce "Everything that has happened has already happened, kawai a kira ƴan Jaridu a shaida masa Sheikh bashi da laifi, sharri ake masa bai san komai ba a wanke sunan shi daga ɓacin da ya yi" cikin martabawa da nuna rashin daɗin abin da duk ya faru I.G ya ce. "Aikinmu ne hakan, za muyi abin da ya dace muma ba zamu so sunan Sheikh ya lalace ba yana da girma da daraja a idanun ba" Mother gaba ɗaya haushin duk wasu jami'an tsaron take ji hakan yasa cikin sauri ta juya zuwa inda Abba Hakimi da Sheikh suke tsaye, idan ka gansu zaka ɗauka da gaske Hakimi shi ne ya haifi Sheikh sbd tsananin haibar dake maƙale a jikin ko wanne kusan duk halin Hakimi Sheikh ya kwashe shi tas. Kallonsu ta yi cike da son ko wanne wanda ke rinjayar zuciyarta ta ce "Thank you Abba Hakimi" murmushi kawai ya yi bai ce mata komai ba, tana ƙoƙarin sake magana ya yi saurin barin wajan zuwa cikin motar da Umar-khan ya buɗe masa baya. Tsaye Sheikh yana bin mahaifiyar tasa da kallo ganin tai shiru ya waro mata manyan Idanun shi yana son cewa wani abu amma ya ja bakinsa ya yi shiru a hankali ta ce "zaka bini ko Abban naka za kabi?" Bakinsa ya motsa yana rufe idanu tare da fara buga ƙafa yana riƙe jikinsa da kyau cikin In-ina ya ce "Zazzzza... zan zan zanje gida wajan fa... fa.. father ina soooo son ganinsa" haushi ne ya kama Mother ganin duk abin da ake Sheikh yana maƙale da son mahaifinsa. "Father baya gari, kaje wajan Hakimi ka huta da kyau gobe sai kazo mu tattauna, ina tunanin za a haƙura da zuwa Madina haka" girgiza mata kai ya yi bai ce komai ba ya juya ganin har lokacin Abba Hakimi na zaune bayan motar, yanzu zuwa shima ya shiga baya Ishaq-hakim ya jasu. daga nan Bar Zainab gidanta ta shige hakan yasa Umar-khan ɗaukan Mother a ɗaya daga cikin motocin Sheikh suka nufi gida, Saif-Wazir kuma ya tsaya domin magana da ƴan jarida. Suna tafe a hanya Sheikh na yiwa Abba Hakimi hira cikin nutsuwa duk da In-ina yake amma Hakimi na fahimtar komai da Sheikh ke faɗa, a duk maganganun Sheikh ba za kaji kalmar MACE ta fito daga bakinsa ba, balle har ya ware wata musamman yana magana a ganta, Murmushi kawai Hakimi yake Ubangiji ne shaidar son da ya kewa Sheikh a jinin jikinsa yake. A haka suka ƙarasa haɗaɗɗan gidan Abba Hakimi dake Dawaki roud, gida ne irin na sarauta mai kyan tsari da fasali ko'ina ma'aikata ne , motar na tsayawa Sheikh ya fito ƙwayar idanunsa na nuna gajiyar da yake ciki. Bai tsaya jiran Abba ba, kai tsaye ya nufi part ɗinsa wanda yake cikin gidan Abba Hakimin wanka ya yi da ruwa mai zafi yana gamawa ya fito ɗaure da babban towel idanunshi na janye wa barci na cin ƙarfinsa ya ɗauki wani tsadaddan lotion, Shea body butter ya shiga shafawa saman fatarsa a kasalance, Engage Cologne Spray ya fesa a fatarsa sbd ɗauke zafin da ya keji yana gamawa ya miƙe zuwa clothes ɗinsa ya ɗauki wani trousers mara nauyi ya saka ko riga bai saka ba, ya cilla mint bakinsa ya kwanta saman bed yana lulluɓe jikinsa da bargo, ganin rana ce ya sa ya kunna A.c tare da rufe idanunshi cike da fatan barci ya ɗauke shi. Washegari gari tun da Sheikh ya farka bai koma barci ba, har ya fita sallar Subhi sai da gari ya yi haske wajan 6:30 ya dawo gida jikinsa duk ciwo yake masa sbd rashin gym da bai ba, wanka ya ƙara yi ya shirya cikin Scabal wool suit white colour sai red ɗin necktie. Sai Diamond Rolex daya maƙala a hannunsa, yau a Yaa Lee ya fito ba a Sheikh ba, domin kusan siffa biyu gare shi, idan zashi bank shigar suit yake duk abin da ya danganci addini ajjiye shi yake a gefe amma yana zuciyar shi, idan kuma ya sanya Alkyabba da rawani yana matsayin Sheikh a wannan lokacin ne ba Yaa Lee ba. Wayarsa ya ɗauka jacket ɗin sa a hannu cikin nutsuwa ya fita zuwa main parlour. Ƙamshin ROJA shi ne ya fara kaiwa su Abba Hakimi ziraya yana zaune da jallabiya gefensa kuma Ishaq-hakim ne da Saif-Wazir shirya zasu shi wajan aiki, sai Momi A'isha tana zubawa Abba Hakimi Shayi mai zafi. "Mrng Yaa Lee" jinjina kai ya yi idanunshi akan Abba Hakimi ya furta. "B...bar bar barka da safi fifi fiya". "Ya ka kwana? da ciwon kan?" Rufe ido ya yi tare da buɗewa alamar "Allahamdulillah" Momi A'isha ta amsa gaisuwar Sheikh ɗin wacce ya yi mata ita cikin In-ina, tea ta haɗa masa mai zafi ta zuba 2spoon na honey ta juya kaɗan tare da bashi. Amsa ya yi a kame yake shan tea ɗin yana sauraran maganar Abba Hakimi da yake ce masa "komawa Madina ba yanzu ba, kada ya fara tunanin hakan" sanin ba zai iya ja da maganar Abba Hakimin ba yasa ya miƙe yana ajjiye cup ɗin hannunsa, Ishaq-hakim da Saif-Wazir suka miƙe tare da bin bayansa, wata farar mota ya shiga mai Sheikh no 5 yana shiga driver ya ja. Ishaq-hakim da Saif-Wazir kowa ya shiga motarsa suka nufi S.A.H BANK. tun kafin ya Ƙarasa cikin bank ɗin wanda ya kasance mallakinsa ma'aikatan bakin Sheikh Aliyu Haydar bank suka shiga mutuwarsu ƙwarai. miƙewa ake ana gaida shi hannu kawai yake ɗaga musu har ya shige wani baban office. Wunin ranar Sheik cikin duba files and Ducoments yake. 3:30 yana ƙoƙarin barin Office ɗin saƙon father ya sauka Wayarsa. Da fararen idanunsa yake bin message ɗin da kallo yana mamakin yanzu kuma kiran gaggawar mene?. Da wannan tunanin ya shiga mota Driver ya ja suka nufi unguwar su Sheikh. Tun a harabar gidan ya san akwai matsala domin kai tsaye idanunshi ya sauka akan motar Abba Hakimi data Yaya Halima sai ta Uncle Haroon. Ƙamshin turarensa ya bayyana zuwansa, Mother dake zaune saman Kujera yana kaɗa ƙafa ta kalle shi kafin ta ɗauke kai, Uncle Haroon ma kallon Sheikh ɗin ya yi, a kame ya ƙarasa kusa da Abba Hakimi ya zauna yana ɗauke idanunshi daga kan jama'ar daya rasa meeting ɗin me ake. "Tun da Allah ya kawo shi sai aji ta bakinsa, amma Sheikh ya shige lokacin da za a yi masa auren dole, a baya ba ai masa ba balle yanzu?" Yaya Halima ta furta cike da jin haushin father. Shi ma father da zuciyarsa ke kusa ya ce. "Bashi da amfani, domin ba zai faɗi abin da kowa ke buƙata ba, na daɗe da sanin cewa Aliyu shi ne ƙaddarata, shi da yake namiji wanda ya kamata ya tsaya kan dukiyata amma ya kasa hakan, duk mutanan da suke buƙatar contract daka gareni idan har suka ji yadda Aliyu ke banzar maganar shi suke contract In-inar Aliyu ta ja mini asara mai yawan gaske, don haka ni bashi da amfani a gareni" sai a yanzu suka fahimci rashin jituwar da babu tsakanin father da Aliyu cikin ladabi Abba Hakimi ya ce "Baka yarda Ubangiji ya ɗorawa Aliyu wannan larurar ba? kenan baka alfahari da Aliyun matsayin ɗa?" Cikin sauri Father ya ce "Aliyu bai taɓa yi mini rana ba, to akan me zan yi alfahari da shi? Idan yana so mu shirya dole ya daina wannan In-inar ko kuma ya yi aure cikin satin nan" "Aliyu akwai wacce ka ke so ne?" Sai a lokacin Sheikh ya kalli Uncle Haroon yana runtse idanunshi zufa na yanko masa a ƙoƙarin shi na ganin ya yi magana babu In-ina amma ina ba zai iya ba ƙaddarar shi ce hakan. Cikin fitar hayyaci yana rirriƙe jikinsa da kyau tare da buga ƙasa da hannun kujera ya ce "ba...ba ba bana son son kowa uncle.. ba ba bazan iyyyya zama dadda da mace ba" shiru duk sukai baƙin ciki ne kuma ya hana mother magana. Father ya ce "Ok good a Sbd haka ka shirya zama da Zahrah ƴar gidan babban aminina, cikin satin nan za a yi aurenku kai da Zahran babu fashi" miƙewa Mother ta yi cikin faɗa ta ce "Wallahi Aliyu kayi kaɗan ka saka Sheik ya auri wannan Yarinyar da ban amince da tarbiyyar ta ba, me Sheikh zai da ita? Yarinyar da take kusan sa'ar shi kaɗan ne babu ta girme shi ba? duk shekarun da Aliyu ya yi babu aure sai kuma ya ƙare wajan tsohuwa, ban amince ba kuma ban yarda ba, ka bawa Aliyu duk wacce kaga dama amma ban da Zahrah" murmushi father ya yi ya ce "Idan har ni ne uban Aliyu ba wani ba? Ya zama dole ya auri Zahrah idan kuma bani ne mahaifinsa ba sai ki bashi wacce kikai niyya Barrister Maryam" hawaye ya cika Idanun Mother ta ce "Oh yanzu kuma sheganta Aliyu zaka fara bayan zarafinsa da ka ke ci akan larurarsa?" Banza father ya yi mata. Uncle Haroon ya numfasa ya ce "Engineer Aliyu Wannan bai kamata ba, idan kana so Aliyu ya yi aure,Let him choose the woman he wants to marry himself, ka sassauta yanayin da ka keji game da Aliyun" Father ya ce "Abu ɗaya ne zai kawo Shira tsakanina da Aliyun shi ne auren shi da Zahrah idan bai amince ba yaje na zare hannuna daga Lamarinsa kuma ya zare sunana a matsayin Uba" Dakawa Father tsawa Uncle Haroon yai ya ce "Wai Aliyu wanne irin banzar magana ce kake haka? Ni da kai na zan iya samawa Aliyu matar aure, ka daina ganin kai ne ubansa ni ma uba ne a wajansa, ga kuma babban Uba hakimi duk mun isa mu tsayawa Aliyu, ka daɗe baka cire hannunka ba, kuma wallahi ka sake na rabaka da Aliyu ka rabu dashi kenan har abada" Girgiza kai Abba Hakimi ya yi ya ce "Ba za a yi haka ba Haroon, haƙƙin Aliyu ne samawa Sheikh matar aure a barshi ya aura masa Zahrah Allah ya sa albarka,kada ka damu da Sheikh nasan zai amince" miƙewa Sheikh ya yi cikin zafin e da kutuwar zuciya irin ta kurmaye Aliyu ya fara faɗa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, idanunshi gaba ɗaya ya rufe Innar ta hana ya ji abin da yake faɗa, idan kuma ya fara faɗa babu wanda ya isa ya tsayar da shi daga faɗan da yake. Saukar wani zazzafan mari da Sheikh ya ji a saman kamilalliyar fuskarsa ya sanya ya yi saurin rufe idanunsa Father ya nuna Sheikh ya ce "Ni kake ɗagawa murya Aliyu? Ni sannu kuturu uban ƴan zuciya daman zuciyar taka nake buƙata auranka da Zahraan kuma babu fashi" ƙwafa Sheikh ya yi domin baya iya riƙe kansa idan zuciyar ta motsa uban kowa sai ya san babu lafiya a gidan. Wuyan rigar Father ya riƙe da kyau zufa na mamaye dukkan goshinsa a wannan karan bai buga ƙafarsa ba amma tamkar zai ɓalla wuyan rigar haka ya riƙeta da kyau cikin huci da faɗa ya ce "heee na... na na amince amma ka ka ka tabbatar mutuniyar kirki ce" Father da yaji shaƙar Sheikh ɗin har ransa ya ce "Idan kuma ba ita bace ba fa Aliyu?" Sheikh ya girgiza kai idanunshi ya yi jajur ya ce "Haaaaa ɗakkkkkk" yana faɗin haka ya saki Father tare da barin gidan baki ɗaya... We're still in free pages🫰🏽 Littafi nan na kuɗi ne, a koda yaushe zan iya datse free pages. Salo na musamman biya 500 ta Wannan acct ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616.*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* 12.... Bayansa suka bi da kallo ganin yadda ya fice a fusace. Father yaja numfashin wahalar da ƙyar kafin ya ce "Irin wannan ban zan yaron za a bawa mace mai ƙarancin shekaru? Ai ko Zahrah sai dai ta yi haƙuri da shi" Mother zatai magana Yaya Halima ta hanata ta hanyar danne hannunta tare da girgiza mata kai. Ganin ba wanda ya sake cewa father komai ya juya zuwa upstairs. Uncle Haroon ya kalli Abba Hakimi ya ce "Afuwa ranka ya daɗe kayi haƙuri da halin Engineer Insha Allah komai za yi daidai, Jadda ba zata barshi ya aikata hakan ba, I'll talk to him" murmushi Abba Hakimi yai yana faɗin "Me ne na haƙuri Haroon? Sheikh ɗan sa ne ba wanda zai yi jayaya da hukuncin da uba ya yi akan ɗan sa, idan hakan zai sa shi farin ciki da amincewa da Sheikh a barshi ya yi" "She's 32 years old Hakimi, tayi wa Sheikh girma ba zata iya yi masa biyayya ba, babu tarbiyya a wajan yarinyar nan na jima da saninta" Mother ta faɗa cikin damuwa. Yaya Halima ta ce "Barrister ke uwa ce a kullum, addu'a kawai za kibi Sheikh da shi, addu'ar ki zatai ta zagaya rayuwarsa sai kiga albarkacin haka Ubangiji ya daidaita tsakani kuma ya shirya yarinyar, ba a jayaya a cikin lamarin aure" Uncle Haroon ya ce "Ki bar Barrister ta faɗi abin da yake ranta, idan akwai wanda yafi sanin halin Sheikh da raninsa to ita ce mai biye mata shi ne Hakimi, babu kyautatuwar a zuwa Engineer idanu yana abin da ya ga dama, idan baya ra'ayin Sheikh a rayuwarsa sai muyi yarjejeniya mun ashe sa mu suke sunan shi daga jikin na Aliyun" miƙewa tsaye Abba Hakimi ya yi yana gyara zaman alkyabbar jikinsa cike da nutsuwa ya ce. "Wannan shawara ta Haroon ba dani ba, ban taɓa jin inda aka raba uba da ɗana ba, lokaci ku barshi ya bayyana mana komai" yana faɗin hakan ya yi waje yana dogara sanda. Uncle Haroon ma ya miƙe tare da yi musu sallama. Bayan tafiyar su Yaya Halima ta kalli Mother ta ce "Barrister ki nutsu kada kiyi jayaya da hukuncin da uban yaron nan ya zartar ni ina ji ajikina akwai wani abu ɓoyayye a ƙasan auren mu amince da hakan" ƙwafa kawai Mother ta yi tana girgiza ƙafa kafin ta kalli Yaya Halima ta ce "Kin san Allah Yaya ko zan amince da auren nan sai dai Sheikh ya auri mata biyu?" Yaya Halima ta waro idanu sosai ta jima tana kallon Mother kafin ta numfasa ta ce "Tab, mata ɗaya ya zata ƙare wajan Sheikh bare mata biyu? Ai Wallahi mantawa zai yi da zamansu a gidan" "Ai ko zai yi shekara ɗaya bai kalli ko wacce ba, Wallahi sai dai ya auri mata biyu" Yaya Halima ta ce "Naji zaɓin Uba, wace kuma zaɓin uwa?" "Bani da zaɓi amma duk wacce Allah ya nufa data kwanta mini ko ƴar gidan wace zan saka Hakimi ya ɗaura musu aure" girgiza kai kawai Yaya Halima tai tana faɗin "Wata drama ɗin abin dry a gidan Engineer da Barrister a bani abinci naci ni dai" Mother ta miƙe tana kiran sunan Maimoon. Fitowa tayi daga part ɗinsu jikinta sanye da duguwar riga ta rusuna ta ce "Ina yini Mama?" Yaya Halima ta ce "Lafiya lou Maimoon ya karatu? Kwana biyu Mother ta hanaki zuwa ko?" Maimoon ta juya ta kalli Mother wacce ta ɗauke kai tamkar bata jin abin da suke cewa ta ce "A'a Mama, karatu ne ya yi zafi amma muna exam zan zo" "To Allah ya taimaka, a kawo mini abinci" murmushi Maimoon tayi ta nufi kitchen. Yaya Halima ta kalli Mother tana mamakin zafin zuciyar ƙanwar ta ta. Arabian Mandi rice wacce ta sha kayan haɗi sai ƙamshi take Maimoon ya zubu a plate tare da haɗin salad da ya sha bama da egg with some of vegetables. "Ki sakko muci abinci Maryam" Mother ta ɗauke tana faɗin "Anya? ci kawai Yaya bana jin zan iya ci" murmushi kawai Yaya Halima tai tana faɗin "Allah ya kyauta komai ya yi zafi maganinsa Allah" Yana tsaye gaban madubi banda huci babu abin da yake maganganun father nayi masa amsa kuuwa a kunnuwansa "Bashi da amfani, bai taɓa yi mini rana ba, ya yi mini asarar contract ɗina" hannu ɗaya ya sanya ya dafe kansa dake masa ciwo sosai, ɗaya hannun kuma ya rufe kunnansa a zatonsa hakan zai taimaka wajan rage tuna maganar mahaifin nasa. Ɗago jajayen idanunsa ya yi ya tsurawa kansa ido ta cikin madubin. A wannan karan dole ya nunawa father shi ma namiji ne yana shiru ne sbd bai damu da duniya da abin da ke cikinta ba. Juyawa ya yi zuwa Library ɗinsa dake gidan Hakimi. Zama ya yi saman kujera cikin sauri ya duba dukkan mayan kadarorinsa kama daga kan filaye, gidaje, ɓangaren Library na karatun addinin dana kimiyya ya buɗe, S.A.H bank duk yana fahimtar dukiyar tasa har ya kasa shi kansa bai yi tunanin abin da ya mallaka ya kai girman hakan ba, a haka kuma bai haɗa dana wajan Mother ba wanda suke mallakinsa. Tunani ya fara tunda yana da bank a kano me zai hana ya buɗe S.A.H BANK a sauran jahohin da suke Nigeria? Da kuma kamfanin sarrafa shinkafa ƴar hausa mai kyau wacce za taiwa talakawa sauƙin siya kan fara shi mai sauƙi?. Da wannan tunanin ya yi na'am da zuciyarsa cikin nutsuwa ya fita daga Library ɗin ya koma haɗaɗɗan bedroom ɗin nasa, kai tsaye toilet ya shige tare da sakarwa kansa shower yana sauke numfashi a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar yama mance da batun aure baki ɗaya. Domin daman shi bai dame shi ba indai macace da kanta zata gudu ta ce bata son shi domin ba zata samu abin da take buƙata ba daga gare shi. Fitowa ya yi yana ƙamshin shower gel Shea body butter ya shafa jikinsa ko body spray bai fesa ba ya cilla mint bakinsa tare da kwanciya saman bed ya rufe idanunsa. Umar-khan ne ya shigo cikin parlourn Abba Hakimi bakinsa ɗauke da sallama. A hankali Abba Hakimi ya ajjiye azkar ɗin hannunsa wanda yake na yamma tare da duban Umar-khan cikin kamala da kamewa ya ce. "Umar-khan yaya dai?" Shafa kai ya yi yana tare da faɗin. "Abba Hakimi daman Mother ta ce ko Sheikh yana nan? Gaba ɗaya baya can gida" murmushi mai laushi Abba Hakimi yai yana zame idanunsa daga kan Umar-khan ɗin "Aliyu ai ba yaro bane?" Abba Hakimi ya faɗa a gajarce Umar-khan ya miƙe ba tare daya samu cikakkiyar amsa daga bakin Abban Sheikh ɗin ba ya ce "Ni ma zan je gida, sai da safe Abba Hakimi" yana buɗe azkar ɗin ya numfasa kaɗan cikin sakin fuska ya ce "A gaida Abdulrashid" "Zaiji sosai" Umar-khan ya amsa wa Abba Hakimi yana barin gidan baki ɗaya tare da tunanin inda Sheikh ɗin ya yi domin yana tsoro idan zuciyar ta motsa kowa sai yaji babu daɗi. Momi A'isha ce ta shigo ɗauke da tray ɗin abinci zama tayi bayan ta ajjiye ta ce "Ina ta mamakin abin da ya sanya mahaifin Sheikh ke aikata haka kamar wani mara ilimi, kuma ya dace ace ka saka baki ko auren ya keso Sheikh ya yi sai ka zaɓa masa ƴar mutunci, kaga hankalin Barrister bai kwanta da zaɓin Engineer ba" gaba ɗaya Abba Hakimi ya tattara nutsuwarsa kafin ya ce "Ku dai mata yawanci tunaninku ɗaya, bani da ikon ture umarnin uwa ga ɗan shi,kada ki manta ni uban rana ne kuma mariƙi, I don't have the courage to deny the Engineer what he wants" "Gaskiya dai, ni ina tunanin ko sbd Sheikh bashi da lafiyar yin magana cikin jama'a ya sanya Engineer ke yi masa haka? Kuma yana ganin He is the only male among his children, shi ne ya kamata ya tsaya kan harkokinsa na yau da gobe ya ɗauki buri ya saka akan Sheikh ɗin?" Abba Hakimi ya amshi fruits ɗin data gama yanka masa kafin ya kalleta da kyau ya ce "Baki ke aiki ko ƙwaƙwalwa? Babu wani abu da Sheikh ba zai iya ba, In-ina kuma Ubangiji ya ɗora masa muna fata a koda yaushe ta zama sauƙi a gare shi" "haka ne Allah ya bashi lafiya, anjima zani gidan Barrister ɗin" Abba Hakimi ya ce "Ki yi zamanki" ta kalle shi ta ce "Amma me ya sa?" Shiru ya yi mata tasan ba zai bada amsa ba, kuma tunda ya ce haka yana nufin hakan har ransa. A can commission Quarter's dake cikin garin Yola/ jimeta a hankali take driving saman makeken kwaltar da zai sadata har zuwa gida, numfashi ta sauke a karo na ba adadin tana kallon titi kunnanta kuma ma sauraran abin da Surayyerh ke faɗa tsaki ta ja ta ce "You bother me with noise wlh Surayyerh koda yaushe problems ɗinki da mahaifiyarki baya ƙare wa?" Surayyerh ke ta ce "A sbd ba ke bace ko? Gaba ɗaya ta takura ni wani lokacin gani nake kamar ba ita ta haifan ba" da sauri Zahrah ta juya ta kalli Surayyerh ta ce "Ashe daƙiƙiyya ce ke? Whatever is your problems ki barni da tawa matsalar" dry sosai Surayyerh tayi tana tafa hannu ta ce "Oh! Sorry ashe fa ciki yaƙi zubewa yanzu dole ki amincewa Deen kuyi aure" Zahrah stopped Surayyerh from what she was saying ta ce "And who told you cikin Deen ne? Ni kai na ban zan cikin waye ba, ban damu kuma dana sani ba kawai na zubar da shi ba aure a tsarina a yanzu dai" Surayyerh ta gyara zama sosai ta ce "Kin san Allah a yanzu babu abin da nake so sama da aure, sai yanzu na fahimci karatun bokon nan is nothing wani abu ne wanda kana cikin gidan mijinka ma zaka iya yinsa" Zahrah bata ce komai ba tunaninta yana can yana da tabi cikin jikinta ya zube ba tare da Mimi ta lura da shi ba. A haka suka ƙarasa gida gatekeeper ya buɗe musu. Sosai tai mamakin ganin motocin Dady yaushe ya dawo bata da labari? Dawowar gaggawa?. Fitowa tayi hannunta riƙe da L.G bag daman babu mayafi jikinta kayan sun kama jikinta sosai, jerawa sukai ita da Surayyerh zuwa cikin gidan. Dady da Mimi ta bi da kallo ganin suna magana a hankali, Dady yai murmushi ya ce "Finally She's back zo nan Zonan Zahrah" ya miƙa mata hannunsa ƙara sawa tayi ta zauna kusa dashi tana rungume shi ta ce "Wlcm Dady" kallonta ya yi da kyau ya ce "Zahrah magana za mu yi mai Muhimmanci" ta gyara zama ta ce "All ears Dad" ya ce "Kin san aminina Engineer Aliyu?" Ta ɗaga ta ce "I think I knw him Dad mene ya faru?" Ya ce "Kin san wancan dake jikin photon?" Juyawa tayi ta tsurawa photon Sheikh Aliyu haydar Aliyu dake maƙale jikin bangon parlournsu zuciyarta ta ɗan buga ta girgiza kai ta ce "Ban shi ba Dad, amma na san yana da muhimmanci tunda aka photon sa a gidanmu" ya jinjina kai ya ce "Yana da muhimmanci a gareni da rayuwata baki ɗaya, Zahrah wannan da kike gani akansa duka wasu burukana suke, ina son na haɗaku aure da Sheikh Aliyu haydar Aliyu cikin satin nan" zabura tayi ta miƙe tana zaro idanunta waje zuciyarta na bugawa sosai ta kasa magana baki ɗaya. Mimi ta ce "Daman nasan Zahrah ba zata amince ba, domin ko Tafsir ɗin ta tsana" Dady ya ce "Ya zama dole ta amince sbd karayar arziƙin dake shirin tunkaro mu ba tare da mun shirya ba, Zahrah ki yarda ki auri Sheikh zaki farin ciki namiji ko a maza samun irinsa zai wahala kiyi mini wannan alfarmar" Ajjiyar zuciya ta sauke ta ce "Dady na amince da buƙatar, amma idan har daga ni ba zai sake auren ko wacce mace ba ina nufin babu kishiya... Na kusa gama free pages. IDAN BA KE it's 500 gaba ɗaya book 1,2 har ƙarshe. Via 6850917335 Na'ima Shuraihu Sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616 ƴan niger suyi mini magana na faɗa musu yadda zasu biya. DESTINY TRUE LOVE ROMANCE TRUST SARAUTAR MARUBUTA*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv sarauta_* 13..... Mimi ta ce "baki son kishiya kuma? Ina ruwanki da wata kishiya?" Dady ya ɗaga hannu yana murmushi ya ce "Ni ma bana fatan Sheikh Aliyu haydar Aliyu ya yi wa Zahrah kishiya,domin za a rage mini abin da nake tunani" cikin rashin fahimta Mimi ta ce "kamarya Alhaji?" "Ba sai kinji ba, ki shirya aurar da yarinyar ki cikin satin nan" ya faɗa yana miƙewa tsaye cikin jin daɗin amincewar da Zahrah ta yi. Jikinta na rawa ta haura upstairs tana zuwa ɗakinta ta samu Surayyerh ciki daman bata tsaya a parlour ba sama ya shige ɗakin Zahran. "Wayyo daɗi kashe ni, na samu mijin da nake fata da burin samu cikin sauƙi" ta faɗa gado tana sakin ƙarar farin ciki. Surayyerh ta ce "Pardon? Ban fahimta?" Miƙewa Zahrah ta yi ta ce "C'mon yanzu Dady yake sanar mini za a haɗa aurena da Sheikh Aliyu" mamaki ya hana Surayyerh rufe baki sai da Zahrah ta saka hannu ta rufe mata baki, Surayyerh ta samu damar faɗin "Are you serious Zahrah? Gaskiya am happy for you daman kina son Sheikh?" Tayi fari da idanu irin na gogaggun matan nan ta ce "Fiye da yadda bakya zato, soyayyar Sheikh ta hanani aure, abin mamaki ban taɓa ganin shi a zahiri ba sai dai photo a wajan Dady ko idan yana tafsir, nasan shi ma bai sanni ba" "Yanzu duk ba Wannan ba, ya ya zaki da cikin jikin ki tunda likita ya tabbatar ba zai zube ba? Gashi kuma aure ya zo babu shiri?" Zahrah ta ce "Kada ki damu da cikin zanyi auren, ko da haihuwa nayi sai nace bakwaini ne ai anayi" Surayyerh ta jinjina makircin Zahrah amma ta share ta ce "Idan kin ɓoye cikin ya zaki idan ya san ke ba budurwa ce ba?" "Oh! My God what exactly wrong with you Surayyerh ki ke neman yi mini baki? Ai ba zai sani bama ɗinki zanje ayi mini" Surayyerh ta ce "Uhm shi fa babban Malami ne You never lie to him Malamai sun san komai infact sun fi kowa iya soyayya kiyi tunani ki nemi mafita" share zan can Surayyerh Zahrah tayi a yanzu yadda za taga Sheikh Aliyu haydar Aliyu a zahiri shi ne burinta. Da magrib Surayyerh ta tafi gida akan gobe zata dawo domin fara shirye-shiryen haɗa events. Tun a bakin parlour Surayyerh ta san akwai matsala tana shiga Umma ta kalleta sosai ta ce "Daga ina kike?" Turo baki tayi tana musmus da bakinta kamar mai zagi ta ce "Wai ke Umma zargina kike ne? Haba don Allah na fara gajiya ciki kike tsoro ko mene?" Umma mamaki ya kasheta a tsaye ta ce "Surayyerh ni mahaifiyar ki kike faɗawa haka sbd ina kare kiwon da Ubangiji ya bani?" "Wani irin kiwo kamar wata dabba Umma? Kawai takurawar taki ce ta yi yawa, ki barni da abin da yake damuna gashi duk iskanci Zahrah rana tsaka ta samu miji na kece raini wanda ba zan taɓa samun irinsa ba" jirin dake neman yadda Umma yasa ta nemi saman kujera ta zauna. Ubangiji ya gani kuma shi ne shaida tayi iya yinta ta fara gajiya tana ganin gaba gaba Surayyerh dokanta zatai ita kam wannan karatun bokon bai mata rana ba. Hawayen daya cika idanunta ta mayar sbd babu dacewar yiwa Surayyerh kuka sai ta sake lalacewa. Surayyerh ta shiga zirga-zirga a bedroom ɗinta tunani ya yi mata yawa abin da bata tsammata ba a yanzu ya kawo mata farmaki. A firgice Halisa Danejo Rome ya farka daga nauyayyen barcin daya ɗauke ta mai cike da mafarkai wanda bata taɓa yin kamarsa ba, me ya sa Balaraban nan ke zuwar mata cikin barci ne? Amma gaba ɗaya yadda ta gansa a daji ya bambanta a farki, na cikin mafarkinta yafi kyau da kamala nutsuwarsa da kamewar shi tafi bayyana, kwarjinin dana mafarkinta yake dashi na zahiri baya da shi, duk mutum ɗaya ne? Ta tambayi kanta a cikin zuciyarta shiru tayi cike da damuwa domin ta fara gajiya da mafarkinsa. Motsin da taji kusa da ita ya sanya ta juya idanuna ya sauka akan Dada wacce take sanƙame numfashi na fita da ƙurar ciwo yaƙi ci yaƙi cinyewa. "Na lalashe na shiga uku Dada jikin ne? Sannu Dadata zaki samu lafiya" ta faɗa hawaye na wanke mata fuska gaba ɗaya ta ƙara zama wata kala damuwar ciwon Dada ya sata gaba, gashi yanzu Hamma Yabi baya yini gida sbd neman kuɗin zuwa asibitin burni. Jigum tayi tana kallon yadda kumfa ke fita ta bakin Dadar amma bata san me zatai mata ba, bata da wanda zata kira a cikin bukkar. Shatu dake rakuɓe ta kalli Danejo ta ce "Dada mutuwa zatai ko?" Girgiza kai Danejo tayi ta ce "Waya faɗa miki? Babu inda Dada zata yafi ta barmu aradu muna tare da ita" wata ƙara da Dada tayi tana sanƙamewa ya sanya Shatu fashewa da kuka, da gudu kuma Halisa Danejo Rome tayi waje. Karo sukai da Hamma Yabi wando ya shigo hannunsa riƙe da ƙwayar magani daya amsu, ya riƙe Danejo da kyau wacce take ƙoƙarin fita daga hayyacinta. "Hande en boni, Danejo lalashewa ya sameka me ya samu Dada?" Gaba ɗaya ta rikice sai ƙanƙame hannun Hamma Yabi take ganin bata hayyacinta ya jata ciki yana zuwa ya kwantar da ita yana rufe mata fuska shiru tayi har lokacin cikinta bai bar rawa ba, domin gani take kamar Dada tabarta kenan ta mutu ta tafi. Ya girgiza yana komawa wajan Dada tare da ɗagata ya bata maganinsu ya shafa mata zuwa fuska da wuya Ajjiyar zuciya ta sauke tana buɗe idanunta, hannun Hamma Yabi ta kama da kyau tana son tambayar shi mene ya samu Halisarta amma ta kasa, a haka barci ya ɗauke ta cikin mayuyacin hali. Washegari kamar kullum Danejo ta tatsi nono a ƙwayar, tun kafin gari ya yi haske ta fita kiwo da shanunsu, sai da ta ɗauki awa uku ta dawo cikin sauri tana tafe tana kaɗa naggen bayan ta ɗaure su ko abinci bata ci ba ta nufi cikin burni kawai tsaye zuwa Abti America. Yadda taje haka ta dawo babu wanda ya sanya kuɗi ya sai nonon balle su samu na abinci, a wahale ta shiga Rugar idanunta na rufewa ta kafa baki a nonon wata nagge ta shiga sha sai da cikinta ya ɗago taja Ajjiyar zuciya tare da nufar bukkarsu. Sheikh Aliyu haydar na kwance saman makaken gadonsa idanunsa akan screen ɗin laptop ɗinsa yana sauraran abin da ake faɗa ta cikin laptop ɗin. Can dai ya ja tsaki ya girgiza kai, speaking calmly ya ce "Ni ni niii da dddddd dama zaka zaka zaka sauya labarin nan naka Khalil, in anyway banga amm am am amfaninsa ba..." Dry sosai wanda aka kira da Khalil ya yi ganin yadda Sheikh ke runtse idanunsa yana buga kai duk dan ya kare kansa "To ai ni yana da amfani a wajena tun da abin da ya shafi Sheikh Aliyu haydar Aliyu ai shafi Khalil Ahmad Sarki, look Sheikh don Allah cire son zuciya ka faɗa mini mai mata sukai maka? Let me know" Sheikh ya shafa lallausan gashin kansa wanda yake kwance gwanin sha'awa, cikin son cire damuwar father a ransa ya dage yake hira da Khalil duk da yana shan wahalar magana ya jima bai magana mai tsayin haka ba, idanunsa lumshe ya ce "kakaka....ka kasan me?" Sheikh ya faɗa yana buga kansa jikin pillow yana riƙe ɗaya hannunsa sbd In-ina. Kallonsa kawai Khalil yake yana jiran jin abin da Sheikh ɗin zai faɗa, a wahale cikin In-ina wacce yake son ya saba magana da ita ya mirgina kaɗan yana riƙe kansa da hannu bibbiyu ya ce "man ta ta manta kawai, ya ya yaushe za za kazo?" Murmushi Khalil ya yi cike da ƙaunar Sheikh Aliyu haydar ya ce "Zamu zo da mai martaba wajan Hakimi, I think I will spend my two weeks vacation with you in Kano" jinjina kai kawai Sheikh ya yi ba tare da ya ce komai ba. "You are just afraid of women because you see yourself as a Sheikh, women are the happiness of a man, try and see" Girgiza kai kawai Sheikh ya yi ba tare da ya ce komai ba ya kashe vedio call ɗin. Umar-khan ne ke driving a hankali idanunsa akan titi amma hankalinsu na kan Sheikh dake manyan mota cikin wata dakakkiyar shadda fara tas ya ɗora golden ɗin Alkyabba sai rawanin daya ƙarawa fuskarsa kyau da haiba ya yi wani irin kyau kamar Balarabe ƙamshin Roja ya cika motar sosai. Yana ki shingiɗe a bayan motar tunani yadda zai sauya ya koma kamar yadda father yake buƙata, a haka suka ƙarasa Wani Restaurant mai kyau da tsari mara hayaniya, Umar-khan ya yi parking kasancewar fitar sirri ce yasa babu wasu masu take masa baya, cikin sauri ya buɗe Sheikh mota a nutse ya fito yana gyara zaman alkyabbar jikinsa tare da goya hannunsa a baya cikin kamala ya yi gaba Umar-khan na biye da shi zuwa cikin Restaurant ɗin. Zama Sheikh ya yi tare da kallon mutanan da zasu tattauna dasu, bayan sun gaida Sheikh ya ɗaga musu kai suka shiga nuna masa zanan bank ɗin daya buƙata na reshe uku, kaduna, Abuja, da Lagos. Baya cewa komai sai da Umar-khan suke tattaunawa gani ya yi zanan bai masa ba, domin babban bank yake so wanda ba a taɓa yin mai girman sa ba. Hakan ya sa ya amshi carbon paper da pen a nutse ya zana yadda yake so, zanan ya bawa ma'aikatan mamaki abin da basu sani ba, kaɗan kenan daga cikin baiwar Sheikh duk abin da ya sanya ransa yana gwadawa yake yi daidai. Sallama sukai bayan anyi musu transfer miliyoyin kuɗi domin fara aiki gadan-gadan. Ɓangaren Kamfanin sarrafa shinkafa ma tuni aiki ya yi nisa, ya yi ordern injina masu kyau daga Chaina. A gajiye ya dawo gida idanunsa na rufewa kansa ya sakarwa shower lokacin 1:30 ya saba barci tsakanin azahar zuwa sallar asr, fresh milk ya tsiyaya a cup tare da zuba honey ya sha kaɗan ya wanke baki, yana kwanciya barci ya ɗauke shi daman ya riga daya saba. Washegari ya kama weekend Sheikh bai san meke faruwa ba, sai daya farka yaji labarin tun 7 su Uncle Haroon da Abba Hakimi tare da Baffansa suka nufi garin Yola nema masa aure. Ko ajikinsa bai ɗauki auren matsayin wani abu, shi dai ya san ko farcen mace bai taɓa sha'awa ba balle ya birgensa. Da yamma su Abba Hakimi suka dawo cikin jin daɗin an basu auren Zahrah nan da sati mai kamawa za a ɗaura aure. Kasancewar yau Friday ne ya sanya Sheikh ya shirya cikin wata bugaggiyar shadda fara tas da ita mai ɗinki jamper da babbar riga, bai sanya hula ba sai hirami daya saka a saman sumar kansa ya ɗauki zagayayyen abun nan na larabawa Black colour ya ɗora saman hiramin, shekarunsa suka bayyana a jikinsa, domin kowa ya kalli Sheikh Aliyu haydar ya san ba yaro bane, girma ya fara hawa jikinsa babu mamaki ya yi aure a same shi da yara biyar haka, shekaru 34 ba wasa bane ba. Kai tsaye babban masallacin juma'a ya nufa sai da ya yi huɗu ba sosai mai ratsa jiki akan tsaida sallah a lokacin ta, tunda duk In-inar Sheikh inda karatu zai yi yana farawa ake nemanta a rasa. Bayan idar da Sallah ya nufi zaga gidan marayu kamar yadda ya saɓa idan yana ƙasa, a hankali yake tafiya hannunsa goye a bayansa kansa a ƙasa fitowar su kenan daga gidan marayu zasu shiga mota yaje gida wajan Mother, kamar daga sama wata budurwa kyakkyawa ajin farko ta tsaya a gabansu da sauri Umar-khan da Saif-wazir suka sha gabanta tun kafin securities su ƙarasu bakinta na rawa ta ce "Don Allah ku barni nayi magana da shi, na jima ina son haɗuwa da shi" Umar-khan ya daka mata tsawa ya ce "Baya buƙatar ganin kowa, kuma a mu'amalar shi baya yi da mata ki nemi wani wajan" A nutse Sheikh ya dakata tare da juyawa idanunsa zuwa inda budurwar take, waro fararen idanunsa waje ya yi yana mamakin abin da ya haɗa shi da bayin Allan nan da suke bibiyar shi. Murmushi mai laushi ya yi ba tare daya bari kowa ya gansa ba, yana mai ƙarewar budurwar kallo musamman ƙafarta. "Ka taimaka mini daga yanzu ba zan sake zuwa inda yake ba" Umar-khan ya yi mata wani ban zan kallo ya ce "Ke ko mayya ce ke baki isa kije inda Sheikh yake ba, kunne masu ƙullawa mutane sharri ko?" Sosai taji zafin maganar Umar-khan sai kawai ta juya kamar zata kifa sbd sauri. Tana barin wajan Umar-khan ya dafe kansa Saif-wazir ya ce "Are you okay?" Ya ce "Kai na ke ciwo, zazzaɓi nake ji" Umar-khan ya faɗa bakinsa na rawa kafin kace wani abu wani zazzafan zazzaɓi ya rufe Umar-khan. Girgiza kai kawai Sheikh ya yi domin ya san za a rina waya aiki Khan musayar yawo da aljani?. Da sauri Hamma Yabi ya shigo bukkarsu hannunsu ɗauke da kuɗi ya kalli Danejo wacce take sumar kanta ya ce "shai Alhmd kuɗi shun samu gobe zan kai Dada asibitin burni" murmushi Danejo tayi wanda ya ƙara fidda kyanta na fili ta ce "Kai Allah abin gdy Dadata zata samu lafiya yau ba zan barci ba sbd farin ciki aradu" Hamma Yabi ya kalli Dada dake kwance kamar haka cikin farin ciki ya ce "Insha Allah, da sassafe sai burni" fita ya yi farin ciki ya cika zuciyar Danejo Dada zata tashi su koma yadda suke rayuwa a baya. Hamma yabi bai dawo ba sai dare riƙe da ƙullin buduri da ƙosai mai zafi wanda ake a can wajan gari. Sai dai ko zama bai ba suka fara jiyo harbi ta ko wanne waje alamar ƴan fashi ne suka shigo cikin Rugar Rome. "Bone Hamma harbi harbi....," Bata ƙarasa faɗa ba suka ji an shigo bukkarsu wani mutum mai riƙe da bindiga ya kalli Hamma Yabi yana faɗin "Kuɗi,kawo kuɗi bamu da lokaci" jikin Hamma Yabi na rawa ya ce "Ba kuɗi bamu da shi" mutumin ya yi wata dry sosai ya ce "Babu? idan na bincika na samu duk hukuncin dana ɗauka akan kai ka sani" yana faɗin hakan ya fara bincike bukkar daga can waje harbi ake ta ko wanne sashe, cikin rashin sa a mutumin yaga kuɗin da Hamma Yabi zai kai Dada asibiti "Aradun Allah kuɗin asibiti ne, kayi mini ka taimaka Dada zamu bawa lafiya.....," Harbin da akaiwa Hamma Yabi a ciki ya sanya ya fasa ƙara tare da faɗuwa ƙasa ihu Danejo ta fasa ganin yadda jini ke zuba a jikin Hamma Yabi tana ƙoƙarin zuwa inda yake mutumin ya ƙara sakarwa Hamma harbi a tsakiyar kansa...... Wannan littafin na kuɗi zaka samu book 1, 2 akan ₦500 daga farkon labarin har ƙarshe ka tura ta wannan account ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616.*🌈 IDAN BA KE 🌈* *_Arewabooks@Nimcyluv_* 14...... Cikin ƙaramin lokaci ƴan Rugar Rome suka shiga cikin tashin hankali musamman wajan su Danejo. Ko kuka ta kasa ta kafe gawar Hamma Yabi da kallo sai Ajjiyar zuciya take, shatu na gefe ta ƙanƙame jikin Dada wacce ke sanƙame bata san meke faruwa ba sbd halin da take ciki. Bata taɓa ganin anyi kisan kai a gabanta ba, yaushe gashi an kashe mata yaya wanda ke kula dasu shi kaɗai ya rage musu. Halisa Danejo Rome ta shiga halin firgici ita kaɗai tai ta razana har lokacin idanunta bai motsa daka kan gawar Hamma Yabi ba a haka Asuba ta risketa. Sarkin ruga da Giɗaɗo ne suka shigo bukkarsu Danejo ba neman iso domin basu damu da cewa Dada matar da za a nemi aminci a wajen ta bace. "Allahu Akbar Allahu ya jiƙan Yabi shai abu bai kyau ba sam" Sarkin ruga ya girgiza kai ya ce "Allah sharki aradu harbi har biyu dole ya mutu" da sauri Danejo ta miƙe jikinta na rawa ta kama hannun Giɗaɗo ta ce "Da gaske Hamma Yabi mutuwa ya yi? Da gaske ba zan sake ganin Hamma ba?" Ta faɗa cikin rauwanin muryar kana ganinta kasan damuwa ta jima da kama zuciyarta ta samu waje ta zauna. "Ya mutu mana kamar yadda Baffanku ya mutu ba zai dawo ba" ƙurr ta kafe Giɗaɗo da idanu kafin taja numfashi mai tsayi sai kuma ta sulale a wajan ta faɗi babu numfashi. A hankali take buɗe idanunta wanda sukai mata nauyi, hannunta ta kai tare da dafa kanta wanda yake mata ciwo sbd barcin data daɗe ta nayi. "Sannu kin farka Danejo?" Shatu ta furta cikin murnar ganin Danejon na motsi bayan suman da tayi. Danejo ta juya tana kallon Shatu kafin a hankali ta buɗe baki ta ce "Ina Hamma Yabi? Ya tafi da Dada asibitin burni?" Shatu tayi saurin faɗin "Hamma Yabi ya mutu ai kuma har an rufe shi a ƙasa" zuciyar Danejo ta buga da ƙarfi tana runtse idanunta sosai tsoro da fargabar makamar rayuwarsu ta dirar mata a zuciya, yaya za tayi da Dada? Ina zata samu kuɗin asibiti ko shanu zata siyar? Mai Hamma Yabi ya yiwa wannan mutunan da shi kaɗai kawai suka kashe cikin Rugar Rome?. Juyawa tayi ta sake kallon Dada wacce kawo yanzu ko motsi ba tayi ruwa ma idan aka bata ta gefen baki yake zubewa, hawayen da take maƙalewa suka sakko daga cikin idanunta Shatu wacce ke shirin yin kuka ta ce "Kuka ki ke Danejo? Me akai miki ba ga Dada ba muna tare da ita?" Danejo ta goge idanunta da kyau ta ce "Ba kuka nake ba, ki zauna wajan Dada bari naje wajan sarkin ruga na dawo" miƙewa tayi jikinta sanye da fararen kaya na Fulani sumar kanta ta naɗeta da wani zare mai ɗauke da kuran duwatsu masu kyau. Kanta a ƙasa take tafiya cikin sanyin jiki kamar ko yaushe a haka ta ƙarasa bukkar su Sarkin ruga ta tsaya daga waje tana neman iso. Matar Sarkin ruga ta ce "A'a Danejo ne bismillah shigo" kamar ba zata shiga ba sai kuma ta shiga ta samu Sarkin ruga zaune yana shan kindirmo a diririce ta ce. "Jamɓanduna. _Ina kwana_" Ya ce "Jamni.. _lafiya_" zata sake yi masa wata gaisuwar ya dakatar da ita da faɗin "mene ya kawo ki?" Kanta a ƙasa tana wasa da yatsunta ta ce. "daman cewa nayi ko zaka sayi nagge guda biyar daga cikin garkenmu?" Kallon tsaf ya yi mata yana sakin murmushi kafin ya ce. "Yabi bai faɗa miki ɗan cewa gaba ɗaya ba naggenku bane? Kiwo kawai aka baku?" Cikin rashin fahimtar maganar Sarkin ruga Danejo ta ɗaga kanta da sauri ta kalle shi tana faɗin "Dada ta sanar mini gaba ɗaya garken na Baffanmu ne, shanuwan sa ne, kuma kowa ya sani Hamma Yabi ma yasan da haka" Ya ce "E, to buɗe kunne kiji kaf cikin garken naggen nan guda biyu ne naku, sauran duk mallakina ne kuma yanzu zan ɗauka aje kasuwar burni a siyar dasu, idan kina buƙata sai a haɗa da guda biyun naku a siyar daga nan sai ku biyawa Baffan naku bashin da ake binsa ma" kasa cewa komai tayi ganin ƙarfen ƙafa da ake shirin yi musu, wanne irin son zuciya ne Wannan? A nagge sama da hamsin ace guda biyu ne nasu? Me ya sa Hamma Yabi bai taɓa cewa naggen Sarkin ruga bane? Da gaske nasa ɗin ne ko ba haka bane?. Jiki a saɓule ta dawo gida zazzaɓi na rufeta sbd fargaba. Kenan tana ji tana gani Dada zata sake mutuwa ta barsu basu da kowa a duniya?. Sheikh Aliyu haydar Aliyu na zaune yana duba yadda ginin bankunan guda biyu suka ɗauki harami cikin ƙaramin lokaci tare da kamfanin sarrafa shinkafa. A nutse cikin kulawa da haibarsa kamar kullum ya miƙawa Umar-khan Album ɗin. "Ina fatan komai ya yi yadda kake so?" Kallo ɗaya Sheikh ya yi wa Umar-khan a hankali ya juya kansa yana mai jinjina shi a nutse alamar "Ya yi" Umar-khan yai murmushi kaɗan yana jinjina halin Sheikh da yawan lokaci ba tare da ya ce komai ba ya juya ya fita. Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya ya sauke yana mai miƙe ƙafafuwan shi saman table a hankali ya fara tunanin yadda zai gina rayuwar shi wanda zai sanya father farin ciki duk ƙoƙarin shi na gano abin da ke sanya father yaji zafin shi har haka ya rasa, da yawan lokaci abubuwan na damun shi nunawa ne kawai ba ya yi. Zuciyar shi na shiga tunani na tsayin lokaci. Miƙewa ya yi cikin kulawa ya shiga takawa a parlourn na shi, ƙarar wayar shi ta dakatar da shi daga tunanin da yake jin ringtone ɗin is different ya sanya ya fahimci mai kiran na shi. Farar Alkyabbar shi mai fidda ƙamshin Roja ya ɗauka tare da ɗorawa saman jallabiyar jikinsa banda dole ko hannun shi bai son a gani sbd tsarin halittar jikin na shi. Kansa a ƙasa ya nufi Main parlour babu kowa sai Hajjir bai ko kalle ta ba ya nufi sashin Abba Hakimi. A zaune ya same shi saman ladduma gabansa ɗauke da kayan marmari sai ƙwaryar zuba da kuma ta fura da nono. Zama ya yi yana fuskantar Abban na shi cikin mutunci bakin na motsa wa alamar gaisuwa Abba Hakimi ya yi murmushi ya ce. "Ba sai kace ba, Allhamdulillah" Sheikh Aliyu a lumshe idanunsa yana mamakin yadda Abba Hakimi ke fahimtar zuciyarshi da yawan lokuta. "Naga baka shirin auren naka, kamar dai you're not ready if i not mistaken?" Sheikh ya buɗe idanu da kyau akan Abba Hakimi cikin mantuwa domin gaba ɗaya ya manta da batun komai cikin In-ina yana riƙe Alkyabbar dake jikinsa da kyau tare da karkatar da kansa yana rufe idanu ya ce. "A...a...au au aure kuma A a Abba?" "E, Aure mana Sheikh haka za ka yi ta zama babu aure ni ma da kaina ban goyi bayan hakan ba, kayi aure kamar yadda Engineer ya buƙata ko dan samun kusanci da shi" Sheikh zai magana Abba Hakimi ya ƙara ɗaga masa hannu ya ce. "Kada kai musu, ka amince Allah ya sanya albarka, Engineer ya buƙata ka tura kuɗin lefin ita yarinyar tun da ba auren kake so ba, yi maka za ayi na fanshe ka na bada kuɗin lefen kamar yadda suka ce 2.5m zai isa komai na lefen" Sheikh ya ware idanu jin wai 2.5m kuɗin lefen yarinyar da ko sanin kamarta bai ba,baya buƙatar kuma ya sani ɗin. Cikin kyakkyawan lafazi Sheikh ya sake furta "2.. 2.. 2.5m A aaaa Abba yai yai yawa fa?" Abba Hakimi ya girgiza kansa yana mmkin yadda Sheikh babu abin da ya sani dan gane da rayuwar mace. "Meke sani Sheikh Aliyu? Kasan kayan mata da tsada, ko kai Alkyabbar nawa kake siya? Duk Alkyabbar ka tafi nawa kuɗi sosai, kuma a arziƙin da Ubangiji ya yi maka dan an taɓa 2.5m har wani abu ne?" Shafa gemunsa zuwa sajansa kawai Sheikh ya yi bai damu da auren ba, amma yaji daɗin yadda Abba Hakimi ke nuna kulawarsa ga duk abin da ya shafe shi. Abba Hakimi bai nunawa Sheikh ya san komai ga Bankunan da yake shirin buɗewa ba, dan haka sai ya ce "Ka tashi kaje can gidan, kuɗi kuma daman hakƙina ne na aurar da kai daga nan har sadaki" jin Sheikh yaƙi cewa komai ya sanya Abba Hakimi ɗago kansa ganin Sheikh ɗin ya yi zaune jingine jikin kujera ya dafe kansa da hannu bibbiyu zufa na yanko masa tsakanin gashinsa jikinsa na rawa kaɗan kaɗan. Girgiza kai kawai Abba Hakimi ya yi tare da jawo rubutun da ya yi da safe ya tsiyaya a cup ya zuba zuma a ciki ya juya kaɗan tare da ajjiyeta gefe guda zuwa lokacin da Sheikh ɗin zai daidai a hankali shi kuma yaci gaba da duba wani littafin Tafsir. Mother na zaune tana girgiza ƙafa cikin damuwa take kallon tilin kayan lefen dake parlourn, da sunan kayan lefen yarinyar da Sheikh zai aura. Yaya Halima ta ce. "Na daɗe banga kayan lefe mai yawan haka ba, shi Sheikh ɗin har nawa ya bada?" Motar ba ta ce komai ba sai Dr A'isha data kalli kayan da kyau ta ce. "Kalli fa Yaya iya gold guda biyar ne, Wallahi sai na ɗaukar wa su Maimoon kowa ɗaya abar shegiya da ɗaya kawai" Mother ta kalli Dr A'isha ta ce. "Tsinke na kayan nan babu mai ajjiye mini cikin gidan nan, balle su Maimoon su saka ba su rasa komai ba, a barwa wacce aka siyawa". Dr A'isha ta ce "Amma Barrister kalli kayan fa? Ni dai sai na ɗauka dukiya ai ba hauka bane" cikin faɗa Mother ta ce "Wai meke damunki haka A'isha akwai abin da kika rasa ne balle kayan nan su dameki idan su kike let me know I'll buy it for you" a sanyaye Dr A'isha ta cewa yayat tata "Am sorry Yaya"... "Sai haƙuri Barrister" cewar Yaya Halima wacce take babba a cikinsu. Miƙewa kawai Mother tai tana faɗin "Idan ban yi haƙuri ba kashe kai na zan? Ina nan dai wlh sai na aurawa Sheikh wata macan ya haɗa mata biyu" Dr A'isha ta ce "Wai ya kaga Sheikh da mata biyu" Dr A'isha ta kalli Yaya Halima ta ce "Nifa ina da shawara Yaya Halima, mai zai hana mu kai kayan lefen nan da kanmu zamu ƙara ganin ita Zahran da ake faɗa sai mu ganu tarbiyyar ta" Yaya Halima ta ce "Gulma zamu kenan? Maza ke kaiwa a bari su kai kawai?" Dr A'isha ta ce "Please mana Yaya Please" da ƙyar Yaya Halima ta amince ta ce zata nemi Engineer domin tasan yadda Mother ta ɗauki Al'amarin ba lallai tai magana ba. Da daddare duk suna zaune a parlour Mother, Yaya Halima, Dr A'isha dasu Maimoon da auta Fattoumah. Motar Sheikh tai parking a gidan da gudu Fattoumah ta miƙe yana faɗin "Yaa Lee Mother ta Yaa Lee nan" murmushin jin daɗi Mother ta yi ba tare da ta ce komai ba. A hankali ya fito da ƙafafuwansa waje kasancewar shi kaɗai ne da kansa ya yi driving hakan ya sanya gajiya ta saukar masa, yana fitowa Fattoumah na zuwa wajansa da gudu ta ce "Wlcm Yaa Lee" lumshe idanunsa ya yi tare da buɗewa, ganinta ƙarama kuma autarsu ya sanya ya sassauta fuskarsa tare da sunkuyawa ya ɗauke ta da hannu ɗaya, ɗaya hannun kuma ya rufe motar. Gemunsa taja ta ce "Yaa Lee ina kake zuwa muna ta missing naka" ya ware idanu bai ce komai ba sai hancinta da yaja kaɗan. Da idanu suka bisa yana sanye da shadda ruwan madara babbar riga da jamper bai saka hula ba sai hirami daya rufe kansa da shi fuskar shi mai ɗauke sanje zuwa gemu ta bayyana ta cikin hiramin daya gewaye fuskar. Ƙamshin Roja tuni ya mamaye parlourn da ƙamshi, Maimoon da Zeefa duk suka miƙe tsaye suna sakin murmushi a tare suka ce "Sannu da zuwa Yaa Lee" bai kalle su ba ya tattara hankalinsa gaba ɗaya ga Fattoumah dake masa surutu, bayan ya zauna saman kujera ya daidaita nutsuwarsa da kyau cikin ƙasa da murya ya ce. "Barka" ya faɗa kai tsaye ba tare da In-ina ba, Dr A'isha da Yaya Halima suka kalli juna. "Dani ka ke ko Yaya Halima?" Bai kula Dr A'isha ba ko kallonta bai ba domin yasan nemen magana ce. Tai dry ta ce "Ka gama kame fuska duk girmata da kayi dole ace da mijin iya baba, ko yanzu goma ta faɗi tafi biyar albarka dole na amsa sunan uwa a gare ka" miƙewa yai da Fattoumah ganin Dr A'isha na neman fasa masa kai da surutu. Kai tsaye Upstairs ya nufa ɓangaren father domin amsa kira. Yaya Halima tabi bayan shi da kallo ta ce "Sannu Dr da tsaurin ido, lallai karanki ya kai tsako Sheikh kike faɗawa haka? Sai da Barrister Maryam ta yi aure ta haifi Sheikh da shekaru huɗu ba aka haifeki?" Dr A'isha tai dry ta ce "Wallahi yaya ƙarfin hali ne kawai, amma ba ƙaramin kwarjini ya yi mini ba, gashi ko inuwata bata samu albarkar kallo balle Ni" dry gaba ɗaya sukai. a zaune Sheikh ya samu Father hannunsa riƙe da jarida idan kaga Sheikh da Father ba zaka taɓa cewa Sheikh ne ɗa ba, domin yafi cika idanu da jiki tsayi faɗi uwa uba fuskar Sheikh data samu sumar ƙwarai ta ƙara fidda asalin shi. A kan carpet ya zauna yana sauke numfashi kansa a ƙasa bakinsa na rawar gaida Father ya yi saurin ɗaga masa hannu ya ce. "Bani da lokacin jin faa kakkkkka yayyyya, na kiraka domin ka shirya zuwa Yola wajan Zahrah kafin akai lefe jibi, umarni na baka Aliyu ba shawararka nake nema ba" Jinjina kai kawai Sheikh ya yi bai ce komai ba. "Tashi kaje idan ka zauna ba zaka amfane ni da komai ba, zan bawa Saif-wazir address ɗin" miƙewa tsaye Sheikh ya yi sai da yaje bakin ƙofa Father ya ce "Ka kwana a nan, ban amince ka koma gidan Hakimi ba daga nan har ɗaurin aure" Sheikh ya juya da sauri ya kalli Father wato ya fahimci duk abin da yake masa baya damunsa shi yasa ya sanya Abbansa cikin al'amarin. Juyawa ya yi kamar yadda ya ce ya nufi Part ɗin nasa yana tattare babbar rigarsa. Washegari tunda ya yi sallar asuba bai koma ba, sbd wani irin mafarki da ya yi, abin ya tsaya masa yana son neman fassarar mafarkin wajan Abba Hakimi amma ya kasa, baya son mafarkin ya dangancin wani jinsi wanda ba nashi ba. Ƙarfe 7 daidai ya shirya cikin Milk ɗin shadda gezner bai saka babbar riga ba, sai golden ɗin Alkyabba daya sanya ya ɗora golden ɗin hirami, da ƙyar ya yi breakfast ɗin da Mother ta kawo masa shi ma sai da ta zauna ya gama jan ajinsa yaci kana ta fita ganin ko ƙala bai ce mata ba. Yana gamawa shirya wa Saif-wazir ya jashi zuwa garin Yola da taimakon Map. Sai da sukai nisa sosai sun ma bar Commission Quarter's ɗin sun nufi wani waje kamar daga Sama Saif-wazir yaji Sheikh yai gyaran murya kaɗan alamar ya tsaya. Waje ya nema ya yi parking gurin kamar jeji kamar ƙauye kuma. Cikin nutsuwa ya fito yana gyara zaman alkyabbar jikinsa, a hankali ya fara bin wata hanya hannunsa goye a bayansa. Sai da ya yi nisa sosai kana yaja ya tsaya. Kwance ya ganta kanta kife a ƙasa jini na zuba kaɗan a goshinta sai ƙwaryar kindirmon dake gefe guda hannunta guda riƙe da cikinta, da sauri ya zame idanunsa daga gare ta sbd kansa da yaji ya sara yana ƙoƙarin barin wajan wasu ƴan Fulani riƙe da Sanduna suka gewaye shi ɗaya ya ce "Aradu mun kama masu fyaɗen yara" Sheikh ya ware idanu amma bai nuna komai ba, wani ya ce "Wannan kamar kidnama waye kai?" nan ma shiru ya yi bai ce komai ba, Labo da yafi su iskanci ya kalli inda take kwance ganin jini a kanta ya ce "Aradu fyaɗe ya yi mata, kuma tunda kayi mata fyaɗe dole doka ta hau kanka" Sheikh trying to explain amma harshe ya sarƙe. "Kai ku saurara" Saif-wazir wanda hankalinsa bai kwanta da yadda Sheikh yabar motar ba, ya faɗa yana nufu wajan. Ƴan Fulanin suka tsaya ya kalle su sosai ya ce "Kuna hauka wanne irin fyaɗe mai yasa baku da tunani ne, yayi muku kama da wanda zai aikata haka?" Labo ya ce "Alkur'an sai na raɗeka da wannan sandan, ga jini nan muna gani ya kwantar da ita, dole kawai ya amshi hukunci" Saif-wazir ya ce "Wanne irin hukunci kuma?" Labo ya ce "Kai maza kira mana Giɗaɗo" abu kamar wasa kafin kace wani abu kusan gaba ɗaya ƴan Fulanin Rugar Bello suka zagaye Sheikh. Giɗaɗo ya kalli Sheikh kana ya kalli Labo ya ce "Zaro mana zoben hannunsa daka gani mai tsaida ne" Labo ya kama hannun SHEIKH tare da zare zoben, kusan mutuwar tsaye Sheikh ya yi yama rasa me zai ce, sai gumi dake yanko masa ya shigo ne domin tsinkar wani ganyen magani kalli yadda tsautsayi ya rutsa da shi. Kamar daga sama yaji Giɗaɗo na faɗin "Allhamdulillah mun riƙe wannan zoben matsayin sadaki" Saif-wazir ya ce "What sadakin me?" Giɗaɗo ya ce "Ai yanzu muka aura Wannan Balaraban aure da yarinyar nan, ni ne waliyin yarinyar Labo kuma waliyin Balaraban hakan shi ne hukuncin duk wanda ya yi wa wata fyaɗe a Rugar Bello, yanzu da shi da ita mata da miji ne halak ɗin sa ce.... Free pages yana gab da ƙare wa biya kuɗin ka domin shiga Paid book tuni sun yi nisa da karatu😂🤷🏾‍♀️.... Biya 500 ta Wannan account ɗin 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank. Shaidar biya 08119237616. Ƴan nijar sun yi mini magana.*🌈 IDAN BA KE 🌈* _*Nimcyluv sarauta*_ 15.... Saif ya ce "Aure kuma? waya ɗaura, dawa kuma?" Sheikh gyara tsaiwa ya yi zufa na yanko masa ta cikin naman jikinsa,kalmar auren ta gigita masa tunani dama lissafi baki ɗaya. Labo ya kalli Saif-wazir ya ce "Aradu aure aka ɗaura musu, babu wanda ya isa ya warware shi sai ikon Rabbi.. kai Giɗaɗo maza jawo mana su cikin Rugar Bello" cikin gargaɗi Saif-wazir ya nuna Labo da hannu ya ce "Saurara fillo kake kowa, an faɗa maka aure wasan yara ne? Kuma wanda kake cewa zaka aura masa ita already yana da aure wajan matar shi ma zamu, don haka babu wani aure idan ma kunyi sai ku warware auren yanzu nan" Labo ya ɗaga sanda sama gaba ɗaya sauran Fulanin suka ɗaga sanda sama tare da zagaye su Sheikh "ƙarya kake Aradu ina shemeka na sheme banza Alqur'anin Allah, aure kuma dole ne hukuncin duk wanda ya yi fyaɗe ko ya nemi lalata ƴar mutane ke nan, ku shige muje Rugar Bello" Saif-wazir zai magana Sheikh yaja numfashi da ƙyar yana girgiza masa kai domin sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi musamman da yake ɓangaren Fulanin suka shigo tsaf za su yi musu gayya. And he doesn't want that to happen. "But Sheikh....," Sheikh ya ware idanu wanda suke ɗaukan hankali kamar ba zai ce wani abu ba sai kuma ya yi ƙasa da murya kamar wanda aka ɗauke wa In-inar ya ce. "Saif-wazir" kallon Sheikh kawai Saif-wazir yake cikin mamaki. Suna ƙoƙarin tsallake ta su shige Labo ya yi saurin faɗin "Waye zai ɗaukar maka matar ka? yadda ka kawo ta nan haka zaka ɗauke ta mu ƙara sa Rugar Bello" a fili Saif-wazir ya ce "Tab..." Domin yasan that's the first thing da Sheikh can't do it ba zai taɓa ɗaukan ta ba. A hankali Saif-wazir ya sunkuya zuwa inda take kwance zuciyarsa ta buga da ƙarfi lokacin da idanun shi ya sauka akanta. A ruɗe ya juya ya kalli Sheikh Aliyu haydar Aliyu wanda ya tattare Alkyabbar jikinsa idanun shi rufe lokaci guda jijiyoyin kansa suka fito hakan kuma tabbaci ne na zuciyar shi na kusa, tashin hankalin da Saif-wazir ya shiga lokacin da idanun shi ya sauka akan fuskar Halisa Danejo Rome yafi ƙarfin tashin hankalin da Sheikh Aliyu haydar Aliyu yaji akan batun auren nashi da suke ƙoƙarin ƙaƙaba mishi. Saif-wazir ya daidaita nutsuwarsa wani kuzari na zuwar masa mmkin abin da idanun shi ke nuna masa ya cika masa zuciya. Ɗaukan ta ya yi daidai lokacin da Sheikh ya runtse idanunsa yana juya baya da ɗan sauri bakinsa ɗauke da sunan Allah. Saif-wazir na gaba ɗauke da Danejo Sheikh Aliyu haydar Aliyu na binsa cikin nutsuwa da daddako haɗi da kamala yanayin yadda ya kame kansa yake tafiya zaka ɗauka sarki ko Hakimi ne. Gaba ɗaya ƴan Fulanin suka mara musu baya har zuwa Rugar Bello lokacin tuni saƙo ya isa wajan Arɗo gaba ɗaya sun fito tare da yin shimfiɗa a gaban wata bukka wacce ta cika da yalwar inuwa, tun daga nesa Arɗo ke kallon Sheikh Aliyu har cikin ransa bai na'am cewa zai aikata abin da Giɗaɗo ya faɗa ba, amma ya kasa fahimtar mene ya sanya yaji auren shi ne mafita a gare shi dama su baki ɗaya?. Saif-wazir na zuwa ya kwantar da Danejo wacce har lokacin bata farka daga suman da take ba, jini kuma bai daina zuba daga goshinta ba. Arɗo ya kalli Sheikh cikin mutumtaka ya ce "Ka zauna mana?" Ko inda yake Sheikh bai kalla ba balle ya ama shi, sai ma tsaiwa daya gyara yana ɗan duba time fuskar shi tai jajir. Arɗo ya jinjina kai yana ƙara samun ƙarfin gwiwar abin da zuciyar shi ke ayyana mishi. Cikin nutsuwa ya ce "Sannunku, an kawo ƙarar an kama wancan yana ƙoƙarin aikata abin da Rugar Bello ta hana, wasu sunce ya aikata ga yarinyar nan kwance, bisa doka duk wanda ya yi hakan muna ɗaura masa aure da ɗiyar wannan ya sanya zamu aura masa yarinyar nan a yanzu ba tare da ɓata lokaci ba" Sheikh dai jin abin yake kamar ta tsuniyar yara ko damuwa bai ba, auren Zahrah ba bai taɓa damunsa ba balle na wannan ƴar tayin yarinyar. Saif-wazir ya ce "Amma wannan kuskure ne, idan mutum baya so ba, kuma ai ba haka ake ɗaukan doka ba, shigowarmu garin kenan fa suka fara ihun ya yi me ne kamar wasu marasa ilimi?" Giɗaɗo ya ɗaga sanda zai makawa Saif-wazir Arɗo ya yi saurin cewa "A'a Giɗaɗo, ko ma dai yaya ne kuyi haƙuri aure babu fashi" Modibbo da tun ɗazo bai magana ba ya ce "Sai a karɓi sadaki wajansa ai babu lokaci" Labo ya ce "Ga wannan a wajansa muka amsa" ya miƙawa Modibbo zoben gold ɗin da suka amsa wajan Sheikh. Sai a lokacin Saif-wazir ya ƙara cewa "Ga kuɗi a bada zoben, yana da tsada sosai kuma yana da muhimmanci ga mai shi" Modibbo ya yi murmushin jin daɗi ya ce "Daman abu mai daraja muke buƙata ai" abu kamar wasa akan idanun Saif-wazir da kunan Sheikh aka ɗaurawa Sheikh Aliyu haydar Aliyu aure da Halisa Danejo Rome akan sadakin zoben gold. Modibbo ya zama waliyin Danejo Arɗo ya zama waliyin Sheikh. Mutane kusan ashirin suka shaida daga ciki harda Saif-wazir. Shiru wajan ya ɗauka Saif-wazir ya rasa ta ya ya zai kalli idanun Sheikh ya ce da gaske Danejo matarsa ce? Zai amince da auren ne ko ya ya? Kamar gilmawar walƙiya haka Sheikh ya juya yana gyara Alkyabbar jikinsa kai tsaye baki n titi kuma ya nufa,ganin haka ya sanya Saif-wazir miƙewa da sauri Arɗo ya ce "Ina zaka baka ɗauki yarinyar ba?" Saif ya juya ya kalleta rauni ya bayyana a fuskar shi har baya son kallon yarinyar gani yake kamar idanunsa ke masa gizau da abin da yake gani ɗin. Da sauri ya ɗauke ta ya marawa Sheikh baya yana zuwa titi ya samu Sheikh zaune acikin mota ya dafe kansa da hannu bibbiyu hayaniyar duk ta sauya masa lissafi baki ɗaya, Saif na shirin saka Danejo cikin motar Sheikh ya ce "N...n.. No!!!!" Ya faɗa cikin tsawa da faɗa idanunsa na fitowa waje sosai da kyau, a tsorace ya ce "Jini na zuba a jikinta kada ta samu ƙarewar jini kuma ba zamu je da ita gida haka ba sai mun fara zuwa asibiti" kallon da Sheikh ya yi masa ya sanya Saif yin shiru yana ƙasa da ƙansa. "Please Yaa Lee Matarka...." Kafin Saif ya ƙarasa Sheikh ya yi wa motar key cikin wani irin azababban gudu ya juya kan motar tare da cillata titi ya nufi hanyar da zata mayar da shi Kano ba tare daya ƙarawa wajan Zahrah ba.. Baki Saif ya saka cike da mmkin zafin zuciya irin ta Sheikh Aliyu da alama za a sha fama kafin Sheikh ɗin ya amince da batun auren Danejo ɗin. Mota ya tsayar ya ce masa asibiti mafi kusa don Allah. Kai tsaye aka kai shi Specialist Yola dake Jimeta. Yana shiga reception yaci karo da wata cikin sauri ya ce "Oh sorry it was a mistake.." Tsaki ta ja ta ce "mistake ko rashin hankali Malam? Kana tafiya kai a sama" kallonta kawai ya yi shi bashi da lokacin ta ma, Saurayina ta ce "Banza kawai" Zahrah da hankalinta ya yi gida sbd zuwan wanda yake shirin zama mijinta ta ce "Wai Surayyerh har lokacin cacar baki gareki ne? Tunda muka zo asibitin nan ki ke neman faɗa" Surayyerh ta ɗaga hannu ta ce "Saurara Zahrah ke tunda kika samu cikin nan kike ji da masifa, daidai nake da ko wanne ɗan iska Wallahi" Saif-wazir ya kalli Zahrah da kyau kaya ne wanda suka kama jikinta sosai hannunta duk farce taci gashin doki, juyawa ya yi ya kalli Surayyerh ba tare ce komai ba ya juya zuwa cikin emergency. Kai tsaye aka bawa Danejo gado Dr ya kalli Saif-wazir ya ce "Suna?" Saif ya shafa kansa sbd sam bai sani ba sai kawai ya wayance da faɗin "Dr ka fara yi mata taimakon gaggawa, sai mu yi magana" Dr ya ce "Dole a buɗe mata file ai" "I knw, amma kulawa da ita ba zai hana buɗe file ba, a duba ta first buɗe file second" Dr ya miƙe tsaye tare da nufar ɗakin da suka kwantar da Danejo abun mamaki ba ita ba alamarta, cikin hanzari ya fito sukaci karo da Saif-wazir ya ce "Yarinyar nan ta gudu bata cikin room ɗin?" Saif ya ce "What?" Da sauri ya juya zuwa waje amma neman duniya babu Halisa Danejo Rome babu ko inuwarta "Innalillahi yau na shiga uku ko dai aljana ce yarinyar nan? Amma babban asibitin irin wannan ina zata?" Ganin bashi da wata mafita ya nemi abin hawa wanda zai dawo da shi Kano domin ba zai iya komawa Rugar Bello ba yace bai ga yarinyar ba, haka kurum su kashe sa a banza. Ɓangaren Halisa ana kwantar da ita a saman gado A.c ta fara ratsa ta, ta farka da sauri tana dabe kanta, tsoro ya kamata tana mamakin yaushe tazo. Ita dai ta fito tallan Kindirmo ta ce bari ta biya ta Rugar Bello a hanya yunwa da jiri suka yarda ita, kanta ya daki wani dutse bata ƙara sanin inda take ba. Miƙewa tsaye tayi jikinta na rawa ta ce "Hande en boni gidan cire kai aka kawo ni wayyo Allah Dadata na lalashe, lalashewa ta sameni" kuka take sosai har da majina fuskarta tai jaa. Leƙewa tayi ta window taga ashe bayan asibitin ne, da sauri ta kama tagar ta dira baya duk da zafin da kanta ke mata amma haka ta dinga gudu kamar barewa a haka ta isa Rugar Rome. Shiri sosai Zahrah tayi ta tarbar Sheikh amma har dare babu labarinsa baƙin cikin duniya duk ya kamata ga ƙawayenta duk ta tara zata nuna musu haɗaɗɗan mijin da zata aura amma ya kwafsa mata. Misalin 10:23 Abba Hakimi na zaune a Main parlour dashi da Momi kamar daga sama su kaga Sheikh ya shigo hannunsa guda ɗaya dafe da kansa, Momi zatai magana Abba Hakimi ya Girgiza mata kai alamar tai shiru,babu wanda ya kula ya shige part ɗinsa dake gidan, kai tsaye bathroom ya nufa bayan ya zame kayan jikinsa abin da bai taɓa yi ba shi ne, amfani da ruwan sanyi ya tsaya a shower na sauka akansa sanyi na ratsa masa tsakiyar kansa, sai numfashi yake fitarwa dan kansa ya kashe shower ɗin ya naɗe jikinsa a cikin wata bathroom mai ɗan kauri, idanunsa na rufewa sbd azababban ciwon kai a haka ya kwanta saman gado ya daɗe kafin barci ya ɗauke sa. "Lafiyar Sheikh ɗaya kuwa?" Abba Hakimi ya ce "Kinga alamar bai da lafiya ne?" Momi ta ce "A'a, kawai yadda na shigo gidan ne" Apple ɗin hannunta da take miƙa masa ya amsa ya ce "Kada ki damu, duk sanda ya yi haka alheri ne ke bibiyarsa" tattaunawa sukai akan gobe za a kai kayan lefen na Sheikh ita ma zata a hankali ya ce "Allah ya kaimu" sai kusan 12 na dare Sannan Saif-wazir ya shigo ganin dare ya yi kai tsaye ya nufi part ɗinsa, motar Sheikh da ya gani ya bashi tabbacin ya dawo gida. Da batun Auren Sheikh ya kwana yana tunanin ya faɗawa Abba Hakimi ko ya yi shiru? Har barci ya ɗauke shi ba samu mafita ba. Washegari da yamma wajan 5. Dr A'isha ta zabga tagumi Yaya Halima ta ce "Dr wai lafiya tun da muka dawo kike wata kala?" Dr A'isha ta ce "Wallahi Yaya tausayin Sheikh nake, ina zai kai wannan uwar matar? Na girgiza ban san rashin tarbiyyar ta ya kai haka ba, kalli da ita aka amshi kayan lefen fa?" Yaya Halima ta kalli Dr A'isha tana mmkin rashin control na bakinta da bata iya riƙe zance. "Kowa da tsarinsa fa Dr Allah dai ya sanya albarka" daga bakin ƙofa akace "Ba Amin ba, mugun ji da mugun gani ruɓaɓɓan baki ya kau daga kan Gadanga, yau ko ni ko uban Gadanga ya zaɓa" gaba ɗaya suka kalli bakin ƙofa, tana tsaye taci lace ɗauri har gaban goshi ta lafta uban Glasses a fuska wanda ya cinye rabin fuska. Cikin farin ciki Mother ta miƙe tsaye tana faɗin "Jadda" haɗe fuska tayi ta nemi waje ta zauna, Uncle Haroon ya shigo hannunsa riƙe da torelly ɗin Jadda ya zauna kusa da ita. Cikin farin ciki Mother ta ƙara cewa "Sannu da hanya Jadda ashe kina tafe" Jadda ta ɗauke kai sai da Mother tabar wajan, ta juya ta kalli Uncle Haroon murya can ƙasa ta ce. "Munafuka Algunguma duk masifa da yaƙin da ake a gidan fa bata sanar dani ba, shi ya sa na haɗe mata fuska na kame kai na, ba kaga jikinta ya yi sanyi ba, ai wlh yau sai sun bala'i ya sauka" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi ta haɗe rai tana ƙanƙantar da idanu ta ce "Kaji masifa ko? Ba murmushi za kai ba cewa zakai nayi daidai" ya ƙara murmushi ya ce "Jadda duk abin da ki kai ai daidai ne" cikin ƙaramin lokaci Mother ta cika gaban Jadda da kaya kala-kala, Yaya Halima da Dr A'isha suka gaidata ta amsa a ciki. "Kinga ba kwaɗayi ya kawo ni ba, maza kira mini mijin naki" Mother ta haura sama yana zaune yana duba Invitation ɗin bikin Sheikh dana Zahrah Mother ta shiga a hankali ya ce "Barrister ya dai?" Kai tsaye ta ce "Jadda na kira" tana faɗin hakan ta juya, yabi bayanta da kallo da sauri kuma ya miƙe shima. A hankali yake sakkowa daga benen yana sakin fuska bayan ya zauna ya ce "Sannu da zuwa Jadda" banza Jadda tayi masa, ta zare Glasses ɗin idanunta ta miƙawa Uncle Haroon, ta cire mayafi shima ta miƙawa Uncle Haroon, fuskar Father cike da tsoro ya ce "Jadda lafiya me kike shirin yi haka?" Bata kula shi ba, ta buɗe rigarta tana nunawa father ta ce "mene wannan?" Kansa a ƙasa ya kasa cewa komai ta ce "Idan ba zaka iya ba, ai Ubangiji ya tsaga mini bakin magana nonon dana shayar da kai ne, kasan Allah tun nonon yana kwance ka lalata batun auren Gadanga da wannan gantalalliyar yarinyar, idan ba haka ba zan ɗaga maka nonon sama ka lalace kaje duk inda zaka... *Not edited* Masu tambayar yadda zasu biya kuɗin IDAN BA KE. Book 1, 2 ne. Mutum zai biya ₦500 har a gama littafin baki ɗaya. 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta nan 08119237616.*🌈IDAN BA KE 🌈* *_Nimcyluv Sarauta_* 16.... *I am proud of my fans wherever they are, nayi mamakin yadda kuka amshi littafin IDAN BA KE fiye da ZAIN-ABEED. Masoya TSINTACCIYA, MOON, UNCLE NE duk ba a barku a baya ba🥰💋for the first time zanyi rubutu akan labarin zanan ƙaddarar soyayya zallah🫰🏿a shirya a gyara zama sosai yanzu aka fara...* #TEAM SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU #TEAM HALISA DANEJO ROME #TEAM EL-BASHIR AHMAD SARKI #TEAM ZAHRAH FAROUK Jadda ta ƙara cewa "Kalle ni da kyau uwarka ce Jadda, Wallahi nono zan ɗaga maka kawai kabi duniya kaje duk inda zaka Aliyu tunda ka gagara, idan ya so ana nunaka da baki ana cewa gashi can uwar shi tai masa baki ta ɗaga masa nono shi ya sa yake ta galantuyi a duniya, duk wanda bai yarda ba, ni nai maka baki ba zaka iya kawo shi wajena na tabbatar masa" zufa ta dinga yankowa Father a hankali ya zame daga kan kujera zuwa inda take ya ce "Jadda don girman Allah kada kice haka, ki tsaya ki fahimci al'amarin nan I have a reason why I want Sheikh to get married with Zahrah." Uncle Haroon ya ce "Mene dalilin naka? Uwar yaron nan bata so, I don't agree either" Jadda dai kaɗa ƙafa take har lokacin tana riƙe da ƙirjinta cikin rarrashi Father ya ce "Jadda don ki fahimce ni Sheikh ba zai iya kula da dukkan al'amarin daya shafi kasuwancina da dukiyata ba, kullum ƙarfina ƙasa yake abubuwa na neman yi mini yawa, na bashi dama yafi sau goma akan ya kawo matar da zai aura amma yaƙi, Umar-khan yace tunda Sheikh yake magana bata taɓa haɗa shi da wata mace ba, kalli sharrin da akai masa tun daga jami'ar Madina, da ace yana da aure babu mai binsa da wannan sharrin shi ya sa na yanke hukuncin aura masa ƴar aminina tasan kan business sosai zata janye hankali Sheikh ɗin zuwa kasuwancin, Jadda ina son Sheikh Aliyu ban taɓa son wani abu kamar shi ba, kiyi mini uzuri ayi auren nan idan yarinyar ba tai miki ba sai ki ɗauki mataki" Mother ta girgiza kai cike da takaicin yadda Father yake tsara zan ce. "Aini duk bani da labarin haka, jiya jiya labari ya saman ana ta yaƙi a gidan naka, kuma yarinyar ƴar iska ce" Father ya kalli Jadda da kyau ya juya ya kalli Mother yana faɗin "ke kika faɗa mata Zahrah ƴar iska ce sbd ba ƴarki bace shi ya sa zaki ai bata musu ƴa?" Rai ɓace Mother ta ce "Ni na faɗa Engineer tunda haka zuciyarka ta shaida maka, kaga yaushe rabon da naje wajanka akan maganar Aliyu ko auren? Aje ayi aure lafiya nima zan zaɓawa Sheikh yarinyar da nayi niyya na aura masa ita" tana faɗin haka ta miƙe tare da nufar upstairs zuciyarta cike da tarin baƙin ciki. Baki buɗe Jadda ke kallon kowa kafin ta ce "Na amince ayi auren kuma na amince Maryam ta zaɓawa Gadanga yarinyar da duk tai niyya" Father ya ce "Amma Jadda daka aura masa Zahrah sai ya yi mata kishiya? Ba ai mata adalci ba" Jadda ta miƙe tsaye tana ƙanƙance idanu ta ce "Wai wacce ƙaniyar ce Zarra ko me? Ba ita ba ko uwarta ka aurawa Gadanga kwaranƙwasa sai anyi mata kishiya, Allah dai ya nuna mini ƴar banzar yarinyar da idanu naga abin da bai mini ba, maza ɓace mini da gani ko mene haɗina da kai dana tsaya shiga sabgar ka" Father ya miƙe tare da barin wajan yana faɗin "A huta lafiya Jadda" sai da yabar wajan Jadda ta sauke numfashi tana raɗawa Uncle Haroon ta ce "Ba gashi ba anyi sulhu komai ya lafa daman duk iskancin mutum ina zuwa shikenan, ai Alsulhu khair" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi yana cewa sai Anjima zai dawo. Sai a lokacin Jadda ta lura da Yaya Halima da kuma Dr A'isha kowa yana danna waya abinsa kasancewarsu masu ilimi da dukiya ya sanya suka kame kansu basu saka baki cikin abin da babu ruwansu ba. Mother na zaune tana waya da wata friend ɗinta kamar daga sama Father ya faɗo ɗakin cikin faɗa ya ce "Burinki ya cika kin haɗani da mahaifiyata,she insulted me in front of people data hana auren Zahrah da naki auren ma sai ya mutu" tunda ya fara magana bata kula shi ba sai ƙafa da take girgizawa tana ci-gaba da yin wayarta hakan ya ƙona ran Father yaso ta tanka masa ya wanke ta tsaf. Saif-wazir na zaune gaban Abba Hakimi ya kasa cewa komai. Abba Hakimi ya ce "Ya kai ne Saifuddeen?" Ya sauke numfashi ya ce "Abba ban san ya zaka fahimci maganata ba" Abba Hakimi ya ɗaga kansa tare da kallon Saif-wazir ya ce "Tunda ba zan fahimta ba ta shi kaje" da sauri ya ce "No Abba I'm sorry" shiru yai can dai ya ce "Daman akan zuwa Yola da mukai da Sheikh ne, tsautsayi ya faɗa masa na auren wata ƴar Rugar Bello" Abba Hakimi ya ƙara kallon Saif-wazir da idanun na fahimta a hankali ya ce "Uhm Aure dai?" In short, Saif told Abba Hakimi about everything that happened daga zuwansu Yola har fitar Sheikh mota da zuwan Fulanin har auren da aka ɗaura da zoben Sheikh ɗin matsayin sadaki, har maganar zuwa asibiti da ɓacewar yarinyar. "Aiki jaa" Abba Hakimi ya faɗa a ransa wannan shi ne dalilin daya sanya Sheikh ya dawo a rikice kenan? "Kace yarinyar ta gudu? Zaka gane ita Rugar?" Saif ya ce "E, ta gudu Abba Rugar ma zan gane domin akan hanya take, amma bana ganin Sheikh zai amince da auren mata biyu lokaci guda" murmushi Abba Hakimi ya yi wanda shi kaɗai yasan ma'anar shi a nutse ya ce "Auren da ai masa na haɗi ne, wannan kuma Ubangiji ya ƙulla, Allah ya nuna mana zuwa Yola ɗaurin aure zamu je can Rugar" Saif-wazir ya jinjina kai alamar gamsuwa ta gefe guda kuma ya kasa faɗawa Abba Hakimi abin da ya gani a tattare da ƴar fillon wanda ya ruɗa masa lissafi ya hana shi bacci daren jiya. "Jirginsu Mai martaba ya tasu, zuwa ƙarfe huɗu zasu sauka yace Sheikh buƙatar ya je ɗakko shi, yanzu kuma lokacin barcin Sheikh ne" Saif ya duba lokaci ya ce "Yana barci tsakanin Zhur zuwa Asr jirgin kuma 4 zai yi landing akwai time Abba" Abba Hakimi ya ce "Mafi mushkila" Bayan fitar Saif-wazir Momi ta ce "Amma bana ganin wannan auren ya ɗauro fa?" "Me ya sa A'isha?" Momi ta ce "Naga babu wani na Sheikh a wajan sai Saif" jinjina kai kawai Abba Hakimi ya yi yana ci-gaba da rubutun shi ta ce "kayi shiru?" Bai kalleta ba ya ce "Idan kika sake cewa I'll do the same thing, aure ba shaidu da sadaki yake buƙata ba? Saifuddeen ya ce shaidu wajan 20 a wajan, Zoben da suka amsa kin san darajar shi kam?, Aure ya ɗauro kamar na ko wanne ma'aurata" Momi tai murmushin jin daɗi ta ce "To Allah ya sa albarka,ya sanya matar shi ce har aljanna sai a faɗawa Barrister" nan ma Abba Hakimi ya ce "A'a Maganar ta tsaya iya mu, bana son ko su Umar-khan da Ishaq-hakim suji, hatta Barrister Maryam da mijin nata bana son suji" hira sukaci gaba dayi. Ƙarfe 4:5 daidai Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya fito sanye cikin dark blue ɗin shadda jamper da babbar riga, sai ƙamshin Roja yake wanda ya a cika parlourn. Ƙafarsa cikin Leather shoe sumar kansa wacce ya rufe da hirami ta sha Ginger Geminal Oil-hair daga sajansa zuwa gemu sai kyallin Luxury Beard oil yake. Bakinsa sai ƙamshin LB Breathe herbal sugar breath freshener spray. Fitowar shi cikin parlourn ya yi daidai da shigowar Abba Hakimi, Umar-khan da Ishaq-Hakim na binsa a baya. "Daman yanzu nake shirin zuwa sashin naka sai gaka" zama ya yi Sheikh yana gyara Babbar rigarsa yau ba saika Alkyabba ba, a nutse cikin kamala murya mai ɗauke da kwarjini ya buɗe baki ya ce "Barka da yamma Abba" kallon kallo akai tsakanin Umar-khan da Ishaq-Hakim jin yau Sheikh bai In-ina ba, Abba Hakimi kam murmushi kawai ya yi hakan bai wani dame shi ba ya ce "Yawwa Sheikh Dadynka Mai martaba ya sauka yanzu kai suke jira" Sheikh ya duba agogo ya riga yasan sai biyar jirgin zai sauka yana komai bisa tsari. Bai ce komai ba ya miƙe tsaye Abba Hakimi ya bisa da kallo yana mmkin sauyawar Sheikh da yawan lokaci kamar mai cin naman wahainiya yanzu zaka ɗauka yana da yara kusan biyar sbd yana yin kamalar shi, amma fuskarsa bata nuna shekarunsa ba kullum cikin kame ta yake. Yana fita aka buɗe masa bayan mota, Umar-khan yaja Ishaq-Hakim da Saif-wazir suka shiga mota ɗaya sai airport. Zuwansu airport ɗin ya yi daidai da saukar jirgin har lokacin Sheikh na mota bai fito ba. Khalil Ahmad Sarki ne ya fara ɗakko daga cikin jirgin sai Mai martaba Ahmad sarki na uku ya shiga ɗakko cikin nutsuwa hannunsu riƙe da sanda, fari kyakkyawa da shi wanda zai iya yin shekaru wajan 65 da haihuwa. bayan sakkowar Mai martaba wani saurayi ya shiga sakkowa ganin saurayi ya sanya hantar cikin Saif-wazir juyawa, nan take kuma ya tuna da abin da idanun shi ke maza gizau. Zai iya yin shekaru 25 da haihuwa fari kamar mahaifinsa mai martaba har yari Mai martaba kyau da haske, Three-piece dinner suit a jinkinsa saɓanin Khalil Ahmad Sarki dake cikin shiga ta sarauta. Gaba ɗaya suka zube tare da gaida Mai martaba Ahmad Sarki. Khalil nata ware idanun ganin Sheikh can ya leƙa bayan mota ya ganshi zaune ya rufe idanun shi. "I expected to see you right here" Sheikh ya buɗe idanu ba tare da ya ce komai ba, cikin tsokana duk da Sheikh ɗin gaba yake da Khalil ya buɗe masa ƙofa yana faɗin "Ango kasha ƙamshi, Finally the Sheikh will get married, praise the couple's line" har lokacin dai Sheikh bai kula Khalil ba sai fitowa da ya yi daga cikin motar a hankali ya ƙarasa Wajan Mai martaba ya ɗan sunkuyar da kansa Mai martaba ya ce "Yau gani ga Sheikh tunda yaƙi zuwa inda muke" ya lumshe idanunshi tare da buɗewa ya saki murmushi wanda ya sanya kyansa fitowa sosai. Sheikh da Mai martaba suka shiga mota ɗaya, Khalil ya shiga bayan motar su Saif-wazir Mai martaba ya kalli matashin saurayin ɗan na shi ya ce "El-bashir..." Wanda aka kira da El-bashir ya ware ido murya a sake ya ce "Mai martaba zan zo" yana faɗin hakan ya juya yana tsayar da mai texsi... Abu kamar wasa ɗaurin auren Sheikh ya rage saura kwana uku cif. Har lokacin da Sheikh da El-bashir ba a haɗu ba, Sheikh ba manta da wata Yola baki ɗaya balle Auren da yake kansa na ƴar fillo. A ranar aka kammala gina Bankunan Sheikh na Lagos da Abuja, tare kamfanin sarrafa shinkafa an zuba komai da komai ranar buɗewa kawai ake jiran Sheikh ya saka sai kuma ɗaukan ma'aikata. Yana kwance a bedroom ɗinsa dake gidan father ya miƙe da sauri kamar wanda aka tsikara yana sanye da embrodiery Islamic jallabiya a hankali ya shiga duba contact ɗin wayarsa abin kunya ko number Maimoon bashi da ita, number mother ya kira aka ɗauka cikin dry akace "Yarona ya akai?" Muryar Dr A'isha ta sanya ya kwaɓe fuska ta ce "Ya akai? Ya kamata nazo na saka maka albarka" numfashi ya sauwaƙe "Uhm Maimunatu fa?" Mamakin maganar Sheikh kai tsaye ba In-ina ta cika Dr A'isha da sauri ta ce "Sorry who am I speaking with?" Kashe wayar ya yi gaba ɗaya. Dr A'isha ta juya ta ce "Maimoon kije part ɗin Sheikh wani yana kira" "wani kuma Aunty?" Dr A'isha ta ce "haka dai na fahimta" Maimoon ta miƙe tare da saka hijabi tasan tana zuwa haka zata ci ƙaniyarta. A parlour ta same shi hannunsa riƙe da Black tea wanda ya aka saka zuba a ciki. Jikinta duk rawa yake ganin yadda ya tsareta da idanun ya zame idanunsa ciki rashin tsammani ya ce "Kinga Aljani ne?" T ɗaga idanu da sauri ta kalle shi ta ce "A'a Yaa Lee kayi haƙuri" ya share zan can tana da zaune sai da ya gama shan tea ɗin son ran shi can ya ce "ki nemi number yarinyar nan" sai kuma ya yi shiru ta miƙe tana faɗin "na fahimta" waje tayi kai tsaye ta nufi upstairs part ɗin father lokacin ya gama raba Invitation baki ɗaya "Daughter ya akai ne?" "Father number Anty Zahrah zaka bani mu fara gaisawa kafin tazo" father yaji daɗin haka sosai ya bata number Zahrah ya ce "Baku fara shirin bikin babban yaya bane?" Ta ce "Father anjima zamu saloon gobe mai zana henna zata zo tai mana" waje tayi da sauri ta koma part ɗin Sheikh tare da kai masa number Zahrah. Zahrah na zaune with her best friends ana musu henna sbd anjima suna da event. Wayarta tayi ƙarar da sauri ta duba text ɗin data gani ya girgiza mata lissafi ta miƙe da sauri ta nufi bedroom ɗinta ganin haka ya sanya Surayyerh bin bayanta ta ce "Wai what's going on Zahrah looks so worried what's up?" Zahrah ta ce "na shiga uku Surayyerh kinji abin da Sheikh ya ce" Surayyerh ta amshi wayar ta shiga karanta saƙon Sheikh a fili. _I agree to marry you, on one condition if you become a good woman like Hurul-in, idan na sameki a yadda ba zan taɓa a daren zan tsinke igiyar aure ukun nan..._ "Tab ga ƙoshi ga kwanan yunwa, yaya za a yi yanzu?" Zahrah ta ce "Ba wannan ba Zahrah cikin dake jikina shi ne matsalar, kuma zan iya zuwa ayi mini ɗinki yadda Sheikh ba zai gane cewa na san namiji ba" Surayyerh ta ce "Ina da shawara kawo kunne kiji" ta raɗawa Zahrah a kunne Zahrah ta ce "Wow wlh na ɗauka jakar ƙwaƙwalwa gareki yanzu ta ina zamu fara nema, Kinga dai yanzu kira ya saman urgent" Surayyerh ta ce "Deen?" "Mtwss kina da matsala tsakani na da Deen sai after married, muje" shiryawa sukai Surayyerh na driving mota Zahrah na baya har zasu shige cikin Abti America idanun Zahrah ya sauka akan ƙwaryar Kindirmo nan da na kwaɗayi irin na masu yaron ciki ya tasu mata cikin sauri ta ce "Stop the car Surayyerh" Surayyerh taƙi tsayawa da sauri Zahrah taja burkin mota "Innalillahi zaki kashemu Zahrah are you at of your sense?" Zahrah ta fita da sauri tana zuwa ta ɗauki ƙwaryar kindirmon ya shiga sha ba tare da tunanin daga ina ya fito ba, sai ta gama sha kwaɗayi ya faɗa ta kalli ƴar fillon wacce kanta ke ƙasa tana rusa kuka da iya ƙarfinta bata san ma Zahrah ta zo wajan ba ta ce "ke nawa ne kuɗin ki?" Ta faɗa tana yatsuna fuska, Halisa Danejo Rome ta kasa magana sai kuka a hankali Zahrah ta ce "ke dallah riƙe kuɗin ki mtwss" Surayyerh ta ce "Zahrah yarinyar nan kamar zatai daidai da tsarinmu" Zahrah ta kalli Danejo da kyau sai kuma ta saki murmushi ta ce "Ƴar ƙanwata lafiya kike kuka?" Danejo ta ɗago kanta idanunta ya yi jajir cikin kuka ta ce "Dadata ce zata mutu bata da lafiya" Zahrah ta ce "Ayyah ki daina kuka to" ta ce "To ai mutuwa zatai bani da kowa kuma" Zahrah da Surayyerh sukai murmushi Zahrah ta ce "Kina son ta samu lafiya kuci gaba da rayuwa da ita?" Danejo ta ɗaga kai da sauri ta ce "Ina so Aradu ina so" Zahrah ta ce "Good, zan kaita asibitin kuɗi" da sauri Danejo ta riƙe hannun Zahrah ta ce "Da gaske kike? Hamma Yabi yace zai kaita asibitin burni shi ne aka kashe sa" Zahrah tai alamar tausaya wa ta ce "Wayyo ni zan kaita zan kashe kuɗi sosai har ta samu lafiya amma da sharaɗi guda ɗaya idan kin amince" Danejo tai shiru alamar tunani da sauri ta ce "Wanne sharaɗi" Zahrah ta ce "Kinga tunda zan taimake ki nima ki taimake ni taimako na rana ɗaya nake buƙata shi ne madadin alheri da nayi miki" Danejo tai murmushi wanda ya sanya zuciyar Zahrah bugawa sbd kyan yarinyar ta ce "Na yarda zan miki taimakon Adda" Zahrah tai murmushi tana ɓoye jin daɗin ta, ta juya suka kalli juna da Surayyerh ta ce "Tom shikenan idan kina so na kai Dadarki asibiti ta samu lafiya nima ina so ki kwanta da mijina na rana ɗaya ranar da akai kaini gidansa zai amshi budurcinki a matsayin nawa.... *Last free pages* _A nan na kawo ƙarshen free pages mu haɗu a paid group ga wanda suka biya, idan mutanan da suka biya basu kai 200 ba zan haƙura da sakinsa a whasap na buga shi zuwa kasuwa, ko kuma na sake shi iya AREWABOOKS.... Bugagge na takarda dubu ɗaya ne 1k... A whasap kuma mutum zai biya 500 (ɗari biyar har a gama labarin)... Ka tura kuɗin ka ta nan 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta wannan number 08119237616 ƴan nijar sun yi mini magana._ Sai mun haɗu a paid grp masoya💋❤‍🔥❤‍🔥 this time al'amarin daban yake salo wanda ban taɓa zuwa da irinsa ba."Mijinki zai amshi budurcina a matsayin naki?" Danejo ta sake maimaita tambayar cikin rashin fahimta kamar taso ta gane budurcin, tun da a lokutan baya Dada nayi mata faɗa akan ta kame kanta sbd ita ɗin maca ce mai ƙima da kuma daraja. "Kinga ba wani abu ne na tashin hankali ba, ki nutsu ok" ta juya kan Surayyerh tana ɓata fuska ta ce "Please Surry explain to her" Surayyerh ta kalli Danejo tana sakin murmushi kafin ta ce "Yama sunanki?" Danejo ta kalli Surry kamar ba zatai magana ba sai kuma ta ɗauke idanunta zuciyarta na bugawa ta ce. "Halisa Danejo Rome" Surry ta jinjina kai ta ce "Ok Good, yawwa ƙanwata Kinga duk mun girmeki zaki iya ce mana Anty mai ma kuke kiran babbar yaya a yaranku?" Danejo ta ce "Adda" ta taɓe baki ta ce "Whatever kice mana kawai Anty, Kinga ƙawata aure za tayi cikin satin nan, kuma bata da lafiya sosai shi ya sanya ta nemi taimako akan ki zauna tare da mijinta na rana ɗaya kawai, rana ɗayanma bai shige awa guda ko 30mnts ba,idan kin amince yanzu sai ta ɗauki Dadarki zuwa babba asibiti ai mata magani" Danejo tai shiru saboda har ranta bata gama fahimtar zan can nasu ba, ita tsoro ma suke bata Wallahi musamman data gansu manya ko wacce da gashin indo anci uban kitson ƙari. Amma da abin da suke buƙata da rayuwar Dadarta wanne yafi? Wata zuciyar ta tambayi Danejo, Dada ita ce komai na rayuwarta, farin cikinta, jin daɗinta. Da ita zata zauna har abada bada su ba. Cikin sauri ta kalli Surry ta ce. "Kuma yana amsar budurcin nawa zan dawo Rugarmu wajan Dadata?" Baƙin ciki ya cika zuciyar Zahrah, jin yadda Danejo ke ta nanata kalmar “budurcin” zuciyarta kamar zatai bindiga sbd tsabar kishin dake damun zuciyar ta. Surayyerh ta kalli Zahrah,Zahrah ta ɗaga mata kai alamar ta amsa da "Eh" kawai. "E, da kin kammala aikin naki zamu dawo dake ai ba can zaki zauna ba" Danejo tai murmushi ta ce "Aikin ba wahala Aradu na yarda nidai" ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya Zahrah ta sauke na jin daɗin kafin ta ce. "Shiga mota muje Rugar taku" Danejo tai shiru kada taje kuma masu yanke kai ne, haka kurum su yanke kan a banza. "Shigo muje mana?" Surry ta faɗa domin tuni Zahrah ta shiga motar tare da yi mata key. Ƙwaryar nonon ta ɗauka tare da shiga inda Surry ta nuna mata, ta shiga a tsorace bakinta sai rawa yake na tsoro, a haka Zahrah taja motar tare dabin direction ɗin da map ke nuna mata har suka isa Rugar Rome. Da gudu Danejo ta fito tana ƙanƙame ƙwaryar kindirmonta. Surry ce ta fara kallon rugar Zahrah ta dinga taɓe baki kamar wacce taga makusa domin Rugar Rome abin sha'awa ce ba ƙazanta cikinta. "Bari na faɗawa Sarkin ruga anyi baƙi ko?" Da sauri Zahrah ta riƙo Danejo ta ce "A'a kada ki faɗawa kowa, sbd zasu hana akai Dada asibiti muje kawai" cike da gamsuwa ta yarda ta nufi bukkarsu, suka bi bayanta. A kwance suka samu Dada idanunta nayin sama kumfa na fita daga cikin bakinta kamar ko yaushe, Shatu na gefe tana jijjiga Dada sai ihu take domin jikin Dadar ya yi tsamari fiye da ko wanne lokaci. Surry ta zaro idanu sosai bata ɗauka ciwon yai girma har haka ba, da sauri ta ce "Kamata muje Zahrah subuhanallah haka jikin nata ya yi" Danejo na kuka ta ce "Na shiga uku na lalashe Dadata kada ki mutu ki barni kinji" Zahrah ji take kamar ta shaƙe Danejo sbd baƙin ciki haɗa jiki da zatai da mijinta nan da bada jimawa ba, hakan ya sanya taji harta fara tsanar yarinyar. A mota suka saka Dada shatu da Danejo suna baya kusa da mahaifiyar tasu, a wannan lokacin Surry ke driving motar, Zahrah na gefe lokaci zuwa lokaci tana kallon Danejo ta madubi anya batai kuskure ba?. A Specialist Yola motarsu tai parking nurse's suka fito da gado kai tsaye tare da saka Dada akai, kasancewar Babban asibiti ne kuma an san Zahrah Farouk cikin ƙaramin lokaci aka buɗewa Dada file aka fara yi mata medical check up. Dr ya fito da sauri Surry ta miƙe tsaye ta ce "Dr ake ciki?" Idanunshi akan Zahrah ya ce "ki saman office" yana faɗin hakan ya shige Office ɗinsa. Surry ta kalli Zahrah ta ce "Muje Madam" ta tsuna fuska ta ce "No I'll wait here, kije yadda ake ciki let me know" ta girgiza kai tare da bin likitan zuwa office nasa. Yana zaune akan kujera ta same shi bayan sun gaida Surry ta ce. "Dr ya ake ciki ne?" Dr ya sauke numfashi yana zare Glasses ɗin idanunshi ya ce "Allahamdulillah kun kawota lokacin da ya dace, matar na jin jiki wani ƙari ne ya fito mata a ciki shi ne ke wahalar da ita" Surry ta ce "Thank God, yanzu mene mafita zuwa yaushe zata samu lafiya?" Ya gyara zama da kyau yana duba file ya ce "Zaku biya kuɗin da za ayi mata aiki, a daren yau misalin 10 za a yi aikin, muna da ƙwararrun likitoci cikin kwana ɗaya biyu komai zai daidai a ɗora ta bisa magani" cikin jin daɗi Surry ta ce "Dr hakan ya yi, nawa ne kuɗin?" Ya ce "Dubu ɗari biyu da hamsin ne har magani" ta miƙe tsaye tana ɗaukan waya da hand bag ta ce. "Ok bari naje na biya kuɗin" tana faɗin hakan ta fito ta samu Zahrah zaune tana waya, Danejo da Shatu sun rakaɓe waje guda sai zare idanu suke. Danejo ta miƙe da sauri ta nufi wajan Surry domin tafi fuskar rahama akan Zahrah muryarta na rawa ta ce "Ina Dadata? Tun ɗazo ban ganta ba ina kukai mini ita?" Zahrah ta ja tsaki Surry kuma tai murmushi ta ce. "Haba ƙanwata kin san babu inda zamu kai Dada sai wajan likita,ya ce gobe zata fara magana ki kwantar da hankalin ki" fararen haƙoranta masu kyau suka bayyana dalilin murmushi da tayi ta kalli Shatu ta ce "Shatuna Dada zata lafiya, aradu wannan ƴa ƴan albarka ne dole nayi musu aiki suma" Surry ta girgiza kai ta ce "ku zauna nan yanzu zamu dawo, kada kuje ko'ina har abinci zamu kawo muku" a tare suka ce "To Adda" Surry da Zahrah suka nufi wajan biyan kuɗi, tare da cike komai da komai. Driving take jifa jifa tana murmushi Zahrah ta gaji ta ce "Wai murmushin me kike haka Surayyerh ko tausaya mini bakya yi wata zata kwanta da mijina?" Surayyerh ta girgiza kai tana bin waƙar dezell can ta ce. "Yarinyar ce abin tausayi bake ba Zahrah" Zahrah ta ce "kamarya? Mijina zai san wata bani ba" Driving amma bai hanata fashewa da dariya ba sosai tana buga kan motar "What funny Zahrah? Serious daneja ko Danejo take ita ce abar tausayi, look how young she is bana tunanin zata iya ɗaukan al'amarin namiji,and she didn't understand what we meant". "And so what kuma? Idan har za a amshi budurcin nata? Look Surayyerh ni bana tausayin ta yadda na kai tsuhuwar ta asibiti dole ta cika mini nawa aikin" Surayyerh ta juya kaɗan ta kalli Zahrah ta ce "I don't feel sorry for her either,kawai Sheikh ba zai iya haɗa jiki da ita a yadda take ba, dole a sauya ta" Zahrah ta ce "like how wanne sauyi?" Kai tsaye Surry ta ce. "Ta daina warin da take, ta zama mai tsafta ƙamshin ya zauna mata ki sanya ta nutsu sosai nutsuwar da shi kansa zai fahimta cewa eh da gaske ke ɗin ce" da ƙarfi Zahrah ta ce "Tab hauka kenan, Please stop it bana son jin haka.." Surayyerh taja tsaki a ranta ta ce "mahaukaciya" Maimoon ce ke zaune tana tura baki Mother ta ce "Oh kina so ace ni na hanaku yin kwalliya a bikin yayan naku ko Maimoon?" Maimoon ta ce "Haba Mother bakya farin ciki da auren akan me mu kuma za mu yi har muje muyi wani henna da saloon?" Zeefa ta ce "Wallahi Moon, ni fa tun kafin naga amaryar naji na tsaneta kamar Father ya fifita ta akanmu" Auta Fattoumah fuska a haɗe hannunta riƙe da handle ɗin game ta ce "I hate her too, because of her the happiness in our house is gone" Mother ta saki baki da hanci tana bin yaran nata da kallo kafin ta ce "Akwai wanda ya halicci Zahrah a cikin ku? Balle kuyi ƙorafin sauyin halittar ta? Kul na kuma jin magana irin wannan, musamman ke Maimoon, Mamana ke kuma waye ce miki sbd ita farin cikinmu ya tafi?" Fattoumah ta yarda handle ta ce "Mother nasan komai fa, gashi har father yana cewa ana nemawa Yaa Lee mahaifi" Mother ta runtse idanu sosai wato kaf yaranta idan aka ɗauke Sheikh babu mai kaifin tunani da basira irin Fattoumah,ga riƙo tana lura da komai. A sanyaye ta ce "Maza ga mai henna can tana yiwa Dr A'isha kuje ayi muku" tana faɗin hakan tai waje. A main parlour ta samu Dr A'isha da Yaya Halima sai friends ɗinta irin su Barrister Zainab. Mother ta zauna a kujera idanunta akan t.v ba tare data cewa kowa komai ba. "Sheikh ya yi lunch kowa?" Cewar Dr A'isha. Mother ta ɗan kalleta kaɗan ta ce "Anya? Kamar dai azumi yake" Yaya Halima ta ce "ba kama bane, yau Alhamis ai" "Oh haka ne fa, na manta azumin Alhamis da Litinin Allah ya bamu lada" Barrister Zainab tai murmushi ta ce "Wato ke Dr A'isha ba zaki iya ba? Shi yasa ɗan naki ya rainaki" tai dry sosai ta ce "Azumi kam sai manyan malamai irin su Sheikh Aliyu haydar Aliyu". Sheikh na zaune shigowar shi kenan daga masjid yin sallar asr, a hankali ya sauke numfashi. A nutse ya ajjiye azkar ɗin hannun shi tare da miƙewa yabar cikin Library ɗin na shi kai tsaye ya nufi haɗaɗɗan bedroom ɗin sa wanda yaji kayan more rayuwa ko'ina na bedroom ɗin ƙamshi yake, ya zame jallabiyar jikinsa wanda ƙa'ida idan zai shiga wanka sai ya cire komai ya rage daga shi sai boxer yake shiga. Tsarin halittar jikinsa ta bayyana yana ɗan kare jikinsa da hannu a haka ya shige bathroom tare da sakarwa kansa shower ta warm water. Fitowa ya yi sanye da towel jikinsa ka fitar da ƙamshin MUD BEGIN Natural shower Gel. Idanunsa na lumshewa kamar mai jin barci a haka ya shafa versiline mai kanshi tare da fesa body spray. Wata duguwar Jallabiya mai nauyi da tsada ya ɗauka ya sanya, jallabiyar daban take domin har wani zane ne jikinta kamar alkyabba. Yana gama sawa ya naɗa rawani kamar kullum tare da ɗora hirami saman ƙafaɗar shi. tsaf ya kammala shigar shi irinta manyan malamai wanda suka san me suke ko a maluntar. Jikinsa na fidda ƙamshin Roja wanda ya bayyanar da zuwan shi cikin Main parlour ɗin gidan. Kansa a ƙasa ba tare daya kalli kowa ba, kamar yadda zuciyar shi ta raya masa hakan ce ta kasance Dr A'isha na ganinsa ta fara buɗa tare da faɗin. "Ayyiri yiri the lastest ango of the year" ya ƙara kame fuskar shi babu walwala hannun shi akan gemunsa yana ɗan ja haka yai waje ba tare da kalle ta ba, balle yace mata wani abun duk da yaso ya tsaya yayi mata bayanin aya da hadisai Manzon Allah akan muhimmancin muryar mace. Da kuma rashin amfanin wannan ihun da take. Chevrolet silverado car wacce ta kasance blue black ya nufa, harabar gidan shiru hakan yasa ya rufe idanu yanayin na masa daɗi na shaƙar fresh air ga ƙamshin na'ana'a dake ɗan nesa da shi, Bismillah ya yi tare da shiga motar sai da ya yi addu'a kafin a hankali ya yi wa motar key gatekeeper ya buɗe masa, cikin nutsuwa da haiba yake driving motar har ya harbata kan titi. A harabar gidan Abba Hakimi ya yi parking motar, ganin motoci da yawa ya sanya shi taɓe fuska baya son hayaniya sam. Ya fito a kame yana jan gemunsa kaɗan ta baya yabi a ƙoƙarin shi na son shiga part ɗin nasa ba tare da kowa ya gansa ba. Yaje corner kenan yaji ance. "Yaa Sheikh" Khalil Ahmad Sarki ya faɗa yana murmushi hannun shi riƙe da gorar ruwa. "Yanzu nake shirin zuwa can gida muji yadda al'amarin bikin zai kama, nasan dai bikin Yaa Sheikh dole ba events ba D.j" Sheikh ya ware idanu da kyau yana bin Khalil da kallo. Khalil ya ce "na ƙosa naga matar Yaa Sheikh, nasan dole ta zama Malama kamar haka, Wow! Ga Yaa Sheikh ga Malama what a beautiful couples wlh dole love yaci ƙaniyar shi" Yaa Sheikh ya ɗauke Idanunshi tare da kama hannun Khalil Ahmad sarki suka nufi hanyar ƙofa Khalil ya ce "Ya dai kamata ka fito tun ɗazo Mai martaba ya shigo" har lokacin Yaa Sheikh bai ce komai ba, yana zuwa bakin ƙofa ya tura Khalil waje tare da rufo ƙofar ya murɗa key. Khalil ya dinga dry daman ya lura zan can damun Yaa Sheikh yake yana mmkin yadda baya ƙaunar ai masa maganar mace?. Ya juya inda yabar su Abba Hakimi yana zuwa ya ce "Abba Hakimi ai ga ɗan naka can ya gudu part ɗin shi" Abba Hakimi ya ce "Za mu yi faɗa dakai yanzu Ibrahimul-khalil" Khalil ya yi murmushi ya ce "Nikam ina ruwar gida Momi ne?" Abba Hakimi ya ce "Tana can tana kayan buɗe baki na Aliyu, ƙosai da kunun gyaɗa"... "Ah! Lallai aikin lada take kenan" Mai martaba Ahmad Sarki ya kalli Ishaq-Hakim cikin kamala ya ce "kira Sheikh" da mutumtaka ya ce "To ranka ya daɗe Allah yaja kwana" kafin Ishaq-Hakim ya miƙe El-bashir wanda tun ɗazo yake hakimce saman kujera ya miƙe cikin nutsuwa hannu cikin aljihun suit ya nufi hanyar fita Abba Hakimi ya bisa da kallo yana nazartar yanayin yaron wanda baya son haɗa inuwa da Yaa Sheikh gaba ɗaya. "El-bashir kada kai nisa" cewar Mai martaba. He just nods his head and quickly leave the parlour. Bayan sallar magrib Yaa Sheikh na zaune a ƙawataccen parlournsa gabansa ɗauke da kayan buɗe baki, inibi yaci sai ƙosan da yake mai zafi ya yi laushi sosai sbd ƙwai da aka zuba cikin haɗin, hakan yasa ya ɗan saki jiki ci ƙosan da kunun gyaɗar. Yana jin gine da jikin kujera yana kallon Aljazzera yaji Sallamar Abba Hakimi shi ne kawai ke shigowa kai tsaye cikin part ɗin na shi, ya gyara zama sosai yana mai amsa sallamar ta Abba Hakimi. Bayan Abban ya zauna ya dubi Yaa Sheikh ya ce. "Aliyu haydar" Yaa Sheikh ya ɗaga kansa gaba ɗaya tare da kallon Abba Hakimi da yake faɗin "Jibi ɗaurin auren ka, ya ya zakai da uwar gidan naka kafin amaryar tazo?" "Uuuu...uu... Uwar gggg gida? Am am amarya?" Ya faɗa yana kallon Abba alamar rashin fahimta. Abba Hakimi ya lura da gaske Yaa Sheikh bai gane ba ya ce "Yarinyar da aka ɗaura maka aure da ita a can Yola? Ka tuna?" Tab yakan manta abubuwa amma wannan abun ya zama abu na farko da ya yi saurin mantawa da shi. "Ina jinka,ina so muje can rugar tasu ne" magana zarar bunu cikin rashin sani Yaa Sheikh ya ce "Uhm bani da labarin hakan Abba, idan akwai auren ma zan kunce shi yanzu... *Don Allah kada a fitar😒 littafin IDAN BA KE na kuɗi it's 500 via this account 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank. Via evidence 08119237616. SARAUTAR MARUBUTAMurmushin manya Abba Hakimi ya yi yana mamakin yadda kai tsaye Yaa Sheikh yake nuna zallar ƙiyaya ga ƴa mace balle kuma ai masa batun aure, ya san dai rayuwa ba zata taɓa yin yiwuwa ga babban mutum irin Sheikh Aliyu haydar Aliyu ba aure ba. Yana sakin murmushi ya ce. "Baka sonta? Ko auren ne baka so?" Yaa Sheikh ya yi shiru kansa a ƙasa ba tare da ya ce komai ba, hakan bai damu Abba Hakimi ba domin ya riga yasan waye Yaa Sheikh sai dai ya bawa wani labari sanin da ya yi masa baya tunanin ko Mahaifin shi Engineer ya sani. "Shi kenan, Allah ya kyauta, ka jira sakin muga ko?" Abba Hakimi ya furta hakan yana miƙewa tsaye hannun shi riƙe da sanda. Yaa Sheikh ya a miƙe tsaye shima suka jera shi da Abban na shi duk da bai so fita wajan ba. A parlour suka samu Mai martaba Ahmad Sarki shi da Khalil suna tattaunawa a hankali lokacin guda kuma fuskar Mai martaba ɗin ta sauya launi sosai. Bayan sun zauna Khalil da bakinshi baya shiru ya ce "Abba ka fito da ango kenan, ban taɓa ganin ango kamar shi ba He doesn't want to talk about his marriage at all" Abba Hakimi ya kalli Mai martaba ya ce "Your highness mai ya sa ka taho da wannan ne? Ina ya bar matar ta shi" murmushi girma kawai Mai martaba ya yi ba tare da ya ce komai ba idanun shi akan Yaa Sheikh yana taso ya faɗa masa wata magana amma ya kasa. "Yaushe El-bashir ya zama haka ne? Kamar wanda wani abu ke damun shi?" Khalil cikin rashin jin daɗi ya ce "Na lura da hakan, matsalar El-bashir taurin kai, komai ya yi zafi a rayuwa maganin shi Allah yabi komai a sannu har Ubangiji ya bayyana abin da yake rufe ko?" Abba Hakimi ya ce "haka Innalillaha ma'al sabirin" a hankali Mai martaba ya duba lokaci yana mai miƙewa tsaye kafin ya kalli Yaa Sheikh ya ce "Yaa Sheikh aci gaba dayi mana addu'a, ina nan ina ta sadaƙa, kamar yadda kace" Yaa Sheikh ya buɗe ido wanda tunda suke magana idanun suke rufe, tare zubawa Mai martaba idanun cikin nutsuwa ya ɗaga kai tare da ɗan faɗaɗa fuskar shi da murmushi. Abba Hakimi ya ce "ba zaka zauna a nan ɗin ba?" Mai martaba yana gyara sandar hannun shi ya ce "Anya? Gwara naje can hotel ɗin zaifi" sai da safe ya yi musu Yaa Sheikh da Abba Hakimi suka zauna zaman karatu kamar yadda suka saba kullum. Juyi yake saman lafiyayyan royal bed ɗin na shi ya kasa barci baki ɗaya mafarkin da yake ya hana shi runtsawa, gashi duk karatun shi bashi da masaniyya akan fassarar mafarki, ya miƙe zaune yana mai motsa bakinshi alamar addu'a cikin nutsuwa ya kunna blue light haske ya ƙara bayyana a bedroom ɗin, daga shi sai white night wears masu taushi da kyau, ya saka Hermes slippers tare da shigewa bathroom ya wanke bakin shi tas kai tsaye ƙaramin parlournsa ya koma, hannunshi riƙe da kwalin Dabino yana zama kan kujerar ya zari dabino ɗaya ɗaya tare da kaiwa bakinshi, zaƙi da garɗin dabinon suka ratsa saman harshensa tare da kaiwa jijiyoyin dake sarrafa kwakwalwar dake basa umarnin ziyara, kai tsaye dukkan wani daɗin dabinon ya gama ratsa ko'ina na bakinshi. Iska mai daɗi ta fara kaɗa shi kafin can kuma ya fara jiyo kukan mage ƙasa-ƙasa bashi da wata alaƙa da mage infact baya son mage a rayuwarshi da alama kuma so ake a firgita shi da ita. Babu tsoro a fuskarshi ya miƙe hannu goye a bayansa bakinsa ɗauke da addu'a a haka ya fara bin hanyar da kukan yake tasuwa ba tare da tunanin komai ba. A can corridor ya ga wata baƙar mage jibgegiyya wacce bai taɓa ganin irinta ba, a kallo ɗaya kuma ya fahimci ba mage bace irin jama'arsa ce masu takura masa. Girgiza kai kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba ya nufi hanyar bedroom ɗin kamar daga sama yaji magen ta ce. "Zahrah da zaka aura tana da ciki, tana ciki, tana da ciki" ya tsaya daga tafiyar da yake tare da juyowa baki ɗaya yana harɗe hannu a ƙirji, duk kusan wani abu da zai faru da shi a rayuwa yana mafarki da shi, inma mai kyau ko mara kyau, ya yarda cewa kuma mafarki ba gaskiya bane bai taɓa yarda da abubuwan da yake gani ɗin ba. Wani lokaci jama'arsa da suke bibiye da shi sune suke faɗa masa wani abun. Ya sauke numfashi cikin laushin murya ya ce. "Ta nan aka ɓullo, raba aure zaku koma?" Ya faɗa a taushashe yana zubawa magen idanun ta ce "musan abin da baka sani ba, tana da ciki, tana da ciki" Yaa Sheikh ya jawo aya mai zafi cikin kamilalliyyar muryarsa gumi na tsastsafo masa ya ce "Ubangiji shi ya san komai" ya sauke numfashi yana mai ƙara cewa "matsa nan, kafin raina ya ɓaci" kasancewa ko a malamai suna shakkar Yaa Sheikh cikin ƙaramin lokaci ta ɓacewa ganinsa, da ya san sune ma babu abin da zai tsanya ya fito Maganar Zahrah da cikin ya tattara ya sanya su a mala. Washegari ya kama juma'a Yaa Sheikh ya fito cikin wata dakakkiyar shadda gezner fara tas sai ɗaukan idanu take, bai saka Alkyabba ba kasancewar jamper da babbar riga ya sanya sai rawani kawai da ya yi ya ɗora hirami saman ƙafaɗarsa. 1:30 daidai motarsa tai parking a babban masallacin juma'a dake nan Kano. Cikin sauri gudu harɗewar harshensa ya fara huɗu ba akan muhimmancin sadaƙa da kariyar da take bayarwa dan gane da asara. 2:00 ya data iƙima na sallah ana idarwa kamar yadda ya saba ya nufi gidan marayu da naƙasassu yana basu taimako. 3:30 ya dawo gida kiran Father ne ya ƙara sanyawa ya yo gidan kai tsaye ba tare da tunanin komai ba, yana gaba Khalil na gefen shi a haka suka shigo cikin parlourn mai ɗauke da some of relatives nasa, idanunsa akan Fattoumah wacce akai wa henna a hannu da ƙafa tana ganin shi ta miƙe da sauri tana faɗin "Yaa Lee, Yaa Lee" da sauri yaja baya domin baya son abar hannunta infact he doesn't know menene ba, ya zauna saman kujera yana harɗe hannu a ƙirji ba tare daya kula Auta Fattoumah ba. Dr A'isha ta ce "Ango kasha ƙamshi, wata tsiyar ma sai jibi amarya ta zo can wait to see this day" Yaya Halima ta ce "ke dai Dr bakya kalan girma Wallahi ta ya ya ɗan naki zai girmama ki?" Kafin kowa ya yi magana Jadda ta fito zani na faɗuwa ta ce "Ga Malam ga Malam, huhu azabar duniya ya naga duk an sa shi gaba kamar wata tattabara sabuwar ƙinƙisa? Nifa masifar Sa'idu ce bana son uban kowa kuma ya san babu kyau ai" Khalil ya saki baki yana kallon Jadda. "To dan mun gaisa da shi ai bai zama laifi ba ko?" A fusace Jadda ta ce "Alkur'an ya zama? Ki faɗi inda kuka haɗa jini da Malam? Ba dangin iya balle na baba, sai ihun cewa ke ƙanwar uwar shi ce, gaba kuma kice ke uwar shi bayan ko ƙaton kashi baki taɓa ba, balle haihuwa tirrr da iri na irin naki, ke dai baki yo gadon haihuwa ba, Insha Allah duk inda wata tara tayi matar Malam ta sauke cikin fari ke dai kiyi ta zama" nan da nan idanun Dr A'isha ya cika da hawaye babu abin data tsana irin ai mata gorin haihuwa. Yaya Halima itama da ranta ya ɓaci ta ce "Jadda amma dai kin san haihuwa lokaci ce ko? Duk wanda ya haihu Allah ne ya bashi ai" Jadda tai mitsi mitsi da idanu ta ce "Ai baki cika ƴar halak ba Halima indai baki zo kin dake ni ba, na faɗa ta haihu ne? Naga shekara guda akai bikin ita A'isha take kowa da kuma siyan Akuyar da nayi, gashi nan sai haihuwa take kamar almara ko yanzu ciki gareta ina ta rabawa jama'a domin su sami irin albarka" Dr A'isha ta fashe da kuka sosai tana ciwo sosai a ranta. Yaa Sheikh dai yana zaune tare da sauraran komai ba, jin ihun Jadda ya yi yawa ya sanya ya miƙe tsaye tare da saurin barin wajan, yana zuwa dab da Dr A'isha ya kama gefen rigarta ya jata can part ɗin mother. Bai ce mata komai ba, amma ya lura da irin zafin da take ji a zuciyar ta. Sai data gama kukan ta fara shassheƙa ya lumfasa kaɗan ya ce. "ka yi bushara ga masu hakuri (155) su ne waɗan da idan wata musiba ta same su, sai su ce: mu daga gare shi muke kuma gare shi za mu koma, Baqara (!56)" ya yi shiru saboda In-inar data zo masa, shirun daya sanya Dr A'isha ɗago jajayen idanunta tare zuba masa su, sai taga ba ita yake kallo ba, gaba ɗaya ya tattara gaban babbar rigarsa ya riƙe ƙam hannunsa na rawa, alamar da gaske magana yake son yi, jikinsa ya bashi kallon shi take da sauri ya juya zai bar wajan kamar fitar gashi daga cikin nono haka maganarsa ta fito ya ce. "Wannan ayar ta kur’ani ana kiranta da ayar maidowa kuma tana karantar da mu darasin cewa kada mu yi baƙin ciki da faduwar falala, domin duk wannan baiwar Allah ce. Wata rana ya yafe, washegari kuma ya ga dama ya dawo mana da ita, su biyun su ne maslahar mu. Ki yi haƙuri" Yana faɗin hakan yabar wajan kamar walƙiyya Dr A'isha ta saki Ajjiyar zuciya tana jin sanyi a ranta, yau Yaa Sheikh da kansa ya jata har ya yi mata wa'azi lallai ta zama ta musamman ko a cikin ƴan uwa. Jadda kuma ta inda ta shiga bata nan take fita ba. "Ko wanne ɗan hau idan ba zai iya zama bai yai gaba, idan mutum yaja baki yai gum sai ace ya yi wulaƙanci, ya yi magana kuma ace shi ɗan iska bai iya magana ba, huuuu wannan azabar Alkur'an ba dani ba Alsulhu khair" tana ganin Yaa Sheikh yaja baki tai shiru akan idanunta ya haura upstairs part ɗin father, kamar yadda yai tunani yana parlourn shi zaune sai haɗa gift yake wanda zai bawa bride's family. Yaa Sheikh zai sallama Father ya ɗaga hannu ya ce "shigo kawai, riƙe sallamar ka" hakan bai damu Yaa Sheikh ba, ya nemi waje ƙasan carpet ya zauna. "Akwai events da Zahrah zatai, kuma tana buƙatar kaje iya friends ɗinta ne, kai ma kaje da friends naka, 12 na dare zasu fara event ɗin gobe, You can check by yourself" Yaa Sheikh bai ce komai ba, kuma bai amsa ba, domin ya san ba za shi ba. Ya miƙe tsaye yana gyara zaman hiramin jikinsa. Sai da ya ɗan jima a tsaye ya ce "Allah ya taimaka" yana faɗin hakan ya juya cikin sauri tare da barin gidan baki ɗaya shi da Khalil. Surayyerh ta zame jikinta daga cikin friends ɗin Zahrah tana duba agogo dake nuna 10:15 na safiyar ranar asabar. Cikin sauri ta nufi compound na gidan tare da shiga mota, tana yi tana dubawa gudun kada wani ya kanta, driving motar dake da gudu har tabar Commissioners Quarter's kai tsaye ta nufi wani babban mall parking tayi, kasancewar mall ɗin na manyan mutanai ne ya sanya aka fara yi mata Wlcm tun daga bakin gate. Tana shiga ciki wata mata ta ce "Wlcm Maaah" ta ɗaga mata kai, kai tsaye ta nufi ɓangaren kayan mata ta saka wata maid ta zo. Tana zaune saman kujera lemo a hannunta maid ɗin ta ce "Yes Maaah, how can I help you?" Surry ta ya motsa fuska tana kallon maid ɗin ta ce "Ina buƙatar, Abaya's, perpumes, body spray, body lotion, shower gel, everything na mace masu kyau na ƴar 17yrs ki haɗu ki kawo mini yanzu" Maid ɗin ta rusuna ta ce "Insha Allah Maaah, enjoy your time" ta juya da nufin tafiya Surry ta ce "hiii nace ba" Maid ta ce "Yes" Surry ta miƙe tsaye tana ƙare wa wajan kallo ta ce "Ki tabbatar body lotion ɗin sai sauya fata cikin kwana biyu" Maid ɗin tai murmushi cikin hausar ta ta ce "kada ki damu kinji" kaya masu mahaukacin kyau aka haɗawa Surry ga tsada ka cika aiki, komai na babban company aka zaɓo, ta biya kuɗi aka loda mata kayan aleda daga mall ɗin Specialist Yola ta nufa, tana zuwa ta samu Danejo zaune a gaban room ɗin da aka kwantar da Dada, ta miƙe tsaye fuskarta ɗauke da fara'a ta ce "Sannu da hanya Adda" Surry ta haɗe rai ta ce "Ba nace bana son Addar nan ba, kice Anty" tai ƙasa da kanta tana wasa da hannu "Ya na ganku a nan?" Danejo taƙi cewa komai sai Shatu da ta ce "Ana duba Dada ne" ta jinjina kai tare da neman wajan zama, sai duba lokaci take tasan anytime Zahrah zata iya nemanta sbd shirye-shiryen zuwa event anjima. Likitocin suka fito Danejo na ganin haka ta shiga room da sauri Shatu ta mara mata baya, Surry tabi bayansu A zaune ta samu Dada cikin ranta ta ce "Wow, ashe Halisa gado tayi" Kyakkyawa ce sosai Dada ajin ƙarshe, ta faɗaɗa fuska idanunta akan Surry wacce ke mata sannu cikin sanyin muryar ta ce "Allahamdulillah, ke ɗaya yau?" Surry ta ce "Wallahi, hanya ta biyo dani bama sai an faɗa mata nazo ba, anjima likita zai sallame ki" Dada ta ƙara sakin murmushi ta ce "To ba damuwa, Allah ya saka muku da alkairi, Halisa ta faɗa mini aiki sai dai ban gane ba" Surry tai murmushi ta ce "Oh! Daman ƙawata zatai aure shi ne za a ɗauke ta aiki sbd mun yaba da hankalinta, kuma duk shekara ko wata za a dinga biyan ta kuɗin aikin, kuma sa a sakata a makaranta akan wannan sharaɗin da tace zata cika muka kawo ki asibitin" da sauri Danejo ta kalli Surry domin tasan ba haka akai ba, bakinta na rawa kasancewar bata barin magana a ciki ta buɗe baki ta ce "Lalashewa ta sameki Anty Aradu ƙarya ne ba haka akai ba, shewa sukai zan..." cikin sauri Surry ta tare Danejo da faɗin "wannan daban ne kinji ƙanwata Halisa, zo kiga kayan da na siyo miki" tai shiru tana ware idanunta itafa haka kurum ba za a dinga rainata mata hankali ba. Surry ta buɗe ƙatuwar shopping bag ɗin ta shiga zaro dugwayen riguna kala-kala, masu kyau da tsari. "Wannan kayan duk na mene?" Cewar Dada domin ganin kayan ya sanya kanta sarawa ta rufe idanu da sauri. Surayyerh ta ce "Kaya ne, na kawowa ƙanwata Halisa ta fara amfani da su kafin mu tafi da ita" Dada ta kasa cewa komai domin tana ganin tafiya da Halisa wani wajan ba ƙaramin babban ƙibi bane a rayuwarta, kuma ba zata jure kalar rayuwar da suke ba, Halisa tana da saurin baki bata da haƙuri wani lokacin kana yi mata take maka zafin rai gareta. Surry ta ce "Anjima Dr zai zo, zuwa anjima ko da safe zamu zo mu tafi da Halisa ɗin, akwai wani Sani mai p.o.s a wajan shi zaki dinga karɓar kuɗin aikin Halisa na duk shekara, zan baki number waya koda kina buƙatar jin muryar yarinyar ki sai ki bawa mai p.o.s ɗin ya kira, gaba ɗaya aikin shekara biyu zatai...." Da sauri jikin Danejo na rawa ta ce "Wallahi ba inda zani, ba zan biko ba taimakon da ku kaiwa Dadata Allah ya saka ni dai ba zani ba daman wayo nayi muku dan ku kai Dadata asibitin burni... Pay before you read.... IDAN BA KE it's paid book 500. Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616.... Don Allah kada a fitar😒😂. SARAUTAR MARUBUTA"Subuhanallah yi haƙuri bata kula ba" Surry ta faɗa da sauri tana kama hannun Halisa ba tare data bari ta buɗe liƙab ɗin ba. Ita dai Halisa kallon Yaa Sheikh take kamar idanunta zai faɗo ta cikin liƙab ɗin. Yaa Sheikh ya ratsa ta gefen Halisa zai shige tayi saurin shan gabansa tana kwace hannunta, duk da ta tsorata da yanayin shi amma bai hanata ƙara binsa da idanu ba da ƙarfi ta ce. "Laa Wallahi shi ne, Balarabe ashe zan sake ganinka?" Dam! Zuciyar Surry ta buga, Umar-khan zai magana Abba Hakimi ya girgiza masa kawai alamar yai shiru. A wannan karan ba Yaa Sheikh bai kalli yarinyar dake gabansa ba, sai ƙara ɗauke idanu yake gefe guda, ganin yadda ya yi mata ya sanya Halisa ta saka hannu ta cire liƙab ɗin tare da matsawa gaban Yaa Sheikh ta ce "Baka gane ni ba? Nasan ka gane ni ni ce fa Halisa Danejo Rome ka manta ni? Ina kaje bana ganinka?" Tarin makami da ya yiwa Saif-wazir yawa ya sanya ya hangame baki, anya yarinyar nan ba aljana bace ko kuma wacce Aljanu suka shafa?. Khalil Ahmad Sarki ya juya da sauri ya kalli El-bashir dake can gefe ɗaya yana waya, ya ƙara juyawa ya kalli Halisa wacce ɗan ƙaramin bakinta ke motsawa tana yiwa Yaa Sheikh rantsuwar Wallahi ya gane ta yana sani yaƙi kulata. Ahmad Sarki da har yanzu yake kallon Danejo sai ya juya ya kalli El-bashir makami kamannin su na rikita masa lissafi musamman da yaji muryar Danejo wacce take iri ɗaya data El-bashir sak! Sai dai ita ɗin macace saɓanin El-bashir da yake namiji. "The wonder never ends" Khalil ya furta a fili na dafe kansa. Danejo ta ce "Yanzu baka gane ni ba, nice fa? har ka taɓa bani mangoro?" Yaa Sheikh ya ware fararen idanunsa sosai tare da sauke ganinsa akan zagayayyiyar fuskar ta, kai tsaye ƙwayar idanunsa ta shiga cikin nata. Danejo ta haɗiye sauran maganar sbd idanun Yaa Sheikh da sukai mata kaifi, a kallo ɗaya da ya yi mata ya saka mata shakkar shi, tsoro da kuma ganin girman shi. A hankali ya zame hannun yana mai barin wajan Danejo ta bisa da idanu.. "Kin san shi ne?" Danejo ta kalli Saif-wazir kamar zatai magana sai kuma ta murguɗa masa baki Surry ta kama hannun ta suka shige cikin gidan su Zahrah. Saif yai dariya son ran shi ya ce "Akwai rigima Yaa Sheikh za ai raino" Khalil Ahmad Sarki ya daki kafaɗar Saif ya ce. "I couldn't understand, wai wace yarinyar nan? Na ruɗe fa" Saif ya ce "wato abinne gaba ɗaya is complicated, muje mu zauna" Ya juya zuwa ga Abba Hakimi wanda ke sauraran su ya ce "Abba ita ce ƴar fillon da nake baka labari" Abba Hakimi ya jinjina kai cikin nutsuwa ya ce "Ikon Allah ya kamata mu zauna, Umar-khan maza kira mini Barrister Maryam a waya" Umar-khan ya ce "To Abba" Abba Hakimi ya yi gaba Saif-wazir ya bi bayan shi, Umar-khan ya tsaya kiran Mother a waya. Khalil Ahmad Sarki ya nufi inda El-bashir yake tsaye ya zuba hannun shi cikin aljihun wandon shi ɗaya hannun yana shafa sumar kansa. "Kaga abin da na gani kowa El-bashir?" El-bashir ya juya zuwa ga yayan nashi kamar ba zai magana ba sai kuma ya ce "A'a duk an cika waje da ihu me zan gani haba kun zama kamar wasu mata" Khalil ya ce "let's keep a joke a side wata na gani mai mugun kama da kai" El-bashir ya nuna kansa yana fiddo idanu waje ya ce "Ni kaga me kama dani?" El-bashir ya tambaya yana gyara tsaiwar shi. Khalil Ahmad Sarki ya ce "Ai kamannin har sun ɓaci hatta beauty point da gashin girarka daya rabe biyu, hatta muryarku iri ɗaya ne El-bashir na girgiza" a karo na farko El-bashir ya yi murmushi kawai yana girgiza kansa ba tare da ya ce komai ba, hakan ya fusata Khalil ya ce "Ya ina magana akan abu mai muhimmaci kana dariya?" El-bashir ya jingina jikin mota baka iya gane yanayin shi ya ce "Me zance Abu Juwairah? Kawai kun haɗu da aljana banda haka ina za a samu wata mai kama dani? ni ba ƙanwa ba ni ba ƴa ba, Please mu bar wannan maganar" Khalil zai magana wayarsa ta shiga ringing ganin matarsa ce Oum Juwairah ya sanya yabar wajan yana amsa sallamar ta. Tunda suka shiga ɗakin Danejo bata kalli inda Zahrah ke zaune ba, kanta a ƙasa ta haɗe fuska sosai. Zahrah gabanta ya faɗi ganin yadda cikin kwana biyu Halisa Danejo ta sauya kamar ba ƴar fillo ba, fatar ta na ƙyalli ko'ina na jikin fes yake duguwar rigar da Surry ta bata ta saka mai purple ta amshi jikinta sosai. Surry ta ce "kina ta kallon ƴar fillo kamar baki san taba lokaci na shigewa" Zahrah ta sauke numfashi ta ce "Kada dai ki mata matsayin mai aikatau zaki cikin gudana ƴar fillo" Danejo ta ɗago kai ta kalli Zahrah cikin sautin siririyar muryar ta ta ce "Ban manta ba, sunana Halisa Danejo Rome ba ƴar fillo ba" Zahrah taja tsaki ta ce "Ji banza ina cewa a cikin ruga muka ɗakko ki? Banda warin shanu dana Kindirmo me kike? Har kece za kice wai ke ba ƴar fillo bace?" Danejo ta shiga kallon Zahrah zuciyarta na jin zafin maganganun data faɗa mata idanunta har ya cika da ruwan hawaye saboda ba zata iya mayarwa da Zahrah magana ba bisa umarnin Dadarta. Surry taja gefe guda tana murmushi jin daɗi ba tare da kowa ya lura ba, ita kanta baza taso tun yanzu Halisa ta fara mayarwa da Zahrah magana ba. Cikin sauri ta ce "Zahrah dama shiryawa ki kai yanzu 1:30 ance 2:00 daidai jirgi zai tashi" Zahrah ta miƙe ta ce "Ina son haɗuwa da Deen wlh kwana biyu bana iya barci Surayyerh abin cikina masifa yasa mini ba zan iya jurewa ba idan ban samu abin da nake ba dole naje naga Deen" a fili Surry ta ce. "Wallahi baki da tunani Zahrah ganin Deen a halin yanzu bai dace ba kuma nasan abin da zaku aikata" a zuciyarta kuma ta ce "Well-done Zahrah ban fatan ki daina bibiyar maza tun yanzu" Zahrah ta ɗauki hijabi tare da juyawa ta kalli Surry ta ce "Meye sunan abin da kika bawa yarinyar nan ta saka bani" Surry ta amshi liƙab ɗin hannun Danejo wacce ta haɗe rai sosai taƙi yarda ta ƙara kallon inda Zahrah take. Cikin sauri ta gama shiryawa babu mai cewa Zahrah ce ta nufi ƙofar baya akan nan da 20 minutes zata dawo. Tana fita Surry ta kalli Halisa ta ce "Kina ji ƙanwata, Kinga wannan mutumin da kika ganu har kika ruɗe kina cewa Balarabe?" Halisa dai kallon Surry take kafin Surry ta ce "To shi ne mijin Zahrah, ina so ki nutsu ki fahimta Kinga daga can kano Madina zaku shige, kina wanka sau biyu ko sau uku a rana, haka ma brush da saka kaya masu kyau...." Ta ci-gaba da faɗa mata komai na yadda zata gyara jikinta da tsafta ta ɗora da faɗin "Kin fara Al'ada ne?" Danejo ta girgiza kai. Surry ta ce "stop raising your head, magana zaki" ta ce "Ni ban san wani Al'ada ba" Surry ta zare ido sai ba tace komai ba, ta shiga lodar kayan shafawa ta sakawa cikin jakar Halisa tare da faɗin. "Kada ki kuskura ta gani ko da wasa, idan ta gani ma ki san me za kice kar ki ambaci sunana" Abba Hakimi ganin maganar mai muhimmanci ce ya tattara ya barta zuwa lokacin da za su koma gida ayi a gaban kowa, duk family su san matsayin yarinyar. Yaa Sheikh yana kwance saman gadon hotel ɗin da suka sauka idanunsa rufe kamar mai tunani daga shi sai farar Jallabiya ko barcin ya kasa, har lokacin bai bawa auren muhimmanci ba, balle ya sakawa ran shi nauyi wata ƴar mace ya hau kan shi, iya auren daya san da gaske an ɗaura kuma matarsa ce bisa tsarin addinin Musulunci, na ƴar fillo kam yama mance da shi at all baya tunanin shi. Ya miƙe a hankali zuwa bathroom tare da sakarwa kansa shower ya jima kafin ya fito ɗaure da bathrobe a jikinsa, cikin sauri ya shirya cikin wani kyakkyawar Voyel mai manyan zane maroon colour ya ɗora farar Alkyabba ya wani irin sahihin kyau kamar Prince Hamdan bin Mohammed. Ya fito cikin parlourn ɗakin ƙamshin Roja ya cika ko'ina a wajan wanda ya jawo hankalin Khalil dake waya da Oum Juwairah ya ɗago kai bai san lokacin da ya ce "Masha Allah" duk rashin tsaurin idon mutum ba zai iya tsayawa gaban Yaa Sheikh ya yi ba, Ilhamar da Ubangiji ya bashi ta musamman ce, a kallo ɗaya yake dagula lissafin mutum. Yaa Sheikh da jikinsa ya bashi kallon shi ake ya ɗago kai suka haɗa idanu da Khalil ya kafe shi da ido alamar lafiya? Wannan kallon fa? Khalil ya shafa kai sbd Kunya ya ce "Muje ko?" Yaa Sheikh yana gaba Khalil na bayan shi, cikin nutsuwa yake tafiya har suka ƙarasu wani room a ƙofar room ɗin suka ci karo da wani saurayi rungome da mace wacce take rusa masa kuka kamar ranta zai fita. Yaa Sheikh ya ɗauke ido da sauri a ransa ya ce "Asstagafirullah Yaa Allah" Khalil kuma ya taɓe baki a haka suka fitar zuwa reception na hotel ɗin daidai nan kuma Mai martaba da abokin nasa El-bashir suka fito suma, haka Abba Hakimi da nasa abokan Umar-khan, Ishaq-Hakim, Saif-wazir. Father daman yana can ba Alhj Farouk mahaifin amarya. Jirginsu Yaa Sheikh daban na Amarya da ƴan uwanta da suka yanki tickets daban. A airport suka haɗu baki ɗaya har lokacin Zahrah bata taho ba, Danejo tunda idanunta ya sauka akan jirgi ta gigice tsoro ya kamata. Yaa Sheikh da Abba Hakimi da kuma Mai martaba Ahmad Sarki tare da Father duk suna Vip. Sauran kuma suna nrml waje. Jirginsu ne ya fara tashi babu jimawa Zahrah ta ƙarasu wajan ta sha kwalliya cikin wata lafaya mai kyau da tsada. Tofa kallon ya dawo kan Danejo ta rantse da abin da zai kashe ta ba zata shiga jirgin ba kuka sosai. Wasu nayi mata dry. Da ƙyar Surry ta lallaɓata gudun abin da zai je ya dawo ta zauna kusa da ita. Danejo ta ƙanƙame jikinta wanda yake rawa hawaye na zubuwa daga cikin idanunta ta ce "Na lalashe Dadata na kaɗe, na bushe shikenan zai a shige sama dani" Surry ta ce "ki nutsu Halisa babu abin da zai sameki kinji ko?" Ita dai kuka take when the plane will take off numfashinta ya tsaya cak Surry ta shiga girgizata tana amsar ruwa tare da yayyafa mata da ƙyar ta dawo daidai ta fara yunƙurin amai yaƙi zuba, lokaci guda ta fita hayyacinta jirgin yana wullawa sama ta fara wata uwar ƙara tana faɗin "Na mutu, Wallahi na mutu.." Misalin 4:45 manyan motocin da suka ɗakko dangin amarya daga airport suka shiga parking a harabar gidan Mother. Wasu ƴan uwan Zahrah da yayar mahaifiyarta da ƙanwar mahaifiyarta sune suka kamo Zahrah da aka rufe mata fuska zuwa cikin gidan sauran friends suka bi bayansu. A parlour akai musu masauƙi su gaisa da dangin miji kafin a basu masauki. Jadda dake zaune ta ce "Wai ina matar Gadangar ne sai wasu yamutsastsun fuskoki nake gani?" Ladidi ta ce "Gata nan Zahrah buɗe fuskarki ai miki bayanin dangin miji" Mother dai na zaune hankalinta na can waje guda sai kaɗa ƙafa take. Dr A'isha ma na zaune taci uban kwalliya kana ganinta kasan ba talauci inda take, Yaya Halima ma haka, sai Momi tare da ƴan uwan father, da matar Uncle Haroon. "A meye haka? Alsulhu khair buɗe fuskar uban kowa ya gani" "Ai Hajiya kin san amare da kunya" Jadda ta ce "kaji masifa ko? Waye sa dake wace ke? daga gidan wa zuwa ina?" Ladidi tai shiru amma Jadda ta fara ƙular da ita. "Muhammadur Rasulullah s.a.w wannan ai uwa aka aura Aliyu ba mata ba? Gidan ubawa Aliyu zai kai ɗirkekiyyar matar nan ni kai na ta kusa haifata yau na shiga uku da gaske wannan ce matar Malam ɗin?" Jadda ta faɗa bayan ta saka hannu ta buɗe fuskar Zahrah. Surry na gefe tana danne dariyar dake ranta. "Maryam zo kiga abin al'ajabi yoo Allah na tuba ko ke ai kinfi matar malam kyan gani? Allah sarki Gadanga an haɗaka da uwar mata" sai kuma ta fashe da kuka sosai ta ce "Innalillahi ashe har gashin doki take saka zunubi babba" ta saka hannu ta kama hannun Zahrah ta ce "Wanne tsinannen abu ne wannan kuma?" Ta faɗa tana duba farcen hannun Zahrah. "Haba Hajiya wannan abun duk na mene? Ya daga kawo yarinyar sai cin mutunci?" Jadda ta miƙe ta nufi kan me maganar ta dungure mata kai ta ce "Algunguma ai duk duniya an gama cutar Malam an haɗa shi da arniyya" "Arniyya wacce ira kuma Hajiya?" Ladidi ta faɗa rai ɓace. Jadda ta kunce ɗan kwalin kanta tare dacin ɗamara ta ce "Arniyya ƙatuwa ma, mene bambancin su? ga tafkeken zunubi ba tausayi ba komai aka cirewa doki gashin shi aka saka mata, gata narkekiyya mai idanu a tsakar kai, gashi ta wani ɗashe kamar mace mai shigar sabon ciki Innalillahi masifa ta saukarwa Malam" gaban Zahrah ya faɗi tai saurin rufe fuskarta. Dr A'isha ta fashe da dry wacce tun ɗazo take danne ta. Yaya Halima girgiza kai kawai take kafin ta ce "Kuyi haƙuri don Allah muke ga masauƙi can" Mother hankalinta na kan Danejo wacce take ɗan ɗaga liƙab ɗin fuskarta tana leƙewa da sun haɗa idanu da mother sai ta mayar ta rufe. Babu wanda Jadda bata ciwa mutumcin ba kafin su bar wajan. Mamaki ya kama Ladidi ganin uwar mijin ta Zahrah ci kanku ba ta ce ba. Kwanan su biyu suka koma Yola aka bar Zahrah tare da Halisa. Yaa Sheikh ne durƙushe a gaban Abba Hakimi da Uncle Haroon sai Uncle Bashir ga Mother da Yaya Halima da kuma Momi matar Abba Hakimi. "Ina magana kayi shiru Aliyu?" Abba Hakimi ya faɗa cikin sassauta murya. Yaa Sheikh ya ɗago kan idanunsa ya sauka akan yarinyar da ake nuna masa, ya ƙara duban Halisa da kyau sai yanzu yai mata cikakken kalo ya mai da idanunsa kan Abba Hakimi ya ce. "Wace? kamar ban waye ta ba?" Uncle Haroon yai murmushi yana jinjina halin Yaa Sheikh. Abba Hakimi ya ce "Amma kasan Rugar Bello? Ka kuma san Arɗon rugar ka gane abin ya faru,ka kuma shaida zoben hannunta?" Yaa Sheikh ya ɗan kallin kyakkyawan hannun Danejo wanda yake maƙale da zoben da yake so har ransa nan take ransa ya ɓaci, a lokacin ya tuna everything ya shanye mmkin kamannin da yake gani a fuskar yarinyar, shi kam a rayuwa ko zai so mace ai banda ƴar cikinsa wannan gwaliliyyar yarinyar bata shige raino ba, ita za a kalla ace wai matarsa? Shi kam ya zai yi da mata biyu ba?. Yai shiru yaƙi bada damar da za a karanci halin da zuciyarsa ke ciki. Uncle Bashir ya ce "Da alama ya fahimta" Abba Hakimi ya ce "Halisa maza je aikyan yayar taki kada taga kin daɗe" ta miƙe da sauri domin daman a takure take Yaa Sheikh duk ya firgitar da ita. Abba Hakimi ya ce. "Ba wasa muka zauna yi ba, jibi zaka shige Madina kafin nan kana son yarinyar nan ko baka son ta?" Yaa Sheikh yai shiru ya kasa fahimtar abin da suke nufi dashi, shi kam duk ranar da ya ce yana son mace ai sai ya yi azumin kaffara shi ya sa har abada ba zai taɓa cewa yana son wata ba. Ya girgiza kai a hankali "Baka son ta?" Cewar Uncle Haroon. Bai kalli Uncle Haroon ba ya kalli Abba Hakimi. Abba Hakimi ya gyara zama yana sakin murmushi ya ce "Ka shirya sakinta? baka san me gobe zata haifar ba?" Yaa Sheikh ya riƙe hannunsa da kyau yana girgiza kansa harshen shi na harɗewa ya ɗan motsa ƙafarsa ɗaya cikin In-ina ya ce "Ha...hhh...har... Har abada ba ba ba zan zan so ta ba" _IDAN BA KE it's paid book ₦500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616..... Isn't free if you read for free🤷🏾‍♀️_Yaa Sheikh ya faɗi hakan kai tsaye. Abba Hakimi ya ce "To kafin nan muyi wata game mana, idan kaci ni kuma nayi al'ƙawarin raba aurenku har abada, ka zauna kai ɗaya da ita Zahrah tunda ba a son Ƴar fillo" Mother ta juya ta kalli Yaa Sheikh kafin ta ce. "Yanzu meye laifin yarinyar? ba tafi wacce aka haɗaka da ita ba? to a karo na farko zan faɗa maka zama da wannan babu fashi a wajanka Aliyu" Uncle Haroon ya ce "A'a Barrister labarin aure baza kici haka ba, ana yin aure dan farin ciki da kwanciyar hankali,idan ba yajin yarinyar a ran shi bai kamata a takura masa wajan zama da ita ba, zai iya amincewa bisa takurar kuma ya cutar da ita, a dai bi komai a hankali" Mother ta girgiza kai ta ce "Uncle Haroon ka rabu da Aliyu, tunda ya amince dana Zahrah zai amince da wannan ɗin ma sai ya tattara su tafi can Madina su ƙarata" Yaya Halima ta kalle su baki ɗaya kafin ta ce "duk ba Wannan ba, na tambayi Zahrah a sigar wasa cewa wannan ƙanwarta ce? Sai ta ce mini wai ƴar aiki aka samu mata, That's the position of a maid in Aliyu's house" Dr A'isha tai murmushi ta ce "Matar gida ko ƴar aiki? dama a ɗauke ni aikin gidan Aliyu naga yadda zaman zai kasance" Yaa Sheikh ya ɗaga kansa a hankali kamar zai kalli Dr A'isha sai kuma ya fasa ya mai da kan ƙasa. Sai a lokacin Uncle Bashir ya ce "Ya kamata kada ita Zahrah tasan cewa itama yarinyar matar Yaa Sheikh, a barta ta tafi da ita a matsayin ƴar aikin kamar yadda tazo da ita da manufar hakan" "I also agree with this decision, she took it as her worker" cewar Dr A'isha. Abba Hakimi ya sauke numfashi yana duba lokaci,bayan nazartar maganganun sauran ya ce. "Na amince baka son ƴar fillo, suma sun yarda da hakan, zaka tafi da ita can gidanka dake Madina matsayin matar ka kuma ƴar aikin matar ka, zaka iya zuba idanu matar ka ta zama baiwa a cikin gidan aurenta, ra'ayinka ne, Ni bance kaji tausayin ta ba, kawai ina son ka riƙe mini ita a wajanka na tsayin shekara ɗaya ciff, ka sata makaranta, ni bance ko sau ɗaya kayiwa Halisa Danejo kallon matar ka ba, ita ɗin kamar ajjiya ce na baka, ka dawo mini da ita shekara guda, kada naga wani sauyi a tare da ita, ka tabbatar yadda take budurwa a haka ka dawo mini da ita, nayi maka al'ƙawarin shekara nayi zan raba auren naku rabawa ta har abada" gaba ɗaya mutanan parlourn suka zubawa Abba Hakimi idanu, su basu ga dabarar haka ba, sun san ko shekarar biyar aka bawa Yaa Sheikh there is nothing he will do, there will never be any change from him, balle ya furta da bakin shi ya ce yana son ta,That will never happen. Abba Hakimi ya gyara zama sosai idanunsa akan Yaa Sheikh ya ce "Amma Wallahi Wallahi Allah kenan Aliyu ban taɓa rantsuwa akan ka kamar haka ba, shekara guda tayi ka dawo mini da yarinyar nan saɓanin yadda nai tunani zaka sha mamakina, kai ba yaro bane ka fahimci mai nake son faɗa maka, babu dalilin da zai sanya ka lalata budurcin yarinya kuma ba son ta kake ba, This is a deal" Uncle Bashir ya ce "Amma Abba Hakimi wannan deal ɗin bai tsauri ga Malam ba?" Abba Hakimi ya ce "Ba kaji kai ma kace Malam ba? Yaa Sheikh zai iya ɗaukan wannan game ɗin" Murmushi Uncle Haroon ya yi kai tsaye ya yarda da abin da Abba Hakimi ya zartar cikin fara'a ya ce "To idan haka ne ina tsagin uwar gidan Halisa, za muje matsayin masu aikin gida kawai" Uncle Bashir ma ya ce "Ni ma dai ina team ɗin uwar gida" yaya Halima tai murmushi ta ce "Ikon Allah, to ina team ɗin Aliyu koma mai zai faru ya faru she is his wife matar shi ce babu laifi" Dr A'isha ta ce "Ni dai ba zan zaɓi team tun yanzu ba, sai naje Madina naga yadda zaman zai kasance" Idanun Yaa Sheikh ya yi jajir shi kam a rayuwa mai Abba Hakimi ya mai da shi? Ina ruwan shi da wata ƴar fillo balle har yaje gareta matsayin miji mai buƙatar hakƙin shi wajan matarsa? Zai bawa kowa mamaki. Miƙewa ya yi a hankali zai bar wajan Abba Hakimi ya ce "No tayaya ka taɓa ganin anyi deal ba saka hannu, maza saka hannu a wannan dairy ɗin" Yaa Sheikh ya kalli Abba Hakimi da kyau, shi kam Abba Hakimi ya ɗauke kan shi alamar bai gane meke nufi ba. Cikin sauri ya saka hannu tare da saka suna da date da kuma time. Yana gamawa ya juya jiri na ɗaukan shi sbd ciwon kai ya nufi Part ɗin shi. Abba Hakimi yabi bayan shi da kallo a zuciyarsa ya ce "let's see ko Aliyuna waliyyi ne" Wajan ya yi shiru kowa da abin da yake tunani a ran shi, Mother na tunaninsu yadda zata cusa Halisa a zuciyar Yaa Sheikh, kallo ɗaya ta yi wa yarinyar hankalinta ya kwanta da ita, kawai dai ta fahimci bakin yarinyar babu control kamar ba a gasa mata shi ba. Yaya Halima kam gani take kamar Yaa Sheikh ba zai iya tsallake wannan gasar ba, lura da yanayin Halisa da komai sai tafi Zahrah jan hankalin ɗa namiji kowa zaman zai kaya ohhu! "Kada a bari Jadda da Engineer su san maganar auren wannan yarinyar Halisa da Yaa Sheikh, mu bari muga abin da hali zai aga yanayin zaman maybe a samu sauyin ra'ayi game da Yaa Sheikh akan yarinyar" cewar Uncle Haroon. Abba Hakimi ya miƙe tsaye haka Uncle Haroon da Uncle Bashir sukai wa Mother sallama. Bayan tafiyar su yaya Halima ta kalli Mother ta ce "Yanzu me zaki Barrister?" Mother ta girgiza kanta idanunta akan wayarta tana neman contact ɗin wata mata ta ce "me zan yi kowa yaya? ga Abban Sheikh nan ya gama magana" ta faɗi hakan tana danna call. "Tun ɗazo da nace ki kawo mini bottle water ina kika tsaya?" Zahrah ta tambayi Halisa tana zare mata idanu. Ta turo baki gaba ita tsakani ga Allah take son faɗawa Zahrah abin da ta fahimta wajansu Abba Hakimi. Zahrah ta ce "ba dake nake ba dan ubanki?" Da sauri Halisa ta kalli Zahrah bakinta na rawa ta ce "Baffana kika zaga? Ya mutu fa?" Wani tsaki Zahrah taja ta ce "Idan ya mutu ni na mutu? Waye shi da ba za a zage shi ba" Halisa ta jima tana kallon Zahrah idanunta ya yi jajir ga abin masifa babu halin yi sbd ka shaidin Dada a gareta. "Matsa ki bani waje ai dama har uwar suka haɗu suka mutu Kinga baki da sauran wani gata kiyi mini aiki hankali kwance" Halisa ta juya da gudu tare da fashewa da kuka hannunta a fuskarta tana karewa. karo suka ci da Maimoon data ɗakko warmers ɗin lunch wanda akace ta kaiwa Zahrah, Maimoon ta ja baya da sauri tana faɗin "Subuhanallah ya akai kike kuka haka ke dawa?" Halisa ta kasa kuka sai shassheƙa da zata iya ita gida kawai zata gudu wallahi. Maimoon ta ce "Ok ya isa daina kukan jirani a nan wajan kinji?" Ta ɗaga kai a nutse alamar "to". Zahrah na kwance waya a hannunta suna vedio call da Deen wanda gaba ɗaya ba vedion Allah da Annabi bane, ita dai Maimoon taji wani sauti kamar gurnani da sauri Zahrah taja duguwar rigarta zuwa ƙasa tana rufe wajan data buɗe. She pretended not to notice what she had done. Tana ajjiye warmers zata juya Zahrah ta ce "Hey you" Maimoon tai banza kamar ba taji ba. "Ina magana" Maimoon ta juya kaɗan suka haɗa idanu ta ce "dani kike?" Ta ce "to waye a ɗaki?" Maimoon ta ce "Huh na ɗauka kina magana da wayar hannun ki ce" Zahrah ta sakko daga kan gadon ta ce "what the do you mean by that?" Maimoon tai shiru can Zahrah ta ce "What's your name?" "Maimoon" ta bata amsa Zahrah ta ce "Ok At least you have to respect me ni matar yayanki ce, kin shigo bedroom without my permission da muna tare Yaa Sheikh fa?" Maimoon ta ware idanu sosai ta ce "Yaa Lee a bedrooms ɗinki? Shhhh" tana faɗin hakan tai waje da sauri. "Kan uba wannan yarinyar sai na saita mata zama kalli Yadda take mayar mini da matar tani?" Waya ta ɗauka ta shiga kiran Surry. Maimoon ta kalli Halisa wacce ke zaune a ƙasan carpet ta ce "Sister tasu muje part ɗin mu" Halisa ta girgiza kai Maimoon ta ce "Anty Zahrah ta ce mu tafi tare zuwa dare sai ki dawo" ta miƙe tana faɗin "Ita ta ce haka?" Maimoon ta ce "ita ce mana" hannunta ta kama suna zuwa Main parlour El-bashir na tashi tare da ɗaga waya ya nufi ƙofa, Halisa ta bi bayan shi da kallo ta ɗauka Balarabe ne. Maimoon taja hannunta har zuwa part ɗin su, Zeefa da auta Fattoumah suna zaune ganin Halisa yasa Auta Fattoumah faɗin "Wow yaya Moon wannan kyakkyawa ce She's very beautiful she looks like bro El" Maimoon ta ce "to sarkin surutu" ta zaunar da Halisa ta shiga ɗakko mata su ice cream da chocolate amma sam Halisa taƙi ce sbd bata saba dasu ba, ta ɗago kai a hankali ta ce "bana cin irin wannan" Nazeefa ta ce "To sai me?" A hankali kanta a ƙasa ta ce "Kindirmo nake shu" a tare suka zare idanu tare da faɗin "what?" Tai shiru tana kallon su can Maimoon ta ce "Zeefa haɗa mata ruwan wanka a bathroom bari na kawo mata kindirmon" tana faɗin hakan tai waje har lokacin Maimoon ta kasa mance abin da idanunta ya gani a bedroom ɗin Zahrah. Cikin sauri Zeefa ta haɗa mata ruwan wanka tare da nuna mata komai a toilet ɗin da yadda ake amfani da su. Suna bakin toilet ɗin suka ji ana knocking "Halisa duba kiga waye?" Kamar ba zata ba sai ta nufi ƙofar jiki a sanyaye zagin da Zahrah tayi mata har yanzu damun zuciyarta yake. Halisa ta tsaya bakin ƙofa ta rasa me za ta ce can dai ta ce "waye?" Ta faɗa cikin ƙasa da murya. El-bashir ya gyara tsaiwa hannunsa riƙe da waya da kuma chocolate ya ce "Buɗe ki gani mana?" Halisa ta murguɗa baki tana ƙoƙarin buɗe ƙofar Zeefa ta ce "jeki kiyi wankan bari na buɗe ƙila Maimoon ce" Halisa ta juya zuwa bathroom ba tare da ta ce komai ba, Zeefa na buɗe ƙofar taga El-bashir tsaye fuska ɗaure ta ce "Yaya El" ya wurga mata harara ya ce "wace take tambayar waye?" Zeefa ta juya ta kalli ƙofar bathroom ta ce "Laa Halisa ce bata sanka bane" ya ce "I'll break her legs" chocolate ya bawa Zeefa ya juya yana faɗin "Kira mini Fattoumah" ya nufi Main parlour Mother dake zaune ta ce "Yau zaka shige ne?" Ya ce "I don't think so.. sai abin da Mai martaba ya ce" ta ce "Ohh abokin Mai martaba". Washegari Zahrah na zaune ta caɓa ado cikin wata atamfa mai kyau ruwan ƙwai ta yafa mayafi babba kamar ta Allah. A hankali ta fito zuwa Main ta samu Mother zaune ita da Jadda suna hira sai Maimoon Zeefa da Auta Fattoumah suna makaranta. Zahrah ta durƙusa ta ce "Ina yini Mother?" Mother ta ce "kina lafiya ya kwanan baƙunta?" Zahrah ta ƙara sunkuyar da kai alamar kunya ta ce "Allahamdulillah, daman cewa nayi bari nazo idan da aiki nayi" Jadda da bakinta ke rawa ta ce "Allah ya yi gutsi gutsi da maƙaryaci" Zahrah taƙi kallon Jadda. Mother ta ce "Ayyah jeki ki huta ba aiki" Zahrah dai ta kasa riƙe abin da yake ranta ta ce "Yaa Sheikh fa? daman ina son gaishe shi ne" da hannu Mother ta nuna mata wani part ta ce "zaki iya samun shi can" ta miƙe da sauri ba kunya ta nufi Part ɗin Yaa Sheikh. Mother ta ce "Maimoon kira mini Halisa yanzu" Maimoon ta nufi part ɗin Zahrah ta samu Halisa sai zuba kayan Zahrah take cikin trolley bag tayi saurin riƙe hannunta ta ce "Kizo Mother na kiranki" Halisa ta ce "Bari na ƙarasa aikin Anty" Maimoon ta ɗaga ta tsaye ba tare da ta ce komai ba ta jata zuwa waje. Bata samu Mother a parlour ba sai suka shige bedroom ɗinta tana zaune bakin gado. Mother ta ce "shigo Halisa, Maimoon jeki ko" Maimoon ta juya Halisa ta shiga kanta a ƙasa haka kunyar Mother tai mata nauyi taji kunyarta ta ce "Saki jekin ki zo nan" ta kama hannunta tare da zaunar da ita bakin gado ta ce "Yaya sunanki ma?" A hankali ta ce "Halisa Danejo Rome" Mother ta jinjina kai ta ce "Ok Zahrah ƴar uwar ki ce?" Ta girgiza kai ta ce "A'a wai aikatau zan mata" ta faɗi haka a taƙaice. Mother ta jinjina kai sosai ta ce "Saurare ni da kyau, Zahrah matar Yaa Sheikh ce Wannan babban mutumin da kika gani fari dashi?" Halisa ta ce "Balarabe?" Mother ta ce "Yawwa shi" haka kurum idanun Halisa ya cika da ruwa Mother ta ce "Shi ne mijin Zahrah kuma kema mijinki ne, dan haka ke ba ƴar aiki bace matar shi ce ke, kamar yadda Zahrah take matar shi haka kema kike matar sa" Halisa tai ta kallon Mother har lokacin idanunta cike yake da hawaye da gaske Balarabe shi ne mijin Zahrah?. Mother ta katse mata tunani da faɗin. "Kece uwar gida, aurenki aka fara ɗaurawa sannan na Zahrah, na kira ki muyi magana sbd Yaa Sheikh ya ce baya son ki" da sauri Halisa ta miƙe tsaye hawaye na zubu mata bakinta na rawa ta ce "Amma ni ina son shi ai..... Ni ina team Yaa Sheikh ku fa? 08119237616 Paid book ₦500"Kin san shi ne da kike son shi?" Mother tayi tambayar idanunta akan Halisa wacce hawaye ya gama cika mata idanu. Ta kasa cewa komai amma bakinta bai bar rawa ba, ganin yanayin ta ya sanya Mother sassauta murya ta ce "Kina da ƴan uwa a garin nan?" Ta girgiza ta ce "Aradu babu" "Ok to ki Saurare ni da kyau, listening to me..." Tsayawa tai da maganar idan ma tayi ta san a banza, Halisa does not speak English, let alone understand what is being said. Ganin bata da wani option wanda ya shige tayi magana da harshen da Halisa zata gane ya sanya Mother tattara nutsuwarta ta ce "Ki ɗauke ni matsayin uwa kafin ki koma gida, zan riƙe ƙo kamar ƴar dana tsuguna na haifa, da farko ki yarda cewa ke matar Yaa Sheikh ce Balarabenki kamar yadda kika ce ɗin, Kinga zoben hannunki shi ne sadakinki, abu na biyu kada ki kuskura koda wasa ki faɗawa Zahra kema matar Yaa Sheikh ce, duk aikin data saki kiyi zaki samu lada albarkacin igiyar auren dake kanki, duk abin da Yaa Sheikh zai ce kiyi just do it ina nufin kiyi kai tsaye, ba zai cutar dake ba, infact ai kin riga da kin san shi ko?" Halisa ta ɗaga kai da sauri kuma ta ce "Kuma ina son shi ai, ina ganin shi idanuna idan ina barci" Mouth ta ce "Good, a kullum yana tashi tun ƙarfe 4 na dare baya komawa barci sai ƙarfe 12 sbd ƙarfe 8 yake zuwa wajan ɗaliban shi, duk inda 12 tayi ya dawo gida, bai damu da abinci ba sosai ba zai taɓa cewa yana jin yunwa ba, tsakanin azahar da asr yana barci idan bai ba, ciwon kai yake sosai, sannan baya rabo da black tea da zuma a ciki, duk ranar Alhamis da Litinin azumi yake, yana son ƙosai sosai" Halisa ta saki murmushi tare da riƙe hannun Mother ta ce "Innalillahi ƙoshai aradu daɗi akwai burudi to? Wayyo Allah zanci ƙoshai na mure" dariya Mother zatai ko takaici bata son duk wannan shirman a wajan Halisa.. "Zaki samu abin da yafi ƙosai ba, amma can idan kina shirme gidan yankan kai suke kai mutum, ki zama a nutse, bayan haka yana son abincin gargajiya tuwo, dambu da sauran su dai, ki tabbata kina wanka sau biyu zuwa uku a rana, idan ba haka ba Yaa Sheikh kurarki zai yi daga gidan shi, kuma kishiyarki ta rabaki da mijinki har abada" Idanun Halisa ya sauya kala jin abin da Mother ta ce. Bayani Mother taci gaba dayi mata cike da ƙwarewa ta ɗora da faɗin. "Kina jin alamun ya dawo, ko babu abin da zai miki kije wajan shi kice kanki ke ciwo ko ya koya miki karatu, zan zuba miki kayan amfani masu kyau ki tabbatar kina using dasu amfani kinji?" "Zan yi ai, amma dai ba zata ƙwace mijina ba ko?" Mother ta haɗiye dryar data zo mata ta ce "Akan me? Idan kina yin abin da nace bata isa ta ƙwace miji ba, amma idan bakya yi uhm ko ganin shi kin dai na yi, yawwa sai gaisuwa kullum da safe kije ki gaishe sa, da yamma haka da kuma daddare, akwai lokacin da yake ciwon kai bai azabar zafi ganin shi har ɗauke yake ya zama kamar makaho, zan faɗa miki abin da za ki yi idan ciwon ya tashi, yanzu maza jeki gama aikin ki za kuje a gyara miki wannan gashin kan" Halisa ta miƙe tsaye kanta a ƙasa ta ce. "Na gode" "is nothing jeki daughter" sai da taje bakin ƙofa ta juya a hankali ta kalli Mother idanunta ya yi raurau da hawaye ta ce. "To yaushe zan faɗawa ina da miji? kuma yaushe zan fara dama masa fura" a ranta Mother ta ce "na shiga uku, wannan za ayi sirri da ita kam?" A file ta ce "zan faɗa miki ranar jeki" ta juya ta fita tana ayyana cewa da gaske dai Balarabe mijinta ne. Kai tsaye ɗakin Zahrah ta koma taci gaba da shirya mata kayan da zata tafi Madina dasu, zuciyarta cike da tunanin maganganun da Mother ta faɗa mata. Ta sauke ajjiyar zuciya a fili ta ce "Wallahi kyakkyawa da shi, Allah ya sa na zama kamar shi" ta faɗa tana taɓa fuskarta sai kuma ta miƙe da sauri tana nufar inda mirror yake, a hankali ta shiga ƙarewa kanta kallo, bata hango nata kyan zallar kyan da Rabbil izzati ya yi wa Yaa Sheikh idanunta ke hangowa. Tsaye tayi a bakin ƙofar da zata kaita parlourn Yaa Sheikh tun a nan kuma ta gane Yaa Sheikh daban yake a gidan, tsarin shi da yadda yake tafiyar da rayuwar shi, bata taɓa shakkar tsayawa gaban namiji ba, amma a yanzu tsoro da fargabar tsayawa gaban Yaa Sheikh da yadda kaifin idanun shi ke tasiri a zuciyarta sun gama cika Zahrah. "No Zahrah Aliyu mijinki ne, ki koyi zama da shi kafin ki fara juya rayuwar shi tamkar waina a tanda, dole ragamar rayuwar shi ta dawo tafin hannunki" wata zuciyar ta shiga gargaɗin haka, jikinta ta kalla tsaf duk da kasancewar ciki ne jikinta amma ƙirjinta yana kwance ya manne da fata, ita kalar halittar ce ko kuma garin yawan ta zubar aka gama lalata halittar da Ubangiji ya yi mata wacce kuma iskancin kawai ta sani sam bata san tsaunin da zata hau tabi ba, zuwa tubalin da zai gyara mata garkuwar jikinta. Ta tura ƙofar a hankali ƙamshin air-con da wani air freshener sune suka daki hancinta, shigar ta parlourn ya yi daidai da sautin karatun Yaa Sheikh dake ratsa cikin wajan har ya kawowa kunnenta farmaki. Yana zaune saman kujera ya ɗora farar ƙafarsa akan table idanunsa rufe a haka yake motsa bakinsa yana karatun cikin baiwar da Ubangiji ya bashi ya sahale masa yin karatun ba tare da harɗewar harshe ba.. Zahrah ta bi farar Jallabiyar dake jikinsa da kyau da kyau, zuwa kansa dake rufe hirami hannunsa guda ɗaya riƙe da carbi yana ja. Ta nemi wajan a kujerar dake kusa da shi ta zauna tana fari da idanu tare da juya jiki amma ta kasa yi masa magana balle gaisuwa. A jikinsa yaji ana kallon shi bambancin ƙamshin turaren da bai taɓa ji a gidan yasa ya fahimci ko waye ba ɗan gidan bane. Zahrah ta gyara murya ta ce. "My Excellency" "Shhhh" Yaa Sheikh ya furta a ran shi gaba ɗaya murya ko a maza bai taɓa jin mai amonta ba. Ganin ya yi shiru ta ɗauka ko bai ji mai tace bane?. "Daman nace bari nazo muga juna muyi hirar ku mintuna biyar ne kafin mu tafi gidanmu" still shiru ya yi mata, ta miƙe tsaye cike da kwarkwasa ta ƙarasa har zuwa inda yake tare da zama kan armchair ta saka hannu ta shafi fuskar shi kaɗan zuwa dugun gemun shi ta ce. "You're just quiet, but I know you hear what I'm saying" a wannan lokacin Yaa Sheikh ya ɗauka gangar jikinsa zata ƙaryata zuciyarsa, amma sai yaga abin ya zama diro, ya ƙara tabbatarwa lallai to da gaske bashi da cikakkiyar lafiya irin ta cikakkun maza, mace ƴar 32 tazo har inda take suyi very close da juna amma ko tsigar jikin shi bai ji ta motsa ba, balle ya yi zaton zai ji abin da Khalil ke masa surutu akai. Zahrah ta kai hannu zata ƙara jan gemun shi ya buɗe narkakkun idanunsa na mai kama da mai jin barci. He didn't give her a full look, because looking at people is not his style. Bai sake kallonta ba ya miƙe tsaye yana goya hannunsa a baya, ya nufi bedroom ɗinsa, Zahrah ta ce "Amma dai ni matarka ce ka sani?" Ya tsaya cak ba tare daya juya zuwa gare ta ba, kamar zai magana sai kuma ya fasa ya shige cikin bedroom ɗin, Zahrah tabi bayan shi da kallo me hakan yake nufi? Ta ɗauka zuwanta gare shi zai nuna wata buƙuwa ta miji ga matar shi sai kuma taga saɓanin haka. Ta juya ta sauri Dr A'isha dake Main parlour tabi Zahrah da kallo wato halitta kala-kala ce, ita bayan shekaru da zubin halittar jikinta har wani tumbi take dashi kamar namiji?. A fili Dr A'isha ta ce "Allah ya kyauta" tana faɗin hakan ta miƙe zuwa bedroom ɗin Mother itama a yau take son shigewa gidan mijinta. Zahrah na shiga bedroom ɗinta ta saka ƙafa ta murje yatsun Halisa cikin faɗa ta ce "ke kam wacce jakar yarinya ce? kina ganin mutum ba zaki matsa daga hanya ba?" Halisa da idanunta yayi jaa sbd zafin da yatsun suke mata, ta kalli Zahrah ta ce "Kiyi haƙuri" ta saka hannu ta ɗauke Halisa da mari ta ce "haƙurin uwarki? Ni dai na shiga ban ɗauka fulani mahaukatan gaske bane sai yanzu" gigicewar da Halisa tayi yasa ko gabanta bata iya gani, ba a taɓa yi mata mari da tafkeken hannu kamar na maza irin wannan ba. Ruɗewar da tayi yasa ta nufi wata ƙofa a tunaninta part ɗin su Maimoon ne, tana fita taci karo da mutum a hanyar zuwa swimming pool. El-bashir yaja baya da sauri yana kallon farar kyakkyawar yarinyar data fito hannunta a fuska tana shassheƙar kuka, ya taɓe baki yana ƙoƙarin shigewa Halisa tayi saurin kama hannunsa cikin matsanancin kuka ta ce. "Hamma fuskata zata cire wayyo Dadata fuskata ka taimaka mini" sai murza fuskar take da hannunta guda ɗaya, ɗaya kuma ta riƙe hannun El-bashir da shi. Hannunsa ya sanya zuwa hannunta dake fuskarta cikin ƙasa da murya ya ce "Sorry" ya faɗi hakan yana ɗauke hannunta. Cikin daƙiƙo ya nemi ji da ganinsa ya rasa, tunaninsa ya tsaya cak, ya zama kamar wani stateu yana ganin tarin kamanni amma bai taɓa cin karo da zallar kama irin ta yau ba. Hannunsa na rawa ya kama fuskar Halisa da kyau yana ƙare wa hukuncin Rabbil izzati ido, ita dai kuka take sosai ba ƙaramin gigita marin ya yi ba. El-bashir ya sauke numfashi yana daidaita nutsuwarsa tare da haɗiye mamakinsa, ko ita ce yarinyar da Khalil ke bashi labari?. Ya shiga goge mata hawayen fuska tare da faɗin "ke dawa? Wace ke? Mene sunanki?" Ya jera mata tambayoyin. Halisa ta marairaice fuska tare da shagwaɓewa ta zama wata narkakkiyya hannunta cikin baki alamar shagwaɓarta a zahirance take bata ɓoyewa. "Uhm magana nake" tai saurin ɗaga kanta zuwa fuskar shi, baki da hanci ta saka ta kasa cewa komai El-bashir ya ƙifta mata idanu tare da ware su ya ce "Keee. "Wallahi kama muke, kai ma kasanni ya naga fuskarmu iya ɗaya?" Ta ƙare maganar tana ƙoƙarin taɓa fuskar shi domin tabbatarwa. El-bashir ya haɗe fuska ya ce "Bani amsa? Wace ke?" Ta tura baki gaba ta ce "Sunana Halisa Danejo Rome, kuma ni matar Balarabe ce" El-bashir ya ware idanu ya ce "What are you married? Waye Balarabe?" Ta ce "Ace kada na faɗawa kowa sai lokaci ya yi amma dai ni zan dinga yiwa Matar Yaa Sheikh aiki, kuma ance jibi zamu tafi ko'ina ne, haka.....," "Heyyy will you shut up your mouth caaaaa haba" ta tura baki gaba fuska duk a shagwaɓe taƙi cewa komai. Ya gyara tsaiwa ya ce "Oh Halisa, dake Yaa Sheikh zai tafi ko?" Tayi saurin kallon shi ta ce "Eh" ya ce "Ok good, daman shi ya aike ni yanzu, kuma ke ya ce na bawa aikin domin ya yarda da hankalinki" tamkar wacce bata yarda da maganar El-bashir ba haka take kallon shi, wanne aike? daman yana sane da ita kenan yana son ta shi ma?.. "Riƙe wannan, ya ce ki ɓoye wajanki har sai kunje Madina, maganin shi ne, zaki zuba masa a cikin shayi ko abinci, kada ki bar kowa yasan da abin a wajanki, idan ba haka ba zai kureki daga gidan shi kinji?" Ta ɗaga kai ta ce "Amma bari na bawa Mother ajjiya ko?" Ta faɗa zata juya ya yi saurin riƙe hannunta ya ce.. "Ai har Mother ba a so tasan da maganin a wajanki, ki zama mace mai sirri ki tabbatar kin zuba masa, idan ba haka mutuwa zai gaba ɗaya" ta shiga girgiza kai tsoro da fargabar abin da El-bashir ɗin ke faɗa suka firgitar da Halisa ta ce "Wallahi ba zai mutu ba, ba zan barshi ya mutu ba, ni da kai na zan zuba masa maganin" wani irin kyakkyawan murmushi mara sauti El-bashir ya yi kafin ya ce "Good girl" ganin ya yi gaba ta ce. "Kai ya sunanka to?" "Ki ce El" ya faɗa a taƙaice tayi saurin faɗi "Ban iya faɗa ba, tunda muna kama ɗaya zan dinga cewa Hamma ka yarda?" Ya tsaya tare da juyawa wani abu nayi masa yawo akan abubuwa da yawa, kalmar kamannin data faɗa suka ƙara dagula masa lissafi. Ya jinjina mata kai tare sakar mata murmushi. Halisa bata da riƙo lokaci guda ta mance marin da Zahrah tayi mata. Cikin sauri ta ɓoye maganin da El-bashir ya bata tare da juyawa tabar wajan. Barinta wajan ya sanya Yaa Sheikh sauke numfashi tare da zame idanun shi daga saitin wajan da Halisa da El-bashir suka tsaya, yana mai ɗan girgiza kai tare da ya motsa fuska. Father ya kalli Yaa Sheikh ya ce "Kaje ka duba visa ɗin Zahrah da Yarinyar da zatai mata aikin" Yaa Sheikh ya jinjina kai alamar "to" tare da miƙewa sai da ya je bakin ƙofa Father ya ce "Ka shiga part ɗin nata, da kanka ba aike ba kace ta shirya kuje tare, matarka ce saɓa mata tamkar zaɓa mini ne, kai ne mai auren amma ni ne mai zartar da hukunci ko da wasa ka sake Zahrah ta kawo ƙararka za kaga yarda za mu yi dakai Aliyu, kaji tsoran Allah kai Malami ne kasan hakƙin aure da sauke nauyin miji ga mata, kada ka yarda saboda baka son ta kace zaka tauye hakƙinta wallahi wallahi Allah Aliyu akan aurenka da Zahrah sai nayi maka baki" Yaa Sheikh ya juya da sauri ya kalli Father kalmar shi ta ƙarshe ta daki zuciyar Yaa Sheikh, kansa a ƙasa ya nufi wajan Father yana zuwa ya zube a wajan ƙafafuwan Father, cikin ƙasa da murya mai tarin nutsuwa da Ilham yana mai ɓoye abin da yake ransa a kame ya ce. "Kada ka aibata ni Abbi, zan riƙeta, ka saka albarka a kai na a karo na farko na rayuwata Father" Father ya kalli Yaa Sheikh kafin ya ce "Kaje Allah ya yi maka Albarka" Yaa Sheikh ya kifa kansa a ƙafar Father farin ciki ko baƙin ciki zai ji? Yau Father ya saka masa albarka dalilin Zahrah?. "Ka tashi kaje nace, kuɗi ne kama fini shi me zan maka? Ko akwai abin da ka ke buƙata?" Yaa Sheikh ya yi shiru can kuma ya miƙe tsaye tare da yin waje. A hankali ya haɗu da Maimoon da Halisa shi sam ba zai ce yaga Halisa ba domin direct idanunsa ya sauka akan Maimoon ɗin. Part ɗin Zahrah ya nufa lokaci wata farar riga ce a jikinta iya gwiwa waya riƙe a hannunta ta ce "No Deen ka bari muyi 1week a Madina sai ka zo ɗin? I will arrange a day when we can meet, I don't want to be recognized....," Ƙamshin Roja da hancinta ya shaƙa yasa tayi saurin ajjiye wayar tana duban door way, idanunta ya sauka akan Yaa Sheikh dake tsaye bakin ƙofar yaƙi shigowa ciki. Zahrah duk ga ruɗe bata tsammaci ganin shi a yanzu ba, ta sakko tana yin murmushi tare da girgiza jiki ta ƙarasu tana faɗin "My Excellency" Yaa Sheikh ya duba ta da kyau, har zai larabci ya tuna ba lallai tana ji ba, shi kuma he's not interested akan english. "Ki saman waje, mota" ya faɗa a taƙaice cikin rarrabe murya. Bai aune ba yaji Zahrah ta shige jikinsa tare da rungome shi. Bakinsa na rawa cikin rashin ya ce "Asstagafirullah, Allah na tuba" ya faɗa yana zame jikinsa tare da barin part ɗin da sauri. Yana zaune a bayan mota idanun shi rufe yana ta Asstagafirullah akan rungumar da zara tai masa, ba wani sauyi a jikinsa amma that is forbidden. Umar-khan ya ɓoyewa Zahrah bayan mota har zata shiga sai kuma ta tsaya ganin kamar maca ce a gaban motar, ta tsaya tana faɗin "Umar-khan wace wannan a gaban motar mijina?" Umar-khan ya kalli Halisa wacce take sanye da wata Marron ɗin turkish Abaya wacce Mother ta bata, Maimoon kuma tai mata rolling vail ɗin abaya a fuskarta, ƙaramar round face ta fito sosai farinta ya ƙara bayyana, gashin idanun nan lub zara-zara dasu idan ba magana tai ba, ba zaka taɓa cewa ƴat fillon Rugar Rome bace, ta kame kanta sosai bisa gargaɗin Mother. Umar-khan ya danne dariyar dake cin sa ya ce "Motar mijinku dai" "me kace?" Cewar Zahrah ya ce "cewa nayi baki gane wace ba?" Ta girgiza ta ce "Idan na gane wace mene amfanin tambayar?" Yaa Sheikh dai duk abin da suke cewa yana jinsu bai magana ba. Umar-khan ya ce "Ikon Allah, Ƴar fillo ce fa? Mai aikinki ina nufin Halisa ce a gaban motar garkuwarta" wani irin bugawa ƙirjin Zahrah tayi ta ƙara leƙa motar Halisa ta sakar mata wani cute smile ta ce "Laa Anti ni ce fa, mai aikin ki Halisa Danejo Rome" wani jiri ya ɗebi Zahrah tayi saurin riƙe motar a cikin ranta ta ce "Da sake wallahi ba zai yiwu ba.... _IDAN BA KE it's paid book... ₦500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616. If you read for free😂🤷🏾‍♀️_Umar-khan ya katse mata tunani da faɗin "Ki shiga muje" Zahrah ta ɗan basar tare da faɗin "Dake ban kula da kyau bane, amma ita me za ta je yi?" Ta tambaya idanunta akan Halisa wacce wayar Umar-khan ke hannunta sai latsa ko'ina take ba tare data san ta kanta ba. Umar-khan ya ce "Ayya ko kin manta Glasses ɗin naki ne, ita za ai mata visa ne" baƙin cikin maganar da umar-khan ya yarfa mata ya sanya ta kasa cewa komai ta shiga cikin motar tana sauke numfashi sbd ƙamshin Roja data shaƙa ga daddaɗan freshener dake tashi a motar. Tana shiga Umar-khan shi ma ya shiga a hankali ya yi wa motar key sbd Yaa Sheikh baya son gudu da yawa, gatekeeper ya buɗe gate suka nufi wajan da za ai photo a haɗa musu visa. Bayan sun yi nisa akan titi Umar-khan ya juya ya kalli Halisa ya ce "Madam idan kika latata mini waya mijinki zai biya" Zahrah ta ɗago kai tare da duban saitin Umar-khan, bata fahimcin zancen ba domin ita ta ɗauka waya yake. Halisa ta buɗe fararen daidaiton haƙoranta masu kyau ta ce "To ai baya da kuɗi" "Injiwa?" Umar-khan ya tambaya idanunsa akan titi, ta ɗan turo baki tare da watsa hannu alamar bata sani ba, ya girgiza kai ya ce "Shi ke da kuɗi, hakan ne ma ya sa ban ƙwace wayata ba, albarkacin ki sai a siya mini iphone 13max pro Matar Malam na makka da madina" taja lulu eye's ɗinta lumshe wanda hakan ya zama jiki a gareta, magana zarar bunu cikin rashin sani da kuma sabo da surutu yasa Halisa faɗin. "Kai ma kasan ayi mini aure ne? Ko na faɗa maka yanzu" Umar-khan ya tuntsire da dariya sosai yana faɗin "Ina zan sani ƴar fillo? Kuma......," Yaa Sheikh da tun ɗazo idanunsa yake a rufe ya buɗe su a hankali kai tsaye ganinsa ya sauka akan ƙaramin bakinta wanda yake motsawa a hankali ta cikin madubin motar. Yaa Sheikh ya ɗauke idanunsa da sauri yana mai ɗan dafe kai cikin nutsuwa da kamewa wacce ta zauna a jikinsa ya buɗe baki da ƙyar ya ce. "Ka kula, Umar-khan" "Ok Yaa Lee" cewar Umar-khan with so much respect. Zahrah ta matsa kaɗan kusa da Yaa Sheikh tare da ɗora hannunta a saman na shi. "Asstagafirullah, Allah na tuba" ya furta cikin ranshi a zahiri bai motsa ba, sai ma rufe idanunsa da ya yi kamar mai barci. Zahrah taja gemunsa wanda yake matuƙar ɗaukan hankalinta ta ce "I love you My Excellency" baki ta miƙa zata sumbaci gefen fuskar shi, tari ya turnuƙe Halisa a kiɗime Umar-khan ya ƙara slow da driving ɗin ya ce. "Sannu mene ya sameki, are you sick? Baki da lafiya ne?" Ganin tarin ya kasa tsayawa yasa Umar-khan faɗin "Yaa Sheikh ko zaka taimaka mata da ruwan wajanka, babu raguwar a motar" bai ɗago ba, ba kuma zakai tunanin da shi ake maganar ba.. "Sannu, sannu" ya ƙara jerawa Halisa cike da tausayi. Yana driving ya kalli Yaa Sheikh ta madubi da kuma Zahrah wacce takaicin Halisa ya cika ta duk ta hana su sakat tasu a lokaci na farko ta bawa Yaa Sheikh ɗin kyakkyawar sumbata wacce zata ruguza shi tun yanzu, tasan ba lallai ya iya riƙe kansa ba, dole ya zo gareta. Umar ya ɗauke idanunsa yana faɗin "Yaa Sheikh Please ta wahala da yawa" ya ajjiye carbin hannunsa tare da ɗago kansa kamar mai nazari ya shiga kallon Umar-khan, not looking at her place ya kame kansa murya kamar anyi forcing nasa na magana ya ce.. "Stop the car" Yasan idan har Yaa Sheikh ya buɗe baki ya yi magana to yana nufin abin da ya faɗa ne har cikin ran shi a hankali ya yi parking motar zuwa gefen titi. Zahrah ta kalli Yaa Sheikh ta ce "Daman bai kamata mu shiga mota ɗaya dasu ba, ga wannan shegiyar yarinyar ƴar fillo, kawai su nemi abin hawa i can drive us kaji My Excellency" ya ɗan kalleta kaɗan ta wani kashe masa idanu tana shirin kama hannun shi ya fita daga cikin motar, yana fitowa ya shiga takawa a gefen titin hannunsa goye a bayansa, ganin yadda ya tsaya waje guda kansa a ƙasa yada Umar-khan fita yana tunanin ko lafiya? Ya nufi wajan shi tare da faɗin "Yaa Lee lafiya?" Ya ɗago kai ya kalli Umar-khan, mamaki ya kama Umar ganin yadda goshin Yaa Sheikh yake fitar da zufa ya jiƙe sosai da gumi. Bai magana ba ya miƙa hannunsa tare da amsar key car ɗin hannun Umar-khan, da hannu ya nunawa Umar-khan bayan motar alamar ya shiga ciki ya zauna, mamaki ya kashe Umar a tsaye yau Yaa Sheikh zai yi driving ɗin mutane a mota bana shi ɗaya ba? Me hakan yake nufi. Zahrah dake bayan mota tana jiran ace Halisa ta fita ita kuma ta dawo gaba ita da mijinta su tafi iya su biyu sai gani tayi Umar-khan ya buɗe bayan motar ya shigo, mamakin sauyin al'amarin cikin ƙaramin lokaci ya hanata magana. Yaa Sheikh ya sanya tattausan farin hannunsa mai ɗauke da suma lub ya buɗe murfin gaban motar, ƙafarsa ta hannun dama ya fara shigarwa kana ya shiga ya zauna baki ɗaya. "Ban gane wani ƙaton namijin ya zauna dani ba, bayan ina matarka?" Babu wanda ya bata amsa sai ji tayi ya yi wa motar key. Murmushi kawai Umar ya yi yana ayyana wani abu a ran shi.. Yaa Sheikh ya yi tunanin zata cika shi da surutu kamar yadda ta cika Umar-khan da hayaniya mara tushe, amma sai yaga saɓanin haka bawai kallonta ya yi ba, ya fahimci hakanne ta madubin motar. Kanta a ƙasa idanunta ya yi masifar jaaa jikinta na ɗan rawa a hankali, saukar sautin ƙira'ar daya cika motar har ya kawo zuwa kunnenta yasa ta sauke numfashi mai ƙarfi jikinta ya saki kafin su ƙarasa barci ya ɗauke ta sai ajjiyar zuciya take saukewa. Bayan magrib Mother na zaune a parlour ita da Jadda. Jadda ta kaɗa ƙafa ta ce "Amma dai Allah ya isa, an munafurce ni ko waye kuma yaje shi da Allah, shi yasa yadda zai yi dashi danni ba zan iya komai ba" "lafiya dai Jadda?" A fusace Jadda ta ce "Ina batun lafiya Maryam? Ashe haka aka haɗawa Uwar matar can lefe hadda na Allah ya isa fa? Ni dai babu ruwana na kusa zare hannuna daga al'amarin Aliyu ko na ɗaga masa nonon kawai tun da nayi niyya" Mother tai murmushi kawai tana jiran zuwan Maimoon. Zahrah ta ƙarasu parlourn sanye da ƙaton hijabi irin ta Allah ɗin nan nace, ta zauna tana faɗin "Sannu da hutawa Mother" a taƙaice ta ce "Yawwa" ta juya kan Jadda wacce ta haɗe rai sosai ta ce "Barka da gida" Jadda tai mitsi mitsi da idanu ta ce "Allah ya isa, Allah ya isa wallahi ban yafe ba" Jadda ta faɗa tana kallon Mother tare da fashewa da kuka ta ce "To me nayi mata da zata gaishe ni? Sbd Allah ina ruwanta dani ko nace ina buƙatar gaisuwarta" Zahrah bata ƙara bi takan Jadda ba ta kalli Mother tana sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Daman zan mayar da Yarinyar nan ne gida" Mother ta kalli Maimoon dake shigowa tana faɗin "Wacce yarinya?" Zahrah cike da nuna cewa tafi kowa iya ladabi ta ce "Ƴar fillo, zan tura ta gida" Jadda ta miƙe ta ce "Wannan farar yarinyar kyakkyawa mai zubin labarawa kamar ita tai kanta? Idan kin isa Allah ya tsine" Mother tai murmushi ta ce "Me ya sa?" Zahrah tai ƙasa da kai ta ce "Daman Mimi tace na dawo da ita gida, da ƙyar aka yarda aka bani ita kuma tana karatu" Mother ta karkaɗa ƙafa ba tare da ta ce komai ba ta danna wayarta babu jimawa aka ɗaga wayar ta ce "Umar-khan, kayi waya da mutananku na can Madina, a fara nemawa Halisa gurbin karatu a matakin ajin farko na secondary" gaban Zahrah ya faɗi, ganin how smart she had. Bayan gama wayar Mother ta ce "kada ki damu Zahrah, I'll talk to your mom, ki fara shirye-shiryen tafiya" ta miƙe tana faɗin "Na gode Mother" da sauri ta shige part ɗinta. Tana zuwa ta rufe ƙofa tare da cire hijabin jikinta inners ne kawai a jikinta cikin faɗa ta ɗaga wayarta ta ce "haba Deen wai kai wanne irin maye ne?" Deen dake cikin wayar ya ce "Muna vedio call kika tafi kin barni cikin wani hali Beb" cikin ɗaga murya ta ce "Jarbabbe duk kai ka koya mini jaraba kwana nake bana barci, nifa batun tafiya da yarinyar nan ne na fasa,ina hangowa kai na matsala gaba ɗaya ji nake kamar wani abu zai faru idan na tafi da ita" Deen ya numfasa ta wayar yana faɗin. "Ya kukai kuma me kike so ayi?" Ta faɗa masa duk yadda sukai da Mother ya ce "Uhm Sirikarki Educated ce kuma Barrister, ta fiki tunani da hankali idan kina wannan haukan da wuri za a gano shirinmu, dole ki yafe ɗan cikin ki a gidan Yaa Sheikh, shi ne zai bamu damar cimma burinmu ya zama dole ki samu kusanci dashi ina nufin ki samu mu'amalar aure da shi, hakan shi ne hanyar farko, ai ana haihuwa bakwaini ki san duk yadda kikai kina zuwa Madina ku samu daidaito Zahrah, kece madafin cimma burina na faɗa miki irin cin amana da zaluntar da akai mini" ta sauke numfashi tare da ta ce. "It's ok Deen, na maka al'ƙawarin ƙwato maka hakƙin ka, ina son ka, burina ka tsaya dani banda wata macen" ya yi murmushi ta wayar ya ce. "Zahrah kenan, kina so na kullum kike cewa, amma son da kikewa Yaa Sheikh yafi son da ki ke mini, duk da hakan me ya sa kika amince zaki cutar da shi bayan kina son shi?". Zahrah ta ce "kada ka damu wannan sirri na ne, sunna or later zaka sani, Yaa Sheikh manufa ne, kai kuma makami ko wanne nada amfani, amma dole muyi wani abu akan Halisa" ya ja tsaki a ran shi sam bai ga abin damuwa akan wata Halisa ba. "A kashe ta? Ko kuma a haukata ta?". Zahrah ta ce "Hauka kuma, zan yi tunani akan haka, muje vedio call na nuna maka wani abu mai yaji" dry ya yi ya ce "Zahrah bana son ganin wannan shafaffen ƙirjin naki, wanda yake kwance har ciki serious tun kafin Yaa Sheikh yasan wace ke ya kamata ki nemi magani" maganar Deen ta daki zuciyar Zahrah ta kashe wayar rai ɓace. Khalil ya ce "Mother daman zuwa nayi nai miki sallama, yanzu zamu tafi airport" ta ce "To sai yaushe kuma" ya shafa kai ya ce "Ina tunanin sai bikin Maimoon ko idan matar Yaa Sheikh ta haihu". "Ikon Allah daga aure sai haihuwa, Maimoon kam ai da sauran ta" ya ƙara shafa kai idanunsa akan Maimoon dake tura masa baki. "To Allah ya tsare, a gaida Oum Juwairah" ya miƙe yana faɗin "za taji ai tana gidan Abba Hakimi" kafin Mother tai magana idanun Khalil ya sauka akan yatsun Halisa da mmkin yake kallon Zoben dake maƙale a yatsar zai magana El ya ce "Zan tafi ni dai" ya ce "kafi jirgin sama tashi" Halisa ta kalli El suka haɗa idanu sun jima suna kallon juna kafin tai ƙasa da kanta, tun jiya da suka je visa ta daina walwala taƙi kula kowa surutun ya rago sosai. El-bashir ya fita Khalil ya ce "Ƴar tsuhuwa Maimunatu zo ki kaiwa Matar Yaa Sheikh gift ɗinta" ta miƙe kafin ta ƙarasa yayi waje, tana zuwa corridor taji an jawota zuwa jikin mutum, a tsorace ta buɗe baki zatai ihu Khalil ya yi saurin rufe bakin ya ce "Haba Amaryata yaushe za mu yi auren ne?" Ta ce "Allah ya sauwaƙe na auri me mata ni ban so" ya ce "Ni kuma na miki al'ƙawarin wallahi sai kin aureni na haɗa mata biyu a cikin masarauta" tai masa shiru, tun Maimoon na ƙarama yake mutuwar son yarinyar. Ya ɗan ƙara matseta a jikinsa daidai kunnanta ya ce "I love you" yana faɗin hakan ya saketa yana damƙa wani box ya ce "For our In-law, and this na ki ne" ya ƙara damƙa mata wani box ɗin ya juya da sauri tare da ficewa. Washegari gari da safe Yaa Sheikh ne yake fitowa a hankali daga part ɗin sa, yana sanye da jallabiya fara tas ƙafarsa sanye cikin slippers, hannunsa goye a bayansa ya ɗan tsaya a parlourn sbd shiru da yaji juyawa ya yi idanunsa ya sauka akanta tana ƙawance akan duguwar kujera ta kifa kanta a hannunta kamar mai barci, jar rigar dake jikinta ta ƙara fidda tsarin jikinta, madaidaitan hips ɗinta sun bayyana a fili ya ɗauke idanu yana ya mutsa fuska, remote ya ɗauka tare da kunna karatun Alkur'ani ya danna ƙara ya cika gidan. A firgice Halisa ta miƙe tsaye jikinta duk rawa yake, jajayen idanun da kusan kwana biyu suka ƙi dawowa dade ta buɗe su akan Yaa Sheikh dake zaune akan kujera yana ɗan jan gemunsa. Ba tare da ta ce komai ba sbd kanta dake juyawa da sauri ta nufi hanyar da zata fitar da ita daga cikin parlourn wacce kai tsaye kuma zata kaita har waje bakin hanya, Allah Allah take ta fita sbd karatun dake gigita mata lissafi kamar zai fasa kanta. Tana zuwa daidai inda yake zata gilma ta shige ya sanya farin hannunsa mai laushi ya damƙota tare da dawo da ita baya... Paid book It's 500 Via 08119237616Dawo da ita baya ya yi tare da zaunar da ita a ƙasa wajan ƙafafuwansa, yana mai sakin hannunta da sauri. Tamkar wacce take gane abin da shirun nasa yake nufi haka ta zauna waje guda taƙi yarda ta ɗago kanta kamar yadda yasu sbd ya fahimci abin da yake tunani. Yasan har abada indai tana cikin wannan yanayin to ba zata taɓa kallon cikin ƙwayar idanun shi ba, sai dai idan marasa kunya ne suke tattare da ita.. hannunsa daya riƙe nata ya dunƙule waje guda a haka Mother ta fito sanye da duguwar riga ganin Yaa Sheikh a main parlour da sassafe ya bata mamaki, idanunta akan shi kana ta zame zuwa kan Halisa dake zaune kusa da ƙafar shi ta dama. Da mmki tana zama ta ce "lafiya dai Haydar? fitowa da safiya, Halisa fa?" Ta tambaya tana kallon Halisa elxty yadda Yaa Sheikh yake abu lokacin yana yaro haka yanzu Halisa tayi. Ya buɗe idanun shi yana ajjiye carbin hannunsa cikin kamilalliyyar muryarsa ya ce. "Mun tashi lafiya Mother?" Ta saki murmushi tana faɗin "Allahamdulillah Haydar, Halisa fa?" Ya ƙara ware idanu yana kwaɓe fuska alamar tambayar batai masa ba, kamar zai share ya numfasa kaɗan ya ce. "Wafa?" Mother ta ce "Meya fito da Halisa da wannan safiyar kuma gata kusa dakai kamar bata da lafiya?" Ya jima yana tunanin amsar da zai bawa Mother baya ƙarya baya kuma faɗin abin da bashi da tabbacin sai ya yi shiru Mother ta miƙe tsaye tana faɗin. "Black tea ko? Bari na kawo maka,ka jira ina son magana dakai" ya jinjina kai. Mother na tafiya ya juya kansa zuwa inda Halisa take zaune a hankali ya miƙa tattausan farin hannunsa mai taushi ya ɗora saman goshinta. Zabura tayi zata gudu ya riƙe kan da kyau, sosai yaji kanta ya ɗauki zafi yana harbawa. Ya jima riƙe da kan yana ɗan murza babban yatsar shi a tsakiyar goshinta kafin yaji taja duguwar ajjiyar zuciya tare buɗe idanu. Ya zame hannun shi daga kan, itama ta kasa kallon shi ta kuma kasa motsawa. Kamar wacce aka tsikara haka ta miƙe jiri na ɗaukanta ta nufi part ɗin su Maimoon domin anan ne take kwana yanzu. Barin ta parlourn ya yi daidai da dawowar Mother daga kitchen, bayan ta zauna tare da tsiyayawa Yaa Sheikh black tea ɗin tare da 2 spoon na honey yana tiriri ta miƙa masa. A nutse yake sha ganin ya kusa shanyewa ta kalle shi ta ce "You need more? with chips or kunnu?" Ya jinjina kai alamar "Eh" kitchen ta shiga not too long ta dawo ɗauke da tray, Spoon ɗin ya ɗauka ya fara cakar chips yana taunawa a hankali, haka kawai jikin shi ya bashi ana kallon shi gently ya ɗago kai da sauri ta koma ciki tana dafe ƙirji, ya girgiza kai domin idanunsa sun riga da sun ganta tuni. Mamakin cin abincin na Yaa Sheikh yau ya kama Mother tana zaune tasan ko tayi magana ba zai fahimta ba, sai da ya goge baki da tissue kana ya zaro Aswaq daga cikin aljihu ya fara yi. "Ina son yin magana da kai ta fahimta Aliyu" ya maida hankali sosai akan Mother ta gyara zama ta ce. "Halisa bata da kowa, bata da wanda kareta ya kuma ja ragamar rayuwar ta, ko da baka san yaya akai tazo gidan nan ba, amma ka tuna cewa matar kace, ban damu da kai mata kallon mata ba, wannan deal kai da Abbanka, amma ka zama garkuwa a gare ta don Allah don Annabi ba danni ba Aliyu" ta haɗe hannaye biyu alamar roƙo a gare shi, a taushashe ya kama hannun Mother duk biyun, ya jima kafin ya ce. "Fiye da yadda kike zato, al'ƙawari ne" tai murmushi ta ce "Allah ya yi maka Albarka Malam, tare da matanka, kayi ƙoƙarin sauke hakƙin ko wacce mace a cikinsu, kada ka tauye na wani ko fifitawa" ya jinjina mata kai yana miƙewa tsaye. Kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa tare da ɗaukan system ya shige Library ɗinsa, wasu muhimman ayyuka ne dashi gashi yana son tattara komai wajan Saif-wazir tunda da Umar-khan zasu koma, ɗalibai na can suna jiran shi da gidan marayunsa. Misalin 10 kowa yana zaune akan dinning ana dinner Father ya ajjiye Spoon ɗin hannunsa ya kalli Zahrah ya ce "Aliyu ya faɗa miki 12 jirginku zai tashi ko?" Ganin Idanun Mother yasa Zahrah faɗin "Eh Father, nama gama shirya kayana" Jadda ta fashe da kuka tana share majina da gefen zani ta ce "Ubangiji ya bawa Malam haƙuri, an haɗa shi da wacce tafi ƙarfin shi, na rantse uwata ta haifan ban taɓa ganin ƙatuwa budurwa irinta ba, an bashi sa'ar babar shi da kaɗan fa na girme mata, gaskiya dole Malam ya ƙara aure zan nemi Hakimi da kai na ai shela a sama masa mata ko cikin masarauta ne" gaban Zahrah ya faɗi sosai kishiya za ayi mata? To ai Yaa Sheikh shi da wata mace har abada,da ita zai ta rayuwa da daɗi ba daɗi,idan har tana raye babu wacce ta isa ta shigo cikin gidanta, ba zata taɓa haɗa Mijinta da wata ƴa mace ba. Father ya ce "Bayan auren da yake dashi?" Jadda ta ce "A'a zan maka Allah ya isa Aliyu, tun nazo gidanka kaji na kulaka? Nifa ba zan yarda Malam ya zauna da ɗirkekiyyar mace kamar durunar ruwa ba, ko ni bata ban sha'awa ba balle namiji, kana kallon ƙirjin kamar an zuba kwalta a titin gwammaja, dole ya auri ƴar ƙarama wacce zai mure ƙuruciyarta ai Alsulhu khair" bakin Halisa na rawa ta ce "To ai nima matar shi ce kuma ƴar ƙarama ce ni....," Kafin ta ƙarasa maganar Mother tayi saurin rufe mata baki, faɗan da Jadda kewa Father yasa babu wanda yaji maganar sai Maimoon. Baƙin ciki ya cika Zahrah jin daɗinta ɗaya babu Yaa Sheikh a wajan. Cikin makirci Zahrah ta fashe da kuka tana zubewa gaban Jadda ta ce "Don Allah kiyi haƙuri Jadda, kada ki rabani da mijina yana so na, ina son shi" Jadda tai mitsi mitsi da idanu tana riƙe haɓa ta ce "Mai ƙarya aƙona shi a wuta, nifa na rarrashi Malam na bashi baki akan ya aureki da ƙyar sai dana zubar da hawaye, nace zanbi duniya kawai idan bai yarda da aurenki ba, shi ne zaki ce yana son ki?" Da sauri Zahrah ta nufi part ɗin ta, sbd gab take da yiwa Jadda rashin mutuncin wallahi. Jadda ta ce "To ai kaga nayi mata bayani cikin sauƙi,ta fahimta da faɗa nai mata sai ta ƙulla ce ni, ai Alsulhu khair" "Ai kam dai munga Sulhu, bamu sani ba ko zai zama alheri" cewar Auta Fattoumah. Jadda ta ce "A'a kowa ya yi ta kansa, bana shiga abin da bai shafan ba, amma fa na girgiza a bawa mutum auren sa'ar uwar shi?" Halisa ta ajjiye Spoon ɗin hannunta idanunta ya yi jajir kalmar.. _“Yana so na, ina son shi”_ ya shiga yi mata yawo a cikin kunne. Ta miƙe a hankali tare da nufar ɗakin su Maimoon. Tana zuwa Mother ta biyu bayanta.. Ta kasa kallon Mother bakinta kuma ya ƙiyin shiru ta ce. "To yaushe zan faɗawa kowa ina da aure kuma Malam ne mijina?" Mother ta girgiza kai ta ce "Ba yanzu ba, inda kika faɗawa wani to mun ɓata kuma zance Yaa Sheikh kada ya saki makaranta" Da sauri tana zare ido ta ce "A'a ba zan faɗa ba, amma zan dinga ce masa mijina ko? ko Baffa?" Mother ta rasa me zata ce, surutun yarinyar baya sarrafuwa idan har ya fito to dole ta furta.. "duk yadda kika gani, amma idan kika ce miji ai Zahrah zata gane, kice Abba Sheikh" bayani ta ƙara yi mata cike da hikima na zaman rayuwa, da kuma wasu muhimman abubuwa akan Yaa Sheikh ɗin. "Maza ta shi kije Maimoon ta ƙara yi miki saloon" ta miƙe tana cewa "To" sai da taje bakin ƙofa zata fita ta tsaya tare da kallon Mother ta ce. "Amma idan naje can Madina zan iya faɗawa kowa ayi mini aure ina da miji?" Mother ta tafe kai tare da faɗin "Na shiga uku".. Zahrah ce ke waya da Surry ta ce "Wallahi Surry ko da wasa aka bawa Yaa Sheikh auren wata sai na kasheta, ina da tsananin kishi akan abin da nake so, balle mutum kamar Yaa Sheikh wanda banyi tunanin zan same shi matsayin miji ba" Surry ta ce "Tab, sai ki san yadda ki kai kika tare da mijinki idan kuka tara zuri'a babu mai rabaki da shi ai" Zahrah ta ce "You're right jirginmu zai tashi, yama sunan maganin dake saka mutum feelings in 5 minutes?" Surry ta faɗa mata sunan maganin ta ɗora da faɗin "Amma dole Yaa Sheikh ya gane bake bace" murmushin mugunta Zahrah tayi tana girgiza kai ta ce "Idan kuma yana cikin maye fa?" Surry ta zare ido ta cikin wayar ta ce "Bugar dashi zaki? Kada ki cutar da ƴar mutane yafi ƙarfin ta ba" "Surayyerh kenan, na shige duk tunaninki, kada ki manta Zahrah Farouk nake, ita kuwa Zahrah ba mahaukaciya bace ta san me take, Ƴar fillo data gama aikinta zan aiwatar da burina a kanta gudun matsala" Zahrah tai wa Surry ba zata, gashi bata da hanyar da zata taiwa Halisa magana. "Do you want to just leave me alone now? these past few days have been a bother" "Okay bey" cewar Zahrah. Tana gama wayar Halisa ta shigo tai tsaye fuska a haɗe. "Oh su ƴar fillo an samu duniya, bari muje wannan farin na jikin ki sai na ɓatar da shi" ta tura baki gaba cikin surutu ta ce. "Ai farin daga Allah ne" Zahrah ta ce "magana ki kai?" Tai shiru ta kalleta da kyau ta ce.. "Ki gane baki da haɗi da dangin mijina, ke ƴar aikina ce, ki daina cusa kanki inda baki da mazauni ba zaki taɓa samun karɓuwa ba, saura ki faɗawa wani ke ba ƴar uwata bace kamar yadda nace" "Sai dai kishiya ba ƴar uwa ba" da sauri Zahrah ta ce "kika ce me?" Ta girgiza kai ta ce "Salati nayi" Ta ja tsaki tare da cewa "Get out jakar kawai" 11:00 Yaa Sheikh ya fito cikin wata haɗaɗɗiyar Alkyabba mai kyau da tsari, ya naɗa rawani wanda ya ƙara fidda haibarsa da cikar kamalar da yake da ita, fuska kame. Hannu goye abaya tare da carbi yana ja. Banda ƙamshin Roja babu abin da ke tashi a main parlour. "Allahu Akbar Allah ya baka haƙurin zama da uwar mata Malam, ni tsoro na ɗaya kada a dinga nunaka da baki ana ka mijin sa'ar babar shi" Zahrah data ƙarasu parlourn tai tsaye a gefen Yaa Sheikh ba tare data kula Jadda ba ta ce. "You look good My Excellency". A can bedroom Kuka sosai Halisa take sai rigima take ita kawai wajan Dada zata, da ƙyar Mother ta rarrasheta, ta zuba mata komai na buƙata cikin torelly bag ba tare da sanin Zahrah ba. Maimoon ta ce "Matar Yaa Lee ga gift inji Yarima Khalil" Mother ta ce "Gift?" "Eh, shi ya bani wai na bawa matar Yaa Sheikh, ni kuma kawai zan bawa Halisa" Mother ta amshi box ɗin ta buɗe, wani gold ring ne mai kyau sai ƙyalli yake, ta ce "Zan ajjiye waje na, hannunta akwai ring har biyu ya isa, Allah ya tsare ya ki yaye sai na kira waya Daughter" Halisa ta kalli Maimoon tana mata gwalo ta ce. "Yarinya na tafi gidan mijina, duk abin da ya faru zan ajjiye miki labari ko na dinga faɗawa Mother tana gaya miki" Mother ta ce "A'a na shiga uku bani a nan" Yaa Sheikh tuni ya shiga mota, shi kaɗai ne a baya Saif-wazir na driving.. Zahrah a motar Ishaq-Hakim ita da Halisa da Maimoon. Mother ta ce ba zai taje rakiya ba. Kai tsaye gidan Abba Hakimi suka nufa. Yaa Sheikh ne kawai ya shiga sbd babu lokaci, ya shige jikin Abba Hakimi yana sauke numfashi, rauninsa ya bayyana kasancewar yana jikin Abban nasa, a karo na farko ya riƙe Abban da kyau murya bata fita ya ce. "Ba zan iya ba Abba" Abba Hakimi bai fahimta dan haka ya ce "Kai mutum ne mai tsoran Allah da gudun hakƙin wani, balle matarka kada ka damu, ita Halisa ƴar riƙo ce shekara nayi zan amshi abata" ya zare jikinsa yana sauke numfashi tare da yin sallama. Daga nan suka ɗauki Umar-khan kai tsaye suka shige Airport inda jirgi ke jira. Tunda daga jirgin hankalinta ya tashi amma bata nuna ba, ta riƙe hannunta da kyau, Umar-khan na gaba sai Zahrah Halisa na biye da ita a haka suka shiga cikin jirgin, suna shiga Halisa ta riƙe kanta sbd tsoro, Umar-khan ya kalli Zahrah ya ce "Wajenku na cikin vip" Zahrah ta kalle shi ta ce "Yana ciki ne?" Umar na zama a mazauninsa ya ce "Gaskiya ban sani ba, ku shiga ku gani" ba tare da Zahrah ta ce komai ba ta nufi vip ɗin, jin takun tafiya a bayanta yasa ta tsaya tare da kallon Halisa ta ce "Ke kuma lafiya kike boye ni? Na manta ba a saba ba, Umar nuna mata wajan zama"bai ɗago kai ba ya ce "Wajan zamanku ɗaya ne ai duk vip" Zahrah ta riƙe ƙugu ta ce "kan uba, tayaya haka ya kasance kana nufin tare zan zauna da ita ga mijina kuma?" Sai a lokacin ya ɗaga kansa tare da kallonta ya ce "To ai suna ɗaya kuka amsa, matsayi ɗaya" "Kamar yaya suna ɗaya? Umar ya kamata kasan me zaka ce dani, ka gane" ya haɗe hannaye waje guda ya ce. "A'a ranki ya daɗe, mai da wuƙar mijin naki shi ne ya bada umarnin haka" ta haɗiye yawun takaici tare da shigewa vip, daman ita Halisa ta jima da shigewa, dan haka Zahrah na shiga ta samu Halisa zaune ta sunkuyar da kanta ƙasa, wajan ya haɗu sosai akwai duguwar kujera wacce Halisa take zaune akai, sai kujera mai guda biyu, tunanin Zahrah ya bata mai guda biyun ita ce wacce zasu zauna ita da Yaa Sheikh, ta nemi waje ta zauna idanunta akan Halisa ta ce. "Ina mijina?" Tai shiru taƙi cewa komai. "Ba magana nake miki ba, na lura kin fara ganin wajan barcina?" Ta ɗago lulu eye's ɗinta wanda suke sheƙi kamar an tara musu ruwa sbd yadda hawaye ya kwanta cikinsu. A tsiwa ta ce. "Ina mijina?" Zahrah ta zare ido tare sakin baki da jin abin da Halisa ta ce. Ƴar fillo tai murmushi kawai tare da girgiza kai ta ce "nifa kamar haka naji kince Anti shi ne nake ƙara tambaya, to a haka naga wajan kam" Zahrah ta ɗaga hannu zata ɗauke Halisa da mari suka ji gyaran murya. Gaba ɗaya suka ɗaga kai a tare daga Uwar gidan har amarya Zahrah, basu yake kallo ba wayarsa yake sakawa a airplane mode. Yaa Sheikh ya riƙe ya saba akan duguwar kujera yake zama, sbd yana ɗan samun hutu yayi barci kafin ya isa inda zashi, kai tsaye ba tare daya lura da Halisa ba ya nufi duguwar kujera tare da zama dab da ita. Numfashin Halisa ya kusa ɗaukewa sbd wani mugun shaƙar ƙamshin Roja da tayi, gashi Yaa Sheikh ya zama ƙato babba sosai har kafaɗar shi na rufe kanta. A karo na farko zuciyar Zahrah ta shiga bugawa gabanta ya faɗi,ta juya ta kalli Halisa wacce ta kafe Yaa Sheikh da idanu, a hankali kuma ta kalli Yaa Sheikh wanda ya nuna kamar bai san da mutane a wajan ba. Ta kasa magana ta rasa a wanne ma'auni zata saka haka, anya bata hau tsaunin da zai kaita zuwa ga hallaka ba?. A zahiri Yaa Sheikh ya mance ya taho da matayen nasa har biyu, da uwar mata da kuma ƴar rainon shi. A hankali aka fara sanarwar a ɗaura blet, Zahrah ta ɗaura Halisa kuma ta rasa me ake cewa sbd cikin harshen turanci ake maganar, sai faɗa computer take tana ƙara sanarwa. A nutse ya ware rawani kansa domin duk a zaton shi, shi kaɗai ne a cikin vip ɗin, kyakkyawar sumar shi ta bayyana abin mamaki ilahirin sumar kan shi daga gaba jajir take tamkar wanda ya fara furfura, daga baya kuma baƙaƙirin tai luff har wuyan shi. Ya sauke hannunsa akan Alkyabbar jikinsa ya ɗan buɗe gaban kaɗan sbd nauyi da tayi masa, yana kammalawa yaja blet, daidai lokacin aka fara sanarwar a shirya jirgi zai tashi, Halisa ta razana ta ƙanƙame jikinta, kanta ya shiga juyawa sai tayi nan luu tayi nan luu, lokacin da jirgi ya ɗaga zuwa sama Yaa Sheikh ya lumshe idanunsa ba zato ba tsammani yaji an fasa wata gigitacciyar ƙara kafin ya buɗe idanu ta faɗo kan cinyarsa babu numfashi.... Paid It's 500 08119237616"Shiru" ya ce yana sakin bakin tare da mai da Idanunsa kan glass cup ɗin da ya tsiyaya tea aciki. Ta tura baki gaba ba tace komai ba duk da irin ƙaiƙayin da bakin yake mata, haka nan taji kamar ana mintsininta akan Halisa yi magana cikin sauri ta ce. "Nima ina jin yunwa na sha shayin naka?" Cak ya ajjiye tea ɗin daga hannunsa yana ɗaukan tissue tare da goge bakinsa, ta ɗauki shayin daya rage zata kai bakinta ta ji ance "A'a" ta ajjiye cup tana miƙewa tare da bin bayansa, sahun tafiya da yaji a bayansa yasa ya tsaya, tayi saurin dawowa gabansa suna haɗa ido ya ware mata manyan idanunsa masu kaifi ta tura baki ta ce "Na sake magana banga ka riƙe bakin ba ai" Yaa Sheikh ya girgiza kai kawai tare da shigewa bedroom ɗinsa yana ɓoye yanayin fuskar shi. Ta kalli inda ya shiga sai kuma ta juya tana kwashe tray ɗin. A main parlour ta samu Zahrah zaune tana breakfast ga wata maid nayi mata tausa a ƙafa. "Ke zonan" cewar Zahrah Halisa ta dawo ta zauna tana ɗauke kai gefe guda, saboda har yanzu bata mance mari da zagin da Zahran tai mata ba, Zahrah ta ajjiye spoon ɗin hannunta wanda take shan tea da shi ta ce. "Kai breakfast ɗin sai yanzu? Ko bai ta shi bane" Halisa ta kalle ta sai kuma ta ɗauke kai tana faɗin. "Shi ya ce na tsaya" Zahrah ta ce "Shi Yaa Sheikh ɗin?" Tai shiru ba tare da ta ce komai, tasan indai zatai magana to zata saki layi ne, Maid ɗin ta kalli Halisa da sauri, ai ko ita da tayi shekara da shekaru tana aiki a gidan Yaa Sheikh magana bata taɓa haɗa su ba, infact ko parlourn shi bata san ya yake ba, Ummul ce kawai take kai masa breakfast ita ma iya dining room, sai ya gama yabar wajan take zuwa ta kwashe, idan kuma yini gida zai yi a ranar basa taɓa zuwa part ɗin, Umar-khan ne ke kai masa dinner, bai fiya cin lunch ba sai dinner, anytime yana tare da butar shayi kamar buzu. Mamaki ya cika Maid ɗin jin abin da Halisa ta faɗa wai shi ya ce ta jira? Who is she to him?.... "Whatever, Ke yama kika ce sunanki?" Maid ɗin ta ce "Bara'at" Zahrah ta ce "Ok, duk wani aiki na part ɗin nan, zuwa part ɗin Yaa Sheikh ya dawo hannun wannan yarinyar, idan kun kammala abinci na Yaa Sheikh ita zata dinga kai masa, bana son na dinga ganin wani abu na ba daidai ba, bana son surutu da hayaniya yana saka mini ciwon kai, ko a gidan ubana ban taɓa sanin hanyar kitchen ba, to a nan ba zan fara saninsa ba, kuna gama girki ki bata ta kawo mini nawa" daga Halisa har Bara'at kallon Zahrah suke, suna mamakin ƙarfin ikon nata, duk da cewa Bara'at bata san matsayin Zahrah ba, amma tasan dole da akwai abin da ta taka a gidan... Zahrah ta kaɗa ƙafa tana faɗin "Ku ɗauke idanunku daga kan mijina, daga nesa kuka ganshi ku sauya hanya, duk abin da kuke nema ni zaku faɗawa, koda abin cin gidan ne ya ƙare" Bara'at ta ce "Ok, amma kula da abincin gidan yana wajan Ummul" It's your problem, I just finished planning what I want" ta juya kan Halisa tana faɗin.. "Jeki breakfast ki saman a bedroom" tana faɗin hakan ta shige part ɗinta, Halisa ta bita da kallo a zuciyarta tana mmkin halin Zahrah. Miƙewa Bara'at tayi Halisa ma haka, tabi bayanta har zuwa sashen kitchen, ma'aikata ta gani mata da yawa ko wanne da abin da suke a kitchen ɗin. Da sauri Bara'at ta nufi wajan Ummul tana ce wa "Yau naga abin mamaki Ummul" kyakkyawar matashiyar matar wacce zata iya shekaru 50 zuwa sama ta kalli Bara'at ta ce. "Da akai me Ukkuti Bara'at?" Bara'at ta sauke numfashi ta ce "Wata mata na gani, mai iko da isa, wallahi na tsorata da yanayinta" Ummul tai murmushi tana ajjiye abin hannunta ta ce "Faɗimatul-zahrah bin Umar Farouk, matar Yaa Sheikh" a tare duk suka ce "Matar Yaa Sheikh?" Ummul ta kallesu ta ce "Na manta ban shaida muku bane, sai a haƙuri da juna ko?" Idanunta ya sauka akan Halisa wacce take dube dube duk abin da suke faɗa tana ji amma hirar bata gabanta, Ummul ta girgiza kai kawai, tana mai jin wani abu a ranta, yarinyar tana nan dai babu sauyi a tare da ita kamar yadda yake nuna mata ita a waya. Hawaye ya sakkowa Ummul ko yanzu ta mutu ta yi farin ciki, Aliyu ya samu gefen rayuwar shi kamar yadda yake faɗa mata a koda yaushe. Bara'at ta ce "Ummul wace ita kuma wannan?" Ummul ta ce "Masu gidan ce" "Masu gidan kuma?" Cewar Suhaima Ummul ta ce "Ina nufin mai aikin Zahrah ce" ta kalli Halisa da kyau tana mai sakin murmushi ta ce "Sunanta Halisa, ƴar uwar Zahrah ce an bawa Yaa Sheikh riƙon ta amana ne, zatai amfani da sunan Halisa bin Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Halisa ta ƙarasu wajan Ummul da sauri fuskarta ɗauke da kyakkyawan murmushi ta kama hannun Ummul ta ce "Laa kema kin sanni ashe, kuma kin san anyi...." Ummul tayi saurin rufe bakin nata tana cewa "Ba'a yin surutu a ɗakin girki, Bara'at akwai tray tana shirya breakfast ki bawa halisa" Bara'at ta ɗakko tray ta bawa Halisa ita kuma ta ce a kitchen ɗin zata zauna ta ci. Bayan ta gama cin abincin Ummul ta miƙa mata farar madara mai ɗauke da zuma a ciki, batai musu ba ta amsa "Nima ina son na iya girki sosai, ina son yi wa Yaa Sheikh girki mai daɗi" Ummul tayi kamar bata ji zancen na Halisa ba, taci gaba dayin aikin gabanta tana son a akai gidan ciyarwa Yaa Sheikh abincin akan lokaci. Zahrah na tsaye a gaban mirrow anci uwar kwalliya sai ƙarinin mai take, wayarta dake ringing ta ɗauka ganin sunan Deen ta ce "Uhm maye daman nasan babu mai kirana sai kai" daga cikin wayar ya ce "Ba wannan zaki tambaya ba, fara duba number" da sauri Zahrah ta duba number da mmkin take kallon number ta Saudiya ce,what does that means? Ya katse mata tunani da faɗin "Ki daina mamaki na riga ki sauka a Madina, ke kawai nake jira, don't make any mistakes nazo da maganin da ki ke buƙata, ina son ganinki" The surprise of his behavior prevented Zahrah from speaking. "Wallahi ki san yadda akai ki ka zo, ko ki ganni a gidanki" yana faɗin haka ya kashe wayar babu jimawa ya tura mata address ɗin inda yake, Zahrah ta dafa kai da sauri kuma ta juyawa zuwa ɗaya bedroom ɗin nata a nan ta samu Halisa tana shirya mata kaya a wardrobe, zama tayi ta ce "Ke kin fara menstrual?" Halisa ta ɗauka gyaran kayan take nufi kai tsaye ta ɗaga mata kai alamar eh. Juyawa tayi ta nufi part ɗin Yaa Sheikh. Fitowar shi kenan daga Library room ɗinsa, ya zauna sanye da wata tattausar Jallabiya a jikinsa hannunsa cikin sumar kansa, cikin nutsuwa ya gyara zama akan duguwar kujerar da yake kai hannunsa riƙe da Cup yana shan green tea wanda Ummul ta kawo masa da kanta, speaking calmly ya ce da Khalil. "Uhm surutu dai" Ta cikin waya Khalil ya saki dariya ya ce "Ya muke da matarka? Allah ya nuna mini ranar da zata barbabaɗa tana ɗauke da cikin Yaa Sheikh, koda yake kace baka son ta ai, auren dole akai maka" Yaa Sheikh yaja idanu ya rufe yana jinsa fresh sbd barcin da ya yi, cikin son dakatar da Khalil ya ce. "Wallahi ba auren dole bane, ni na zaɓi matata It was completely my plan..." Katse wayar ya yi jin yana faɗin abin da mai shirya ba, tare da rufe kansa. Tsaye ya ganta a kansa babu sallama ya ɗauke kai kawai yana ci-gaba da danna waya tare da duba abubuwan da Umar-khan ya tura masa. Ta zauna kusa da shi tana cewa "My Excellency baka fito ba har yanzu hope lafiya?" Kai kawai ya jinjina mata ba tare daya kalleta ba, ta haɗe jikinta da nashi tana cewa "Daman nace ina neman permission zamu shopping da ƴar fillo" har lokacin idanunsa yana kan waya bai ce komai ba. Ta shafi fuskar shi tare da cewa "Ba jimawa za mu yi ba kaji My Excellency" Jotter ya ɗauka da pen ya yi rubutu kana ya ajjiye mata a gefenta haka kurum yaji harshensa ya harɗe baya jin yin maganar. Ganin ƙoƙarin rungome shi take son yi ya ɗan miƙe tsaye, yasan cewa hakƙinta take nema, kuma yasan girma da ƙarfin hakƙi amma ya zai? He's not interested at all, baya son Ubangiji ya kama shi da wannan laifin. Tabi bayan shi da kallo, tana ji a ranta dole ne ma tayi gaggawar aiwatar da burin dake ranta, Yaa Sheikh ya dawo hannunta sai yadda tai da shi tayi imani da Allah idan ya zo hannunta shi da wata ƴar mace kuma har abada, ba zai iya kallon kowa a matsayin mace ba dole sai ita, What is the solution? where will she start and what will she do now. "You can go, Ina buƙatar gyaran part, With food" shi ne abin da ya rubuta mata a jikin Jotter ɗin, ta duba kenan dole mutum ɗaya ya tsaya, ita gasky ba wani gyaran ɗaki da zata iya, bayanta ciwo yake idan ta yi,kuma bata saba ba. Fita tayi ta samu Halisa a main parlour a kwance barci ya ɗauke ta tunda ta farka da asuba bata koma ba, gashi tai aiki ta gaji sosai bata san barcin ya ɗauketa bama sbd kallo take. Tana zuwa ta fisgo ƙafar Halisa zuwa ƙasa ta faɗo daga kan kujerar, a tsorace ta ce "Hande en boni me na yi Anti?" Zahrah ta ce "Ai hutu kika samu kenan? Ai babu ranar da zaki huta, zaki ta wahala har abada, kije ki gyara part ɗin Yaa Sheikh, ki kai masa lunch zan fita unguwa" kanta a ƙasa ta kasa cewa komai, tana zaune a parlourn Zahrah ta fito cikin wata duguwar riga ta yana mayafi hannunta riƙe da hand bag, kamar yadda Zahrah bata kulata ba itama bata kula ta ba. A compound ta ci karo da Umar-khan yana fitowa daga mota hannunsa riƙe da takarda. Ya ce "Evening" ta share sa, ta nufi wajan wani da alama shi ne drivern gidan. Kai tsaye Umar-khan gidan ya shige ya samu Halisa zaune kanta a ƙasa tana gyangyaɗi ya ce "Matar Malam" tai saurin jan mayafin abayar ta ɗora a kanta tana yi masa murmushi ta ce "Ina yini?" "Lafiya, barci a nan kuma? Yaa Sheikh ɗin yana ciki?" Ta ce "Ban sani ba" ya jinjina kai ya ce "Ok bari na duba, kije ki kwanta mana" ita dai ba tace komai ba ya nufi Part ɗin Yaa Sheikh barci yaci ƙarfinta, ta kwanta nan ƙasan carpet. Umar-khan ya zauna bayan ya gaida Yaa Sheikh ya ce "Na cike komai na makarantar, gobe aka bada izinin ta fara zuwa, Mother ta ce komai cikin gaggawa take buƙata" ya miƙawa Yaa Sheikh file ɗin takardun Halisa bai amsa ba, sai tsare Umar ɗin da idanu da ya yi, Umar yana fahimtar shirun na Yaa Sheikh hakan ya sa ya ce. "Al Aqeeq International School for Girls, Safiya Opens 7:30 ita ce makarantar" Yaa Sheikh ya jinjina kansa tare da miƙewa ya shigewa ɗaki. Wajan mintuna goma suka fito tare da Umar-khan wata Milk ɗin jallabiya ce a jikinsa, sai golden ɗin Alkyabba daya ɗora a kan jallabiyar, ya fito a babban malaminsa sai ƙamshin Roja yake bazawa, yana fitowa idanunsa ya sauka akan Halisa wacce ta cure waje guda tana barci, ya tsaya cak tare da kallon Umar-khan, Umar ya nufi ɓangaren Ummul babu jimawa suka dawo tare, Ummul ta kallesa ta ce "Malam za a fita ne? Ba kaci abincin kirki ba?" Ya ɗan ɗauke kai zuwa hanyar fita yana faɗin. "Sanyi zai illata ta, a sauya mata waje" sai a lokacin Ummul ta lura da Halisa. "Tom babu damuwa, Allah ya tsare" ta nufi wajan Halisa ta shiga tashinta tare da faɗin "Matar Malam, matar Malam" ta buɗe ido tana kallon Ummul ta ce "Maza ta shi ki koma ɗaki, a kwai sanyi zai kama jikin ki" ta buɗe ido sosai ta ce "Anti Zahrah ta dawo ne?" Ummul ta ce. "Fita tayi ne? ta shi lokacin sallah ma ya yi ai muje ko" har part ɗin Halisa Ummul ta shiga, akan idanunta Halisa tai alwala kana tai Sallah. Ummul ta ce "ƙarfe biyar kizo ɗakina, zan nuna miki yadda ake cikakkiyar sallah, na fara karanta miki Alkur'ani, yanzu ki kwanta wajan ƙarfe 4:30 ki tashi ki wanka ki wanke baki, ki sauya komai na jikin ki, kinji ko?" Ta tura baki sosai ta ce "To wannan duk na mene Ummul" Ummul ta ce "zaki sani ne" ta fice daga ɗakin. Yaa na fita kai tsaye Al Masjid an Nabawi ya nufa sbd wani karatu da yake dashi na musamman, kuma acan yake son yi Sallah ma, da kuma zaman tattaunawa da za su yi da mahukunta kula da Masallaci harami ana son naɗa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu matsayin limamin masallacin Haramin wanda zai jagorancin sallar Taraweeh da Tahajjud, gaba ɗaya azumi saura wata guda ya rage a fara. Tamkar uwa mahaifiyya haka Yaa Sheikh ya ɗauki Ummul yana ɗaukan minti goma yana magana da ita, tasan kusan komai nasa kuma tasan da yawa abin da Mother bata sani ba, tunda yafi rayuwa a Madina fiye da Nigeria. Sai bayan sallar issha Zahrah ta shigo a gajiye tana tafiya da ƙyar idanunta ya yi jaa, Halisa ta bita da idanu ganin yadda take tafiya kamar yaron da akaiwa shayi. Duk yadda Halisa tasu taga dawowar Yaa Sheikh bata gani ba, barci ya ɗauketa a Main parlour. Ƙarfe 12:30 ya shigo gidan shi kansa a gajiye yake sosai, ganinta a parlourn ya sanya ya tsaya yana binta da idanu, a hankali ya dubi lokaci sai kuma ya shige part ɗinsa. Kiran sallar asuba ya farkar da ita, da mmki take bin makeken gadon da take kai da kallo, an rufe ta da wani haɗaɗɗan duvet mai ƙamshi ga laushi an kuma rage ƙarfin a.cn ɗakin, ita dai tasan a parlour ta kwanta waya kawota nan? Ko ita ta shigo da kanta. Ta miƙe ta nufi toilet yadda Ummul ta koya mata haka tayi, tai wanka da ruwan zafi ta shafe jikinta da Vaseline Intensive Care Cocoa Glow Body Lotion. Shiryawa cikin Abaya ta ɗora hijab a nutse take duba littafan da Ummul ta bata, Ubangiji ya bata fikirar hadda ce, da yawan lokaci ita abu a kanta yake zama, duk wani abu mai muhimmanci bata wasa da shi. Tana zaune taji saukar muryarsa a kunnanta yana data kabbarar sallah, shiru tai bata taɓa tunani muryar shi takai daɗin haka ba sai yanzu. Sallah ta gabatar sannan ta nufi ɓangaren kitchen ta samu tuni sun Bara'at sun fito. 6:30 Ummul ta ce tayi sauri ta shirya za a kaita makaranta, wani tsalle tayi ta rungume Ummul daɗi ya kamata jin za a kaita makaranta abin da take buri a rayuwarta. Ta shirya ta fito tsaf a cikakkiyar ƴar fillonta Ummul na ganinta tai murmushi tana cewa "Kije ki gaida Abban naki" Halisa ta ce "Abba kuma Ummul" ta ce "Eh, uban riƙon ka ai uba ne jeki maza" hannunta ɗauke da yam balls ta nufi ɓangaren shi. Cikin siririyar murya tai sallama tare da shiga tsaye ta gan shi cikin kyakkyawar shiga mai ɗan kauri sbd sanyin garin da aka tashi da shi, hannunsa goye a bayansa ta ƙarasa cikin da sauri tana durƙusawa har wajan ƙafafuwan shi ta ce. "Jamɓanduna, Noi sare,Noi kuɗe" ta jera hausuwar ma'ana _“Ina kwana, ya ya gida, ya ayyuka”_ ya ware gajiyayyun Idanunsa a kanta, yana bin shigar makarantar nata, ta ɗaga kai ta gan shi tsaye ta miƙe tana kallonsa, ya dubi yam balls ɗin hannunta da raguwar na gefen bakinta. "Jiya nai barci baka dawo ba, yanzu kuma wai makaranta za a kai ni inji Ummul" ya jinjina mata alamar _"Eh"_ yana ƙoƙarin juyawa tayi saurin riƙe ƙugunsa da hannu ɗaya ta ce "Miyetti masin, Allah ya ƙara arziƙi" Ɗan ƙaramin bakin maganar kawai yake bi da kallo, gumi na tsastsafo masa ta goshinsa ta saki kyakkyawan murmushi ta ce "Mijina" da sauri ya kalli cikin idanunta ta ɗauke nata idanun sai murmushi take sbd daɗin zata makaranta. A hankali ta buɗe baki a taushashe kuma cikin ƙasa da murya ya ce "Matar m......" Maganar ta tsaya sbd yam balls data tura masa a cikin baki ta dinga tsalle tana cewa "Nayi maka wayyo daman ance baka cin abinci" ya lumshe fararen idanunsa tare da nufar kujera har lokacin tana riƙe da shi. Yana zama ta zauna a ƙasa Yaa Sheikh sai mai da numfashi yake sam bai niyyar cin komai ba, bisa dole ya shiga tauna yam balls ɗin bakinsa yana goge zufar dake goshinsa, wanda kuma shi kansa ya san zufar ta mece ce. Ya ɗauki bottle water tare da tsiyayawa a cup bayan ya sha ruwan ya mai da numfashi. Halisa ta ce "nace Ummul tayi maka wani na cinye gaba ɗaya tas" gently ya buɗe idanun a kanta ganin yadda yake bin fuskarta da kallo sosai yasa tai masa kyakkyawar murmushi tana lumshe idanu tare da buɗewa kamar yadda yai, a hankali ya ɗan ranƙwafa daidai kanta ya sanya fararen tafukan hannayensa tare da kama fuskarta da kyau babban hannunsa yasa yaja kumatunta numfashinsa na sauka a fuskarta ya ce. "Zaki fasa mini kai da surutu Matar Malam, shiru kan na ɗinke bakin...... Not edited Paid book ₦500 08119237616 Sarautar marubuta. _Ubangiji ya haɗamu da alkairan da suke cikin jumma'h. Mu haɗu Monday🥰❤‍🔥_Da fararen idanunsa masu tsari yake bin ta da idanu da mamaki, ganin da gaske bata mutsi tsoran da ya yi mata yawa ya sanya numfashinta ya ɗauke, hannunsa basu taushi ya sanya akan fuskarta kamar mai jin tsoran gently ya shiga bubbuga kumatunta amma ko motsi ba tayi ba, ya ɓata fuska ganin tun ba a je ko'ina ba, yarinyar zata fara bashi wahala. Yatsun hannunta biyu ya kama yaja da ƙarfi yana buga tsakiyar kanta ajjiyar zuciya ta sauke da ƙarfi tana jan numfashi, sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe wanda taji kusa da ita sosai cikin fillatanci take faɗin. "Don Allah ku sakko dani ƙasa zan mutu wayyo Dada wajanki zan dawo" saukar numfashin da yaji yana sauka a fuskarta da ƙamshin da ba zata manta da shi ba ya sanya ta buɗe idanunta wanda ta rufe su saboda tsoro, wanda ta gani take jikinsa ya bata mamaki numfashinta ya kusan ɗaukewa, sbd yadda ya yi mata kwarjini a idanu ga Alkyabbar jikinsa duk ta rufe mata jiki, a jikinsa yaji shi take kallo bai kalleta ba, ya sanya hannu tare da riƙo kafaɗunta da kyau yana zaunar da ita akan kujerar sosai. Yana daga inda yake ya ranƙwafa sosai tare da miƙa hannu zuwa inda blet ɗin take, kwantaccen sajansa ya shafi fuskarta ta sauke numfashi mai zafi wanda ya sanya Yaa Sheikh daka tawa da kama blet ya jima kafin ya zaro blet ɗin da sauri ya maƙala mata, yana ƙoƙarin janye jikinsa ta ɗora hannunta a tsakiyar tafin hannun shi.. "Uhmmm" ya ce a ransa yana ɗaga idanunsa zuwa gareta ya kalli cikin idanunta ba tare da ya ce komai ba, Halisa ta sake damƙe hannunsa da kyau cikin rawar murya ta ce. "Usako miyetti masin" idanu kawai ya lumshe mata tare da matsawa waje guda. A fusace Zahrah ta kunce blet ɗin jikinta tare da tashi tayi kan Halisa tana kumfar baki ta ce. "Ke dan uwarki mijina sa'anki ne da har zaki faɗa kansa da ƙazamin jikinki? Shegiya mara ƴan ci" Halisa ta kalli Zahrah ta ce "To Anti godiya nayi masa fa, kuma dana faɗa ƙasa naji ciwi ba ƙwara na faɗa kan shi ba, kuma ai ban masa nauyi ba ko kaji ciwo?" Ta faɗa tana juyawa tare da kallon Yaa Sheikh, shi gaba ɗaya hankalinsa baya kansu hannunsa riƙe da darija yana dubawa, tuni ya mayar da hiramin kansa baya buƙatar kowa yaga wani sashe na jikinsa. "Kauuu!!" Zahrah ta ɗauke Halisa da mari tare da nuna ta hannu ta ce "zanci uwar data haifi babarki" ƙarfi da girman zagin yasa Yaa Sheikh kallon Zahrah a zuciyarsa yana Istigifari bai ɗauka wani zai iya zagin ba, ba a taɓa zagi a gaban shi ba, hakan ya zama abu sabo a gare shi. Bai ce komai ya ɗauke kai tare daci gaba da duba jaridar hannunsa, zafin marin yasa Halisa fashewa da kuka sosai tana kifa kanta a cinyarta, kuka take sosai wanda rabin kukan baƙin cikin zagin da Zahrah tayi mata ne. Yaa Sheikh kukan yake ji har tsakiyar kansa jin kukan na neman tarwatsa masa kai yasa ya miƙe tsaye tare da buɗe wata ƙofa ya shiga. Zahrah ta kasa haɗiye mamakin yadda Yaa Sheikh ya nuna kulawa ga Halisa, haushin abin da ya yi yasa ta huce akan Halisa ɗin. Sun yi nisa da tafiya sosai wata maid ta shigo cikin wajan tana tambayar Zahrah me za a kawo musu, Zahrah ta karɓi abin hannun matar ta duba, kana ta zaɓi abin da take so. "Nace ko zaki iya sauyawa wannan yarinyar waje?"Flight attendant ta ce. "Her name please?" Zahrah ta ɗan kwaɓe fuska ta ce "Something Halisa.." ta ɗan danna wani abu a jikinta tare da yin magana bayan ta gama ta ce. "I think ita ce Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu right Maah?" Zahrah ta ce "No, bana tunanin ita ce her name is Halisa Danejo Rome" Flight attendant ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Sorry Maah babu da wani suna a jerin wanda za su yi tafiya yau, Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu shi ne" A fili Zahrah ta ce "Kan uba" sai yanzu ta tuna sunan Yaa Sheikh kenan, da sunansa akai mata visa kenan?. "Oh maybe she's the one, zaki iya sauya mata wajan zama?" Matar ta ce "Yes Maa, daman yanzu na duba ta samu sauyin wajan zama tuni" Zahrah tai murmushin jin daɗi matar ta kalli Halisa wacce ko inda suke bata kalla ba sai Ajjiyar zuciya take saukewa. "Can you follow me please?" Zahrah ta ce "ki mata hausa maybe she understand you" matar tai murmushi ganin yadda Zahrah take kwaɓe fuska ta ce "But she's your daughter?" Wata uwar harara Zahrah taiwa matar ta ce "Kinga alamar ina da ƴar ne?" Ita ma tai murmushi ta ce "Ai babu mmki idan nace miki a tunani zaki haifi yara biyar ma" Zahrah ta kalli jikinta da kyau ta kasa cewa komai, sbd baƙin cikin Flight attendant. "Halisa biyo ni kinji" a sanyaye duk da tsoran jirgin da take tabi bayan matar har zuwa champer 2 na jirgin. Nan ma dai kujeru biyu ce kawai a wajan ba kowa, ta nemi waje ta zauna cike da tsoro. Not too long da zamanta ya shigo tare da zama kan kujera da sauri ta sunkuyar da kanta domin a tunaninta faɗa zai mata, sai taga mai kulata ba ƙafarsa kawai ya miƙe. Tana zaune aka turo basket na abinci, zallar fruits ne sai gorar ruwa, aka ajjiye a gaban Yaa Sheikh ita kuma aka ajjiye mata chips da egg sai haɗin salad da ruwa. A hankali ya ɗauki orange ya saka bakinsa ya shiga taunawa cikin nutsuwa, Halisa ta kalle shi bakinta na rawa ta ce. "Amma wannan abin yabann sha'awa ɗan sammani" ya jita sarai amma yai mata banza sai da orange ya ɗin ya rage guda uku ya ɗauki guda ɗaya zai ƙara sakawa a bakinsa tayi saurin riƙe hannun shi, bai zaici haka ba ya kalli hannunta tare da kallon gefen fuskarta ta langwaɓar da kanta gefe ta ce "Ayya ka sammin bana, ni ma idan kaga abuna zan maka naga kana ta haka da idanu" yabi idanunta da kallo yadda ta lumshe su tare da buɗewa tana gwada masa yadda yake, ta kwance na hannunsa tare da kawai bakinta, ta ɗauka wani daɗi ne a orange ɗin. Ya sauke numfashi ganin hannunta na neman taɓa dugun gemun shi cikin ƙasa da murya mai sanyi ya ce. "Ci kani" ta yi saurin saƙona tana komawa wajanta, bai ƙara taɓa komai ba a kayan sai ruwa daya sha sosai. Misalin 10 na dare jirginsu ya sauka a Prince Muhammad bin Abdul'aziz International airport, sai nasarwa ake kowa ya saka blet jirgi zai sauka, ganin bata fahimci me ake cewa ba ya kalleta da kyau, ya riƙa ya saka blet a jikinsa ba damar cirewa kuma sun ɗan bada tazara, a hankali jirgi ya fara girgiza yana rawa Halisa ta rikice daga tai nan sai tayi nan, shuuuuu jirgin ya yo ƙasa tai gaba luuu zata kifa shiru tayi jin an riƙo kafaɗar ta, ya haɗa da gefen ƙirjinsa tare da riƙeta. Ƙuri tayi masa da idanu ganin nasa idon a rufe ta kasa motsawa shima kuma bai saketa ba, tunda har lokacin jirgin bai gama daidaita ba, balle ya samu damar sauka a titinsa. Ɓangaren Zahrah sosai taji daɗin ganin an ɗauke Halisa yanzu zata samu damar kasancewa da mijinta hankali kwance, sai dai tun tana jiran dawowar shi amma shiru gashi bata da ikon tambayar wani, bisa dole tai shiru. Bata tsammaci abin haka ba, sai ji tayi ana faɗin sun ƙarasu Madina tuni ai. A hankali ta saka blet tasan dai dole tare zasu tafi gida. Jirgi na yin parking ya saketa da sauri kafin ta buɗe ido ya fice daga cikin wajan, ta shiga zare idanu yanzu idan guduwa sukai yaya zatai?. Tana wannan tunanin Umar-khan ya shigo yana murmushi ya ce "Matar Malam tasu muje" ta miƙe tana kallon Umar-khan ta ce "To kai gida kaje ka dawo ne?" Yai dare ya ce "Hhhhhh ai kam na koma Nigeria na dawo" tabi bayansa da sauri ta ce "Kasan me" ya ce "sai kin faɗa" ta lumshe idanun ta buɗe ta ce "A ciki da abin ya tashi sama kawai na faɗa kan Malam na ɗauka zai dukeni kamar yadda anti da dake ni, sai naga kawai ya lumshe idanu ni kam nace masa na gode" "Uhm" kawai Umar-khan ya ce domin bashi data cewa a wanann batun, suna fitowa Zahrah na fitowa suka kalli juna da Halisa kowa ya ɗauke kai. Bayan sun sauka daga jirgin Zahrah ta kalli motar dake gabansu ta ce "Ina My Excellency?" Ya ce "Yana da meeting ne, sai zuwa 12 zai dawo" Zahrah ta ce "meeting da wannan daren?" Umar-khan ya ce "Manyan mutane daman sai dare suke meeting, muje kada mu ɓata lokaci" Zahrah ta shiga bayan mota Halisa ba haka, Umar-khan na gaba shi da driver. Wata haɗaɗɗiyar area suka nufa gaba ɗaya mazauna wajan larabawa ne, gidan dake kusa da na Yaa Sheikh sune hausawa, faɗar kyau da tsarin gidan Yaa Sheikh ɓata baki ne, flat gida na zamani, motoci birjik a harabar gidan ga tarin flowers da ɓangaren swimming pool, ga Wajan tsuntsayen shi kusan duk rubutun gidan da rabci ne, yana da ɓangare na Musamman da yake bawa manyan mutane darasi. Zahrah ta dubi haɗaɗɗan parlourn mai ɗauke da wasu ƙawatattun kujeru, sai ƙamshi yake, ga wasu fitito masu kyau iya haɗuwa ya haɗu. Umar-khan ya kammala shigo da kayansu ya ce. "Ɓangare uku ne a gidan, wancan ɓangaren Yaa Sheikh na tsakiyar kenan, na gefen dama babu na kowa na hango ma babu kowa, ya ce ki zaɓi wanda kike so, ɗayar ki bawa mai aikin naki" Zahrah ta kalli part ɗin hannun hango taga bayan na Yaa Sheikh yafi kyau dan haka ta ce "Na ɗauki na ɓangaren hango ka shigo mini da kayana ciki" tana faɗin haka ya miƙa mata key ɗin ɓangaren ta amsa hana shigewa ciki. Ya kalli Halisa ya ce. "Daman girman kine shiga ɓangaren damar" murmushi kawai tayi, Umar-khan ya riga yasan da ɓangaren Yaa Sheikh da wanda Halisa zata zauna a manne suke, domin akwai ƙofa kai tsaye daga ɗakin Yaa Sheikh wacce zata kawo shi ɓangaren Halisa ɗin. Ya ja mata kayan zuwa jiki, ya yi mata bayanin komai da kitchen da banɗaki komai dai, kana ya nuna mata yadda ake amfani da kayan kallon ɓangaren ta.. "Sai da safe Matar Malam" ta jinjina masa kai. Zahrah ma ya kai mata kayan kana ya nufi nasa gidan. Misalin 1:30 motar Yaa Sheikh tai parking driver ya buɗe masa ƙofa, a hankali ya fito ya ɗan tsaya yana duba ko wanne ɓangare yana yin addu'a sbd ya saba, ganin hadari a garin kuma yasa duk ya rufe Windows na gidan. Ya nufi ɓangaren shi, wanka ya yi ya ɗora jallabiya mai kyau a jikinsa, black tea yake son sha amma bai san yarda zai ba, gashi kuma yasa a sallami masu aikin shi. Haka dole ya zame jallabiyar ya saka kayan barci yana buƙatar hutawa sosai, sbd ya samu peace of mind kwana biyu yana stressed kansa da yawa. Kiran sallar farko a kunan Yaa Sheikh da Halisa domin zamanta wajan mother ta saba da tashin asuba, a hankali ya nufi bathroom tare da sakarwa kansa ruwa mai zafi kana ya yi alwala tare da yin brush, cikin zafin nama ya shirya cikin kyakkyawar shigar shi wacce ya saba, farar jallabiya ya ɗora hirami a kan shi, bakinsa ɗauke da aswaƙ ya nufi Masjid Malik wanda shi ke gabatar da jam'i a can, bayan idar da Sallah ya yi karatu wa jama'a kamar yadda ya saba. 7:00 ya shigo gidan da mmki yake jin parlour ƙamshi mai daɗi, yana ƙoƙarin shigewa part ɗin shi ta ce "Jamɓanduna?" Jin fillatanci yasa ya fahimci ba Zahrah bace amanar shi ce kuma ƴar riƙonsa, ya juya tare da kallon ta, tana cikin wata duguwar riga mai kyau plush pink sai baby hijab a kanta, kai ya ɗauke ta ce. "Anti Zahrah ba ta shi ba, ni tun ɗazo na tashi ina ta kallo" shi dai bai ce komai ba ya shige part ɗinsa tabi bayan shi da kallo kafin ta juya zuwa kollon girke-girken da ta keyi. Yana shiga part ɗin sa ya zauna saman kujera, tare da kiran number Umar-khan babu jimawa ya ɗauka a nutse ya ce "Ka yi komai, kada ya shige kwana biyu a nemi gurbin karatun" yana faɗin hakan ya kashe wayar, tare da kiran wata number mgn ɗaya ya yi ya kashe.. Halisa na zaune taji telephone line na ƙara ta miƙe sauri daman Umar-khan ya faɗa mata yadda ake amfani da ita, tana ɗagawa taji ance "Mrng maaa, the breakfast is ready Yaa Sheikh na jira" Halisa ta ce "Kika ce me?" Ta ce "Abincin Yaa Sheikh ya kammala kina magana da ɓangaren kitchen, yanzu maid zata kawo" Halisa ta taɓe baki tare da komawa ta zauna, babu jimawa wata mata mai fararen kaya ta shigo ɗauke da tray da butar shayi ta ce "Mrng Maa ga shi Yaa Sheikh na jira" Halisa ta amsa tana miƙewa tsaye Zahrah ta fito cikin kayan barci da alama ko sallar ba tai ba, ta kalli matar ta ce "lafiya?" Tai mata bayani ta ya mutsa fuska ta ce "Ok daman ita ce mai aiki bata ta kai, ki sama mini breakfast mai kyau yanzu" matar ta juya Halisa ta riƙe tray Zahrah ta ce "Sai ki fara aikin ki tun yanzu, kije ki kai masa breakfast ɗin ki dawo ki shirya mini kayana a wardrobe" Halisa ba ta ce komai ta juyawa zuwa inda taga Yaa Sheikh ya nufa, bakinta ɗauke da sallama bata sani ba ko ya amsa ko bai amsa ba, yana zaune kan kujera ta ƙarasu har inda yake ta tsuguna ta ce "Ga shi wai" ya gyara zama yana tsiyaya tea ɗin tare da kaiwa bakinsa. "To kai iya wannan kake sha ne? Ko nayi maka abinci?" Da idanu kawai yake bin gefen fuskarta da kallo ta gyara zama ta ce "Mother ta ce kai mijina ne" ya ware idanu da sauri yana binta da idanu, ta buɗe baki zata sake magana caraf ya saka hannu tare da kame bakin..... 08119237616 Paid book Not edited_I unite you with the greatness of God a daina fitar mini da littafin IDAN BA KE. What you want will not be difficult for you to buy. This is not appropriate at all.🫰🏿har zuwa ake a nuna mini wai an samu book ɗin Idan ba ke as free irin ga masifaffiyar nan bari nai ta ihu a media😂 I love my book lovers wherever they are. Amma don Allah a daina fitar da book ɗin... It's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616_ Kasa ƙarasa maganar ya yi sbd gemunsa data kama tana cewa "Yasunan wannan abun? Kuma da gaske ni matar malam ce, naje na faɗawa Ummul nace kace mini matar malam?" Ya lumshe idanunsa na wani lokaci kafin ya buɗe su a kanta tare da ɗora hannunsa akan nata data riƙe gemunsa ya zare yana girgiza mata kai. Zata sake yin magana ya miƙe tsaye yana nufar hanyar bedroom ɗinsa dole sai ya sauya kaya gaba ɗaya ta goge masa maiƙon hannunta a jiki, da sauri ta biyo bayansa ta ce "To baka faɗa mini sunan wannan dugun abin ba, kuma waye zai kaini makarantar ina son zama babbar mace" ya juya tare da kallonta a nutse yana mai mamakin surutun ta, yana da masaniyya akan yadda take amma bai ɗaukan surutun ya yi girma da tsayin haka ba. Bai ce mata komai ba ya juya yana mai sakin murmushi shirmanta a karo na farko da suka kasance tare domin sauran duk baɗini yake ganinsu. Ummul na kitchen Halisa ta dawo ta kalleta cikin kyakkyawan lafazi ta ce "Ba dai haka kika je da hannunki ba?" Ta kalli hannun kuma ta kalli Ummul ta dafe ƙirji ta ce "Wallahi na goge masa" Ummul tai shiru daman tasan za a rina, kuma sam ba tayi mamakin hakan ba. Maid Suhaima ta ce "Wa kika gogewa?" Da sauri Halisa ta ce "Malam, nikam ya sunan wannan dugun abin na fuskar shi? naji yana da laushi aradu" Ummul ta dafe kai da sauri kuma ta miƙe tsaye tana kama hannun Halisa suka nufi can part ɗin Ummul ɗin. Bayan sun shiga Ummul ta kalli Halisa sai kawai tai murmushi kafin ta ce "jeki wanke hannun ko?" A sanyaye ta ce "To" ta nufi bathroom ta wanke tas tare da wanke bakin ta fito har lokacin Ummul na zaune tai shiru tana kallon hanyar toilet ɗin, ganin yadda Ummul tai shiru yasa Halisa faɗin "Ummul" ta buɗe idanu ta ce "Kin gama? Lokaci na tafiya zaki buƙaci abinci a can, lunch box naki yana cikin mota" suka fita Main parlour daidai nan Zahrah ta fito da kayan barci da alama ko sallah ba tayi ba, balle ashirin zancan wanka tabi Ummul da kallo ta ce. "Wace ke? daga ina bana hana ana shigowa kai tsaye ba, ba tare da permission ba, ke kuma jeki gyara mini bed ki haɗa mini ruwan wanka" Halisa ta ce "makaranta za a kai ni, idan na dawo zan haɗa miki sai Kiyi wankan" Ummul ta danne dryar data zo mata. Da mamaki sosai Zahrah ta ce "School? Da izinin waye kuma? babu wata makaranta da zaki, baki zo gidan nan dan kije makaranta ba" ta faɗa tana fisgo hannun Halisa daga kusa da Ummul. "Ke kuma da kika tsaya kina ƙwalala mini idanu da alama kina da masaniyya, tell me waye zai kai ta makarantar" "Ni ne" ya faɗa a taushashe yana mai fitowa daga inda yake tsaye, yana sanye da sabbin shiga saɓanin ta ɗazo, farar dakakkiyar shadda ya sanya mai jamper da babbar riga, ya ɗora hirami ɗaya a kansa ɗaya kuma a kafaɗa.. Ta saki Halisa ta nufi inda yake ta ce "My Excellency amma daga zuwa sai batun makaranta, kuma ya kamata a faɗa mini, ni bani da ra'ayin yarinyar nan tai makaranta" Halisa ta tura baki tana mai jin haushin yadda Zahrah ta wani matsa kusa da Yaa Sheikh haka kawai taji zuciyarta ta cunkushe, amma hakan bai hanata cewa. "Amma ai Dada tana da niyya ko Anti, da izinin zani makaranta ta baki...." Cikin rawar murya Zahrah ta ce "Oh ok it's ok you can go, but waye zai kai ta?" Sai a lokacin Ummul ta ce. "Umar-khan, kafin driver ya fara kai ta, Aliyu yana da lecture da ɗaliban shi, zai iya magana" Ummul ta faɗi haka ne domin Zahrah ta bawa Yaa Sheikh hanya. Haka kurum Zahrah taji sha'awar kasancewa da mijinta ya bijiro mata, musamman da ƙamshin Roja ke ƙara narkar da zuciyarta, Yaa Sheikh na musamman ne, idan zaka kalli cikin idanun shi yayin magana to ba zaka taɓa yi masa ƙarya ba, ɗaya daga cikin baiwar shi kenan. Babu kunya ta rungome shi a gaban Ummul tana faɗin "Am going to miss you My Excellency back soon please" gani sukai Halisa ta juya da sauri zuwa part ɗin ta, Ummul ba tai magana ba. A hankali ya zame jikinsa daga na Zahrah ta ce "Bari naje nai wanka da Sallah bye" Ummul ta kalli lokacin 7 harta gota ba dai sallar asuba ba, sai dai walaha. Bayan shigewar Zahrah Yaa Sheikh numfasa yana mai gyara murya a kasalance ya ce. "Mun kwana lafiya, Ummul?" Ummul ta ce "lafiya lou, kaga ƴar rigima ko? kamar kuka naga ta nayi?" Ya saki fuska daga kamewar da ya yi shima yana duba lokaci a diamond rolex watch ɗinsa. "Aje a duba, kin san hali tun ba yau ba" tai murmushi ta ce "Wallahi fa" ta nufi part ɗin Halisa shi kuma ya goya hannunsa a baya tare da tsaiwa a tsakiyar parlourn. Kwance Ummul ta samu Halisa ta cire baby hijab ɗin jikinta sai kuka take kamar ranta zai fita. Ummul ta zauna cikin sakin fuska ta ce "Matar Malam lafiya? Wani abun ne? ko wani gurin ke miki ciwo?" Kuka kawai take taƙi magana tamkar zata shiɗe haka take kukan. "Faɗa mini mene? ke dawa" ta miƙe zaune cikin shassheƙar kuka ta ce "Ummul Dada zani, ni na fasa zaman wajan Dadata zani ki saka a bayar dani" Ummul ta ware idanu da kaɗuwa sosai ta ce. "Yanzu Matar Malam ina ke ina zuwa gida, keda kika zo bautar Ubangiji? Maza tashi akai ki makarantar ga shi can yana zuwa kin san kuma akwai inda zashi" idanunta ya yi jajir hawaye na zuba daga cikinsu ta ce "banso, na fasa makarantar ni rugarmu zan koma" yin duniya taƙi yarda Ummul ta ce "To dai na kukan bari na faɗa masa" ta juya tana mmkin sauyin da yarinyar ta samu lokacin gudu, me akai mata me kuma ya sauya mata tunaninta daga sha'awar zuwa makarantar. A tsaye Ummul ta same shi, bai kalleta ba amma tunaninsa da hankalinsa na kanta ta ce. "Kuka take sosai, wai bata son makarantar kuma a bayar da ita can ruga" maimakon ya fita sai ya juya zuwa part ɗin shi ba tare daya amsa maganar ta Ummul ba. Ta gane yaran kuraman nashi dan haka ta ƙarasa juyawa zuwa sashin na Halisa. kanta kife idanunta data rufe su take hango rungumar da Zahrah taiwa Yaa Sheikh, kuma bata manta maganar da Maimoon ta faɗa mata ba, idan kana son mutum da zarar wata macen ta raɓesa zaka ji kishinsa, ita a yanzu ta kasa fahimtar me ya sa taji komai ya dameta zuciyarta babu daɗi ne? Da wannan tunanin Ummul ta dawo ɗakin tare da ce mata "Ki saka hijab ɗin, kije Abban naki yana kira zai mayar dake" ta kalli Ummul sosai amma bata ce komai ba, hijabin a hannu ta nufi part ɗinsa. Ummul ta girgiza kai tana sakin murmushi kawo yanzu ta gama gane abin da ke damun Halisarta ta fahimci zallar rigima da shagwaɓa ce ke damunta akan dalili mara toshe. Yana zaune hannunsa riƙe da azkar yana dubawa yaji saukar siririyar muryarta tayi sallama, amsata ya yi a rai, yana mai ɗago kansa tsaye ya ganta taƙi ƙarasuwa sai cukurkuɗe hijab ɗin hannunta take. Shi bai fiya son yin surutu ba kwana biyu kuma tana neman sashi, gashi kamar ciwon kanshi na neman ta shi. Ajjiye azkar ɗin hannunsa ya yi, tare da miƙa mata hannunsa alamar tazo, kanta a ƙasa ta matsa inda yake zata zame a ƙasan ƙafafuwansa ta zauna a ƙasa ya kamo hannuna tare da zaunar da ita a gefen shi yana kafeta da idanunsa. Kafin ya ce komai ta fashe da kuka sosai tana jan numfashi, ya tallafo haɓarta da hannunsa mai taushi idanunsa na yawo a fuskarta. "Ya akai? Ke dawa?" Ya faɗa yana mai sauke numfashi tare da jan jikinsa zuwa jikin kujerar. Muryata na rawa ta ce "Abba gida zani, ni Dadata zan koma" ya lumshe ido kana ya buɗe a sauƙaƙe cikin son dakatar da kukan dake neman fasa masa kai ya ce. "Karatun fa? Ban son rigima" ta girgiza suna haɗa ido ta tura masa baki ta ce "Shi ma banso, kuma..." Sai kuma tai shiru tana ɗauke kai. Kallon yadda fuskarta tai jajir ya yi sosai duk ta birgita kanta sbd rigima, he's still holding her face ya fesar da iska ya ce. "Gida kike so? Ta ɗaga masa sai kuma ta ce "Eh wajan Dada zaka kaini kaji Abba" "Baki son Malam?" Ya tambaya kai tsaye domin shawo kan rigimar tata, ta riƙe hannunsa ta ce "Ina so bana, to ba naga Anti Zahrah ta rungomeka ba, shi ne naji kawai kuka yazo mini kaga gwanda na tafi gida" ya miƙe da sauri tare da shigewa bedroom ɗinsa not too long ya dawo fuska a kame, a tsaye ya sameta kallon da yake masa yasa ta saka hijab ɗin. Kana tabi bayansa babu kowa a main parlour dan haka ya nufi compound direct. Yana zuwa Umar-khan na fitowa daga mota tare da faɗin. "Good Mrng Yaa Lee" kai ya ɗaga masa ya shiga bayan mota, itama Halisa ta shiga bayan motar gatekeeper ya buɗe musu fita. Sun jima da tafiya amma abin mamaki Halisa bata ce komai ba, ko Umar-khan bata gaisar ba, a haka suka ƙarasa Al Aqeeq International School. Umar-khan ya yi parking a harabar makarantar tare da fita yabar musu motar, ƙoƙarin buɗe motar take ta fita taji ya kamo hannunta taƙi yarda ta kallesa alamar dai She's still angry with him. Wani sirrin baƙin zare ya ɗaura mata a hannunta, ya riƙo hannun da kyau ta yadda dole ne ta matso kusa dashi idan taji an jawota, sukai kusa da juna. "Ƴar fillo" ya ce a hankali da sauri ta kallesa sai taga ba ita yake kallo ba, ta ce "gidan zaka bayar dani?" Sai a lokacin ya juya gaba ɗaya zuwa gareta a hankali numfashinsa ke sauka cikin murya ta yanayin gajiya da kasala ya ce. "Anti ba zata sake ba, Amma idan Anti bata rungome Malam ba waye zai rungome shi?" Bakinta na rawa ta ce "Ni matar malam zanyi" ya buɗe ido sosai da sosai yana mmkin ƙarfin halinta. "Da gaske ni kullum sai na rungome ka nace maka mijina" bashi da wani option wanda ya shige bin bakin mganar da kallo ya daɗe yana kallonta kafin ya ce. "Uhm" da sauri bakinta na rawa ta ce "Ai na iya bari ka gani" kafin ya yi magana ko wani yunƙuri yaji gaba ɗaya ta zagaye hannuwanta tare da rungome shi, ta ɗora kanta a ƙirjinsa, ya buɗe idanu da sauri cikin In-inar data zo masa ya ce. "Su...su... Subuhanallah Ya Allah....Ta saki dry sosai ta ce "Abba Allah na iya kaji ai?" He was completely lost for words and just shook his head. Bayan wasu giftawar seconds ya nuna mata ƙofa da hannu ta buɗe ƙofa tare da fita, a hankali shima ya buɗe ƙofa ya fita tare da fitowa yana ƙara covering jikinsa da kyakkyawar shigar dake jikinsa. Umar-khan na ganin fitowar Yaa Sheikh ya ƙarasu wajan yana mai sakin murmushi,kai tsaye office ɗin headmaster school ɗin Yaa Sheikh ya nufa, gaba ɗaya teachers na school mmkin ganin Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu a cikin makarantarsu ya kama su, kowa sai durƙusawa yake yana miƙa gaisuwa a nutse cike da kamala nutsuwa yake ɗaga musu hannu yana ƙara kame kansa wanda yake fidda kwarjinin shi. Cikin mutunci Headmaster ɗin mai suna Ayyan ya miƙe yana gaida Yaa Sheikh. Umar-khan ya ce "you did the interview for her, then you look at the one class that is suitable for her" Headmaster ɗin ya kalli Halisa cike da birgewa ya ce. "What's your name?" Tai ƙasa da kanta sam bata ji me yace ba, balle ta fahimci me yake cewa. Ya ɗauka bata gane english sai ya juya zuwa cewa. "ma asmuk? kam eumarka?" Nan ma tai shiru Ayyan ya kalli Yaa Sheikh cike da martabawa ya ce "سنضعها في الصف الأول حتى تتمكن من أخذ الدروس" _“Zamu sakata a matakin farko domin ta fara darasin”_ cewar Ayyan Yaa Sheikh ya numfasa ba dai ce komai ba. Ayyan ɗin ya ce. "Zata samu gogewa cikin ƙaramin lokaci Insha Allah, kuma a nemata mai darasi a gida,that will help her study more" Umar-khan ya yi murmushi ya ce "How long do you think she can take the time before she can learn everything, and get experience" Ayyan ya ɗan kalli Halisa yana karantar how smart she's kafin ya ce "I can't say how long it will take,But she will get good academic training" Umar-khan ya ce "that's good, amma matar...." Gyaran Muryar da Yaa Sheikh ya yi ya hana Umar-khan faɗin abin da ya ke shirin faɗa ɗin. Yaa Sheikh ne ya fara miƙewa yana kallon lokaci a nutse ya ce. "A kula, banda wasa" ta miƙe tsaye tana shirin yin magana ya yi waje abinsa domin yasan zata iya faɗin abin da ba shikenan ba, bai shirya ɗaukan abin kunyarta cikin mutane Yanzu ba. Idanunta ya cika da hawaye sosai tana neman yin kuka a haka Headmaster ɗin ya kaita Jss 1. Akan idanunta kuma motar Abban nata da Umar-khan ta fita waje. Ita ɗaya ce a table nata, gaba ɗaya class ɗin basu da yawa dukkansu farare dasu gwanin sha'awa, itama ta saje dasu sbd farin da take dashi mai tsari. Shiru tayi tana kallon kowa da idanu kowa na ajin harkar gabansa yake a haka Headmaster ya gabatar da ita ya fita. Babu jimawa wani kyakkyawan balarabe ya shigo cikin jallabiya ash ya ɗora half ɗin hula a kansa, bai tsaya jiran gaisuwarsu ba. Ya nufi blackboard inda suke duba kamar computer haka ya shiga latsa abubuwa sai ga sunan subject ya fito _Social studies_ A ƙasa kuma aka rubuta _MEANING, SCOPE AND NATURE OF SOCIAL STUDIES_ Matashin ya kalli students ɗin dake gabansa, har lokacin idanunsa bai kai inda Halisa take ba, cikin kamala ya ce. "Alhmd, yau zamu fara da meaning na social studies, please who can tell me the full meaning of Social studies?" Duk sukai shiru ya ce. "It's okay" ya ɗan duba abu kaɗan kana ya mai da attention nasa ga ɗaliban ya ce. _“Social studies can be defined as the study of man and his environment. Social studies can also be defined as the totality of man’s physical and social environment”_ daga nan ya yi musu explanation yadda zasu fahimta ya saka english ya saka Larabci maybe they can understand very well. Yana ƙoƙarin yin magana yaji ance. "To aradu nidai tunda ka fara magana ban san me kace ba, idan zaka faɗa da hausa kawai ka faɗa ko kayi shiru" ya juya gaba ɗaya zuwa direction ɗin da daddaɗar muryar dake tashi, yana juya a ƙaramin bakinta idanunsa ya sauka, magana take sosai ko haɗiyar yawo ba tayi. AZAAN ya ware fararen idanunsa akanta da kyau, da alama ita ɗin new student ce, yasan magana take amma baya gane me take cewa sosai, ya dai san hausa take. Ya ɗauke bai tankata ba ya ce. _“SCOPE OF SOCIAL STUDIES”_ _The word “man” in the definition given above connotes human beings while man’s environment has a huge influence on mankind in all spheres of life. Man’s environment affect their language, dressing, food and every other thing one can think of in the society,_ _Man also interacts with two environments which are:_ Physical environment (Natural) Social environment (Artificial)". "Tab ni dai dama ba wannan makarantar aka sani ba, malamin ba babu abin da ya iya" Azaan ya dubi Halisa ya ce "What's your name" ta tura ƙaramin bakinta ta ce "Me kace?" Wata wacce ba zata shige age mate ɗin Halisa ba mai suna ABIR ta ce "Ya ce ya ya sunanki?" Halisa ta ƙaramin murmushi kawai cikin siririyar murya ta ce "Halisa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Azaan ya buɗe idanu da kyau cike da mamakin jin sunan data alaƙanta kanta dashi, Yaa Sheikh take nufi ko wanne? Dama yana da yarinya yaushe ma ya yi aure har ya samu yarinya kamarta?. Azaan ya ce. "Abir make her understand, explain to her" Abir ta ce "Okey Sir" mai Hali baya fasawa domin Azaan na shirin fita ta ce "Kuma na manta na faɗa maka ina da aure" Azaan ya kalleta sai kawai ya fice dan ya lura bama tasan shi kansa auren ba har take cewa haka. Ya tafi cike da sha'awar surutunta wanda ya birgesa lokaci guda. Abir taiwa Halisa bayanin komai na topic ɗin cikin harshen hausa, ta ce amma ta rage surutu da yawa a haka ta ƙare zaman makarantar wani karatun ta gane wani a'a, Umar-khan da kansa yazo ɗaukanta sbd Yaa Sheikh yana can wajan lecture ba zai samu dama ba. Sarki Ahmad Nuran Kingdom. Da sauri yake tafiya hannunsa zube cikin aljihu cikin yanayin kaɗuwa da kuma tashi hankali, saukarsa kenan ƙasar kullum cikin tafiye-tafiye yake, kana kallon fuskarsa kasan baya cikin nutsuwa da walwala. Ko'ina ya gilma acikin gidan sarautar bayi da kuyangi ke zubewa suna gaida shi, amma kallon arziƙi basa samu daga gare shi. Kai tsaye sashin Fulani Atine ya nufa, wata kuyanga ta sanar da Fulani Atine zuwan yarima cikin jin daɗi ta bashi izinin shigowa bayan ta sallami hadiman nata. Tsaye ya yi yana kallonta kafin ta ce. "Meke faruwa da kai El-bashir? Yaushe ka tafi da har zaka dawo?" Yaƙi magana sai huce yake tamkar zakin dake neman abinci bai samu ba. "Wannan ɓacin ran na mene What is the reason for bringing you back to this country now?" Ya ɗauke idanunsa cikin ɗaga murya ya ce "Idan ina raye sai naga bayan Yaa Sheikh hankalina zai kwanta, sai na tabbatar ya wahala a rayuwa kamar yadda ya wahalar dani, zan tirkesa na musguna masa kamar yadda ya sanya ni cikin damuwa da ƙonar zuciya na tsayin shekaru, sanyi amfani da uniform ɗin dake jikina na police na jasa zuciya hanyar da zata ɓata suna da martabar da yake iko da su, ba zan taɓa farin ciki ba muddin ina ganin gilmar Yaa Sheikh a duniya" Fulani Atine tayi murmushi tana mmkin zafin zuciyar da El-bashir yake da ita, a hankali ta ce "El-bashir duk bai kai wannan extent ɗin ba, pls i want u to calm down" cikin zafin zuciya El-bashir ya ce "Ya kai har ya shige extent ɗin da da kike faɗa, a wannan karan dole nayi gaba da gaba da Yaa Sheikh dole nai amfani da mutum mafi kusanci da shi wajan ruguza rayuwarsa data ahhalinsa" Fulani Atine ta ce "Kana da hujja kenan? kana da shaidar da zaka iya kurfanar da Yaa Sheikh a court? Kada ka manta lokacin da al'amarin nan ya faru Yaa Sheikh baya ƙasar bare ka zurfafa cewa shi ya aikata, kada ka tirke kanka maimakon Aliyu, nice shaidarka akan idanuna komai ya faru" El-bashir ya riƙe hannun Fulani Atine ya ce "Ki taimaka mini na ɗauki revenge akan Yaa Sheikh, ba zan iya ba, na kasa haƙura na kasa jurewa Fulani, ya rabani da jin daɗina" Fulani Atine ta ce "Kafin ɗaukan fansa, dole ka nemi kusanci da Yaa Sheikh, dole ka nemi gurbi a zuciyar ƴar fillon da ake magana, kasan yadda kayi ta fifitaka akan shi" El-bashir yai shiru for some minutes kafin ya ce "Mene amfanin saka ƴar fillo cikin al'amarin nan?" Fulani tai murmushi yaro yaro ne, daman ance daka na gaba ake gane zurfin ruwa, ta ce "Idan ka taɓa ƴar fillo kamar ka taɓa zuciyar dake sarrafa tunani Yaa Sheikh ne, nasan abin da kai baka sani ba, kayi hakan" ya shiga safa da marwa He was completely at a loss, unable to understand what she was saying to him. "Nayi masa da baibayi ta ko'ina ina da investigator a cikin ma'aikatan dake aiki a can gidansa na Madina" yana faɗin hakan ya fice rai ɓace. "Well-done El-bashir Ahmad Nuran Sarki, kana yin komai bisa tsari kamar yadda aka shirya" Fulani Atine ta faɗa tana bin bayansa da kallo. Ma martaba Ahmad Sarki ne ke tafiya shi da Khalil yana yi masa bayanin sauyawar da El-bashir ya yi cikin kwana biyu. Mai martaba na ƙoƙarin yin magana El-bashir yazo ya shige ta gabansu tamkar zai ta shi sama, meke damun El? Kamar wanda ya zauce ko wani abu ya taɓa tunaninsa? "That's what am going to tell you, El ya sauya ko dai akwai abin da yake faruwa ne?" Mai martaba ya numfasa bai ce komai ba ya shige babban sashinsa, Khalil kuma ya nufi wajan Oum Juwairah. Halisa na zaune tana duba Assignment ɗin da aka bata juya littafin kawai take amma ta rasa ta ina zata fara. Tunda ta dawo gida bata ji motsin Yaa Sheikh ba, ko taji Ummul ta ce akai masa abinci. Ta miƙe tsaye jikinta sanye da wata riga mai kyau wacce tazo mata iya gwiwa wandon jikinta 3gauter ne. Zahrah data fito daga ɗakinta zuwa parlour hannunta riƙe da plate ɗin da aka soya masa ƙwai ta kalli Halisa ta ce. "Ke ubanwa ya ce kina saka wannan kayan a cikin gidan nan?" Halisa ta kalleta ta ɗauke kai ita bata ita take ba "Kan uba? Ke dan ƙaniyarki ni sa'ar ta ruga ce ina magana kina jina?" Halisa ta murguɗa baki cikin tsiwa ta ce "Ban ɗauka magana ki ke ba" hannu ta ɗaga zata wanka mata mari taji an riƙe hannu, ƙamshin Roja daya cika parlourn ya gama shaida mata wanda ya riƙe ta. Ta juya da sauri har lokacin yana riƙe da hannunta ta ce. "My Excellency yarinyar ta fara raina ni ne, ka barni naci.." wata kyakkyawar tsawa ya daka mata wacce bata taɓa jin irinta ba, Halisa ta firgita da tsawar ga Yaa Sheikh ta kwasa da gudu zuwa part ɗin Ummul tana haki. Zahrah ta ce "Tsawa kai mini akan wannan mara gata da ƴancin ƴar aiki na ce ita ga Yaa Sheikh?" Ya saki hannunta fuska kame yana gyara yanayinsa ya ce. "Ba a kanta ba, Akan zagin da ki ke mana, idan zaki ki bari kije waje" ya faɗa a taƙaice kwarjininsa yasa Zahrah kasa tanka masa a ranta kuma ta ɗauki niyyar cin uban Halisa. Cike da kissa da buƙatar mijinta kusa da ita, cikin dake jikinta ya ƙara sanya mata son kasancewa da namiji ƙwarai da gaske. Ta rungome Yaa Sheikh tana shassheƙar kuka ta ce "Amma kasan ni ba sa'ar ta bace, kawai zan mayar da ita, tunda akwai masu aiki a gidan" ya yi mata shiru shi dai bai kuma hanata rungome shi ba, kallo ɗayan da ya yi mata ya karanci yanayinta. Ganin abin da take ƙoƙarin yin yasa Yaa Sheikh faɗin. "Asstagafirullah Allah" Zahrah ta tsaya tana kallon shi kafin ta ce "what do you mean by that? Am your wife exit?" Ya zameta daga jikinsa tare da juyawa zuwa part ɗinsa sai da ya kusa shigewa ya ce "Lokacin Sallah, akwai alwala tare dani" tai murmushin jin daɗin ganin ya juya da alama alwalar da yake riritawa ta lalace dalilin rungumar shi da tayi. "Shikenan, anjima zan zo" ta juya zuwa nata part ɗin. Ummul ta kalli Halisa dana cewa "Wannan hakin fa? yana da kyau ki nutsu sosai matar malam" Halisa ta dafe ƙirji ta ce "Wallahi na tsorata sosai Ummul, Allah yasa ba dokan Anti Zahrah ba" Ummul ta dubeta ta ce "Doka wanne iri, ni wannan Assignment ɗin naki ba Abin da na gane, kije wajan Abban naki" ta kwanta cinyar Ummul tunanin Dadarta ya faɗo mata a rai. Tai shiru can kuma ta ce "Ummul Abba mijina ne ko?" "Me ya sa kike tambaya matar malam?" Cewar Ummul. Halisa ta miƙe zaune zance na cinta ta ce "Ummul naji baya ce mini matar shi, kuma ni bana son naga Anti Zahrah..." Wayar Ummul tai ƙara hakan ya hana Halisa ƙarasa maganar. Bayan kammala wayar Ummul ta ce "kije ya duba littafin naki,ko a buge ki a makaranta" Halisa ta ɓata fuska ta ce "haka kurum ya dakeni, zaro ido naga ya yi fa?" "Ko zai daki kowa, Ai banda matar malam, kawai baya son taurin kai ne, kuma na lura kina da shi tun ba yau ba" Halisa zata sake magana Ummul ta ce "Tashi kije, sai ki dawo kici dinner muyi karatu" ta miƙe tana ɗora hula akanta tana tafe tana waƙa da fillatanci. A hanya taci karo da Bara'at tai mata murmushi. A hankali ta shiga parlourn dake part ɗinsa, gaba ɗaya baya cikin parlourn sai kyakkyawan ƙamshin daya bari wanda yake tashi a hankali, tabi ƙofofin dake parlourn da kallo ta rasa wanne Kofar bedroom ɗinsa, a hankali take tafiya kamar mara gasky tana raɓewa jikin bango ta shiga leƙa wani ɗaki tsarin bedroom kaɗai ya tabbatar mata shi ne. Ji tayi an tsaya a bayanta ta juya da sauri taci karo dashi tsaye towel a hannunsa yana tsane gashin kansa daya kwanto, ganin ruwa na zuba a jikinsa tasan wanka yayi, maimakon taji kunya a matsayinta cikakkiyar bafullatana sai ta zubawa wani waje a jikinsa ido. Ya tsare ta da idanu. "Abba" ta faɗa dimple ɗinta na lomawa ya ɗauke kai ya ce. "Me kike leƙe? Kin yi ajjiya ne?" Ya tambaya yana bata hanya ta tura baki fuska a narke sai juya bakinta take ta ce "Ummul ta ce ka koyan karatu, ni ba kai nake nema ba" ya dubi bakin maganar da kyau, ya ɗauke kai wato fushi take har yanzu. Ganin yaƙi bata amsa ta saki kuka tana juyawa zata bar wajan, ya damƙi hannunta ya dawo da ita gabansa. Cikin kula da tausasa harshe ƙamshin shower gel yana fita daga cikinsa ya saka hannu tare da tallafo haɓarta ɗaya hannun ya dafa kanta dashi, tayi saurin riƙe ƙugunsa da duk hannunta biyu. "Abba" ta ƙara faɗa idanun na cika da hawaye wanda suka ƙarawa idanunta sheƙi. "Rigima dai matar malam, nayi busy banje makaranta ba" ta tsora masa idanu masa idanu tana ƙara riƙe ƙugunsa ta ce "To darasi zaka duba mini, Abba kuma me ya sa Anti Zahrah take riƙe ka" ya saki fuskar yana dafe kai ta saki kuka zata juya ta fita ya saka hannu ya ɗaga ta cak tare da yin bedroom ɗinsa da ita... If you read for free🤷🏾‍♀️ it's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616.Kokawar ƙwace kanta take amma ta kasa ya sauke ta saman kujerar dake kusa da bed ɗin ɗakin nasa, bai kula ta ba ya nufi deep freezer ya ɗauki Apple guda ɗaya wacce tai sanyi. Cikin nutsuwarsa da son kame kansa daga yanayin da yake ciki ya nemi waje saman gado ya zauna, kyakkyawan numfashi ya sauke yana ƙara daidaita kansa a karo na babu adadi. Ya ɗago kai yana duban direction ɗin da take, dole sai ta sanya ma gantu ya miƙa hannu cikin taushin murya ya ce.. "Zonan naji, rigimar me ce?" kanta a ƙasa ta ƙarasa inda yake domin bata iya bijirewa umarninsa. Ya dubeta da kyau amma taƙi yarda ta kallesa cikin son jin meke faruwa ya kamo hannunta zuwa inda yake zaune muryarsa har kullum a taushashe ya ce. "Ya akai matar malam? waye?" Hawaye na sakko mata ta ce "Abba kai ne, Mother ta ce kai miji na ne, me ya sa kake bari Anti Zahrah take taɓa ka" ya dafe kansa cike da mmkin kaifin bakin Halisa ya ce "Ba zaki bar mganar mijin nan ba? You're too young to understand that" "Abba ina son ka ai" Ya girgiza kai ya lura rigima take ji kuma ta shirya bashi kunya a Idanun kowa. Yana mamakin yadda maganar miji ta zauna a bakinta raɗau kamar wacce akewa bita akan hakan. Ya dubeta yana dawo da ita gefensa tare da riƙe hannunta ya ce "Matar Malam ki bar mganar mijin nan, ba zaki gane ba, ki dai bar Anti ta faɗa ok?" Ta maƙale ka faɗa alamar bata amince da zancan ba kaifin ta ce "Abba...." Sai kuma tai shiru ya ɗago kanta tare da tallafo haɓarta yana duba cikin idanunta da hawaye ya kwanta. "Matar malam" ta marairaice fuska tare da faɗin "Abba yaushe zan zama matar malam ɗin? Kuma yaushe zan zama kamar Anti Zahrah nima na dinga rungomeka?" Ya kau da fuska tare da lumshe idanunsa a hankali ya ce "Baki son Antin naki tana haka? Ni kuma fa" ya ƙare maganar yana ƙara riƙe fuskarta a hannunsa da kyau, gaba ɗaya ta marairaice fuska ita a dole bata son abin da Zahrah ke masa, haka kurum ranta ke ɓaci taji kuka yazo mata ta ce "Abba zanna yi maka, da safe da rana, da daddare" ya shafa kanta cikin nutsuwa ya ce. "Kada mu fara haka, ki tsaya a ƴar rainonki" ta langwaɓe kai ta ce "Abba ni ban son rainon Ummul ta ce kayi mini karatu" bai biyewa surutun nata ba, ya amshi littafin nata duk dan a rabu lafiya, burinsa kuma bai shige ta tafi part ɗinsa ba, ko zata barshi ya samu salama daga surutun nata mara dalili da toshe. Cikin sauƙin harshen yake mata bayani akan Social studies ɗin, da kuma muhimmancinsa. Ya kama hannunta ya ɗora saman littafin a hankali ya ɗora nasa hannun akan nata ya fara nuna mata yadda zatai rubutu, yana lura da ƙwazonta ko dan akwai son karatun a ranta duk abin da ya nuna mata ɗauke shi take. Ta ɗago kai ta kallesa taga hankalinsa baya kanta gaba ɗaya ya tattara nutsuwarsa zuwa ga abin da yake nuna mata. "Abba" Halisa ta faɗa tana ƙarewa fuskar shi kallon yaƙi kulata ta leƙa fuskar shi ta ƙara cewa "Abba kana da kyau sosai, kaga gobe idan naje makaranta zance mijina ne ya yi mini aikin ko?" Nan ma bai kulata ba amma tsat yake ɗauke zancan nata a zuciyarsa tasbihi kawai yake. Taja gemunsa cikin sauri ya miƙe tsaye yana damƙa mata littafin tare da janta zuwa bakin ƙofa kamar an masa dole ya ce. "Ki kula, akwai sanyi" ta ɗaga kai tana faɗin "To Abba" har ta juya zata fita ta dawo da sauri zuwa bedroom ɗin Yaa Sheikh kuma a lokacin ya juya hannunsa ɗauke da azkar na dare yana dubawa.. Kyakkyawar rungumar data bashi da baya ya sanya Azkar ɗin suɓuce masa cikin In-inar data zo masa a lokacin zufa na yanko daga goshinsa ya ce. "Yaaa....yaaaa... Allahu ya ya... Ya Rahman, Yasubuhanallah" ta saki dry tana riƙesa ta ce "Abba kaga nayi maka ta dare sai da safe" kasa magana ya yi tana sakinsa ya buɗe ƙofar bathroom ya shige ciki... Cikin farin ciki da murna yau itama tayi abin da Anti Zahrah keyi ta nufi part ɗin Ummul. Ummul ta kalleta ta ce "Kin dai gane karatun ko?" Ta ɗaga mata kai kawai tana jan plate ɗin da Ummul ke mata, tana cikin cin abincin ta ce "Ummul kin same?" Ummul ta girgiza kai ta ce "Sai kin faɗa matar malam" Halisa ta ture abincin dan ba wata yunwa ta keji ba ta ce. "Me ya sa gumi ke fitowa a goshin Abba? Kuma naga wani abu a jikinsa ba, duk sanda na gani kaina juyawa yake" Ummul a zuciyarta addu'a take Allah ya sa ba wata maganar da zata bata Kunya zatai ba, ko wani abu ne ya faru tsakaninta da Yaa Sheikh ɗin take son faɗa, duk tai mamakin haƙurinsa, daya kawo har yanzu, ta riga tasan waye Yaa Sheikh da kuma yadda ya ɗauki al'amarin Halisa da girma ko yana jin tsoran yanayin rigima da ƙuruciyarta ne?. Halisa ta dawo da Ummul daga tunanin data tafi ta hanyar faɗin "Ummul ni ina son Abbana" Ummul ta ce "Kina iya bakinki, ba dan abinci kawai Ubangiji ya bamu ciki ba, hadda ɓoye maganar da bata da ikon a faɗa da riƙe sirri, ki nutsu idan kina wannan shirman Abban naki ba zai so ki ba" Halisa ta kwanta tana juyawa Ummul baya ta ce "to naga mijina ne, kuma ina son sa" kamar wacce aka tsikara ta miƙe da sauri domin abu biyu ne ya faɗo mata a wannan lokacin, da maganin da El-bashir ya bata, wanda take tunanin shi ne ya sanya Abban nata Yaa Sheikh yake fitar da zufar goshinsa, sai kuma tuna Dada da tayi. Ummul tabi bayanta da kallo sai kawai ta girgiza kai ta ce "Ubangiji ga Danejo ka shirya mana ita, Allah ka kawo zama na har abada tsakaninta da Aliyu, ita ce farin ciki Aliyu, Aliyu shi ne garkuwarta" Halisa na fita ta nufi part ɗin Zahrah lokacin tana tsaye gaban madubi sai turare take fesawa ajikinta, ta sanya wasu kaya kamar zata gasar rawa a club Halisa ta ce "Anti" ta juya ta kalleta ta ce "wai ke wacce daƙiƙiya ce ne? Ko acikin ƴan fulani ke daban kike, kawai ki faɗo ɗaki kamar wata dabba?" Halisa taji zagin har ƙasan zuciyarta ta kalli Zahrah ta ce "me ya sa kike haɗani da dabba? Bayan ni mutum ce kamar ke?" Zahrah ta tsaki ta ce "baki da wani suna da ya shige haka, and you'll never be like me never" ta goge hawayen idanunta ta ce "Yaushe zan miki aikin ki? Ina son ki mayar dani rugarmu, ban san haka kike ba kinyi al'ƙawarin kula dani da kuma Dadata" Zahrah tai wata dry ta ce "Aikin kin kusa gabatar da shi, dan kin gama zan mayar dake nima zamanki bai mini ba, yanzu bani da lokacin zani wajan mijina" Halisa ta kalleta da sauri zuciyarta har ɗagawa yake sbd jin zata wajan Yaa Sheikh. Ta juya idanunta fal hawaye tare da barin ɗakin. Zahrah ta nufi part ɗin Yaa Sheikh ko'ina na part ɗin gwanin sha'awa ne, ko wacce kusurwa an kafe kalmar sunan Allah, a hankali sautin ƙira'ar Alkur'ani ke tashi, amma ta nemi ƙofar bathroom ɗin nasa ta rasa. Ta juya da sauri zuwa sashin Ummul ta sameta tare da Bara'at daga tsaye ta ce "Naje part ɗin Yaa Sheikh na rasa ina ne bedroom ɗinsa, ina buƙatar sani sbd ina son kasancewa da mijina" "Amma shi mijin na son kasancewa dake?" Cewar Ummul. Zahrah ta ce "Ni matarsa ce, dole ya buƙace ni" Ummul tai murmushi ta ce "Zahrah ki zauna muyi magana mai muhimmanci, maybe ki gane sosai" Zahrah ta ce "ki riƙe maganarki mijina nake tambaya" Ummul ta ce "Malam yana kan rabuta Alkur'ani yanzu, kafin azumi yake son kammala rubutun, ba zai iya ganin kowa ba" Zahrah ta juya rai ɓace gashi masifa ke cinta kamar taci babu. Ummul bata da zaɓi wanda ya shige faɗin hakan, tasan ba lallai Zahrah ta samu abin da take so ba. Washegari tun da Halisa ta tashi bata da wani karsha shi ta wakana da tunanin ko Zahrah ta je wajan Abbanta? Tai sallah Asuba tare da Azkar ɗin da Ummul ta bata, 6:30 ta nufi kitchen tasan a nan zata samu Ummul ɗin, Tana zuwa Bara'at ta ce "Sannu da zuwa Halisa" Suhaima ta ce "Baki zo da wuri ba" tai murmushi kawai ta ce "Ina kwana Ummul?" Cike da farin ciki Ummul ta ce "Allhmd. Sanyi bai ka maki ba?" Ta ɗaga kai tana taya Bara'at aiki tare da ita suka kammala breakfast. Ummul ta bata shayin Yaa Sheikh ta kai masa bayan ta shirya zuwa kayan makaranta. Ta amshi shayin ta mufi part ɗinsa kai tsaye. Fitowar sa kenan sbd barcin da bai samu ba jiya, kana kallon yanayinsa da sauyin idanunsa kasan akwai matsala. Yana zama kan kujera ta shigo bakinta ɗauke da sallama ta ajjiya tray ɗin tana zubewa wajan ƙafafuwansa ta ce. "Abba ina kwana?" Ya jinjina tare da zuba black tea ɗin ya shiga sha a hankali ta gyara zama ta ce "Abba" ya ware ido a kanta ba tare daya tanka ta ba. Ta ce "Anti Zahrah ta zo jiya?" Hawaye ya cika idanunta ganin ya kasa cewa komai, zai gumi dake tsastsafo masa ta goshinsa jijiyoyin kansa sun ta shi. Ya ajjiye mug ɗin hannunta bayan ya gama shan tea ɗin tare da miƙewa tsaye, ta miƙe da sauri ta ce "Abba baka da lafiya?" Sai a lokacin sauke numfashi yana jin kansa kamar zai rabe yana ɗan yin gaba ya ce. "Ki kula,ba wasa" ranta bai mata daɗi ba, shi kansa ya kasa riƙe sauyin nasa gudun kada wani ya ankare baya son kuma Ummul ta san halin da ake ciki... Ta fita tana jin kamar kada taje makarantar. Har ta yini a makaranta cir bata da wata walwala haka kurum ta tsinci kanta cikin sukuni, Abir tai ƙoƙari sosai wajan fahimtar da ita duk subjects ɗin da sukai attending. Har suka taɓa hira sai lokacin ma Halisa ta saki jikinta jin Abir itama asalinta ƴar Nigeria ce. Yau ma Umar-khan ya dawo da ita ya lura da sauyin nata bai kulata ba, tunda ba huruminsa bane yin magana da matar malam ɗin. Tana shigowa gidan bata nufi part ɗin Ummul ɗin ba, ta nufi Main parlour zata shige part ɗin ta Zahrah ta ce. "Yawwa ke nake jira dama, ki shirya zamu asibiti" Halisa ta kalleta tana mmkin waye babu lfy kuma? Sai kuma gabanta ya faɗi ko dai Abbanta ne bashi da lfy, ta rikice rikicewar da Zahrah taso ta ɗaure mata kai ta ce. "Bana son shirme mene haka kuma? Kije kafin mu tafi ki gyara mini ɗaki kizo ki ɗan danna mini ƙafata" Halisa ta tsurawa cikin Zahrah idanu har bata ji abin da Zahran ta faɗa ba, tayi saurin jan riga ta rufe cikin da ya ƙara girma fiye da ko yaushe. Ta juya tare da shigewa part ɗin nata, duk ta gigice tana shiga kuma ta fara duba maganin da El-bashir ya bata, ƙila shi ne maganin da Abban nata yake sha bata sani ba. "Kayi haƙuri Abba, laifi na ne" ta faɗa a sanyaye idanunta na cika da hawaye. Zahrah ta miƙe tare da shigewa ɓangarenta, kai tsaye wayarta ta ɗauka tare da kiran number Deen, kamar wanda yake jiran kiran nata yai picking call ɗin ta ce "Akwai matsala Deen" ta cikin wayar ya ce. "Yanzu muka fara samun matsala idan har ba zaki abin da ya dace ba, yanzu mene?" Ta ce "Cikin nan girma yake, yau ƴar fillon nan ta gani amma kamar bata gane ba, kasan kamar shirme ya yi mata yawa, shi ya sa na zaɓi nayi aikin nan da ita" Deen dake zaune idanunsa sauke akan wata Balarabiyya dake ɗakinsa ya ce. "Kada ki damu da wannan ƴar fillon na yanke shawarar abin da za mu yi mata, kawai ki tabbatar Yaa Sheikh ya samu kusanci da Halisa, ki daure ko a tea ne ki zuba maganin feeling ɗin, yana da ƙarfi sosai" Zahrah ta sauke numfashi ta ce "Amma kada a raunata ƴar mutane, nice daidai da Yaa Sheikh mai zai hana ni naje gareja bana tunanin zai gane bani da budurci" Deen yaja tsaki sosai ya ce "Kina da matsala Zahrah,ki fito kice bana gamsar dake mijinki kike buƙata tunda naga alamar ba sanya a wannan ɓangaren ba, listing to me Zahrah nasan waye Yaa Sheikh, nasan shi sanin da zaki mamaki, duk yadda kike tunanin basirarsa ya shige nan, duk abin da zai same shi yana ji a jikinsa, ki tura yarinyar kawai babu damu da duk irin abin da zai mata ba" ɓoyayyan numfashi ta sauke tare da shafa cikinta wanda ya fara motsawa alamar yana cikin ƙosashiyar lafiya ta ce "Deen what's your plan?" Ya ce "ban gane ba? Ina tare dake muke tsara plan ɗin? Are you doubting me?" Ta kasa cewa komai sai kashe wayar da tayi. Ta shiga zirga-zirga a bedroom ɗin duk ranar da Yaa Sheikh ya kusanci Halisa maybe ita kuma zuciyarta ta buga, a ƴan kwanakin nan wata sabuwar Soyayyar Yaa Sheikh ta wanzu a zuciyarta, duk da bai bata wata dama ta Kasancewa dashi ba, amma kullum da soyayyar shi take kwana a rai. A hankali Halisa ke tafiya cikin wasu kayan shan iska sbd sanyin garin ya lafa, ta sauke numfashi ganin Zahrah bata parlour kai tsaye ta nufi part ɗin Yaa Sheikh, ta shiga bakinta ɗauke da sallama Umar-khan dake yiwa Yaa Sheikh bayani ya ɗago kansa tare da kallon Halisa, da sauri ya ɗauke kai ganin kayan dake jikinta, Yaa Sheikh dake jingine jikin kujera sanye da Jallabiya sabuwa kamar ko yaushe ya miƙe tsaye tare da amsar ducoment ɗin da Umar ke basa, Umar ya ce "Ban gama yi maka bayani ba" Yaa Sheikh shiru da Umar ganin haka yasa Umar miƙewa yana ɗauke idanunsa daga kan Halisa, Ta ce "Umar-khan teacher ya ce gobe ka same shi a officer" ganin kamar bai jita ba yasa ta sake cewa "Umar-khan, Umar-khan" ta faɗa tana ƙoƙarin bin bayansa cak taji anyi sama da ita tare da nufar bedroom da ita.....Ya direta gabansa yana binta da gajiyayyun Idanunsa masu kaifi, ya shiga ƙarewa kayan jikinta kallo can dai ya juya zuwa wani ƙaramin bedroom dake jikin wanda suke ciki, ya dawo hannunsa riƙe da hawaya bai ce mata komai ba, sai hannunta daya kama zuwa bakin gado ya nemi waje ya zauna tare da zaunar da ita a gefensa. "Kina son Allah ya kama ki ne matar malam?" Ta marairaice tana narke fuska ta ce "Abba me na yi? Kuma wai baka da lfy naji Anti ta ce wai na shirya zamu asibiti" ya dubeta da kyau tare da kawar da batun Antin ya ce. "Baki san me ki kai ba? Ki nutsu ƴar fillo" ta tura baki zata ta shi ya tsare ta da idanu sosai kafin ya yi magana wayarsa ta fara ringing ganin sunan Abba Hakimi yasa Yaa Sheikh ya danna wayar a handsfree. "Malam, ina ajjiyata ne?" Halisa tai murmushi jin muryar Abba Hakimi, kafin Yaa Sheikh ya ce wani abu ta ce "Jon wuro" Abba Hakimi ya saki murmushi ta waya ya ce "To matar ni dai ban iya yaran nan ba, dama dai Abban naki ne" ta juya tare da kallon Yaa Sheikh taga idanunsa a rufe amma kamar mai jin zafi duk zufa ta gama rufe masa fuska sai gemunsa yake shafawa. "Jon wuro Abba ya iya fillatanci ne?" Abba Hakimi ya ce "Eh sosai, fiye da ke ɗin, baki taɓa ji ya yi bane?" Ta ce "Jon wuro ai baya nunawa yaji me nace ko da fulde nai magana, to Bafullatani ne Abban nawa?" Abba Hakimi ya ce "Matar baga ki kusa dashi ba? Ki tambaye shi, ni dai nasan duk wani motsi na Fulani a idanunsa yake" tai murmushi kawai har lokacin kallon Yaa Sheikh take shi kuma yaƙi yarda ya buɗe idanu, amma yana jin idanunta na yawo a jikinsa. Abba Hakimi da yaji shiru ya ce "Abban naki yana kula dake? kuma yana kusa yanzu" da sauri ta ce "Ai shi ya ɗauke....." Tattausan hannunsa da taji a bakinta yasa tayi saurin zaro ido suna haɗa idanu ya ware mata ido yana ya mutsa fuska gaba ɗaya yanayinsa ya sauya jin tunan asirin da take shirin yi masa. Ya miƙe baki ɗaya yana daidaita zamansa ya zagaya hannunsa ɗaya ɓangaren nata. "Shhhh" ya ce yana tare da yi mata alamar tai shiru. Abba Hakimi ya saki murmushi daga wayar kafin ya ce "Da alama kinyi nisan kiwo, ki bawa Abban naki" ta sauke numfashi bayan Yaa Sheikh ya zare hannunsa daga bakinta cikin ƙasa da murya ta ce. "Jon wuro Abba ya ce nai shiru kada nace ya ɗauke ni" tamkar Yaa Sheikh ya ce ya shiga uku haka yaji shi kam tayaya zai fara nuna mata illar surutun nan? Abba Hakimi ya yi kamar bai ji ba ya ce. "Me kika ce, ntwrk na rawa" Yaa Sheikh ya zare wayar tare da kashe handsfree ɗin a hankali ya manna wayar a kunnansa ya ce. "Abba" ya faɗa tamkar baya son maganar. "Aliyu" Abba Hakimi ya kira sunan cike da girmama kamar yadda yawancin lokaci yake ambatar sunan kai tsaye. Yaa Sheikh ya ce "Uhm". "Ina fatan baka mance deal namu ba, ka watsa mini ƙasa a idanu, kai tsaye na nuna buƙatar ka zauna da yarinyar nan, amma ka ce baka sonta? acikin shekara munci sati ko sama da haka, kamar yau Ubangiji zai nuna mini cikar shekarar. Wallahi Aliyu naga saɓanin yadda muka ajjiye yarjejeniyar zaka san bani da kirki zaka san waye Ostman-zannur" Yaa Sheikh ya juya tare da kallon ƴar rainon da ake kafa masa sharuɗa akanta cikin lafazi mai kyau ya ce. "Abba zan dawo da ita" "Alfarmar riƙon nata ne ba zaka iya ba?" Yaa Sheikh ya ɗan ya mutsa fuska kaɗan ya ce "Ramadan zai zo Abba, ba lokaci ba zan iya ba" sautin murmushin Abba Hakimi ya ratsa kunnan Yaa Sheikh ya ce "Kai kaɗai ne a gidan? da wasa ka bari Matarka taci zalin Halisa wallahi sai nayi maganinku duk" kafin Yaa Sheikh ya sake cewa komai Halisa ta miƙe tare da zama kan ƙafafuwansa tare da zagaya hannunta ta riƙesa da kyau ta ce. "Ina son ka Abbana, kuma...." Ƙitt Yaa Sheikh ya kashe wayar baki ɗaya yana rufe idanu tare da dafe kansa da hannu. Tuni Abba Hakimi yaji abin da Halisa ta faɗa kafin Yaa Sheikh ya kashe wayar. Halisa ita bata ɗauka wani abu tai ba ta ce "Abbana, ni ma kace kana so na" ya sanya hannu ya share zufar dake binsa kafin ya buɗe ido ya kalleta a hankali ya ɗagata da kyau ya zaunar da ita saman cinyarsa ya kifa fuskarsa daidai nata numfashinsa na sauka a hankali saman nata ya jima yana sauke Afra kafin ya ce. "Me... Me.. me..." Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! In-ina ta dawo sabuwa a lokacin da bai zato ba, kuma daman tuni tuni jikinsa ya bashi hakan zai iya faruwa. Ta zuba masa idanu ganin yadda yake ɗan karkatar da kai yana damƙe hannunsa. "Abba kayi haƙuri ban sakewa ka yafe mini" ya girgiza idanunsa sukai jajir cikin son nuna mata kuskuren kaifin bakinta ya tallafo haɓarta sai kuma ya saka ya riƙe hannuwanta da kyau ya ƙanƙame, yana buga ƙafa duk don maganarsa tazo amma abu ya gagara. Ta zuba masa idanunta wanda ya cika da ƙwalla sosai tsoron da tausayin Abban nata ya ɗarsu a zuciyarta. A hankali ya zame hannunsa zuwa rigarta ya riƙe gaban rigar da kyau yana cukurkuɗata ba tare da sanin cewa gaba ɗaya rigar ya tattare ba, ya jawota kusa da shi sosai ba tare daya haɗe jininsu ba, wasu hawaye suka kwanta a idanunsa na zallar asabar fitar maganar. Tamkar wanda zai shaƙeta haka ya rirriƙe gaban rigarta ƙwayar idanunsa kwance cikin nata, cikin Muryar In-inar ya buga ya ce. "Ma...mama.... Mata ma matar maaa ma malam...." Ya faɗa yana buga ƙafa Halisa ta saki kuka bana shaƙar da ya yi mata, na tausayin Abban nata na, da yanayin da taga ya shiga ta ɗauka duk rashin lafiyar ce. A hankali ya saketa tayi sauri ta zame jikinta tare da shigewa cikin jikinta ta rungomesa cikin kuka ta ce. "Abbana" ya dubeta kana ya ɗauke yana shafa kanta a nutse. Ganin kuka take da gaske ya ƙara tallafo fuskarta tare da kama hannunta ya ɗora a ƙirjinsa, wani irin bugawa sosai taji saitin zuciyar shi nayi kamar zata tsago ƙirjin shi ta fito. "Shhhhh" kalmar ta ƙwace masa yana mai lumshe idanunsa tare da buɗewa ya zareta a jikinsa ta ƙwace ta koma tana ƙara riƙesa. "Abbana ka barni" ta faɗa a tsorace shi kifa kansa kawai ya yi a wuyanta sbd tsananin yanayin dake hura wutar abin da yake ji, ya jiƙe sharkaf da gumi. Ya goga hancinsa a wuyanta tayi saurin kallonsa ta ce "Modibbo" ma'ana Malam ko malami, ya cireta a jikinsa yana miƙewa tsaye itama ta miƙe da sauri wata Jotter ya ɗauka da pen ya shiga yin rubutu cikin good handwriting. Yana jin hakan da ya yi shi ne mafita, idan akwai divorced tsakanin su dole Abba Hakimi ya daina tunanin wani ba. Bayan ya gama rubutun ya naɗe tare da sakawa cikin envelope. "Abbana mene wannan" ya dubeta tare da tsugunawa daidai da ita a hankali ya ɗaga ta ya ɗora saman ƙafarsa ɗaya a taushashe ba tare da rauni ko yanayinsa ya sauya ba. Cikin sakin harshe saɓanin ɗazo ya ce "Matsayinki ne a nan Matar Malam, ki yafe mini kinji?" Bata gane ba dan haka tai murmushi ta ce "Abba nima ka yafe mini naji tsoro" ya shafa kanta kana yaja ƙaramin sirrin hancin ya ce. "Ga Malaminki ba tsoro, kina ji ni ba mijinki bane zanci gaba da riƙeƙi matsayin ƴa" ya ɗan yi shiru yana sauke numfashi ya ce. "Ba zaki gane karatun ba yanzu, ki riƙe wannan a wajanki zuwa shekara guda, yanzu ke ƙawata ce ki cire miji a bakin ki" tai murmushi bata fahimta amma haka kurum jikinta ya yi sanyi, duk wata mace da aka saka dole ta samu wannan raunin. Ya miƙe yana cewa "Muje muyi darasi" Zahrah ce gaban likita tana jin abin da yake faɗa ta ce "Da zan baki shawara ku bar cikin jikinki yana cikin ƙoshin lafiya sosai" Zahrah ta kalli Deen dake kusa da ita ta ce "Dr akwai matsala ne, ko nawa ne zan iya baka, ayi duk yadda za ai cikin nan ya kwanta zuwa wasu watanni" Dr ya ce "Ki fahimta wannan ganganci ne" Deen ya gyara zama fuskarsa da face mars ya ce "Daga miliyan 5 zuwa sama ka faɗi abin da kake so, ka yi mata scanning da sai nuna cuta ce a cikinta harta kumbura, za ai mata aiki zuwa watanni huɗu ko biyar" likitan ya yi murmushi ya ce "Wannan ba damuwa bane, ka bada kuɗin duk sanda kuka shirya sai kuzo" Deen ya ce "Your Account number, zan kiraka idan zata zo, ya zama sirri bana lamuntar ha'inci da cin amana, zan iya ɓatar da mutum" Zahrah ta ce "Dr macan da bata fara al'ada ba, zata iya ɗaukan ciki?" Ya girgiza mata kai ya ce. "Al'ada Ita ce hanyar dake nuna cewa mace ta shirya amsar namiji, kuma zata iya amsar dukkan wasu ƙwayaye da zai zuba mata, sai dai bisa tsari ƙwan ɗaya ke nasarar samu shiga cikin wani gurbi na mahaifa, idan ƙwan namiji guda biyu ya samu damar shiga cikin mahaifar mace lokaci guda, shi ne ake iya samun twins, twins ɗin da suke a mahaifa guda sune ake kira da identical twins, masu tsananin kama da juna, wanda suka zo a mahaifa daban daban suna iya kama amma ba can ba, mahaifa na buɗewa ne lokacin da mace ta fara al'ada magana ya gaskiya babu yadda za ai mace ta samu ciki ba tare data fara al'ada ba, wannan shi ne" Zahrah ta sauke nauyin jin daɗi kana ta miƙe daga nan Hotel ta nufa, tana murna plan ɗinta zai cika cikin ƙaramin lokaci. Daman dai fargaba kada ace Halisa ta samu ciki a mu'amalar da zatai da mijinta, amma yanzu ta samu nutsuwar zuciya. Washegari bayan Halisa ta tafi makarantar Yaa Sheikh na gida sbd baƙin da zai masu ɗaukan tafsir da ake sakawa a Channel. Ummul ta kallesa ta ce. "Ka tafka babban kuskure Aliyu, mene amfanin abin da kayi? Idan zaka rabu da ita mene yasa ka aureta tun farko?" Kansa a ƙasa domin yana martaba Ummul ƙwarai da gaske. Ya kalleta yana miƙewa tsaye ya ce "Ƙaddara Ummul, ƙila ba rabon zama Inuwa ɗaya, mganar ya tsaya iya mu" Ummul ta goge hawayen idanunta ta ce "Malam kada ka manta kai da kanka ka zaɓa mata suna Halisa, kai ne kayi mata huɗu ba, kai me ka reneta meye duk wannan wanne irin abu ne? Zaka yanke hukunci ba shawara" ya juya kawai ba tare da ya ce komai ba, sbd kansa dake juyawa sosai. A haka ya nufi Part ɗinsa. Yau da murna Halisa ta dawo sbd yaba mata da Ayyan ya yi harda gift ya bata bayan ya ce tana da kyau. Wanka tayi tai sallah ya shirya cikin wasu english wears masu kyau. Bata nufi wajan Ummul ba, kai tsaye wajan Abban nata ta nufa lokaci yana kwance akan bed ya yi rigingine. "Abba, Abbana" ta hango shi can bed kallon da ya yi mata yasa ta juya tare da dawowa ta ce "Assalamu alaika" ya amsa a ransa. Ta matsa kan gadon tare da hayewa saman gadon, kai tsaye ta yi wa kanta masauki a bayansa, ta zauna a bayan ta ce "Abba yau nayi ƙoƙari sosai, Teacher Ayyan ya ce ina da kyau kuma yana so na" ya mirgina tare da dawo da ita saman cikinsa ya riƙe hannunta ya ce "Uhm" ta shafa fuskarsa tana wasa da gemunsa ta ce. "Amma Abbana nake so shi ne mijina" ya ƙurawa bakin indo yadda take juyawa babu sassauta zan can. A hankali ya mirginata, ta koma ƙasan bed ɗin, shi kuma ya yi mata rumfa. "Abba" ta faɗa tana kallon idanunsa tamkar ba na Abbanta ba. Ya kame bakin surutun a hannunsa ya ce. "Kina buƙatar darasi Matar Malam" ya shinshina wuyanta sak irin turaren daya siyawa su Maimoon da mother. Ta ce "Abba ai na san darasin" ya buɗe ido ya ce "Za dai ki sani" kamar yadda ya yi mata haka itama ta riƙe bakinsa, ya rufe ido yana janye jiki tare da jan duvet ya rufe jikinsa baki ɗaya har kansa, gaba ɗaya jikinsa rawa da karkarwa yake kamar mazari. Ta miƙe a rikice tana faɗin "Abba, Modibbona, Abba" da sauri ta fita wajan Ummul ta amsa black tea kana tayi ɗakinta maganin wajan El-bashir ta buɗe tana zubawa a tea ɗin, ta juya shayin da sauri ta nufi bedroom ɗin, har lokacin yana kwance ta ce "Abba ga shayi kasha kaji" yai mata banza har zata janye duvet ɗin sai kuma ta tsaya a fili ta ce "Bari muji ko babu ɗaci shayin" ta ɗauki cup ɗin shayin tare da kaiwa bakin, tai karɓa ɗaya biyu har zuwa uku samun kanta tayi da shanye shayin baki ɗaya.....Zuciyar Yaa Sheikh tai kyakkyawan bugawa a duk lokacin da ya shiga wannan yanayin yasan akwai mummunan abun da zai faru da rayuwar shi. Ya akan iya gani a mafarki ko jikinsa ya shaida masa hakan ta hanyar sauyawa. Ya zame duvet ɗin jikinsa a hankali ya mirgina zuwa gefen ya rufe ido yana sauke numfashi bakinsa ɗauke da addu'a. A hankali ya sakkowa daga kan bed ɗin zai shige bathroom idanunsa ya sauka a kanta tare da cup ɗin shayi. Kansa ya sara a nutse ya nufeta tare da durƙusawa daidai inda yake, yanayinta ya nuna sam ba lafiya ta kifa kanta a gefen gadon ta kifa kamar zata faɗi. A taushashe ya ce. "Kee!" Shiru bata amsa ba abu ne mai wahala Halisa ta nutsu haka dole akwai wani abu. Ya riƙe numfashi ya ce "Ƴan matan Abba" nan ma shiru ya ɗora hannunsa tare da girgizata gaba ɗaya tayi baya zata faɗi ƙasa ya yi saurin taro ta zuwa cinyarsa. Wani irin zafi yaji fatar jikinta ɗauka sosai tsoro ya kama Yaa Sheikh amma ya riƙe kansa ya riƙota tare da bubbuga kumatunta ya ce "Ƴar fillo, ƴar fillo!" Ta buɗe idanu da ƙyar yana kallon fuskarsa amma ta kasa cewa komai sai hawaye dake fita daga gefen idanunta yana gangaruwa fuskarta. Yaa Sheikh ya juya idanunsa ya sauka akan cup ɗin shayin ya ɗauka da sauri ya jima yana kallon cup ɗin. Da sauri ya ajjiye ya riƙota gabaɗaya ya ce. "Ina ki ka samu wannan? Waye baki?" Gaba ɗaya ya nemi rasa nutsuwata duk yadda yasu ya kame kansa daga shiga firgice ya kasa. Ya jawota sosai muryata na rawa ta ce "Abbana" ya shafa kanta ya ce "Yes, Amanata. Me ya sa? Zaki kassara rayuwarki akai na?" Ta riƙe hannunsa jikinta na rawa na tsananin azabar da take ji, domin ji take kamar ana hura mata wuta a naman jikinta idanunta ya kasa tsayawa sai lumshewa take tana buɗewa ta ƙara riƙe sa ta ce. "Kashe mini kai za ayi Abbana? Me ya sa? Me kayi don Allah kada a kashe mini kai" wani irin hawaye na zubuwa daga idanunta. "Amanata why? Guba ki ka sha tayaya Abbanki zai jure?" Ta girgiza kai ta ce "Na san maganin mutuwa ne Abba, amma ni babu abin da zai mini, Abba ka ɗaukeni jikina bafii ciwo Abbana" ta saki numfasa, sanyi kawai take buƙatar ji zafin jikinta ya tsananta azaba da raɗaɗi kawai take ji, ta gwammace taji azabar da ace Abban nata yaji, ba zai iya ɗauka ba. "Nothing... Nothing will happen Amanata" ta ƙara buɗe idanunta daya fara sanyawa ta ce "Modibbona" "Na'am ta Malam?" Ta kallesa da kyau ta ce "Modibbo bafii ina jin ciwo" tausayinta ya kama shi a zahiri ya yi mugun rikicewa, amma dake ya iya riƙe kansa fiye da kima ya girgiza kai kawa tare da ɗaukanta zuwa kan bed ɗin da ya kwantar. Telephone line ɗinsa ya ɗauka ya kira wata number, babu jimawa akan ɗauka. A nutse ya yi bayani wanda aka kira ya ce. "Blood poison ne, wanda yake ƙona jinin mutum cikin ƙaramin lokacin, am on my way" Yaa Sheikh ya yi shiru tunani kala-kala a ransa yana ƙara maimaita kalmar _“Blood poison?”_ waye? Daga ina? Akan wanne dalili?. Dr ɗin ya ce "Ka bata taimakon gaggawa kafin nazo, zaka iya yin body connection da ita sbd ta samu zafin jikinta ya ragu a jikinta, ma'ana dai sanyin jikinka ya shiga nata, zafin jakinta ya shiga naka....," Yaa Sheikh bai tsaya jiran jin abin da Dr ɗin zai ƙarasa faɗa ba ya ajjiye wayar tare da nufar bathroom, gaba ɗaya ya zare sutturar jikinsa ya rage daga shi sai farar singlet da trouser a karo na farko wani zaiga jikinsa kuma waninma ƴar rainonsa. Ya sakarwa kansa shower da ruwa mai mugun sanyi, bai taɓa wanka da ruwan sanyi ba sai warm water amma yau shi ne tsaye shower na dokan tsakiyar kansa, sai daya jiƙe sosai sai ko'ina na jikinsa ɗiga yake kafin ya fito daga bathroom ɗin. Direct bed ɗin ya nufa tana kwance ba zaka taɓa ɗauka tana da rai ba, sbd ita kaɗai ta san abin da take jin bakinta wani irin ɗaci ya yi idanunta ya fara yin fari sosai, da hanzari ya hau kan gadon yana ɗaukanta tare da zaunar da ita saman cinyarsa, ta buɗe ido tare da zuba masa su alamar "Me zakai Abba?". Ya saka hannu ya shiga ɓalle gaban rigar ta, ita dai kallonsa kawai take ya zame rigar tare da yin cilli da ita ya rage daga ita sai farar vest da White Padded bra sai under wear. Ya saka hannu zai zare vest ɗin yaji ta riƙe hannun, yana ɗago kai suka haɗa ido, ta rufe ido ta buɗe kai tsaye ya fahimci me take nufi. Ya ɗora hannunsa akan ta yana shafa sumar kanta a taushashe ya ce. "Abbanki ne amanata, ki nutsu" lokacin daya zare vest ɗin ta rufe idanu a hankali ya kwanta, tare da ɗorata saman shi, wata iriyar ajjiyar zuciya ta sauke mai nauyi tana ɗana zabura sbd sanyin daya ratsa fatar jikinta, wani irin daɗi ya kamata zafi da raɗaɗin na raguwa, Yaa Sheikh ya rufe ido tasbihi kawai yake a ran shi. A hankali zafin jikin Halisa ke shigewa nasa, sai da jikinsa ya ɗauki zafi sosai ya zameta a hankali tare da miƙewa ya koma bathroom ya ƙara sakarwa kansa shower ɗin. A wannan karan ƙanƙame shi tayi sosai sbd samun sassaucin da take kallo ɗaya zakai mata kasan ta jigata. Yaa Sheikh addu'a yake yana tofa mata hannunsa zagaye da bayanta ki sau ɗaya bai tsaya ya sauke idanunsa akanta ba. Ringing ɗin telephone da yaji yasa ya kwantar da ita yana miƙewa tsaye ya san Dr ne. Ya zura jallabiya da hirami tare da nufar ƙofar part ɗinsa ta baya yana zuwa ya samu Dr da Umar-khan. Yaa Sheikh ya kalli Umar-khan gane abin da yake nufi yasa kai tsaye ya nufi sashin Ummul. Yaa Sheikh ya juya zuwa ciki Dr ya biyo bayansa, cikin sauri ya shiga buɗe dukkan wasu abun gwaje-gwaje da zai tabbatar da zargin da Yaa Sheikh yake. Gwajin farko ya nuna guba bace mai ƙarfin gaske ba wacce zata kashe mutum lokaci guda ba, a hankali zata dinga ƙona jinin mutum har ya ƙare cikin watanni biyu ko uku ya mutu. Ya kalleta yaga kamar barci ya ɗauketa sbd yadda numfashinta ke sauka, Dr zaiwa Halisa allura ya ɗaura mata drip tare da saka mata wani abu acikin baki, Yaa Sheikh ya yi gyaran murya ya ce. "Kada a manta am a doctor, zaka iya tafiya" Dr ya ce. "Allah ya ƙara sauƙi da afuwa" fitar Dr ya yi daidai da shigowar Ummul a rikice ta ce. "Poison a gidan nan? Kuma wajan Halisa Aliyu? A ina aka samu guba?" Ya sauke numfashi a ɓoye yana ɗauke kansa, da kansa ya saka mata drip tare da yi mata Injection. "Kaga abin da nake faɗa? ba za a barka ba Malam Wannan shirun naka bashi da amfani, nasan kasan masu nufinka da haka, abin tambaya ya akai Halisa ta samu guba?" Ya zauna saman kujera ya jima kafin ya ce. "Maganar ta tsaya iya mu Ummul, a nemi abin cewa" ta ce "Shikenan amma na fara gajiya ba zan iya zuba idanu mu rasaka ba, kalli halin da yarinyar nan ta shiga" Sai a lokacin Umar-khan ya ce "Abin tambaya ne ina ta samu poison?" Yaa Sheikh ya miƙe tsam yana buƙatar hutu da nutsuwar Zuciya ko zai samu ya yi cikakken tunani mai kyau. "Zan huta, ina buƙatar kyakkyawan lokaci Ummul, a nemi wacce tayi shayin nan" yana faɗin haka ya shige ɗakin dage gefen bedroom ɗin.... Basu da wani zaɓi wanda ya shige fita. Ummul ta nufi kitchen gaba ɗaya ta kira ma'aikatan ta ce "Waya haɗa shayin Yaa Sheikh?" Duk sukai shiru domin sun san babu wanda ya kewa Yaa Sheikh abincin bayan Ummul. Suhaima ta ce "Ummul ina tunanin ke kika haɗa fa? Ko kin manta ne?" Ummul ta ce "Ko ɗaya dole an sauya" Bara'at da tun ɗazo ba tai magana ba taja duguwar ajjiyar zuciya ta ce "Wanni abin ne?" "A'a. Daman ya ce ya masa yadda yake so, an zuba suger ya yi yawa, wanda ya ɓata ɗanɗanon. Kuma saƙon daɗin yaje har ƙwaƙwalwar shi, wacce aka bawa kwangilar tana buƙatar a bata tukucin kai goran albishir" Ummul ta juya rai ɓace, gabaɗaya suka bi bayanta da kallo tare tunanin ko dai wani abun ya faru ne?. Tunda Ummul ta shiga ɓangarenta ta rasa yadda zatai da ranta, ko dai iyayen Yaa Sheikh zata kira ta faɗa musu abin da yake faruwa su sani? Kada a wayi gari da gawar Yaa Sheikh ya zatai?. Ta nemi waje ta zauna tare da faɗin. "Ubangiji kamar yadda ka bawa Yaa tsayin shekarun daya ɗauka yana kula da Halisa tun tana ciki, har kawo haihuwar ta, Ubangiji ka ƙara masa wasu shekarun da zai tabbatar da mauradinsa ta zama cikakkiyar mata a garesa, Ya Allah Ya Rahmanu ka nufi Yaa Sheikh da mayar da wannan taɓargazar da ya yi, Yadda take ƴar raino a garesa Allah kasa ta zama mata a gare shi har abada" Ta goge hawayen daya sakko mata, tana son komawa taji yadda jikin nata yake amma tasan taga Yaa Sheikh tasan riƙe kansa yake amma baya jin daɗi, ko zazzaɓin Halisa baya jurewa yanzu zai zo yana cewa. "Ummul ƴar fillona" balle yanzu data sha poison ason kare rayuwar Abban nata. A daddafe Yaa Sheikh ya gabatar da Sallar Issha a masallacin da yake ɗaukan su jam'i. Bai tsaya yi musu karatu ba, ya dawo gidan ma'aikatan dake kula da dukkan wasu abubuwa daka waje ya shiga bi da idanu gabaɗaya suka sha jinin jikinsu wannan shi ne karo na farko daya kallesu har haka. Zahrah na ganin shigowar Yaa Sheikh ta miƙe da sauri tare da rungomesa ta ce. "My Excellency yau duk ban ganka ba, sai yaushe zamu kasance tare?" Ya zareta daga jikinsa ta ce. "Na fara gajiya, matarka ce ni amma kana nunawa sam baka damu dani ba, ina da hakki a kanka kasan ni macace mai rai wacce jini ke gudana a jikinta kuma....," Kaifin idanunsa daya sauka cikin nata ya hanata ƙarasa maganar duk rashin kunyarta bata isa taiwa Yaa Sheikh. "Me kike so? uhm kada ki damu shekaru biyu ne kawai na baki" maganar ta tsaya mata a zuciya, wato kada ta damu ko dan tai masa rashin kunya?! Ta tsiri kukan ƙarya idanunta rufe ta ƙara rungomesa ta ce. "Ina buƙatar My Excellency, ina son kasancewa da mijina" Yai mata shiru ta riƙesa sosai ta shiga yi masa wani abu, amma ko gizau bai ba, al'amarin daya bawa Zahrah matuƙar mmki kenan. Sumbatar shi zatai daidai lokacin kuma ɗan dake cikin cikinta ya yi wani kyakkyawan juyawa tare da harba ƙafa wanda ya a sanya taji mararta ta ɗaure tana da tabbacin Yaa Sheikh yaji juyawar ɗan dake cikin nata.. Ya ɗauke kai tare da shigewa abinsa. A ruɗe Zahrah ta nufi bedroom ɗinta tana kiran number Surry gaba ɗaya ta fara rasa mafita tashin hankali ya bayyana akan fuskarta. Tun daga bakin ƙofa Yaa Sheikh ya fara jiyo numfashinta tana kwance jikinta zai rawa yake kumfa na fita daga cikin bakinta, tuni ta fisge drip ɗin hannunta. Ya ƙarasa da sauri yana zama kan bed ɗin tare da ɗagota, ko magana ya kasa jinta jikin mutum yasa ta ƙanƙame Yaa Sheikh tana ɓoye kanta kwantar da ita ya yi tare da kama hannunta ya shiga murzawa da sauri da sauri, ya daɗe yana murza hannunta kafin ta ja numfashi ta sauke jikinta ya saki sai hawaye dake bin fuskarta. Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya shi ma sauke yana janye drip ɗin ta buɗe ido tana kallon Yaa Sheikh ta ce. "Modibbo zan mutu kai ni Dadata" duk yadda yasu kame kansa da riƙe yanayin kasawa ya yi, ya jawota jikinsa tare da yi mata masauki da kyakkyawan ƙirjinsa ya rufeta ruf ya yi mata rungumar da rabon da ya yi mata tun tana shekara biyar a duniya. Ta sauke numfashi tai luff a jikinsa ƙamshin Roja na ratsa zuciyarta a hankali ta ce. "Abbana" ya dubeta bai ce komai ta ce "Abbana me ya sa zasu kashe mini kai? Su waye mai kayi musu zan basu haƙuri ni su kashe ni kaji?" Ya ɗora hannunsa a bakin nata "Shhhhh" ya ce yana ƙara matseta a jikinsa. "Modibbo, Abbana kada ka mutu kaji?" Idanunsa da suka gama juyawa ya buɗe tare da kwanto da ita saman hannayensa ya kifa kansa a fuskarta suka kalli juna muryarsa bata bita sosai ya ce.. "Rayuwa, mutuwa na hannun lillahi wahidul ƙahhar, ban son hawayen" A hankali Halisa ta fara tunanin vedion data gani a wayar Anti Zahrah komai ya dawo cikin tunaninta ita kanta Zahrah bata san Halisa taga wannan vedion ba. Yaa Sheikh yana ƙoƙarin zame fuskarsa daga kan ta Halisa kamar a mafarki, kamar gilmar tunani cikin ƙwaƙwalwar mutum haka yaji saukar bakinta cikin nasa..... Paid book It's 500 08119237616"Ya subuhanallah, wa...wa wa'auzubillah" sune kalmomin da suka samu fita daga cikin bakin Yaa Sheikh wanda suka kasance iya zuwa. Ya riƙe kanta da kyau yana ƙara ware idanunsa akan ta, mmkin ya cika shi yaushe matar malam ƴar amanar shi tasan duk wannan? ya ɗauke numfashi yana ƙoƙarin sauya yanayin yaji ta ƙara riƙe bakinsa da kyau idanunta rufe, al'amarin da bai taɓa ji ba shi yake neman bijiro masa. Ilahirin jiyoyin kansa sun fito tare da yin kwance a saman goshinsa. Ya zare bakinsa da ƙyar ba dan ta daina abin da take ba, Halisa ta marairaice fuska idanunta na cikowa da hawaye ta ce "Abbana" ya goga fuskarsa a wuyanta yana tura dukkan hannunsa cikin sumar kanta ta sauke numfashi tana bin fuskar shi da kallo tare da kama gemunsa tana ja.. Cikin wata kalar raunatacciyyar murya wacce shi kaɗai yasan ma'anar ta ya ce _"Ta fuɗɗu ko a wawata famtugo nder majuum"_ karo na farko da taji fillatanci a bakinsa wanda ya zauna raɗau kai kace harshen shi ne na Iyaye. Ta ce "Abba zan iya gane darasin da gaske" "Uhm" ya ce kawai dan bakinsa ya yi nauyi sosai, yarinyar ta shayar da shi mmki. "Sallah zaki" ta ce "Abba ba zan iya tashi ba, kuma zanyi fitsari" ya miƙe da ita tsaye tare da nufar bathroom. Suna zuwa ya sauketa tare da ƙoƙarin juyawa tayi saurin maƙale kafaɗa ta ce. "Ka tsayani, tsoro ina" ya kalleta sai kawai ya tsaya tare da juyawa mata baya. Bayan ta kammala ya yi mata alwala da kansa a taushashe ya ce. "Walk" bata gane zaran zancan nasa ba da hannu ya nuna mata ƙofa ta shagwaɓe fuska sosai kamar yadda take masa a shekarun baya amma duk ta mance. "Ni ka ɗaukeni ba zan iya tafiya ba" ya girgiza kai tare da sunkuya ya ɗauketa ta saƙalo wuyansa. A jingine a jikinsa a haka ta gabatar da Sallar duk yana kallon ta, saura kaɗan gabar ya kassara mata jiki gabaɗaya bata da kuzari duk babu kazar kazar ɗin. ganin tana lumshe idanu ya ce "Gajiya? Jikin? Yunwa?" Ya faɗa a taƙaice ta girgiza kai ta ce. "Abba Dadata yaushe zan ganta? Ni goyani take idan bani da lafiya" ya ware manyan idanunsa yana hango zallar rigima dake kwance a nata idanun. "Abba ka goyani" ya dubeta a dole sai ta saka ya magantu ya ce. "Ki rufa mini asiri, goyo tun shekarun baya baki mance ba?" ta saki kuka da gaske domin ita har zuciyarta take son a goyatan ƴar rigima ce, idan abin ya motsa bata ji bata gani. Ta saka kuka sosai ya ɗauketa gabaɗaya tare da jijjigata ya ce "Kina son rikitani Amanata, ki tauyasawa Abbanki" ta maƙale kafaɗa daidai kunnanta ya shiga yin wasu baitotoci na waƙar larabci na addini. Tai shiru tana tunani kamar tasan waƙar, Yaa Sheikh yasan dole ta haka zai shawo kan rigimar ta ce "Abba kai ma ka iya?" Ya zauna bakin gado yana ɗorata akan cinyarsa ya ɗan kalli time yaga goma ta kusa. "Kin taɓa ji ne?" Ta ɗaga masa kai ta ce "Kamar dai" tai shiru alamar tunani da sauri ta ce "Abba na tuna, wani na manta sunan mai rufe fuska shi ne yake yi mini a Rugar Rome" ya ɗauke kai yana mai sassauta fuska kamar wanda murmushi zai ƙwacewa. Ya gyara mata zama tare da zagaye bayanta ya ɗora kansa a wuyanta tattausan gemunsa na gogar fatar wuyanta ya ce. "Duba can?" Ya nuna mata direction da hannu idanunta ya sauka akan wani photo a prame photon baby girl ne zata iya yin 10 mnts da haihuwa, idanunta rufe sumar kanta har gaban goshi. Anyi wani rubutu kala biyu ɗaya da hausa ɗaya da turanci. _“Angel my world”_ shi ne abin da aka rubuta da turanci da larabci kuma aka saka _“Ƴar Aljanna Mrs Aliyu haydar Aliyu”_ yanayin yadda aka tsara photon zaka san cewa ana matuƙar ji da shi, ta juya ta ce "Abba wace?" Ya shafa kanta da hannunsa har lokacin fuskarsa na kifa a wuyanta yana murza mata sajansa mai laushi ya ce. "Zaɓin Allah, matar ƙwarai, hasken zuciya" nan da nan yanayinta ya sauya ta ce "Abba nifa? Da gaske baka so na?" Ya ware bakinsa kamar zai magana sai kuma ya fasa Halisa tau saurin sauke numfashi jin tongue ɗinsa a skin na wuyanta yana yawo. "Baka so na Abba?" Ya buɗe ido tare da ɗagowa baki ɗaya. "Kina so a soki ne?" Ta ɗaga masa kai ya numfasa tare da kwantar da ita yana sauke mata numfashi ya ce. "Ban son ina kwana, every morning come and Peck my cheeks, left and right, shi ne gaisuwar" ta ɗaga masa kai. Duk sukai shiru can ya miƙe ya bisa da idanu. Kai tsaye sashin Ummul ya nufa Ummul na ganinsa ta miƙe tsaye ita kanta kwarjinin Yaa Sheikh rikita ta yake haibarsa da kamala har sun yi yawa. "Ya jikin nata? da sauƙi dai? ta faɗa maka wanda ya bata gubar" Ya juya yana yin wace ya ce. "Allhmd. Ba buƙata" daga nan ya nufi Library ɗinsa, yaci gaba da rubutun Alkur'anin da yake da ka, wanda yake son ya zama cikakken kafin zuwan Ramadan da shi zai amfani wajan yin tafsir. 1:00 ya tashi bayan ya tabbatar komai lafiya yake, ya watsa ruwa tare da yin alwala. Sallah ya gabatar sosai ya zauna zaman azkar sai 2:30 ya shirya cikin fararen kayan barci ya fesa turare ya nufi duguwar kujera tare da duvet ya kwanta, daga ina yanke ya hangota sai barci take numfashi na sauka a hankali gabaɗaya ta kwaɓe fuska. "Rigimammiyata" ya furta a fili yana rufe idanu. Cikin dare sanyin zazzaɓi ya takura mata da wani irin ciwon kai sosai kuma duk yana cikin matsalar da gubar ya haddasa mata, ta yayar bargon da take ciki kai tsaye idanunta ya sauka akan Abban nata ta nufi kujerar tare da hayewa saman shi ta zagaye hannuwanta ta riƙesa sosai kanta a ƙirji nan take barci ya sake ɗauketa. Ba barci yake ba yana jinta kuma dama ya san dole zata ta shi yaja bargon ya rufesu tas sai a lokacin barci ya ɗauke shi. Duk yadda ya makara a kwanciya hakan bai hana shi tashi tun kiran sallar farko ba. Ya buɗe bakinsa ɗauke da addu'a a hankali ya yunƙura zai tashi yaji an ƙanƙamesa, ya kai idanunsa zuwa jikinsa ya sauke numfashi tare da komawa ya kwanta gaba ɗaya ya manta a jikinsa ta kwana, gently ya miƙe da ita yana ji tana riƙesa tsoran kada ta faɗi a haka ya kwantar da ita saman bed tare da rufeta da duvet yana matsawa ta mirgina tare da cire duvet ɗin a haka taci gaba da barcin. Cikakken wanka ya yi tare da ɗaura alwala ya shirya cikin embrodiery Islamic jallabiya jikinsa sai fidda ƙamshin Nivea Men Active Clean Shower Gel, ƙafarsa sanye cikin Scuff faux-shearling slippers ya nufi fita daga gidan zuwa Masjid sai baza ƙamshi Roja yake. Sai da ya gabatar da raka'atul fjr kana yaja jam'i cikin daddaɗar muryarsa cikin makarijul huruf da fidda hakƙin tajwid yake karatun. Ana idarwa ya fara gabatar da karatu wanda ya kasance da mutane da yawa, ya ɗago kai tare da kallon mutanan kana ya bayar zuwa ga littafin dake gabansa a taushashe ya ce. _“ Babin da yake bayani akan tilasta mace zuwa ga shimfiɗa bada yarda ta ba, a turance kuma Sexual violence”_ ya gyara zama sosai gaba ɗaya larabawan wajan sukai shiru suna sauraran abin da zai ce. A hankali ya ce. 7:00 ya shigo gidan bayan ya biya ta wajan tsuntsayensa, daman yasan ba zai samu kowa a main parlour ba. Kai tsaye part ɗinsa ya nufa da mmki yake dubanta tana kwance saman prayer kar sai gyangyaɗi take. Ya nufeta bai ce komai ba taji an ɗagata sama tayi saurin buɗe idanu suka kalli juna sai kawai tai murmushi mai kyau tana kwantar da kanta. Bayan ya sauketa saman bed ya ce. "Sanyi sai kama ki, a daina kwanciya ƙasa" ta ɗaga masa kai tare da faɗin "To Abba makaranta fa?" Ya tsare ta da idanu kafin yai magana wayar shi ta gida ta fara ringing ya miƙe tsaye a hankali ya manna wayar a kunnansa. Umar-khan dake kan layi ya ce. "Barka da safiya Yaa Lee, ya mai jiki? Ummul na neman iso na shigowa sashin naka" "Uhm" ya ce yana ajjiye wayar. Babu jimawa Ummul ta shigo hannunta ɗauke da babban tray. "Barka da safiya, ya jikin nata?" Yana zama kan kujera tare da naɗe ƙafarsa ya ce. "Mun tashi lafiya?" Ta ce "Allahamdulillah, Ya jikin ƴar Abba" Halisa tana daga kwancan ta ce "Naji sauƙi Ummul, tambayi Abba kiji shi ne ya ɗaukeni yanzu kuma a jikinsa na kwana" kamar ƙasa ta tsage ta shiga haka Ummul taji kunyar Yaa Sheikh ta kamata Halisa ta ƙara cewa. "Ummul Abbana ɗan gayo ne ba kiji bakinsa ba..." "Ya isa haka, yau naga takai ne ni Ummul" Halisa ta juya za taiwa Yaa Sheikh magana amma ko inuwarsa babu a bedroom da alama ya daɗe ta ficewa tun da yaji abin kunyar da take neman haɗa shi da ita. Ummul sam batai wani mmki ba, ita juriya da haƙurin Yaa Sheikh kawai take gani. "Ƴar Abba ba komai ake faɗa ba, shi aure sirri ne, duk abin ya faru ki barshi a ranki, kinji?" Ta ɗaga mata ta ce "maza sha tea kinji?" Ta maƙale kafaɗa ta ce "Modibbona zai ban kije kawai Ummul, kuma me ya sa ki ka daina cewa matar malam?" Ummul ta ce. "Because he's no longer your husband" tana faɗin haka ta fita. Ita kuma Halisa sam bata gane ba. Tana fita Yaa Sheikh ya fito daga bathroom suna haɗa ido da Halisa ya watsa mata harara ita dry ya bata ma. Zahrah na tsaye ta kafe Ummul da idanu tana tirketa da manyan tambayoyi. "Ina ƴar aikina take, ya zama last question da zan miki" Ummul ta ce. "Bata jin daɗi, a part ɗina ta kwana" Zahrah tai shiru sai kuma ta ce "Muje akwai aikin da za tayi mini yanzu?" Ummul ta ce "Bata lafiya fa?" A fusace Zahrah ta ce "And so what? Ke rashin lafiyarta ya dama" Ummul ta ɗauke ta ce. "To Umar-khan ya tafi kai ta asibiti" yaja tsaki tare da juyawa ta ce "Bari naje wajan Yaa Sheikh ɗin naji wanda ya bada lasisin yiwa ƴar fillo abu ba tare da izinina ba" Ummul tai bedroom ɗinta da sauri ta kira Umar-khan ta ce. "Ka kira Yaa Sheikh yanzu ga matarsa Zahrah nan zuwa, kasan Halisa na wajansa" tana faɗin hakan ta kashe kiran. Kiran telephone line ya tsayar da Zahrah daga tafiya part ɗin Yaa Sheikh, ta ɗaga kiran tare da cewa "Hello" Jadda dake bisa layi ta ce "Waye ne za a fasa mini kunne kamar yaƙi?" Zahrah taja tsaki a ranta ta ce "Matar Aliyu mana?" Jadda ta zabga Salati ta ce "Yaushe Gadanga ya yi aure kuma?" Zahrah ranta ya ɓaci ta ce "matarsa Zahrah" Jadda ta ce "Uban meye kuma Zahra? A to Allah ya isa ban yafe ba maganar da nayi dake, maza maza mutum nake nema bake ba don Allah, kije kiji da Iyaye abu a kwance kamar tawul ɗin wankan mai jego" wani kyakkyawan tsaki Zahrah ta ja. Tamkar Jadda ta fasa wayar haka tayi ta ce "Uwarki ki kaiwa tsaki, ai sai yanzu na tabbatar Gadanga bai aure mace ba, mai siffa irin ta fir'auna da ƙaruna, baki kamar maliya tayi ambaliya" kashe wayar Zahrah tayi baki ɗaya tsanar mata ya ƙara zama daram a zuciyarta. Ko sallama ba tayi ba a haka ta shiga part ɗin Yaa Sheikh, a tsaye ta gansa ya baza Alkyabba sai ƙamshi yake zabgawa wani irin kyau ya yi mata wanda bata taɓa ganinsa ba, ya ƙara girma da faɗi. Ta sauya tafiya tana kaɗa jiki cike da kissa ta nufesa tana zuwa ta ce. "My Excellency, you look good kayi kyau sosai" ta rungumesa ta ce "I love you husband" ya buɗe ido yasan daman babu gaisuwa a tsarinta. "Yaushe zaka bani damar zuwa sashinka na tayaka barci? Na fara gajiya kawaici na ya ƙare ina buƙatar mijina" sai a lokacin ya kalleta sosai a hankali ya ce "Sanda ki ka shirya" zata sumbaci bakinsa taji kamar wani abu yana yi mata yawo a jiki ta ɗan motsa ta ce "Uhm daman nace a daina fita da ƴar aikina ba tare dana sani ba, kuma idan da hali ta kwashe kayan zuwa sashen masu aikin gidan nan" ta zabura sbd abin da yake ƙara bin jikinta gudun kada ta bata kanta a gaban Yaa Sheikh tayi saurin cewa "I'll be back" ya lumshe idanun tare da buɗewa tai saurin ficewa. Wani irin fisgar numfashi ya yi jin yadda ta riƙesa sosai ta baya, gaba ɗaya ta jiƙa masa bayan riga ta bakinta. Ya saka tattausan hannunsa tare da fito da ita waje daga cikin Alkyabbar jikinsa. Ya dubeta ya kalli hannunta brush ne wanda ta wanke baki ta tura baki ta ce. "Ji nayi tana cewa zata kwana dakai fa Abba shi ya sa" wato ita ta kuri Zahrah?. Ya juya zuwa bedroom har lokacin jikinta baƙwari sosai suna zuwa taga ya jawo Injection yana zuƙar ruwa gabanta ya faɗi sosai. "Allah sarki Abbana waye babu lafiya kuma?" Da ace dry halinsa ne babu abin da zai hana shi yi ya juya ya ce. "Ƴar fillo" ta haɗiye yawo ta ce "A'a wallahi lafiya nake,don girman Allah Abba kada kayi mini don soyayyarka da Annabi wlh banso" ganin ta gaske yi mata zai ta kwasa zata gudu ya damƙota tare da zama da ita akan cinyarsa ya ce. "Shhhhh, ina gaisuwata?" Ya faɗa yana ajjiye allurar gefe ɗaya. Ta sauke numfashi ta ce "Naji tsoro ashe bani za aiwa ba" ya dai bita da idanu a hankali ta saƙalo wuyansa tare da ɗora bakinsa a kumatunsa, ta sakar masa kiss ya saka hannunsa a bayanta tare da yin ƙasa da trousers ɗin jikinta, idanunsa cikin nata a haka ya ɗauki Injection. Halisa tai murmushi tana ƙara yi masa kiss a kumatu shi kuma ya saita Injection ɗin a jikinta. A hankali ta dawo bakinsa sai kuma ta fasa ta ɗaga idanu tare da kallon Yaa Sheikh ta ce "Abbana ina son ka" a karo na farko ya sakar mata murmushi wanda yasa ta zuba masa idanu kamar bata taɓa ganinsa ba, ya sumbaci goshinta ya ce. "I na... Ina.." tai dry ta ce "Yawwa Modibbona ni ma kace kana so na" ya ɗora tsinin allurar sosai a jikinta ya ce "Ina.. ina son" bai ƙarasa ba ta ce "Ina son k....," wani ihu ta fasa daidai lokacin daya tsira mata tana ƙoƙarin sakin kuka ya kame bakin kukan da nasa bakin ya rungometa sosai a jikinsa... Paid book 500 08119237616 Allah ya nuna mana Monday ai weekend lfy🥱*_A jiya da France sunci ƙwallo tabbas da littafin IDAN BA KE free book zai dawo. Wannan yaron Mbappe ajin tsoran gabansa, ko yanzu ya jijjiga zuciyar Messi. Wlh ban taɓa zaton Argentina zasu ɗauki cup ba👉🏾🏆.Mufa har gobe CR7 shine real GOAT kuma kowa yabi idan Ma ba kabi ba anbima eheeennnn...dama tun farkon wasan Saudi Arabia dA Argentina muka gano FIFA Messi suke so yaci world cup, then lokacin dA muka bata na kallan world cup ɗin nan bamu yafeba wuta bal bal😏_* Haɗiye kukan nata tayi, Yaa Sheikh yabi duk wata hanya da yasan zata iya yi masa rigima ya toshe ta. Tai shiru tana sauraran sabon lesson ɗinsa gently ta buɗe ido kai tsaye suka haɗa idanu ya zame fuskarsa baki ɗaya still holding onto her "Abba kayi mini wayo" ya girgiza kai hannunsa cikin sumar kanta yana shafawa ta ƙara tura baki ta ce "Munyi faɗa, Allah sai na faɗawa Ummul kuma fa Allurar bafii wayyo Dadata" sai a lokacin ya dubeta murya bata fita sosai ya ce "Zaki samu zunufi, a daina kiran faɗa" ta kwaɓe fuska ta ce "Abba bakai bane? nace banso banso kayi mini" ya riƙe fuskarta yana gyara mata zama a cinyarsa ya ce. "Idan baki so me kike so?" Ta riƙe dugun gemun shi tana ya motsawa idan ta kitsa sai ta ware ko ta murmuɗe, duk da zafin da yake ji amma bai kulata ba ta ce "Modibbona nake so, Abba ka siya mini nagge kaji?" Ya buɗe ido sosai ta langwaɓe kai tana shafa lips ɗin shi ta ce "Don Allah Modibbona, an ƙwace mana Naggenmu wanda Baffa ya bar mana, wai ana bin Baffa kuɗi shi ne Sarkin ruga ya ƙwace, kuma ma ai kayi mini al'ƙawari ko?" Shi dai bakin maganar yake kallo yana mmkin yadda bata gajiya da surutu, banda ya riga ya tsara yadda karatun ta zai kasance a zuciyarsa da bbu abin da zai hana ya juya akalar karatun zuwa Mass communication. "Ni ka siya mini nagge irin na Rugar Rome kaji Abba" ya riƙe hannunta daga kan gemunsa idanunsa cikin nata ya ce.. "surutun ya ƙaro fiye da baya, ki sassauta mini" ta ce "To kace zaka siya mini mana" ya juya kai tare da ɗaukan cup ɗin shayin da Ummul ta kawo ya kai bakinsa zaƙi da garɗin zumar dake ciki ya ratsa cikin kunnensa sai da ya gama shanye na bakinsa ya ce. "Kada ki damu, Abbanki nada garken nagge masu yawa" tai murmushi ta ce "Abba ina suke zaka kai ni na gansu?" Ya numfasa ya ce "Je Rugar Bello ki tambaya, ban son surutu karatu za ai ok?" Ta ce "To Abba" domin ta lura da sauyin fuskarsa ya kame ta sosai babu wasa, ya lura tsaf zata sanya ya faɗi abin da bashi kenan ba, tana son ya yi ta surutu kamar yadda bakinta bai gajiya. Miƙewa ya yi ta biyo bayansa a hankali sai da yaje bakin ƙofa ya tsaya tare da juya yaga ta sunkuyar da kai ƙasa taƙi kallonsa. Ya ɗauke nasa kan tayi saurin cewa "Abbana cikina ciwo" cak ya tsaya kana ya janyo ta zuwa gabansa a taushashe ya ce "ba nace ba surutu ba?" Ta ce "To gasky a ɗinke bakin kawai Abba, wlh ban san ina yi ba" bata san mene ya samu Yaa Sheikh ba sai gani tayi a durƙosa dai tsayinta tare da rungometa a jikinsa yana shafa bayanta wani irin kyakkyawar murmushi mai tsananin kyau da tsari ya suɓuce masa, wanda kuma ya rungometa ne sbd baya son taga murmushin nasa. "Kada ki damu, zan ɗinke shi kamar yadda ake ɗinke ƙwarya" ta ƙanƙame shi ta ce "Abbana zai rufe mini baki" ya cirota daga jikinsa yanayin kallon da yake mata yasa ta nutsu sosai a hankali ya ɗora bakinsa a goshinta ya sauke mata wata kyakkyawan sumbata forehead kiss ma'anar shi, shi ne _“I Care About You”_ a daidai kunnanta ya ƙara ɗora bakinsa cikin Jamila muryarsa ya shiga karantu wasu adduo'i yana tofa mata a cikin kunnen tai shiru tana jinsa sai ajjiyar zuciya da take saukewa. _"Allah ya yi miki Albarka, Ubangiji ya kare ki daga sharrin mutum, Allah ya shirya mini ke"_ ya faɗa yana miƙewa tsaye tai murmushi tana riƙe hannunsa ta ce "Ina son ka Abbana" bai kulata ba ya fice abinsa tana biye da shi. A main parlour yaci karo da Umar-khan na shigowa ganin Yaa Sheikh yasa Umar-khan durƙosawa ya ce "Barka da safiya Sheikh" ya jinjina kai. "My Excellency ka fito?" Suka ji saukar maganar nan da nan annurin fuskarta Halisa ya ɗauke ta tsaya kawai tana kallon fuskar Abban nata. Zahrah ta ƙarasu tana cewa "Yanzu nace bari nazo na faɗa maka bana jin daɗi ne, ko zaka iya kai ni asibiti" Ba tai tunanin zai magana ba amma sai taji ya ce "kuje da Umar-khan" ta ce "Kamarya Umar-khan? Da mijina nake son zuwa bada wani ba, matsayina ya shige kana haɗani da masu aikin ka" Umar-khan ya nemi waje ya zauna idanunsa akan Halisa wacce tai tsaye jikinta na rawa kamar an buga gangar biki.. Ummul ma data shigo ta lura da yanayin na Halisa. "Babu lokaci" Zahrah ta ce "to kayi dropping nawa a hospital ɗin daman Dr na son ganinka ai, hold on meya faru da gemunka" Umar-khan ya saki murmushi domin tuntuni yaga kitson da gemun na Yaa Sheikh yasha. Ummul wata kunya ta kamata ganin yadda gabaɗaya aka kitse gemun na Yaa Sheikh tasan babu mai aikata haka sai oganniyya Halisa.. Yaa Sheikh bai gane ba amma jikinsa ya bashi wani abun ne, duba da yadda Ummul taƙi kallonsa a hankali ya kai hannu ya shafi gemun nasa. Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Ya furta a ransa da sauri irin saurin da bai san yana da shi ba ya juya zuwa part ɗinsa babu wanda yake jin kunya sama da Ummul. Dry ta ƙwacewa Umar-khan ya ce "Ummul ya mai jiki?" Ta girgiza tana faɗin "Da alama yau akwai daro duba ka gani?" Ya juya zuwa inda Halisa take har yanzu tana tsaye idanunta ya kakkafe. Zahrah couldn't understand what's happening ta ƙarasa wajan Halisa ta ce "muje kiyi mini tsifa" Halisa tai shiru Zahrah ta daka mata tsawa ta ce "sufa daman yaran matsiyata masu iya neman waje ba, na kusa rabuwa da masifa na huta zaki shige ko sai nayi ƙwallo dake" daga Umar-khan har Ummul suka zuba idanu. Zahrah ta kai hannu zata daki Halisa taji an riƙe hannunta cikin kakkausar murya ta ce "kada ki dakemu, ki fita sabgarmu za mu yi bankaɗar da kike ɓoyewa" Zahrah ta kalli hannun Halisa daya riƙe nata, har lokacin kan Halisa a ƙasa yake cikin ɓacin rai Zahrah ta kifawa Halisa mari, wani irin ihu Halisa ta fasa wanda kai tsaye ya sauka har kunnan Yaa Sheikh dake sauya kaya. Gaba ɗaya tai kan Zahrah kamar mahaukaciya duk girman Zahrah sai da Halisa ta kai ta ƙasa tare da hayewa kan cikinta ta dinga dukanta da ƙarfi cikin ɓacin rai. Naushin da akaiwa Zahrah a ciki yasa ta fasa ihu tana neman taimako tare da kiran sunan Yaa Sheikh. Al'amarin ya yi wa Ummul daɗi Umar-khan kam gyara zama ya yi ya ce "wannan faɗan yafi ƙarfin sa" Yaa Sheikh ya jima da fitowa amma yaƙi ƙara sawa, sosai Halisa ta birkice tana ihu tana dukan Zahrah ta yaƙoshi "Please My Excellency zata kashe ni ka taimaka mini wallahi mahaukaciya ce, ba ƙarfin ta bane" wata dry ta ƙwacewa Umar-khan ya kifa kai a armchair ya dinga dry yana buga ƙafa. A hankali cikin nutsuwa Yaa Sheikh ya ƙarasu tare da saka hannu ya ɗauke Halisa daga kan Zahrah, nan fa ta shiga kokawa daga hannunsa zata ƙwace ya riƙeta sosai yana faɗin. "Meye haka? Ni za aiwa ƙaddama?" Ta girgiza masa kai sai kawai ta faɗa jikinsa tare da ƙanƙame shi tana sakin wani irin kuka jikinta duk rawa yake, gashi kanta harya fashe idanunta ya juye tausayinta ya kama shi. Gabaɗaya ya manta da wata Ummul a wajan bare kuma wani Umar-khan ya riƙeta sosai a jikinsa. Zahrah ta dafe cikinta ta ce "My Excellency kalli zata kasheni amma ita kake taimakawa?" Umar-khan ya ce "Haba matar Yaa Sheikh ba kiga ita kamar ba yin kanta bane, taimako kika nema gashi nan kuma ya ɗauketa, ai Malam shi ne taimakon dani da Ummul babu mai iya tunkarar Aljanu" kasa miƙewa Zahrah tayi wani irin nishi take kamar mai naƙuda mararta na riƙewa ta ce. "Wallahi dole ta koma gidan ubanta ta tafi can Rugar su" Umar-khan ya ce "Ruga kuma? Ba ƴar uwarki bace meye haɗinta da Ruga?" Zahrah ta ce "Ruɗewa nayi, gida zan mayar da ita" Yaa Sheikh dai ya ɗauke ƴar amanar shi ya nufi Library room da ita. Umar-khan ya miƙe daman yazo akan batun zakkar da Yaa Sheikh ɗin zai raba sbd zuwan Ramadan. Ummul ma ta nufi kitchen ranta fes. A daddafe Zahrah taja jiki zuwa part ɗinta tana shiga jini ya ɓalle mata a rikice ta kira number Deen yana ɗagawa ta fashe da kuka ta ce. "Na shiga uku Deen kamar haihuwa zanyi ko bakwaini?" Ta cikin wayar ya ce "Haihuwa kuma?" Tai masa bayanin komai. "How many times zan ce ki daina shiga sabgar yarinyar nan? Kina son rusa mana plan nan ko?" Nishi Zahrah take sosai jini na fita a jikinta ta ce "ba wannan ne matsalar ba, yarinyar kamar tana da Aljanu kuma tana iƙirarin zata tona mini asiri, ga yadda Yaa Sheikh yake nuna kulawa gareta ya fara bani tsoro ina son mijina" Deen ya buga mata tsawa ya ce "Ni ki ke faɗawa kina son mijinki? Me kike nufi?" Ta ce "ina nufin abin da nace mana Deen, wallahi ina son Aliyu ba zan iya rabuwa da shi ba, duk abin da ka ke nema zan maka amma banda rabuwa da Yaa Sheikh" Deen ya furzar da Iska yama rasa me zai ce. "Kisan yadda zaki ki fito yanzu na kai ki asibiti idan ki ka haihu a gidan ko ki kai ɓari ba ruwana" yana faɗin haka ya kashe wayar, a daddafe Zahrah ta shirya bayan ta saka pads da tsumma bata tsaya jiran komai ba ta nufi wajan bisa umarnin na Deen ɗin, Address ɗin daya bata tafi ta samu motar shi a gefe guda tana zuwa ta zube a ƙasa, Deen ya ɗauketa zuwa mota suka nufi asibiti.. _2hours Left_ Deen ne zaune a gaban a gaban Dr ya ce "kana nufin kace cikin dake jikin Zahrah ya zube?" Dr ya ce "haka ne, duk yadda muka so dakatar da cikin mun kasa, sai dai hqr" Deen ya dafe kai gaba ɗaya plan ɗinsa ya ruguje ya ce "Amma Dr kwanaki munyi ƙoƙarin cikin ya zube, wani Dr ya ce ba zai taɓa zubewa ba" Dr ya gyara zama ya ce "Anya? Sai dai idan baya so ya zubar da cikin, amma cikin ƙaramin lokaci za a iya zubar da cikin" Deen ya yi shiru idan haka ne akwai wanda yake son yaga Zahrah ta sha wahala ko ya tuna mata asiri. "OK Thank you" yana fita ya ƙarasa ɗakin da Zahrah take, ita kanta Zahrah ta rasa me zatai farin ciki ko ɓacin ciki? Kuka ko dry?. Sai dare aka sallameta Deen ya kawota har ƙofar gida ta lallaɓa ta shiga. A hankali yake tafiya yana tattare Alkyabbar jikinsa dawowarsa kenan daga sallar Issha kai tsaye kuma part ɗinsa ya nufa, kwana biyu yana stressed kansa sosai, yana buƙatar yaje Nigeria kafin zuwa Ramadan shi ya sa yake ƙara takura kansa. Yana shiga bedroom yaji ta rungomesa ta baya ta ce "Abbana sannu kaji" ya jawota gabansa idanunsa akan bakinta ya ce "Sallah?" Ta ce "Nayi Abba, Darasi zaka bani" yana da ayyuka amma dole ya ware lokaci ga karatun ta. Akan table ya zauna itama ya nuna mata waje ta zauna, littafin Fiqhu ya buɗe ya ce. "Nutsu sosai, abu mai muhimmanci ne" ta miƙe tsaye tare da dawowa wajansa ta zauna saman cinyarsa ta ce. "Abba zanfi ganewa haka" ya ɗauke idanu ya lura kwana biyu taiwa jikinsa kyakkyawan sabo, hannunsa ya zura ta ƙasan nata hannun ya ɗora kansa a wuyanta a hankali ya sauke numfashi cikin nutsuwa ya ce. _“Babin dake bayani akan abubuwan da suke ja ayi wanka”_ zata juya ta kalle shi ya sakar mata nauyin kansa ya jima a haka kafin ya ce. "Abubuwan dake jawo wankan Janaba, wanka ɗaya ne, amma ya kasu kashi kashi, ko wanne kuma akwai dalilin dake sawa ayi, idan nace Janaba ina nufin najasa" ya yi shiru yana lura da Yadda ta nutsu tana bin duk inda ya nuna da hannu da idanu. A hankali ya ɗora da cewa. "Fitar maniyyi a cikin bacci, ko a farke, daga namiji ko mace, ta hanyar lafiya da jin daɗi, saboda hadisin da ya ce, “Idan ruwa ya fita a yi wanka.” Wato idan ruwan maniyyi ya fita, a yi wankan janaba" ya ƙara yin shiru na wani lokaci kafin ya ce. "Idan mutum ya yi mafarki yana saduwa da mace, amma da ya farka babu alamar fitar maniyyi, babu wanka a kansa. Idan mutum ya yi mafarki yana saduwa da mace, bayan ya farka sai ya ga maniyyi a jikinsa, wajibi ya yi wanka. A nan ana nufin ko da kayi mafarki kayi mu'amala mace kuma baka fitar da komai ba, to wanka bai hau kan mutum ba, idan kuma akasin hakanne dole ai wanka" ya saurara da maganar ya ce. "Kin gane?" Ta girgiza kai ta ce "Wallahi Abba ji kawai nake ni wannan karatun bana ganewa, sai abu ɗaya naji kana faɗa wai Mani..." Ya jima yana kallonta yama rasa ta ina zai ɓullo mata ya numfasa kaɗan ya ce. "Bakin ce ke matata mace? To idan nayi mu'amala dake ake nufi mu'amala ta aure" ta tuntsire da dry ta ce "Ina ji ci-gaba" ya murmusa a ɓoye ya ɗora da cewa. "Idan mutum ya tashi daga barci sai ya ga maniyyi a jikinsa, amma bai yi mafarkin saduwa ba, wajibi ya yi wanka, saboda samuwar maniyyi a tare da shi, wanda fitarsa ne yake jawo wanka" tayi saurin kallonsa ya ware mata idanu sosai ta ce. "Abba to kai ma ka gani dana kwana tare da kai" tambayar ta Girgiza tunaninsa bai tunanin cewa tana ganewa ba, sai kawai yai mata shiru ta juya gaba ɗaya suka fuskanci juna ta ce. "To gsky misali zaka bani idan ba haka ba, ni bana gane karatun naka Malam" a taushashe ya ce "ban gani ba" ta ce "To sbd me? Kai mafarkinne ba kayi ko me?" Ya numfasa sosai tare da ajjiye littafin ya riƙe fuskarta a hankali ya ɗora tashi fuskar saman tata, ya kama hannunta ya ɗora saman gemunsa suka kalli juna a hankali kuma ya sauke idanunsa akan ƙaramin bakinta ya ce. "Sbd da kwaila na kwana... Paid book 500 08119237616"Mene kwaila?" Ya yi shiru zata sake magana Yaa Sheikh ya sanya hannu tare danne bakin a hankali ya ce "Shhhhh shiru" dole tai shiru badai ta rasa abin faɗa ba. Yaci gaba dayin karatun cikin salo da nutsuwa yadda zata fahimci komai ta kuma gane abin da yake magana akai. Ya lura kuma tana ganewa duba da yadda tayi shiru, bayan sun kammala Halisa ta kalli Yaa Sheikh dake murza hannunta ta ce "Yaa Sheikh ya zan gane wankan janaba ya hau kai na?" Da hannu ya nuna ta kawo kunnanta tayi saurin miƙa masa kunnen ya ɗora bakinsa ya faɗa mata magana tayi saurin kallonsa tana zare ido ya ɗaga mata gira ya rungometa sosai a jikinsa a taushashe ya ce "Zaki Albarka, tare da zuri'ar ki" Halisa ta kalle shi ta ce "Yaa Sheikh" Yaƙi magana ta ce "Yaa Sheikh mun gama darasin?" Ya ɗaga mata kai tare da cewa "Sai wanda zaki ban" tai murmushi tana son ganin idanunsa amma yaƙi yarda ta gani sbd juyewar da sukai "Yaa Sheikh me ya sa ake son kashe ka? Kuma ina gani kana kuka cikin barcina kana cewa na taimaka maka ni kuma inaƙi" Ya dubeta yana nazartar maganganun nata kafin ya ce "Kina son sanin sirrin Abbanki?" Ta ɗaga masa kai alamar eh ya riƙe fuskarta yana ɗora tasa kai ya ce. "Mafarki ƙarya ne, wani lokacin gsky ke kam naki ba daidai ba ne" buɗe baki tai zatai magana ya sakar mata wani hot kisses a lips ɗinta idanunta cikin nasa al'amarin ya girmi tunaninta ji take tamkar ba Yaa Sheikh ɗinta ba, wani irin sahihin abu yake mata ta kasa jure al'amarin hawaye ya shiga gangaro mata ganin ƙirjinta na ɗagawa tana riƙe hannunsa sosai ya yi saurin sakinta tayi luu zata koma baya ya yi saurin dawo da ita zuwa jikinsa.. El-bashir ne tsaye a gaban motarsa idanunsa sanye cikin Sunglass ya zuba hannun a cikin aljihu, farar t.shirt ce a jikinsa sai wandon uniform na ƴan sanda. Ya daɗe tsaye a inda yake kafin wani saurayi ya ƙarasu wajan yana sarawa El-bashir ya ce "Mun gama dukkan wani binciken da muke a Company amma babu wata hujja dake nuna an zuba haramtattun kaya a kamfanin sarrafa shinkafa na Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" El-bashir ya jinjina kansa ya ce "Okey, kaci gaba da saka idanunka" Yasir ya ce "Amma sir ga shawara, mai hana kabi ta wata hanyar kai ka zuba hudar iblis cikin kayan nasu, tunda na samu labarin kayan nasu yana gab da shigowa, idan har aka kama kayan kamfanin sarrafa shinkafar dole sai an nemi shugaban kamfanin kaga a nan ka jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, ka kai Yaa Sheikh gidan yari, kuma ka ɓata masa suna tare da lalata kamfanin baki ɗaya" El-bashir yai shiru a hankali kuma ya juya ya shiga mota yana cewa "I'll think about it" El-bashir yana son privacy life shi ya sa bai fiya fita da wasu securities ba, infact ba kowa yasan abin da ke zuciyarsa ba. Burinsa bai shige yaga bayan Yaa Sheikh har ƙarshen rayuwa ba. Direct masarauta ya nufa, yana buɗe ƙofa yaci karo da Khalil wanda ya fito daga ɓangaren Mai martaba. "Am glad you are here, yanzu nake shirin kiranka Mai martaba na son ganinka" El-bashir ya ce "Ok tom" har ya yi gaba Khalil ya ce "hold on, nayi maka magana baka ɗauki abin serious ba ko El?" El-bashir ya jingina da jikin mota yana kaɗa key ya ce "Maganar me kenan Yarima? Na manta fa" Khalil ya ce "Maganar yarinyar da nace kuna kama sosai, kamar ya ɓaci fiye da tunanin mutum shi ya sa abin ya tsaya mini rai" El-bashir ya kalli yayan nasa da kyau yana sakin murmushi ya ce "Na kasa fahimtar me kake nufi Yarima, i don't even have a wife balle nace ita ta haifa mini yarinyar har muke kama, kuma dai nasan kaf cikin masarauta ba wanda ya haihu ɗan ya ɓata right? Infact banga wata kama ba" "Amma mu ai munga kamar ko? Da Fulani Atine za taga yarinyar ina da yaƙinin zata tai tunanin abin da nake tunani" El-bashir yai gaba abin sa ya ce "Ai shikenan, ni wannan kamar bata gabana" Khalid yai murmushi yana ganin gabaɗaya akwai sauyi a rayuwar El-bashir ɗin. Daga nan ɓangaren Mai martaba El-bashir ya nufa, kasancewar baya cikin fada yasa damai bai tunanin zuwa can ba. Yai tsaye har sai da akai masa iso kafin ya shiga ƙawataccen parlourn wanda ya sha ado da kayan sarauta kala-kala. Da mmki El-bashir yake kallon Abba Hakimi yana tunanin mene ya kawo shi garin a wannan lokacin? Ko abin da yake tunani ya faru ne?. Ya nemi waje ya zauna yana faɗin "Barka da hutawa Daddy, Allah ya ƙara girma" Mai martaba Ahmad Sarki ya sauke numfashi kafin ya kalli Autan ɗan nasa ya ce "Mubasshir ka shirya dai?" El-bashir ya ce "Dady ina? Akwai aiki habaka" Mai martaba ya yi shiru na wani lokaci kafin ya ce "Aikin hajji, ina son ziyara tare da miƙawa Ubangiji buƙata tuna, Khalil ya kammala komai jirgi zai ta shi gobe" El-bashir bashi da ra'ayin zuwa aikin hajji wannan shekarar baki ɗaya amma hakan kamar wata dama ce a gare shi. Abba Hakimi daman yasan ba lallai El-bashir ya kulasa ba, kamar yadda baya kula Yaa Sheikh ga mmkinsa sai yaji ya ce. "Barka da hanya Abba Hakimi" Abba Hakimi ya yi murmushi irin nasu na manya kafin ya ce "Allhmd Mubasshir" El-bashir ya ce "Yaa Sheikh lafiya yake dai ko?" Ba Abba Hakimi ba hatta Mai martaba sai da ya kalli El-bashir. "Kaji ance bashi da lafiya ne?" Ya girgiza kai Mai martaba ya ce "A gidan shi zamu sauka kafin fara aikin hajji, naji ance shi ne zai jagorancin sallar Taraweeh da Tahajjud a masallacin ka'abah" El-bashir ya miƙe ba tare daya ƙara cewa komai ba, gabaɗaya suka bi bayan shi da idanu. "Ina tunanin amsar Halisa daga hannun Yaa Sheikh, ba zan iya bari tai shekara guda ba" mmkinsa maganar Abba Hakimi ya kasa ɓoyewa daga kan fuskar Mai martaba sai daya ja numfashi cikin tarin martabawa da bawa Abba Hakimi girman na shi ya ce "Don me ya sa?" Abba Hakimi ya ce "Don ya magantu, ina sanin ina alƙibilar Aliyu take akan aure dama mace baki ɗaya, ka sani na sani Aliyu kaifi ɗaya ne, ba a taɓa sauya masa tunanin dama shi ne a kwakwalwar shi ba. Lokaci yana shigewa shekaru na ƙara girma a tare da Yaa Sheikh, ban san ina tunaninsa yake ba, ban san mene tsarin shi ba, amma a wannan karan ba zan zuba masa idanu ba, ina da yaƙini da kuma tabbacin Yaa Sheikh ba zai saurari Zahrah Farouk ba, ina son saka masa soyayyar Halisa ko ta halin yaya" Mai martaba ya jinjina kai yana mai jin cewa gasky Abba Hakimin ya faɗa. "Hakan yana da kyau" Abba Hakimi ya ce "Da zarar an kammala aikin hajji ka tawo mini da ita, nasan ba zai ce komai ba" tattaunawa sukaci gaba dayi. El-bashir na fita ya nufi sashin Fulani Atine ya sameta ita da tarin kuyanginta bayan sun fita ta kalle shi ta ce "Sarkin gobe na Wannan masarauta ya akai ne?" Ya tura hannunsa cikin sumar kansa tare da fesar da Iska mai zafi sai kawai ya juya kamar wanda mayan ƙarfe ke janshi. "Sannu sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba aje ba. Ko yanzu goma ta faɗi tafi biyar albarka, sahun giwa kuma ya zarce na raƙumi, ƙadangaren bakin tulo ban fito ba sai dana shirya ja muje zuwa El-bashir Ahmad Sarki" Fulani Atine ta faɗa tana sakin wata dariya ita kaɗai. Kafin ta sanya ai mata iso da Jakadiyya. Fulani Balaraba tana ɓangarenta babu mai jin kanta daga ita sai ɗan ta Khalil Ahmad sarki suke mu'amala. Iska mai ƙarfi ce ta mamaye cikin dokar dajin da suke, kafin wani kuka da ihu mara daɗin saurare ya maye gurbin iskar. Wata kururuwa Prince Bilal ya saka bakinsa na fitar da hayaƙi cikin jin daɗi da farin ciki, murya mara daɗin Amo! Ya ce. "Sandu kayi ƙoƙari ban taɓa zaton matata zata kasance a Madina, ka tabbatar ita ce?" Sandu ya ɗaga fikafiki yana shawagi a sama ya ce. "Naga zoben a hannunta, na ganshi ta fito daga makaranta ita ce" Prince Bilal ya ƙara sakin dariya ya ce "Lokacin ya yi da zan nunawa wancan Bil'adama ɗin bai isa ba, bashi da ƙarfin ikon da zai rabani da matata a karo na biyu, idan a lokacin baki da iko yanzu ina da ikon da bai isa yaja dani ba" Sandu ya yi dry sosai har lokacin shawagi yake a sama ya ce "Da tuni na ɗakkota zaren dake hannunta yasa bani da ikon tunkararta" Prince Bilal ya ƙara kwarara ihu wanda ya ƙara hargitsa dajin da suke ciki farin ciki mara misaltuwa yake ji a ran shi ya ce "Zani, zani lallai zani idan har Ramadan ya zo bana da iko ko kaɗan dole naje yanzu" yana faɗin hakan yabi iska ya ɓace. Wajan sati biyu kenan da shan poison ɗin da tayi, taji sauƙi sosai ta koma makaranta, sosai take fahimtar karatun da har malamai take bawa mmki ɓangaren Yaa Sheikh bai saurara wajan bata karatun addini ba, musamman karatun Alkur'ani. Al'amarin da yake bashi mmki duk yawan karatun Alkur'ani da zai mata ba, nan take zata haddace wani lokaci kallonta kawai yake wani lokacin kuma sai ya yi murmushi a ɓoye yana da yaƙini da taimakon wasu a karatun nata. Tun yana mata surah ɗaya ya koma biyu. Zarah ce zaune a gefen bed ɗin ta hannunta riƙe da waya tana lalubar number Surry. Daily ta danna babu ɓata lokaci Surry tai picking call ɗin "Ai ta kiran number ki ba a samu, meke damunki Surry?" Surry ta ce "Nothing ya akai?" Zahrah ta sauke numfashi ta ce "Cikin jikina ya ɓare Surry ki ta yani murna" da ƙarfi ta cikin wayar Surry ta ce "What,ya zube?" Zahrah tai shiru kamar mai nazari sai kuma ta ce "Haka ne, amma ya naga kamar kin firgita" ta ƙirƙiri murmushi ta ce "A'a farin ciki ne ya yi mini yawa, congratulations" Zahrah tai murmushi ta ce "Naje anyi mini ɗinki tas, na dawo kamar budurwa duk da Dr ɗin ƙi ya yi wai sai na bashi rabon shi" Surry tai dry sosai ta ce "kice zamu samu ɗan Dr kenan?" Taja tsaki mara sauti ta ce "Ba wannan ba, nifa na fasa aikin nan da Halisa, da kai na zan tunkari mijina nasan ba zai gane komai ba, tunda na riga nayi ɗinki, yau ɗin nan nake son zuba masa maganin cikin shayi" Surry ta ce "That's great, za a sha amarci kenan?" "Uhm bari kawai ashe yarinyar Aljanu gareta? Itafa tayi sanadiyar zubewar cikin nawa" Surry ta saki murmushi kawai kafin ta ce "To gida zaki dawo da ita?" "Ina tunanin haka, nifa wlh idan naga yarinyar gabana faɗuwa yake sam jini na bai haɗu da ita ba, yanzu ma zuwa zanyi naci ubanta na sakata aiki ba tai ba" kashe wayar tayi tana miƙewa tsaye tana mmkin yadda cikinta yake a kumburem kai tsaye part ɗin Halisa ta nufa a hanya taci karo da Yaa Sheikh tun safe daya fita sai yanzu ya shigo gidan a hakama sai daya gabatar da sallar Issha dan haka a gajiye yake sosai ga ciwon kan dake neman tashi. Murmushi tayi ta ce "Wlcm My Excellency" ta faɗa tana rungome shi ya ɗan jinjina mata kai taƙi sakin sa ta ce "Can i help you naga ka kaji sosai" ya zareta a jikinsa a hankali kamar wanda akaiwa dole ya ce "No thanks" ta ce "Ok bari naje wajan yarinyar can naci ubanta na sata aiki ba tai ba" ta juya ya yi saurin riƙe hannunta da mmki ta kalle shi sai taga ya sassauta fuskar shi.. "Uhm haka ake tarbar miji? I need green tea" she can believe Yaa Sheikh shi ya riƙe mata hannu har ya yi mata mgn cike da kulawa. Ta juya idanu ta ce "Bari na saka ƴar fillo ta kawo maka My Excellency, ni kuma zan shirya amsar mijina yau" ya ɗauke ya jima kafin ya cire hannunsa a nata ya ce "Ba zaki iya ba ke? Ita kullum cikin samun lada take" ta zaro ido ta ce "Wace? ladan me kuma?" Ya kame fuska sosai kamar bashi ya yi maganar ba. "Ok bari na karɓo maka love You My Excellency" ya sumbaci gefen fuskar shi kana ta juya zuwa kitchen a karo na farko. Yaa Sheikh yana shiga part ɗinsa ya nufi ƙofar da kai tsaye zata kaishi har sashin Halisa. A hankali ya murɗa handle ɗin tare da turawa, idanunsa yaja ya rufe sbd ƙamshin daya ratsa hancinsa wanda ya haifar masa da kasala a jikinsa, da ƙyar yaja jikinsa zuwa bedroom ɗin ganin bata parlour yana shiga tana fitowa daga bathroom ɗaure da towel wanda ya tsaya mata iya gwiwa. Ya zubawa babban yatsarta idanu a hankali ya dubi wanda yake kusa dashi, motsawar dugun gemunsa shi ne zai nuna cewa murmushi ya yi. Bai tsaya yi mata cikakken kallo ba sbd abin da hakan zai haifar. Halisa na ganinsu ta zame towel dake kanta tana tsane ruwa gaba ɗaya ta sauya tana zuwa wajansa ta shige jikinsa ta ce "Yaa Sheikh ɗina Modibbona" Ya riƙe kansa da kyau ta ƙara rungome shi ta ce "Modibbona ina ka shiga yau ko gaisheka ban ba" da sauri ya saka hannu a ƙirjinta yana riƙe towel ɗin da kyau wanda yake neman faɗuwa ƙasa "Abba riƙe mini towel ɗin na ɗakko kaya" Yaa Sheikh ya kasa magana Halisa ta fara ƙoƙarin zame towel ɗin shi kuma ya riƙe gam. "Zaki lalata Malam Amanata" ya faɗa daidai kunnanta yana sauke mata numfashi tayi saurin riƙe ƙugun shi sbd gaba bata kai tsayin shi ba. "Yaa..Yaa Sheikh" ya sauke numfashi tattausan gemunsa a wuyanta yana manna mata sai shaƙar ƙamshin shower gel ɗinta. Jikinta ya ɗauki rawa sosai ta ƙara cewa "Abba zan yi fitsari" bai ɗago ba amma ya riƙeta sosai muryarsa bata fita ya ce "Ba fitsari bane, zama jaruma" ta ɗaga masa kai ta ce "To na zama Jaruma Abbana, amma zan rama" Al'amarin ya tsananta har lokacin yaƙi yarda ya saki towel yasan ba zai haifar da ɗa mai ido ba. Ganin duk dariyarta amma ƙirjinta na ɗagawa ta riƙe shi sosai. Ya zame bakinsa daga nata idanunsa cikin nata daya sauya kala ya ɗaure towel ɗin sosai a hankali ya ce. "Sabon Darasi a shafin الحياة الزوجية alhayat alzawjia" Halisa ta ce "To banga littafin darasin ba?" Ya kalli bakinta wanda ya yi jajir kafin ya ce "Ni ne littafin, kece darussan ciki, fahimtar darasin yana ƙarshen littafin" bugun ƙofar da yaji ya sanya ya kama hannunta da sauri ya nufi sashinsa yana fita ya rufe ƙofar. Zahrah ta kaji da bugawa ta buɗe ƙofar bakinta ɗauke da masifa amma babu Halisa a bedroom, idan ba kuskure hancina yaji ba to ƙamshin turaren Yaa Sheikh taji a bedroom ɗin. Sai kuma tai murmushi babu mmki jikinta ke ƙamshin sbd ɗazo data tsaya wajansa. Tana ƙoƙarin juyawa idanunta ya sauka akan envelope fari mai kyau ta nufi wajan tana warware wa, bata fahimci komai a rubutun paper ɗin ba. Sai zanan hutun zuciya data gani, ga kuma zanan idanu yana kuka. Gaba ɗaya rubutun paper ɗin Larabci ne. Tai tsaki tare da ajjiye paper ɗin tana fita. Yaa Sheikh ya saki hannun Halisa yana nufar bathroom idanunsa rufe a hankali ya ce "A saka kaya, kada sanyi ya kamaki" ta ce "To Abba" ya jima a bathroom kafin ya fito cikin bathrobe duk da haka sai da ya rufe jikinsa da towel gudun abin magana da akun tasa. Tsaye ya ganta bayan ta saka wata duguwar riga mai kyau sosai shi kansa ba zai ce ga inda ta ɗakko rigar ba. Ganin Attention ɗinta sam baya kansa da alama akwai abin da take gani ya ƙarasa a hankali da sauri ya kwance prame ɗin ƙaramin hutun dake hannunsu ta kalle shi ta ce "Abba kai da wace a photon" ya ɓoye hutun yana jawota gefensa ya ce. "Mrs Talkative zo muyi sallama" ta ce "Abba wace?" Bai kulata ba ya sumbaci goshinta a hankali ya ce "Ubangiji ya yi miki Albarka Fillo" ya sumbaci kumatunta ya ce "Allah ya kyautata gobenki" ya ƙara sumbatar ɗaya gefen ya ce "Zuri'a mai tarin albarka" a hankali ya ɗora bakinsa a hancinta ya ce "Ubangiji ya tausasa mini bakin ƴar mutum Rome" ta saki murmushi tana kallon shi, shi kuma ya kalli bakinta a hankali ya ɗora nashi ya sakar mata light kisses ya ce "Tayi ta son Modibbo har abada" tai dry hannunta a gemunsa tana murɗewa kamar yadda ta saba kafin ta sumbaci cheeks ɗinsa kamar yadda ya bata darasin haka ta ce "Allah ya kashe masu son kashe mini Abbana" ya juya idanu kawai ta ƙara sumbatar ɗaya gefen ta ce "Allah ya bawa Modibbona zuri'a mai tsafta" ta kalli bakinsa dake juyawa da sauri ya rufe idanu sbd kyakkyawan al'amarin data sakar masa ta ce "Allah ya bawa Yaa Sheikh arziƙi mai amfani" Ya rungometa a jikinsa sukai shiru na wani lokaci Yaa Sheikh na sauraran yadda jikinta ya saki kullum a rigimar ba zata tafi bedroom ɗinta ba take, ita kuma tana sauraran yadda zuciyar shi ke bugawa da ƙarfi. Har bakin ƙofa ya rakata ta saki kuka sosai shi kuma ya lalace wajan lallashi. Yana zuwa part ɗinsa bathrobe ya shige ya ƙara yin kyakkyawan wanka mai kyau kafin ya sauya shiga. Parlour ya dawo ya ɗauki green tea ɗin da Ummul ta haɗa. A hankali yake sha lokaci zuwa lokaci ya saki Ajjiyar zuciya ya ce "Allahamdulillah Ya Allah" a haka ya shanye green tea ɗin tas ya koma ya yi brush kasancewar a gajiye yake yasa ya kwanta. Sai da me barci ya gagari idanunsa, zufa sai yanko masa take naman jikinsa na rawa Al'amarin daya fara sauya kamewar tashi kenan. Ya miƙewa a hankali ya nufi bathroom ya sakarwa kansa shower amma kamar an ƙara masa hutar abin da yake ji a gangar jikinsa. Ya kifa kansa jikin Sink bakinsa na rawa ya ce "Yasubuhanallah, Ya Allahu" ya koma kan bed ya rufe jikinsa sosai amma ina marar shi sai ɗaurewa take, bai taɓa jin abu kamar haka ba. Zahrah ta buɗe ƙofa ta shigo sai baza ƙamshin take ta nufi kan Royal bed ɗin ta ce "My Excellency me ya faru are you Okey?" Tana neman shigewa jikinsa ya yi saurin ja baya ya ce "Ummul, kira mini Ummul" Zahran ta ɗauka bashi da lafiya ganin yadda ya rikice sosai jikinsa na rawa da ɓari sam ta mance maganin data zuba cikin shayin. Ta juya da sauri ta fita, tana fita ya miƙe tare da ɗaukan key ɗinsa ya saka jallabiya. Halisa na kwance tana barci taji anyi sama da ita ta buɗe ido da sauri "Abba" ta faɗa cikin muryar barci mai kulata ba ya nufi ƙofar fita daga gidan baki ɗaya tsoro ya kamata domin tana jin yadda naman jikinsa ke rawa haƙurin shi na haɗewa ta ce "Abba ina zamu?" Cikin sabon al'amarin dake bijiro masa ya ce "Kuyar da babban darasi cikin littafin alhayat alzawjia.....*Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.* *Ina masu kananan nono?* *Ina masu yaye?* *Ina yammata da ake shirin aure?* *Ina matan gida masuson gyara?* *Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?* *Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?* *Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.* BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679 IG Bintus-spa-nd-more.. *FTR* 43 A ƙofar gidansu Asad Haji Isah yayi parking ɗin motarshi bayan ya kashe suka fito a tare shi da Alhaji, Shina gab a Alhaji yana baya suka tura gate ɗin gidan suka shiga ciki da Sallama ɗauke a bakunan su. Hassana dake goge tiles ɗin tsakar gida ita ta aje mopar tana musu Barka da zuwa kafin ta tsugunna har ƙasa tana gaishe su. Alhaji yana amsa wa cike da tsokanar ta yake cewa. "Bana zan aurar daku na huta da zaryar samarin ku tunda kunƙi ni nai muku tsufa" Hassana na dariya! Haji Isah na taya ta haka suka wuce zuwa falon Ummi wadda take ninke kaya ganinsu yasa ta kira Hussaina ta kai kayan Bedroom bayan ta gaishe dasu Alhaji. Samun guri sukai a saman kujeru suka zauna Da sauri Ummi ta fita waje tana cewa. "Bari a ɗora muku ko ruwan zafi ne kun tarar mun gama karyawa" Da azama Alhaji ya tare ta da cewa. "Idan dammu ne kowa ya ƙoshi ta so min Aliyu idan yana gida" Ummi ta dawo tana cewa. "To shikenan Alhaji, Asad kam yana gida sai dai ina tunanin ya sami bacci ne don jiya bai rintsa ba ya kwana........" Sai tai saurin datse maganar ganin Alhaji Isah sabida kada yaga anwa ƴarsa cin fuska sai ta waske da cewa. "Ya kwana cike takardun Kuɗin hayar su da aka kawo" Tana faɗi tai Istigifari a zuciyarta. Alhaji yayi murmushin jin daɗi yace. "Allah ya ƙara kintsa mana shi dan na ɗagu naga ya koma shugabancin Kamfanin Mahaifinsu dan ban ga amfanin Yahaya a kamfanin ba, Tunda ba haushe yace Dukiya sai mai ita" A zuciyar Ummi tace Maganarku ce ta jini ɗaya ta wuce ɗakin Asad dake ɓarinsa. Sai da tayi sallama sau uku kafin ya amsa. Bata shigaba sabida bata san a wani yanayi yake ba, duk da ya halarta gareta amman sai tace masa. "Kazo Alhajin Galadanci yana kiranka a falo" Da "Tom Ummi" Ya amsa mata a ranshi yana cewa shikenan Yazo yi masa tunin tariyar Aysha ne. Ummi ta juya ta gayawa su Alhaji ga shinan ta miƙe ta shiga bedroom tana cigaba da aikinta sabida taga kamar ba wajanta suka zoba. Ya jima a kwancen kafin ya tashi da ƙyar yana hamma duk idanunsa sun kumbura sunyi jajir sabida bashin bacci. Jikinsa sanye da Guntun wando iya gwiwarshi babu riga sai hamma yake saki ya faɗa Toilet ya sakarma kanshi ruwa kafin ya fito ya shafa mai sama sama ya saka Baƙar jallabiya tare da fesa turare ya fita yana zuba ƙamshi. Ya zira takalmi yayi Falon Ummi. Da sallama ya shiga ya soma gaida Alhaji sannan ya gaida Surukinsa Haji Isah. Ya zauna a ƙasan carfet kansa yana ƙasa. "Aishatu zo mana" Cewar Alhaji. Da azama Ummi ta fito ta zauna kusa da Asad cikin ladabi ga surukin nata. Alhaji ya gyara murya kana yace. "Alhamdulillahi ba komai ya kawo mu nan ba sai dan na sanar muku da cewa Aliyu dai Nauyi ya ƙara hawa kanka wato mahaifin yarinyar da ka nema ya aiko ɗansa da katin ɗaurin aure har gidana a matsayin yana gayyata ta bayan munje wajan ɗaurin auren kuma sai Maganganu marasa daɗi sukai ta tashi akan ka da ita yarinyar wanda har ana dangana ku da kuna mu'amala kamar ta miji da mata wannan tasa yaron yace ya janye aurenta Ni kuma nai maka shigar sauri a karo na biyu na kuma nemar maka aurenta yanzu haka tana a matsayin matarka domin babanka Isah ya Biya maka sadakin Fatima fatana dai kayi adalci acikin matan naka kada ka zama namiji mai son zuciya" Alhaji bai jira cewar kowa ba ya ɗora. "Sam bana zargin ka akan maganganun mutane danni hasko alheri ma nake acikin zaman naku kai dai ka riƙe matanka amana" Tunda Alhaji ya soma magana Ummi take tasbihi ga sarki Allah. Kuka zatai ko dariya sai ta kasa kowanne sabida alkunyar Alhaji isah dan ana barin halak don kunya. Shiko Asad ya koma kamar wani sakarai yasan dai Alhaji baze masa ƙarya ba. Lallai babu wani sarki sai Allah bayan ya fidda ran samun Nur sai gashi ta Halarta cikin sauƙi gare shi lallai babu abin yabo da Godiya sai sarki ALLAH. Wani irin farin cikine ya lulluɓe shi tai tsananin bashi tausayi ashe shi yana nan ita tana can cikin tsangwama akan soyayyarshi har ana musu mummunan zato. Ya lumshe ido yana hasko sanda take gaya masa. Nazeer yayi mata halacci tana son shi. Sai yaji duk farin cikinsa ya gushe ɗaci na zagaye zuciyarsa idan da abin da ya tsana yaga tana fifita wani namiji akan shi. Muryar Ummi ce ta katse shi tana cewa Alhaji. "Mun gode Allah ya ƙara girma kuma in sha Allah zai riƙe duk ɗinsu a bisa adalci" Alhaji Isah yayi murmushin jin daɗi yana cewa. "Ai ɗan nawa jarumi ne Allah ya baka ikon yin adalci cikin matankan kasan mata biyu rago baya iyawa" Ummi da Alhaji sukai dariya ban da Asad da zuciyarshi take can wajan son hango wani hali Nur ke ciki a yanzu zatai murna ko kuma zatai baƙin cikin auren nasu. "To sai ka gyara in da zaku zauna dan nan da kwana biyu ko wacce zata tare ya kama ranar lahadi mai zuwa kenan" Cewar Alhaji. Cikin nutsuwa yace. "Ai komai yana gyare fa Alhaji gidana dake Gaida, dama ɗakuna Huɗu ne a falon ko wacce sai ta ɗauki ɗaya abar mini Biyun falo kuma yana haɗe kicin ma haka su zauna kafin muga mai Allah zaiyi kuma na hutar da kowacce ni zan zuba Kayan furnitures ɗin gidan" Alhaji yayi murmushi yace. "Yawwa zaki na haka nake son ka Allah ya zaunar daku lafiya sai maganar lefe kuma" Sai yace. "Zan turawa Nabila kuɗi a haɗa wa ko wacce nata in Allah ya yarda" Ummi sai murmushi take tana jin farin ciki marar misali. Da haka su Alhaji suka miƙe ya raka su har waje yana ta godiya sannan ya dawo gida. Haba wa rungume Ummi yayi yana cewa. "Alhamdulillahi Ummi Na sami Nuri tah" Haka yake ta faɗa cikin farin ciki kafin ya bar falon Ummi yayi ɗakin shi ya ɗauki waya sukai magana da Nabila ya tura mata kuɗin lokaci ya ƙure amman dai a ranar Tace zasu shiga kwari tare dasu Hassana. Tsalle ya buga saman katifa yana rungume fillo yana godiya ga sarki Allah. Hasko abin da baka zata ba baka kawo ba na alheri ya same ka? ********* Daga gidan su Nuriyyah............ *Hannuna saɓa yake afuwan**Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.* *Ina masu kananan nono?* *Ina masu yaye?* *Ina yammata da ake shirin aure?* *Ina matan gida masuson gyara?* *Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?* *Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?* *Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.* BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679 IG Bintus-spa-nd-more.. *FTR* 44 Kowa ka duba yana farin ciki da wannan aure hatta Baba Usman ƙanin malam bakin sa ya kasa rufuwa sabida tsananin murna, Sabida Nazeer yayi niyyar tozarta su ne sai Allah ya nuna Ikon shi da isar shi akan lamarin auren domin wanda aka danganta shi da itan ya auri abarshi. Haka su Ya salisu sukai ta fitowa da mutane tuwon ɗaurin aure suna ci sai dai waɗansu mutanan ma gulmace ta kawo su najin Nazeer ya fasa sai kuma su koma da Labarin Zaki ya amshi auren. Kafin kice me magana ta cika unguwa wasu ma cewa suke bara zana Zaki yayi wa Nazeer shiyasa ya haƙura maganganu dai kala.kala tunda dama mutum ba'a raba shi da magana. Daga cikin gida ma hakan ce ta kasance Domin Da matiƙar tsumar jiki Ya jidu ya shiga yana kiran Innah Wadda taci adon jan lace mai uban tsada sai baza ƙamshi take sabida ƙyan jikinta baka ce ta haifesu ba. Innah dake tsakiyar dangi suna tsokanarta akan nan da wata tara zata goya jika ita ta amsa masa tana tasowa zuwa wurin sa. "Innah kinga mayen nan sai da ya auri Nuri" Sam bata fahimta ba sai ta ce. "Kai ban gane ba waye mayen Nazeer ɗinne ya koma maye?" Da sauri ya shiga girgiza mata kai Baki na rawa sabida zaƙuwa yake shaida mata Yadda ɗaurin auren ya kaya har yana cewa shi dan tsabar takaici ma bai tsaya jiran a shafa fatiha ba yabar wajan. Wata uwar ƙara Innah ta zunduma kamar mai shigar iskoki kana ta zube a wajan tana kuka wiwi wanda hakan yayi tsananin bawa Jidu mamaki kukan da take ne ya janyo hankalin ƴan uwanta dake ɗakin suka fito suna tambayar mene ne? Da taimakonsu suka kaita ɗaki Jidu ya shiga gaya musu meke faruwa. Wata yaya a wajan Innah tayo kanshi tana zagin shi. "Munafuki kaja da yin Allah ne ai duk wata wutar kai kake kunnawa ina jiyar maka ranar da zakaji kunya, Ke kuma Binta kin zauna kina kuka kamar wata ƙaramar yarinya wannan aure ya isheki ishara da duk wani mai takara da soyayyarsu dan Allah kubar yarinyar nan ta huta haka wannan jaraba da mai tayi kama" Cikin kuka innah tace. "Haba yaya da zaki faɗi haka yaron fa ance ɗan daba ne kwanaki har bursun yayi akan ana zarginsa yayi kisan kai sannan na ɗauki ƴata guda ɗaya tilo na bashi haba Yaya bakwa tausayina" Salati yayar Innah ta hauyi sai kuma tace. "To wanda yafi kowa sonta ya bashi sai ki raba igiyoyi ukun da aka ɗaura musu yau ina zaton baki taɓa ko ganin yaron nan ba amman kin ɗauki karan tsana kin saka masa haba Binta kamar ba musulma ba duk yadda akai akwai rabon zuri'a tunda kika ga Rabo ya nace sabida haka ki taka a hankali kada kiji kunya nan gaba kaɗan" Da ire iren waɗannan nasihohin masu kama da faɗa ƴan uwan Innah suka shawo kanta harta sami nutsuwa shikuma jidu suka masa zagin tsame nama suka kuma gargaɗe shi akan ya daina gaya mata irin waɗannan maganganun domin tana da ƙaramar ƙwaƙwalwa marar jure damuwa gudun kada ta shiga.matsala Ita ko Baba sabuwa saboda farin ciki sai da ta taka rawa haka ma Maryam da abin yayi matiƙar birgeta dan har albarka sai da ta sakawa Babar Nazeer. Maƙota nata shigowa suna Allah sanya alheri kuma ba dan komai suke zuwa ba sai don gulma Idan suka zo kuma haka Baba sabuwa zatai ta gaya musu magana a fakaice. Dole su Ya Saudat suka tafi gidan Nazeer aka kwaso kayan da aka jera. Haka suka dawo gida da kayan. wanda zuwa wannan lokacin Nazeer ya faɗi an tafi kaishi asibiti yana ta sumbatu shi bai haƙura da Nuriyyah ba hankalin Umman shi ya tashi shine ta shigo gidan Su Nur A fusace tana dukan ƙyaure. Wallahi sai Innah taje ta cire asirin da sukai wa ɗanta. Hayaniya ce ta kaure domin Sosai su Ya saudat suka yo kan Babar Nazeer wanda hakan ne ya tashi Nuriyyah data ke ta bacci sama sama take jin muryoyi na tashi har ta gaji ta miƙe a hankali ta fita tsakar gidan duk da yadda hannunta da ƙugunta ke mata zugi. Amman haka ta ƙarasa ta janyo hannun innah dake mayar wa da Babar Nazeer martani. Itama Babar Nazeer ƴaƴanta ne suka fitar da ita waje. A ɗaki Nur ta saki Hannun Innah wadda jikinta har rawa yake. "Duk ke kika cuce ni kika nace sai wancan yaron gashi nan uwar nazeer tazo tana aibata mu abanza" Da rashin sani Nuriyyah tace. "Wani abun ne ya faru Innah?" "Nazeer ya fasa auren ki a wajan ɗaurin aure sai Kakan Asad ya amsar masa auren ki" Cewar Maryam dake shigowa ɗakin yanzu. Luuu tai zata faɗi da sauri Innah ta janyota jikinta tana shafa bayanta. Numfashi taja tare da sakin kuka tana cewa. "Shine Kuma zasu bawa Asad aure na kamar an gaji dani bayan yayi auren shi ya barni sannan a kuma bashi ni" Sai ta soma shure ƙafafu a ƙasa tana kuka kamar wata ƙaramar yarinya. Abin sai ya bawa Innah mamaki duk zaton ta Nuriyyah zata fi kowa farin ciki ne sai ta ga akasin haka wannan yarinya kishin wa ta gado haka ita dai bata da wannan kishin. "Shagali yau ina ganin bidiri munafuka bayan koke koken da kika gama yi sai shi shine zaki zo kina kuka" Innah ta faɗa tana ƙoƙarin fita tsakar gida don ba zata iya da iya shegen Nuriyyah ba don ita zuciyarta tai sanyi da lamarin tunda ƴan uwanta suka Nunnuna mata gaskiya akan ta bar wannan aure domin ba'a ja dayin Ubangiji. Da sauri Nuriyyah ta rungumota tana kuka sosai da iya gaskiyarta tana cewa. "Innah dan Allah kicewa malam ya raba auren nan wallahi bana son shi ni yanzu Nazeer nake so" Innah na dariya maryam na taya ta innah tace. "Haba tattabara uwar soyayyah tunda nima nai mubaya'a da wannan aure kema sai kiyi manyanki sun nuna isarsu akai Nikam ina muku fatan alheri dan wannan aure naku ya bani tsoro ya ƙara sawa naji tsoron Ubangiji sosai Allah yasa hakan ya zame muku alheri" "Amin Binta haka ake son mutum ya zama mai karɓar shawara muma ƴan uwanki munji daɗin yadda kika amshi shawararmu kuma ina tabbatar.miki auren nan alheri ne sha Allah, Bama son ƙiyayyarki ga surukinki tai yawa gaba kiji kunya Shiyasa amman yanzu kam tunda kin gane gaskiya Alhamdulillahi Allah ya basu zaman lafiya amin" Cewar Yayarta wadda tai tai mata faɗa a ɗazu. Innah bata iya amsawa ba sabida kunyar kukan data dinga yi ɗazu sai ma fitar datai tabar Yayarta da Maryam da Nuriyya a ɗakin. "Ke kuma kukan me kike haka?" Cewar Yayar Innah. "Babu komai" Nur ta bata amsa. "To kinga dai bake ɗaya bace ance yana da mata" Gaban Nuriyyah ya faɗi itafa tsoron kishiyar ma take ji. "To ki nutsu ki kula da mijinki ladabi biyayya kinga dai yadda uwarki take da Baba bamai cewa zaman kishi suke haka zalika tunda take bata taɓa yaji ba dan Allah fatima kema ki zauna lafiya kinji ko" Nuriyyah ta share hawaye! kana tace. "In sha Allah Hajiya Yaya nagode" Haka Yayar Innah taita mata nasiha kana ta fita. Nuriyyah ta kwantar da kanta a cinyar maryam tana cewa. "Allah mai iko maryam yau wai Asad ya zama mijina kinga lamarin Allah ko, Nifa na ɗauka Innah zata dake ni ne fa sai naga kuma ta saki kam yanzu ta daina jin haushin Asad" Maryam ta murmusa kana tace. "Kina ji fa Hajiya yaya tace sun mata nasiha akan auren kuma ta burgeni da ta ɗauki Nasihar su wallahi" Nuriyya tace. "Dama fa Rigima ce irin ta Innah ita bata ga Asad ba Amman Jidu yana ta zugata tana hawa" Nuriyyah ta faɗa tana dariya. Maryam ta ɗan dake ta a baya tana cewa "Yau sai kiyi bacci mai daɗi ai buri ya cika" Ta wani lumshe idanu Sannan tace wa Maryam. "Ba bacci mai daɗi ai sai a jikin Ogana Na matsu yazo na ganshi duk da dai wallahi Wannan matar tashi ta shige mana hanci da ƙudundun ne" Dariya maryam tai. "Dama shegantaka kike wa Innah ɗazu wallahi dama tace to bari ta gayawa malam a warware auren" Zare Ido Nur tai tana yamutsa fuska sabida zafin da hannunta ke mata. Haka suka wanzu suna ta hirar su cike da farin ciki. ********** Daga gidansu Asad Ummi tace bazatai wani taro ba amman ƴan Biyu sunce wallahi tayi ai yawan rai ne haka suka yanke shawarar kama Waje wanda zatai wuni anan har da su Nuriyyah da Aysha da Asad. Wajan Biyar na yamma ya fito cikin shirinsa na ɗanyen boyel milk colour sai baza ƙamshi yake ya shiga ɗakin Ummi bayan sun gaisa yace zashi gidan su Aysha. Ummi tace. "Gidan su Nuriyyah fa? yakama ta itama kaje kaga yaya suke ciki" Ya ɗan gyara zaman hularshi tare da cewa. "Ita sai gobe naje ummi Rigimarta yawa ce da ita yanzu naje sai ta san yadda tai ta ɓatamin rai na" Ummi tai murmushi tace. "Kunfi kusa amman dai ya kamata ka leƙa Domin ma ka sanar mata da Wunin da zamuyi" Ya ɓata rai kaɗan yana cewa. "Nifa Ummi bana son wannan bidi'ar dan Allah abar wani wuni kawai akai su gidansu haka" Ummi tai dariya tace. "Wannan baka isa ba in sha Allah jibi asabar zamuyi wunin ko wacce tai kwalliya aje a ɗauko min su harda kai ƴan uwa da abokan arziƙi su taya mu murna" Dariya Ummi ta bashi yadda ta hakimce tana tsara yadda za'ai yasan kuma huɗubar ƙannen shine dan haka bai ce komai ba ya miƙe ya fita. Motarshi ya buɗe ya shiga ya tayar sai gidan Haji Isah wajan Uwar gida sarautar mata gimbiya Ayshatu................... *Team Nur how market*😝 *Littafin FITAR RABO na kuɗi ne akan farashi mai sauƙi domin biyan kuɗin zaki tura naira 300 ta wannan asusun bankin 0078174806 sterling bank shedar biya ta 08142105218, idan kuma card ne mtn card na 400, zuwa wannan number 08142105218**Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.* *Ina masu kananan nono?* *Ina masu yaye?* *Ina yammata da ake shirin aure?* *Ina matan gida masuson gyara?* *Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?* *Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?* *Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.* BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679 IG Bintus-spa-nd-more.. *FTR* 45 Yana tuƙi yana jinsa acikin farin ciki da nishaɗi Allah mai alheri yau shine da zuƙa zuƙan mata har guda Biyu ba tare daya yi zato ba. Haka ya ƙarasa ƙofar gidan Haji isah wanda sai da ya kusan ɓatan kai damma yana da fasaha da baze gane gidan ba sabida yadda ya jima bai zoba. A ƙofar gidan yayi parking ya jingina da seat ɗin kujera yana auna yadda zai ya kirata don bai da Numbern wayarta kuma da kunya ya kira Haji Isah yace yazo wajan Ƴarsa. Haka yasha zaman shi a mota har akai magariba shi bai tafi ba miskilin kuma bai fita ya tambaya ba. Sai da yaji masallacin dake gefen shi Ana ƙoƙarin tayar da sallah sannan ya fita ya sai pure water a wani shago ya ɗaura alwala ya shiga masallacin. Sai da suka idar da sallah ya fito suka ci karo da Haji Isah. Da sauri ya zube yana gaishe dashi, cikin sakin fuska Haji Isah yace. "A'a Asad kai ne a unguwar tamu dafatan ka shiga gidan nima yanzu na dawo daga wajan aikin" Ya shafa gemu tare da cewa. "A'a Abba ban shiga ba, Dama bani da numberta ne da zan neme ta" Mamaki ya kama Haji Isah na yadda Asad ya nuna kamar wani baƙo sai yace masa. "Muje to tunda gidan ya zama baƙon ka" Haka ya saka Asad A gaba wanda kunya ta kamashi har zuwa cikin gidan. Wanda ya cika da ƴaƴan Haji Isah guda uku mata ƙannen Aysha dake aure duk da ƴaƴansu sai ƙanwar Umman Aysha itama da yaranta waɗanda suka zo tattaunawa akan Batun Auren Aysha wanda yazo musu ba zato don a ranar da aka ɗaura auren ma gidan sai da ya zama babu masaka tsinke sabida ƴan taya murna. Daga Bakin ƙofar falon Asad ya tsaya Haji Isah ya shiga kiran. "Mamata fito ga mijin ki yazo" Daga cikin falo Aysha data idar da sallah tai cikin ɗakinta aguje duk kunya ta kamata wai yau ita keda miji lallai babu abun yabo da godiya sai Allah. Ƙarasa shiga falon yayi yana cewa Umma. "Kinga ɗanki da miskilanci wai tun yamma yake cikin mota ya rasa yadda zai ya kira Aisha sai da na dawo yanzu na ganshi a masallaci muka shigo" Umma da daɗi ya kamata duk da taji zafin Auren da Su Haji Isah sukai wa Asad na biyu sabida ya gaya musu tun ɗazun amman yadda Asad ya tako yazo sai daɗi ya kamata domin ta tabbata baze wulaƙanta mata ƴarta ba. Sai ta miƙe ta bi Haji Isah cikin ɗaki sauran ƙannen Aysha ma sukai ɗaki suna murnar zuwan Mijin yayar tasu. Aysha kuwa tsintar kanta tayi da cancaɗa kwalliya ƴar gaske ta saka doguwar rigar atamfa ja da baƙi sai tai amfani da baƙin mayafi abin ka da farar mace sai tai matiƙar yin kyau. Ta fesa turare mai jan hankali ta ɗauki wayarta ta fita kai tsaye kicin ta nufa ta haɗa mai frut,tare da ruwa da lemo ta haɗa a ƙaton try ta nufi falon. Ta aje a ƙasan carfet sannan ta nufi wajan sa don tai masa iso. Da taji nauyin auren amman lecture ɗin da Ummanta da Ƙannenta sukai mata yasa taji ta aje kunyar agefe tana jin zata kula dashi don kulawa ita ke janyo namiji ga mace don namiji kamar yaro yake mai kula dashi yake liƙewa bata tabbatar da zata iya bashi dukkan kulawarta bama sai da taji Abban ta ɗazu yana gayawa Ummanta sun ƙara nemar masa auren wannan yarinyar harma an ɗaura auren tunda taji ba ita kaɗai gare shiba ta ƙara jin ita ma mace zata Bashi dukkan kulawarta. Tun kan ta ƙarasa wajan da yake tsaye ƙamshin turarenta ya masa maraba. "Subuhanallahi" Yace a ƙasan maƙoshi sabida ƙamshin shu'umin ƙamshin ne. Da sassanyar murya tai masa sallama. Tare da yi masa iso zuwa falo. Yabi ta abaya yana kallon yadda take juya jikinta cikin nutsuwa. Saman kujera ya zauna sai ta zauna a daidai ƙafarsa a ƙasan carftet, Dab dashi sosai ta tsiyaya ruwa a cup ta miƙa masa babu musu ya amsa yana mata godiya. Cikin kulawa yace. "Ya kamata ki dawo nan sabida magana nazo muyi kina ƙasa ina sama tayaya zamu ga juna kamar wasu surukai" Sai tayi dariya kaɗan tare da dawowa kujerar dake saitinta tana cewa. "Na haɗa maka frut?" Ta faɗa kanta a ƙasa. "A'a na ƙoshi ki ɗaga kanki mana kya sunkuyar da kai ƙasa" Ya faɗa yana ɗan leƙenta. Gaskiya bata da makusa kuma baya ce yana ƙinta ba tunda matar shi ce ta sunna. Maganar ƙannenta ce ta hanata bashi amsa suka shigo dukkan su suka zube suna gaidashi. Ba yabo ba fallasa yake amsawa suka miƙe aransu suna yaba mijin yayar tasu suna kuma yi mata fatan alheri. "Duka fa ƙanne na ne waccan gajerar ita ke bina yaranta huɗu, mai binta uku ƴar auta biyu" Duk da yayi mamaki lallai tana da kyan jiki amman bai nuna mamakin ba sabida kada taga kamar yayi mata cin fuska don aure lokaci ne sai yace. "Kema huɗun zamu haifa next year da izinin Allah" Sai tai ƙasa da fuska tana dariya. "To Meemah ga dai ni kin ganni" Wani sanyi taji yau ɗaya ya ɓoye mata suna zuwa wani da ban. "Sunan Ummina kenan sunan ki nada daraja wajena gaku ma matata duka dole bazan iya faɗi kai tsaye ba" Tayi murmushi bata ce komai ba. "Haka Allah ya tsara auren namu ta dalilin kotu zamu haɗu fatana dai Allah ya bamu zaman lafiya, kuma bake ɗaya bace Akwai Nur Mun jima muna tare kuma Allah ya ƙaddara kece uwar gida na ita amarya Nur yarinya ce don Allah ku zauna lafiya danni bana son tashin hankali" Tabi bakin sa da kallo wannan ƙatuwar budurwar ce yarinya lallai ma, taji wani dutse ya tsaye mata a zuci amman sai ta danne tana cewa "In sha Allah baka da matsala dani" Namiji shike nuna ai kishin sa ada ta ɗauka zai wulaƙanta ta ya nuna auren dole akai masa, amman sai ya bata mamaki ya karrama ta ya bata martabarta bai nuna waccan ta fita ba tunda in wani ne cewa ze sun jima suna soyayyah da Nur amman shi sai yace sun jima suna tare baiyi kalaman cin fuska gareta ba. Take taji ya amsu acikin zuciyarta da rayuwarta da gangar jikinta duk suna maraba dashi. Haka sukai ta hirar su tun suna jin nauyin juna abinka da ƴar boko Tuni Aysha ta siye shi har yana dariya kaɗan kaɗan da tana bashi labarin Samarin datai a baya. Haka suka wanzu har akai Isha'i Da ƙyar ta barshi ya tawo bayan ta saka Numberta a wayar shi ta kira yayi saved da Meeamah ita ma tai saved tashi ta raka shi har bakin Mota anan ma sun jima suna Tsaye kafin suyi sallama ya shiga mota tana ɗaga masa hannu ya tafi. Sai da yayi sallar Isha'i a wani masallaci sannan ya nufi Unguwarsu haka ya karkata layin Gidan su Nuriyyah.... *************** Tun suna hirar daɗi da maryam har hirar ta isheta sabida tana ta ƙirga lokaci duk zaton ta Asad zaizo da yamma wajanta sabida ɗaukin auren nasu amman har akai magariba shuru sai ta shiga tunanin ko haushin da yaji ne bai huce ba. Har akai Isha'i tana baza Ido shuru wata zuciyar ce ta ankarar da ita fa ba ke kaɗai bace ƙila yana wajan sugar momyn shi. Wani takaici yazo mata wuya ita daman bai aure taba don da ta buɗe idanu ta ganshi da wata gwara ta rasa shi gaba ɗaya...... Muryar Malam taji a tsakar gida yana cewa Innah ku kintsa ga Aliyu nan Mijin Nuriyya zai shigo............. *Ba Editing sai kunyi haƙuri da typing erro* *Littafin FITAR RABO na kuɗi ne akan farashi mai sauƙi domin biyan kuɗin zaki tura naira 300 ta wannan asusun bankin 0078174806 sterling bank shedar biya ta 08142105218, idan kuma card ne mtn card na 400, zuwa wannan number 08142105218**Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.* *Ina masu kananan nono?* *Ina masu yaye?* *Ina yammata da ake shirin aure?* *Ina matan gida masuson gyara?* *Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?* *Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?* *Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.* BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679 IG Bintus-spa-nd-more.. *FTR* 46 Da sauri su Ya Saudat dake tsakar gidan suka hau gyara kwanuka, Baba sabuwa ta baza ƙatuwar tabarma daman ga Hasken ƙwan solar da aka jona a tsakar gidan ya haska ko ina dan ko allura ce ta faɗi zaka iya gani wannan aikin su Ya salisu ne suka haɗa ƙwan sabida ƴan Biki. Ko ina yayi kyau su Ya saudat sun gyara tsakar gidan, tsaf da ike gidan duk babu ƴan biki daga Baba sabuwa sai Ya Amina da Ya saudat sai Maman Mufida matar Ya Auwal, sai Maryam da Innah da Nuriyyah dake cikin ɗaki amman su duk suna tsakar gida suna hirarsu don a gida zasu kwana, Jin Malam yace ga Mijin Nuriyyah nan yasa suka tattare kwanuka da sauran tarkacen Tsakar Gidan. Innah dake zaune saman kujera bata ko motsa ba sai da Ya Saudat ta shiga ɗakin Innah ta ɗauko mata mayafi tana cewa. "Innah da Baba ku zauna a gefen can shi sai ya zauna anan" Ta tsara musu yadda zasu zauna ɗin suka zauna ita dai Innah bata ce komai ba tabarwa Baba surukanta kar taja baki tai shuru. Haka Ya Saudat ta ƙara komawa Ɗakin Innah ta tarar da Nur inda ta barta. "Ki tashi ki cire wannan Farin Hijabin ki gyara ga mijin ki nan malama" Sake gyara zama tayi tare da yatsine fuska. "Ya Saudat bana jin daɗi Rabu dashi Don Allah" Babu yadda Ya Saudat batai da ita akan ta tashi ta gyara ba amman taƙi haka ta gaji ta rabu da ita ta fita tana cewa. "Idan kwa wannan kafar kan zaki masa zaki ci wuya don Namiji baya son taurin kai, Fisabilillahi ai kya gyara jikin ki ko" Ita dai bata tanka wa Ya saudat ba haka ta ƙara jan hijabinta ta rufe fuskarta sosai sabida zazzaɓin dake cin jikinta. Ya Saudat na zama Ya Auwalu ya shigo bayan sa Asad ne dake sunkuyar da kai ƙasa don sosai yake jin Nauyin shigowa gidan. Ya Auwalu ya sami gefen Innah ya zauna tare da Nuna wa Asad wajan zama. Tunda Asad ya shigo gidan su ya saudat ke tasbihi ga Allah kyau iya kyau ah dole Nur tai hauka akansa ashe haka yake Baba kam ta kasa rufe bakinta sai far'a take tana cewa. "Maraba da ɗan albarka zauna sosai maryam kawo ruwa" Innah na ƙasa da kai tana kallon shi ta wutsiyar idanu, sosai nutsuwar shi ta bata mamaki uwa uba tsantsar kyau da cikar zatin da Allah yayi masa anya Jidu ma ba ƙarya yake masa ba, Don wannan yafi Nazeer komai hatta shekaru. "Mama ina yinin ku da fatan na same ku lafiya" Muryarshi cikin nutsuwa ta bugi kunnen Innah. Baba kaɗai ta amsa, sai su Ya saudat dake gaishe dashi ya Auwal ya shiga gabatar masa dasu a matsayin yayin Nuriyyah da sauri yace. "Ai da kun jira ni na soma gaida ku Yayinmu" Dariya ya Amina tai tare da cewa. "Ai ga uwar ɗakin matarka nan saudat ita zaka gaisar nikam faɗa muke da ita dan tamu bata jiƙuwa" Dariya Su ya saudat sukai ban da shi daya ke raba idon inda zai hangota. "Ga kuma mahaifiyar ta nan Hajiya Innah" Cewar Ya Auwalu. Asad ya ɗan ɗago kaɗan yana sakin murmushi suka haɗa ido da innah yaga kama tsantsa ita Da Nur da sauri ta kauda kai tana jan mayafi. Cikin haka Malam ya shigo ya zauna ya fuskanci Asad ya shiga yi masa nasiha akan shugabancin gidanshi tare da yin adalci a tsakanin matanshi. Kamar ɗa da mahaifi malam yake ta yiwa Asad nasiha mai ratsa zuciya Har ya ƙare ya miƙe ya Auwalu na take masa baya. "Ina fatima ne ga mijinta" Cewar malam. Ya Saudat tace. "Babu yadda ban da ita akan ta fito ba taƙi" Aran Asad yace Hali zanan dutse ashe bani kaɗai take wa kafiya ba Allah sa ba wani laifin nayi ba. "Ai bata jin daɗi ne Shiyasa" Cewar maryam da sauri tana kare ƴar uwarta. "Toto Allah ya bata lafiya tashi muje ka duba jikin nata ka wuce gida" Cewar Malam wanda da kanshi yayi wa Asad jagora zuwa ɗakin Innah. Ɗakin babu haske sosai, Malam ya nunawa Asad gefen darduma yace ya zauna kana ya shiga kiran. "Uwata sannu kina ina ne kinsan idanun nawa sun fara dishewa,ga mijin ki nan yazo taso uwata sannu" Tana jin muryar malam ta ƙara rufe fuska sosai murya a shaƙe kamar an mata dole tace. "Na'am Baba gani" Gaban Asad ya faɗi jin yadda take magana da ƙyar Allah yasa ba laifi yayi ba dan yana gane muryarta in tana cikin damuwa. "To taso mana kona kama ki" Cewar malam. Asad ya ware ido da alama fa ƴar so ce ya rasa wayafi son ta tsakanin shi dasu malam dan shi ji ike kamar yayi tsuntsu ya ganshi a gabanta. "A'a zan iya taso wa" Ta faɗa tana cije baki kafin a hankali ta taso tana dafa bango ta ƙaraso kusa da Asad ta zauna. Wata nutsuwa Asad yaji wadda ya jima bai jita ba. "To ga mijin ki nan, Aliyu ina waje idan kun gama" Asad yayi godiya malam ya fita wanda ya cewa su Innah gaba ɗaya subar tsakar gidan su shiga ɗakin baba. Haka suka koma ɗakin Baba suka cigaba da hirar su wadda rabi akan yabon Asad Ne. Malam yana fita ya ɗan matsa jikinta kaɗan murya cikin raɗa yace. "Babyy......." Da wata irin narkakkiyar murya ya fitar da salon. Wata irin tsuma jikin Nuriyyah ya soma da ƙyar tai ta maza ta maze tai masa banza. "Magana fa nake a taimaka a mayar mani da martanin ta" Sai ta juya masa baya. Ya ɗora hannunshi saman hijabin nata. "Yaya jikin naki ko muje asibiti" Ta saka hannu ta zame nashi hannun murya cikin jin haushi tace. "Da ka wurgoni daga motarka bakai tunanin asibitin ba sai da wajan yayi tsami ko ajikinka" Ƙara matsota yayi tare da kai hannunshi cikin hijabin yana lalubar haɓar zaninta yana cewa. "Muga wajan bari na duba shi" Ƴar ƙara ta saki tana cewa. "Asad ka bari don Allah kada Innah tazo" Sai ya miƙe tsaye yana kallonta. "Taso muje asibiti wallahi sai an duba wajan tunda kikai min ƙorafi" Jin ya rantse yasa ta miƙe wai sai ya matso zai kama hannunta aikwa ta goce tai gaba. Sabida kunya batai wa su Innah sallama ba ta fice shine ya ƙarasa wajan Malam yace zai kaita asibiti ya dawo. Malam yayi musu fatan dawowa lafiya da kanshi ya buɗe mata gidan gaba ta shiga shima ya zagaya suka soma tafiya. Shike janta da hira tana bashi amsa sama sama wadda duk rabi akan yadda auren nasu yazo ne ba zato, da haka suka ƙarasa wani ƙaramin asibiti wanda ya barta a mota ya fita sai da yayi komai sannan yazo ya buɗe mata ya kama hannunta suka jera gwanin sha'awa. Suka shiga ɗakin da Likitar take mace don yace baya son namiji ya taɓa.masa Nurin sa. Suka shiga bayan sun gaisa likitar ta shiga yi mata wasu ƴan tambayoyi tana bata amsa daga ƙarshe ta nemi ta duba wajan. Da ƙyar Asad ya lallaɓata ta kunce zaninta likitar ta tattaɓa wajan kafin ta cafki ƙashin wajan tana murza mata haɗe da wani Cream, Ihu Nur take tana faman kiran sunan Innah da malam. Asad yabi ya kanainaye ta ajikinsa yana shafa gadon bayanta. "Ka sake ni wayyo zafi innah malam Zanyi fitsari wayyo zafi" Duk yadda yaso danne dariyar shi ina sai da ta fito kamar ba ita kewa mutane allura ba. "Yi fitsarin anan" Ya faɗa yana ƙunshe dariyar shi. Haka likitar ta gama duba ta tsaf sannan ta sallame su ita kanta dariya takewa Nur ɗin. Tunda suka shiga mota ta juya masa ƙeya yayi maganar duniya tai masa banza haka yaja motar ya cigaba da tafiya a bakin wani gun sai da nama ya tsaya ya fita ya siyo mata haɗe da lemuka ya dawo ya tayar da motar wanda hakan yayi daidai da sanda Aysha ta danno masa kira. Wayar tana a tsakaninsu sai ya basar sabida yasan halin Nuri. Sai dai ina ya makaro domin tuni Idanunta sukai mata tozali da Sunan. "Meemah" Raɗo raɗo ajikin screen ɗin yana yawo. Wani hazo hazo ta soma gani kafin ta danne zuciyarta ganin yana ƙoƙarin katse kiran tace. "Ba matar ka bace ka ɗaga mana" Mamakin jin furucinta ya kama shi tunda suka tawo yake magana taƙi tanka shi amman jin ana kiran shi yasa tace ya ɗaga. Ba yabo ba fallasa ya ɗaga wayar sai dai garin sauri ya saka ta a handsfree. Cikin kirsa Aysha dake kwance a saman gado tace. "Amincin Allah ya tabbata agare ka my prince da fatan kaje gida lafiya?" Ya ɗan saci kallon Nuri aikwa yaga rannan nata a haɗe kamar kace kat ta fashe sai yace. "Lafiya ina draving bari na sauka" Da sauri tace. "Gaskiya ka koma gida wato tun yamman daka fito baka koma gida ba kenan?" "Ummh inna koma mayi magana Bye" Ya faɗi tare da katse wayar ya cigaba da tuƙinsa sai dai yayi ƙoƙarin haɗe ranshi tamau dan yaga ƴar rigimar tashi ta cika so take ta fashe. Har ya ƙarasa layin gidansu bai saki ranshi ba. Ta hakan ya sami sauƙi da buhun rigima zata kwance masa ta ɗaga masa hankali. Tun kan yayi parking ta nemi ɓalle murfin motar ta fita. Sai yaƙi bata dama ya riƙo hannunta. Murya a tausashe yace mata. "Ga namanki ina zaki bamu yi sallama ba?" Jin maganar take kamar saukar dalma a zuciyarta dan wani irin haushi ya bata. "Kasan ni mayya ce dalla sakar min hannuna ni" Sai ya haɗe rai sosai. "Waye dallah? Nur nifa ba sa'anki bane kuma yanzu ina mijinki ya kamata ki shiga hayyacin ki" Ta ɗago a zafafe. "Kasan shaye shaye nake, to dole ne auren a rabu mana ni da kai waya liƙewa wani mtsssss"! Taja tsaki. Ya dafe kanshi yana ƙoƙarin danne takaicin daya taso masa. "Zagina ai ba yau kika soma ba jeki gida na gode madalla nina jawa kaina" Sai kuma taƙi fita Ganin yayi fushi sai ta shiga tashin hankali, dama haka ne idan taja yaja yayi fushi sai ta sauko sai ta shiga nutsuwarta don a duniya idan kana son ganin tashin hankalin Nuriyyah to Asad yayi fushi da ita duk sai taji ta tsani kanta,Kuma gata da shegen rashin kunya bata raga masa ko kaɗan ga kuma muguwar soyayyar sa aranta. "To kayi haƙuri" Yayi mata banza. "Nace Allah ya baka haƙuri" Yaja ajiyar zuciya mai ƙarfi. "Ni na kasa gane kanki wato a haka zamuyi zaman auren? a haka zaki haifar min yara ki basu tarbiya suna ganin yadda kike wa Ubansu rashin kunya kamar sa'anki, Ni ba zan ɗauki wannan ba kije ki koyi yadda ake magana da miji danni ba sakarai bane, ba zaki bani ciwon kai ba" Ya faɗa da ɗan fushi a saman fuskar shi duk da dai baya fushin da ita sai dai dole ya saita ta idan yace a haka zaman nasu zai tafi zata zamo ita ce mijin shi matar kenan. "Allah ya baka haƙuri ni dai ba faɗa naja ba" Ta faɗa tana ƙoƙarin fita. "Sai kuma ta bashi tausayi yasan duk acikin soyayyar shice yasa ta wannan fushin domin kishin sa ya sa ta hakan wanda yama ga ƙoƙarin ta sosai akan danne kishinta ga Aysha" "To na haƙura yi min dariya" Ya faɗa yana leƙa fuskarta. Sai ta fashe da kuka mai tsanani tana cewa. "Ashe da sauran dariya a fuskata bayan ina kallonka kana waya da wata har kana sauya mata suna bana ta na asali ba har kana wuce ni kaje wajanta bayan tsananin buƙatarka da nake yi" Innalillahi yake ta ja aran shi Nuriyya danja wutar baya Nuriyyah rigima. A hankali ya janyota ya haɗeta da jikinsa ya shiga gaya mata................. *Littafin FITAR RABO na kuɗi ne akan farashi mai sauƙi domin biyan kuɗin zaki tura naira 300 ta wannan asusun bankin 0078174806 sterling bank shedar biya ta 08142105218, idan kuma card ne mtn card na 400, zuwa wannan number 08142105218**Assalamu alaikum yan uwamata :muna farincikin sake gabatar muku BINTU* *-SPA-ND-MORE.. inda zaku sami ingantaccen garin maganinmu,na zallar magungunan gargajiya daya hada da hakukuwa,ganyaye,kauci,huda,sassake da hatsi kala kala wadanda basuda illah ko kadan ajikin Dan adam.wannan maganin an hadashi ne bisa yarda da amincewa da da hannun gwanaye kuma masanan* *magungunan gargajiya nagarin kano.wannan magani yana gyara nono wanda ya yamushe,ko wanda ya kwanta,ko wanda ya tartare,ko wanda akeso ya cicciko,ya daga, ya mike,yayi kyau.* *Ina masu kananan nono?* *Ina masu yaye?* *Ina yammata da ake shirin aure?* *Ina matan gida masuson gyara?* *Ina zawarawa masu shirin aure ko gyara don zawarci?* *Ina ramammum mata dasukeso suyi kiba su murmure?* *Wannan gari shine kuke bukata.yana* *tadakomada,yana da kiba,yana ciko nono,yana sawa mace tayi* *mulmul,tayi dumimi,tayi kyau tayi* *haske,sheki,sulbi da santsi kamar kinyi gyaran jikin yan* *maiduguri.koina ze cike Tatar data yamushe zata mike tayi fes kamar sabuwar amarya.*💯💯💯🔥🔥🔥 *A BINTUS-SPA-ND-MORE muna gyaranjiki* *gangariya,inda za a gyara Amarya ko uwargida ciki da waje kifita fes ga kamshi ba a magana.Akawai turarukan wuta, na daki,na jiki,na tsuguno, na kaya ,humrori.Akwai zafafan kuma gangarinyan* *magungunan mata sha yanzu magani yanzu da yardar Allah,Akwai ingantatun supplements na nono,hips skin,na kiba,na saukar da niima da dai* *sauransu.kayanmu guarantee ne,babu cuta babu cutarwa.muna aikawa koina a Nigeria cikin aminci.yar uwa kada ayi babuke,kada abaki labari.sai angwada akansan na kwarai takenmu shine gaskiya da amana.* BINTUS-SPA-ND-MORE... na nan a mandawari nagoda street daidai asibitin yara na marmara @kano.Zaku samu BINTUS-SPA-ND-MORE @CALL\WHATSAPP 07067338694/ 08136259679 IG Bintus-spa-nd-more.. *FTR* 47 Kalamai masu daɗi tare da kwantar da zuciya, Sai dai ko da wasa bai yi gigin nuna mata tafi Aysha a wajan shiba wannan sirrin ya barwa zuciyarshi sabida yana son yayi adalci a tsakanin su ne. Sabida yadda Alhaji da Malam Mahaifin Nur ɗin sukai ta jaddada masa yayi adalci a tsakanin matan nashi. Koma ba haka ba, Shima kan sa yasan matsayin wanda ya ƙi yin adalci a tsakanin matanshi a ranar gobe ƙiyama duk da akwai wadda tafi kwanciya aranka sai aka ce ka bar Abin a ranka. Sun jima Rungume da junansu don sai da yaji tana ajiyar zuciya alamun tayi shuru sannan ya ɗago ta ya saka tafin hannun sa yana share mata hawayen ta. Cikin son ya rarrashe ta yace mata. "Aysha ita ma matata ce kamar ke Nur don Allah ba danni ba ki tayani nayi adalci a tsakanin ku, ki ƙaddara cewa daman can Allah ya rubuta bake kaɗai ke gare ni ba, kuma maganar naje wajan ta ai ya zamar min dole tunda matata ce, Sannan maganar suna dana ɓoye ta yaya zan dinga kiranta da Sunanta bayan sunan Ummi ke gareta Haƙiƙa Aysha tana da girma a idanuna" Ya faɗa muryar shi tana sauka a hankali. "Kuma gata matar ka ba, Dama ni nace kar kayi adalci ne? kona ce karka je wajanta ka dawwa ma kana zuwa wajanta wani ya dama" Ta faɗa ranta na mata suya tana jin rashin dauriya akan abin da yake taso mata wanda ta tabbata kishin sane mai tsanani. Yabi ta da kallo yana girgiza kai wallahi har kanshi ya soma ciwo wato Nur danja ce iya danja duk yadda zata ɓullo maka da rigima ta santa, Ga rashin iya magana kamar Gogon gwauro kamar ba yanzu ya gama nuna mata ɓacin ranshi akan rashin iya magana ba amman gashi harta ƙara yan ko wata wai ka dawwa ma ya maimaita aran shi. Nan da nan ya ɗaure fuska babu alamun wasa a tare dashi yace. "Ke kam kinƙi fahimta ɗauki ledar ki wuce gida In sha Allah jibi Ummi zata yi yinin ta zaku je tare da Meemah, zan aiko da kayan da zaki sa sabida nafi son kuyi iri ɗaya sannan kice wa Mama Gobe za'a aiko da akwatuna Jibin daga wajan yinin Ummi zaki wuce gidan ki" Ya faɗa hankalin sa kwance yana duba wayar shi. "Kai baka da baki sai ni, da kata malam babu wani yini da zani kuma tare wa ba yanzu ba sai wani satin inna gama shiri na dan ammin kutsen auren da ban shirya masa ba" Yaji ciwon maganganun ta sai yayi tagumi ya sunkuyar da kanshi ƙasa idan ya biye mata ransu zai ɓaci ne shiyasa ya danne ranshi sosai, Innalillahi yake ta ambata a hankali sabida yadda kanshi ke sarawa Nuri zatai ajalinsa idan ba'ai wasa ba damuwarta da rigimarta sun yi yawa daga wannan sai wannan ita ko tausaya masa ma bata yi kowa yasan auren Aysha ƙaddara ce Kamar yadda itama auren nata ya zama FITAR RABON SHI domin ba daban ta fita daga hannun Nazeer ba da baze same ta ba to inda ta auri Nazeer yaya kenan?. Motar tayi tsit babu wanda ya kuma magana acikin su, shi yayi shuru ne sabida ya daidai ta nutsuwar shi ita kuma taji matiƙar haushi sabida ya mayar da ita shasha sha yayi mata banza tana magana. "Kiyi haƙuri Nuri kije yinin Ummi don Allah ki kwantar da hankalin ki duk abin da kike tunani ba haka bane ita ƙaddara tana zuwar wa bawa ne ba tare da ya zaton zata zo ba sabida haka duk yadda ta zo masa sai ya amsa" Ya faɗi maganar cike da rashin sabon jure hayaniyar mace. "Allah ba in da zani" Sai ya juyo ya zuba mata ido. "Sai kinje ni kuma nace ke har kin isa mahaifiyata tace ayi abu amman ki ce a'a" Ya faɗa a wannan karon da zafin shi. "Wallahi ba Ummi bace kai ne ka shirya hakan domin ka nuna wa duniya bani kaɗai kake so ba" Da sauri ya katse ta a zuciye. "Dama na taɓa gaya miki ke kaɗai nake so? to kiyi duk yadda zaki wallahi sai kinje wawiya kawai fitar min a mota marar kunya" Ya faɗa da tsananin jin zafi. Wallahi ba da ban yana son Nuri ba da ya haƙura da ita ya huta sai dai ita ɗin ta zame masa ƙaddara acikin rayuwarsa tun da ya haɗu da ita yake ganin ƙalubale kala kala yaushe ne zasu huta zuciyoyinsu su huta daga wannan sai wannan ita kanta rigimar ta yawa gare ta. "Dama ai ba motar ubana bace in Allah ya yarda daga yau bazan ƙara shiga motar nan ba koda yaushe sai kace na fitar maka a mota Kuma zancen so da ka so ni da ka ƙini duk kai kaji ko a yau ka sake ni akwai dubu dake jira na" Ta faɗa da tsananin fushi tana ƙoƙarin buɗe motar yayi saurin saka Luck yadda baza ta iya fita ba yaji zafin kalamanta sosai dan haka shima da son ya ƙular da ita ta yadda ko gaba bazata kuma gigin gaya masa haka ba, Kuma sannan kada ya kwana da baƙin cikin shi kaɗai gwara su raba ya dube ta ido cikin ido yace. "Dama akwai masu jiran ki ni aka liƙa min nifa na ma fidda rai da ke sai kawai aka zo aka ce an bani ke, To ni sai na rabu dake ai wannan mai sauƙi ne kije dubun su aure ki" Ya faɗa yana danne Dariyar shi, sabida yadda ta kumburo fuska kamar fanke duk yadda yaji ɓacin rai sai da dariya tazo masa domin kalaman shi sun dama nata nesa ba kusa ba. Bata da bakin magana sai Hawaye shaaaa! dake zuba a idanun ta kamar famfo ta kuma kafe shi da ido taƙi ɗauke wa yau Asad ke gaya mata haka tashin hankali baƙin ciki fargaba duk su suka rufeta. Ya zaga ta bayanta ya buɗe mata ƙofar motar ya ce. "Sai da safe matar maza dubu" Ya ɗora mata ledar saman cinyarta. Idan tace zatai magana to Zata gaya masa abin da dukkan su zasu yi nadama ne shiyasa ta sauke ledar daga cinyarta ta fice daga motar ko murfin bata rufe masa ba. Yayi dariya yana shafa gemu a fili yace. "Ashe da zafi naga alamun na barki sai kin kassarani gwara nima na nuna miki ɗan fari ne ni na asali ma, Nuri tawa ƴar rigima ta" Da sauri ya ɗauki ledar yabi bayanta sai dai kafin ya kai harta kai bakin ƙofa. Da gudu yabi bayanta. Yana kai wa soron zata shiga tsakar gida malam dake alwala yace. "Nuriyyah ba mijin ke bin bayan ki ba ko abu zai baki" Da matiƙar fushi ta dawo da baya ko arziƙin kallo Asad bai samu ba ya miƙa mata ledar ta amsa fuwww yana sai da safe ina bata ko kula shi ba tai ciki. Sai da yaga ta shiga sannan ya koma sukai sallama da Malam ya nufi mota duk kuma sai ya shiga damuwa na yadda yaga tayi ɗin, Yasan duk cikin soyayyar shine wannan fushin. Haka yaja motar ya tafi kamar marar lafiya ya tabbata Nur ita ce farin cikinsa amman ta kasa fahimtar hakan ko kaɗan. Koda ta shiga ɗakin ma yarda ledar tai ta kifa ciki saman gado tana gursheƙen kuka babu yadda Innah batai da ita ba akan tai shuru taƙi Innah har ta shiga zargin wani abu haka Innah ta tattara ledar da naman da lemon ta aje bata gaya wa Innah zancen kawo kayan lefan ba haka ta kwana washe gari ta tashi jikinta duk babu daɗi fuska ta kumbura. Wajan sha biyun rana kuwa. Kawunan shi yayin Ummi suka kawo lefe akwatuna Shidda da kit sosai malam ya shiga kiran su Baba Usman da Ya Auwalu sabida ba shirin amsar lefan haka dai aka haɗu aka fita kunyar juna suka tafi malam ya sa aka shigo da kayan wanda Nan da nan maƙota suka soma zuwa ganin kayan masu kyau da tsada. Ko kallo kayan basu isheta ba Hatta naman bata ciba su Innah ne suka ci gaba ɗaya Innah ta kasa gane kan Nuriyyah kamar mai iskoki da magariba Ya Jidu ya shigo yana cewa Ga Asad yazo yana kiran Nuriyyah aikwa tace babu inda zata je babu yadda ba'ai da ita ba taƙi zuwa. Maryam ce ta fita tana dariya tace. "Alhaji Asad daga gani wannan family issue ne madam tace baza ta zo ba" Yayi murmushi tare da miƙowa Maryam leda. "Ga kayanta kice wa Mama ƙarfe uku ne Yinin daga nan kuma za'a wuce da ita ɗakinta za'a kawo motocin da za'a ɗauki mutane anan sharaɗa ne wajan Yinin Royal Event Center" Maryam ta amsa tai masa godiya sannan ya wuce gidan su Aysha dan ya kai mata nata. Dama babu wata matsala dan gane da kayan ɗaki domin tuni ya sanar da malam baya buƙata Aysha ce tace ita tana buƙatar ganin kayanta dan haka ya ce ta saka kujeru a falon shine ƴan uwanta sukaje suka haɗa babban falon da kayan Aysha a ciki. amman komai na gida ya gama zubawa tunda harka ce ta kuɗi. Haka zalika maganar matakin Jini genotype Aysha A'A ce kamar yadda ta turo masa ta wayarsa a watsapp, shima A'A ne, Nuriyyah ce bai sani ba tunda basu yi maganar ba. Lokacin da Maryam ta kai kayan Nur ko kallon su batai ba sai da Innah tai mata da gaske sannan ta gwada tana kuka. "Nina rasa wannan jaraba taki ya aure kin ma kin hana zuciyarki sakat To maza kije ki masa rashin albarka ya kore ki sai aji daɗin yi mana dariya a unguwa kuma maganar Tariya ba fashi Allah ya kaimu goben maryam maza gayawa Baba maganar yinin a gaggayawa dangi" Haka Nuriyyah taita tura bakinta gaba Duk bidirin da ake bata tanka ba. Duk hankalin Asad yana kan Nur koda yaje gidan su Aysha ma bai jima ba yayo gida anan yake jin Goben daga wajan Yinin Ummi zasu yi Dinner wadda suka shirya ƙarfe shaɗayan dare daga wajan Dinner ɗin za'a kawota wadda kuma ta buƙaci yaje tunda ƙarfe uku zuwa shida na yamma za'a gama na ummin suna da lokaci sosai. Haka ya dawo gida. Yana idar da sallah ya kuma komawa gidan su Nuriyyah. Wannan karon ma da ciwon kai ya koma gida domin daya aika yace tazo sabida ƙofar gidan ba kowa Malam baya nan sai ya sami yaro ya aika aikwa sai ta faki Idon Innah tace wa yaron yaje yace masa Idan shi maye ne ya cinye ta ɗanya baza ta zo ba. Shine yaron yaje ya gaya masa wannan takaicin baƙar maganar shiya haifar masa da zazzafan ciwon kai haka ya koma gida cikin ƙunci............... *Littafin FITAR RABO na kuɗi ne akan farashi mai sauƙi domin biyan kuɗin zaki tura naira 300 ta wannan asusun bankin 0078174806 sterling bank shedar biya ta 08142105218, idan kuma card ne mtn card na 400, zuwa wannan number 08142105218*"Modibbo darasi da daddare" ya ɗauke Idanunsa domin maganar ma a wahale yake yinta, bai taɓa jin tsananin azaba irin wannan ba. Bai kuma taɓa tsintar kansa cikin sabon yanayin nan mai wahalar fassaruwa a baki ba. Shi dai yasan tabbas akwai abin da yake buƙata kuma a wajan Ƴar tashi kuma ƴar rainon shi yake buƙatar abun nan. Ita tafi dacewa da kuma cancantar samun shi. Sbd ita yake adana dukkan abin da ya shafi girma da ƙimar wannan al'amarin. Dalilinta ya mayar da kansa tamkar nakashasshe wanda bai san daɗin lamarin ma. "Yaa Sheikh ni ba zan gane darasin nan ba, barci zan" yana buɗe gaban mota ya ce. "Yanzu ne lokacin ganewa ƴar fillo, darasin mai sauƙi ne sai wahala" "To Abbana" ta ce tana maida idanunta tare da yin shiru. Yaa Sheikh bai iya ajjiyeta ba domin gani yake raba gangar jikin nasu kamar rabuwa da numfashinsa ne. A haka ya zauna ɓangaren driver bakinsu ɗauke da addu'a ya yi wa motar key tare da nufar gate. Gatekeeper ya buɗe masa daman ba wani barci yake sosai ba, rabon da Yaa Sheikh ya ya yi driving da kansa a ƙasar ta makka shi kansa ba zai iya faɗar adadin shekarun ba. Kai tsaye ya cilla motar saman titi tare da nufar haɗaɗɗan gidansa wanda muhimmun abu kawai k kai shi. Ummul dake tsaye ta saki labulan window tana sauke numfashi, zuciyarta cike da zullumi tasan Yaa Sheikh ba zai taɓa cutar da Halisa ba, amma fargaba ya kamata sosai. Ta juya zuwa parlour inda Zahrah ke kiranta. "Naje part nasa baya nan,ina ya fita" Ummul ta ɗauke kai cike da mmkin ƙarfin hali irin na Zahrah kana son miji kana son kasancewa dashi amma bata san hanyar kulawa da kyautata masa ba? Anya rayuwa zata tafi haka? Wani bokan ma sam bashi da amfani. "Da alama ya fita ne" a ruɗe Zahrah ta dubi Ummul cikin tashin hankali mara misaltuwa ta ce "Ya fita? zuwa ina bangane fita ba" Ummul zata juya zuwa cikin bedroom Zahrah tayi saurin fisgota cikin ƙara ji ta ce "Ina magana kina sharewa? Kin san halin da nakr ciki i want my husband, i want to sleep on his arms" da ɗinbun mamaki Ummul ke kallon Zahrah kafin ta ce. "Ya kike so? kike bedroom nasa ki kira" kau!! Zahrah ta ɗauke Ummul da mari tana nunata da hannu ta ce. "Ke awa? ko a gidan ubana ban ɗauki rainin hankalin masu aiki ba, balle gidan mijina ina magana kina bani banzar amsa kamar kina magana da sa'arki? Ko an faɗa miki sa'ar uwarki ce ni?" Ummul ta dafe kuncinta wanda zanan yatsun Zahrah ya fito rau! a kansu idanunta ya cika da hawaye ta ce. "Nayi miki uzuri rashin sani, a lokacin da zaki wace ni da matsayina a lokacin zan nuna miki irin ƙarfin nawa ikon" Zahrah ya cakumo wuyan Ummul ta ce. "Zaki faɗa mini inda mijina yake ko sai na illata rayuwarki? Ko kece uwar shi Maryam wallahi baki isa ki shiga tsakanina da mijina ba, a duk inda yake mace yake buƙata ki faɗa mini ina mijina yake zan bisa zuwa duk inda yake am warning you" "Waje mai muhimmaci, tare da abu mafi muhimmanci a rayuwar shi, kije kiyi tunani" Ummul na faɗin haka ta juya zuciyarta fal takaicin yadda bata da ikon rama cin zarafin da yarinyar tai mata. Tai ƙwafa tana rufe ƙofar. Zahrah ta zama kamar mahaukaciya domin raba maganin biyu tayi,ta sakawa Yaa Sheikh rabi, ta shanye rabi. Ga masifar da take ji na neman kassara rayuwarta ba zata iya jurewa ba. Kamar zautacciyya ta nufi ɓangaren Halisa ta dinga ƙwala mata kira amma babu ita babu labarinta ƙirjinta ya yi mummunan bugawa wani gurɓataccen tunani ya shiga kaiwa kwakwalwarta farmaki. "Yaa Sheikh, Halisa?" Ta furta a fili da ƙarfi ta ce "No! Wallahi zan iya kashe mace akan mijina" ɓangarenta ta koma tana kiran Deen idanunta ya a gama juyewa yana ɗagawa ta ce "kana ina? I need you right now" ya kalli Balarabiyyar dake maƙale dashi ya ce. "Ina hotel,ya kai?" Ta sauke numfashi ta ce "Akwai matsala Deen" "daman matsala kullum cikinta ki ke tunda baki da kyakkyawan tunani" bata tsaya bi ta kan maganar shi ba, ta zayyana masa yadda akai ta ɗora da faɗin. "Ban san haka maganin yake da ƙarfi ba, ina jin kamar naci babu kayi mini kazo gidana" Deen ya yi shiru yana juya tunaninta a ma'auni na hankali ya ce. "Yaa Sheikh ba zan bi macan banza ba, kuma ba zai iya jurewa yanayin ba, dole akwai wani abu a ƙasa, akwai abin dake faruwa,mene shi?" Ya faɗa yana ture matar dake jikinsa tunaninsa ya rabu gida biyu. "Na kasa fahimta, kai na ya kulle Deen ka bani haske" da sauri ya ce "Yaa Sheikh nada zubin halittar da babu mai gano abin da yake shiryawa, something is fishy" Zahrah ta ce "Gani nan zuwa" ya ce "Okey" cikin mintuna kaɗan ta shirya jikinta duk rawar yake tana zuwa ta cewa mai gadi ya buɗe mata. "Hajiya ina zaki dare ya yi?" Taja tsaki ta ce "Ka haifi ne? aikin ka ne kayi kawai" zai ƙara magana ta daka masa tsawa ta ce. "Banza shasha! dallah buɗe mini kafin na saka a kore ka" ya buɗe mata ƙofa tare da ɗaga hannu ya ce "A sauka lafiya Hajiya". Tun daga nesa Yaa Sheikh yake danna horn har zuwa gaban makaken gate ɗin gidan nasa, aka wangale gate ɗin kai tsaye ya tura hancin motar ciki ikon Allah ne kuma ya kawo shi gidan, a lokacin ya gama galabaita idanunsa da ƙyar yake buɗewa. A hankali ya yi parking a harabar ajjiye motoci kusan rabin motocin daya mallaka a ƙasar Madina suna cikin gidan. Ya sauke numfashi tare da buɗe gajiyayyun Idanunsa wanda suke nuna zallar abin da yake buƙata. Cikin magagin barci Halisa ta buɗe ido tare da saka hannu ta shafa fuskarsa ta ce. "Abbana baka da lafiya ne?" Ya buɗe ido a hankali tare da zubuwa akan fuskarta. Ganin da gaske baya jin daɗi yasa ta mustsike idanun gabanta na faduwar ta gyara zama a jikinta tana tattaɓa fuskar shi ta ce. "Abbana kayi magana, meke maka ciwo" ya damƙi kafaɗarta kamar zai raba ƙashinta gida biyu, cikin raunatacciyyar murya a karo na farko wacce ya bayyana rauninsa ya ce. "Bani da lafiya Ƴar fillo" idanuna ya cika da ƙwalla ta ce "Abba kuma ba magani" ya tallafo fuskarta idanunsa kamar an kaɗa gauta ya ce. "Ke ce maganin ciwon Abbanki" da sauri ta ce "To ina maganin yake a wajena?" Bai iya magana ba sai manna fuskar shi ya yi da nata yana sauke zazzafan numfashi. "Kiss me, just kiss my lips" ya faɗa murya can ƙasa yana ƙara riƙe fuskarta da kyau. Haka kurum tsoro ya kamata amma idan har hakan zai zama magani ga ciwon Modibbonta dole tayi. Slowly cike da nutsuwa ta ɗora bakinta. She started kissing his mouth in a different style, cikin mintuna kaɗan ta ƙara gigita Abban nata, Yaa Sheikh numfashi kawai yake saukewa. A hankali ya miƙa hannu ya kashe hasken motar tare da yin baya da kujerar da suke kai a hankali ya mirginata yana rufe fuskar shi a wuyanta wani irin abu yake ji na fisgar shi, kamar ana jansa da mayen ƙarfe. Kyakkyawar matsar da ya yiwa ƙirjinta yana ɗora kansa a wajan yasa ta fara numfashi yatsun shi a kanta jikinsa duk rawa yake ya zama kamar ba Yaa Sheikh ba, ya ajjiye malunta da rainon ƴar ta shi a gefe. "Ya Rasulullahi manzon Allah, Ya Rahmanu ya mujibud-da'awati" ya faɗa a fiye jin yadda Halisa ta kafa bakinta a nasa ƙirjin kamar yadda ya yi mata, Just like a mother breastfeeds her child. Yaa Sheikh ya birkice da salon Halisa duk yadda yasu riƙe kansa da hana bakinsa magana ya kasa, da sauri ya ɗakkota ba tare daya rufe motar ba, kai tsaye ya haura upstairs. Yana shiga ya sauketa a gado tare da kashe gaba ɗaya hasken ɗakin. Ihu! Halisa ta kurma jin abin da ba tayi zata ba, cikin sauri ta zille tana cewa. "Wallahi Abbana bana son darasin ba zan iya ba, mutuwa zan wallahi ban so" duk inda ya bita sai ta zille ya durƙushe a tsakiyar bedroom ɗin yana rufe jikinsa da duvet. Wani irin tausayinsa ya kamata irin tausayin mata zuwa ga mijinta ta ƙarasa wajansa tana shigewa duvet ɗin ya haɗa da ita ya matse a jikinsa cikin ƙasa da murya ya ce. "Ban son ki fara da zunubi kiji tausayin Abbanki, mace ta ƙwarai nagartacciya bata nesa da mijinta kinji Matar Malam" ta ɗaga masa kai ta ce. "Malam darasin da wahala" ya shafa kanta yana sumbatar goshinta ya ce "Matar Malam zama Jaruma" ta rungume shi sosai tana jin wani irin abu da yake mata anan suka shimfiɗe tsoro duk ya cika zuciyar Danejo. Abin da Yaa Sheikh yaji yasa ya tsaya yana kallonta a sanyaye kamar zai saki kuka yana marairaice fuska ya ce. "Yaushe wannan abun yazo?" Ta kalli idanunsa ta ce "Yau, Ummul ta ce kada na faɗa maka amma daman zan faɗa" ya kifa kansa a jikinta yana sauke numfashi. Sam ba haka yasu ba amma ya ya zai yanzu. Ya miƙe tare da ita ya kwantar da ita cikin dabara ya nuna mata sabon darasin da yake so ta ɗoro akai a duk sanda take al'ada. Lokacin da yaji daidai ya rungometa jikinsa na rawa, ya ɗora hannunsa a goshinsa ya ce. "ALLAHUMMA INNY AS'ALUKA MIN KHAIRIHA WA KHAIRI MA JABALTAHA ALAYYA.WA A'UZU BIKA MIN SHARRIHA WA SHARRI MA JABALTAHA ALAYYA, Ya Allah ka kula mini da ita, ka sanya albarka a iyalina" ya ƙara sumbatar goshinta bisa sunna ya ce "Rabbi ya yi miki Albarka Ƴar Aljanna" ta kallesa da kyau bakinta na rawa ta ce "Abba kaga me na gani kowa?" Ya rufe bakin ya ce. "Shahh, Al'amarin aure ne" ya zame jikinsa har lokacin bai dawo daidai ba, tabi shi da idanu. Ya ɗauki lokacin kafin ya fito fuska a ɗan kame gudun surutun nata amma duk da haka sai ta miƙe zaune ta ce "Wankan Janaba kayi Abba?........ *Idan kana buƙatar posting har weekend wani time ɗin sau biyu a rana. Zaka biya 1k... Idan ka riga ka biya 500 zaka ƙara adding 500 a saka ka cikin Special grp 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman fidelity bank shaidar biya 08119237616."Ga Yaa Lee muna tare da shi, yaushe yazo ya ɗauki Halisa?" Headmaster ya goge zufar dake bin fuskarsa al'amarin ya fara bashi tsoro ya ce. "Wallahi ina faɗa maka, yanzu ka shigo ka tafi da ita, har kana ce mini ya karatun nata, kuma sai ka dawo kace tana ina?" Yaa Sheikh ya yi shiru. "Wani irin murɗaɗɗen abune, ba dai Yaa Sheikh yazo ba, sai dai wani kai kuma baka duba ba" "Ta ya ya za kai mini musu? bayan muna da cct.v Camera yanzu sai na duba maka" Umar-khan ya ce "Muje, amma da sake" Yaa Sheikh ya ɗaga kansa sama a hankali cikin sauyawar murya ya ce. "Na fahimta,muje" Umar-khan zai magana Yaa Sheikh ya ɗaga masa hannu alamar ya yi shiru. Tunda suka ɗauki hanya Yaa Sheikh ya kasa samu damar yin cikakken tunani. "Waye?" Ya furta a zuciyarsa ya ɗauka tuntuni ya magance wannan matsalar ashe ya kashe maciji bai sare kansa bane. Yanzu kuma ya yi girman da idan ya ce zai raba shi da ita babbar matsala ce. Duk da bashi da cikakken hujja akan abin da ƙwaƙwalwarsa take faɗa,amma zuciyarsa na son gaskata hakan. Har suka iso gida Yaa Sheikh bai san sun ƙarasu ba. Sai da Umar-khan ya ce. "Lafiya kake dai?" Ya kame fuska tare da saukowa sai da ya yi nisa ya tsaya ya ce. "Ka nemi abin faɗa" Umar-khan ya ce "Kada ka damu da hakan" bai bari ya shiga ta asalin ƙofar gidan ba, ya ratsa da bayan gidan ya shiga sashinsa. Umar-khan na shiga ya samu El-bashir da Mai martaba Ahmad Sarki zaune suna hira sama-sama Ummul ta cika musu gabansu da kayan cima kala-kala. "Ina Aliyun fa?" Umar-khan ya zauna cikin matartabawa ya ce "Yana ɓangaren shi,baya jin daɗi" Ummul ta ajjiye plate na hannuna ta ce. "Halisa fa?" Ya ce "Tana makaranta" Ta kallesa alamar bata fahimta ba ya ce. "Tana ɗaya daga cikin yaran da aka zama masu ƙwazo, wanda za ai quiz dasu, an riƙe ta zuwa kwana biyu dan bata huro" Ummul ta ce "Something fishy" maganar ta tsaya iya ranta, ta san babu hujjar da zata sanya Yaa Sheikh yabar Halisa a wani wajan har tsayin kwana biyu, dole akwai abin da yake ba daidai ba. Ko yini ya yi bai ji motsinta ba, ba zai tambayi ina take ba, amma daya fito Main parlour tasan neman lafiyarta yake son ji, da rashin jin motsinta. Tai murmushi kawai ta ce. "Ah ba shakka, Allah ya bada sa a" Umar-khan ya ce "Amin" "Umar-khan ya batun Companyn Sarrafa shinkafa na Aliyu?" Umar ya ɗan kalli El-bashir da yake danna waya hannunsa riƙe da Apple yana sha ya ce "Allah ya taimaki Mai martaba, komai lafiya yake cikin yarda da amincin Ubangiji" Mai martaba ya sauke numfashi yana jinjina kai kafin ya ce. "Ina son Mota guda da za a rabawa jama'a na kyautar Ramadan, waye manager na Companyn?" Kan Umar a ƙasa sbd nuna girmamawa ya ce "Yarima Khalil Ahmad Sarki shi ne Manager na Companyn Sarrafa shinkafa na Yaa Sheikh" El-bashir ya ɗago kai da sauri jin abin da Umar ya ce, wato Yaa Sheikh ba ƙaramin kai wayo bane, kamar yana da sanin cewa za a iya yi masa sharri cikin kayan da yake kawowa, shi ne ya saka Khalil matsayin Manager ya san cewa El-bashir ba zai taɓa cutar da Khalil ba, dukkan abin da ya faru za a alaƙanta shi da Khalil tunda da saka hannunsa komai ke tafiya. "Ikon Allah, bani da labari zanwa Khalil ɗin magana" Mai martaba ya miƙe tsaye domin ziraya yake son ya fara kaiwa tun kafin watan Ramadan ɗin ya fara, zuciyarsa har yanzu ta kasa yarda da ƙaddarar data faɗa masa gani yake kamar akwai wani abu dake shirin faruwa. El-bashir ya miƙe tsaye tare da bin bayan mahaifinsa har zuwa harabar gidan Yaa Sheikh suka shiga mota. Yaa Sheikh ne zaune gaban Alƙibila hannunsa riƙe da ƙaton Alkur'ani gaba ɗaya ya rufe fuskarsa karatu yake cikin suratul Yaásin, ɗakin baki ɗaya yai duhu sai zoben dake hannunsa ne kawai yake bada haske mai kyau. Ya yi nisa sosai cikin karatun yaji ɗakin ya fara girgiza wata ƙaramar ƙara ta fara cika ko'ina na ɗakin. Cikin murya mara daɗin saurare aka shiga faɗin. "Laifinka ne, laifinka ne, laifinka ne" Yaa Sheikh ya saurara da karatun da yake tare da sauke numfashi ajajjere kwana biyu abu na neman fin ƙarfinsa, Shikenan ba dama ya karanta suratul Yaásin sai su bayyana kamar dai ya kirasu, sun nace sai sun zauna tare dashi amma me yasa yanzu suke neman takura masa duk da sharuɗan daya kafa musu?. Ya buɗe fuskarsa yana ƙara gyara zaman shi ba tare daya saurari abin da suke cewa ba. Abin da ke magana ya bayyana a suffar wata baƙar mage mai manyan idanu. Can nesa da Yaa Sheikh taja ta tsaya ta ce. "Ba zai taɓa rabuwa da matarka ba, indai baka mayar da ita cikakkiyar mace ba, ka halakta auren dake tsakaninku, kasancewar ku tare da kuma mai da ita babbar mace kamar ko wacce matar aure shi ne zai kawo ƙarshen shi, a ranar da kuka zama ma'aurata a ranar komai nasa ya ƙare" Yaa Sheikh ya miƙe tsaye yana son barin ɗakin don yasa abin da ya daɗe bai tasar masa ba yana gab da tashi, kafin ya fita magen tai tsalle ta hau saman wuyan shi bakinta na wani irin hayaƙi ta ce. "A shirye yake, a shirye yake, a shirye yake, kawo yanzu muma bamu san inda ya kaita ba" a fusace kamar wanda ya samu juyewar tunani haka Yaa Sheikh ya damƙi magen bakinsa ɗauke da addu'a ya bugata da jikin bango, a tare suka saki ihu ita da Yaa Sheikh sai dai nasa ihun yana da banbanci da nata, shi mai ɗauke da kiran sunan Ubangiji ne, ita kuma ji tayi kamar Yaa Sheikh ya zuba mata dalma a jiki. Cikin gilmawar haske a cikin duhu haka magen ta ɓace ɓat, Yaa Sheikh kuma ya sulale a tsakiyar carpet ɗin bedroom ɗinsa, tare da ɗaukan hiraminsa ya naɗa wani rawani mai masifar kyau a kansa, a nutse ya harɗe ƙafafuwansa kamar wanda yake tsakiyar fada zaune akan karagar mulki. Ilahirin fuskarsa zufa ce take yankowa kansa a ƙasa ya ɗora hannunsa saman cinyoyinsa. Zuwan Ummul huɗu sashin Yaa Sheikh tana samunsa a rufe, yanzu ma tana tsaye a zuwa na biyar tana mmkin abin da ya hana Yaa Sheikh fitowa tasan kuma azumi yake tunda yau Alhamis ne. Ta duba lokaci taga lokacin sallar Asr ta kusa kuma shi ne zai ja jam'i ta shiga bubbuga ƙofar amma taƙi buɗewa. Cike da damuwa ta juyawa daidai lokacin kuma Mai martaba Ahmad Sarki da Umar-khan suka shigo Parlour ganin yanayin Ummul yasa Umar-khan cewa. "Yaa Lee?" Da sauri ya ƙarasa wajan ƙofar yana tambayar Ummul "Lafiya mene ya samu Yaa Lee?" Ta girgiza kai ta ce "Kawo yanzu ban sani ba, amma nasan dole akwai abin da ke faruwa aciki" Umar-khan ya ciro key ɗin sashin na Yaa Sheikh jikinsa na rawa ya fara buɗewa, ƙofar na buɗewa Ummul ta ce. "Tsaya a nan Umar, ganinka zai sanya yaƙi kulamu" Ya tsaya yana addu'ar Allah yasa lafiya. A hankali Ummul ta shiga baya parlour kai tsaye ta nufi cikin bedroom ɗinsa idanunta ya sauka akan shi zaune tsakiyar parlour, hakan kaɗai ya isa ya zama hujja da zai sanya Ummul tasan yau fa ba iya Yaa Sheikh bane, hadda sarakunan da suke bibiyar rayuwar shi. "Aliyu, Aliyu!" Ta faɗa tana bubbuga kafaɗar shi, bai kalleta ba bai kuma motsa ba a fili ta ce. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Wanne abu ne haka Aliyu kake gani a rayuwarka daga wannan sai wannan" ta saki kuka tana juyawa. Mai martaba bai ce mata komai ba yabi gefenta ya shige bedroom ɗin Yaa Sheikh. A rikice Umar ya ce "Ummul lafiya? Me ya samu Aliyun naki?" Ummul hawayenta yaƙi tsayawa cikin shassheƙar kuka ta ce. "Umar-khan na gaji, wallahi na gaji ina tunanin lokaci ya yi da kowa zai san abin da ke faruwa, ba zan jure ganin halin da Aliyu ke shiga ba, kasan cewa wani lokacin ki barci bama yi idan hakan ta faru? Mene yasa duk ƙarfin ilimi da sanin da ubangiji ya bawa Aliyu Aljanu ke bibiyar shi ne?" Umar-khan ya goge zufa ya ce. "Kiyi addu'a Ummul, ita yake buƙata daga gareki kada ki zubar da hawaye azabace a gare shi, kowa da zanan ƙaddarar shi, Yaa Sheikh kalar tasa kenan, mu gode Allah da iya abin yake tsayawa, kuma da yawan malamai zai wahala ki same su, su kaɗai" Ta goge idanunta ta ce. "Shikenan, amma Umar ka faɗa mini gaskiyar abin da yake faruwa, ruwa baya tsami banza" ya kalli ko'ina kafin ya ce. "Munje makarantar su matar malam ance wani mai kama da Yaa Sheikh ya zo ya tafi da ita, na ƙaryata Headmaster ɗin ya ce muje ya nuna mini CCTV camera amma Yaa Sheikh ya ce a'a ya fahimci komai, Halisa missing" murmushi kawai Ummul tayi ta ce "Na sani daman, ba haka kurum bane wallahi duk ranar da Aliyu ya rasa Halisa a rayuwar shi ka tabbatar za a ɗauki gawar shi ne" baki buɗe Umar-khan ya ce. "But baya son ta ai, zuwa yanzu na fahimci da gaske Yaa Sheikh baya son Halisa" Ummul ba tai magana ba ta juya zuwa ɓangarenta, Umar-khan kuma ya shiga cikin part ɗin Yaa Sheikh amma ya tsaya iya parlour. El-bashir ya saki murmushi yana sauke numfashi gabaɗaya conversation ɗin Ummul da Umar-khan a kunnensa. Idan har rashin Halisa zai iya ajalin Yaa Sheikh me ya sa yake wahalar da kansa, idan ya raba Halisa da duniyar ba shikenan ba?. "Yaa Sheikh ka gama yawo" ya furta a fili. Juyawar da zai suka haɗa idanu da Zahrah wacce ta fito sanye da wasu shegun kaya, suka kalli juna. Ganin ta nemi waje ta zauna yasa El-bashir ya sauke ɓoyayyiyar Ajjiya, sai da hantar cikin El-bashir ta kaɗa saboda tsananin tsoro daya shiga. Tunaninsa ya tsaya na wani lokaci domin zaton shi Zahrah taji abin daya faɗa sai yaga saɓanin haka. Shima ya zauna idanunsa akan t.v kamar daga sama yaji ta ce. "Kana da alaƙa da Halisa ne?" "Me ya sa zan samu alaƙa da ƴar uwarki?" Zahrah tai murmushi ta ce "Ba ƴar uwata bace, kamanninku sun ɓaci" ya taɓe baki ba tare daya damu da tace ba ƴar-uwarta ba ce. Ta miƙe tare da nufar wajan Training ko cikinta zai sace daga kumburin da ya yi mata, ita kumburin har tsoro ya bata. Mai martaba ya kalli Yaa Sheikh daya miƙe tsaye sai kuma ya juya ya kalli Abba Hakimi dake kan screen suna vedio call ya ce "Ina ganin komai ya yi daidai" Abba Hakimi ya rufe Kur'anin gabansa shi kaɗai yake iya daidaita hargitsin na Yaa Sheikh kafin ya ce. "Ina tunanin lokacin da Aliyu zai dawo kusa dani har abada ya yi, banga me yake a Madina ba, shi ba uwa ba, shi ba Uba ba balle ƴan uwa a can ɗin ba, na rasa me ya liƙewa a can ɗin" Mai martaba ya ce. "Abi komai a sannu, komai zai shige" Sallama sukai Mai martaba ganin babu Yaa Sheikh a bedroom ɗin ya nufi hanyar fita. A hankali take buɗe idanunta wanda ya yi mata nauyi sosai tare da kallon inda take wani ƙaramin ɗaki ne amma mai kyau da tsari ta yunƙura kaɗan tana jin kanta na sarawa. "Kin farka matata?" Tunaninta ya tsaya tunda take Abbanta bai taɓa cewa matata ba, kenan ya yarda yanzu ita matar shi ce. Ta juya hannunta dafe da kanta sukai idanu huɗu, yana tsaye a cikin kyakkyawar shigar shi kamar kullum sai dai a wannan karan Jallabiyar duka ta rufe masa ƙafa ta buɗe baki da ƙyar ta ce. "Abba, ina ne nan kuma?" Prince Bilal wanda ya yi suffar Yaa Sheikh sak ya ƙara su inda take yana kama hannunta ya ce. "Sabon gida mukai Danejo matata, yadda zan samu damar kasancewa dake muyi soyayya sosai" ta kalle shi ya akai yau Abban nata yake sakin zance ba dadin ita yau ba darasi sai soyayya ta ce. "Zanyi wanka Abba, jinin ya tsaya" Bilal ya ce "Jini? Shikenan an gama dani" bata gane zancan nasa ba, ta nufi bathroom tai wanka duk abin da Ummul ta faɗa tayi ta fito ɗaure da towel Bilal ya dinga kallonta ya kama hannunta zai rungometa yaji kamar an buga masa guduma a kai ya saketa da sauri yana faɗin. "Da akwai wani abu a jikin ki, maza cire" Halisa ta dinga duba jikinta amma ba taga komai ba ta ce "Abba ba komai, wai Abbana meya sameka?" Ta faɗa tana shigewa jikinsa Bilal ta birkice ko ya ya Halisa ta taɓa shi masifa ya keji. Ya cireta yana cewa "Lafiya nake shirya kiga" tai murmushi tana cewa "Ko wanka ne baka son kayi ne?" Ya yi mata shiru tare da ɗauke kai domin ya fara riƙiɗewa kamar Aljani. Ta shirya cikin kayan daya bata tai sallah duk a ɗakin. Dare nayi ya bata abinci taci kaɗan kamar wacce tasan meke faruwa sai bata ƙara zuwa inda yake ba, Bilal kuma ya wanzu yana bin jikinta da kallo ko zai gano abin da yake masa shamaki da ita. Cikin dare Yaa Sheikh ya kasa barci duk inda yake tunanin zai ga matar Malam babu ita. Wajan uku na dare ya fito direct ɓangaren Ummul ya nufa kamar tasan zai zo ƙofar a buɗe take, tana zaune saman ladduma taji ƙamshin Roja ta kallesa taga ya kalleta shima ta ɗauka zai je saman kujera sai taga kai tsaye ya dawo kusa da ita ya zauna, bai ce komai ba ya ɗora kansa a cinyarta ya dinga sauke ajjiyar zuciya. Abu kamar wasa har ana igobe ɗaukan azumi babu Halisa, babu wanda yasan halin da ake ciki na rigimar Yaa Sheikh sai Ummul, Zahrah ko a jikinta. Da sassafe Yaa Sheikh ya fita Zahrah kuma ta shiga ɗakin Ummul tana zuwa ta ce "Ki faɗa mini abin da yake faruwa da mijina da baya son raɓar inda nake" Ummul tai shiru Zahrah ta ce "Wallahi munafuka ce ke kin san komai ki faɗa mini abin da zan yi mijina ya raɓeni" Ummul tai murmushi ta ce "Tausayi ki ke bani, naga har yanzu kin kasa fahimtar waye Aliyu kin kasa gane cewa shi ba cikakken namiji bane, shiyasa aka auren haɗi tsakanin ke da Aliyu" gaban Zahrah ya faɗi ta ce "Kina nufin Yaa Sheikh bashi da lafiya?" Ummul ta ce "Ba a faɗa miki bane daman? Aliyu ai ba zai taɓa iya tarayya da mace ba, likitoci sun tabbatar da haka, zaman ibada zaki da kulawa da shi" Zahrah ta ƙunduma wani zagi tare da yin waje wayarta ta ɗauka ta shiga kiran number Father ringing ɗin farko aka ɗauka Father ya ce. "My daughter ya ki ke?" Cikin rashin ladabi Zahrah ta ce "Ban san ya nake ba, ashe kasan cewa ɗanka Aliyu nakashasshe ne bashi da lafiyar tarayya da mace shine kasa mukai aure?.... Paid book 500 08119237616*"Kada ka kusantar mini mata, zan illataka na illata Ahhalinka Malam" Yaa Sheikh bai saurari maganar da Bilal yake ba, idanunsa akan fuskar Halisa wacce jikinta ke rawa tsoro ya kamata kallo ɗaya zakai mata kasan cewa ta gama firgita da abin da yake faruwa. Ƙirjinta na ɗagawa sosai numfashinta nayin sama hakan yasa Yaa Sheikh ƙara shigar da ita jikinsa da kyau yana mai zame bakinsa daga nata sbd ganin Bilal ya gama haukacewa ihu yake da kururuwa wanda Yaa Sheikh da Halisa ne kawai ke jin haka. "Ban son cutar da wata halitta ta ubangiji,, meyasa ka zaɓi cutar dani?" Bilal ya buɗe tangamemen bakinsa ya ce "Kai ne ka fara cutar dani, me ya sa zaka rabani da wacce na saba da ita? na wanzu ina rayuwa a jikinta, rana tsaka kayi mini kutse ka rabani ruhi da gangar jikina dana sahibar zuciyata" Ya faɗa yana ƙara sautin kukansa yana cewa. "Matata, matata yake matata kizo gareni, na wanzu ina son uwa yanzu na dawo kan ƴa shi ne za a rabamu, zan rasa jin daɗi kwanciyar hankali idan bake Danejo, kada ki bari ya yi ajalina" Ta ɗago kanta tana son fitowa daga cikin Alkyabbar Yaa Sheikh ya yi saurin mayar da kan ya haɗa da ƙirjinsa wanda gaban Jallabiyar ya ɗan buɗe kaɗan sai kwantacciyyar sumar wajan da tayi luf. "Abba me ya sa muryarka ke rabuwa gida biyu? Me ya sa kake kuka?" Ya matseta a jikinsa sosai hannunsa guda ɗaya yana shafa kanta. Cikin nutsuwa ba tare daya kalli Bilal ba ya ce. "Dani kai wanda ya fasa, yanzu zan nuna maka ƙarfin ikon Allah, zan ƙonaka da manyan ayoyin Alkur'ani mai girma" yana faɗin hakan ya fara karatu cikin nutsuwa ayoyi masu zafin gaske yake karantawa, Bilal ya birkice cikin ƙaramin lokaci guduwa ta mamaye wajan tare da ƙara da kururuwa. Ƙam! Yaa Sheikh ya rungome matarsa itama ta zagaye hannuwanta ta riƙe ƙugunsa ta ɓoye fuskarta a tsakiyar ƙirjinsa yana jin yadda take sauke masa numfashi mai zafi. "Shikenan naji zan fita, zan tafi zan barta amma kai ma ya zama dole ka rasata kamar yadda na rasata" Yaa Sheikh bai saurara da karatun ba cikin kuka Bilal ya ce. "Ashe zaki iya bari a rabamu? Ni ne mijinki abin son ki nace zaki bani ƴa ƴa da yawa ki tausaya mini" Wani ihu da ƙara Halisa ta fasa jikinta ya saki baki ɗaya tana neman zubewa ƙasa Yaa Sheikh ya yi saurin taro ta tare da saka hannu ya ɗauke ta cak ya mannata da jikinsa. A nan kuma ya nemi Prince Bilal ya rasa sai wani hayaƙi dake fita daga bakin Halisa, ta dinga jijjiga tana kaiwa Yaa Sheikh doka ta ko'ina tana neman ƙwacewa amma ya riƙeta sosai tare da ɗora bakinsa a kunnanta yaci gaba da karatu. "Wallahi zan tafi ka barni haka da raina, yanzu haka ka ƙona mini rabin jikina, zan bar maka mata amma kada ka kusanceta kada ka sadu da matata Danejo" Yaa Sheikh yaja numfashi sbd yadda take son fin ƙarfinsa ya ce. "Ikon Allah ne kawai zai hanani mallakar matata cikin watan Ramadana" tun Halisa ƙara ta dawo kuka sosai a hankali kukan ya fara raguwa can kuma tai hamma tare da yin atishawa ta kwanta jikin Yaa Sheikh barci ya ɗauketa.. Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya shima Yaa Sheikh ya sauke daga ita harshi zufa ke yanko musu ta ko'ina duk da kasancewarsu a saman dutsen Jabal an-Nour ɗin. A hankali ya fara tafiya yana sakkowa ƙasa har ya gama sakkowa da idanu yake bin Umar-khan ba tare da ya ce komai ba. "Mai martaba ya gama zirayar da zai a madina yana son ɗaukan azumi a Makka, yanzu haka yana masaukin da aka bashi, shi da El-bashir, Ummul ta shaida mini zatai aikin hajjin tama biye kuɗin an gama komai" Yaa Sheikh ya jinjina kai tare da shiga bayan motar ya zauna har lokacin yana rungome da ita. Umar-khan ya shiga motar kai tsaye ya nufi wani babban masaukin da aka bawa Yaa Sheikh wanda bashi da nisa da masallacin ka'abah. Sai da sukai nisa Umar-khan ya ce. "Father ya kira, da alama magana ce mai muhimmanci kuma ta shafi Zahrah ya ce dai ka kira shi immediately idan ka dawo" Yaa Sheikh yaja idanunsa ya rufe shi kansa a gajiye yake kuma ya wahala, amma zuciyarsa yanzu ta samu nutsuwa dan dan ba a tantance farin cikin Yaa Sheikh da baƙin cikin Yaa Sheikh shi ya sa ba a iya gane sauyin yanayinsa. Zubin halittar da Ubangiji ya yi masa daban ne dana sauran dukkan Ahhalin gidan nasu. Ya buɗe idanu yana faɗaɗa fuskarsa kamar anyi masa bushara da gidan Aljanna ya kalli fuskar Halisa a hankali ya riƙe tafin hannunta ya haɗa tana shi ya riƙe sosai cikin ƙasa da murya ya ce. "Matar malam mai gayyar aljanu shikenan an gane mini matasan ƙirjin da nake kiwo" "Magana kake?" Cewar Umar-khan Yaa Sheikh ya yi masa banza. A haka suka kawo gidan tun daga nesa yake ɗauke da jami'an tsaro ta ko wacce kusurwa. Umar-khan ya tsaya sbd wani Security daya tsayar da shi cikin harshen larabci ya ce. "I.d card" kafin Umar-khan ya yi magana Yaa Sheikh ya zuge Glasses ɗin ɓangaren da yake zaune ya ɗan leƙo kaɗan, ganin Yaa Sheikh yasa gabaɗaya suka rusuna tare da bashi girma. "Kayi haƙuri daman an shaida mana idan ba kai ba kada mubar kowa ya shigo duk zaman jiran zuwanka muke" Ya jinjina musu tare da komawa ya jingina da jikin kujerar yana zuge Glasses ɗin sama. Aka buɗe musu gate suka shiga har gaban ƙofar da zata kai mutum zuwa parlourn daya ya raba parts ɗin gidan Umar-khan ya tsaya, bai ƙoƙarin fitowa ba ya fara danna wayarsa. Yaa Sheikh ya buɗe ƙofar tare da ɗan dubawa yaga babu mutane wajan a hankali ya fito yana naɗeta baki ɗaya da Alkyabba ko fuskarta ba a gani, a wannan lokacin ya ƙwammace a kalli surar jikinsa wacce take shekara da shekaru a lullube da dai a kallin sirrinsa. Ya nufi ƙofa yana shiga direct ɓangaren da yafi kwanciya a ransa ya nufa can Upstairs yana shiga ya kulle ƙofar ya nufi bed ya zauna yana zare Alkyabbar ya rage daga ita sai ƴar rigar dake jikinta wacce Bilal yasa mata. Ya kama hannunta ya zare zoben hannunta mai ɗauke da tambarin masarauta, sai yanzu ya lura babu baƙin zaren daya ɗaura mata. "Matar mutum da Aljani" ya faɗa a taushashe yana zaunar da ita saman cinyarsa amma har lokacin barci take,yasan tana buƙatar barcin a yanzu ya kwantar da ita tare da rufe mata jikinta har ya juya ya dawo ya ɗan ranƙwafa daidai kanta ya sumbaci goshinta kana ya juya yana gyara zaman alkyabbar jikinsa tare da ɗaukan hiraminsa. Sakkowa yake daga saman strais ɗin benen yana gama sakkowa ya zauna saman kujera, Umar-khan ya ce. "Na manta ban faɗa maka ba, an gama komai na aikin hajjin Hali.....," Kallon da Yaa Sheikh ya yi wa Umar-khan yasa ya haɗiye maganar can ya ce. "Na matar malam, komai ya zama ready" Yaa Sheikh ya miƙe tsaye tare da juyawa sai da yaje ƙarshen benen ya ce. "A shaidawa Ummul muna nan, tare da Zahrah" Umar ya ce "In shaa Allah" Umar ya fita. Wanka Yaa Sheikh ya yi ya sauya kaya masu kyau na shan iska, idanunsa har rufewa yake sbd gajiya yana buƙatar nutsuwa sosai bayan ya kunna karatun Alkur'ani ya kwanta gefe guda yana rufe jikinsa kamar wacce tasan yana wajan ta gangaro tare da shigewa jikinsa, suka sauke numfashi lokaci guda. Wata kasalalliyyar ajjiyar zuciya ya sauke yana mai matse idanunsa wanda suke a lumshe, tsananin mamaki da kuma tarin al'ajabi ya sanya Yaa Sheikh fesar da wata zazzafar iska, yayinda daya kejin wasu masifaffun abubuwa nayi masa yawo a saman jijiyoyin kansa, abin da bai taɓa tunanin faruwa kenan dashi ba. "Shhhh" ya furta a ransa sbd yadda Halisa ta manna bakinta a daidai ƙirjinta tana murzawa duk a cikin barci hakan ya ƙara dagula lissafin Malam. Ya riga daya Sallama akan wannan murɗaɗɗan yanayin abun gashi a lokacin da bai taɓa tunanin faruwar hakan ba, babu zato bare tsammani yaji mararsa ta ɗaure baki ɗaya, al'amarin ya kumbura tare da harbawa wanda ya kusa tafiya da nutsuwara. Ya riƙe ta sosai kamar zai tsaga ƙirjinsa ya maida ta ciki haka yaji, a hankali yaja duvet yana rufesu baki ɗaya yana ɓoye fuskarsa a wuyanta. Ƙara lumshe idanunsa ya yi wanda suka tashi daga launin farare suka koma jaa, saboda tsananin azabar da ciwon da kansa yake masa lokacin guda, a tare suka fitar da wani irin wahalallan numfashi, yadda gangar jikinsu da ƙirkinsu ke haɗewa waje guda, haka ma zuciyoyinsu suke manne, yayinda numfashin ko wannansu yake fita tare dana juna. A haka cikin wannan yanayin barci ya ɗauke sa. 6:45 aka fara shelar anga jaririn watan Ramadan a garin Saudiyya, hakan yasa da Saudiya da ƙasa Nigeria da sauran ƙasashe aka ɗauki niyyar fara ɗaukan azumin Ramadan. Cikin nutsuwa yake shigowa cikin gidan bayan ya gabatar da sallar Issha cikin Masallacin harami, ya fara haurawa upstairs yana tura ƙofar ɗakin tayi saurin ɗago kanta suka haɗa idanu, ya lura kamar har yanzu a tsorace take ya rufe ƙofar tare da zame Alkyabbar jikinsa ya nufi inda take yana zuwa ya zauna yana ƙara dubanta da kyau. "Kika tsareni da ido?" Ta kwaɓe fuska tana marairaice fuska bakinta sai rawa yake tana son cewa wani abu amma ta kasa sai hawaye dake bin idanunta.. Ya ɗagata sama tare da ɗorata saman cinyoyinsa suka fuskanci juna ya shafa kanta ya ce. "Na gane, wato so yake yana kasa mini ke? Shi ne ya tafi da bakin mganar" ta nuna masa hannunta ɗaya wanda ya riƙe tare da riƙe hannunsa sosai hawaye na ƙara zuba a fuskarta ya goge hawayen ya ce. "Daga bakin har hannun daya riƙe miki zai sake su" tai murmushi tare da shafa sajansa taja gemunsa ta hannunta ta nuna masa bakinsa sannan ta nuna wuyanta. Ya ɗora goshinsa a nata tare da yin copping face ɗinsu numfashinsa na sauka a fuskarta. "Ya kalleki ko?" Ta ɗaga masa alamar _Eh_ Ya runtse sosai ta bugi kafaɗar shi tare da ɗaga hannu tai masa alama da _"Menene?_ Ya kalli ƙirjinta wanda yake so masha Allah fiye dana shakerunta. "Tausayin matsan abun ko?" Tai wani kyakkyawan murmushi tana saka hannunsa a baki tare da sakar masa cizo a dole aka mayar da ita kurma dole. Ya girgiza kai kawai yana kwanciya akan gado tabi jikinsa ta kwanta sosai taji tsoran yadda zuciyarsa ke harbawa sosai. ta miƙe tsaye tare da fara ƙoƙarin cire rigar jikinta taji anyi saurin kame hannunta mai lafiyar ya fesa mata numfashi ya ce. "Ban shirya ganin zubin lemon tsami ba" ya sakar mata light kisses mai sanyin wanda yasa tai saurin yin zillo cikin ɗaga murya da ƙarfi ta ce. "Abba!!" Ya kama hannunta tare da ɗorawa a gemunsa ya dinga shafawa kansa a wuyanta yana shan shana ko'ina ya ce. "Na'am, ƴar kurmar Modibbo" ya shiriri ce tare da ita yasan daga yau bashi da wadataccen lokaci nayi hakan. Wayarsa ta shiga ƙara ya saketa tare da nuna mata hanyar bathroom. "Assalamu alaiki Ummul" a bayyane Ummul ta sauke numfashi ta ce. "Congratulations! Halisa ta dawo naji ko a muryarka" ya tura hannunsa a suma jifa jifa yake faɗaɗa fuskarsa ta ce. "Zata dawo nan ne? Ko wajanka zata zauna" ya yi shiru dan bai san me zai ce mata. Ta ce "Na fahimta, Zahrah fa ya zakai da ita, Umar-khan ya ce bayan azumi Father na nemanka da gaggawa" Yaa Sheikh ya yi saurin dafe kansa gabaɗaya ya manta ya sha'afa. "Ta zauna nan, ita kuma zatai aikin hajji ne" Ummul ta saki murmushin jin daɗi ta ce. "Ah! Masha Allah za a zama Hajiya Halisa Danejo Rome banji motsinta ba?" A kasalance ya ce "An rufe mata bakin ne, hannunma an riƙe sa" Ummi ta ce "Ikon Allah wannan mutane Allah kayi mana tsakani dasu, sharrinsu sai su, amma kana ganin babu matsala?" Ya jima kafin ya ce "Da izinin Ubangiji" sallama sukai ta kashe wayar. Number Father ya kira yana ɗagawa ya ce "Da kyau Aliyu gwara ka nunawa duniya ban isa da kai ba, idan har nine uban dana haifeka to....," Yaa Sheikh ya yi saurin cewa "Kayi haƙuri don Allah Father, na manta ne kawai" Father ya tari numfashin Yaa Sheikh ya ce "Dole ka manta, kasan duk yadda kayi ka lallaɓa yarinyar nan Zahrah bata saba ɗaukan hayaniya a gidan ubanta ba, duk inda ka ke to ka sanya a kawota wajanka daga nan har a gama Ramadan wallahi idan kaƙi bin umarnina zan yafewa duniya kai babu kai babu ni" ya kashe wayar yana sakin huci kamar zaki. Yaa Sheikh ya tsaya wani irin abune uban daya haife shi ya dinga iƙirarin zai tsine masa ko ya sallama shi, me ya sa daga wannan sai wannan ne? Laifin mai ya yi me ya sa hakan ke faruwa ne wai?. Yaji tasa ƙaramin hannunta mai danshin ruwa ta taɓa shi ya kasa kallonta ta leƙa fuskar shi nan ma ya ɗauke yasan zata iya fahimtar halin da yake ciki sbd wayonta ya yi yawa kuma tayi masa sabo mai yawa. Yaji shassheƙar kukanta na tashi ya juya tana ganin ya juyo ta faɗa jikinsa tare da sakin kuka. Zahrah na kwance cikin dare tana barci taji cikinta ya juya an daki mararta ta farka a firgice sbd fitsarin daya zubo mata, ta tashi tare da nufar bathroom tai fitsari ta fito me take ji haka kamar motsin ɗa? ɗan ma irin wanda yake cikin ƙoshin lafiyar nan, shiyasa yau gabaɗaya bata fito ba sbd yadda cikinta ya ƙara fitowa sosai like 7mnt ɗin nan. Tana wannan tunanin taji cikin yaji gaba da zillo daga ya yi nan gefen sai ya yi nan. Aka fara bubbuga ƙofar ɗakinta ta miƙe tare da buɗewa Bara'at ta gani tsaye da tray ta ce. "Ya akai da wannan daren?" Bara'at ta ce "lokacin sahur ya yi ne, anga wata yau za a fara azumi" a fili Zahrah ta ce "Tab" Bara'at zata shiga bedroom tayi saurin cewa "Bani nan" ta miƙa mata kana ta rufe ƙofar, Zahrah ta kasa tunanin mene gaskiya shin da gaske cikin yana nan ko ya ya?. Dubban jama'a musulmai suka tashi da azumi daga ciki hadda matar malam cikin Ikon Allah bakin ya buɗe bayan ruwan zam-zam da Yaa Sheikh ya bata. Ita kaɗai ce a gidan domin tun 3:50 yabar gidan. A hankali kwanakin azumi ya dinga gangarawa har aka gabatar da guda Ashirin sha shida yau ana daren na Ashirin da bakwai daren da ake saka ran ganin Lailatul-ƙadr. Halisa Azumin sai addu'a idan yau an kai lafiya yau kuma da kuka musamman idan taga idanunta Yaa Sheikh wani lokacin kuma tsakaninta dashi sai dai a t.v idan yana tafsir ko an hasko yadda Sallar Taraweeh da Tahajjud take wakana dake shi ne limamin... Yaa Sheikh yana tsaye gaban ka'abah yana karatun mu'ujizal Alkur'ani ta sauka akansa harshensa ya harɗe ya kasa gaba ya kasa baya, ga ayar sosai a kansa amma bakinsa ya gaza furta komai wani hawaye ya shiga sauka daga cikin idanunsa. Shiru masallacin ya yi na wani lokaci a hankali ya ƙara dawowa baya amma faɗin ayar ya gagara sai kawai ya fashe da kuka. Sheikh Hafix ya janye Yaa Sheikh tare da komawa mazauninsa yaci gaba da karatu. Cikin lokacin ciwon kansa ya motsa a daddafe ya fito tare da bin ƙofar baya ta wajan ƙofar Sarki Abdul'aziz-Bab Abdul'aziz ya shiga mota kai tsaye aka kaisa gida, Halisa na zaune tana karatun Alkur'ani domin yau bata fita Ka'abah ba, taji an shigo ana bin bango tayi saurin miƙewa ta ce. "Malam?" Ta nufesa da sauri tana zuwa ta riƙe hannu a ta ce "Kan ka ne ko Modibbo?" Ya buɗe da ƙyar ya akai tasan kansa ke masa ciwo? Ta kama hannunsa har zuwa bakin gado ta zaunar dashi ta nufi kitchen ta haɗo tea mai zafi ta saka honey ciki. "Abba zaka samu lafiya kaji Abbana" ta bashi shayin ya saka hannu ya ture tare da fisgota suka faɗa gado ta ce "Abba baka da lafiya fa, bana son komai ya sameka" ya mirginata zuwa ƙasa tare dayi mata rufa yana zame Alkyabbar jikinsa muryarsa bata fita ya ce. "Azumi nawa akai yau?" Ta juya idanu ta ce "Ashirin da shida" ya shafa gefen cikinta ya ce "Muna dare na nawa?" Ta riƙe numfashinta ta ce "Daren ashirin da bakwai, daren ganin Lailatul-ƙadr" Ya yi cilli da Alkyabbar yana kama maɓallin gaban ruwa rigarta ya shiga ɓallewa kama ana jona masa shucking haka yake tura kansa a wuyanta yana murza gefen cikinta gabaɗaya ya sake mata nauyin jikinsa a hankali ya zame ya dawo da kansa daidai ramin cibiyarta ya yi mata wani kyakkyawan zuƙa Halisa tayi zillo ta ce "Wayyo Abba zaka cinye mini cibiyata" riƙe kansa kawai yake ha ciwon kai ga kuma abin da ya kejin yau ikon Ubangiji ne kawai zai hana faruwarsa ya tallafo fuskarta baki ɗaya ya ce "Mu ribaci wannan daren mai albarka matar malam" bai bata damar magana ba ya cafke bakinta ya riga ya manta ita ɗin ƴar raino ce, ya manta da deal ɗin Abba Hakimi neman maida Amanarsa yake zuwa cikakkiyar mace...Numfashin Halisa ya tsaya sbd nauyin da ƙirjinta ya yi mata muryarta na rawa ta ce. "Ribata? Me zamu ribata Yaa Sheikh?" Shi kansa idan ya ce zai iya magana a wannan lokacin ya yi ƙarya kalamansa bakinsa gabaɗaya suka tsaya idanunsa rufe ta cikin zuciyarsa yake tasbihi ga Allah da kuma neman dacewa da rai mafi girma da tarin albarka. Daren da miliyoyin mutane suke neman tabarraki a tattare dashi, a hana idaniyya barci kowa na neman gamawa da duniya lafiya, a takura zuciya da kirari haɗi da karatun Alqur'ani, daren wuya! Ga wanda ya sanyawa ransa ba zai iya ribatar lokacin ba, daren ladama ga wanda ya yi hasara yana mai yin barci a lokacin. Daren alheri ga muminin daya damu dacewa da ganinsa. Wannan daren na Lailatul-ƙadr shi ne mafarin buɗe zanan ƙaddarorin ɓangaren zuƙata guda biyu, shi ne ya zama fitila wajan haska abin da yake ɓoye tsayin shekaru, shi ne ya zame raba kaddama tsakanin igiyoyin auren dake saman gajimare suna yawo. The night became the reason for the separation of Humanity and the demon. Ya zama hasken daya haska zuciyar Halisa Danejo Rome ta gano wacece ita, hakan ya zama barazana ga rayuwar Yaa Sheikh Aliyu haydar. _(Now is the beginning of the manifestation of everything)._ Yaa Sheikh ya sauke numfashi mai zafi yana ƙara shigar da fuskarsa tsakanin wuyanta tare da goga mata tsinin hancinsa a fatar wuyan nata idanunsa rufe ruf! While yana murza hannunsa guda ɗaya a waist ɗinta tare da murza blet ɗin data riƙe trousers ɗin data sanya. "Abbana sallah ake, kace kada ga shige...," Fuskarsa da taji tsakanin ƙirjinta da saukar tattausan labɓansa a fatar wajan ya sanya maganar ta tsaya a fili a wahale ya ce. "Yasubuhanallah" Ya riƙe numfashinsa da kyau wanda ke neman ƙwacewa sosai kuma ya jarumtar kame kansa da hana bakinsa abubuwan da suke masa yawo a zuciya. He followed her body and kissed her with a certain style, ta zabura jikinta na rawa sosai tare da ɓari idanunta ya raina fata duk da har yanzu bata san me yake ƙoƙarin yi ba, kuma bata san meke faruwa Cikin aure ba. Amma ta firgita da sauyawar Abban nata baya sauƙi a zafafe yake cikin salo mai narkar da zuciyoyin manyan mata balle ta ga da take jaririya mai sauƙin kama tarko. "Abba wani abu yana bin ƙafata wayo kamar tsotsa Abba ka duban" baya gane yaran maganganun nata yake ji can saman kansa yana masa amsa kuuwa! A cikin kunne. "Shhhh Li....li..liserh" Ya faɗa cikin rawar murya shi kansa al'amarin kunya yake bashi, idan ya tuna how hot he's da tazarar dake tsakaninsa da ita. Bai da tabbacin zata iya ɗauke girman abun da yake shirin tunkararta da ita. Ya zame fuska a hankali daga kan ƙirjinta wanda ya bashi mmkin zubinsa a daidai kunnanta ya sauke bakin yana fesar da huci in a romantic voice ya ce. "Kin ce kina son sanin sirrin Abbanki?" "E, ina so Abba. Amma ka ƙi faɗa mini" Halisa ta faɗa tana riƙe fuskar shi kamar yadda ya riƙe nata. Yadda zuciyarsa ke rawa haka gangar jikinsa ke rawa ya yi kiss neck skin ɗinta ya ce. "Ina jin tsoran bakin nan" ta girgiza kai tana turo bakin Yaa Sheikh ya kasa ɗauke bai ƙasa a gwiwa ba wajan kame ƙaramin bakin tsoran da take ji sam bai hanata bawa Modibbo martanin abin da yake mata ba, ya riga daya ɗorata akan darasin da tayi masa mugun sabo. Idanunsu manne cikin na juna Yaa Sheikh ƙungiyar Halisa kawai yake hangowa wacce take ƙara sanya shi cikin nutsuwa. Bata ƙarya bata kuma barin bakinta ya huta. Ta cire bakinta idanunta cike da ƙwalla ta ce.. "Modibbona" ya ware idanunsa sharr! Hawayen ya zubo mata ta ce "Abbana" ya dubeta da kyau a wannan lokacin tare da son jin dalilin kiran ta ce. "Yaa Sheikh.... Malamina ina son ka Malam ina son ka Abbana zaka so ni ka faɗa mini sirrinka ko?" Bai bata amsa ba sai kifa fuskarsa da ya yi a slowly slowly ya shiga share hawayen da harshensa na salatin Annabi tare da jan duvet ya rufe su sosai ta saki kuka tana riƙe sa sbd abin da taji Yaa Sheikh bakinsa na rawa ya mirginata tare ƙoƙarin tunkarar inda yake son samun nutsuwa. Ta fasa ƙara da ihu! Tana dukan ƙirjin shi tare da cewa. "Zaka ɓallani Abba, kayi haƙuri ka yafe mini don Allah..." Ya riƙe ta da kyau ya ce. "Sau ɗaya kawai Fillona" ta girgiza kai hawaye na fita daga cikin idanunta bata san mene ya faru ba kuma tasan yanayin sutturar dake jikinsa ba, amma gabaɗaya fatar jikinsu a manne take.. "Modibbo baffi Allah mutuwa zan" ya shafa kanta ya ce "Ba zaki mutu ba" ta marairaice fuska ta ce "To amma" ya tsare ta da jirkitattun idanunsa. "Kayi haƙuri Abba ai dan kasan da zafi kuma ƙafata naji zata cire" shi dai bai ce mata ci kanki ba kaifin idanunsa mai nuna ki tausaya mini kawai yake binta dasu. A raunace ya ce. "Kina son fushin Allah?" Ta girgiza kai ta ce. "Ko fushinka ban so balle na Ubangiji" ya sauke numfashi mai zafi ya ce. "To ki bani dama" ta ƙara ɗaga masa kai ta ce. "Tom Abba, amma kaɗan zakai kada ƙafar ta cire" ya ɓoye fuskarsa na wani lokaci kafin ya ce. "Kalli cikin idanuna" ta saka ƙwayar idanunta cikin nasa. Daidai lokacin iska mai daɗin gaske da sanya zuƙata cikin shauƙi da nutsuwa ta shiga kaɗawa ta windown bedroom ɗin, garin ya yi tsit ko kukan tsuntsaye babu. Sai ƙira'ar Sheikh Hafix dake ratsa ko'ina dake garin Makka, dalilin abin sautikan da akai amfani da su. Yaa Sheikh ya rasa yadda zai da ransa tausayin ta na cinsa haka abin da yake so na damunsa, da alama kuma faruwar hakan al'amarin ya daɗe da zanuwa jikin allon lauhil-mahfuz sbd baya jin zai iya rabuwa da ita. samartaka zai sauke mata, ko gwaurantakar, ko kuma tsofan nasa?. Bai san meke faruwa ba sai jin bakinsa ya yi yana faɗin. _“Allahumma Jannib na-sshaiɗana wa jannibi-sshaiɗana ma Razaqtana”_ Halisa ta fasa ihu jikinta kamar mai farfaɗiyya haka yake jijjiga idanunta ya yo waje numfashinta ya tsaya. A fili cikin murya wacce shi kansa bai san ya take ba ya ce. "Allahu Akbar, Allahu Akbar Allahu Akbar ikon Allah, Allahu Akbar" shi kawai yake maimaitawa cikin rawar murya kansa jurewa da ya yi, ya sake furta. "Wayasubuhanallah! Walahamdulillah Asstagafirullah Allahu Akbar!" lokacin daya tabbatar ya mayar da ita halaliyar shi ajjiyar zuciya ya sauke ya ƙanƙameta a tsakiyar ƙirjinsa ya ce. "Yaa! Rasulullahi manzon Allah, Assha Allahu Akbar" zikiri kawai bakin ke fitarwa banda haka baka jin komai daga gare shi, duk abin da zai sanya Yaa Sheikh magantuwa a fili kuma a zahiri abin ya kai. Domin ko zikiri zai iya zuciyarsa yake sai dai kaga bakinsa na motsawa alamar tasbihi yake ga Ubangiji.. Halisa ta kasa jurewa ta kasa karɓar abin numfashinta ya yi hijira daga jikinta, komai nata ya tsaya cak. Kiran sallar farko ya sanya Yaa Sheikh dawowa cikin tunaninsa duvet ɗin daya rufe musu jiki ya jiƙe gabaɗaya da zufar da Yaa Sheikh yake fitarwa. Ya buɗe gajiyayyun Idanunsa yana fisgar numfashi da ƙyar bakinsa ya yi nauyi ya kasa yarda cewa ƴar rainon ta shi ita ta shayar dashi wannan mamakin ita ta ɗauke buƙatarsa na tsayin shekaru har talatin da huɗu zuwa da biyar. Al'ƙawarin da ya yiwa zuciyarsa ya cika, ya tsare mutuncinsa ga amanar shi. Ya ƙara jan numfashi sbd kansa dake sarawa naman jikinsa na rawa sbd zazzaɓin daya kawo masa farmaki lokaci guda! Haƙoransa sai gamuwa suke dana juna sona basa sautin mai ƙarfi. Ƙarfafa jikinsa ya yi tare da zare jikinsa baki ɗaya daga nata, duk da cewa a hankali ya fita amma cikin halin soman da tayi sai data sauke numfashi tana zabura. Ya tattaro Alkyabbar jikinsa daya jima da cilli da ita ya saka a hankali yana dafe bango tare da riƙe jikinsa ya nufi bathroom shower ɗin dake fitar da warm water ya nufa tare da saita ƙarfin zafin da yake so yana daga tsaye ya sakarwa kansa ruwan tare da zame Alkyabbar. Juyi kaɗan motsi kaɗan ya furta. "Allhamdulillah Allahu Akbar!" Cikakken wanka ya yi yana jin nauyin jikinsa na raguwa, mararsa tai wasai sai masifaffan ciwon kai da zazzaɓin dake tsoma shi..ya ɗaura bathrobe a jikinsa kana ya haɗa ruwa mai zafi sosai cikin jakuzzie. Gently ya nufeta ya sunkuya tare da bubbuga pillown, bata motsi bai lura da numfashi ba, zuciyarta ta ɗan buga ya ƙara riƙe kansa tare da kama kafaɗarta yana jijjigata nan ma bata motsi ya dafe kansa a ransa ya ce. "Oh! Ni Sheikh bai nai?" Sai kuma ya saki wani irin kyakkyawan murmushi tuna cewa wannan ƴar mitsitsiyyar yarinyar ce ta saka shi farin cikin da yake ciki. Ya ɗagota zuwa jikinsa tare da shigewa bathroom ɗin a hankali ya sakata cikin ruwan ta saki numfashi tare da zabura sai gata ƙasa idanunta rufe wani marairaccen kuka ya ƙwace mata. Bai ce komai ya ɗauketa tare da zama cikin ruwan ya zaunar da ita jikinsa bata da wani ƙwari amma haka ta fara neman guduwa ya riƙeta da kyau ta saki kuka shagwaɓa dana azabar da take ji ta ce. "Bana son ka Abbana,kayi mini mugunta bana son ka" ya ƙara matseta daidai kunnanta ya ce.. "Sorry ƴan mata" "Ka mayar dani wajan Ummul" ya yi kissing bakin mganar kuka take sosai tana narke masa cikin shagwaɓa ta nemi dagula masa lissafi. Da ƙyar ya yi mata wankan tana rufe ƙirjinta bayan ance ya rufe ido. Duk abin da tayi murmushi kawai yake mata wani lokacin ya rungometa tare da yin shiru. Yadda jikinta ke ɗauke da zazzaɓi haka nasa,bayan yai mata alwala shima ya yi ya kwantar da ita saman kujera duk jikinsa ciwo yake bai kuma saba ba, ya sauya bedsheet. Wata farar jallabiya ya saka sai baza ƙamshi yake na musamman ya ɗora hirami. A hankali yake sauka daga upstairs zuwa downstairs. Ya danna telephone line bai ce komai ba ya kashe. Not too long wata maid ta kawo abin sahur a tray. Ya ɗauka tare da komawa har lokacin tana kwance jikinta na rawar sanyi sai ƙananun koke-koke take. Ya dubi lokaci yaga har yanzu da sauran time na yin sahur daman dabino kawai yake ci kuma baya sahur da wuri yau kuma ji ya yi kamar an kwashe komai na cikinsa. Ya ɗagota tayi saurin sakin kuka sbd ciwon da take ji ya manne da jikinsa tare da ɗakko shayi mai zafi ya bata, ta ɗauke kai ta ce. "Uhm ni a'a" ya ware idanu sosai muryarsa a matuƙar sanyaye Ya ce. "Take it, drink" ta girgiza kai ta ce "Ni Ummul zani ban son zama wajanka baka sona jikina baffi bayana,kai na, ƙirjina ƙuguna, ko'ina ciwo" ya shafa sumar kanta yana jan hancinta ya ce. "Kibar mini sunan Ummul ɗina ya huta,ni kaɗai kika sani, ita kuma ta Sanni Okey?" Ta ɗauke tana kuka sosai hadda majina ita gabaɗaya tsoran Abban nata take ji ganin rawar da ƙafafuwanta suke ya ƙara tabbatarwa akwai rauni jikinta. "Lokacin Sahur zai shige" ta ƙarawa kukanta sauti ta ce "Ni ba zan iya azumin ba, bani da lafiya" ya riƙe kansa ya ce. "Ina matar malam ina fashin azumi" ta kwaɓe fuska sosai shi kansa tausayinta ya keji ta ce "Allah yana gani ai bani da lafiya kuma lada kace zan samu" ta ƙare maganar tana kuka sosai jikinta zafin rau! Ya mayar da ita ƙirjinsa ya rungome sosai wani abu na ratsa masa jiki bai ƙara mgn ba, ya dinga shan tea ɗin a hankali tare da Soyayya ƙwan da akai ya buɗe ciki ya sha farfeson naman da akai, yana jin yadda take surutan zazzaɓi da yadda ta jiƙe masa gaban jallabiya da yawo idan zafin ya yi mata yawa ta sakar masa cizo. A haka ya kammala sahur ɗin ya haɗa da dabinon ajwa da Inibi ya ɗora da zam-zam. Yana yi yana duban lokacin yana riƙe kansa shima dauriya kawai yake. Ganin da lokaci ya haɗo Injection tare da kayan aiki, tace sam bata san wannan ba. Ya riƙeta da kyau ya ce. "Matar malam Aliyu" ta kalle shi ta ce "Abba matarka ce ni?" Ya jinjina mata kansa ta ce. "To dan girman Allah kada kayi mini allura kaji Abbana ɗan albarka" ya kama hannunta tare da manna shi da sajansa ya shafa ya ce. "To riƙe ni, ki kalli ido na" ta riƙesa suka kalli juna ya sakar mata murmushi mai laushi dimples ɗinsa suka loma ta saka yatsa a ramin wajan "Ina son ka Abbana" ya zame towel ɗin jikinta tare da yin ƙasa dashi ya ɗora tsinin allurar a jikinta, while idanun cikin nata ya ce. "Kwailar malam" ta danna hannunta a dimple ɗin ta ce "Modibbona" ya ɗaga mata gira ya ce "Ina....ina..ina" ta ƙarasa da cewa "Ina son ƴar fillo, haka zaka ce ko Yaa Sheikh?" Ya ɗaga mata kai duk da ba hakanne a ransa ba. Ta ce _“I love y....”_ ta saki kuka da ƙara sbd zafin shigar Allurar ya yi saurin zare allurar yana rungometa tare da jijjigata. "Shhhhh, it's okay sorry fillo" ta dinga kuka sosai tana dukansa da cizo a hankali numfashinta ya dinga sauka barci ya ɗauke ta a jikinsa. Ya sauke numfashi tare da matseta a jikinsa.. "Allah ya yi miki Albarka _Hubbb,_ _zawja,Omry,Hayaty_"Ta cikin wayar Father ya ce "Kika ce me? Na kasa fahimtar zubin maganar taki" Zahrah ta ce "An shaida mini Yaa Sheikh bashi da cikakkiyar lafiyar zama da mace,shi ya sa tunda akai auren bamu taɓa haɗa shimfiɗa ba" Father ya yi sai yaushe Yaa Sheikh ya samu larura? Ko hakan yasa bai damu da yin aure ba tsayin shekaru?. Zahrah ta katse tunaninsa da faɗin. "Kasan ɗanka lusari ka aura mini shi? To idan bashi da lafiya ni ina da ita, kuma ba zan jure zama haka ba, inma ya samu mafita ko ya sakeni" mmkin Zahrah ya cika zuciyar Father shin daman haka take babu manner of speech? Ko yanzu ta sauya hali? Kafin ya yi magana Zahrah ta kashe wayar ta shiga safa da marwa tunaninta ya tsaya baki ɗaya. Cikin sauri ta kira Deen tai ta ringing kafin ya ɗauka rai ɓace ta ce. "Ai ta kira kamar baka kusa?" Ya gyara zama a ina yake zaune ya ce. "Nasan ta tsuniyar gizo bata shige ta ƙoƙi, Yaa Sheikh.. Yaa Sheikh.. Halisa ƴar fillo haka dai, something new?" Ta ce "Babbar matsala, Yaa Sheikh bashi da lafiyar tarayya da mace shi ya sa yaƙi bani da ta haɗa shimfiɗa da shi" Deen ya yi shiru for some minutes kafin ya ce. "Just go to the point, ban fahimta ba" Ta ce "I mean by words, target naka shi ne maƙalawa Yaa Sheikh cikin jikina, ciki kuma ya zube, mu ɗauka zai saurareni daya sha maganin sai muka ga saɓanin haka,mene next what's your plan?" Kamar ya shiga tunaninta taji ya ce. "Ki bari zuwa bayan Ramadan, I'll think about it" badan ta so ba ta ce "Ok" daga ta kira Surry suka tattauna sai kuma ta kira Babarta. Halisa ta saki murmushi idanunta akan Bilal wanda zaton ta Yaa Sheikh ne ta ce. "Abba yau ba darasi ne?" Bilal ya ƙara ɓoye kofaton ƙafarsa yana sakin murmushi ya ce. "Akwai mana, so nake kiyi barci sai abin ya fi" ta kama gemunsa sosai tana murɗewa kamar yadda ta saba ta ce. "Shikenan, amma ni ai ina so ko?" Gabaɗaya dauriya yake ya yi tunani da bincike amma ya kasa fahimtar wanne kalar ƙulli Yaa Sheikh ya yi wa Halisa da har akai masa hijabi da jikinta. Ta riƙe shi ta ce "Yau nayi mafarki, wai kana ta kuka Abbana,bana son ganin kukan ka kaji?" Bilal ya faki Idanun Halisa ya wangale asalin tafkeken bakinsa kafin ya dawo daidai ya ce. "Idan baki son nai kuka kiyi mini al'ƙawari" ta juya idanunta a cikin nasa tana sauraran abin da zai ce. "Kiyi al'ƙawarin bayan ni ba zaki kula kowa ba, kiyi mini al'ƙawarin ba zaki taɓa bawa wani namiji damar shiga fadar daba tashi ba" tayi saurin cewa "Fada kuma, ina ne fada?" Bilal ya kalleta wato dai har kullum ba zata sauya ba? Ya ce "Ina nufin kada ki bari wani namijin ya kusance ki, ni nake da wannan ikon ni zaki haifawa yara dan ma anyi mini asarar cikina amma zan baki wani cikin" Ta hangame baki sosai ta ce "Tab, shi cikin to ta ina zan same shi?" Ya kalli gabaɗaya ɗakin da suke ciki ya ce "Zan faɗa miki, amma kafin nan akwai wanda yake son rabani dake, yake son yaga ya wahalar da zuciyoyinmu, kada ki manta nine na kawo rugarku lokacin da kika ɓata, kuma nine na taimaki lokacin da aka haɗaki gasa da maciji, wani zai zo mai kama dani zai so ya rabamu kada ki bashi damar haka, ni kalli hannuna akwai zane, koda wani yazo idan baki yarda ba ki fara duba hannunsa idan babu wannan zanan to bani bane" Tai shiru tana sauraran Bilal ganin ta kasa cewa komai ya riƙe hannunta ya ce "Kada ki barni, kada ki bari a rabamu" idanunta ya cika da hawaye ta kasa magana sai girgiza kai take tana shassheƙa kamar zatai kuka. Bilal ya riƙo fuskarta ya ce "Ko baki son Abbanki Danejo kizo muje duniyata, na miki al'ƙawarin zamanki sarauniyar duniyar" ta girgiza kai ta ce "Ina son ka Abba, ka daina cewa za a rabamu tsoro nake ji, ina son ka kada ka barni?" Ta faɗa jikin Bilal tana ƙanƙame shi.. Ya runtse idanunsa azaba yake ji kamar ana huda masa jiki. Ya dinga busa mata isa a fuska wanda yasa cikin ƙaramin lokaci barci ya ɗauke ta barcin da aka sanyata yi na dole. Cikin barci taji kamar tana mafarki ta shiga motsa ƙafafuwanta wanda ake ƙara wara mata su cikin hukumcin Ubangiji a mafarki ta dinga ambaton sunan Allah. Amma al'amarin yafi ko wanne mafarkinta tsamari, sai nishi nake jikinta na jijjiga. A hankali yake tafiya cikin farar jallabiya mai kyau ya ɗora Alkyabba akai rawaninsa ya fito sosai ya bayyana a salin Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu babban malamin da ƙasoshi da dama suke alfahari da shi. Ya ɗan saurara da tafiya yana sauraran abin da Sheikh Hafix yake cewa. "Naga Dutsen Jabal an-Nour" Yaa Sheikh ya jinjina kai domin hankalinsa baya wajan, bai ma ɗauka da ya zo Makkah ɗin ba zai daɗe haka ba. Yana ƙoƙarin komawa Madina Sarkin Makka ɗin ya ɓukaci a tattaki domin tabbatar da komai Lafiya yake kafin a ɗauki azumi a daren yau. _Jabal an-Nour dutse ne da ke kusa da Makka a yankin Hejaz na kasar Saudiyya. Dutsen ya kunshi kogon Hira'a, wanda ke da mahimmaci ga musulmi a duk fadin duniya, kamar yadda aka ce annabin Musulunci_ "Ina tunanin ai ba sai ka koma Madina ba, waye zai fara jan jam'i, an kammala shirya maka gidan daka buƙata" Sarkin Makka ya kalli Yaa Sheikh dan ya lura baya tare da su ya ce. "Ina fatan za a sakani cikin addu'a wacce ta kasance mai muhimmanci, Masallacin harami ya ɗauki niyya da dubban mutanan da suka ziyarci aikin hajji daga ƙasashe daban-daban, da kuma na garin Makka da Madinah" Yaa Sheikh ya sauke numfashi ya ce. "Allah ya kaimu, ya haɗamu da ladan dake cikin wannan wata" duk manyan malaman da Sarkin Makka suka amsa da _“Amin”_ kafin Sheikh Hafix ya duba lokaci ya ce. "Wa'adin duba wata a sama ya yi, daman ma'aikata sun ƙara sa filin duba wajan da abin hange" _Masallacin Harami da ke Birnin Makka na kasar Saudiyya shi ne masallaci mafi girma da tsarki a ban-ƙasa,Shi ne masallacin da ake nunka ladan sallah sau dubu dari fiye da sallah a sauran masallatai.A cikinsa ne Dakin Ka'aba yake, wanda shi ne ginin farko a duniya kamar yadda musulunci ya nuna, kuma shi ne Al-Kiblar da Musulmai ke kallo a duk lokacin da za su yi sallah daga ko ina a duniya. Girman Masallacin Harami na Makka ya kai murabba'in mita 356,800, kuma yana iya daukar kusan mutum 800,000 masu ibada a lokacin aikin hajji, A wannan tsarkakakken masallaci akwai Ka'abatul Musharrafa, wato Dakin Allah Mai Tsarki, inda nan ce alkiblar da duk musulman duniya ke fuskanta idan suna salla. Tsawon Ka'aba ya kai mita 12, fadinta kuma mita 10 sannan tudunta ya kai mita 15. An lullube ta da Bakin Yadi da ake kira Kiswah, wanda yake dauke da rubutun Kur'ani mai girma da ruwan gwal. Duk shekara ake sauya Kiswah. Kofar shiga Dakin Ka'aba tana daga bangon arewa maso gabashin dakin. A jikin Ka'aba akwai Bakin Dutse, wato Hajrul Aswad inda daga nan ne ake fara dawafi, kuma ana so mai dawafi ya sumbanci dutsen, in ya samu dama. In kuma bai samu damar sunbata ba, sai ya taba da hannu, ko kuma ma ya nuna shi da hannu in bai samu damar tabawar ba.Multazam ma wani bangare ne na Ka'aba da masu ibadah kan tsaya don yin addu'a. Yana tsakanin dutsen Hajarun Aswada da kofar Ka'aba. Ana so idan mutum ya samu dama ya kara kirjinsa da cikinsa da hannayensa a wajen. Yana daga wuraren amsa addu'a. Fadinsa ya kai mita biyu. Akwai kuma Makamu Ibrahim inda a bayansa ne ake so a yi sallah raka'a biyu bayan kammala dawafi. A nan ne aka ajiye dutsen da ke dauke da alamar sawun Annabi Ibrahim AS wanda ya taka lokacin da ya ke ginin Ka'aba. Hijri Isma'il wanda ake kuma kira Hateem wani bango ne a jikin Ka'aba. An zagaye bangaren kadan, kuma yana daga bangaren arewa maso yammacin Ka'aba. Wajen shi ma yana cikin Ka'abah. Kuraishawa ne suka fitar da shi daga Ka'aba lokacin da suka sake ginin ɗakin,Dutsen Safa da Marwa kamar yadda Allah ya fada a Alkur'ani mai girma "Lallai ne Safa da Marwa suna daga wuraren ibadar Allah, to, wanda ya yi aikin Hajji a dakin ko kuwa ya yi Umra, to, babu laifi a kansa ya yi dawafi tsakaninsu. Kuma wanda ya kara yin wani aikin alheri to, lallai ne wadannan su ne shiryayyu." Surah Bakara aya ta 158. Dutsen Safa inda daga nan ake fara Sa'ayi yana da nisan kilomita 0.80 daga Dakin Ka'aba. Yayin da Dutsen Marwah yake da nisan mita 100 daga Dakin Ka'abah. Nisan da ke tsakanin duwatsun biyu kuwa mita 450 ne.Rijiyar Zam-zam Rijiyar Zam-zam na daga ɓangaren gabas da Ka'aba da nisan mita 20. Wannan rijiya na samar da isasshhn ruwan da bai taba ƙafewa ba tun lokacin da Ubangiji Subhanahu Wa Ta'ala ya samar da ita a zamanin Annabi Ibrahim AS, kamar yadda malaman tarihi suka ruwaito. Kofofin masallacin Akwai kofoi biyar waɗanda su ne manya-manya a Masallacin Harami da suke hada da: Kofar Sarki Abdulaziz - Bab Abdulaziz Kofar Fateh - Bab Fateh Kofar Safa - Bab Safa Kofar Umra - Bab Umra Kofar Sarki Fahad - Bab Fahad". Sheikh Hafix ya saki kyakkyawan murmushi ganin yadda aka ƙara ƙawata komai a Makka ya ce "A wanann shekarar naga dubban mutane sun ƙaro akan adadin mutanan da muke samun ziyarar tasu" Sarkin Makka ya ce "Nima nai mamaki ƙwarai, Ubangiji ya ƙara ɗaukaka musulunci da Musulmai" A taushashe Yaa Sheikh ya ce "Amin Ya Allah" tsayawa ya yi daga tafiyar ba suyi masa magana ba sanin cewa yana da tsari, a hankali yake hawa saman Dutsen Jabal an-Nour tunda yaji kamar ana jansa wajan yasan akwai matsala, yana zuwa idanunsa ya sauka akanta tana kwance a saman dutsen wasu ƙananun kaya ne a jikinta farar cinyarta sai sheƙi take gashinta ya bazu wato nan aka cillota? Walking slowly ya nufeta kafin ya ƙarasa inda take yaga an ɗagata sama ba tare daya ga mutum ba. Wani lallausan murmushi ya saɓucewa Yaa Sheikh ya ce. "Ba hayaniya zaman, domin a waje mai tsarki nake" Bilal dake tsaye ba tare daya bayyana kansa ba ya ce "Ba kai ba matata, ka fita hanyar matata" Yaa Sheikh ya kalli gabas, yamma, kudu, arewa yaga akwai ɗaiɗaikun mutane wanda suka zo neman tabarraki a Jabal an-Nour ɗin. "Sauketa" ya faɗa babu alamar wasa a fuskarsa Bilal jikinsa ya fara rawa ya ce "Kada kayi mini haka, na fika sonta" Yaa Sheikh ya gyara tsaiwa ya ce. "Banda son zuciya da mugunta irin na Aljani mene haɗinka da Bil'adama? Ina tunanin munyi yarjejeniya dakai tun ba yanzu ba" "Ba zan iya jurewa ba, ina son matata, kuma na shirya tafiya da ita duniyarmu" Bilal ya faɗa murya na rawa kallon Yaa Sheikh ɗin kawai ya firgita shi. "Me nace maka?" Bilal ya ce "Kace idan na sake bayyana zaka ƙona ni" Yaa Sheikh wani baƙin ciki da takaicin yadda ya ɗaga masa Ƴar Aljannar shi a sama ya cika masa zuciya ya ce. "Bani da laifi idan nayi haka yanzu, kabar uwa ka dawo kan ƴar ka yi wa kan ka adalci kowa?" Bilal ya ce "Abin da kayi nayi, yadda kabar uwa ka dawo kan ƴar haka nima nayi, kuma ba zan barta ba ina tare da ita har abada" Yaa Sheikh ya nemi waje mai kyau a saman dutsen ya zauna yana harɗe ƙafafuwansa waje guda cikin kamilalliyyar muryarsa ya ce. "Bisimillah!" Fatih ya fara karantawa ya ɗora da Yaásin. Bilal ya fara motsi cikin sauri ya sauke Halisa ƙasa nan take ta farka daga barcin da take, Bilal ya rungometa a jikinsa lokaci guda kuma ya dawo suffar Yaa Sheikh shima, sai ya zama dashi da Yaa Sheikh kamar twins ne. Zafin karatun dake rasa jikinsa yasa Bilal fara ihu tare da sakin kuka cikin sautin murya mara daɗin Amo! "Kada ka yi haka, kada ya rabani da ita kayiwa Allah kada rabani da matata wallahi ina son ta" Yaa Sheikh ya dakata da karatun ya kalli yadda ya rungome masa mata ya ce. "To ai nima matar tawa ce" Bilal ya ce "Na fika iko da ita, har cikina ta samu aka cire" Yaa Sheikh ya jinjina kai yana goge zufa ya ce. "Nima zan tabbatar da hakan, zan cike nawa igiyoyin" Bilal ya kwarara ihu wanda ya sanya Halisa firgita ta saki kuka ta kasa gane abin da yake faruwa, muryoyin Abbanta ya kaso biyu, ɗaya cikin kuka kuma mara sauti ɗaya kuma a nutse cike da Ilhama. "Baka isa ba, zan kashe kowa naka idan ka kusanci matata ni kaɗai nake da wannan ƙarfin ikon" "Dan gidanku sai ka hana, nawa ma ba irin naka bane, ba ciki ba, ni cikkona zan zuba mata da ƙwayayen da Ubangiji ya azurtani dasu" Yaa Sheikh ya ci-gaba da karatunsa Bilal kuma ya dinga ihu da kururuwa Halisa ta ƙwace jikinta a ruɗe take kallon Abbanta sai kuma ta juya ta kalli Bilal dake tsaye wanda ya yi kama da Yaa Sheikh sak! Tunaninta ya raɓauta firgice na son kassara ƙaramar ƙwaƙwalwarta. Yaa Sheikh ya kalleta tare da miƙa mata hannu alamar ta zo. Bilal ya yi saurin cewa "Kinyi mini al'ƙawarin babu mai rabamu,daman nace wani zai rabamu ki biyuni muje" Zaratan mazan suka dagula mata lissafi wa zata bi? Waye kuma Abbanta. Kamar ana janta tayi saurin riƙe Bilal ta ce "Tsoro nake ji kai ni gida Abba" Yaa Sheikh ya ce. "Ki matsa daga jikinsa shi ne wanda ke son jawo rayuwarki daga inuwa zuwa rana, matsa nan nace" cikin ƙarfin murya da ɗaga sauti Bilal ya ce. "Ƙarya yake, ƙarya ne kada ki yarda da shi" aka shiga fafatawa tsakanin Yaa Sheikh da Aljani Prince Bilal. Ganin a wannan karan da gaske Bilal ba zai bar masa mata ta daɗi ba, yasa Yaa Sheikh miƙewa a hankali ya shiga takowa yana ƙara sautin ƙira'ar da yake wanda yake ƙara zautar da Bilal yana zuwa yasa hannu ya finciko Halisa ya mannata da jikinsa tare da rungometa tsam, ta sauke wani ɓoyayyen numfashi lokacin da jikinta ya haɗu dana Abbanta. Bai fasa karatun da yake ba Bilal bai fasa ihu ba da ƙoƙarin kamo Halisa. A hankali Yaa Sheikh ya zame Alkyabbar jikinsa tare da riƙo ƙugun Halisa ya manna da nashi ya ɗora mata Alkyabbar tare da rufe ruf a jikinsa. Ya saurara da karatun da yake gently ya tallafo haɓarta tare da manna fuskarsa akan nata yana fesa mata zazzafan numfashi ya kalli bakinta wanda ya bushe sosai sbd wahala cikin nutsuwa ya ɗora bakinsa akan nata wani irin damƙa ya yi wa lips ɗintaGanin barcinta na sauka a hankali ya sanya Yaa Sheikh gyara mata kwanciya tare da saka mata pillow ta rungome sosai a jikinta. Ya zuba mata kyawawan idanunsa kamar mai tunanin wani abu, zuciyarsa fal mmkin yadda yaga ko ciwo bata ji ba, sai jaa sosai da wajan ya yi alamar tasha gurza da gaske, ya san ya saki dukkan ƙarfinsa a kanta.. "Allhmd Yaa Rabbi!" Ya furta a taushashe cikin nutsuwa ya fita yana mai jan ƙofar ya rufe, kai tsaye harabar gidan ya nufa driver ya buɗe masa mota ya shiga, direct Harami suka nufa idanuna rufe yana tasbihi jikinsa duk ciwo yake ga wani matsanancin ciwon kai. Ta ƙofar baya suka tsaya sbd cikar mutane da ƙafarsa ya yi takkaci zuwa cikin masallacin kai tsaye kuma ƙofar da zata kaisa ga mazaunin liman ya shiga. Dukkan wasu manyan limaman da suke garin Makkah suna zaune a sahun farko har sarkin Makka. Ba wanda ya yi wa magana ya je ya zauna yana jan Alkur'ani ya fara karatun a nutse sashi guda na zuciyata yana wajan amanarsa. Lokacin Assalatu nayi aka gabatar daga baya kuma yaja dubban mutane sallar asuba. Tunda yake gabatar da Sallah bai taɓa daɗewa a sujja kamar yau ba, wasu irin manya-manyan adduo'i yake wanda shi kaɗai yasan akan me, kuma waya kewa?. 7:00 motarsa tai parking ya ɗan jima yana sauke numfashi kafin ya fito hannunsu riƙe da casbawa ya ɗan ɗaga kansa sama kamar mai nazari sai kuma ya shiga cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama cikin sanyin murya. "Wasalamu Alaika" Yaji an amsa, ya san kuma bai bar kowa ciki ba, ya shanye mmkin daya kama shi tare da kallon direction ɗin inda aka amsa. Suka kalli juna da El-bashir wanda yake zaune cikin shigar aikin hajji sai jakarsa dake gefe. "Barka da safiya" El-bashir ya faɗa yana kallon Yaa Sheikh.. Yaa Sheikh ya jinjina kai kawai maimakon ya yi upstairs sai ya zauna saman kujera 3seater yana lumshe idanun. "Barka da safiya Aliyu" Ya ware idanunsa jin muryar Mai martaba. Ya faɗaɗa fuskar yana yin ƙasa da kai ya ce. "Barkanmu dai Mai martaba, ya ibada?" "Allahamdulillah" Mai martaba ya furta yana mmkin ganin yadda yau Yaa Sheikh ya ƙara masa kyau da kamala a idanunsa, tsofan nasa ya ragu sai tarin kwarjini, sai haske fuskar keyi kamar sabon ango.. "Annurin fuskarka ya shaida nutsuwar zuciyarka Aliyu, Allah ya tabbatar da aminci a abin da ya tausasa zuciyar Haydar" Ya ɗauke kai yana jin kamar Mai martaba ya fahimci abin da ya aikata. "Daɗi ne ya yi mini yawa, kankana ta bada ruwa" zuciyata ta faɗa cikin ranta. A bayyane ya ce. "Asstagafirullah!" Sbd yasan maganar ƙwacewa tayi ga kuma Azumin dake bakinsa. "Dame fa?" Cewar El-bashir da yake son cusa kansa a rayuwar Yaa Sheikh. Yaa Sheikh ya juya ya kalli El-bashir kallo ɗaya mai nuna fassarar abubuwa da yawan gaske. Ya ɗauke kansa yana fuskantar wani wajan daban ya ce. "Mubasshir ko? Ya aiki?" Takaici ya cika El-bashir, wato yana nufin bai da tabbacin haka sunan yake? Ko tsabar iya nuna cewa shi ɗin ba mai laifi bane. "Aiki yanzu muka fara, sai fatan tsuntsunmu ya shiga tarkwan da muka ɗana" Mai martaba ya girgiza kai ya rasa Meye ƴar tsamar dake tsakanin zuciyoyin guda biyu? Tamkar Musa da Fir'auna akan rashin jituwa, El-bashir na jinsa kamar wani ƙaruna sbd iya ɗauke kai. Yaa Sheikh kuma yana jinsa kamar Muti menk sbd tsantsar addini daya ratsa shi da rashin ko in kula da al'amarin da bai shafin duniyar shi ba. Abin nasu kamar wani wasan kwaikwayo ko labarin littatafan hausa. "El-bashir kasan tazarar dake tsakanin sama da ƙasa?" El ya ware idanu akan mahaifin nasa ya ce. "Nasan dai tsayin dake tsakanin duniya da wata kilomita 384.400" ya faɗa yana ɗaga kafaɗa irin he doesn't care about the question. "Ƙaddara haka ne tsakanin shekarun haihuwarka dana Aliyu, kada ka kuskura kada ka fara wasan, na ɗauki hakan matsayin gargaɗi" El-bashir ya kalli Mai martaba ya ce. "I did not understand you correctly, Your Highness" fuska babu walwala ya ce "Ina nufin abin da nace Mubasshir, tashi ka bamu waje" tsanar Yaa Sheikh ta ƙara ninkuwa a zuciyar El-bashir Ahmad Sarki, kamar yadda Fir'auna ya tsani haihuwar yara maza a ƙarninsa haka El ya tsani Yaa Sheikh. Bayan fitar El Mai martaba ya gyara zama cikin nutsuwa ya ce. "Yaa Sheikh Aliyu" sai a lokacin Yaa Sheikh buɗe kame kansa kawai yake yana jin kamar ya yi fiffike ya tashi zuwa ɗakin da ƴar fillon shi ke ciki. A sanyaye ya ce. "Na'am" Mai martaba ya furta. "Ina jin kamar kukana ya kusa zuwa ƙarshe, idaniyyar dake ta kuka shekara shekaru zata samu barci, zuciyar dake cike da zullumi, ruɗu, ƙunci, damuwa zata samu sassauci a wannan karan, ina miƙo ƙoƙwan bara ta gare ka, da ka tayani roƙan Ubangiji akan buƙatata kasan bakinsa mai tsafta ne" Yaa Sheikh ya lura da da kwantacciyyar damuwa dake manne a fuskar Mai martaba cikin kyakkyawan lafazi ya ce. "Ina jin adadin abin da ka ke ji, ko fiye da hakan, Ubangiji na gani kuma zai sanya mana hannu cikin al'amarin" murmushi ya ƙwace a fuskar Mai martaba ya ce. "Allahamdulillah, naji na samu ƙarfin gwiwa, na manta zan koma da Halisa Nigeria kona faɗa maka?" Yaa Sheikh ya riƙe numfashi ya yi ta kallon Mai martaba ya kasa cewa komai. "Umarni ne daga wanda yake da kima a idanuna dole zan tafi da ita" Yaa Sheikh ya miƙe tsaye a zuciyata ya ce. "An nemi tuzartani kawai" Mai martaba ya ce "Magana kayi?" Ya saki murmushi mara sauti yana ɗauke kai. "Zan shige, daman tunda aka fara aikin hajji bamu haɗu ba, na dai ga wannan maid ɗin Ummul ko? Shi ya sa nace bari na shigo mu gaisa" Yaa Sheikh ya ƙara jinjina kai yana take masa baya. "Idan ta tafi da ƙwayayena a mararta to!" Yaa Sheikh ya ƙara furtawa cikin rashin zato. Bibbiyu yake taka strais ɗin benen ya murza key tare da shiga baki ɗauke da sallama, idanu biyu sukai da ita tana jingine da jikin gado ta kasa tashi tun sallar data lallaɓa tayi idanunta ya yi jaa ya kumbura sosai alamar taci kuka. Ta ɗauke kai tana kwaɓe fuska tare da sakin wani sabon kukan shagwaɓar. Ya zame Alkyabbar jikinsa tare da cire hiramin a karo na farko wanda yake tabbatar da cewa shi da ita ɗin sun zaɓa abu ɗaya. Yana zuwa ya durƙosawa daidai inda take tare da zuba mata idanu alamar "mene?" ta ɗauke kai irin da gaske bata son ganinsa ko kuma laifin da ya yi mata ya gawurta ya numfasa yana riƙo fuskarta a hannunsa cikin taushin murya mai sanyi sosai ya ce. "Ni ne ko?" Ta ɗaga masa kai sai kuma ta fashe da kuka harda shassheƙa tana neman birgima a wajan ya yi saurin dawo da ita jikinsa ta ce. "Abba sai da nace kar ka yi kar ka yi, idan ma zakai ka yi ɗan mitsitsi, gashi ƙafar zata cire me zan faɗawa Ummul?" Ta faɗa da iyakar gaskiyar ta ita bata taɓa ji ko ganin abun mai zafin haka ba, Abban nata ya nemi kashe ne ki yamar da ita gurguwa. Ya shafa kanta fuskarsa a yalwace da kamilallan murmushi daidai kunnenta yana fesa mata zazzafan numfashi ya ce. "Matar malam raki, ba aiwa wajan kashe difa" hawayenta na sauka a ƙirjinsa ta ce "Me ya sa Abba?" Ya ɗauketa bakiɗaya zuwa saman gadon daya gyara kamar bashi ne wanda Yaa Sheikh ya tumurmushi ba. Zai kwantar da ita tayi saurin riƙe gaban rigar shi suka kalli juna ta marairaice sosai ta ce. "A hankali wajan zai yage" Yaa Sheikh ya riƙe yanayin dryar daya kama shi bayan ya kwantar da ita ya cire mata hijab ɗin ta kalle shi ta ce. "Abbana yanzu wannan shi ne sirrin?" Ya juya mata baya ba tare daya biyewa surutun nata ba, dan ya lura hadda san batun zazzaɓi. Daga shi sai Jallabiya ya nufi wani ɓangare babu jimawa ya dawo da tray tayi saurin kallonsa ta ce. "Abba ba allura za kai mini ba ko?" Ya zauna gefen kanta kamar ba zai magana ba sai ya ce. "Ƙafar data yage zan gyara" ta kafe shi da idanu duk da zazzabin dake damunta bai hanata cewa. "Tsakani da Allah wasa nake, leƙo kaga ƙafar a jikina, kar ka yi mini allura kaji Modibbo" Ya saki lallausan murmushi wanda yasa Danejo bin fuskar shi da kallo gani tayi gabaɗaya Abban nata ya ƙara kyau fiye da kullum. Ya lura da kallon mmkin data ke bin shi da shi, ya share tare ɗagota ya jinginata da jikinsa a hankali yake bata tea mai zafi tana sha hannunsa ɗaya a goshinta yana share mata zufa ta shanye shayin tas, ya ɗauki ferfesun naman wanda ya sha romo ya bata shima ta sha sosai, ta ɗauke kai gefe guda. "Ƙara sa, zaki samu ƙarfi" ta ce "Na ƙoshi" ya bata ruwa ta sha ya ɗauki tissue ya goge bakin. Zai kwantar da ita ta saki kuka ta ce. "Modibbo ka barni a nan" ta nuna jikin shi, ya buɗe ido sosai a kanta ya ce "Kin tabbata za ki ji daɗi haka?" Ta ɗaga masa kai, ya gyara mata kwanciyar tare da zagaye hannunsa a cikinta ta ɗora nata hannun akan nasa ta kwantar da kanta a ƙirjinsa. Yaa Sheikh ya yi saurin riƙe hannunta jin tana shafa gashin ƙirjinsa a taushashe ya ce. "Rufan asiri matar malam, azumi fa" ta ce "To, ka goyani Abba jikina ciwo" ya buɗe ido ya ce "goyo kuma?" Ta ce "Eh Abba, ko ka mayar dani wajan Ummul" a hankali ya ce "Ummul ta bar Madina,tana Makka kibar rigimar nan haka Ƴar fillo" ta saki kuka sosai ta ce "Ka goyani ni a bayanka zan barci" ya yi mata shiru. Ta ƙara sautin kukanta wanda rabi duk na rigima ne da neman magana ya riƙe hannayen ya ce "goyo ko?" Ta ɗaga masa kai ya ce. "Done, don Allah matar malam kada naji mganar goyan bakin wani Okey?" Tai masa shiru ya zameta tare da miƙewa tsaye ya shiga kallonta, tai kicin-kicin da fuska ya juya mata baya tare da durƙusawa. "Ga bayan nan" tai masa gwalo wanda yaji hakan a jikinsa yana ji ta haye bayansa tana rungome shi. Ya miƙe da ita kamar ya ɗauki baby bata nauyi gabaɗaya ya tsaya cak ta leƙa fuskar shi ta ce. "Saura zani ai" ya dafe kai ganin ƙaramar yarinya na juya shi kamar juyin waina a tanda ya ce. "Ki nutsu hakan nan" ta shiga zamuwa ƙasa ta ce "Sauke ni kawai Modibbo, baka iya goyo ba gsky" bai kulata ba, sbd yana son a wanye lafiya ya ɗauki towel ya ɗaureta da shi. "Allah sarki Abbana ɗan albarka, idan na samu kuɗi zan baka da yawa" a fili ya ce. "Kin bani abin da ba a taɓa ban ba Kankanata" ta riƙe shi ta ce "Kankana zaka sha?" Ya girgiza mata kai yana biye mata kamar yadda take so ya ce. "Daga yau sunanki Kankana" haka ta dinga Suratu wani ya tanka wani idan yafi ƙarfinsa ya yi shiru. A haka yaji saukar numfashinta a bayansa yana sauka a hankali cike da nutsuwa har lokacin zazzaɓi bai bar jikinta ba. Tarihi ya maimaita kansa rabon daya goyata tun tana shekara biyar a duniya cif. Ƴar rainon shi ta zama gefen rayuwar shi. Ya kwantar da ita yana ganin yadda ta sauya fuska alamar bata so. Ya rufeta sosai yana ɗaukan remote ya ƙaro gudun a.cn baya son yi mata allurar bare ya tasu da rigima shi ma jikinsa duk ciwo yake. Wajan wata box yaje ya danna password dake jiki ta buɗe. Ya ɗauki ducoment da files tare da wani small box ya dawo wajanta. Small box ɗin ya buɗe wani ƙaramin gold ring ya bayyana sai sheƙi yake sosai kana kallonsa kasan an kashe dubban kuɗi a kansa daman na musamman yasa akai masa. Da Alphabet ɗin A&H. Ya kama hannunta ya zare zoben masarauta wanda bai mmkin ganinsa a hannunta ba, yasan duk sharrin Prince Bilal ne. Ya maƙala mata ring ɗin kusa da zoben sadakin da aka ƙwace a Rugar Bello. Ya riƙe ɗan ƙaramin hannun a nata yana kallon yadda zoben ya zauna sosai a hannunta. Ɗaya bayan ɗaya ya dinga kama hannunta yana sign a files da ducoment ɗin daya ɗakko wanda saka hannun ya bada tabbacin komai ya zama mallakinta. Yana gamawa ya mayar ya rufe tare da dawowa ya kwanta kamar jira take ta mirgino jikinsa ya shafa kanta tare da sumbatar goshinta ya rungometa a ƙirjinsa. Cikin magagin barci ta ce. "Malam ɗina, Yaa Sheikh Abbana, Modibbona ɗan albarka" ya riƙe bakin yana sakin murmushi mai kyau ya ce "Shiru Kankanata".. lokacin sallah nayi yake tashi ya nufi masallacin harami yaja jam'i, daman duk wata ziyara da ita yake ta riga data kammala komai na aikin hajji. Ƴar mutum Rome ta dawo Hajiya Halisa Danejo Rome. Suna zaune a parlour gabansa cike da kayan buɗe baki kala-kala, itama tane gefensa kwance akan cinya, hannunsa cikin sumar kanta. Umar-khan ya yi sallama Yaa Sheikh ya fara ƙoƙarin ɗaga Halisa ita kuma taƙi, ya kame fuska sosai tare da amsa Umar-khan. Umar-khan ya nuna kamar bai lura da Halisa ba, zuciyarsa cike da farin ciki ya zauna ya ce. "Barka da shan ruwa Yaa Sheikh,ya ibada?" Ya jinjina masa ya ce. "Ummul na bisa hanya, Father ya ƙara kira akan da an sallame azumi ka sauka a Nijeriya" Kallon da Yaa Sheikh ya kewa Umar-khan ya sa ya ce. "Zahrah na lafiya, har kawo yanzu bata san anga matar malam ba" Yaa Sheikh ya numfasa ya ce. "Oh!" Umar-khan ya maida hankalinsa ga Tafsir ɗin Yaa Sheikh ɗin da ake haskawa a t.v Halisa ta miƙe zaune cikin raɗa ta ce "Abba" bai kalleta ba sbd Umar-khan dake parlourn sai hannunta daya matse ta tura masa goshinsa ta ce "Kiss me" ya ɗora bakin a goshin tare dayi mata kiss, ta murmushi can ta ƙara tura masa goshin ya ɗan kalli wajan Umar-khan yaga kallo yake ya manna mata kiss. Ta juya masa kumatunta nan ma ya yi mata ta ƙara yin ƙasa da murya ta ce "Yaa Sheikh saura nan" ta nuna masa baki ya rausayar da kai irin ta rufa masa asiri ta buɗe baki da ƙarfi zatai magana ya yi saurin manna bakinsa akan nata daidai lokacin Umar-khan ya ɗago kai suka haɗa ido da Yaa Sheikh Umar-khan ya kalli bakin Yaa Sheikh dake manne dana Halisa.Yaa Sheikh ya zame kansa fuska ba walwala Halisa ta kalle shi ta ce "Abba barci zan ka goyani kamar ɗazo bayanka daɗi" Yaa Sheikh ya yi kamar bai ji me ta ce ba, Umar-khan kuma yaƙi tashi shi ma ya ɗauke kai ba tare daya ƙara kallon direction ɗin su ba. Ganin da gaske Halisa na son bada shi a gaban Umar-khan yasa ya sauke numfashi tare da buɗe idanu akan Umar-khan ya ce. "Zan huta" Umar-khan ya ce "Oh! to sai anjima ni ma ina ɗan jira ne, but lemme find my way" ya miƙe yana ce wa. "Lailatan sa'ida, ai ibada lafiya" shi dai Yaa Sheikh bai ce komai ba, Halisa ta buɗe baki zatai magana ya yi saurin rufe bakin da tafin hannunsa. Bayan tafiyar Umar-khan Yaa Sheikh ya sauke ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya. "Naga ka haɗe rai? Ko a kira Umar-khan?" Ya kalleta tare da kallon ƙaramin bakin dake Sarrafa surutu daya ɗagata kuma sai ihu ƙafa zata yage. "To kawai Umar-khan ya dawo muyi hira" Ya riƙe bakin da hannunsa yana shafa labɓanta ya ce. "Ya dawo ki bashi labarin yadda Ayaba tai nutsu cikin kankana?" Itama ta kame bakinsa kamar yadda ya yi mata ta ce. "Ka daina magana babba, ni ban gane me kace ba" Ya cire hannun yana kwanciya kan kujera kansa a armchair ya ce. "Na gane ni" ta ce "Ni ma ka nuna mini mana" ya lumshe idanunsa ba tare da ya ce komai ba, numfashinsa na son fisgewa sbd yadda ta zura hannunta a ƙirjinsa tana shafawa ita kawai bata son ta zauna haka lafiya kamar kowa. Da sauri kamar an tsikarota ta ce. "Abba" ya buɗe ido ya kalli bakin kiran sunan nashi a hankali ya mayar ya rufe ta ce. "Abba ka gani?" Still idanunsa na rufe ya ce "Me?" Ta ce "Kawo kunnenka kaji" har lokacin idanunsa rufe ya ce "Bana jin gulma" ta marairaice sosai ta ce. "Ba gulma zan ba" yaƙi kulata ta barshi ya yi barci abu ya gagara da alama sai ya sata barcin dole. Ta bi jikinsa ta kwanta tana ɗora bakinta a kunnen shi tare da kare hannayenta murya ƙasa-ƙasa a dole raɗa ake masa duk rabi ta zirara masa yawo a kunne garin saurin surutu wanda hakan ke sawa tsigar jikinsa ta shi sosai tana zubewa. "Abba ka gani? Allah yasa baka gansu ba yanzu na tuna" bai gane me take nufi ba bisa dole ya buɗe idanunsa wanda suka fara jirkicewa ya juya mata su alamar "Me kenan?" Da hannu ta nuna masa ƙirjinta dake riga ta ce "Kace baka gani ba" ya kalli ƙirjin ya ɗauke kai zuwa fuskarta ya ce "Me ki ke nunawa?" A son faɗa masa gaskiyar ta ta kama hannunsa tare da mannawa a daidai ƙirjinta. Zuciyar Yaa Sheikh ta bada wani kyakkyawan bugu kansa a sara labɓansa suka shiga rawa ya kasa furta komai. "Wannan nake nufi?" Ya daɗe yana mai da numfashi yaga Allah so take ya zama bita zai-zai ko zaji-talau ko dai irin masan Novels ɗin nan. Ya kame jikinsa daga yanayin da yake ji ya ce. "Oh! Lemon tsami, ban gani muga" ta cire hannunsa tana mai da numfashi ta e "Allhmd, Allah na gode maka" ya riƙe kafaɗunta da kyau ya ce. "bari na gani sai ki gode masa da kyau, bisa lada" ta zame zata gudu ya damƙota ya ce. "Nuna mini" ta maƙale ta ce "kai da ka ke cewa lemon tsami, naƙi barci zan daman" ya ce "Bari na kira Zahrah naga nata" nan da nan annurin fuskarta ya ɗauke hawaye ya cika a idanunta wanda ta kasa riƙe su sai daya sakko ta ce. "Shikenan zan nuna maka, amma ka rufe ido" ya mirgina daga kwanciyar da yake ya ce "Kin so mugunta Kankanata, ni da ba makaho ba" ta langwaɓe kai ta ce. "To je ki kawai, miƙo min wayata" tunaninta Zahrah zai kira jikinta na rawa tayi saurin yaye rigarta tare da ɗagata sama daman ba komai a jikin. "Gashi" Ta ce tana ƙanƙame idanunta kunyar Abbanta ya kamata a karan farko. Yaa Sheikh lissafin ya kunce masa bai tunanin zubin halittar ya kai girman haka ba, bai tunanin zai tsole idanunsa har haka ba, Ya kasa cewa komai idanunsa ya sauya launi ya jirkice bakiɗaya. Ya miƙe da ƙyar bata san da zuwansa ba sai numfashinsa ta ji, ta buɗe ido zata saki rigar ya ce. "No! Haliyserh!!" Ya kira sunan! Taji har tsakiyar kanta kawo yanzu ta fara fahimta da fuskantar komai. Ya riƙe rigar yana kallon zatsarin komai cikin wadataccen hasken dake gidan nashi. Cak ya ɗagata sama ta riƙesa da sauri a hankali cikin dauriya ya ce. "Kankanata haka lemon yake? Ya nuna har haka?" Ta rufe idanunta tana sakin murmushi. Har kan gado ya direta cikin sauri ya shiga bata sabon darasi cikin darasin da bata gama sanin kansa ba. Idanunta ya raina fata shi kansa bai san ya yi losing control ba, ya manta cewa sabon shigace ita a harkar. Kuka ta saki da ƙarfi tana dukansa da cizo a yanzu da gaske ƙafar zai cire mata, tun zuwansa ya daina gani bare fahimta bai niyya ba amma ita ta jawo hakan kuma yana son ta saba da buƙatar shi, bashi da sauƙi a wannan lokacin. "Allahu Akbar, Yasubuhanallah Allahu Akbar" shi ne kawai abin da bakinsa ke furtawa. Bayan daidaitar komai ta saka masa kuka. "Abba da gaske baka so na, zaka cire mini ƙafa wayyo ƙafata" ya fahimci rakinta a fili ya ɗauketa zuwa bathroom. "Sorry Zawja" Ya furta a taushashe lokacin da yake sakar musu ruwa a jiki ta luff tana sauke numfashi, ruwa ya haɗa mata tare da sata ciki yana sata ta fara barci, ji tayi kawai ya fara yi mata wankan ta buɗe ido ta ce. "Abbana" ya kalli idanunta ya ce "Zawja" _"I love You Abba"_ Yaja hancinta ta ce "Kai ma ka ce" ya ce "Na faɗa ai kankana" ta tsare shi da idanu ta ce. "Yaushe" a hankali ya sumbaci goshinta ya sunkuceta bayan ya naɗeta da towel ya nufi bedroom ɗin ya cire bedsheet ya saka wani kana ya kwantar da ita.. Ya koma ya yi cikakken wanka ya sauya shiga zuwa kayan barci ya ɗauki cup mai zafi ya shiga yasan ba zata iya cin komai ba. Tuni barci ya ɗauketa daman ya ce sai sakata na dole. Wayarsa ta fara ringing ganin sunan Mother ya sa ya ɗauka yana sassauta yanayin. "Assalamu alaiki Mother" ta cikin wayar ta ce "Wasallamu Alaika Aliyuna, ya ibada?" Ya ce "Allahamdulillah" ta ce. "Allah ya ƙarba, ina daughter fa?" Jin ya yi shiru ta ce. "Nasan tai barci ko?" Ya lumfasa ya ce "Haka ne, Maimoon,Auta Fattoumah, Nazeeferh?" Mother ta saki murmushi ta ce "Duk suna lafiya, Maimoon ce ma take son magana da Daughter,ya azumin tana yi dai?" Ya sauke numfashi na wasu daƙiƙo ya ce. "Yau ne ba ai ba" ta ce "Allah ya sa lafiya?" Ya saka hannunsa cikin sumar kansa yana jin kansa fresh sosai "Kamar bata jin daɗi" ta ce "To Allah sarki, Allah ya ƙaremu da lafiya" hira suka shiga yi ta ɗa da uwa hakan yaiwa Yaa Sheikh ya ƙara jin sassauci daga abin da yake ji. "Ga Jadda" ta miƙawa Jadda wayar ta ce "Waya ne? daga shan ruwa za a gallabi mutane ban fiya son surutu a goman ƙarshen nan ba" Yaa Sheikh ya ce "Baki mutu ba?" Ta saki salati tana miƙewa tsaye ta ce "Wa nake ji kamar Gadangana?" Ya ce "Ana" ta ce "Allahu Akbar malam jiya ba sai ga Lailatul-ƙadr munyi ido biyu da shi ba?, Harfa kukan daɗi nayi yanzu haka kukan nake ina ƙara bada labarin yadda naga daren shi ne fa aka miƙo mini waya na ɗauka wani ɗan asarar ne ashe Aliyu ne" ya murmusa kaɗan. "Me ki ka roƙa" ta samu waje ta zauna ta ce. "Wlh kai na fara yiwa addu'a, Allah baka zuri'a ta gari Allah ya sa ka samu farin ciki na har abada, Allah ya haɗaka da MACEN SIRRI!" Fili ya ce. "Ƙwayayena sun shiga gida" ta ce "Me ka ce" ya ce "Ubangiji ya amshi addu'ar ki Jadda" ta ce "Wanne tabbaci ka ke dashi?" Ya numfasa ya ce "Ki ka ce Allah ya haɗani da farin ciki? Gashi agefe na" ita bata gane ba. Ta dinga masa surutu kusan halinsu ɗaya da Halisa tai ƙasa da murya ta ce "Ina durinar matar nan ta ka, ta nan dai nono kwance a ciki, nifa nai mafarkin ta haihu ina farkawa mai sadaƙa domin mugun mafarki nai, bana fatan ka haɗa zuri'a da ita" Bayan sun gama wayar ya kira Father harta gama ringing bai ɗauka ba. Ya kira Abba Hakimi vedio call. Wayyo Allah zo kuga shagwaɓa wajan Yaa Sheikh. Ya ajjiye shekarunsa gefe da Abba Hakimi ya tambayi Yaa Sheikh amanar daya bashi sai ya ɗakko wani zancan. Gabaɗaya ya manta da batun wani deal Abba Hakimi ya ce. "Deal ɗin namu ya zo ƙarshe ai, Mai martaba zai taho mini da ƴata" cikin rashin fahimta Yaa Sheikh ya ce "Wanne deal Abba?" Ya yi murmushi irin na manya ya ce. "Deal na riƙon Halisa ko ka manta? Ai baka sonta ita ɗin bisa yarjejeniya na baka ita, da zarar kun dawo zan raba auren" Yaa Sheikh ya yi shiru ya juya ya kalli fuskar Halisa data marairaice fuska ko a barci bata huta da shagwaɓa ba. Ƙit! Ya kashe wayar bakiɗaya yana kwanciya tare da rungometa jikinsa kamar wani zai kwace ta. Da asuba da ƙyar ta tashi sbd gajiya tai wanka da ruwan zafi sosai ta sauya Jallabiya mai hula, shi ma wanka ya yi ya sauka downstairs ya ɗakkota tray ɗin sahur, a tare cikin plate ɗaya sukai sahur ɗin da idanu kawai suke bin juna, shi tunanin da yake daban ita kuma tana tsoran yin magana ya sake maimaita abin da ya yi. Ta gama ta wanke hannu tare da brush ta ɗaura alwala. Shi ma ya yi hakan yasan ta ɗauki niyyar azumi sai ya barta. Lokacin da zai fita Masjid ya jawota jikinsa tare da yin shiru suka rungome juna kamar masu tunani. "Ina son ka Abba" ya kasa cewa komai sai sumbatar goshinta da ya yi. Har ya tafi sai yaji yana son ya tafi masallacin da ita, duk da bata da wani ƙwari da cikakkiyar lafiya da zazzaɓi ta kwana. Ta shirya cikin duguwar riga tai shigar aikin hajji hannunta cikin nasa suka fito harabar gidan driver ya jasu zuwa masallacin. Mutane sun cika kamar ko yaushe daman tuni an sanar da cewa a gobe za a duba watan Shawwal. Ta nufi ɓangaren mata cikin ikon Allah ta haɗu da Ummul suka rungome juna. Bayan idar da Sallah Ummul ta tafi da ita masaukin ta. "Ummul ki yi mini magani ƙafar zata cire Abba ya iya mugunta" da rashin fahimta Ummul ta ce "mugunta kuma?" Hawaye ya sakko mata ta ce "Nace kar ya yi, kar ya yi amma yaƙi jiya ma ya ƙara" kamar Ummul ta nutse cikin ƙasa haka taji, yanzu asirin Malam take faɗa mata. Ta kama hannunta bayan ta haɗa ruwa mai zafi sosai ta ce ta shiga tasa ta gasa jikinta sosai. Ummul ta jata a jiki sosai Soyayyar yarinyar na ƙara ratsa zuciyarta ta shiga mata nasiha da muhimmancin ɓoye sirrin miji. Daga nan barci ya ɗauke ta. Yini guda cirr bata haɗu da Yaa Sheikh shi kuma abubuwan sun ɓoye shi. Tana zaune ita da Ummul bayan ansha ruwa haka kurum ta shiga ɓata rai Ummul ta gane Abbanta take son gani amma bata kulata ba. Ƙamshin Roja ya cika parlourn Halisa ta miƙe da sauri ta nufi inda yake ya dinga girgiza mata kai amma ina. Tana zuwa ta rungome shi. "I miss You Modibbona" Ya kalli direction ɗin Ummul yaga tuni tabar wajan ya jata tare da mannata a jikinsa ya ce. "Kankanata" ya zameta yana zama kan kujera ta zauna saman cinyar shi. Ta fara masa surutu Ummul ta fito hannunta riƙe da tray. Tai kamar ba taga gansu ba, Yaa Sheikh kuma ya rasa abin yi. "Ummul" Halisa ta kira sunanta ta ce "Matar Malam, Abar Malam ya yi buɗe baki" Halisa ta ce "Ummul wlh ina son Abbana, ina son shi sosai na fiki son shi nafi kowa son shi a duniya" Ummul tai murmushi ta ce "Daman, ni mene haɗina da shi da zan so shi?" Yaa Sheikh ya marairaice fuska cikin shagwaɓa da sauya murya ya ce. "Ummul" ta ce "Daɗi naji hau an samu wacce ta fini son Aliyu a duniya" Halisa ta ce. "Ummul ni har kiss nake masa ke kina yi masa? Kuka har goya..." Yaa Sheikh ya yi saurin matse hannunta wanda ya sa tai shiru. Ummul tuni tabar wajan. Ya kalleta yana dafe kai ya ce "Why? Kin san wace ita?" Ta kasa yi masa magana sai kissing bakinsa data shiga yi, ya rufe idanu yaga azumi kala-kala amma bai taɓa ganin irin na yau ba, ya buɗe baki da sumbata ya riƙe fuskarta ya shiga tayata abin da take sunyi nisa suka ji an fasa ihu akan su tare da jin sautin fashewar abu, cikin tsoro da firgitar da Halisa tayi tai saurin rungome Abbanta tana mai da numfashi, a wahale ya shiga buɗe ido kafin ya gama wanin waye akansu yaji anyi kukan kura an cafki Halisa tare da bugata da jikin table.... Littafina na kuɗi ne Ba zan ta surutu a media akan ana fitar mini da book ba, amma kuji tsoran Allah da mai fitarwa, da mai karantawa free. Ku daina raina hakƙi komai ƙanƙantar shi. ₦500 08119237616 Na'ima sulaiman Shu'aibu Nimcyluv sarauta. #Sarautar marubuta #team Yaa Sheikh #team Halisa #team Zahrah #love #destiny #jealousKafin Father ya ƙarasa faɗin sauran mugwayen maganganun na shi akan Mother, cikin Jadda ta yi tsalle ta dire ta ce. "Kana ƙarasa sakin sai dai ka nemi wata uwar bani Jadda ba, ka tabbatar mini kai ba ɗan arziƙi bane wanda ya san addini, ashe baka da imani da taƙawa Ali? Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Duk duniya suna maka kallo mai hankali ashe mahaukaci na haifa bani da lafiya, sai da da jama'a suka dinga samu na, suna cewa nayi hankali da kai, sam banji ba shi ne yanzu zaka nuna mini kai mahaukaci riƙaƙƙe ne kuma?" Father ya kalli Mother ya ce. "Jadda baki san me tayi mini ba, ta nuna ban isa da ita ba ta kunya tani a idanun abokina, tai wa Aliyu aure ba tare da sani ko yarda ta ba a matsayina na uban shi, ta kuma san danginsu Zahrah ba ai musu kishiya" Cikin ihun murna Jadda ta ce "Ka ce Malam ya yi aure? To Ubangiji ya yi miki Albarka Maryam, ita kuma zuza take ko zura ba zan iya masifa ba, Allah ya yi gutsi gutsi da ita da dangin nata, Daman ai cutar Malam sukai na rantse sai da suka buga tabbatiyada kafin su yi maganar aurenta da Malam, mace babu fasali balle tsari har naci ƴan matanci na auri ubanka ban taɓa ganin mai zubin halitta irin nata ba, nono shimfiɗe kamar kamar dindimari ta hau kwalta, ɗuwawun nan tamkar wainar fulawa ta kasko, huhuhu! Azaba Allah dai ya isan Gadanga an haɗi shi da irin bokan irin masifa wannan ba lallai ta san hakƙin aure ba, dole ne na kira Daurawa ko isa Fantami su yi wa ƴar banza wa'azi, Kai kuma ba zan kulaka ba, ba san masifa da kai ba, jama'a su yi ta kwashe mini Albarka sai na fara bincikar ƙwaƙwalwarka, fita kuma babu inda Maryam zata daga nan har Malam ya sauka a Larjeriyya minti nawa ne zuwan" Father ya ce "Jadda yarinyar nan Zahrah kaf Familynsu babu mai iliminta, tayi primary, secondary, N.c.e, degree, H.n.d, master duk wani kwali da ɗan boko yake mafarkin samu ta samu, ba gata akaiwa Aliyu da aka haɗa shi aure da wacce zata kula da dukiyar shi ba? Shi za a wulaƙanta ta, a aura mini ƴar aikinta, to wlh bada yawuna ba, ni nake da ikon zaɓarwa Aliyu macen da tayi mini, Kuma ita uwar ta shi data ɗaure masa gindi ina ita ɗaya ce a gidan aurenta ko nayi mata kishiya ne?" Jadda ta fashe da kuka sosai tana kama bakin zani ta ce "Yanzu daga magana akan la'ananniyar yarinya wacce shaiɗan ya yi wa fitsari aka shi ne ka ke zagina Ali? Ni kake tsinewa ka ke cewa na fitar maka daga gidana ai ba kai kaɗai na haifa ba? Ni ce uwar banza ko ba shakka, sbd Allah ina ruwana da shiga masifar yara daga cewa Malam bai kyauta ba shi ne ka zageni ka zagin uwa da uban da suka kawo ni duniya" ta face majina tayi mitsi mitsi da idanu ta ce. "Maimunatu masa kira mimi Haruna, shi da ɗan uwan shi Ubangiji ya ƙaddara na haifi wasu ba shi kaɗai bane" Father ya ƙarasu wajan Jadda ya ce "Don Allah Jadda kiyi haƙuri wlh ba zagi nayi ba, fushina na sauke akan muna.....," "Idan ka sake cewa Maryam munafuka zaka tabbatar ƴar iska ce ni, fita ka bani wake kada na sake ganin fuskarka a gabana" Mother dai na zaune a kujera kanta a ƙasa ta harɗe hannu a ƙirji sai girgiza ƙafa take, ko ba a faɗa ba kasan cewa ranta ya yi mugun ɓaci. Maimoon ta bawa Jadda waya jin Uncle Haroon ya ɗaga ta cikin wayar ya ce "Maimunatu ƴar Engineer da Barrister ya akai ne ƙawar?" Jadda ta ce "Masifa da bala'i,to kakar Maimunatu ce" ya yi saurin cewa "Barka ansha ruwa lafiya Jadda?" Ta fashe da kuka sosai hankalin Uncle Haroon ya ta shi ta ce "Kana can gidan matanka yaƙi ya ɓarke a gidan Ali, kafin ya kashe ni maza maza na ganka a gidan kai da Bashir, amma dai Ali yaci mini mutunci ya zageni tas zagin da ba a taɓa yi mini ba" ta kashe wayar murya can ƙasa ƙasa ta ce. "Alsulhu khair! Gashi nayi magana a nutse ba faɗa ba ihu, ke kuma Maryam ki barni da shi zai gane ni ba tsohuwar banza ba ce" Father ya kasa cewa komai, gabaɗaya kansa ya kulle kunyar Alhaji Farouk ta kama cinye shi. Maimoon da Zeefa sai kuka suke, Auta Fattoumah tai shiru tare da kafe Father da idanu tana jin zafin shi a ranta fiye da ko wanne lokaci. A kusan tare manyan motoci guda uku sukai parking a harabar gidan, Uncle Haroon daga Zaria road, Uncle Bashir da ga unguwa uku, sai Abba Hakimi daga Dawaki road. Uncle Bashir ya fara fitowa cikin wata dakakkiyar shadda sky blue, sai Uncle Haroon ya fito cikin farar shadda shi ma, gabaɗaya suka tsaya domin gaisawa da Abba Hakimi, Saif-wazir ya buɗewa Abba Hakimi mota, ya fito cikin kyakkyawar tufar shi shadda ruwan madara ɗinkin jamper da babbar riga, ya ɗora hirami akan shi kamar yadda Yaa Sheikh. Suka rusuna bakiɗaya tare da haɗa baki wajan faɗin. "Barka da dare Abba Hakimi, Ya ibada?" Ya saki murmushi irin nasu na manya ya ce. "Allahamdulillah, baƙo na shirin tafiya ya barmu da kewa" duk sukai murmushi Uncle Haroon ya ce "To Allah ya bamu lada ya wanke dattin Laifuka" ya ce. "Amin" Abba Hakimi ya kalli Saif-wazir ya ce. "Ka jira nan" Suka nufi cikin gidan, a main parlour suka samu Jadda zaune, Mother ma na zaune har yanzu bata motsa ko gyara zamanta ba, sai da taji muryar Abba Hakimi ta ɗago kai cikin rauni suna haɗa ido ya girgiza mata kai. Suka zauna bayan sun gaida Jadda ta amsa ba yabo ba fallasa. Mother ta gaida Abba Hakimi dasu Uncle Bashir. "Fatan lafiya ne, wannan kiran gaggawa dare har ya fara" Jadda ta fara matse ƙwalla ta ce. "Lafiyar kenan, ku kira ɗan uwanka kuji dalilin sakin Maryam har saki biyu" Suka saki salati Abba Hakimi ya yi murmushi kawai he's speechless. "Wanne irin saki ana zaune lafiya,saki kuma cikin azumi?" Jadda ta ce "Idan mutum ya fara shan wiwi da tiramol sai abin da aka gani" Uncle Bashir ya miƙe zuwa upstairs ya samu Father na waya daka gani mai muhimmaci ce, yadda yake ta begen. "Ka fito muna jiranka" ya miƙe tsaye tare dabin bayan Yayan na shi. "Wani irin shirme ne haka Aliyu? mai Barrister ta aikata a gareka har haka?" Ka tsaye Father ya ce. "Ta yi wa Sheikh aure ba tare dana sani ba, kuma ta aura masa yarinya mafi ƙasƙanci a idanun Zahrah, daɗin da ɗawa ba aiwa Familynsu Zahrah kishiya na shaida mata hakan, shi ya sa na yanke hukuncin laifukan da tayi mini, kafin Aliyun ya sauka ƙasar" Uncle Haroon ya ce. "Mu kuma sai ka ɗaure mu, tunda mune muka bada shawarar kada ka sani ɗin, mun san da auren tun kafin Aliyu yabar ƙasa zuwa wajan aikin shi, auren Halisa aka fara ɗaurawa kafin na ƴar gaban goshin taka". "Ni dai bada yawuna ba, Aliyuna ɗa na ne" Uncle Bashir ya ce "Sannu mai ɗa, ka faɗa mana wanda bai da zuri'a a nan balle kayi mana gori, ko ɗan kana ne to yanzu ƙarfin ikonmu ya ƙwace Malam daga wajanka" Jadda ta ce "Gwara ya zage ku kamar yadda ya yi mini, abin duka ya ɗauka zai dake ni fa? Uhm uhm Allah kada ka nuna mini masifar dana gani ɗazo" Uncle Haroon ya ce "kaga let by gone be by gone, mu duka ba sa'aninka sa'insarka bane, ba zamu ce komai daga nan har Sheikh ya sauka ƙasar nan, kuma Barrister tana gidan nan ina tabbatar maka za kai ladamar sakin da kayi mata" sai a lokacin Abba Hakimi ya ce. "A'a Inn shaa Allah da Maryamu zan tafi, ya riƙe yaran shi na tafi da ƴar ɗan-uwana" ya juya kan Mother ya ce. "Ta shi ki shirya" Uncle Haroon ya ce "Baza ai haka ba Abba Hakimi, ko sbd su Fattoumah" Abba Hakimi ya miƙe ya jima da sanin Father ba ɗan ƙwarai bane son rai dana zuciyar shi kawai yake bi. Mother ta kwantar da Auta Fattoumah saman kujera, ta nufi bedroom ta ɗauki mayafi waya da hand bag sai kayanta dake torelly bag. Maimoon ta dinga kuka tana rungome Mother. Mother ta kasa cewa komai idanunta ya yi jaa ta nufi Main parlour. Abba Hakimi ya kama hannun Mother suka fice daga gidan zuciyoyin ko wannensu babu daɗi. Da ƙyar aka samu jinin dake zuba a hannun Yaa Sheikh ya tsaya, akai masa Allura baya son magani shi kuma sai dole, Zuciyar Halisa ta ɗauki zafi haka kurum taji har Abban nata zafin shi take ji, don mai zai bari wata banza tana faɗa masa magana kuma ta gaji ta ɓoye batun auren su. Ta shige ɗaki ta kwanta sai kuka take, cikin dare ta kasa barci ta dinga juyi ta saba da jikin Yaa Sheikh. Ta dubi lokaci taga ƙarfe 2:30 na dare, ta miƙe a hankali jikinta sanye da farar night gown kanta ba kitso, ta saka slippers har ta fita sai ta dawo ta ɗauki perpumes ta fesa, ta shiga fitowa a hankali. Ta samu Ummul zaune saman kujera a main parlour hannunta riƙe da casbawa. Suka kalli juna ta ce "Lafiya ki ka fito a daren nan?" Ta ce. "Wajan Abbana zani" maganar ta girmi Ummul ta ce "Ina jin ya yi barci fa?" Halisa ta kalli Ummul ta ce "Bana jin Abbana ya yi barci tun da ni ma na kasa" kunya ta kama Ummul ita kam oganniyyar ko a jikinta. "Koma to, tunda baki san yadda zaki riƙe Abban naki ba" Halisa bata gane ba, bada son ranta ba ta juya Ummul ta bita da idanu, dole ta gyara mata zama shi namiji a rayuwa bashi da tabbas idan kullum zaka sakar masa jikinka haka yake buƙata, amma dole ta koyi yadda zata dinga juya Yaa Sheikh duk da bata da haufi a kan shi. Babu jimawa da tafiyar Halisa Yaa Sheikh ya fito cikin ash ɗin Jallabiya mai ƙaramin hannu a wannan karan bai ɗora hirami ba, sumar kansa mai kala biyu ta bayyana. Mamaki ya kama Ummul ta ɗauka tuni ya yi barci ya dawo kusa da ita ya zauna. "Bakai barci ba Arɗo?" Ya jinjina kai ya ce "Bana ji Ummul" ta ƙara gasgata zancan Halisa ashe da gaske duk ba za su iya barci ba juna ba? Yaushe sukai wannan mugun sabon har haka? Ta share shi tana kallo yana duba ɓangaren Halisa amma baya da ikon zuwa sbd zaman Ummul ɗin,ai kam kamar daga sama su kaga ta sake fitowa. Da sauri ta ƙarasu ta ce. "Ummul daman nace ba zai iya barci ba" ta faɗi hakan tana nufar Yaa Sheikh ya yi saurin rufe idanunsa sbd nauyin Ummul yake ji. Halisa ta zauna saman cinyar shi tare da kwanciya jikinsa ta rungome shi ta ce. "I miss You Modibbo" Ummul ta miƙe domin tuni salatin ya ƙwace mata ta ce. "Allah ya kyauta" tana barin wajan Yaa Sheikh ya sunkuceta yana mannata da ƙirjinsa duk da ciwon hannunsa ya ciji fatar kunnenta kaɗan ya ce. "Kankanata, yau ban sha ruwa ba" ta lumshe idanunsa tana jin soyayyar shi na ƙara haɓawa tare da tunɓasa a zuciyarta tana yaɗo ta ko wacce ƙofa dake zuciyarta.. Washegari tun Subhi ya farka ita kam kasa motsi tayi har yanzu ta kasa sabawa da yanayin Abban nata kullum da salon da yake zuwar mata. Yau take sallah, an sallame azumi mutane Al'ummar Annabi kowa yana haramar tafiya masallaci, ranar da ko yake jiran zuwanta farin ciki a fuskar musulmai ba a magana.. A hankali yake sakkowa cikin wata dakakkiyar shadda fara tas sai ɗaukan idanu yake, ya ɗora Alkyabba jikinsa wani irin sahihin kyau ya yi na musamman, bakinsa ɗauke da tasbihi na tafiya masallaci. "Allahu Akbar, Allahu Akbar, la'ilaha illallah! Allahu Akbar khabira, Walahamdulillah kasira, Wasubuhanallahi bukuratan wa'asila" a fili yake faɗa har ya sakko ƙasa. Ya samu Umar-khan cikin sabbin tufafi, sai Mai martaba Ahmad Sarki da El-bashir tare da Ummul. Kafin kowa ya yi magana idanunsa ya sauka akanta ta fito cikin duguwar riga fara sol da ita ta yi rolling kanta da veil ba wani make up tai ba, amma tai wani kyau mai ɗaukan hankali bakinta sai kyallin lips lamp yake, ta ƙara girma da kyau da haske ko'ina na jikinta ya buɗe. Idanunta rufe ba tare data lura da su Mai martaba ba ta nufi wajan Yaa Sheikh. A hankali ya furta.. "No kankana bar Abba" shi kaɗai ya yi maganar shi kaɗai kuma yaji tana zuwa ta faɗa jikinsa ta rungome shi tana riƙe hannun ta ce. "Kafi mazan duniya kyau Abbana, ina son ka da yawa" Suka ji saukar maganar Mai martaba ya ce. "Abbanki dai ki ka sani, amma ko ni ai nafi shi kyau" Yaa Sheikh dai ya kasa cewa komai ita daman Ummul tasan za a rina. "Da gaske Abbana mai kyau ne Mai martaba, banda abinka ai kai ka tsofa" Umar-khan ya ce. "Kuma ke ki ke kiɗanki ki ke rawar ki, Yaa Lee bai ce kinyi kyau ba" Yaa Sheikh ya fahimci kowa shi dai bai isa an saka ya faɗi abin da bai niyya ba.. "Kafin nace ya yi kyau shi ya fara faɗa ai" "Mu bamu ji ba, yaushe akai haka?" Ta ce "Idanunsa sune suka faɗan, Modibbo ka faɗa yanzu kowa yaji kaga suna tsokanata Please kace nai kyau" gabaɗaya suka gyara zama, sun san da Kamar wuya gurguwa da auren ne sa. "Abba ka ce, ka faɗa musu na yi kyau zan yi fushi idan ka ƙi" nan da nan zufa ta fara yanko masa harshensa ya harɗe ya shiga ƙoƙarin yin magana ya kasa, cikin ƙarfin hali ya ɗan buga ƙafarsa a ƙasa ya riƙe kafaɗunta da kyau kamar zai kuka cikin In-ina ya ce... *Allah ya nuna mana Monday lafiya, mai son posting har* *weekend zai ƙara adding 500 a saka shi a Special grp* *08119237616*Kamar zakin dake neman kalace tsayin shekaru haka Zahrah ta ƙara damƙar Halisa cikin tashin hankali kiɗima da gigita kamar mahaukaciya sabon kamu, kafin ta kamata Yaa Sheikh ya yi saurin miƙewa tare da riƙe hannun Zahrah yana tsareta da idanu ya ce. "Lafiya? Me tai miki?" "Kan ubancan! Ni ka ke tambaya ko lafiya Aliyu? Ban sani ba amma idan na nakasata sai ka gane manufata tayin hakan" ta faɗa tana cire ɗan kwalin kanta gabaɗaya idanunta ya rufe ta mance batun cikin dake jikinta wanda ya gama bayyana kansa a zahirance. Ta ƙara kai wa Halisa damƙa Yaa Sheikh ya ƙara tarewa idanunta ya jirkice masifa da wutar ɗaukan fansar cin amanar da Halisa tai mata sune kaɗai abin da ake hangowa cikin Idanun nata. "Wallahi sai na kasheta, na ga uban wanda ya tsaya mata da har ta nemi cin amanata, yarinya ƙarama ta zama karuwarka?" Halisa ta leƙo ta bayan Yaa Sheikh idanunta ya yi jaa sosai sbd bugewar da tayi amma taƙi kuka sbd tsabar dauriya da ƙarfin zuciya! Cikin rawar murya ta ce. "Ni ba karuwa ba ce, kuma tambayi Abbana kinji" tana faɗin haka ta koma bayan Yaa Sheikh da sauri tana riƙe ƙugunsa sbd kukan kurar da Zahrah tayi ta ce. "Ni ce ajalinki ko uwarki tayi kaɗan ta shiga sabgar mijina balle ke, daman talaka bai iya neman zama ba, taimako ya zame mini masifa yanzu Aliyu ka rasa dawa zakai iskanci sai da ƴar aikina? Ni zaka wulaƙanta a idanunta? Daman da yawan malamai duk ƴan iska ne" Halisa ta ƙara leƙowa ta ce. "Abbana ba ɗan iska bane, ke ce dai" Da ƙarfi Yaa Sheikh ya bugawa Halisa tsawa ya ce. "Haliyserh!" Cikin sauri ta shiga nutsuwarta ta koma bayansa ta ce "Kayi haƙuri Modibbo" Zahrah ta lailayo wani ashar ta ƙunduma gabaɗaya kanta ya ɗaure ta kasa fahimtar abin da yake faruwa ko yake shirin faruwa, tunaninta ya tsaya zuciyarta na ɗagawa Allah ya gani tana son mijinta akan Yaa Sheikh zata iya komai. "Kai cuceni daka bawa wannan tsinanniyar yarinyar abin da nake fata da burin samunsa daga gare ka, sai na zama ajalinta kuma sai na faɗawa duniya irin zaman da ka ke da ƴar aikin ka, ka mayar da ita karuwar ka, ka fake da addini kana aikata zini aban ƙasa" kamar da ga sama suka ji Ummul ta ce. "Matar ƙwarai bata taɓa faɗar sirrin mijinta" kafin kowa ya yi magana Halisa ta ƙara leƙowa ta bayan Yaa Sheikh ta ce. "Shi ya sa ban faɗin darasin auren da mukai da Abba ba, har ya ce sunana kankana" Yaa Sheikh ya dafe kansa abin da yake ta gudu kenan gashi ta kasa sarrafa bakin nata. "Kankana?" Zahrah ta faɗa a bayyane cikin ɗaure kai! "Eh kankana Anti Abbana ya ce ina da zaƙi" a wannan karan Yaa Sheikh ya kasa jurewa sbd tsananin kunyar Ummul dake binsu da idanu tayi mutuwar tsaye, yawun bakinta ya ƙafe. "Zan naka saki kuma zama a gidan mijina ya ƙare ki koma can wajan muguwar uwarki wacce bata iya haihuwa ba, daman ko sisi ban taɓa aika mata mata ba" Jikin Halisa ya yi sanyi idanunta ya cika da hawaye ta ce. "Kada ki sake zagin Dadata" a hargitse Idanun Zahrah har rufewa yake sbd masifar dake cinta ta ce. "Naci uwar data haifeta bama ita ba, dan kaza-kazanta" Halisa ta fito daga bayan Yaa Sheikh ta ce. "Idan ki sake ni ma zan rama, ke ki ka ɗakkoni har Rugar Rome, bada son raina ba, mene laifina da zaki dinga jifana akan abin da bani da laifi? Idan kishi ne ya saki hakan, wannan ba kishi bane hauka ne, kuma duk kishinki baki kama ƙafata ba, ina son mijina fiye da yadda ki ke son sa, ina son Abbana, ina son Modibbona kada ki sake zagin wanda ya zame mini garkuwa akan idanuna" Ummul ta girgiza da jin maganganun Halisa masu cike da hikima kuma a nutse Yaa Sheikh tsaye ya yi ya kasa cewa komai, ban yi tunanin ranar zata zo nan kusa ba, duk da ya kwana da sanin cewa dole Zahran zata san gasky soona or later. Zahrah ta rasa a wanne tubali zata saka zancan na Halisa wanda da tunaninta ya kasa fahimtar da ita komai. Cikin rashin fahimta ta ce. "Waye mijin naki? A gidan uban ki kai auren? Ko maza ki ka fara bi shi ne ki ka biyo ta kan mijina? Ko dai takari ki ka zama?" "Ai ko giwa ta faɗi,ta fi ƙarfin Allah sarki, ko yanzu goma ta zube tafi biyar albarka" Halisa ta juya kan Yaa Sheikh tare da riƙe ƙugunsa cikin ƙasa da murya wacce shi kansa bai santa da ita ba ta ce. "Abbana ka shaida mata ni matarka ce, ta daina cin zarafin biyayyar da Dada ta bani, ka faɗa mata ba zaman haramci muke ba, ta daina lalata maka sunanka, _I love You so much Sweetheart Abbana_" Yaa Sheikh yaja numfashi ya kasa riƙe mmkin da take shayar da shi ya yi saurin riƙe hannunta. Kafin ya yi magana Ummul ta fasa ƙara ta ce. "Aliyu, Halisa!" Ta faɗa cikin fargabar yadda taga Zahrah ta zari plate ɗin glasses wanda yake shaƙe da fruits ta yo kan Halisa. Yaa Sheikh ya yi saurin juyar da Halisa ta koma cikinsa ya rungometa sosai. Tass! Sautin saukar Glasses ɗin akan Yaa Sheikh ya runtse idanunsa sbd sosai ya shigesa jini ya fara zuba. "Ka faɗa mini wace ita, ka faɗa mini matsayinta kada ka sake bakinka ya ambace ta matsayin matar ka" Yaa Sheikh bai iya hayaniya ba, bai san ya ake ba, amma dole ya nuna mata shi namiji ne tsayayye a gidansa.. Kansa na zubar da jini ya juya zuwa gare ta ya ce. "Matata ce, halaliyata, abu mai daraja na bayar na sameta ki sassauta maganganun naki akan ta" jiri ya kwashi Zahrah tayi baya luuu! Ummul tai saurin tare ta, domin ta lura abin da abin da yake jikinta. A zafafe ta kai hannu ta ɗauke Ummul da marin. Kafin ta sauke hannunta taji saukar maruka a jere har sau uku, marin daya sanya tayi zaman ƴan bori a ƙasa, ɗan cikinta ya motsa sbd faɗuwar da tayi. Idanunta ya cika da hawaye ta nuna Ummul da hannu ta ce. "Akan wannan ƴar aikin taka ka mareni Aliyu? Wannan matar wacce bata isa na haɗa inuwa da ita ba?" Yaa Sheikh yanayinsa ya sauya ya ce. "Mene? Ƴar aiki fa ki ka ce, to ita ɗin" Ummul tayi saurin rufe bakin Yaa Sheikh ta ce "Aliyu! Wannan duk bai dace ba, kada kaga laifinta ko wacce mace zata iya aikata haka idan har tana son mijinta, balle batun kishiya lokaci guda" Zahrah ta fashe da kukan baƙin ciki ta ce. "Don Allah kada kayi mini haka Aliyu, kada ka haɗani kishi da wacce nafi tsana a rayuwa sama da komai, idan ka ƙi yarda wlh zan kasheta mahaukaciya ce ni akan soyayyarka" Halisa ita ma ta fashe da kuka ta riƙe Yaa Sheikh ta ce "Ina son ka ni ma Abbana, idan na tuna Anti Zahrah matarka ce ina jin kamar na ɗauki wuƙa na cakawa kai na" Kafin su yi magana Zahrah ta miƙe a sukwane ta nufi inda taga wuƙa kamar zautacciyya ta nufi wajan Halisa ta ce. "Na kashe ta, na kashe ka Aliyu, na kashe kai na gabaɗaya ma haɗu lahira ai mana hisabi, nasan ni ce da riba" Halisa ta firgita ta fasa ihu ganin yadda Zahrah tai kanta da wuƙa, kafin ta caka mata Yaa Sheikh ya saka hannu ya tare wuƙar ta sauka a hannunsa jini ya fara zuba. A ruɗe Ummul ta ce "Modibbona, Aliyu, Arɗona" ita kanta bata san ta faɗa ba, ta kama hannun Aliyu wanda yake zubar da jini ta cire wuƙar da ƙyar ta ce. "Kana kallo zata kashe mini kai, ba zan iya ba Aliyu wacce matar ƙaddara ce da bata iya ɗaukan ƙaddara?" Sai a lokacin jikin Zahrah ya yi sanyi ganin yadda wuƙar tai rami a hannun Yaa Sheikh. Halisa ta riƙe Yaa Sheikh cikin kuka ta ce. "Abbana me ya sa zaka tare mini, akai na take faɗan nan, idan zata kashe ka akai na, gwara ka rabu..." Ya saka hannu ya damƙi hannun Halisa idanunsa akan Ummul ya ce. "Ummul shirya ki fito, ke kuma taku ɗaya ki ka ƙara bare ki fita akan igiyoyinki" Ummul ta juya ta shirya tare ɗakko jakarta. Har ya fita ya tsaya ya ce "kin ce ƙari ya fito miki, amma baki duba yanayinki ba?" Ya fi ce a hanya ya ci karo da Umar-khan, ganin yanayin ya sa Umar-khan kiran Dr a waya. Gabaɗaya suka shiga mota,kuka sosai Halisa take kamar ranta zai fita, Ummul ta riƙe hannun Yaa Sheikh ta naɗa masa wani gyalle amma har lokacin jini zuba yake.. A haukace Zahrah ta dinga jifa da komai na parlourn ta shiga fasa Glasses ɗin ko'ina dake parlourn ta jiwa kanta rauni gabaɗaya ta zama abar tausayi. "Ina son ka Aliyu, wallahi ina son ka" sai surutai ta ke. Ta ɗauki waya ta kira Deen ta faɗa masa komai da sauri ya ce. "Gani nan zuwa" cikin kuka ta ce "A'a kada kazo, ka bani hasken yadda za mu yi da yarinyar" Deen ya ce "A kasheta kawai" ta ce "Kasheta kawai, kayi duk yadda kayi tabar duniya" ta kashe wayar tana ƙara sautin kukanta..... Cikin sauri Father yake tako steps ɗin benen zuwa downstairs "Maryam, Maryam" ya shiga kiran sunan Mother wacce ta gama cire henna ɗin da akai mata, ta miƙe tana kallon Maimoon ta ce "Maimoon je ki duba kayan aikin da aka kawo, ina son kammala komai cikin daren nan kafin gobe idi" Maimoon ta ce "Tom" Maimoon ta nufi kitchen wajan da ake aikin abincin sallah, mother ta nufi inda take jin Muryar Father. Gabanta ya faɗi sosai ta ce "Engineer lafiya ka ke wannan kiran?" Ya nunata da hannu ya ce. "Munafuka, magulmaciyya, makira shaiɗaniyya" shi ne kalaman da Father yake jifan mother dasu, a sanyaye ta ce. "Me nayi maka ka ke jifana da wannan maganganun Engineer? Lokaci na samun lada ka mayar matsayin na data husuma?" Ya tare ta da faɗin "Dole ki ƙasƙantar da kan ki, saboda abin da ki ka aikata" ta ce "me na aikata har haka, a wannan watan na samun lada da rahamar Ubangiji me nayi maka Engineer?" Ya jinjina kai yana ƙwafa ya ce. "Da haɗin bakin ki Aliyu ya yi aure? Auren ma ƴar cikinsa mai aikin Zahrah?" Mother tai murmushi ta ce "Oh! Akan haka ka ke ɗaga murya? to! Bani naiwa Sheikh Aure ba, duk da ina niyya faɗuwa ce ta zo daidai da zama" ya ce "Ƙarya ki ke, daman kinyi iƙirarin mata biyu zai aura, kin yi abin da ki kai niyya kuma ki ke so, ni ma zan yi abin da naga dama" Mother ta ranta ya fara ɓaci bata son ta ɗaga murya sbd su Maimoon ta ce. "Zaka iya, amma ka sani bani naiwa Aliyu aure ba, auren shi da Halisa tsarin Ubangiji ne" Father ya haura sama ba tare da ya ce komai ba. Jikinta a sanyaye sbd musayar yawun da tayi da mijinta cikin azumi. Ta dawo Main parlour da sauri Auta Fattoumah ta ce. "Mother ke da waye?" Mother ta ce "Ban son surutu Fattoumah, kije ki kwanta zaki sallar idi gobe" kafin Fattoumah tai magana Father ya sakko tare da cillowa Mother paper ta ce. "A cikin daren nan, ki tattara kayan ki, ki bar mini gida, na sake ki saki ɗaya ni da ke sai a hanya kada ki tafi da yara ko ɗaya" saki cikin watan Ramadana, Innalillaha wa'inna ilahir raji'un! Ta miƙe idanunta cike da hawaye ta ce "Me kace Engineer kamar saki naji?" Ya juya hannunsa riƙe da key ya ce "Na sake ki Maryam, na sake ki Maryam ki Bama ɗaya ba na sake ki saki biyu!... *Am sorry ina ta samu matsala ban kula ba, sai yanzu dana dawo baya ina karantawa, nace aikin Hajji maimakon Oummara! Please bear with me ba aikin hajji bane, muna watan Ramadan ne omara ce. Ita kuma Omara ko wanne lokaci, ko wanne wata ana iya yinta.*Domin ƙara tabbatar da abin da zuciyarta ke faɗa mata ya sanya ta ɗaga hannu tare da shafa kamilalliyyar fuskar shi, Hannunta ya sauka a kwantaccen gemun shi mai laushi. Tsoro ya ƙara kama Halisa tayi saurin tashi zata miƙe ya riƙe ta sosai numfashinsa na sauka a hankali yanayin fitar numfashin kaɗai zai tabbatar bashi da lafiya, A ruɗe ta kira sunan shi cikin sanyin murya ta ce "Abba" ya yi shiru yana sauke numfashi mai zafi Ganin bai amsa ba kuma bai da niyya ta amsawa ya sanya ta miƙa hannu, Zata kunna socket ɗin dake gefen gadon. A hankali cikin murya mara hayaniya ya ce "Ban son haske" "To Abba" was yadda ya yi mata magana. Sukai shiru na wani lokaci ta ce "Yaushe kazo? Ina ne Ummul taje?" Sai a lokacin ya yunƙura daga kwancan da yake har time ɗin yana riƙe da ita, ya gyara mata zama bisa tattausan cinyar shi. ya fesar da numfashi cikin wani irin sabon yanayi na kasala ya manna gemunsa a wuyanta. Ta sauke numfashi tana riƙe kafaɗar shi. "Nazo ne ki nemi yafiyata" tayi saurin cewa "Yafiya kuma?" Ya jinjina mata kai har lokacin fuskarsa ɗaure take. "Kina cikin fushin Allah, dana Manzon shi haɗi da Mala'iku"Halisa ta zare idanu domin ita bata san babban laifin data aikata Har haka ba, wanda yaja mata fushin Ubangiji. "Me nayi Abba, taya zan jure fushinka bare na Ubangiji?" Ya sauke numfashi a hankali ya zura hannunsa ta ƙasan rigarta ya cusa fuskarsa tsakanin wuyanta yana shaƙar wani sahihin ƙamshin, Wanda yake sanya shi ya yi over acting ba tare da ya yi niyya ba, a nutse ya buɗe baki tare da manna softness lips ɗin shi ya lashi wuyanta, Tayi saurin zabura sbd tsigar jikinta data tashi haɗi da zubewa, a karo na biyu ta ƙara riƙe shi muryarta na rawa ta ce. "Wayyo Abba" Ta faɗi hakanne sbd wani sumbata da ya yiwa fatar wuyanta tare da ɗan cizawa, a hankali yake bin gabaɗaya wuyanta da hot kisses masu zafin gaske da tsayawa a rai, Ita kanta tayi kewa to ya rayuwarsu zata kasance idan sukai nisa na wani lokaci? ganin yadda Yaa Sheikh yake komai a gaggauce yasa ta san yau ba sauƙi. Bai kuma nemi hanyar bi ta sauƙi ba, jikinsa ya ɗauki zafin zazzaɓin masassara dake damun shi. Ya zame fuska tare da komawa jikin frame ɗin bed ɗin ya jingina yana sauke numfashi. "Laifin me na yi Yaa Sheikh? Mena aikata wanda Ubangiji ke fushi dani?" Da ƙyar ya ware idanunsa ya watsa a kanta yana son gasgata cewa da gaske bata son laifinta ba? Ko faɗa kawai take. "Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce, kada ku sake ku fita ba tare da umarnin mazajanku ba, domin sune ku ke ƙarƙashinsu, hadisi ingantacce" Ya ɗago bakiɗaya tare da manna fuskar shi a nata fuskar ya zagaye ƙugunta da hannayensa ya goga mata tsinin hancinsa "Why?" Hawaye ya sakko mata ta ce "Mai martaba ne Abba, nace zan faɗa maka ya ce a'a" Yaa Sheikh ya dinga kallon bakinta da yadda hawaye ke zuba cikin idanunta kafin ya ce. "Anya kin nemi hanyar rabauta da aljanna?" Kuka na son fashe mata ta ce "Kayi haƙuri ban sakewa ka yafe mini" ya sauke numfashi yana komawa jikin frame ɗin ya kwanta idanunsa lumshe. Ta matsa har ruwan cikin shi tana wasa da sumar ƙirjin shi ta ce "Abbana kayi haƙuri" ya yi mata banza ita kuma shirun nasa ne bata so, ta lura yau a sama yake da yawan lokaci tana mamaki yadda amsa sallama ke masa wahala da kuma yadda yake sake mata suke magana. Yanzu dai ba Abbanta bane a gabanta, asalin Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu take gani. Maganganun Abar suke dawo mata, tayi saurin kwanciya saman shi tare da yin flat a hankali ta kama hannunsa ta manna a ƙirjinta na daba wani irin kukan shagwaɓa da sangarta ya ƙwace mata "Yaa Sheikh susa mini danna mini ƙirjina baffi ciwo yake mini" lokacin ƙanƙani ta rikita shi ya yi iya yinsa ya kasa kame kansa da son nuna bai damu ba, amma Halisa sai faman manna hannunsa take saman ƙirjin tana kuka tare da ƙanƙame idanunta. Jikinsa na rawa na wutar data kunna ga zafin zazzaɓi ya mirginata zuwa ƙasa, idanunsa rufe ya ɓalle bra ɗin tare da yin wurgi da ita gefe guda, tsit! Kukan ya ɗauke maimakonsa taji tausar hannu sai taji ana yi mata ta baki, ta rufe idanu sosai sbd zafin da ƙirjinta ya ɗauka, Bai taɓa yunƙurin kai bakin shi wajan ba sai yanzu, ta fahimci dalilin shi nayin haka sbd mugun son abun da yake,yana kuma tsole masa idanu ainun. Ta faɗawa ƴan mutan Rome, da dukkan Fulanin dake cikin Rugar. A yau ta fahimci da ɓangaren Abba kawai take kallo, amma yau Yaa Sheikh ne gabanta babu tausayi ba zaka taɓa cewa ya kwana biyu cikin harkar ba, yadda yake yi tamkar yanzu ne me yasan daɗin auren. Ta saki kuka sosai lokacin daya mirgina gefenta, a hankali cikin nutsuwa na mutuwar jiki ya ɗagota bakiɗaya zuwa jikinsa ya rungume abar shi sosai ya shiga bubbuga bayanta alamar rarrashi amma taƙi yin shiru, ya ciji kunnen tare da kisses skin ɗin wajan yana hura mata iska ya ce. "Meye na kuka kin cinyewa Mother ɗan ta" ya sauke numfashi "Abin da ki ke so ne, sai kiyiwa Malam godiya" Ta saki kuka ta ce "Kuma na yau yafi na kullum" a hankali shi ma ya ce "Na haɗa da hukunci ne" ya gyara yanayin murya ba wasa ya ce "Haliyserh!!!!" Gabanta ya faɗi jin kiran da ya yi mata. "Na'am Yaa Sheikh" ta furta a sanyaye tana kwantar da kanta a ƙirjinsa, hannunsu cikin gashinta yana ya motsawa ya ce "Fita ko nan da gate sai da umarnin Abbanki, balle barin ƙasar rabauta nake nema miki" ta jinjina kai ta ce "Ba zan sake ba, ka yafe mini" ya maƙale kafaɗa kamar yadda tayi yana son kuyi da Annabi akan jan iyali tare da yin wasa dasu bisa sunna. "Zanyi sai anyi abu ɗaya" ta ce "me zan yi?" Ya nuna mata wuyan shi ya ce "Kiss" ya ɗora bakin tare da yin kiss kamar yadda ya ce. Ya ƙara nuna mata tsakiyar ƙirjinsa ya ce "Kiss" nan ma tayi ya kalli cikin idanunta tare da nuna mata marar shi ya ce "Kiss" ta zare idanu sosai ta kalli wajan ta ce "Aba...." Ya tare ta da faɗin "riƙe abinki na riƙe yafiyar, Aljanna nake tayaki nema" ta runtse idanunta sosai kunya ta kamata a hankali ta ɗora baki wajan suka sauke numfashi a tare Yaa Sheikh ya yi saurin riƙe sumar kanta. Tai kisses a wajan kafin ta ɗago ya danna kanta yana faɗin "Ubanmu, sarki wanda ya sanya mana numfashi a gangar jikinmu, ka bamu lafiya da iskar shaka ba tare dako sisi ba, ina roƙo kayi ma Diƴar Sheikh albarka,ka tsare mutuncin Matar Malam!" Tayi saurin rufe ido tana rungome shi ta ce. "Amin Abbana" ya shafa kanta kawai ta ƙara cewa "Abba baka taɓa cewa kana so na ba, me ya sa ko dai baka so na?" Ya yi shiru ta riƙe hannunsa ta ce "Abba ko akwai wani abu ne?" Ya riƙe hannun ya ɗora daidai saitin zuciyar shi, sosai taji ƙirjin shi na bugawa kamar zai fito. "Ba kowa zai gane ba, ki nutsu ƙilan ke ki fahimci Abbanki" ta kasa ajjiye maganar shi a ko wanne ma'auni, kiran sallar farko na asuba ya fargar da Yaa Sheikh ya zame ta yana miƙewa tare da saka jallabiya har ya yi waje sai ya dawo da baya ya zuba mata gajiyayyun Idanunsa ta miƙe tsaye a yanayin da suke ta taka har zuwa inda yake. Kamar haɗin baki ta nufe shi, shi kuma ya buɗe hannun shi da sauri ya saketa yana faɗin. "Ki kula, ki fahimta,kuma ki yarda da Abbanki, ki riƙe amana" Tabi bayan shi da kallo tai murmushi tana shigewa cikin toilet ruwa mai sanyi ta haɗa tai wanka ta tsarkake jikinta Ta shirya cikin duguwar riga fitted gown ya atamfa ciganvi. A can masallaci mamaki ya kama su Abba Hakimi sbd jin muryar Yaa Sheikh yana jan jam'i cikin daddaɗar muryar shi,bayan an idar da Sallah Yaa Sheikh ya tsaya tafsir. Abba Hakimi ya kalli Umar-khan ya ce "Lafiya Umaru? Saukar yaushe?" Umar-khan ya ce "Abba ƙarfe 2:5 muka shigo gidan nan, Father ya matsa da kira" Abba Hakimi ya jinjina kai ya ce "Ina ita ɗaya matar Aliyun fa?" Ya ce "Umma tasan mun dawo, ita ta bata bedroom ta kwana" Abba Hakimi ya ce "Ba laifi, ka cewa Engineer ina son ganin shi by 10" Mai martaba da El-bashir da Ishaq-Hakim jinsu kawai suke. "Banga Saif-wazir ba?" Ishaq-Hakim ya ce "Saif baya ƙasa ai, amma ya ce yau zai dawo ko gobe" a haka suka shiga cikin gida, Abba Hakimi ya zauna parlour Umma A'isha ta kawo masa coffee mai zafi sun jima suna tattaunawa. Mother ce ta fito daga bedroom cikin kyakkyawar shiga ta light blue ɗin lace mai kyau hannunta riƙe da mug ta nufi ɗakin Halisa, kwance ta ganta tana barci na gajiya sai ta ajjiye cup ɗin tare daja mata ƙofa ta fita. 9:30 ya fito cikin dakakkiyar shadda sai ɗaukan idanu take kalar sararin samaniya babbar riga da ƴar ciki, ya ɗora hirami akan shi, ya fito a cikakken Malami kuma Yaa Sheikh ɗin shi. Mother ta bisa da kallo ta ce "Saukar yaushe Haydar?" Ya nemi waje kusa da Abba Hakimi ya zauna yana rufe idanu for some minutes ya ce "Jiya da dare" ta ce "Ikon Allah, bari na kawo maka coffee" ya duba agogo ya ce "Allhamdulillah,zan duba ɗalibai na" sai a lokacin Abba Hakimi ya ce "Anya? Muna da meeting ka jira, kaje kazo da Zahrah da Halisa" Mother ta kalli Abba Hakimi ta ce "Halisa na barci" ba tare daya kalleta ba ya ce "A tashe ta" ta ce "to" ta miƙe ta nufi bedroom ɗin. "Malam Aliyu ko baka ji ba?" Without saying anything ya miƙe kai tsaye wani bedroom ya nufa, a tsaye ya samu Zahrah tana ganinsa ta ce "My Excellency" ya dubeta sosai ganin yadda ta faɗa ya ce. "Lafiya ki ke?" Ta ƙarasa inda yake ta ce "Bana jin daɗi, maybe ƙarin ke damuna" cikin kulawa da son sauke nauyin dake kan shi ya ce "kamar lokacin aikin ya yi, sai aje asibiti, Allah ya sauwaƙa fito" ta ɗauki ƙaton hijabi ta saka hannunta a gaba tana kare cikinta. Fitowar su ya yi daidai da shigowar Father, suka kalli juna da Yaa Sheikh father ya kalli Zahrah bai ce komai ba ya shige zuwa parlourn. Lokacin Halisa ta shigo ta saka hijabi tana zaune ƙasan carpet, Yaa Sheikh ya zauna, Mai martaba haka, suna zaune Uncle Haroon ya shigo da Uncle Bashir. A wannan lokacin ko breakfast basuyi ba, Abba Hakimi ya buɗe taro da addu'a kafin ya numfasa ya ce. "Engineer Aliyu ka takura Akan auren da Malam ya yi, har ka saki babar shi saki biyu, akwai laifi ne?" Father ya ce. "Yasan da cewa ba a yi wa familyn su Zahrah kishiya, kuma babu umarni na da sahalewa ta cikin auren da ya yi, infact am not interested for the married" gabaɗaya suka kalli Father. "Amma ba hujja ba ce kace ba yiwa Familynsu kishiya, faɗar Ubangiji cewa. وَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تُقْسِطُوا۟ فِى ٱلْيَتَـٰمَىٰ فَٱنكِحُوا۟ مَا طَابَ لَكُم مِّنَ ٱلنِّسَآءِ مَثْنَىٰ وَثُلَـٰثَ وَرُبَـٰعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تَعْدِلُوا۟ فَوَٰحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰٓ أَلَّا تَعُولُوا۟ Kuma kai awa duk wannan ayoyin kace ba za ai kishiya ba? Bayan Ubangiji ya halarta yinta,kuma Malam nada wadatar riƙe su? Anya Engineer ka ɗauki hanya mai ɓullewa kada ka shiga lamarin Ubangiji" Father ya ce "Haka ne duk abin da kace Abba Hakimi, amma ba haka mukai da iyayenta ba, idan harni na haifi Aliyun dole ne ya rubuta takardar saki yanzu agaban kowa ya bawa yarinya ita kuma ta nemi mijin aure" Uncle Haroon ya ce "Ikon Allah, kai ka ke da iko ko kuma Yaa Sheikh? Idan kuma akwai idda ko ciki fa?" Father ya ce "Bare ma babu, na tabbatar da haka" "Mene hujja?" Cewar Uncle Bashir, Father ya ce "Sbd Zahran ta shaida mini Aliyu bashi da lafiyar zama da iyali" Yaa Sheikh ya ɗago da sauri ya kalli Zahrah itama ta kalle shi. Halisa ta miƙe tare da yin waje da gudu ba zata iya zama akan idanunta a rubuta mata takardar saki ba. "Kuma Wallahi idan Aliyu ba saki Halisa ba sai na tsine masa" Zahrah tayi saurin cewa "Ina son Yaa Father kada ya barni" ya ce "kwantar da hankalin ki" Abba Hakimi ya ce "Ni kuma idan har Aliyu ya buɗe baki a yanzu ya ce yana son Halisa zai zauna da ita wlh Engineer kayi tsararo kasa ya saketa, ruwanka bai kai tsaiko ba" Ya juya kan Yaa Sheikh dake zaune ya kasa cewa komai ya ce "Nasan akwai yarjejeniya tsakaninmu, amma nasan ka riƙe amana tunda ance baka da lafiya, idan har ka faɗa mini yanzu a gaban kowa kana son Halisa a yanzu zan baka ita ka koma Madina ko ka nufi gidanka da ita, kana son Halisa kana son zama da ita matsayin mata da miji?" Waje ya yi shiru Yaa Sheikh ya kasa furta komai sai zufa dake yanko masa. Da gudu Umar-khan ya shigo ya ce. "Yaa Lee Halisa..." Mother ta Mike tana faɗin "Mai ya sameta?" Ina Yaa Sheikh tuni ya yi waje bai tsaya jiran jin komai ba, Umar-khan ya ce "El-bashir ya ya ɗauketa, yaja mota sunyi waje akwai matsala" suka ɗauki salati. Gabaɗaya sukai waje, suna fita harabar gidan motar Yaa Sheikh na fita daga gate. Cikin sa a ya hango motar El-bashir ya ƙara gudun tashi, ta cikin madubi El-bashir ya hango motar Yaa Sheikh ya yi murmushi yana sakin dariya, burinsa ko zai mutu ya kashe Halisa ya ɗauki fansar abin da Yaa Sheikh ya aikata masa shekarun baya. Ihu sosai Halisa take tana kiran sunan Dada da kuma Yaa Sheikh, da ganga El-bashir ya saki kan motar gabaɗaya ta nufi wajan wata ƙaruwar tirela sukai aran gama, motarsu Halisa ta kifa ta ƙara kifawa a hankali ta gangara ta tsakiyar titi ta daki wani ƙaton dutse....Kukan jaririn ya dakatar da Jadda daka shigewa cikin parlourn, ta tsaya cak hannu riƙe da zanin dake neman faɗuwa a jikinta ta ce. "Yaushe A'isha ta samu ciki ni ƴar nan? Ciki tsofe-tsofe kamar a zamanin baya?" Mother ta kasa magana al'ajabi ya kamata, me zata gani haka? Cikin da aka ce cuta ce a cikinsa daga nishi sai suji kukan Jariri? Umma A'isha murmushi kawai tayi, kasancewar ta babba mace mai hangen nesa, Ya sa kallo ɗaya da tayiwa Zahrah ta fahimci ciki gareta, Tayi shiru ne sbd bata da ikon yin magana akan abin, babban dalilin yadda Engineer ya shaida akan idanun kowa ta ce Yaa Sheikh bai da lafiya zama da mace, to ina cikin ya samu? "Masifa da bala'i kowa ce ƴar banza taci kanta ina magana ko wacce tai kunnen uwar Shegu, nace yaushe ne A'isha ta yi ciki har aka haife shi yanzu? Kuma banda asara duk faɗin gidan nan sai a parlour zata baje mazaunai ta haihu?" Daga Umma A'isha har Mother suka kasa cewa komai, bakinsu ya kulle ganin Zahrah na neman danne jaririn ya sa Umma A'isha faɗin. "Maryama zare babyn ki yanke cibiyar" Mother ta ce "To!" A sanyaye jiki ba ƙwari. Sai a lokacin ne kuma Jadda idaniyyar ya sauka akan Zahrah ta hangame baki, idanunta ta buɗe domin ƙara tabbatarwa da gaske Zahrah ce dai ta haihu, ta miƙe tsaye tana yin mitsi mitsi da idanu kafin ta ce "Me zan gani ɗan shege cikin gidan Hakimi, la'ilaha illallah Muhammadur Rasulullah s.a.w rabon dana ɗan shege ido da ido tun ina budurwa da tsautsayi ya rutsa da ƙawata, to wallahi ba a gidan nan ba, daman tun kallon farko nasan idanun yarinyar nan a tsakar ka yake, faɗa ne kawai ban ba, taje can ta buɗewa gantalallun masa mazauna sun sha bidiri da bushasha, sunyi hajji da umara akan shi, bawai ashe da karuwa muke zaune, ashe shararriyar ƴar hannu aka aurawa Malam to Allah ya isa" Umma A'isha ta ce. "Kiyi haƙuri mubi komai a sannu, babu tabbacin abin da Zahrah ta haifa bashi da uba, auren Aliyu take ba kuma a gidan shi take zaune. "A'a kada ki fara kada ki sake, wlh rufe idanu zan naci biki mutunci muddin zaki goyi bayan iskanci ga zahiri, gabaɗaya wata nawa da bikin? Bai fi wata huɗu bane ina ji fa? Ko bakwaini bai isa a haife shi yanzu, balle ga Muryar jaririn nan yadda yake inya ko ni ba zan iya buɗe maƙogaro nayi haka ba" Umma A'isha ta jinjina kai, itama ta yarda da batun Jadda amma baza su yanke shawarar hakan ba, dole a bincika. "Bari Hakimi yazo, sai anyi maganar komai a nutse" Jadda dai sai kaɗa ƙafa take tayi ƙwafa tare da zabga Salati ta ce. "Ɗan shege ne wallahi" Mother ta duba Zahrah taga bata buɗe ba ta ce "Da sauƙi bata samu ƙari ba" caraf Jadda ta ce "Ina zatai ƙari abin da ya zama kamar rariyya? Tun tuni ƴan iskar suka mayar dashi ƙofar waika" kunya ta kama Umma A'isha amma ta kasa cewa komai. Zahrah Tunda ta samu kan ta haihu taji kamar an zare mata gabaɗaya ciwon dake damunta, ta rufe idanu ta kasa motsin kirki bata taɓa jin kunya a duniya irin yau ba. _“What should I do?”_ Ta tambayi zuciyarta abin ya zo lokacin da sam ba tayi tsammani ba, Umma A'isha ta naɗa kyakkyawan jariri fari tas dashi cikin showel, Mother ta goge wajan tas ta zuba turare ta kunna boner tare da air-con. Da taimakon Mother Zahrah ta miƙe suka nufi bedroom ɗin da take ciki, ta haɗa mata ruwa mai zafi sosai duk abin da mai jego ke buƙata akai mata. Bayan mother ta fito daga ɗakin Zahrah ta nufi nata bedroom ɗin direct number Abba Hakimi ta kira, ta jima tana ringing kafin a yi picking call ɗin cikin kamala ya ɗaga yana faɗin. "Maryama ya akai ne?" Ta sauke numfashi kaifi ta ce "Abba ya jikin daughter dana El?" Ya juya ya kalli Halisa wacce har lokacin bata farka ba hannunta riƙe dana Yaa Sheikh da tun ɗazo yake ɗakin yaƙi cewa kowa komai akan maganar daya furta ɗazo. "Allhamdulillah, fatan lafiya?" Ta ce "Abba akwai matsala nan gida, idan babu damuwa abar Umar-khan wajan El-bashir, ku taho yanzu har Malam ɗin" Ya yi jim! Na wani lokaci kafin ya furta "Allah ya a jisshemu alheri, gamu nan" ta ce "Amin, Ishaq ya ƙara sa boutique ya siyo mana baby set na kaya, da oil, Pampers, everything na baby dress kuma baby boy" "meke faruwa Maryam?" Mother ta ce. "Abba ka bari ka ƙarasu, idan ka gani za kafi yarda, yanzu ba lallai ka yarda ba" ya ce "To ba shakka,gamu nan" har zai kashe wayar ta ce. "Abba" "what again Barrister?" Ta ce. "Muna buƙatar Engineer a wajan Please" Abba Hakimi ya yi shiru kafin ya ce "Bana son fitina a Maryam" ta ɗan marairaccen masa tunda kamar uba yake a wajanta ta ce "Ka yarda dani, just trust me" bai ƙara magana ba ya kashe wayar. Abba Hakimi ya juya ya kalli Yaa Sheikh kafin ya ce. "Ta shi muje, zuwa anjima ka dawo ko?" Ya ɗaga kan shi ya kalli Abban nashi sai kuma ya jinjina kai ba tare da ya ce komai ba, Abba Hakimi ya fita. A sanyaye cikin nutsuwa yana jin komai na jikinsa na sauyawa ya ƙara damƙe hannun Halisa hannunsa ɗaya dafe a goshinta wanda tunde ya zauna yake mata addu'a yana tofa mata.. Ya ɗora fuskarsa akan nata His breath fell gently on her face,Not everyone understands the situation he is in, the only one who understands is lying in a hospital bed. Idan labɓansa sun kasa furta abin da zuciyarsa ke son bayyanawa, yana da yaƙinin ita zata gane, kuma zata fahimtar da Abba Hakimi, a lokuta da dama yana yunƙurin furta wannan kalmar mai daraja a gare ta sai ya samu kan shi cikin sarƙewar harshe. Ya goga mata tattausan gemunsa a fuskarta yana jin yadda ta sauke ajjiyar zuciya ya kalli bakinta gabaɗaya lips ɗinta sun bushe, gently kamar mai tsoro ya ɗora bakinsa akan nata ya shiga kissing nata, can ƙasar zuciyar shi addu'a yake karantawa ya tara yawu fal bakinsa na addu'ar ya juyewa mata cikin nata bakin. Ƙut! Sautin shigewar yawun ya bayar a hankali ya sumbaci goshinta kana ya ɗora bakinsa daidai wuyanta ya jima yana kissing fatar wuyan da dukkan zuciyar shi.. "Wow, I've been looking for someone who can kiss like that for a long time, irin wannan sai malamai" Khalil Ahmad Sarki ya faɗa yana ƙarasa shigowa cikin room ɗin. Yaa Sheikh ya zame fuska yana haɗe rai sosai lot looking at his direction. Khalil ya yi dry sosai yana buga cinya kafin ya ce. "Stop pretendinglike you didn't do anything, take your time. And enjoy, tuzuru kamar Malam Aliyu ya samu ɗanyar yarinya ƴar Fulani sai abin da muka gani" Yaa Sheikh yaƙi cewa komai da sauri kuma ya rufe tafin ƙafar Halisa da bargon asibitin, a tsari nashi babu abin da za a gani a jikin iyalinsa sai fuska itama dan ta zama dole ne. "Da alama an yiwa zuciyar Malam mugun kamo, naga alamar ya kusa zama jani talau" sai a lokacin Yaa Sheikh ya ware gajiyayyun Idanunsa akan Khalil ya ce. "Kamar amaryar a lalle?" Khalil ya saka dry ya ce "Ai ba kamo na aure ba, kamo na zuciyar data kamo da soyayyar wani, _Love of the opposite sex_" "To akwai wanda na taɓa cewa ban so?" Khalil ya ce "Eh, babban misali ƴar fillon nan kace baka sonta, ƴar ce wajanka, auren dole ne fa ko ka manta" Yaa Sheikh ya kame fuska yana yin gaba ya ce "True love, between heart to heart, ka daina munafurci Khalil Ahmad Sarki, Ubangiji ya yi hani da shi" "Ba batun munafurci, nafa ɗauka zanga ka rame ka fita hayyacinka, kasan auren dole masifa ne" Yaa Sheikh ya tsaya cak tare da juyawa suka kalli juna sai kwarjinin Yaa Sheikh ya cika idanun Khalil, kusan age mate ne tsakanin Yaa Sheikh da Khalil shi ya sa yake yawan jan Yaa Sheikh da hira,wani lokacin ya biye masa wani lokacin ya share. Ga mamakin Khalil sai yaji Yaa Sheikh ya ce. "Wanne kalar so ka kewa Oum Juwairah? yaushe kuka haɗu" Khalil was silent trying to remember the time, day, month, and year. "I can't remembering, but a school muka haɗu, time ɗin shekarunta 20" Al'ajabin ganin murmushi mai laushin cike da kamala a fuskar Yaa Sheikh ya kusa zautar da Khalil ya ce. "What make you laugh?" Suna tafiya a jere sun jima kafin Yaa Sheikh ya ce. "Shirmen Khalil, ka kwatanta da yarinya da akan idanunka aka raini cikinta, ka raɗa mata suna, ka goyata a bayanka, ka raineta da hannayenka, ka kalli Kyakkyawa fuskarta ta yarinta ka ce _IDAN BA KE_ ba zan iya rayuwa ba, ya zaka kwatanta da Oum Juwairah?" Khalil ya ce "Tab, to ai ba zan iya haɗa son ta dana ko wacce ƴa mace ba, zan ce mata IDAN BA KE ba zan ƙara aure ba" Yaa Sheikh ya girgiza kai ya ce "Ka ɗauka idan ba ita babu rayuwar wanda ya reneta ne, ba komai ake bayyanawa ba, wani abun sai dai gangar jiki tayi aiki" Khalil ya saki baki domin ya gama ƙaddara wa ba Yaa Sheikh ne gabansa ba, yafi masa kama da Yaa Lee. Har suka ƙarasa harabar asibitin Khalil ya kasa cewa komai. Suna zuwa suka shiga mota, daman zuwan Khalil ƙasar kenan, Abba Hakimi da Mai martaba a mota ɗaya, Umar-khan ya jasu domin El-bashir yana barci. Ɗaya motar kuma ta Yaa Sheikh Khalil ya shiga masanin driver Yaa Sheikh bai fiya driving ba sai dole, motar da Khalil ya shigo da ita asibitin kuma tun ɗazo Ishaq-Hakim ya tafi kai saƙon mother. Kasancewar Khalil baya driving a hankali duk da faɗan Yaa Sheikh amma sai da ya riga su Umar-khan zuwa, cikin sa a yana sauka motar su drivern su Maimoon na sauka. "Am lucky wallahi da rabon zanga amaryar dake wahalar da zuciyata" Yaa Sheikh ya taɓe fuska ya jima da sanin Khalil na son Maimoon amma taƙi bashi dama. Suka fito kai tsaye Yaa Sheikh ya yi cikin gida suka jera da Abba Hakimi da Mai martaba suka zama kamar wasu abokai ko sa'anni. Naomi tunda ta hango Khalil ta haɗe fuska ya ƙarasa yana cewa. "Autar Mother an girma" Auta Umar-khan ta ce "Ina yini Uncle K" ya ce "Lafiya" Zeefa ma ta gaida shi ya ce "Maza ku shiga anjima samu shopping amma banda mara gaida mutane" Maimoon ta ƙare haɗe fuska ta ce "Ina yini Uncle?" Ya haɗe fuska ya ce. "Yana kwano, ni ki ke bawa wahala ko Moon?" Ta tura baki ta ce "Me nayi kuma?" Ba wasa a fuskarsa ya jingina da jikin mota yana harɗe hannu ya ce. "Saboda ina son ki? Shikenan na haƙura kije ki auri wanda ki ke so, nima zan nemi wata, be happy" maimakon tai farin ciki sai yaga ta sunkuyar da kanta ƙasa hawaye na zuba a idanunta. Ya saka hannu ya tallafo haɓarta ya ce. "Meye kuma? Na ɗauka farin ciki zaki yi?" Ta fashe da kuka ta kasa cewa komai. Ganin ba mutane a wajan ya miƙa mata hannu ya ce "Zonan" kanta a ƙasa ta ƙarasa wajan shi sai kuka take kamar yarinyar, ya riƙe hannunta ya ce. "Ya akai? Meye na kuka Prince guda kince baki son shi ba dole na haƙura ba" ita dai Maimoon kuka kawai take ya riƙe hannun ya ce. "Ok tell me, do you love me? Do you want to marry me?" Ta kasa cewa komai ta yi saurin shigewa jikin shi tana kuka, ya saki dariya yana rungometa ya ce "Oh! Ina ganin halin kwailaye ni Ibrahimul-khalil" Shiru parlourn ya ɗauka, Abba Hakimi, Mai martaba, Father wato Engineer Aliyu, Uncle Haroon, Uncle Bashir, sai Oga Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu! Ɓangaren mata kuma, Mother, Umma A'isha, Zahrah, sai Yaya Halima, tare da Jadda wacce ta kafa ɗauri a gaban goshi kaɗan take jira. Aka kasa samun maiwa su Abba Hakimi bayani Jadda ta miƙe ta nufi bedroom ɗin Zahrah baby boy ɗin na barci cikin kwanciyar hankali ta figaloshi tana Asstagafirullah! Na taɓa ɗan shege da tayi. Tana zuwa ta ɗora jaririn a kan cinyar Zahrah ta ce "Ubangiji kawai nake tsoro ba wani shege, a yau idan Malam bai saki Zura take kowa wallahi ban cika ƴar banza ba, kuma duk abin da aka kashe na aurenki sai an biya, tunda cakawa Malam akai, ashe dauɗa aka bashi raguwar masu gajeren wando" ta girgiza kai ta ce. "Na rantse da zatin Ubangiji nafi shekaru arba'in rabon da naga ɗan shege sai yau a gidan Hakimi" Abba Hakimi ya kalli Umma A'isha ya ce. "Meke faruwa Aishatul-humaira?" Umma A'isha ta sauke numfashi ta ce. "Matar Yaa Sheikh ce ta haihu ɗazo, yaro namiji" Da sauri Father ya kalli Zahrah wacce take kuka sosai. Yaa Sheikh ya yi ƙasa da kan shi, Abba Hakimi ya yi ta jinjina kai. Uncle Haroon ya ce. "Ikon Allah, haihuwa kuma bakwaini kenan?" Jadda ta ce "Wanne bakwaini? Shekararran ɗa a ciki, kalli fuskar yaron da kyau, da ƙyar bai gado iskanci a ciki ba" "This is complicated, Sheikh kasan da cikin ne?" Yaa Sheikh ya yi shiru can ya ce. "Ku tambaye ta" Uncle Haroon ya ce "I'll do the same thing har sai ka ban amsa, kasan da cikin Zahrah" Yaa Sheikh ya ce. "Eh" gabaɗaya suka kalli Yaa Sheikh Father ya ɗaga hannu zai ɗauke Yaa Sheikh da mari daga bakin ƙofa aka ce. "Kada ka kuskura hannunka ya sauka akan ɗana Engineer Aliyu" suka kalli bakin ƙofar zumbur Mother ta miƙe tsaye tana nuna matar da hannun ƙirjinta na ɗagawa kamar zata shiɗe ta ce "Ummul-khairy!" Ummul tai murmushi hannunta riƙe da key ɗin mota, Abba Hakimi ya kalli Ummul da kyau kaifi ya ce. "Ɗanki kuma?" Ta ƙarasa shigowa ta nemi waje ta zauna ta ce. "Na katse muku hanzari ko? Ku gama sai muyi magana daka baya" Father ya ce. "Ni da ɗan dana haifa a cikina za kice ɗan ki?" Ummul ta girgiza kai kawai ta juya kan Zahrah ta ce. "Kin tuna magana ta? The day you slapped me, you insulted Aliyu's grandfather, nace zan nuna miki ikona a lokacin da ki ka san wacece ni, In sha idan harni na haifi Arɗo a yau zan baki divorce paper ya zauna da zaɓin zuciyar shi" Father ya miƙe cikin faɗa da ɗaga murya ya ce. "Ke awa? Ni nake da ikon saka Aliyu ya yi abin da nake so bake ba, ɗana ne mallakina ne" Ummul ta juya ta kalli Mother ta ce "Barrister Maryam me ya sa kika ɓoyewa mijinki, while I doesn't f****** care" ta juya kan Father ta ce "Tunaninka me? Biyayya Yaa Sheikh ya yi maka, baka san cewa kafin ya amince sai daya samu yarda ta ba? Na maka uzuri" Abba Hakimi ya gaji da jin duk wannan maganganun ya ce. "Zahrah ɗan waye a hannunki" cikin kuka ta ce "Yaa Sheikh" Jadda ta miƙe tare da dungure kan Zahrah ta ce. "Annamimiyya to Allah ya isan malam Alkur'an" "Aliyu? Kin tabbatar ɗan Aliyu ne?" Ta jinjina kai ya ce "Ya akai kuma kika san Aliyu bai da lafiya? Kuma yakai ɗan ya zama na Aliyu bayan mu'amala bata taɓa haɗa ku ba" ta fashe da kuka sosai ta ce. "Don Allah Abba kayi mini alfarma idan na faɗa maka gaskiya ba zaka bar Yaa Sheikh ya sakeni ba, don Allah Abba wallahi zan iya mutuwa idan babu Aliyu nayi ladama" ya jinjina kai ya ce "Inaji" ta share idanuna ta ce. "Ba ɗan shi bane, lokacin da mukai aure ina da cikin wata huɗu" Jadda ta hangame baki ta kasa cewa komai. Ta ɗora da faɗin. "Nayi ƙoƙarin ganin na samu mu'amala da Yaa Sheikh domin na ɗora alhakin cikin akan shi amma ya rusa duk wata ƙofa, har maganin sha'awa na zuba masa wanda na tabbatar ba zai iya jurewa ba sai ya keɓe da mace,amma bai kulani ba, Ummul ke sanar dani ai bashi da cikakkiyar lafiyar ɗa namiji sai na faɗawa Father" ta rushe da kuka sosai ta ce. "Don Allah Ummul kada ki rabani da mijina don Allah Kiyi haƙuri" Ummul murmushi kawai take. Father kunya ta mamaye shi, ya kasa haɗa idanu da kowa tashin hankalin shi bai shige yadda Ummul ke iƙirarin Yaa Sheikh ba ɗan shi bane. Abba Hakimi ya sauke numfashi ya ce. "Aliyu ya akai Halisa ta zama ƙanwar El-bashir?" Yaa Sheikh ya yi shiru Ummul ta ce. "Bari kaga babbar hujja sai ka gasgata da idanunka" ta miƙe tare da fita, wata iriyar zabura Mai martaba ya yi dashi da Umma A'isha lokacin da sassanyar muryarta ta ratsa cikin parlourn.... Littafin kuɗi ₦500 08119237616 Mai son posting har weekend 1kBa iya su Mai martaba ba, hatta Mother ta girgiza da ganin wacce ta shigo, wani abu yake shirin faruwa mai kama da almara banda haka yaushe zasu ganta a daidai wannan lokacin? Abba Hakimi ya sauke numfashi yana girgiza kansa da son tabbatar da abin da idanunsa suke gane masa, da gaske ita ce. Har kawo lokacin Mai martaba bai gasgata abin da ƙwayar idanunsa ke gane masa ba, ya ƙarasa gareta yana mai gyara Alkyabbar jikinsa. Idanu cikin idanu wato eyeballs to eyeballs. "Fulani" Mai martaba ya furta cikin rawar murya yana riƙe hannunta, ta dai kalle shi ta kasa cewa komai amma irin kallon da take masa yafi kama da kallon wanda ka sani shekara da shekaru. "Fulani ke nake gani, da gaske ke ce?" Farin cikinsa ya kasa ɓoyewa har bai san lokacin daya rungometa ba a gaban mutanan ya ce. "Allhamdulillah! Lallai Ubangiji ya yi gaskiya,duk wanda ya yarda da Allah to zai isar masa, you're still alive. Zuciyata bata yaudareni ba da kullum take faɗa mini kina raye saɓanin wasu da ki ka zama matacciya a idanunsa, Shukru ilaika Ya Allah" Ya saketa a hankali har lokacin bata ce komai ba, kamar bata gama dawowa daidai ba, duba da yanayin yadda take kallon mutane. Umma A'isha ta ce "Nana idanuna ke gane mini ikon Allah, da gaske ke ce Nana?" Gabaɗaya idanunta ya cika da hawaye bata taɓa tunanin zata ƙara saka ƴarta a cikin idanunta ba, Wacce ake ta magana a kanta sai binsu take da kallo zaka ɗauka bata taɓa saninsu ba sai yanzu. "Besty" Ta ce tana nufar inda Yaa Sheikh yake zaune shi ma yana binta da idanu, tana zuwa ta zauna kusa da shi tana riƙe hannunsa ta ce. "Besty where is my daughter, ina Danejona take?" Abba Hakimi ya yi murmushi mai sauti ya ce "Idan duniya da gaske daman bai ci a manta Besty ba" Sai a lokacin Ummul ta saki murmushi itama tana bin su da idanu kafin ta ce "Ta ya ya zata manta wanda yake kula da ita da wanda ya reni yarinyarta?" Uncle Haroon ya ce "Na kasa fahimta, kuyi mini dalla-dalla, Khadijah ba cewa akai ta ɓata ba? Ina aka sameta aure ta sake har ta samu yarinya kamar Halisa? Ya akai Yaa Sheikh ya san inda take, kuma ya akai Aliyu ya auri Zahrah bayan yasan akwai cikin wani a jikinta? Meye dalilin El-bashir na son kashe jininsa, Ya akai Yaa Sheikh ya zama ɗan matar nan bayan gabaɗaya mun Shaida ɗan gidan Engineer Aliyu ne da Barrister Maryam? A fitar da zuciyata daga cikin zullumi wallahi kai na kulle kamar wani drama haka nake ganin abin" Ummul ta ce. "You don't have to be worries, i think this is the right time daya dace gaskiya ta kuri ƙarya, kowa kuma ya san abin da yake ɓoye, duk abin da zai je ya dawo ku ɗauka tsararre ne daga Ubangiji, hukumu lillahi ya tsara komai a lokacin daya so, ya kashe wanda ya so, ya kuma raya wanda ya so, kada muyi baƙin ciki, har abada ba zan taɓa amsar Arɗo daga wajanku ba, ina son dai kuyi mini adalci akan abin da zan faɗa muku" Ummul is an educated, beautiful, intelligent woman in the community. Mother ta riƙe hannun Ummul cikin kuka ta ce "Don Allah ki rufa mini asiri Ummul-khairy, Wallahi ina son Aliyu kada ki rabani dashi, ina jinsa kamar ɗan dana haifa a cikina" Father baya gane karatun da ake idan hankalin shi ya yi duba to ya tashi. Ummul ta ce. "Kada ki damu Barrister, kawai ina son nunawa Engineer ƙarshen shi da yake son tirsasa Aliyu yin abin da bai niyya ba, nayi imani da Allah ko kai ne ka haifi Aliyu to a wannan karan ba zai iya yi maka biyayya wajan sakin Halisa ba" Tai shiru tana sauke numfashi ita kanta zuciyarta babu daɗi a hankali ta ce. "Ka tuna lokacin da matarka ta haihu acikin asibitin Specialist Yola dake Jimeta?" Father ya jinjina kai yana furta. "I remember the day, we went to visit Yola" Abba Hakimi kallon Ummul kawai yake sai yanzu ya lura gabaɗaya nutsuwarsu ɗaya da Yaa Sheikh, har yarda take juyawa hannunta da yadda take son tankwashe ƙafa lokaci zuwa lokaci kuma tana son girgiza kai musamman idan abu ya bata mmki, ko acikin wayayyun mata masu tarin ilimi da wahala a samu kamar Ummul-khairy Abdullahi Abdul-majeed. Ummul ta miƙe tsaye sai kuma ta zauna ta ce. "A wannan rana ni ma ina cikin Specialist Yola, lokacin ina ɗauke da cikin Aliyu rayuwa ta mini zafi, bana da kowa mijina daya kasance Arɗo cikin Rugar Bello Allah ya yi masa rasuwa, wanda kuma kashe shi akai akan wani cikar buri, iyayena sun yi nesa dani, infact bana cikin Familynmu sbd fushin da mahaifinsa ya yi, baya son Abou-Aliyu ni kuma na kafe shi nake so, ya ce naje idai auren Fulani ne zan gani, lokacin da mukai aure da Abou-Aliyu Arɗon Rugar Bello ban sha wahala ba, mun rayu cikin farin ciki walwala kwanciyar hankali da jin daɗi, ban taɓa ɓatan wata ba. Rana tsaka Arɗo ya shigo gida da ciwon ciki a ranar bai kwana da rai ba, gari na wayewa aka naɗa sabon Arɗo, a cikin satin ciki ya bayyana a jikinsa, na fara shiga wata sabuwar rayuwa, nasha wahala da taimakon Ubangiji na raini cikin nan, ranar haihuwa a daddafe naje asibitin Specialist Yola dake ina da file acan, aka amshe ni ina shiga kuma aka shigo da Barrister Maryam itama tana naƙuda, mu duka mun sha wahala mun ɗauka ba zamu kai labari ba, cikin ikon Allah Barrister Maryam ta haihu kuma namiji amma ya zo babu rai, sakamakon duguwar naƙuda da ruwan da babyn ya sha a ciki, tana Haihuwa ni ma na haihu, kyakkyawan jariri duk da wahalar rayuwar da muka sha amma girman Aliyu ya bani tsoro, sumar kanshi har rufe ido take saboda yawa, tun a lokacin sumar kan nashi kala biyu ne, nayi farin ciki amma na kasa bayyana shi a fili, a lokacin tunanin yadda zan kula da shi kawai nake, na lumshe jajayen idanuna zuciyata cike da zullumi a hankali na kalli Barrister Maryam na ce. "Ina tunanin addu'a za mu yi da Ubangiji ya sauke mu lafiya, baƙin ciki bai kamace mu ba" cikin kuka ta ce. "Dole nayi kuka, baki san tsayin shekarun dana ɗauka ina addu'ar Ubangiji ya bani ciki na haihu, saboda uwar mijina ta takura mini tana tunanin ni juya ce, gashi Allah ya amshi addu'a ta kuma Ubangiji ya amshi abin dana haifa" Nayi murmushi kawai ina sauke ajjiyar zuciya mai nauyi kafin na furta. "Riƙe Babyna idan kina so bani naki wanda ya rasu" bisa mamakina sai naga Barrister Maryam ta tsorata komai take tunani a lokacin ohu! Kamar na shiga ranta na ce. "Kada kiyi kaddama, ki ɗauka ɗana Aliyu shi ne wanda zai kawo daidaito tsakanin ki da uwar mijinki, mu duka muna cikin damuwa bani da hali bani da ikon kula da Aliyu, bani da wadatacciyar cimar da zan samu ruwan nonon shayar da shi, wandon da zan sakawa Aliyu bani dashi, ina da zuciyar nema da tawakkali amma a wannan karan na gaza, na bar miki Aliyu duniya da lahira na bar miki shi, ki ɗauka shi ne ɗan da ki ka haifa yanzu, ni kuma Ubangiji zai bani wani a lokacin da ya so" ni kai na nasan na faɗi hakan ne, akan rashin mafitar da bani da ita, da kuma son nemawa Aliyu kyakkyawar makoma, ilimi, nagarta, kyakkyawar tofa. Farin cikin Barrister Maryam ya kasa ɓoyewa da sauri ta amshi Aliyu,ni kuma na ɗauki babynta, babu wanda yasan abin nan sai mu uku, ni, ita, da kuma wacce ta amshi haihuwarmu" Ummul tai shiru tana sauke numfashi idanunta ya yi jajir, ta ɗago kai taga kowa kallonta yake anyi shiru ana sauraranta. Yaa Sheikh kallon Ummul ɗinsa kawai yake wacce itama take kallon shi. Khadijah Dada tana kusa da Yaa Sheikh taƙi matsawa, ƙuruciyar shekarun sun motsa yadda take very close da Yaa Sheikh koda iyayenta Abba Hakimi Umma A'isha ba tayi, sun tasu tun suna ƙanana. Ummul ta ɗauki ruwa ta sha kafin ta ɗora da faɗin. "Ban san cewa kuskura nayi ba wajan sadaukar da jinina ga wacce ban sani ba, kullum da soyayyar ɗana nake kwana nake tashi, gabaɗaya jama'ar Rugar Bello sun ɗauka ɗana ya jima da rasuwa, ni kuma nasan yana nan yana rayuwa a duniya, gidan da yake, da rayuwar da yake duk na sani" tai shiru kafin ta ce. "Babban kuskuren da ki kai Barrister Maryam barin address details naki a jikin file, na amshi komai wajan Dr, ashe har photo taiwa Aliyu, ganin rayuwar da nake ciki ba sauyi na fara tunanin komawa gidan iyayena, senato Abdullahi Abdul-majeed, a lokacin ya sauka kan mulki, ban sha wahala ba, domin iyayena suna bala'in so na, na tattara komai nawa na fara neman aikin police na samu, lokacin nasan halin da Aliyu yake ciki, shekarar farko ta zaman Aliyu a Madina a shekarar nima na sauka na haɗa plan da komai, naje masa matsayin ƴar aiki ya kuma ɗauke ni, shi kaɗai yake rayuwa Umar-khan ke musu girki da komai, a zahiri plan ɗin El-bashir ne zuwana gidan Aliyu,a baɗini kuma nawa plan ɗin ne domin na samu connection da ɗana, tun kafin bayyanar komai haka kurum Aliyu zai sakani a gaba da kallo, sai nace masa yaya? Sai kawai ya miƙe yabar wajan, wata rana na ce ko kana buƙatar wani abu, sai naji ya ce. A'a, ina ji kamar ke nake cikin barcina, nasan ƙwayar idanunki, kai tsaye na shaida masa ni ce really mother ɗin shi biological. Ya kasa yarda ya ce mother ita ce babar shi, nasan shi Dr ne a ɓoye a zahiri kuma Malami kuma lecture kuma kai D.N.A test komai ya nuna ni ce babar shi, tun a lokacin Aliyu ya ɗauki ma'adanin ajjiye sirrin shi saɓanin baya da yake da zuciyar shi, ni na bawa Aliyu shawarar kai Dada Rugar Rome, a lokacin da akai mata kurciyya, Dada ta zauna wajan Abokin mijina, yana da ɗa Yabi, suna zaune da matar shi Shatu, fitar Dada daga masarauta ya yi daidai da bayyanar cikin jikinta, nan take aka Shaida mini ni kuma na faɗawa Aliyu, duk sati sai yaje Rugar Rome, kaya kala-kala yake kaiwa Dada, lokacin da ya jima bai ce ba, shi ne suka shiga mayuyacin hali, Aliyu da kan shi amshi haihuwar Danejo ya gogeta da zaitun ya rungometa ya kuma raɗa mata suna Halisa ya ɗora da Danejo, duk sanda zashi yana ɓoye kan shi baya bari aga fuskar shi, sunyi sabo da Halisa ya goyata a bayan shi, yana mata waƙa wani lokacin ya ce _IDAN BA KE ba Aliyu_ har takai shekaru biyar lokaci kuma Aliyu ya kwanta ciwo na tsayin shekaru, daga nan ne bai ƙara waiwayar Rugar Rome ba, sai lokacin da za ai masa aure da Zahrah, rigima sosai ya yi mini akan baya so, shi fa Halisa kawai zai rayu, na rasa soyayyar da Aliyu ke mata,amma hakan baya rasa nasaba da soyayyar da ya kewa Khadijah, ba iya Halisa ba son da Aliyu ya kewa El-bashir ya ɓaci, duk abin da El-bashir ke masa ya sani, amma ya ce ba zai taɓa cin mutuncin jinin Besty ba" Tai shiru tana ƙara ɗaukan ruwa ta sha kafin ta ce. "Auren Halisa da Yaa Sheikh ba tsautsayi bane, everything that happens is a plan, Aliyu planned how to marry his adopted daughter. I also supported him, na koma Rugar Bello da Aliyu kafin lokacin nai musu bayani suka fahimta, nan take kuma ya maye gurbin Mahaifinsu na shugaban Rugar, shi ne yasa a karɓe Naggen su Halisa daga wajan shugaban Rugar Rome, wannan shi ne" jikin kowa ya yi sanyi ana zaton wuta a maƙera sai gata a masaƙa. Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh ya ce. "Malam ya akai kasan Inda Khadijah take bayan mun wayi gari ba ita cikin Masarauta?" Kamar Yaa Sheikh ba zai magana ba sai ya gyara rawanin kansa yana miƙewa tare da sauya waje, so yake ya yaki ce Dada daga gare shi tunda sirika take wajan shi, ƴarta yake aure, bayan ya zauna ya ce. "Abba na buɗe idanu a wajan Mother, Soyayya ta gaskiya ta nuna mini, ban san ya akai na kasance wajanka ba, amma mother ta shaida yaye aka kawo ni wajan Umma A'isha, lokacin shekarar Besty ɗaya a duniya, mun shaƙu sosai mun taso tare komai tare, babu abin da nake sha'awa irin yadda Abba ke karatu tare da mutane tun ina shekara goma na sauke Alkur'ani na shaddace Hadisai, a makaranta ɓangaren Islamic nayi na samu abin da nake so, ina gamawa na juya fannin likitanci, lokacin da Mai martaba ya nemi auren Besty ban damu ba, lokacin data bar gidan nan a Matsayin Matar shi, dukkan wata walwala tawa ta ɗauke sai kuma a lokacin na gane ba Soyayya ce ya shaƙuwa ba, abin yafi kama da wanda ka ke so ka rayu da shi irin ta har abada ɗin nan, tun a satin farko na aurenta nake yawan mafarkinta tana kuka, bata cikin kwanciyar hankali, kai tsaye na fahimci Aljani ne a jikinta wanda da bai bayyana kan shi ba sai yanzu, baya ƙaunar kuma ta kasance a gidan mijinta, a wannan lokacin kuma ta samu cikin El-bashir wanda ya ɗagawa wasu jama'ar dake cikin masarauta hankali, bayan haihuwar El-bashir aka sakawa Besty idanu, Aljanin jikinta ya takura mata, bayan shekaru huɗu da haihuwar El-bashir na saka Almajirai na saukar Alkur'ani suka kwana suna yi, 10 a Sakoto tayi mini nasha wahala kafin Aljanin yabar jikinta ta samu barci, sai dai tashin da tayi ta tashi da babbar ƙaddara ta baza tare da fita daga cikin masarautar, komai take akan idanuna cikin sauri nabi bayanta, da ƙyar na kamata zuwa mota na samu wani gida na ajjiyeta,naci gaba da kula da ita tsayin shekaru 3 lokacin El-bashir yana sa shekaru 7. A lokacin kuma na mayar da ita Rugar Rome, a shekara ta 8 da haihuwar El-bashir ta haifi Halisa, wacce take shekaru 17 yanzu El-bashir kuma 25 suna da tazarar shekara 8, nasan El-bashir yana mini kallon wanda na kashe masa mahaifiya ko na salwanta da rayuwarta, wanda kuma bashi da wayo hakan ta faru akwai wanda ya zauna gina shi akan tubalin ƙiyayya dani, Auren Zahrah kuma babu shi akai na domin ba a aure da ciki, na amince zan aureta ne sbd hankalin Father ya kwanta dani kuma nayi masa biyayya kamar yadda Ummul ta ce, na kuma rufa mata asiri, ya akai ta samu cikin ɗan waye ban sani ba, amma nasan tana da dalilin aure na, na kuma san duk wanda ke farautar rayuwata" "Ikon Allah, Al-hakkumu bowayi gagara misali!" Cewar Uncle Bashir. Engineer kunya ta kama shi, tsoro da fargaba suka wanzu a zuciyar shi, tashin hankalin shi ɗaya kada gasky tayi halinta akan shi. "Sannu Aliyu, Sannunka kai da mahaifiyarka bamu da baki ko kalmar gode muku, kin cancanci ki zama uwa ta gari" Abba Hakimi ya juya kan Zahrah ya ce. "Ina da ikon da Malam, kuma nasan mahaifiyar shi zatai mini karar haka, nayi miki al'ƙawarin da zarar ki ka faɗa mini gasky akan wannan jaririn to lashakka Malam zai aureki a karo na biyu" kafin Zahrah ta ce komai wayar Yaa Sheikh ta ɗauki ƙara ganin sunan Dr ya sanya ya ɗaga kiran. "Hello Dr Ibrahim ke magana" Yaa Sheikh ya jinjina kai Dr ya ce. "Mrs Yaa Sheikh Aliyu haydar ta farka daga suman da tayi, akwai babbar matsala muna nemanka yanzu" Yaa Sheikh ya miƙe tsaye yana faɗin "Gani nan" Ummul ta kalle shi sai ba tayi magana ba, Mother ce a sanyaye ta ce "Aliyu ya dai?" Ba tare daya kalli kowa ba ya ce. "Matar malam" duk suka kalle shi da rashin fahimta "Wace haka?" Cewar Mother sai a lokacin ya fahimci mai ya yi ya ce "Ta farka kuma da matsala cewar Dr i think am going.." Abba Hakimi ya ce. "Ɗan da kata, ina jinki Zahrah" Cikin kuka Zahrah kamar ranta zai fita ta ɗaga hannu tare da nuna direction ɗin da Father yake zaune ta kasa cewa komai sai kuka take tari na sarƙe numfashinta. "Ɗan Father ne, shi ne ya yi mini cikin na rantse da Allah Abba..... IDAN BA KE Isn't free book is for sale, nrml grp 500 for Special grp 1k posting har weekend. 08119237616*_IDAN BA KE_* BOOK2 PAID BOOK ₦500 Via this number 08119237616 إِنَّ اللّهَ مَعَ الصَّابِرِينَ Ilahirin jikinta rawa yake ganin Yaa Sheikh take kamar sabon halitta a cikin idanunta, ta koma jikin bango ta maƙale tana mai da numfashi ƙirjinta na ɗagawa numfashinta na sama, ta rufe idanunta ruf bata san ko ganin inda yake. Yaa Sheikh ya ware jajayen idanunsa wanda suka fara janyewa ya miƙe a hankali tare da nufar ta tun kafin ya ƙarasa ta buga tsalle ta koma bayan Ummul ta riƙe Ummul sosai tana ɓoye fuskarta a bayanta. Dr ya ce "Ka rabu da ita" sai a lokacin Abba Hakimi ya ce "Mijinta ne ai" murmushi Dr ya yi ya ce "Matar da bata san wace ita ba, ta ya zata fahimci cewa mijinta ne?" Abba Hakimi ya ce "Hakan na nufin ba zata amince da shi ba?" Dr ya kalli Halisa tare da juyawa ya kalli Yaa Sheikh ya ce "Ita ai kallon abin tsoro taka masa, sakamakon shi ne namiji na farko data fara gani bayan farkawar ta" Ummul ta ce "Akwai matsala idan haka ne, amma mene mafita?" Dr ya ce "Idan har zai rabe ta anta tashin hankali da ita kenan, ita a yadda take ji ko zai shekara bai kulata ba she doesn't care, a ko wanne lokaci zata iya recovering" Ummul ta jinjina kai alamar gamsuwa ba wanda take jin tausayi irin Yaa Sheikh tasan ba zai jure wannan sabon al'amarin ba. "Yanzu ya ake ciki"? Cewar Mother Dr ya ƙara cewa "Sallama zamu bata, a kula da hannunta wanda ya karye, kada a tsauwala tunaninta wajan tuna wace ita, ku fara koya mata dukkan abin da kuka san zai zama mai amfani a gare ta" Ya yi ɗan rubuce-rubuce, kana ya miƙawa Yaa Sheikh, ya sanya hannu ya amsa yana duba abun, some of medicine ne wanda zatai using da su.. "Thank you Dr" Yaa Sheikh ya furta cikin murya mafi sanyi rauninsa ya bayyana sosai akan fuskar shi, da muryar shi, hatta wanda baya fahimtar raunin na Yaa Sheikh yau ya fahimta kuma ya gane, sun ƙara tabbatarwa Halisa Danejo Rome ita ce duniyar Yaa Sheikh ita ce kuma raunin shi. Abba Hakimi ya juya ya fita zuwa Room ɗin El-bashir, Mai martaba ya kama hannun Dada suka fita, haka mother. Room ɗin ya rage daga Ummul sai Yaa Sheikh da kuma Halisa dake maƙale a bayan Ummul ɗin. "Fito daga bayana, tunda yau Abban naki ki ke gudu" ta saka hannu ta zaro ta daga bayanta tare da dawo da ita gaba. Ummul ta tsareta da idanu ta ce. "Ya sunanki?" Halisa ta tsare Ummul da idanu ita ma ta ce "Ya sunanki?" Ummul ta dafe kai ta ce "yau naga abin da ya fi zare tsayi ni Ummul-khairy" ita dai Halisa kallon Ummul kawai take, bata san mene so ko shaƙuwa amma taji hankalinta ya kwanta da Ummul. Ummul ta juya wajan Yaa Sheikh da yake tsaye ya harɗe hannayensa a ƙirji tare da zuba musu ido, ganin idanunsa akan Halisa ya sa Ummul faɗin "Bari na je wajan El-bashir,sai na dawo mu tafi" bai ce komai ba sai lumshe idanunsa da ya yi Ta kama hannun Halisa zuwa bakin gadon tare da zaunar da ita ta ce "Yanzu zan dawo,zauna nan" tai shiru tana marairaice fuska zatai kuka ta ce "Yanzu zan dawo, idan ki kai kuka to zan barki" tayi shiru Ummul ta ce "Ki ce to" a sanyaye ta ce "To!" Ta nufi hanyar fita har ta je bakin ƙofa ta juya ta kalli Yaa Sheikh sai kuma ta fita tana girgiza kai. Yaa Sheikh ya sauke ajjiyar zuciya wacce ta tafi da nauyin zuciyarsa, gently ya nufi hanyar fita daga room ɗin, yana zuwa ya ja ƙofar tare da rufewa ya murɗa mata key. Ya jingina da jikin ƙofar yana jifanfa da wani irin hargitsatsan kallo, wani irin sabon shauƙinta na fisgar shi, burinsa ya haɗa gangar jikinsa da nata ko zai samu daidaito a zuciyarsa, Kan ta a ƙasa tana kallon fararen yatsun ƙafarta har bata san ya ƙarasu wajan ba, sai ji tayi a saka hannu tare da ɗaga ta cak zuwa tsaye. Wani irin zaro ido tayi ƙirjinta ya buga tsoro ƙarara ya bayyana akan fuskar yarinyar ta, bata san me zata ce ba domin sai an faɗi magana take maimaitawa ta shiga girgiza masa kai tana yarfe hannunta, a hankali ya ɗora hannayensa saman shoulders ɗin ta, ya kalli fuskarta, baki ta buɗe zata saka ihu ya ɗora yatsar shi a bakin ya ce "Shiiii" ta maƙale kafaɗa ta zare kafaɗarta zata gudu ya yi saurin kamota tare da haɗata da jikinsa, bayanta ne a jikinsa ita kuma tana kallon direction ɗin gadon, hannayensa duka biyun zagaye da cikinta ya rungometa so tight fuskar shi a wuyanta a hankali yake manna mata sajan fuskarsa mai laushi tare da goga mata tsinin hancinsa a fatar wuyanta. Tsigar jikinta ta shiga tashi, jikinta ya ɗauki wani abu ya fara yawo a jikinta, haka nan taji abin da yake mata har tsakiyar ranta kuma tana buƙatar shi, ta rufe idanunta hawaye tuni ya gama wanke mata fuska har tsoran kallon fuskar shi take sbd yadda yake mata muni acikin idanunta. "Why?" Ya ce a hankali muryarsa bata fita sosai komai ya dai na masa daɗi. Halisa kokawar ƙwace kanta take amma ya yi mata rungumar da ba zata iya hakan ba, ya juyata suka fuskanci juna idanunsa na yawo a kanta ya kama hannunta tare da ɗorawa daidai ƙahon zuciyar shi ya ce "Me ya sa matar malam? Ni ne Abbanki, Modibbonki, Yaa Sheikh na ki, ki daina kafin zuciyata ta buga" taƙi kallon shi tai kicin-kicin da ranta. Ya ƙara manna hannun a ƙirjin shi yana tallafo fuskarta ya ce "Zaki bi ni ko? Nasan kina son Abbanki" kamar wacce aka raɗawa a kunne ta yi saurin faɗin. "Na tsaneka!" Kalmar ta daki zuciyar shi, har sai daya runtse idanunsa ya fesar da Iska, a hankali ya buɗe idanu suka haɗa ido, ba tsoro ko ladama bare fargaba cikin ƙwayar idanunta, kafin ya yi motsi ta ƙara cewa "Na tsaneka, na tsaneka na...," Caraf ya kame bakin domin ba zai iya ɗaukan kalmar tsana daga gare ta, ko a wasa balle har ƙasan zuciyarta maganar ke fitowa. Ta zaro idanu waje ta kuma kasa koda motsi ya yi mata rumfa da faffaɗan ƙirjin shi dake fitar da ƙamshin Roja Hannunsa ɗaya riƙe da kanta ɗaya kuma ya riƙe ƙugunta ya haɗa da jikin shi. Wani irin hot kisses yake mata wanda shi kan shi ya san ya yi abin da zuciyarsa ke umartar shi kenan, ya yi abin da yafi ƙarfin ta da tunaninta bakiɗaya, gabaɗaya ya sauke zafin goma da ashirin ɗin da aka tara masa a bakinta, labɓanta sukai jajir maimakon tayi ƙorafi sai yaga tana lumshe idanunta alamar abin nayi mata daɗi sai numfashi da ajjiyar zuciya yake saukewa, hannunsa guda ɗaya a bayanta yana bubbugawa kaɗan kamar ƙaramar yarinya. Knocking ɗin ƙofa ya dawo da Yaa Sheikh daga duniyar da ya tafi ya zare bakin shi daga nata a hankali, ita kuma tayi saurin ƙasa da kanta he still holding onto her. Ya sauke numfashi ya daidaita nutsuwa da kamewar shi, ya yi over acting da yawa hannunta daya karye ya kama yana kallo, a nan ya fahimci ɗorin bai daidai ba duba da yadda fatar hannun tai laushi har ta fara kure, ya ɗora tafin hannunsa a tsakiyar nata tare da saka babbar yatsar shi ya danna, ta saki ihu saboda zafin da hannun ya ɗauka, ya yi saurin saki yana shafa sumar kanta yana faɗin "Sorry, Sorry!" Har lokacin knocking ƙofar ake Yaa Sheikh kuma yaƙi sakinta shi su yake ko gwarancin tayi yaji muryarta amma tayi shiru sai kuka take tana kaiwa hannun shi cizo, ya haɗata da jikinsa tare da ɗora kanta a ƙirjinsa a hankali ya sauke numfashi ya ce. "تعالي إلي أو خذيني .و أحرص على قلبي لأنك فيه. أريدك أنت،لاسي أخرا فقط أنت". Ya faɗa a taushashe, yasan gabaɗaya ba fahimta take ba, da ace tana cikin hankalinta to zata gane larabcin na shi,amma yanzu jin maganar ta shi take kamar ta kurame, A zahiri kuma idan ka cire larabcin yana nufin _“Come back to me, or take me with you. Take care of my heart, because you're in it. I want you, nothing ey, just you_” Ya manna mata sumbata a goshinta irin ta sunna da kuma cikakkun Malamai tare da sakinta ya nufi ƙofar, yana sakinta tayi saurin kwanciya kan bed ɗin asibitin ta jawo bargo ta rufe gabaɗaya jikinta har fuskarta, abu goma da ashirin ya shiga juya mata tunani, Kiss ɗin Yaa Sheikh ya tsaya a zuciyarta daram! Kamar yadda ƙiyayyar shi ta samu gurbi mai girma a zuciyarta, kuma tana shi she needs more na kisses ɗin, tana jin kuma ba zata sake zuwa inda yake bata ta saka hannu ta ƙanƙame jikinta ta hannunta ɗaya da yake mata masifar zafi da zugi. Yana buɗe ƙofar yaga Mother da Ummul tsaye suna magana, ganin shi tsaye fuska kame ya sa suka ratsa ta gefen shi suka shige, bai koma room ɗin ba, ya nufi room ɗin da El-bashir yake ciki, a nan ya samu Mai martaba yana yi wa El-bashir faɗa kamar ƙaramin yaro, Abba Hakimi kuma na tsaye Dada na zaune saman kujera, ƙamshin Roja data ji ya sa ta ɗago kanta ta kalli inda Yaa Sheikh ya ke, ta saki murmushi tana faɗin. "Yanzu nake shirin zuwa wajanka Besty" ya ɗan kalleta sai bai ce komai ya lura bata yi masa kallon siriki shi kuma yana mata haka da idanun tsarkakkiyar zuciyar shi. Mai martaba ya ce "Ka bani mamaki Mubasshir, ban ɗauka zaka iya jin ƙiyayyar wani musulmi ba, balle mutum kamar Yaa Sheikh, idan ka shiga aikin police da wannan niyyar ne, ya zama dole ka shirya barin aikin dan ba zan lamunta ba" ya yi shiru domin ya manta rabon da ya yi magana mai tsayin haka, ya sauke numfashi kafin ya kalli El-bashir ya ce "Garin son zuciyarka ka sanya Zuciyar wani cikin zullumi da damuwa, ka ɗauke masa farin cikin shi" ya ƙara yin shiru kafin ya ce. "Say sorry to him, ka nemi ya fiyar shi yanzu nan Mubasshir" El-bashir ya ɗago kansa tare da kallon Yaa Sheikh a hankali ya ce "Am sorry Abba, ka yafe mini" bai san cewa har kawo yanzu Yaa Sheikh bai ji zafin shi ba, yasan duk abin da El-bashir yake akwai wanda ya ɗora shi akan hanya, ya taka a hankali zuwa bakin gadon tare da neman waje ya zauna El-bashir ya sake kallon Yaa Sheikh ya ce "Kayi haƙuri Abba" Yaa Sheikh ya jinjina kai tare da kama hannun da yake mai lafiya ya riƙe a na shi, nan take soyayyar Yaa Sheikh ta samu gurbi a zuciyar El-bashir ya yi ta kallon Yaa Sheikh. Ya sauke numfashi kafin ya ce "Ya jikin?" "Da sauƙi Abba, forgive me please, na ɗauka kai na ka kashe mini Ammi ka yafe mini" Yaa Sheikh ya ce "Shhhh! Sannu, Allah ya sauwaƙa" El ya ɗago kai ya ce "Ya jikin Sister ɗina? Nasan bata so na" Yaa Sheikh ya girgiza kai kamar ba zai magana ba sai ya ce. "Zaka iya gina soyayyarka a zuciyarta yanzu, idan akwai wanda bata so yanzu to ni ne" ya saki hannun El-bashir tare da miƙewa ya yi waje, Abba Hakimi yabi Yaa Sheikh da idanu cike da tausayawa, da sauri Dada ta miƙe suka jere da Yaa Sheikh magana take masa yana jinjina kan shi, a hankali yaja ya tsaya tare da juyawa ya kalleta ta ce. "Mene kuma Besty?" Fuska kame ya ce "Koma" ta ce "To ai mun daɗe bamu haɗu ba, akwai abin da nake son faɗa maka" ya yi mata shiru zata sake magana ya buɗe mata idanu cikin gajiyawa ya ce "Ya Allah, surutunki Ƴar fillo ta ɗauka ashe,jeki" ya nuna mata hanya" ta juya ba tare da ta ce komai ba. A hankali Yaa Sheikh yaci karo da Ummul ta ce "Muje ko?" Ya kalleta ya kalli bayanta ta gane me yake nufi sai tayi kamar bata gane ba tace "Ya akai kuma?" Ya marairaccen mata fuska kamar ba shi ya ce "Ummul kin gane" ta ce "Ni ban gane ba, tunda sanin gaibu sai Allah" a hankali ya ce "Matata" Fuska haɗe ta ce "Yaushe Arɗona ya zama haka ne? Koda yake mace na sauya halayya da ɗabi'ar namiji daman, ba shakka Halisa tayi tasiri wajan sau yaka" bai cewa mahaifiyar ta shi komai ba ta ƙara cewa "Ba zaka samu yadda ka ke a wajanta ba yanzu, dole ka nemi haƙuri ka sakawa zuciyarka Aliyu" sai a lokacin ya kama hannun Ummul ya ce "Yaushe haƙurin nawa zai ƙare? Nayi na kuma Ummul, I want her in my life" sai ya bata tausayi tasan duk Abin da Yaa Sheikh ya ce to har zuciyar shi ne, idan abu yafi ƙarfin shi yana faɗa mata kai tsaye ne. "Muje mota" ya kasa motsawa ta ce "Arɗo ka gane ka fahimta, Halisa zata koma masarauta kafin komai ya daidaita sun tafi gida da Barrister Maryam, kai ma kuma zaka bi ni ne" Ya dinga kallon Ummul da rikitattun idanunsa, shi kam a yanzu a shige level ɗin da za ana gindaya masa wasu sharuɗa, ganin ran Ummul ya fara ɓaci yabi bayanta zaune ya sameta gaban mota wajan driver ya zagaya mazaunin mai zaman banza ya zauna, bakinsa ɗauke da addu'a ko zai samu sassauci daga zuciyar shi. Sun yi nisa akan titi ta ce "Lokaci ya yi da zaka koma Yola, ka ɗauki ragamar Rugar Bello a hannunka, ka maye gurbin mahaifinka, suna buƙatar ka a can" ya yi shiru ta juya ta kalle shi, taga ya kifa fuskarsa a tafukan hannayensa ta ce "Zamu matsala da kai idan zaka bayyanar da damuwarka a fili" ya ɗago kai idanunshi sun yi ja sun ri ne ya ce. "'ana 'uhabuha" Ta ce "Ni na nasan haka, amma ita fa? Iyayenta Abba Hakimi fa? Sun sani,ko ka taɓa furtawa kana son ta? Ka aureta without her permission dana iyayenta baka taɓa cewa kana son ta" ya yi shiru can ya nisa ya ce "Kamar ba sai na faɗa ba, amma ki faɗa musu" ta kalle shi kawai ta girgiza kai ta ci-gaba da driving har zuwa Na'ibawa, gatekeeper ya buɗe mata gate ta shi ga da motar a hankali tai parking a harabar gidan tare da fitowa, Yaa Sheikh ya fito kan shi na sarawa sbd ciwon da yake masa zuciyar shi tayi nauyi. Idanunsa ya sauka akan wani dattijo dake zaune a saman kujera, kamanin shi da Yaa Sheikh sun ɓaci komai nasu iri ɗaya, Ummul tai murmushi ta ce "Your grandfather" Yaa Sheikh ya ƙarasa Dattijon ya miƙe riƙe da sanda ya ce "Yau gani ga babban malami lale" gabaɗaya suka shige cikin gidan. A can gida Mother ta nunawa Halisa komai, hankalinta ya kwanta ganin babu Yaa Sheikh a gidan, Zahrah tana ɗakin tana aikin kuka tuni akaiwa iyayenta waya ana buƙatar ganinsu. Misalin ƙarfe 10:30 na dare Mother ta tura ƙofar bedroom da Halisa ke ciki, a zaune ta sameta riƙe da hannun alamar zafi yake mata, ta nemi waje ta zauna cikin kulawa ta ce. "Kina son sanin sunanki ko?" Ta ɗaga mata kai ta ce "Sunanki matar malam, kin gane?" Ta ce "Matar Malam?" Mother ta ce "Eh, sunanki kenan yanzu ki kwanta ki huta" ta nuna mother hannunta ta ce "Zafi" ta faɗa a hankali, hannun ya kumbura sosai ta ce "Ina zuwa" ta miƙe tare da fita waya ta ɗauka ta kira number Yaa Sheikh tana ta ringing not answering, dole ta ajjiye ta ɗauki maganin rage zugi ta bawa Halisa tana nan zaune har barci ya ɗauke ta. Abin da bata sani ba tun 9 Yaa Sheikh yake cikin gidan a part ɗin shi ba wanda ya sani, haka can ma Ummul bata san fitar shi ba, yana kwance Sa juyi yake rana ɗaya tal amma ya faɗa idanunsa ya fito, ya miƙe tsaye yana ɗaukan jallabiya ya zura a jikinsa tare da saka slippers ya buɗe ƙofa ya fito, parlourn ba kowa alamun kowa ya kwanta, direct bedroom ɗinta ya nufa ya tura tare da shiga yana sallama a ran shi, duhu ne ya mamaye bedroom ɗin amma yana hango yadda take zaune a tsakiyar gadon riƙe da hannunta tana shassheƙar kuka zafin da hannun ke mata yasa ko ƙarar ƙofar bata ji ba, a hankali ya zare Jallabiyar jikinsa ya rage daga shi sai trousers ko riga babu, surar jikin shi ta bayyana idanunsa ya juyewa bakiɗaya, hannunsa riƙe da kwalbar man zafi ɗaya kuma na gyaran karaya ya nufi bed ɗin, a hankali ya zauna ba tare data sani ba ya tsaya daidai bayanta murya can ƙasa ya ce. "Matar malam" ta yi saurin ɗago kanta tunda ta sakawa ranta sunanta kenan kamar yadda Mother ta ce, bata ɗauki murya ba, cikin sauri murya na rawa ta ce "Hannu, zafi ban so" ya ajjiye abin hannunsa tare da saka hannu ya jawota jikinsa ya shiga balle gaban rigarta yana gamawa ya yi cilli da rigar ta sauke numfashi ta ƙara cewa "Zafi" ya ɗora kan shi a wuyanta ya zura hannunsa ta ƙasan hannayenta ya riƙe hannunta mai ciwo, ɗaya hannunsa kuma yana cikinta yana shafa ramin cibiyarta a hankali ya shiga hura mata iska a kunne tai luff jikin shi barci na fisgarta, da sauri kuma ta ce "Waye" ya ciji fatar kunnenta in a romantic style ya ce "Malam ya zo wajan Matar Malam yara sunna.....Idan Ba Ke By NimcyLuv Jimeta/Yola Njoɓoli Rugar Rome Gudu Saniyar take tana bin ta a baya itama, hannunta riƙe da sanda na korar Nagge, tamkar wanda suke wasan tsere haka Saniyar ke gudu a cikin jejin ita ma bata fasa bin ta ba, sauran Naggen suna gefe guda ko wacce na cin ciyayi wanda bisa kuskure tana can tana bin Saniya ɗaya tilo, sauran Naggen suka faɗa cikin gonar wani manomi, a yunwace suka rufarwa albarkatun gonar. Cikin siririyar muryarta mai nuni da Yarintar ta, da kuma nuna cewa ita ɗin zallar bafullatanar Yola ce ƴar Usul. "Waru! Waru! Waru" shi ne abin da yarinyar ke ta nanatawa cikin hausarta ta Fulani, yayinda Saniyar tuni tai mata nisa cikin gajiya wa da bin Saniyar ta tsaya a wajan wata gaɓar ruwa tana riƙe ƙugunta ta ce "Bone, lalashewa ta samu Nagge Aradu" da sauri kuma ta ɗauki sandar tana ƙara yin kan Saniyar ganin ta tsaya da gudun da take, cikin sa'a ta cimmata tana zuwa ta kama ƙahonta tare da ƙifƙifta idanunta alamar zallar fitsarar dake tattare da ita "d'ume ngid'd'a?" Ma'ana "me kake so?" Kallon ta Saniyar ta yi sai kuma ta kaɗa jela tare da zubewa a wajan ta shiga shura ƙafafuwa kamar zata mutu, cikin tsoro haɗi da razani HALISA ta ce "Jomirawo ka taimakeni" ta faɗa tana kallon Saniyar wacce tai male-male a ƙasa ga wani ruwa mai kama da jini na fitowa ta ƙasanta, kuka Halisa ta sanya domin idan Saniyar ta mutu a nan wajan ta shiga uku, itama watan mutuwarta ya kama. Tsayar da kukan tai kafin ta fara duba cikin jeji babu kowa sai ita, ga wani kwantaccen baƙin hadari dake ƙasa wanda a koda yaushe zai iya tashi. Juyawa tayi ta nufi wajan wata bishiya inda ta hangi ƙaramar igiya a jiki, tana zuwa jikin bishiyar ta zame hular Fulanin dake kanta, nan da nan sumar kanta ta sauka wacce take jajir babu alamar baƙi ko ɗaya, gashin ba wani cika ne dashi ba, kawai tsayin gashi gareta, domin har fatar tsakiyar kanta ana iya ganowa. cikin sayin jikinta ta fara jan igiyar tana ƙoƙarin kunce igiyar gaba ɗaya daga jikin reshen bishiyar, kamar daga sama taji saukar wani abu mai sanyin gaske zuwa kafaɗunta. Cak ta tsaya tana sauraren yadda abin ke tafiya sululuuuu a jikinta har ya gama sauka, hannunta ta miƙa da nufin kama abin da ya sakko mata domin bata da tsoro ko kaɗan, cikin rashin sa'a hannunta ya sauka saman ƙaton kan maciji wanda yake kwance a jikinta, wani santsi-santsi ta ji a jikin macijin ga wani sanyi sosai dake ratsa fatar jikinta, bata gama yadda da abin da zuciyarta ke ayyana mata ba, a hankali ta juya wani ihu ta kurma wanda ya yi daidai da ɗaukewar numfashinta, baya tayi zata faɗi kafin ta kai zuwa ƙasa macijin ya yi wata girgiza cikin sakanni ya juye zuwa wani saurayi wanda jikinsa ya ke sanye da wasu haɗaɗɗun kayan sarauta na farin saƙi, fari ne tas amma kamar Fatar mace haka fatar hannunsa da sauran jikinsa suke gaba ɗaya gashi ya kwanta luff. Zubewa ya yi a ƙasa ta faɗo jikinsa idanunsa a kan fuskarta, ya jima yana kallonta kafin cikin izza da nutsuwa ya ce "kin tsoratani, kin tsorata kanki Danejo, banyi niyyar zuwar maki ba yanzu" Danejo sunan da ƴan rugar Rome suke faɗawa Halisa ke nan. Sai da ya gama Kallon ta sosai, kallon da ya jima bai mata ba tun tana zanin goyo matsayin Jaririya. Ɗaukanta ya yi ya nufi inda Naggen suke yana zuwa ya tarar da wannan Saniyar dake Shure Shure ta haihu, ashe daman ciwon haihuwa ke damunta. Halisa ya kalla yana sakin Murmushi kafin ya zaro harshesa waje sai ga wani zobe ya bayyana, cikin sauri ya saka mata zoben mai ɗauke da tambarin wata masarauta, kafin ya yi Girgiza sai ga shi ya sauya kama, kamarsa a fuska na nan, amma kayan jikinsa sun sauya sun koma irin kayan Fulani sak komai da komai, goya Danejo ya yi a bayansa, ya ɗauki jaririn Saniyar cikin nutsuwa ya fara kaɗa Naggen zuwa Rugar Rome. Kamar ƙifatawar idanu haka ya ƙaraso Rugar.. Domin samun cikakken Littafin sai ku dannan Bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton 👇👇 https://www.aihausanovels.com.ng/2023/01/idan-ba-ke-by-nimcy-sarauta.html 👆👆👆Cak Yaa Sheikh ya tsaya daga tafiyar da yake, tunda ake wannan abun bai taɓa jin maganar data buge shi irin yanzu ba, ya kasa juyawa gani yake kamar ba gasky bane, ji yake kamar ya nutse a wajan dan kunya, babu wacce yake jin nauyi acikin wannan al'amarin kamar Mother, Father gumi kawai ke yanko masa idan ya miƙe sai ya koma ya zauna "Kin san me ki ke faɗa kowa? Kalamanki sunyi tsauri, tsaurin da ba ko wanne kunne zai iya ɗauka ba" Zahrah ta ce "Abba ina son Yaa Sheikh, akan soyayyar shi na yanke shawarar faɗa maka gaskiya, wallahi Father shi ne Uban jaririn nan" da ƙarfi cikin ɗaga murya Father ya ce. "Ƙarya ki ke, munafuka Algunguma ni zaki yaudara,ina matsayin abokin uban naki? Sbd kuka ko muryarta baya fita ta dubi Father sai ta ɗauki wayarta tare da shiga vedio ta play akan wani vedio tare da juya screen ɗin wayar zuwa ga father, Kasancewar suna waje ɗaya da Abba Hakimi ne yasa shima yana daga zaune yanke hango vedion. "Amma ba zaka ka manta da vedion nan ba ko? Shi kaɗai ya isa ya zama shaida a gareni?" Jikin Father rawa kawai yake da ɓari. Su biyu ne a cikin vedion a ɗakin hotel Zahrah na zaune Engineer Aliyu wanda aka fi sani da Father tsaye yana riƙe da waya a hannu. Zahrah ta dube shi da kyau ta ce "Na faɗa maka ina ɗauke ciki kuma naka baka yarda ba, ga Pregnancy Test ɗin da nayi maybe zaka fahimta daidai" Father ya kalli Zahrah kafin ya karɓi result ɗin ya duba ya ce. "Kin tabbatar ciki na ne Zahrah?" Ta ce "Of course YES! Kada ka manta kai ne ka amshi virgin ɗina" Ya yi murmushi ya ce. "Ni ɗin? ni ki ke kira na amshi Virgin naki?" Ta miƙe tsaye ta ce "Oh! Ka manta before hakan ya kasance nayi Virginity test?" _The only way to know whether or not someone has had sex is to ask. There are no physical examinations or tests that can reveal whether or not a person has had sex before. No, not even so-called “virginity tests._ Ya ce "Ban manta ba, kawai nayi mmkin yadda cikin ya shiga ne, amma ya kamata a zubar da shi kafin kowa ya sani" ta ce "Tab wai ba, ciki ɗaya, ciki biyu, ciki uku duk kana sani subar dashi a wannan karan ba zan yi ganganci da rayuwata ba, kuma Dr ya tabbatar cikin ba zai fita ba ka nemi mafita" Ya sauke numfashi ya ce. "Ok shikenan, amma waye Deen da kuke mu'amala da shi kada kiyi mini ƙarya nasan komai kina nufin shi bai isa ya ɗora miki ciki ba, ko shi ba namiji bane?" Yana sauke magana ta ɗora da faɗin. "Ya isa har ya kai, ba gwanda shi ba, tsakani na da Deen ya sauke mini sha'awata, ta hanyar romance wani abu mai kama da sex bai taɓa shiga tsakanina da shi ba" Father ya ce. "Ki aure shi mana" da ƙarfi ta ce "I can't, cos I don't love him anymore ba zan aure shi ba, idan kuma kana son Ubana ya san halin da ake ciki fine, Dady ne da laifi daya sahale maka shiga gidan shi sama taka da sunan wayewa, sai yanzu nake jin baƙin ciki da kuma taƙacin ilimin da nayi na shige ƙa'ida gabaɗaya wayewar gidanmu bata amfane ni da komai ba" a rikice Father ya ce. "Calm down please Beb, yanzu me ki ke so ayi?" Ta ce. "I want to marry your son Aliyu" a firgice Father ya ce. "Kin san me ki k cewa, Aliyu fa? Kai ba zan iya ba" ta ɗauki jaka ta ce. "Ok fine, zan sanar da Dady komai" ya yi saurin riƙota ya rungome sosai ya ce. "Is okey, na amince ki auri Aliyu kuma zan yi masa ta ƙarfi yadda dole sai ya aureki, kuma ki ɗora alhakin cikin akan shi" Zahrah tai dry ta ce "Gaskiya kai ɗan iska ne, ka ɗorawa ɗan ka cikin ka, to ɗan shi ne ko ƙanin shi?" Father ya yi murmushi ya ce. "I've no option, what ever yanzu muje ki ban kayan daɗi, banda ina mugun so da ƙaunar Barrister wallahi da aurenki zan, amma inawa Barrister son da ba zan iya yi mata kishiya ba" ta taɓa baki. Cikin sauri Abba Hakimi ya ce. "Stop the video" Ya faɗa yana runtse idanunsa ganin ana ƙoƙarin sake aikata zina ta vedion. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Uncle Haroon da Uncle Bashir suke ta maimaitawa Jadda ta kece da kuka ta ce. "Ashe dai ɗaga nono ya tabbata akan Ali, na haifi karuwi a cikina, na haifi ɗan taure mai bin ƴan iskan mata, Allah ya saka mini Allah dai ya saka mini haihuwarka da nayi, da nonona daka sha da tarbiyyar dana baka, wacce masifa ce wannan mutum kamar wani Ayu!" Mai martaba ya yi ta jin abun banbara kwai, wai namiji da suna Hajara, ganin abin yake kamar wani wasan kwaikwayo ko labarin littafan hausa da ake faɗa.. "Ina jinki Zahrah" A hankali ta ce "Tunda mukai haka da shi ya tafi ya fara neman hanyar da zai sanya Yaa Sheikh ya aure ni, cikin haka aka samu matsalar daya sanya Yaa Sheikh dawowa daga Madina ba shiri, lokacin da ya amince da aurena kafin ya faɗawa Dady ni ya fara sanarwa, nasan da komai. kullum da fargabar yadda zan kasance da Yaa Sheikh, i love him with all my heart and soul, ganin bani da mafita ya sa na nemi Deen da ƙawata Surrayerh, ita ta bani shawarar neman yarinya...." Ta faɗa musu duk yadda tsara plan na ɗaukan Halisa da yadda suka kai Dada asibiti, daɗin da ɗawa sun ƙara yi mata asiri wanda ya yi tasiri a jikinta shi ya sa bata fiye damuwa da son zuwa wajan mahaifiyar ta ta ba. Ta share hawaye ta ce "I knw i made a mistake, but isn't my fault domin Deen ya amshi cikin da bana shi ba da hannu bibbiyu, burinsa shi ma ya ɗorawa Yaa Sheikh laifin cikin, mun su dayin auren Aliyu ya kasance dani yadda zan iya cewa bakwaini na haifa, hakan bai kasance ba nasan na cutar da Yaa Sheikh da maganin dana bashi daga baya kuma na fahimci tabbas ya je wajan Halisa be tunda matar shi ce, Sai yanzu na gane dalilin da ya sanya Aliyu baya raɓar inda nake. Ci,sha, ya bani baya takura ni" Tunda ake wannan abun banda kuka babu abin da Mother take ƙirjinta har ɗagawa yake, baƙin cikin mugun tabon da Father ya barwa ya ranta shi ke damunta. Abba Hakimi ya juya kan Father ya ce. "Engineer ka ɓata wayonka, ashe zaka iya yiwa ɗan daka haifa sharrin da zan gina baƙin ciki a zuciyarsa, ya kuma ɓata kyakkyawan tulabin halayyar shi da yake ciki?, Nayi mamaki na kuma kasa fahimtar da gaske abubuwan da kake ji wani waje zai iya faruwa a inda ka ke" Father ya goge zufa ya ce. "Na amshi laifina, amma bani ka ɗai bane a family wanda yake son ganin bayan Yaa Sheikh, sai ki faɗa musu sunan mutumin daya koma Deen" Yaa Sheikh dake tsaye har yanzu sunan Allah kawai yake ambata a cikin ranshi, idanunsa sukai jajir jijiyoyin kansa sun fito, sai huci yake fitarwa. Zahrah tai shiru ta kasa cewa komai Father ya ce. "Bani ki ka tunawa asiri ba?" Kai tsaye ta ce "Duk abin da ya samu shamuwa watan bakwai me ya ja mata" Ya ce. "Ok fine sai ki sanar da su Saif-wazir shi ne Deen stop lying to them" Abba Hakimi ya dafe kai ya ce. "Saif-wazir? How can that be possible? Meye nashi na son cin mutumcin Malam? Me ya yi masa?" Daga bakin ƙofa Saif-wazir daya shigo yanzu ya ce. "Saboda ka fifita ɗan wani fiye da ɗan daka haifa a cikinka Abba" Abba Hakimi ya miƙe tsaye bai tsaya jiran komai ya saka hannu ya ɗauke Saif-wazir da mari ya ƙara ɗauke shi da mari, ya jera masa guda biyar a jere da sauri Mai martaba ya riƙe hannun Abba Hakimi ya ce "Idan rai ya ɓaci, nutsuwa ke nemu shi, marin ba mafita bane" Saif-wazir ya kalli Abba ya ce. "Like this, irin haka sune suka sanya mini tsanar Yaa Lee, kaƙi bawa yaran daka haifa space a zuciyarka, har dukiyar dana mallaka sai dana rasata dalilin Yaa Lee, bani da masaniyya akan Zahrah zata iya auren Yaa Lee wata rana, amma nasan Babanta Best friend ɗin Father ne, na nemi connection da ita na tsara plan ɗin yadda zata jawo hankalin shi harta su kasance abu guda na ɓata masa suna, sai ya zamana bana nasara Yaa Sheikh ko sha'awar dawowa Nigeria ba ya yi, a haka har Allah ya kawo ranar da aka haɗasu aure kasa barci nayi don farin ciki burina zai cika, Abba ka mareni kasa an saka ni acinin mari, tun kafin nai wayo har boarding school nai duk dalilin Yaa Lee, mene laifina dan nayi kishi da shi,bayan nasan ko mutuwa kayi bashi da gadon ka tunda ba ɗan ka bane" Ya ƙare maganar yana hawaye. Tunda Abba Hakimi yake ba'a taɓa masa rai irin na yau ba, ya kama hannun Saif-wazir ya ce "Aliyu shi ne komai nawa, tunda ya so ƴar dana fi so fiye da komai, ya kareta daga mugwaye azzalumai, ya kula da ita hai ta haifi Halisa, akan yarinya ƙarama ya zaɓi aci gaba dayi masa kallon gwauro, tuzuru, wasu na jifan shi da maganganun rashin ɗa'a akan me ba zan fifita shi fiye daku ba? Me ya Umar-khan bai complain ba? Me ya sa Ishaq-Hakim bai complain ba sai kai? ba zan aibata ka ba, amma kaje na yafe ka, ka nemi wani uban!" "Kada ayi haka Abba, don Allah a saisaita abi komai a sannu" Abba Hakimi ya ce. "Sarauta ta girmi tsofa, amma ba zan iya yin haka ba, dole Saif-wazir yabar mini gida" Umma A'isha ta ce "Ya zama dole, tunda ya zaɓi hakan" Saif-wazir ya kalli Umma A'isha ya juya ya kalli Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh dake fuskantar ƙofa, sai kawai ya yi murmushi yabar gidan bakiɗaya. Mother ta goge idanunta tas ta ce "Allhamdulillah! Hakan ya yi mini daɗi ko ba komai nasan halin uban yarana, banyi mamakin yadda Mamana Fattoumah bata son ka, akwai abin data gani tare da kai, Aliyu ina son ka ƙarasa cike mini sakin da kayi wallahi na gama zama da kai" Father ya girgiza ya ce "Abin da ba zan taɓa iyawa ba kenan Maryam, ko sakin da nayi miki ban san nayi ba, wlh ina son ki ba zan iya rabuwa dake ba _*IDAN BA KE*_ am nothing absolutely nothing" Uncle Haroon ya sauke masa wasu tagwayen maruka wanda ya sa Father saurin runtse idanu yana dafe fuska. "Shasha ban taɓa jin kunya a rayuwa irin ta yau ba, ka kunya tamu gaban mutanan da suke da ƙima da martaba a idanunmu, tashi kabar wajan nan" Mother ta ce "Yaje ina? idan yabar gidan nan ka tabbata ya ƙarasa ciki mini raguwar saki ɗayan" Cikin tashin hankali ƙarara Father ya ce "Wlh ba zan iya sakin ki ba, duk abin da za kiyi" yana faɗin hakan ya miƙe jiki ba kuzari, sai da yaje bakin ƙofa Mother ta ce "Mu haɗu a Court" Mai martaba idanunsa akan Dada wani irin sabon son ta na ƙara taso masa ya nisa ya ce. "Allah ya kyauta, Ubangiji kasa mufi ƙarfin zuciyoyinmu. Ya cire masa ƙyashi da hassada" duk suka amsa da abin. Ummul ta duba agogo tare da miƙewa ta ce. "Zan tafi Allah ya ki ya ye" Sai a lokacin Umma A'isha ta ce. "Kiyi haƙuri da abin da aka aikatawa Yaron ki Aliyu, ki yafe mana" Ummul tai murmushi ta ce "Barrister Maryam za ki bawa haƙuri ita ce uwar Malam, kawai zan nemi Alfarmar ya bini zuwa wajan ka kanin shi" Umma A'isha zatai mgn Abba Hakimi ya ɗaga mata hannu ya ce "Allah ya tsare" Ummul tabi bayan Yaa Sheikh suka fita, ita ke driving shi yana gefen mai zaman banza, ba tare da sanin su Abba Hakimi sun biyo bayansu ba. A haka suka shiga cikin asibitin lokaci guda motocinsu sukai parking, har kawo lokacin ba a gane halin da Yaa Sheikh ke ciki, bada kowa yake haɗa idanu ba kuma yaƙi cewa komai akan al'amarin. Kai tsaye office ɗin Dr ya nufa yana gaba Ummul na bayan shi, Dr ya miƙe yana miƙawa Yaa Sheikh cike da martabawa suka zauna Ummul ce ta samu ƙarfin gwiwar cewa "Meke faruwa Dr?" Dr ya zare Glasses ɗin idanunsa ya ce. "Ta farka, ba wani ciwo dake damunta sai babban ciwon daya gama lalata kwakwalwarta" da sauri Ummul ta ce. "Meke faruwa? Kayi magana kai tsaye" Ya zaro File ɗin Halisa da wani X-ray ya miƙawa Yaa Sheikh "Nasan zaka fahimta" Zuciyar Yaa Sheikh ta buga file ɗin ya nemi kwace masa, Ummul tayi saurin riƙe hannun shi tana faɗin "Be careful Arɗo" a fili cikin muryar fargaba ya ce. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Losing memory?" Dr ya ce "Haka binciken ya nuna" Ummul wacce ta lura da rikicewar Yaa Sheikh ta matsa kusa da shi tana bashi side hug ta ce "Memory? Like how" Dr ya danna system ɗin gabansa tare da juyawa Ummul ya ce "Memory loss is unusual forgetfulness. You may not be able to remember new events, recall one or more memories of the past, or both. The memory loss may be for a short time and then resolve (transient). Or, it may not go away, and, depending on the cause, it can get worse over time" Ya ƙara danno waje tare da nuna mata wani waje, kafin ya ce. "Ta samu Short-term memory loss. Short-term memory loss is when you forget things that have happened recently, such as an event or something you did, saw, or heard. It can be caused by a number of factors, including a nutritional deficiency, sleep deprivation, depression, side effects of some medications, or dementia" Ummul ta ce "What causes short time memory loss? Dr" ta faɗa she's still holding onto him, ganin har yanzu Yaa Sheikh ɗin ya kasa cewa komai, Dr ya ce. "Possible causes of reversible memory loss include: Medications. Certain medications or a combination of medications can cause forgetfulness or confusion. Minor head trauma or injury. Emotional disorders. Alcoholism. Vitamin B-12 deficiency. Hypothyroidism. Brain diseases. Sleep Apnea. Ita ta samu dalilin Trauma" Yanayin Ummul duk ya sauya ta ce "Zamu iya ganinta?" Ya ce "Sure" Yaa Sheikh ya juya tare da zare jikinsa daga na Ummul ya fita. Dr ya bi bayan shi, haka Ummul ma. A ƙofar Room ɗin suka samu Dada da Mai martaba sai Mother duk suna tsaye, Yaa Sheikh bai ce komai ba ya buɗe ƙofar Room ya shiga. Tana zaune ta jingina jikin gadon idanunta rufe, da sauri ta buɗe idanunta jin motsi kamar mai tsoron ganin wanda ya shigo haka ta dinga ɗaga lashes ɗin idanunta slowly slowly. Idanunta ya sauka akan Yaa Sheikh ta ƙura masa idanu, shi ma ita ɗin yake kallo ita kuma kallon sabon mutum take masa a sabuwar duniyar data tsinci kanta. Ummul ta shigo ita ma "Sannu Daughter" Tana sauke maganarta Halisa ta ce "Sannu Daughter" Ummul ta kalli Dr ta kalli Yaa Sheikh wanda yake ta kallon Matar Malam. "Ya jikin naki?" Cewar Ummul da sauri ita ma Halisa ta ce "Ya jikin naki?" Kan Ummul ya ɗaure sosai ta juya zuwa waje ba jimawa ta dawo ita da Dada ta ce "Daughter kin gane wannan?" Ta ƙara faɗar the same words ɗin da Ummul ta ce. Tuni idanun Dada ya cika da hawaye ta ce "Danejo baki gane Dadarki ba?" With Emotional kamar yadda Dada tai magana Halisa ta ce "Danejo baki gane Dadarki ba?" Ummul ta dafe kai ta ce "What are the symptoms of short-term memory loss?" A take ya ce "asking the same questions repeatedly. forgetting where you just put something. forgetting recent events. forgetting something you saw or read recently" Mai martaba ya ce "Ya Salam, ƙaddara data samu Princess kenan?" Dada ta fashe da kuka tana faɗin. "Your highness Halisa ta mantani" Ya riƙe ta yana bubbuga bayanta trying to calm her down. Yaa Sheikh ya sauke hannayensa gently ya ƙarasa inda take gabaɗaya suka zuba masa idanu, hatta Halisa kallon shi take a hankali ya miƙa hannu zai riƙe nata tai wani tsalle tare juyawa ta dire daga kan gadon tana fasa wata gigitacciyar ƙara.... Paid book Nrml grp 500 Special 1k 08119237616Yaa Sheikh ya juya paper ɗin a hannunsa ba tare da fuskarsa ta nuna yanayin da yake ciki ba, Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh ba yabo ba fallasa, ganin duk sun kasa magana ya sa Dr ɗin "Akwai matsala ne?" Mother ta miƙe tsaye tare da amsar paper ɗin tana kallo ta ce "No babu, abin ne ya zo Unexpected ne, but ka ce 1 week and three days? Sai naga 1 Week ne kawai" dafe ya dafe kan shi alamar mantuwa ya ce "Oh! Am sorry i almost frgt tunani da ke zuciyata daban, na ɗauki wani zance na faɗa" ta ce "No problem, Thank you Dr" ya ce "Allah ya inganta" Mother da Umma A'isha suka amsa da Amin. Umma A'isha ta ce "Daman ana iya gane cikin sati guda ne?" Mother tai murmushi ta ce "Sosai ma, zamanin baya dana yanzu bambancin su a fili yake, ciki har na kwana uku ana fahimtar shi, kawai is the defend da yadda akai text ɗin, wasu suna yin text at home na HCG for pregnancy test. Testing _(Strip, Cassette, Midstream)_ Typically, medical professionals measure pregnancy week 1 from the first day of a woman’s last menstrual period. Although a woman is not actually pregnant at this point, counting week 1 from the last menstrual period can help determine a woman’s estimated pregnancy due date. However, this article will refer to pregnancy week 1 as starting a week after conception, meaning the literal first week of pregnancy.A missed menstrual period is often the primary symptom of early pregnancy" Umma A'isha tai jigum alamar bata gane ba ta ce "Is hardly ace kai tsaye an samu cikin kwana bakwai, ko da gwajin HCG ne sai da ya nuna cikin kawai" Mother ta ɗauki wayarta ta ce "Bari muji Dr A'isha" Ringing ɗin Farko Dr A'isha ta ɗauki wayar bayan sun gaisa Mother ta ce "At hospital ta ya ya ne za a gane cikin sati ɗaya?" Dr A'isha ta ce "Wake da ciki kuma?" Mother ta ce "Bana son wannan tambayar taki, First answer my question" A hankali cike da gwanancewa ta ce "Blood tests, ta cikin gwajin jini bana fitsari ba ana iya ƙayyade adadin kwanaki ciki, irin wannan gwajin na Blood tests anfi yinsa ga budurwa wacce bata taɓa haihuwa ba, ko kuma wacce akai mata medical checkup, garin duba lafiyarta sai kuma aga ciki, da yawa ba a sanin da shi irinsa koda gwajin fitsari akai kona HCG bai fiya nunawa ba sai bayan kwanaki haka" "To ya ne Blood tests ɗin yake?" Dr A'isha dake zaune a office saman kujera ta ɗan ja kujerar baya idanunta akan system ta ce "Blood tests can tell if you are pregnant about six to eight days after the menstruation. Doctors use two types of blood tests to check for pregnancy: Quantitative blood test (or the beta hCG test) measures the exact amount of hCG in your blood" ta sauke numfashi ta ce "Sanin gaibu sai Allah, abin da mu likitoci muka gani a test ko scanning ba shi ke tabbata, kamar muce zaki haifi namiji sai kizo ki haifi mace, ko muce mutum ba zai rayuwa ba sauran shi kwanaki kaza ko wata musamman masu ciwon Cancer kuma sai mutum ya rayuwa,so komai nufin Ubangiji ne shi ya sa duk muka dai na faɗin irin abubuwan nan ko da mun gani" cike da gamsuwa Mother ta jinjina kai ta ce "Thank sister, Our Dr" Dr A'isha ta ce "Ba wannan ba Please wake da ciki ne?" Mother ta juya ta kalli Halisa dake zaune tana shan orange gabaɗaya hankalinta baya kansu balle ta san bidirin da ake ta ce "Halisa ce" Dr A'isha ta ce "You mean matar Yaa Sheikh?" "Ita nake nufi" jikin Dr A'isha ya yi sanyi, har sai da Mother ta fahimci sauyin nata, kawo yanzu tana jin ita ce bata da rabo na haihu, ta ɗauka abin girma ne sai gashi yarinyar cikinta ta samu ciki a bayanta. "Kada ki damu, kina da babban rabo In sha Allah" Dr A'isha tayi murmushi ta ce "Ina jin kamar ni na samun cikin, abin da ya shafi Malam ya shafe ni" sai a lokacin Mother ta tuna Dr A'isha bata san abin da ya faru ta ce "Haka ne, anjima za mu yi magana bye" sukai sallama. Umma A'isha ta ce "Yanzu kam na fahimta, to Allah ya raba lafiya ya inganta ya sanya mu rabu ƙalau da mai cikin" Murmushin jin daɗi kawai Mother tayi. Yaa Sheikh ya juya a hankali zai fita yaji Abba Hakimi ya ce "Ba zan tsayar da kai ma, amma ka sani kaci amana kuma zaka saman" fuskar Yaa Sheikh ta faɗaɗa bai juya ba ya yi ficewar shi yana jin nauyin zuciyarsa na raguwa, ashe shi ma wata rana zai haifi ɗa? Ashe zai ga jininsa a doran duniya? Wani irin so da ƙaunar Halisa ya ƙara ninkuwa a zuciyar shi, bai san tayi girma da ƙarƙon ɗaukan duka ƙwayayen daya zuba mata, har kawo yanzu kallon ƴar amanar shi kuma ƴar rainon shi yake ba. Ya saka hannu tare da shafa gemunsa yana lumshe idanunsa a sanyaye ya ce "IDAN BA KE ba Aliyu!" Mota ya shi ga ɓangaren driver da sauri Umar-khan dake waya ya ƙarasu wajan ya ce "Can i help with drive Yaa Lee?" Yaa Sheikh ya dubi Umar-khan a nutse ya ce "ka huta Farouk" "Idan an hana Umar-khan ai ba za a hana Prince Khalil Ahmad Sarki rakiya ba" Yaa Sheikh ya kame fuska domin bai fiya son surutun Khalil ba, ya buɗe ɗaya ɓangaren ya shi ga ya ce "Yau zan ji kalar driving ɗin Yaa Lee" bai kula shi ba, bakinsa ɗauke da addu'a tare da bisimillah ya yi wa motar key gatekeeper ya buɗe cikin nutsuwa ya harba motar kan titi. Khalil ya ce "Nikam ka shige mini gaba akan Moon mana" tamkar bada Yaa Sheikh yake ba, idanunsa kwance akan titi yana bin sautin ƙira'ar dake tashi a motar shi. "Wallahi wulaƙancinka ne bana so ina magana kayi shiru, da shekara ɗaya ka girman fa bai ma kai ba" Shi dai bai tanka ba, bakin Khalil yaƙi mutuwa ya ce "Ko dan kaga kana da furfura?" Sai a lokacin Yaa Sheikh ya rage sautin ƙira'ar kaɗan hannunsa ɗaya a gemunsa yana shafawa kamar ba zai magana ba sai ya ce "Nagartattun mutane da ƴan baiwa ke samun furfura irin tawa" "Ni dai mu ajjiye, wallahi ina son moon na shirya aurenta ka shige mini gaba" Yaa Sheikh yana shan quanah ta round-about ya ce "Waye Moon?" Khalil ya ce "Ƙanwarka Maimoon" Ya taɓe baki kafin ya sauke numfashi ya ce "Allah shirya, Maimunatu shi ne Moon? Kuyi ta ɓata sunan mutane" Khalil ya ce "Irin Special name ɗin nan ne, kai ma ai ba Halisa ka ke cewa ba, na kama sai yafi nawa" bai ƙara magana ba har suka isa cikin wani ƙaton waje shi ba makaranta shi ba asibiti ba, wajan ya yi kyau sosai ga yara manya da ƙana na suna ta sabgoginsu, Khalil ya fito tare da zagayo ya buɗewa Yaa Sheikh ƙofa ya ce "Yaushe rabona da zuwa Orphanage ɗin nan, yaran Yaa Lee sun girma" Yaa Sheikh ya fito yana gyara zaman hiraminsa idanunsa akan wata kyakkyawar yarinya data taho wajansa da gudu tana faɗin "Abba.. Abba.. Abba" tana zuwa Khalil ya yi sama da ita ai kowa ya saka kuka irin yaran nan ne masu wayo, ta dinga miƙawa Yaa Sheikh hannu ya ce "Tab, yaran wasu sukai maka wannan sabon ina ga ɗan cikin ka" Ya sauke yarinya Yaa Sheikh ya durƙosa daidai tsayinta yana shafa kanta ya ce "Beeherh" ta sakar murmushi ta ce "Abbana ina Mumyna?" Ya riƙe hannunta da take ja masa gemun ya ce "Na zama maraya Mumy ta guji Abba" Beeherh tai narairai da idanu ta ce "Abba ni ma bana son.." ya rufe mata baki a hankali ya ce "Kul dole ki so abin da Abba ke so Beeherh" ya miƙe tsaye da ita a jikinsa suka ƙarasa ciki gabaɗaya yaran suka fara ihu suna kiran "Abba ina Mumy" Khalil ya ce "Abba zai kawo muku Mumy gobe" Khalil da kan shi ya dinga raba musu chocolate da abubuwa suka pictures da yawa, yaran suka koma wajan wasa Beeherh taƙi yarda da kowa sai Yaa Sheikh a haka har tayi barci jikinsa, suna tsaye wata budurwa ta zo ta sunkuya har ƙasa ta ce "Ina kwana Abba?" Ya dinga kallonta yana son yaran sosai sai ya kasa shareta ya ce "Lafiya Hafsat" ta miƙe bayan ta gaida Khalil Yaa Sheikh ya miƙa mata Beeherh ta amshe ta ce "Kwana biyu rigima take tai ta kiran Abba, har cewa kada sunan Abbanmu ya ƙare" Ya lumshe idanunsa da hannu ya nuna mata hanyar tafiya, daga nan suka shiga mota kai tsaye Yaa Sheikh Na'ibawa ya nufa ba tare da sanin Khalil ba, sai ganinsa ya yi a haɗaɗɗan grandparents ɗin Yaa Sheikh. Ummul na zaune ta ji ƙamshin turaren ɗan nata, ta ɗago kai a hankali ta ganshi tsaye yana tsare ta da idanu "Me ya sa ka ɗauke komai na Mahaifinka ne Arɗo, babu ko kara ka ɗauki wani abun nawa?" Ta dube shi da kyau ganin ya faɗa kamar mai jin yunwa ta ce "Zonan muji, fuskar ka abu biyu ta nuna, akwai damuwa amma farin cikin ya fi yawa" ya ƙarasu wajanta yana zuwa ya zube a gabanta yana ɗora kan shi a cinyoyinta. Ta zame hiramin kan shi tasha shafa sumar kan ta ce "Ya akai Aliyu?" Ya sauke numfashi yana ɗago kan shi ya kalli Ummul ya ce "She hated me" rauninsa duk ya gama bayyana, wanda kuma iya gaban Ummul ɗin ne yake haka Ta riƙe fuskar shi da hannunta ta ce "Abun farin cikin fa?" Ya yi jim nauyin Ummul ya saukar masa, ita ma ta fahimci haka amma tasan dole ita ce abokiyar shekarar "She's pregnant, na ƙara jin son ta" farin ciki ya mayaye zuciyar Ummul sosai jin Halisa nada ciki ta ce "Ma sha Allah, so zan samu granddaughter or son zan ga jinin Arɗo am so happy" ya lumshe idanu idan ba ita ta ce ya tashi ba, zai ta zama a durƙoshe ne ta ce "Haka soyayya ta ke Aliyu, bari na baka labarin soyayyata da Mahaifinka, ban ɗauka zan so shi ba, wulaƙanci daban na gobe daban, ya yi kuka amma bana damuwa a haka har na fara tausayin shi,tausayi ya koma soyayya mai zafi, bana iya barci idan ban ji muryar shi ba, na bijirewa iyeyena ashe duk rabonka ke kira shi kuma ya hadda sa haka" tai shiru na wani lokaci ta ce "Idan Halisa ta tsaneka yau, gobe zata so ka, idan taji haushinka yau, gobe zata tausaya maka, irin haka lamiri mai girma ke tabbatar da shi,tare da rabo bana son Malam ya gaza tun yanzu, labarin Aliyuna soyayya ce mai zafi,ina fatan shafin gobe ya sa soyayyar ta zama kaffara a gare shi" "Ina son ki Ummul" Ta dungure masa kai tana faɗin "Gashi nan akan mace ka bijire mini sai farkawa nayi naga ba mota ka gudu can gidan Abba Hakimi" "Ki yafe mini" ta ce "Kada ka sake, ta shi kayi breakfast idanunka duk ya faɗa da alama ko barci ba kai ba" da hannu irin yaran kuraman nan ya yi mata nunin azumi yake. Ta kalle shi sai kawai ta girgiza kai kafin ya tashi Khalil ya yi sallama, sosai ya yi mmkin ganin Yaa Sheikh zube a gaban Ummul, Yaa Sheikh ya miƙe ya dawo kusa da Ummul. Ta amsawa Khalil tana sakin murmushi sai yanzu kuma Khalil ya lura da wacece Ummul, Kyakkyawar mace mai nagarta kuma wayayyiya mai ilimi addini da boka, macan data ɗauki ɗan ta kamar abokinta friendly to her family. Ta haɗuwa Khalil breakfast, Suna zaune Granddaughter ɗin Yaa Sheikh ya fita da matar shi Zulaiher suna ce mata Hajiya. Halisa zaune tsakiyar parlour Mother ta riƙeta, Abba Hakimi na zaune gabanta hannunsa riƙe da Alkur'ani da kuma ruwan rubutu. Yaa Sheikh daya shigo ya tsaya yana kallonsu da son jin abin da ke faruwa, A wahale Halisa ta buɗe ido ta kalli Yaa Sheikh wata murya ta ce "Modibbo ka ce kada su rabamu ina son ka, ina son ka zasu rabamu" zuciyar Yaa Sheikh ta buga sai yanzu ya gane kuma ya fahimta daidai, ya ƙarasu a karo na farko ya zube gaban Abba Hakimi ya ce "Kada kayi haka Abba, kalli abin da tayi mini da tai losing memory idan ka cire mutanan jikinta ya zan?" Mother ta kalli Yaa Sheikh ta ce "Tayi recovering ɗa zo, tana dawowa daidai kai ta fara tambaya ta ɗaga hankalinta, daman kuma Dr ya ce short-term memory 10-15 seconds ya ke ɗauka, dalilin ruwan daya kwanta a kanta ya sa ta jima, ban san me Abba Hakimi ke nufi ba amma ya ce dole ya raba Halisa da abin da ke kanta" Halisa ta miƙa hannu tana kiran "Abbana ka taimake ni, ka faɗa masa ban hanaka mu'amala ta matarka ba kada su rabani da jikinta" Abba Hakimi ya ɗauki ruwan rubutun ya watsa mata a fuska tai ƙara, da sauri Yaa Sheikh ya riƙe hannun Abba Hakimi idanunsa ya yi jajir jijiyoyin kansa sun fito ya ce "Ka tausaya mini Abba,kada kai haka" Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh ya ce "Kasan da cewa Aljanu basa tabbata a jikin mutum? Kasan nasan ba Halisa ke son ka aljanar jikinta ce, dole na raba su idan har kana son ta ka tsaya ka gina soyayyarka a zuciyarta... Kamar saka number ta ba shi da amfani, kun hana masu siyan special su siya sbd fitarwa, na kasa sani hakan Soyayya ce ko ƙiyayya?*_Ƴan Youtube masu tambaya nawa zan siyar musu da IDAN BA KE su saurara, akwai wanda suke buƙata sai na duba farashi mai yawa tukun😂🫣 TSINTACCIYA,SIRRIN MU, ABU MALEEK Duk Available ne, ZAIN ABEED ma na siyar 08119237616_* Yaa Sheikh ya ware idanunsa sosai akan Abba Hakimi yana son fahimtar da gaske yake masa? Koda yake iya zamansu ai Abba Hakimi bai taɓa yi masa wasa da abu mai muhimmanci ba, dukkan wani ilimin addini mai nagarta da tsafta a wajan Abba Hakimin ya samu, sai wanda ya ƙaro a makaranta da kuma masana manyan malamai,ya haɗa da wanda Yake da shi hakan ya sa ya zama babban malamin addinin na gaban kwatance. Ya daidaita nutsuwarsa tare da kame kansa waje guda a taushashe ya ce "Ka da kayi haka Abba" Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh yana son karantar yanayin shi sai bai ga komai ba illa Ilhama da tarin nutsuwar dake shimfiɗe a fuskar ta shi A karo na babu adadi ya ce "Yaa Sheikh ba son matarka ka ke ba da gaske, kuma baka nemi hanyar da zata soka da gaskiya da amana ba" Ya yi jim kaɗan na wani lokaci ya ɗora da "Ka nemi soyayya ta Gasky wacce take kasancewa har bayan rai, idan kace a haka zaku tafi to abun ba zai haifar da ɗa mai ido ba" Halisa ta ƙwace riƙon da Mother tayi mata jikinta na rawa taja gefe zuciyarta na ɗagawa da sauri Yaa Sheikh ya runtse idanunsa, Wani abu mai kama da zullumi na ratsa masa zuciya ya daidaita lamarin da yake addabar zuciyarsa ya numfasa kaɗan idanunsa a narke ya ce "Ba aljana jikinta" "Na sani" cewar Abba Hakimi. Ya kalli Halisa kafin ya ce "Nayi hakan ne domin nasan wacce alƙibila zuciyarka take fuskanta, bayan kaci amanata ka yaudareni ka rusa yarjejeniyar da mukai, bayan kafi kowa sanin muhimmancin al'ƙawari da riƙon amana" Yaa Sheikh kan shi a ƙasa domin ya manta wanne amana yaci wacce kuma yarjejeniya Abba Hakimi yake magana akai, Ya yi murmushi mmkin ƙarfin halin Yaa Sheikh a karo na farko kafin ya ce "Zan nemeka ne, zaka san kuma da ni ka ke magana, zan nuna maka waye ni, batun aljana kuma ai kasan akwaita banyi ƙarya ba, kuma kasan dalilin daya sanya ta rabu da jikin matar taka, Aljanu ke ɗawainiyya daku, ka rabata da Aljanin dake son ta, sai ka ƙi rabata da aljanar jikinta wacce ke son ka da gaske kamar rai, hakan mugunta ce ko mene? Aljanin dake son ta shi ne ya nemeka da sharri Aliyu, Aljanar dake son ka kuma ita ce ta kare ka daga sharrin aljanin, ita kuma ta sanar dakai cikin jikin Zahrah, kuma ita take hanaka kallon Zahrah da idanun rahama" ya sauke numfashi yana jin dole ya hora Yaa Sheikh ta yarda zai furta kalmar so da Halisa, ya kuma karɓeta da hannu bibbiyu, aman da ya yi agaban kowa ya lashe abin shi ya ce "Ka ɗauka ban san komai ba? Banyi mamaki ba, abu ɗaya ya sanya naji cewa ko wanne namiji zai iya sauya halayyar shi da ɗabi'a da nagartar ƙwarai da yake da ita akan mace, sufa mata shaiɗanun maza ne, idan ka iya kallonka kuma sai ka wanke, yanzu kuka fara rayuwa baka san abin da gobe zata haifar ba, yanzu nayi imani cewa Halisa ita ɗaya ce, ba wasu aljanu amma kai sai da ka mutu tare da naka" babu wanda ya yi magana. Ya juya kan Halisa yana faɗin "Matar kina son Yaa Sheikh? Kina son zama da shi?" Sai a lokacin ta ɗago kanta da rinannun idanunta numfashinta na fita da ƙyar ta juya ta kalli Yaa Sheikh, bai kalleta ba amma ƙirjinsa bugawa na tsoran abin da zata furta "Ina son Abbana" Ya sauke ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya mai ƙarfi na hamdala ga Ubangiji Abba Hakimi ya sake cewa "Me ya sa ki ke son shi?" Ta marairaice fuska tana juya ƙaramin bakin nan wanda yake a shirye wajan fidda zayyana ta ce "To ai mijina ne, gashi zan haifa masa baby ko Yaa Sheikh" Kunya ta sarƙafe Yaa Sheikh a Wajan bai ɗago ba, bare ya ce mata wani abun data kalli ƙwayar idanunsa ko ya furta wani abun to zata faɗin abin da ba shi kenan ba, wanda zai sanya yaji kunyar Idanun mutane ukun nan da suke kan shi "Amma shi yana son ki ne?" Tayi saurin faɗin "Ehmn da yawa ma, yana bani darasin littafin Alhayat alzawjia" Abba Hakimi ya sunkuyar da kan shi ƙasa jin al'amarin ya shahara ya shige tunaninsa. Umma A'isha ta janye kanta can zuwa wani waje tana mmkin yau ɗaya bakin yarinyar ya buɗe, Mother ce tayi ƙarfin halin cewa "Daughter jeki huta ɗakin ki, yanzu dai bakin amince kina son cikin,kuma kina son Yaa Sheikh ba?" Cikin sanyin muryarta ta ce "Eh, Mother". Mother ta ce "To tashi ki ke anjima Dadarki zata zo kafin ta shige Sokoto" nan da nan farin ciki ya mamaye fuskar Halisa zuciyarta yayi fes ta juya tana faɗin "Abba, Abba Hakimi ya fasa kada zuciyarka ta damu.." Wayam! Ko inuwar Yaa Sheikh babu tun a sakin layinta na biyu ya sulale yabar parlourn gudun abin da zata iya faɗa anjima, su kansu ba ita ba sunyi mmkin yadda ya bar wajan ba tare da kowa ya lura ba. Ta miƙe tsaye tare da nufar bedroom ɗinta, Mother ta bita da idanu ganin yadda jikinta ya sauya, ƙirjinta ya ciko sosai fatar jikinta ta ƙara haska sosai fiye da baya har wani yellow take, gabaɗaya sauyin shigar sabon ciki ya bayyana a jikinta. "Yanzu ya za ai da wannan lamarin na Zahrah?" Abba Hakimi ya ce "Dole iyayenta za tabi da zarar sun zo, tunda Engineer yaƙi yiwa yaron huɗuba zan saka Yaa Sheikh ya yi masa" Mother da take jin maganar na dokan ƙaho zuciyarta sosai ta ce "Mene haɗin Yaa Sheikh da wannan yaron kuma? Ni wallahi banga amfanin zamanta a gidan nan ba" "Kada ki zama mai son ki Maryama, ke macace ya kamata ki fahimci zafin da yarinyar ke ji a ranta, laifinta ƙanƙani ne cikin wannan lamarin" Idanun Mother ya sauya ta ce "Abba kasan babu macan da za aiwa haka ranta ya yi ɗaya, idan naga yarinyar da abin data haifa zafi na keji, zuciyata babu daɗi" Abba Hakimi ya miƙe tsaye yana kallon hanya ya ce "Yaro baya da laifi, nasan daman za kiji zafi amma laifin mijinki ne" ran mother ya ƙara ɓaci sosai ta ce "Ni ba mijina bane, nakai ƙara court ma dole ya ƙarasa saki na" Abba Hakimi bai ƙara cewa komai ba ya nufi ɓangaren shi, domin Mai martaba da Dada suna asibiti wajan El-bashir. Yaa Sheikh na zaune daga shi sai Jallabiya hannunsa riƙe da azkar yana dubawa, a hankali ya dubi lokaci ya ga rana ta kusa faɗuwa an kusa kiran magriba Kamar ance ya ɗago kan shi ya hangota a bakin ƙofa tana leƙen shi suna haɗa idanu ta koma ta ɓoya tana dafe ƙirji,gani take kamar Abban nata an sauya mata shi, idan ba kuskure tayi ba gani tayi furfura gemun shi ta sake yawa ainun. Ta ƙara leƙowa taga kan shi a ƙasa yana duba littafin hannunsa ta bishi da idanu tana jin son shi da ƙaunar shi na ƙara ninkuwa a zuciyarta, SO mai tsanani ya ƙara mamaye ko wacce ƙofa dake zuciyarta. Kamar daga sama taji saukar kamilalliyyar muryarsa mai kamala ya ce "Zonan Haliyserh" Ya faɗa a taushashe har lokacin bai ɗago kan shi ba. Ta ƙarasu bakinta ɗauke da sallama sanye da hijabi har ƙasa kamar ma daga wanka ta fito ko shiryawa ba tai ba, ta nufo wajan na shi. Tana zuwa ta nemi zama kan cinyar shi, ya yi saurin riƙe hannunta tare da ɗago kanshi idanunsa ya sauka akan fuskarta idanunsa ya sauka tsakiyar nata tayi saurin janye nata, saboda kaifin na shi idanun. A hankali ya ajjiye littafin yana jawota tare da zaunar da ita saman ƙafafuwan shi tayi saurin juyawa suka fuskanci juna! Ya dubi bakinta ganin kamar tana cin abu tare da saka hannu ɗaya ya tallafo haɓarta tare da saka hannu ya buɗe bakin nata, ya buɗe idanunsa akan ta, tare da mayar da idanunsa cikin bakin tayi saurin riƙe hannun ta ce "Abba ina so, kada ka cire" ya kame fuska tare tsare ta da idanu a hankali ya zare raguwar ƙanƙarar dake bakinta "leƙe ko? baki san mijin naki ba ne" tayi murmushi ta ce "Abba naga ka ƙara babba, kayi kyau shi ne fa" ta ƙare maganar tana son ƙwace ƙanƙarar daga hannu shi. Shiru ya yi hakan ya sa ta ce "Ka bani to, yawuna duk ya tsinke" ya ƙara haɗe fuska ta ce "Don Allah, wallahi zan maka amai idan baka ban ba" Ya sauke numfashi yana juya idanu a hankali ya ce "Me ya sa? sanyi zai miki illa fa?" Ta saƙalo wuyan shi hannunta ɗaya tana shafa sajan shi zuwa dugun gemun shi ta ce "Kawai naji ita nake so, bana son komai sai ita" ganin da gaske ice ɗin take so, gashi nan tana ƙoƙarin kakarin amai ya yi saurin zura mata a baki, taka duguwar ajjiyar zuciya idanunta na lumshe duk ta narke a hannun shi. A hankali ta ji saukar hannunsa a flat ɗin cikinta ya shafa kaɗan, tayi saurin kallon shi, Yaa Sheikh soyayyar abin da ke cikin matar malam ɗin ya mamaye zuciyar shi, yana ƙara yiwa Ubangiji godiya daya azurta matar da zuciyarsa ke so fiye da komai, da samun cikinsa jininsa ke kwance a ƙasan mararta. "Allhamdulillah!" Ya faɗa a taƙaice. Halisa ta ce "Abbana mene?" A daidai kunnanta ya ce "My kankanaty, baki san azumi nake ba? Ohya ɗaga ni" ta ce "Azumin me Yaa Sheikh?" Halisa Said while playing with his beard. Ya ɗaga ta daga jikinsa yana nufar bathroom ya ce "lokaci, sallah" yana ƙoƙarin shiga cikin toilet ɗin yaji ta rungome shi ta baya hannunta bakiɗaya ta saka ta riƙe ƙugun shi, ƙirjinta dake gogar bayan shi ya sanya tsigar jikinsa ta shi, ya rufe idanu a fili ya ce "Yasubuhanallah! Ya Rasulullah! Zaki ɗauki hakki" ta saki dariya sosai ta ce "hakin me zan ɗauka Abba?" Yana ƙoƙarin magana yaji saukar hannunta inda bai yi tunani ba, ya zare hannunta daga marar shi kamar zai kuka, duk ya ɗan birkice ya kame fuska tare da juyawa ya ce "Burinki ki karya azumi? Allah ya takaita mini wahala an kira sallah na yarda mata shaiɗanu ne wannan ɗaukan hakƙi ne Zawja" Ya yi saurin turata baya tare da tura ƙofar tana dariya ta ce _“I love you Yaa Sheikh Ya shehin malamina”_ Ya girgiza kai kawai kamar yadda Ummul ke yi idan abu ya bata mamaki, ya daɗe tsaye yana mai da numfashi, ya tabbatar da kafin a kira sallah tai masa haka to ya yi wahalar banza babu inda azumin za shi. Wanka ya yi sosai kana ya ɗaura alwala, ya fito jikinsa na zubar da ruwa ƙamshin Lifeline skin care pro plus shower Gel na fita daga Jikinsa ya shirya cikin wata white Embrodiery design jallabiya, ya ɗora hirami tare da rufe kan shi sai fuskar shi da gemunsa dake bayyane, direct fita ya yi ƙamshin Roja ya sanya Abba Hakimi da Mai martaba kallon direction ɗin duk da sun riga san waye, bai magana ya nufi Masjid. Bayan yaja sallah ya dawo gida kai tsaye part ɗin shi ya nufa, Mother na zaune ita ma idar da sallarta kenan ta kammala shirya wa Yaa Sheikh kayan buɗe baki. Ta kalli Halisa data fito sanye da blue ɗin hijab ta ce "Daughter ga Abincin Yaa Sheikh maza zo ki kai masa" kafin Halisa tai magana Abba Hakimi ya ce "Ba dai ita ba, ki kai masa da kan ki, idan kin kai kice ina buƙatar ganin shi da zarar ya gama" Halisa bata ji daɗi ba, amma ta kasa cewa komai ganin Abba Hakimi ya haɗe fuska sosai. Mother ta kai masa ta kuma sanar masa umarnin Abba. Suna zaune duka a parlour Dada ta fito wani ihu Halisa tayi tare da rungome Dada idanunta cike da hawaye ta ce "Dadata nai ta jiran ganin ki" Dada tai murmushi sosai wani daɗi ya kamata ta ce "Ke kam baki girma" Umma A'isha ta ce "Ba batun girma, ni dai abin da ke tare da ita nake ji, garin tsalle tsallen nan zai a zubar da shi" Mother ta ce "Ah Allah ya ki yaye Umma, na lura wasan jika da kaka ki kewa Daughter" ita Halisa hankalinta na wajan Dada ta ce "Ina ki kai shiga, Dadata nayi missing naki da yawa" Data ta zauna tana cewa "Munje wajan El-bashir duba jikin shi" Annurin fuskar Halisa ya sauya jin ance El, bata mance abin da ya yi wa Abbanta ba, kuma ita ma ba zata taɓa son shi ba. Ta zauna tana cewa "Ina Shatu?" "Tana Rugar Rome, za a kawota gobe idan Allah ya kai mu" Halisa ta miƙe ta ce "Bari na faɗawa Yaa Sheikh kin zo ko?" Ba walwala a fuskar Abba Hakimi ya ce "Kada naga ƙafar ki a part ɗin shi" tayi saurin cewa "To me ya sa, bayan lada zan samu" Mother ta ɗauke jin za a fara halin, Umma A'isha murmushi kawai take, Dada kuma tai shiru dan ba huruminta ba ne. "Haka na ce, muddin ki ka je ki tabbata zaki bi iyayenki Masarauta" ta haɗe fuska idanunta na kawo ruwa cikin rawar murya ta ce "To a gasky Jon wuro ban gane ba, gwara kawai mu koma makka zaman can yafi daɗi tunda babu saka idanu" Abba Hakimi maganar ta dage shi, yasan kuma da iyakar gaskiyar ta take faɗa. "Tashi kibar wajan nan Dajeno" cewar Dada ta miƙe tare da yin bedroom ɗinta ta ce "Mutum da mijinta" Gabaɗaya sukai kamar basu ji me ta ce ba, Abba Hakimi ya tura a kira Zahrah ba jimawa ta fito ɗauke da jaririn. Zamanta kenan ƙamshin Roja ya daki hancinta, tayi saurin lumshe idanunta nutsuwa na saukar mata, ta tsare Yaa Sheikh da idanu shi kam bai kalli inda take ya nemi waje ya zauna saman kujera yana rufe. "Aliyu na kira ka domin kayiwa Yaron Zahrah huɗu ba" Ya kalli Abba Hakimi na wani lokaci kana ya jinjina kai, da sauri Zahrah ta miƙawa Yaa Sheikh babyn da yake ta barci gwanin sha'awa ya ƙara girma, a hankali ya ɗora bakinsa a kunnen bbyn tare da yin Bisimillah kana ya yi masa huɗuba da suna. MUHAMMAD. "Ma sha Allah, Rabbi ya raya Muhammad" cewar Umma A'isha Dada ta amshi yaron, hawaye ne ya dinga sauka daga idanun Zahrah ji take kamar taje ta rungome Yaa Sheikh ta ɗora kanta a shoulder ɗin shi tayi kuka mai yawa ko zai tauyasa mata, ta goge hawayen ta ce "Na gode Yaa Sheikh, don Allah kayi haƙuri ka yafe mini" Kamar daga sama su kaga Father ya faɗo parlourn hannunsa riƙe da Zeefa ya fita hayyacinsa ya zube gaban Mother ya ce "Maryam ashe zaki iya kai uban yaranki ƙara court?" Tai masa Shiru idanunta akan Auta Fattoumah ta miƙa mata hannu da sauri ta nufi mother tana zuwa ta rungometa, Maimoon na tsaye taci kuka ta ƙoshi komai ya daina yi mata daɗi. "Ki tausaya mini ki janye wannan ƙarar" tai wani irin dariya tana kaɗa ƙafa ta ce "Wallahi Allah kaji na rantse maka Engineer Aliyu sai ka sakeni wannan cikon ɗayar da Jadda ta hanaka ita nake buƙata yanzu" kamar zai kurma ihu ya ce "Wallahi ba zan taɓa rabuwa dake ba Barrister sai dai mu zauna daga ni harke ba aure" Mother ta ce "Ka zauna dai? Amma ni aure babu fashi wata ɗaya ya yi yawa banda darajar idda, kuma banda abinka baga uwar shegen ɗanka nan ba sai ka aureta kuci gaba daga inda kuka tsaya" Da sauri Auta Fattoumah ta ce "Mother bana son babyn na tsane shi ba ɗan uwanmu bane" Mother ta ce "He never been your brother Mamana, tafi bedroom ki kwanta" Father ya yi saurin janye Auta Fattoumah ya ce "Ta tafi ina? Ƙafata ƙafar yarana idan kin damu da su ki dawo gare su, na shirya shi ga Court duk abin da zaki kiyi amma ba zan taɓa sakin ba" ya ɗauki Auta Fattoumah tana rusa ihu ya saka hannu ya kama na Zeefa da Maimoon sukai waje. Da sauri ta miƙe zata bi bayan shi Abba Hakimi ya ce "Kada ki fara" takaici ya sa tayi bedroom tana sakin kuka. Abba Hakimi ya kafa ya tsare daga Halisa ta fito yake fatattakarta bedroom, Ogan da kan shi ya fito yana fitowa suka haɗa idanu da Abba Hakimi, bai ce masa komai har Yaa Sheikh ya gama zaman shi ya koma part ɗinsa, ya kasa barci ɗumin jikin matar dana gudan jinin shi kawai yake so yaji, gashi gobe Alhamis zai ta shi da azumi still, ya miƙe da ƙyar ya nufi bathroom ya saukarwa kansa ruwa mai sanyi ko zaiji sauƙi, ɓangaren Halisa kusan haka ne, cikin dake Jikinta ya ƙara mata muguwar sha'awa ta buƙatuwa fiye da kima, gashi ita babu damara ta dinga malelekuwa a kan gado, da ƙarshe ta miƙe zaune tare da fashewa da kuka, su duka sai bayan sallar asuba barci ya ɗauke su. Washegari parlourn Abba Hakimi ya cika da mutane har wanda Yaa Sheikh bai zata ba, Uncle Haroon, Uncle Bashir, Mahaifin Zahrah da Mimi, tare da Surry, Mother, Umma A'isha, Dada, Yaya Halima, Dr A'isha. Sai Ummul dake zaune gefe guda cikin wani white lace mai kyau da tsari, ƙamshin Roja da taji yasa ta ɗago kanta zuwa inda jarumin ɗan nata yake tsaye, Yaa Sheikh mamakin yadda duk mutanan suka zo lokaci guda yake, ya nemi waje kusa da Ummul babu ko kunya ya zauna. Aka buɗe taro da addu'a Kafin Abba Hakimi ya kalli Uncle Haroon ya ce "Haroon ɗan fito mini da dairy ɗin nan" Uncle Haroon ya miƙawa Abba Hakimi, shi kuma ya buɗe wajan deal ɗin su da Yaa Sheikh da saka hannu da komai. A hankali ya miƙewa Yaa Sheikh ya daɗe kafin ya saka hannu ya amsa. Abba Hakimi ya ce "Ka duba deal ɗin nan, ka yanke hukunci tsakanin ni da kai ga shaidu a gabanmu, ka riƙe amana? Ko dai kaci Amana? Kai inama zaka ci wata mana bayan baka son ta, ba zaka taɓa son ta ba har abada...._*Ga masu buƙatar yi musu tallah su yi magana 08119237616, har kullum Idan ba ke na kuɗi ne akan ₦500 🫰🏽1k for Special*_ Uncle Bashir ya ce "Abba Hakimi da anyi masa afuwa, hakan ma kaɗai ya isa yaji nauyinka" Abba Hakimi ya kalli Yaa Sheikh yana jinjina ƙarfin hali da zurfin cikin shi ya ce "Anya Bashir? Ai Aliyu bai ɗauki hanyar da zamu shirya ba, basshi ya faɗa mini saka hannun waye wannan a cikin dairy ɗin?" Yaa Sheikh ya rufe ido ya buɗe, yana mai ta'ajujin abin a ran shi, gabaɗaya ya manta da batun wani deal a tsakanin shi da Abba, shi bai ga abin ɗaga zancan ba idan ba so Abban yake ya kunyata shi gaban sirikan shi ba. "Sa hannuna ne" Ya faɗa a taushashe yana mai daidaita zaman shi babu tsoro akan idanunsa, cikin nutsuwa ba kwanakwana ya shaidawa Abba Hakimin haka. "Hakan na nufin kaci amana kenan Yaa Sheikh?" Yaa Sheikh ya yi shiru he refuse to answer the question. Ya ƙara cewa "kamar ba babban malamin da ya yi magana akan al'ƙawari da muhimmancin shi ba?" Yaa Sheikh ya zare nauyin Abba Hakimi da yake ji cikin ladabi ya ce "Abba na fa ce maka ba zan iya ba? Ka manta ne?" Dr A'isha tayi saurin cewa "Ba zaka iya riƙe amanar ba?" Ko inda take bai kalla ba, amma yadda ya kame fuska waje guda zaka san mganar ta, sam ba tayi masa ba, kuma bai fiya son shisshigi ba a rayuwar shi. Abba Hakimi ya yi murmushin manya ya ce "To ka amsa mata mana?" Yaa Sheikh ya harɗe hannunsa a ƙirjin tare da yin baya idanunsa rufe, Ummul kanta a ƙasa ba ta ce komai ba, amma ita kanta zurfin cikin Yaa Sheikh yana damunta kuma a shirye take da huran da Abba zai masa "Kada na sake tambaya kayi mini shiru Aliyu" Yaa Sheikh ya ce. "Abba nifa na nemi aurenta, taya zan riƙe wannan deal ɗin?....," Dr A'isha ta ƙara cewa "hakan nuni da cewa kana son Halisa? Ko dai har yanzu kallon ƴar raino ka ke mata kuma ƴar ka?" Bai kulata ba, daman tasan ba zai tanka taba ɗin kamar yadda ta tsammata Kamar daga sama kuma taji ya ce "Zan rayu da ita, daga nan har sanda zan numfashin ƙarshe a kafaɗunta" maganar Yaa Sheikh ta girgiza dukkan jama'ar parlourn musamman Zahrah wacce zuciyarta tai masifar bugawa, kenan ta rasa Yaa Sheikh? Ba zai taɓa son ba har abada? A ɓoye ta dinga shassheƙa kuka tana gogewa duk abin da take akan idanun Mimi Uncle Haroon ya yi murmushi sosai wanda Yake nuna jin daɗi ya ce "Kamar Aliyu ya kawo ƙarshen dramar ko Abba, yana son matar shi, matar shi na son mijinta" kai tsaye Abba Hakimi ya ce "He must pay for what he did" ya gyara zama sosai fuska babu walwala ya ce "Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu, ko ka ce Dr Aliyu haydar Aliyu, kai mutum ne mai daraja, ni kuma ba mutumin banza bane, akan idanun jama'a na soka da alheri kai kuma ka bijire mini? Ba damuwa nasan alkairi ce ita a rayuwarka ko yanzu, am happy for her data samu namiji kamar ka, amma kafi dace da samun kamarta,ita ɗin macan sirri ce, mai nuna soyayyar mijinta a ko wanne lokaci, Na fahimci son da ka ke mata tun kwanaki a waya, So ba ƙarya bane, gaske ne, kuma tsararren abu wanda yake zane a zuciyar ko wanne bawa, amma ka sani..," Ya yi shiru na wani lokaci can ya ce "Za ai muku sabon aure da Halisa, dukkan wani abu da ake a biki dole kayi da arziƙin da Ubangiji ya baka, kuɗin na gani ina so, kayan lefe komai da komai, kafin lokacin auren ka gyara sabon gidanka dake G.R.A, kafin zuwan wannan ranar kada na sake ganinka a gidan nan balle inda Halisa take, a wannan karan ka tsallake umarnina zaka sha mamakins, zaka san waye ni" tunda Abba Hakimi yake magana Yaa Sheikh yake kallon shi, a ran shi ya ce "Tab, ka kashe Aliyu" a zahiri kuma ɗauke kai ya yi gefe guda, Ummul sai a lokacin ta ɗago kai ta kalli Abba Hakimi. Yaya Halima kuma ta ce "Wanne lokaci aka sanya bikin to?" Ya ce "Zuwa lokacin da zata rabu da abin da yake tare da ita lafiya" duk suka kalli Abba Hakimi cikin kamala Ummul ta ce "Abba a dai yi haƙuri, wata tara da yawa, ina laifin ta haihu a gidanta? hakan kamar zaifi nutsuwa" ya kalleta ya ce "Ummul-khairy ko dai baki bar mana Aliyu bane?" Ta yi saurin cewa "Halak malak ɗan kune ba nawa ba, kayi haƙuri" ya jinjina kai Mai martaba ya ce "Bari na shigar Maganar na bada haƙuri madadin Yaa Sheikh, ayi masa afuwa a saka sati uku Allah ya nuna mana lokacin" Mother ta ce "Allah ya ja da ran Mai martaba godiya muke" Abba Hakimi sam ba haka yaso ba amma ya ɗauki niyyar da satin uku sai Yaa Sheikh yaji jiki. Mother ta ji daɗi sosai, zata ribaci satin ukun wajan gyara Halisa ta zama cikakkiyar mace, mai ƴanci a wajan mijinta, zata saka ayi mata haɗin na musamman daga wajan A'isha Aliyu Garkuwa. Za taiwa Halisa huɗubar da zata saka ta ja Yaa Sheikh a ƙasa, wanda zata kaishi bayyana dukkan abin da yake ran shi. Abba Hakimi ya juya ya kalli Alhaji Farouk ya ce "kawo yanzu kun san abin da ya faru da yarinyar wajanku, ba sai an sake maimaitawa ba" cike da tarin kunya da kuma tsananin ladama akan ɗaukaka ilimin boko fiye da komai ya ce "Na sani, muna ƙara bada haƙuri akan wannan babban kuskure da wawta da ta aikata a gareku, shi kuma Engineer Aliyu court zata rabamu da shi, ya amshi ɗan shi ya haɗa da sauran yaran shi" Mother ta wani irin murmushi ta ce "Ɗan shege ba zai samu gurbi zaman cikin yarana ba, balle a cikin zuƙatan su, kuje can dai kusan yadda ku kai" Mimi ta juya ta kalli Mother ta ce "Maryam ai dole ace da mijin iya baba, dole a kira kishiyar uwa da sunan Umma, kamar yadda za a kira Muhammad da sunan Muhammad Aliyu" Mother ta ce "Amma akwai bambanci tsakani halak da haram kin sani, tazarar dake tsakanin sama da ƙasa mai girma ce, sai ki gane kiwa kan ki hisabi" Mimi ta ce "Kema ki sanya a ranki ba a sauyawa tuwo suna, haɗa Muhammad da yaranki ya zama dole" Mother zata sake magana Abba Hakimi ya daka mata tsawa cikin faɗa ya ce "Maryam bana son shirme, wai me ya sa mata basa raina abin magana ne?" Yaya Halima ta ce "Barrister kada ki sake magana" wani abu mai ɗaci ya tsayawa Mother, Dr A'isha ta haɗe fuska tana jifan Mimi da harara ta ce "Amma yaya Halima kin san abin akwai ciwo, a dinga haɗa maka nagartattun yara dana shege?" Da hannu Abba Hakimi ya nunawa Dr A'isha hanya ya ce "Fita waje Aishatul-humaira" ta miƙe rai ɓace tare da yin waje abinta. Yaa Sheikh ya gyara zama bayan ya ɗan kalli kowa ya sauke ajjiyar zuciya, kamar wanda aka tilasta yin magana ya ce. "Taci gaba da riƙe Muhammad, har zuwa shekarun da Ubangiji ya ƙayyade uba ya amshi ɗan shi, idan Allah ya kawo mata mijin aure kuma ta kan iya dawo da shi wajan Muhammad,amma kuskure ne ɗorawa yaron da bashi da laifi hukunci, ba shi ya zaɓi haka ba, da ɗa da dukiya Ubangiji kaɗai ya san mai morarsu" Umma A'isha da yaya Halima suka haɗa baki wajan faɗin "Haka ne, Ubangiji ya datar damu" suka amsa da "Amin" Zahrah ta kasa jurewa ta ce. "Ka ce idan na samu mijin aure, mijin aure na jima da samu gashi nan a gabana, don Allah Yaa Sheikh ka tausaya mini kada ka cutar da zuciyar dake son ka, ko baka so na zan zauna da kai har ƙarshen rayuwa" ya ɗauke kai yana ƙoƙarin tashi tayi saurin riƙe ƙafar shi ta ce "Ka dubi girman Allah, koda hakan zai zama taimakon ka na ƙarshe, ko zai zama jahadi" ya ƙara ɗauke kai dan ya san ba zai iya abin da take so ba sam, ta sake shi da sauri da rarrafe ta ƙarasa wajan Ummul ta riƙe ƙafarta ta ce "Ke kaɗai zai ji maganar ki, ki taimaki ni Ummul don darajar Annabin harama" Ummul ta girgiza kai tana murmushi ta ce "Wacce ni kuma? ni ƴar aikin gidan Aliyu wacce ƴar aikin gidanku ma ta fini muhimmanci, nikam ba ruwana" kuka Zahrah ladamar sakin layin da tayi ya mamaye zuciyarta, bakinta ba linzami haka ta dinga aibata Ummul. Mimi ta miƙe tare da ɗauke Zahrah da maruka ta ce "Ke kuma gaki mayya kamar shi kaɗai ne namiji a duniya,da za a dinga muzantaki ana wulaƙanta ki kamar mara asali toshe!" "To ai mayyar ce, kuma kurwar mijina kur wallahi ba zai taɓa son ki ba har abada, ko da can a baya dan bani da iko ne nake danne kishin mijina akan idanunki, amma idan haukan kishi ne wallahi ni babarki ce akan haka, kuma wutsiyyar raƙumi tayi nesa da ƙasa, ko wacce ƙwarya akwai abokiyar burminta abi wani" Halisa data fito tun ɗazo ta faɗa tana huci kamar zata kaiwa Zahrah doka. Zahrah ta miƙe tsaye tana kuka tana murmushi ta kalli Halisa sosai ta ce "Namiji ne fa? Gudanawa ki ke, mijin daya kasa furta kalmar so a gareki shi ki ke wannan ihun akan shi? Nayi miki al'ƙawari idan ƴar halakce ni wallahi sai na dawo gidan nan Matsayin matar Aliyu,daga nan kowa ta fara goga sa'ar ta aga wace zata zama mowa da wacce zata zama mora" Zuciya da kishin Yaa Sheikh ya cika zuciyar Halisa tayi kan Zahrah tana faɗin. "Ki auri Abbana ki ce me? Dame zaki tutiyya budurci ko me? Abbana ciki ya yi mini kuma zai ci gaba dayi mini ciki ma halak ba zan gajiya ba" Baki buɗe yaya Halima ke kallon Halisa, Ummul kuma murmushi kawai take a yau surutun ya yi mata rana, Abba Hakimi da yake kaka wajanta ya ce "Gidanku matar waya kira ki?" Mai martaba kuma kallon Princess ɗin tasa kawai yake, yana ƙara yaba kyan da Ubangiji ya yi mata da kaifin baki. Halisa ta kalli Abba Hakimi ta ce "Jon wuro ai duk laifinka ne, kawai ka rabu damu mu koma Madina ni wallahi ko barci bana iyawa, mutum da mijinsa" ta kalli Yaa Sheikh daya ɗauke kai ya yi kamar bai san me ake ba, shi kam kunyar duniya ta gama cika shi ta ce "Abbana kai ma baka son zaman nan ko?" Ta faɗa tana zama kan cinyar shi idanunta na lumshe, ya yi shiru ta kama fuskar shi tana jan gemu ta ce "Yaa Sheikh ɗina, kyakkyawan mijina ina son ka, idan na haifa mana baby sunanka za a saka, idan nayi wani ciki na haifi baby girl a saka sunan Ummul" Umma A'isha ta ce "Mu kuma fa?" Tayi fari da idanu tana cewa "Zan iya saka sunanki, amma banda na Jon wuro tunda ya hanani zama da mijina" Abba Hakimi ya haɗe fuska sosai ya ce "Kuma ko zaki me ba zaki bishi ba, Aliyu ta shi kabi babarka yau" ta haɗe fuska sosai ta ce "Ai daman ka tsofa, idan ka mutu kuma fa" Umma A'isha ta ce "Ba kinki ya sari ɗan yan kashi irin mai ɗoyin nan, nida mijina mutu karaba" bata sake kulasu ba tai kissing Yaa Sheikh ta ce "I love You so much bananina" Yaa Sheikh ko wacce kamar _I love You_ ɗin dake fita daga bakin Halisa har ƙasan zuciyar shi yake jin kalmar, tana ratsa ko'ina na Jikinta. Ya miƙe tsaye tare da yin gaba zai fita ta riƙe shi tare da rungome shi ta ce "Abbana, Ya azumi Allah ya baka lada tare dani kaji" ya kalli tsakiyar idanunta sosai a hankali ya janye tare da furta. "Ki dai na ɗaukan magana Zawja" ta marairaice sosai ta ce "Da gaske zan haihu Yaa Sheikh?" Ya ce. "In sha Allah" yana faɗin hakan ya fita. azumin da yake shi ne kawai yake riƙe da shi,ban da haka da tuni anji wani labari. Baƙin ciki kamar ya kashe Zahrah, Alhaji Farouk ya yi wa su Abba Hakimi godiya da ƙara basu haƙuri, Mimi ko magana ba tayi ba hannunta riƙe da Muhammad tai waje tana figar Zahrah. Umma A'isha har ranta taji daɗin abin da Halisa tayi da haka Abba Hakimi zai gaji ya bawa Yaa Sheikh matar shi, Uncle Haroon da Uncle Bashir suka bawa Mother haƙuri akan ta janye ƙarar da tayi amma fur taƙi bisa dole suka haƙura. Ummul ta nufi haɗaɗɗiyar motar ta waya kare a kunnenta "Hajja A'isha ina buƙatar ganinki abu ne ya taso urgently" Wacce aka kira da Hajja ta ce "Lafiya dai Hajiya Ummul-khairy?" Ummul ta ce "Akan ɗanki Aliyu ne, biki za ayi na kece raini nasan dai Arɗo ba zai amince da wata bidi'a ba, lefe zamu haɗa na gani na faɗa a karo na farko daga dangin Aliyu"Hajja ta ce "Ma sha Allah, naji daɗin wannan al'amarin, ina kan hanya In sha Allah daman ban taɓa ganin daughter-in-law ba" sukai sallama. Tasan Yaa Sheikh a yanzu ba zai bita ba, tunda har ya gudu ta shiga mota tare da ficewa daga cikin gidan. Yaa Sheikh zaune sanye da Jallabiya ya ɗora Foreign Alkyabba, golden colour hannunsa maƙale da Rolex Daytona sai ƙamshin Roja yake bazawa ya yi wani irin kyau, a hankali ya ajjiye Rufaida Fura dake hannunsa yana goge bakinsa da tissue, ya dubu lokacin 9:10 amma ko gilmawar ta bai gani ba, kuma yana son bin umarnin Abba Hakimi duk da yasan zai zama cutuwa da azaba a gare shi. Ganin jiran bai da fa'ida ya miƙe a sanyaye tare da saka Leather Tassel Loafers a ƙafar shi yana covering Alkyabbar jikinsa hannunsa riƙe da key ya nufi hanyar fita daga part ɗinsa zuwa waje, kusan duk suna bedroom ɗinsu sbd shirun da parlourn ya ɗauka, cak ya tsaya tsigar jikinsa ta mimmiƙe ya ja wani numfashi mai zafi, tunaninsa ya tsaya dalilin wata kyakkyawar runguma da tayi masa, bai kalleta ba ya saka hannu ya dawo da ita gabansa, ta cikin hijabin ya fahimci babu kayan ƙwarai a Jikinta. Ya juya yaga ba kowa ya damƙi hannunta ta ce "Abbana ina zaka dani?" Yaƙi bata amsa sai daya buɗe mota ya sakata ciki ya shiga ya zauna tare da yin bisimillah ko horn bai ba, sai hasken torch ɗin mota ya kunna, gatekeeper ya buɗe masa. Halisa ta marairaice ta ce "Yaa Sheikh ina zamu? Wajan Ummul?" Bai kalleta ba sai da sukai nisa ya ce. "Zan duba jikan Ummul, naji zaƙin kankanaty ya sauya ko a'a....Halisa ta saki dariya ta ce "Abbana kana da abin dariya" idanunsa akan titi yana ci-gaba da driving bai ce mata komai ba, can yaji tai shiru ya juya ya kalleta idanunta akan titi tana lumshe idanu da sauri ta ce "tsaya tsaya Abba" yaƙi tsayawa cikin sauri ta saka hannu taja gemunsa ya ce "Ya Allah!" Ya ja birki yana riƙe gemun idanunsa a jirkice yake binta da kallo ta narai-narai da idanu ta ce "Ka yafe mini Yaa Sheikh ɗina" ya dubeta ya dubi titi a hankali ya ce "Ya akai Zawja?" Ta nuna masa wani waje ta ce "Naman can nake sha'awa" da mmki sosai ya dubi mai naman sam hankalinsa bai kwanta da abin titi ba ya ce "Amma ɗazo kinci a gida ai?" Ta ce "Eh amma wannan ƙamshin ya yi zai daɗi, kuma daman bai isheni ba" A hankali ya ce "Sannu kura, ba za kici ba" ta shagwaɓe fuska tana narke masa a hankali ta kama hannunsa ta ɗora a cikinta ta ce "ƊAN MALAMA ya ke son nama a taimakawa Zawja Please Yaa Sheikh" kallonta yake sosai yana jin ɗumin Jikinta dake ratsa masa hannu he don't know how much she loves her, the only thing daya sani he can't live without her, ita ɗin rayuwar shi ce, ita kawai ta san haka sbd tana fahimtar shi, banda haka da yawa ba za su yarda yana son Zawja ba. "I understand, zan yi order" ta ce "Ni dai wannan nake so, idan babu shikenan kawai" ya kashe motar yana sauke numfashi tare da buɗe ƙofar zai fita ita ma ta buɗe da idanu ya yi mata magana ta ce "Zan bika ne fa" ya dubi mazan dake wajan, ya dubi shigar dake Jikinta ya fita kawai, ita ma ta buɗe ta fito tana tsaye a wajan ya zagayo bai magana ya kama hannunta ya buɗe murfin motar ya danna ciki tare da murza key. Ta cikin glasses ɗin ya ranƙwafa tare da zura hannu ya tallafo fuskarta ya ce "Ba a wasa da abu mai muhimmanci" ya saketa yana juyawa zuwa wajan, kafin ya ƙarasa wani ya zo da sauri ya ce "Sannu da zuwa, ikon Allah yau gani ga Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu!" Ya yi murmushi tare da miƙa masa hannu sukai musabawa. "Me ka ke buƙata?" Kafin ya yi magana yaji saukar muryarta ta ce "Abbana kazar guda biyu Ɗan Malam ya ke so" mutumin ya leƙa tare da hango Halisa dake zuro kai ta Glasses ɗin motar. "Shikenan na fahimta" Ya juyawa zuwa wajan tare da zaro kaji guda biyu manya masu zafi ya yayyanka tare da sakawa a leda. Ya kaiwa Yaa Sheikh, without looking at him ya ce "Nawa ne kuɗin?" Ya yi murmushi mutumin ya ce "Haba haba, muna ta neman hanyar da zamu gode maka bisa ƙoƙarin da ka kewa Addinin musulunci, amma bamu samu ba, wannan ba wani abu bane a bawa Madam" Yaa Sheikh ya amsa fuska ɗauke da murmushi ya ce "Jazakallah-bil khair" sukai sallama ya nufi cikin motar, yana zuwa ya buɗe tare da shiga ya yi Bisimillah tare da yiwa motar key ya fara driving bai ta kanta ba, fuska kuma ɗaure ba wahala sai jikinta ya yi sanyi duk da zumuɗin cin kazar da take ta ce "Abba mene ya faru? Nayi laifi ne" bai tanka ba ta ƙara cewa "Me nayi maka?" Ya juya gabaɗaya ya ce "Yaushe za ki nutsu Zawja haihuwa zaki fa?" Ta kasa fahimtar maganar ta shi ta ce "Nasan zan haihu amma me nayi?" Ya yi mata banza yana jin babu daɗi idan ya tuna sautin muryarta da mai naman ya ji. Iya abin da yake ji ya ya isa, shi kam data fito a haka mai naman ya ganta ya zai ji?. Har suka isa makaken gidan shi dake G.R.A wanda za a fara gyaran shi gobe bai ƙara ce mata komai ba, ita kuma tayi tambayar tai maganar har ta gaji. Ya yi parking a harabar gidan mai cike da flowers kala-kala gwanin sha'awa, ya fito ita ma ta fito hannunta riƙe da ledar kazar tabi bayan shi jiki ba kuzari, part uku ne a gidan mai ɗauke da 1floor, ya haura saman benen tana biye da shi taji ya yi sallama ita ma tayi tana son taga waye a ciki da har yake sallama sai taji shiru, babban parlour ne mai ɗauke da wasu milk and Brown ɗin kujeru sai t.v da freezer, direct bedroom ya nufa daman kaf gidan iya sama kawai aka zubawa furniture ya zame Alkyabba ya ɗora saman hanger, ya cire hiramin ma, ya ajjiye ya zauna daga shi sai Jallabiya ya yi baya ya kwanta saman gado, idanunshi rufe, a hankali ta ajjiye ledar ta sunkuya tare da kama ƙafar shi ta shiga zare takalmin dake jikin ƙafar, ta zare safar haka ma ɗaya ƙafar tana jan yatsun ƙafar shi ta ce "Kayi haƙuri ban sakewa" Ya tashi zaune tare da ɗagota ya zaunar saman cinyarsa, ya zame hibin Jikinta ta ce "Sanyi Abba" ya dubi cikin idanunta yana cilli da hijabin ta rage daga ita sai vest da trousers designer da idanu yake bin ƙirjinta daya ciko sosai har mmki ya bashi, cikin nutsuwa yana jin komai na jikinsa na sauyawa, yana ƙoƙarin hana kan shi amma zuciya ta rinjaye shi, duk ƙoƙarin kame kansa ya gagara daidai kunnenta ya ce "Ke ɗin sirri ce, sirrina ce Zawja" ta ce "Kayi haƙuri" Yana zura hannu ta ƙasan vest ɗin tare da shafo lafaffan cikinta tare da shafo ƙasan mararta ya sauke numfashi ya ce "haramun ne mace tai magana wajan namiji, idan ba muharamin ta" ya kama hannunta ya ɗora a ƙirjinsa ya ce "Naji zafi a nan, a kiyaye, zaki sauya kaya Abaya's idan zaki fita da liƙab, tare da safa hannu da ƙafa" ta ce "Ai bani dasu" A hankali ya ƙara tura hannunsa can sama daidai ƙirjinta bata san mene ya faru ba sai ji tayi ƙitttttttt! Da sauri ta duba ganin yadda ya keta vest ɗin gida biyu tare da yin cilli da ita ya sa ta hangame baki ta ce "Innalillahi ka yaga min kaya ba kyau suttura ce Abba" ba zai iya magana ba sai kallon cikin idanunta da ya yi, ta tsorata lokacin gudu da yadda idanunsa ya sauya launi, ƙirjinta ya buga hannunsa ɗaya yasa ya saƙalo hannayenta zuwa wuyan shi, ƙirjinta daidai fuskar shi, ya cusa fuskarsa bakiɗaya a ƙirjin yana shaƙar wani irin ƙamshi na musamman, ta rufe idanu Jikinta ya fara saki tsigar jikinta ya shiga ta shi yana zubewa, ta tura hannunta cikin sumar kan shi murya bata fita ta ce "Abbana" wani irin salo yake mata wanda ya sanya numfashinta fara yin sama har basu san lokacin da Yaa Sheikh ya yi fatali da ledar kazar ba, a karo na biyu ya ƙara yaga bra ganin hannunsa na rawa wajan unhooking bra ɗin, ya yi cilli da ita, ta buɗe ido da ƙyar tana ƙara reƙe shi wani abu na mata yawo a dukkan Jikinta kamar ta fasa ihu ta ce "Wani abu yana yawo Abba" Ya ɗago kai a hankali ya kalli yadda idanunta ya jajir ta kasa jurewa ta haɗe bakinsu waje guda tunda ya gagara yin hakan! Ya tallafo fuskarta domin ya bata cikakkiyar damar shan bakin na shi ya jata har tsakiyar gado, lokacin da al'amarin ya zafafa har tsayawa numfashin Halisa ya ke, bata taɓa jin salon Yaa Sheikh ba sai yanzu, ya kuma hanata abin da take buƙata, wani kalar romantic style yake mata, ya yi hakan ne kuma domin ya san matar shi, ya ƙarfnta yake da kuma juriya, how sweetness she's. Lokacin data samu abinda take so kuka ta saki tana riƙe shi, shi kan shi ya yi mamakin juriya da ƙarfin halinta da kuma yadda ta iya ɗauke buƙatar shi tsaf ba tare da gajiyawa ba. Bayan tai wanka shima ya shirya cikin kayan barci yana ta zabga ƙamshin ya zauna gefen gado yana kallon yadda ta naɗe tsakiyar gado ta rufe da lallausan duvet. A tare suka saki murmushi ya yi saurin juyawa ta miƙe zaune tare da kwanciya bayan shi kamar yarinya ta ce. "You're so sweet Abbana, my banani Yaa Sheikh nawa" yana kai inibi bakin shi mai tsafta ya ce "Kin ji daɗi kin cinyewa Ummul ɗan ta?" Tai murmushi tana lashe fatar wuyan shi ya runtse idanu sosai yana jin kamar kunna shi take ta ce "Naji daɗi dai, na faranta wa Arɗon Ummul rai, kankanaty ta sauya" ya girgiza kai kawai ya ce "Allah kana gani, ka shirya mini matar malam" tai lamo a bayan shi tana wasa da gashin ƙirjin shi ta ce "Yaa Sheikh" ya ce "Uhm" Ta kasa magana sai yaji abu mai zafi yana zuba a bayan shi,ya saka hannu ya jawota gabansa shi, ya kalli yadda take hawaye wanda kuma duk na kissa ne "Kuka? Akan me? Wanne dalili?" Ta riƙe hannunsa ta ce "Abbana kada ka auri Anty Zahrah don girman Allah, wallahi zan mutu ba kaji yadda ƙirjina yake mini zafi fa yanzu, wayyo Abbana" Ya riƙe kafaɗunta jin yadda take kuka harda shassheƙa ya ce. "Nutsu Matar Malam, yaushe nace zan aure kuma?" Tana kuka ta ce "Baka ce ba, amma kayi mini al'ƙawari Abbana kaji Modibbo" ya yi mata shiru tare da jawota jikinsa ya rungometa sosai yana bubbuga bayanta ta ce "Kayi mini al'ƙawari ba ko wacce mace?" Ya kame bakin ya shiga bata wani kyakkyawan kisses tai luff a ƙirjin shi. Ya zame yana cewa "Shiru, zo kici kazarki" ta girgiza kai ta ce "Bana ci, ka rufeta bana so wari take" ya lumshe idanu yana matseta sosai. Yana zaune barci ya ɗauketa ya sakkota a hannunsu yafi mintuna biyar yana kallonta faɗuwar gaba ta riske shi a fili ya ce "Auzubillahi, Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, lahaula walaƙuwwata illah billah!" Ya faɗa yana sauke idanunsa akan cikinta sai ya mayar da ita jikinsa ya ce. "qul hayati , 'ana 'uhibuki" ya shafa kanta ya tabbatar barci take a sanyaye ya yi kissing lips ɗinta ya ce. _“I love you Zawja”_ Washegari ya shirya cikin sky blue ɗin shadda gezner jamper da babbar riga, ba tare daya saka Alkyabba ba, ita kuma ta shirya cikin ƙaramar Jallabiyar shi ta ɗora hijabin, basu karya ba hakan yasa ya nufi gidan su Ummul kai tsaye, Ummul na zaune a main parlour ita da Hajja su kaji sallamar Halisa da gudu ta nufi Ummul ta faɗa Jikinta tana faɗin "Ummul ɗita" Ummul bata kalli Yaa Sheikh ba ta zaunar da Halisa tana cewa "Daughter ki daina gudu, zuwan sassafe haka" Halisa ta juya ta ce "A gidan Yaa Sheikh muka kwana, wallahi bedroom ɗinsa mai kyau Ummul" ta girgiza kai kawai ta ce "Naga alama, je Kiyi breakfast" ta ce "To a ina?" Ta nuna mata hanyar da kitchen yake ta ce "Can, akwai maid zata nuna miki kayan breakfast ɗin sai ki zuba abin da ki ke so" ta miƙe ta ce "Abba na zubo da yawa muci tare?" Ummul ta ce "Baya za a zuba masa" Hajja dai murmushi take Halisa ta birgeta lokaci ɗaya. Bayan halinsa ta bar wajan Yaa Sheikh ya miƙe yazo gaban Ummul ya zube bisa quwwuyinsa ya ce "Ina kwana" a taƙaice ta ce "lafiya" kafin ya yi magana ta ɗaga waya tare da faɗin "tana tare da shi" tai shiru can ta ce "To babu matsala gasu nan" ta kashe wayar ta ce "Abbanka na kira yanzu,amma kayi breakfast" ta miƙe ta ce "Ina zuwa Hajja" tana gaba yana binta ta ja shi can part ɗin Dattijo a nan ta haɗa masa breakfast kana ta bar wajan. Hajja ta kalli Ummul ta ce. "Yanzu ya ki ke so lefen ya kasance" Ummul ta girgiza ƙafa ta ce "Saiti biyar nake so, kaya masu kyau" Hajja ta ce "Zasu ja kuɗi fa" "Amma kin san kuɗi ba matsala bane, bani target na fita waje ki duba komai Expensive haka, bana son lace na ƙasa da 200k Please" Hajja ta ce "Babu damuwa" suka shiga wata maganar duk akan haɗa kayan lefen. Suna gamawa Ummul ta samu Halisa tai mata tas akan sakewa namiji jiki da take yana moreta son ran shi. Halisa ta kalli Ummul ta ce "Ummul tausayin shi nake fa" Ummul ta riƙe baki sai kawai ta juya cike da mamaki. Ta samu Yaa Sheikh tsaye a parlour ko bata faɗa masa komai ba, yasan ya yi laife ba zai shige tafiya da Halisa da ya yi ba. Yana tsaye Halisa ta fito sukai waje har suka isa gida basu ƙara magana da juna ba. A harabar gidan suka samu Mai martaba tsaye sai Abba Hakimi da Khalil, da kuma Dada sai kuma El-bashir dake wheelchair, mother da Umma A'isha. Yaa Sheikh ya fito Halisa ma ta fito ta ce "Ina zaki Dada?" Kai tsaye Abba Hakimi ya ce "Sokoto zata koma masarauta, tare dake sai sati uku zaki dawo" farin ciki ya kama Halisa zata dangin mahaifinta, Khalil ya ce "Jirgi baya jira fa" Abba Hakimi ya ce "Halisa shi ga mota, Khalil shigar da Mubasshir ciki" Yaa Sheikh ya tsaya kallon ikon Allah tafiya da matar shi ba tare da an sanar masa ba? Ya rasa me yasa Abba Hakimi yake haka ne? Shi kam yau zai nuna cewa shi ne mijinta zai nuna ƙarfin iko, duk suka shiga mota Halisa ta tsaya tana kallon Yaa Sheikh Abba Hakimi ya ɗaure fuska ya ce "Shige ki tafi, ai zaki dawo wajan shi ne" a sanyaye ta juya zata shi ga mota Yaa Sheikh ya ce "Idan har ki ka bar gidan nan zuwa Sokoto to na haƙura da ke, na cire igiyar aure dake kan ki wallahi Allah.... 08119237616Gabaki daya gurin Suka tsaiya suna kallon ya sheikh da mamaki daanjin abinda ya fada nima jira nake kuma kujira ehe Halisa ta saki dariya ta ce "Abbana kana da abin dariya" idanunsa akan titi yana ci-gaba da driving bai ce mata komai ba, can yaji tai shiru ya juya ya kalleta idanunta akan titi tana lumshe idanu da sauri ta ce "tsaya tsaya Abba" yaƙi tsayawa cikin sauri ta saka hannu taja gemunsa ya ce "Ya Allah!" Ya ja birki yana riƙe gemun idanunsa a jirkice yake binta da kallo ta narai-narai da idanu ta ce "Ka yafe mini Yaa Sheikh ɗina" ya dubeta ya dubi titi a hankali ya ce "Ya akai Zawja?" Ta nuna masa wani waje ta ce "Naman can nake sha'awa" da mmki sosai ya dubi mai naman sam hankalinsa bai kwanta da abin titi ba ya ce "Amma ɗazo kinci a gida ai?" Ta ce "Eh amma wannan ƙamshin ya yi zai daɗi, kuma daman bai isheni ba" A hankali ya ce "Sannu kura, ba za kici ba" ta shagwaɓe fuska tana narke masa a hankali ta kama hannunsa ta ɗora a cikinta ta ce "ƊAN MALAMA ya ke son nama a taimakawa Zawja Please Yaa Sheikh" kallonta yake sosai yana jin ɗumin Jikinta dake ratsa masa hannu he don't know how much she loves her, the only thing daya sani he can't live without her, ita ɗin rayuwar shi ce, ita kawai ta san haka sbd tana fahimtar shi, banda haka da yawa ba za su yarda yana son Zawja ba. "I understand, zan yi order" ta ce "Ni dai wannan nake so, idan babu shikenan kawai" ya kashe motar yana sauke numfashi tare da buɗe ƙofar zai fita ita ma ta buɗe da idanu ya yi mata magana ta ce "Zan bika ne fa" ya dubi mazan dake wajan, ya dubi shigar dake Jikinta ya fita kawai, ita ma ta buɗe ta fito tana tsaye a wajan ya zagayo bai magana ya kama hannunta ya buɗe murfin motar ya danna ciki tare da murza key. Ta cikin glasses ɗin ya ranƙwafa tare da zura hannu ya tallafo fuskarta ya ce "Ba a wasa da abu mai muhimmanci" ya saketa yana juyawa zuwa wajan, kafin ya ƙarasa wani ya zo da sauri ya ce "Sannu da zuwa, ikon Allah yau gani ga Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu!" Ya yi murmushi tare da miƙa masa hannu sukai musabawa. "Me ka ke buƙata?" Kafin ya yi magana yaji saukar muryarta ta ce "Abbana kazar guda biyu Ɗan Malam ya ke so" mutumin ya leƙa tare da hango Halisa dake zuro kai ta Glasses ɗin motar. "Shikenan na fahimta" Ya juyawa zuwa wajan tare da zaro kaji guda biyu manya masu zafi ya yayyanka tare da sakawa a leda. Ya kaiwa Yaa Sheikh, without looking at him ya ce "Nawa ne kuɗin?" Ya yi murmushi mutumin ya ce "Haba haba, muna ta neman hanyar da zamu gode maka bisa ƙoƙarin da ka kewa Addinin musulunci, amma bamu samu ba, wannan ba wani abu bane a bawa Madam" Yaa Sheikh ya amsa fuska ɗauke da murmushi ya ce "Jazakallah-bil khair" sukai sallama ya nufi cikin motar, yana zuwa ya buɗe tare da shiga ya yi Bisimillah tare da yiwa motar key ya fara driving bai ta kanta ba, fuska kuma ɗaure ba wahala sai jikinta ya yi sanyi duk da zumuɗin cin kazar da take ta ce "Abba mene ya faru? Nayi laifi ne" bai tanka ba ta ƙara cewa "Me nayi maka?" Ya juya gabaɗaya ya ce "Yaushe za ki nutsu Zawja haihuwa zaki fa?" Ta kasa fahimtar maganar ta shi ta ce "Nasan zan haihu amma me nayi?" Ya yi mata banza yana jin babu daɗi idan ya tuna sautin muryarta da mai naman ya ji. Iya abin da yake ji ya ya isa, shi kam data fito a haka mai naman ya ganta ya zai ji?. Har suka isa makaken gidan shi dake G.R.A wanda za a fara gyaran shi gobe bai ƙara ce mata komai ba, ita kuma tayi tambayar tai maganar har ta gaji. Ya yi parking a harabar gidan mai cike da flowers kala-kala gwanin sha'awa, ya fito ita ma ta fito hannunta riƙe da ledar kazar tabi bayan shi jiki ba kuzari, part uku ne a gidan mai ɗauke da 1floor, ya haura saman benen tana biye da shi taji ya yi sallama ita ma tayi tana son taga waye a ciki da har yake sallama sai taji shiru, babban parlour ne mai ɗauke da wasu milk and Brown ɗin kujeru sai t.v da freezer, direct bedroom ya nufa daman kaf gidan iya sama kawai aka zubawa furniture ya zame Alkyabba ya ɗora saman hanger, ya cire hiramin ma, ya ajjiye ya zauna daga shi sai Jallabiya ya yi baya ya kwanta saman gado, idanunshi rufe, a hankali ta ajjiye ledar ta sunkuya tare da kama ƙafar shi ta shiga zare takalmin dake jikin ƙafar, ta zare safar haka ma ɗaya ƙafar tana jan yatsun ƙafar shi ta ce "Kayi haƙuri ban sakewa" Ya tashi zaune tare da ɗagota ya zaunar saman cinyarsa, ya zame hibin Jikinta ta ce "Sanyi Abba" ya dubi cikin idanunta yana cilli da hijabin ta rage daga ita sai vest da trousers designer da idanu yake bin ƙirjinta daya ciko sosai har mmki ya bashi, cikin nutsuwa yana jin komai na jikinsa na sauyawa, yana ƙoƙarin hana kan shi amma zuciya ta rinjaye shi, duk ƙoƙarin kame kansa ya gagara daidai kunnenta ya ce "Ke ɗin sirri ce, sirrina ce Zawja" ta ce "Kayi haƙuri" Yana zura hannu ta ƙasan vest ɗin tare da shafo lafaffan cikinta tare da shafo ƙasan mararta ya sauke numfashi ya ce "haramun ne mace tai magana wajan namiji, idan ba muharamin ta" ya kama hannunta ya ɗora a ƙirjinsa ya ce "Naji zafi a nan, a kiyaye, zaki sauya kaya Abaya's idan zaki fita da liƙab, tare da safa hannu da ƙafa" ta ce "Ai bani dasu" A hankali ya ƙara tura hannunsa can sama daidai ƙirjinta bata san mene ya faru ba sai ji tayi ƙitttttttt! Da sauri ta duba ganin yadda ya keta vest ɗin gida biyu tare da yin cilli da ita ya sa ta hangame baki ta ce "Innalillahi ka yaga min kaya ba kyau suttura ce Abba" ba zai iya magana ba sai kallon cikin idanunta da ya yi, ta tsorata lokacin gudu da yadda idanunsa ya sauya launi, ƙirjinta ya buga hannunsa ɗaya yasa ya saƙalo hannayenta zuwa wuyan shi, ƙirjinta daidai fuskar shi, ya cusa fuskarsa bakiɗaya a ƙirjin yana shaƙar wani irin ƙamshi na musamman, ta rufe idanu Jikinta ya fara saki tsigar jikinta ya shiga ta shi yana zubewa, ta tura hannunta cikin sumar kan shi murya bata fita ta ce "Abbana" wani irin salo yake mata wanda ya sanya numfashinta fara yin sama har basu san lokacin da Yaa Sheikh ya yi fatali da ledar kazar ba, a karo na biyu ya ƙara yaga bra ganin hannunsa na rawa wajan unhooking bra ɗin, ya yi cilli da ita, ta buɗe ido da ƙyar tana ƙara reƙe shi wani abu na mata yawo a dukkan Jikinta kamar ta fasa ihu ta ce "Wani abu yana yawo Abba" Ya ɗago kai a hankali ya kalli yadda idanunta ya jajir ta kasa jurewa ta haɗe bakinsu waje guda tunda ya gagara yin hakan! Ya tallafo fuskarta domin ya bata cikakkiyar damar shan bakin na shi ya jata har tsakiyar gado, lokacin da al'amarin ya zafafa har tsayawa numfashin Halisa ya ke, bata taɓa jin salon Yaa Sheikh ba sai yanzu, ya kuma hanata abin da take buƙata, wani kalar romantic style yake mata, ya yi hakan ne kuma domin ya san matar shi, ya ƙarfnta yake da kuma juriya, how sweetness she's. Lokacin data samu abinda take so kuka ta saki tana riƙe shi, shi kan shi ya yi mamakin juriya da ƙarfin halinta da kuma yadda ta iya ɗauke buƙatar shi tsaf ba tare da gajiyawa ba. Bayan tai wanka shima ya shirya cikin kayan barci yana ta zabga ƙamshin ya zauna gefen gado yana kallon yadda ta naɗe tsakiyar gado ta rufe da lallausan duvet. A tare suka saki murmushi ya yi saurin juyawa ta miƙe zaune tare da kwanciya bayan shi kamar yarinya ta ce. "You're so sweet Abbana, my banani Yaa Sheikh nawa" yana kai inibi bakin shi mai tsafta ya ce "Kin ji daɗi kin cinyewa Ummul ɗan ta?" Tai murmushi tana lashe fatar wuyan shi ya runtse idanu sosai yana jin kamar kunna shi take ta ce "Naji daɗi dai, na faranta wa Arɗon Ummul rai, kankanaty ta sauya" ya girgiza kai kawai ya ce "Allah kana gani, ka shirya mini matar malam" tai lamo a bayan shi tana wasa da gashin ƙirjin shi ta ce "Yaa Sheikh" ya ce "Uhm" Ta kasa magana sai yaji abu mai zafi yana zuba a bayan shi,ya saka hannu ya jawota gabansa shi, ya kalli yadda take hawaye wanda kuma duk na kissa ne "Kuka? Akan me? Wanne dalili?" Ta riƙe hannunsa ta ce "Abbana kada ka auri Anty Zahrah don girman Allah, wallahi zan mutu ba kaji yadda ƙirjina yake mini zafi fa yanzu, wayyo Abbana" Ya riƙe kafaɗunta jin yadda take kuka harda shassheƙa ya ce. "Nutsu Matar Malam, yaushe nace zan aure kuma?" Tana kuka ta ce "Baka ce ba, amma kayi mini al'ƙawari Abbana kaji Modibbo" ya yi mata shiru tare da jawota jikinsa ya rungometa sosai yana bubbuga bayanta ta ce "Kayi mini al'ƙawari ba ko wacce mace?" Ya kame bakin ya shiga bata wani kyakkyawan kisses tai luff a ƙirjin shi. Ya zame yana cewa "Shiru, zo kici kazarki" ta girgiza kai ta ce "Bana ci, ka rufeta bana so wari take" ya lumshe idanu yana matseta sosai. Yana zaune barci ya ɗauketa ya sakkota a hannunsu yafi mintuna biyar yana kallonta faɗuwar gaba ta riske shi a fili ya ce "Auzubillahi, Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, lahaula walaƙuwwata illah billah!" Ya faɗa yana sauke idanunsa akan cikinta sai ya mayar da ita jikinsa ya ce. "qul hayati , 'ana 'uhibuki" ya shafa kanta ya tabbatar barci take a sanyaye ya yi kissing lips ɗinta ya ce. _“I love you Zawja”_ Washegari ya shirya cikin sky blue ɗin shadda gezner jamper da babbar riga, ba tare daya saka Alkyabba ba, ita kuma ta shirya cikin ƙaramar Jallabiyar shi ta ɗora hijabin, basu karya ba hakan yasa ya nufi gidan su Ummul kai tsaye, Ummul na zaune a main parlour ita da Hajja su kaji sallamar Halisa da gudu ta nufi Ummul ta faɗa Jikinta tana faɗin "Ummul ɗita" Ummul bata kalli Yaa Sheikh ba ta zaunar da Halisa tana cewa "Daughter ki daina gudu, zuwan sassafe haka" Halisa ta juya ta ce "A gidan Yaa Sheikh muka kwana, wallahi bedroom ɗinsa mai kyau Ummul" ta girgiza kai kawai ta ce "Naga alama, je Kiyi breakfast" ta ce "To a ina?" Ta nuna mata hanyar da kitchen yake ta ce "Can, akwai maid zata nuna miki kayan breakfast ɗin sai ki zuba abin da ki ke so" ta miƙe ta ce "Abba na zubo da yawa muci tare?" Ummul ta ce "Baya za a zuba masa" Hajja dai murmushi take Halisa ta birgeta lokaci ɗaya. Bayan halinsa ta bar wajan Yaa Sheikh ya miƙe yazo gaban Ummul ya zube bisa quwwuyinsa ya ce "Ina kwana" a taƙaice ta ce "lafiya" kafin ya yi magana ta ɗaga waya tare da faɗin "tana tare da shi" tai shiru can ta ce "To babu matsala gasu nan" ta kashe wayar ta ce "Abbanka na kira yanzu,amma kayi breakfast" ta miƙe ta ce "Ina zuwa Hajja" tana gaba yana binta ta ja shi can part ɗin Dattijo a nan ta haɗa masa breakfast kana ta bar wajan. Hajja ta kalli Ummul ta ce. "Yanzu ya ki ke so lefen ya kasance" Ummul ta girgiza ƙafa ta ce "Saiti biyar nake so, kaya masu kyau" Hajja ta ce "Zasu ja kuɗi fa" "Amma kin san kuɗi ba matsala bane, bani target na fita waje ki duba komai Expensive haka, bana son lace na ƙasa da 200k Please" Hajja ta ce "Babu damuwa" suka shiga wata maganar duk akan haɗa kayan lefen. Suna gamawa Ummul ta samu Halisa tai mata tas akan sakewa namiji jiki da take yana moreta son ran shi. Halisa ta kalli Ummul ta ce "Ummul tausayin shi nake fa" Ummul ta riƙe baki sai kawai ta juya cike da mamaki. Ta samu Yaa Sheikh tsaye a parlour ko bata faɗa masa komai ba, yasan ya yi laife ba zai shige tafiya da Halisa da ya yi ba. Yana tsaye Halisa ta fito sukai waje har suka isa gida basu ƙara magana da juna ba. A harabar gidan suka samu Mai martaba tsaye sai Abba Hakimi da Khalil, da kuma Dada sai kuma El-bashir dake wheelchair, mother da Umma A'isha. Yaa Sheikh ya fito Halisa ma ta fito ta ce "Ina zaki Dada?" Kai tsaye Abba Hakimi ya ce "Sokoto zata koma masarauta, tare dake sai sati uku zaki dawo" farin ciki ya kama Halisa zata dangin mahaifinta, Khalil ya ce "Jirgi baya jira fa" Abba Hakimi ya ce "Halisa shi ga mota, Khalil shigar da Mubasshir ciki" Yaa Sheikh ya tsaya kallon ikon Allah tafiya da matar shi ba tare da an sanar masa ba? Ya rasa me yasa Abba Hakimi yake haka ne? Shi kam yau zai nuna cewa shi ne mijinta zai nuna ƙarfin iko, duk suka shiga mota Halisa ta tsaya tana kallon Yaa Sheikh Abba Hakimi ya ɗaure fuska ya ce "Shige ki tafi, ai zaki dawo wajan shi ne" a sanyaye ta juya zata shi ga mota Yaa Sheikh ya ce "Idan har ki ka bar gidan nan zuwa Sokoto to na haƙura da ke, na cire igiyar aure dake kan ki wallahi Allah.... 08119237616*_Mai son ai masa tallah a IDAN BA KE kwana 5 za a bada 1,500.... Kwana goma 3,000 kwana sha biyar 4,500 kwana ashirin 6,000 wanda yake so a saka masa har littafin ya ƙare zai bada 15k dubu goma sha biyar❤️ Littafin Idan ba ke na kuɗi ne 500 nrml grp,1k for Special posting har weekend 08119237616_* Thank you for choosing sarautar's Library💋🫶🏼. Halisa ta tsaya ba tare data ƙarasa motar ba, annurin dake fuskantar ya ɗauke da mmki sosai take kallon Yaa Sheikh, ba tare da ta ce komai ba jiki a sanyaye ta nufi cikin gidan idanunta na zubar da hawaye. Yaa Sheikh yabi bayanta da kallo ta gefen idanu, daman bai riga daya shige ciki ba, murmushi Abba Hakimi ya yi yana jinjina kai ya ce "Khalil ku je, Allah ya tsare ya kai ku lafiya" Mai martaba yaso a wannan karan ya zauna da Princess Halisa, ya nuna mata soyayya irin ta ƴa da uba, amma ba shi da ikon yin magana tunda yanzu ita ɗin ba ikon shi ba ce. Ita kanta Dada bata ji daɗin abin da Yaa Sheikh ya furta ba, sai dai ba kowa za aiwa abin da akewa Aliyun ba ya jure, an shirya tafiya ba tare da sanin shi ba, alhalin shi ne mijinta kuma sai da izinin shi. Mother ta ƙarasa wajan Yaa Sheikh dake shirin shigewa ciki ta ce. "Aliyu!" Ya tsaya yana harɗe hannayensa a baya ba tare daya kalleta ba, ta ce "Ka ba ni mamaki da kunya sosai Malam, ba kaiwa Abba Hakimi al-kunya ba, duk da hukuncin shi ya yi tsauri na tura Halisa,amma yana da kyau kayi magana mai kyau yadda za a fahimta ba tare da zuciya ko ran wani ɗaya daga cikinmu ya ɓaci ba" ta kalle shi taka ba ita yake kallo ba, hannunsa ɗaya dafe da kansa alamar ciwo yake masa ta ce "Ka yi haƙuri, kabar Daughter ta ziyarci dangin mahaifinta a karo na farko na rayuwarta, babu wanda ta sani, yanzu ne ya kamata ta zauna dasu, su bata Soyayyar dangin mahaifin data rasa, baka duba yadda tayi farin ciki ba ko? baka duba yadda furucinka a yanzu ya sauya mata lissafi ba? Ko dan son da take maka" Abba Hakimi ya ɗagawa su Mai martaba hannu har suka fice daga harabar gidan, ya juya zuwa inda Mother take tsaye da Yaa Sheikh, ba yabo ba fallasa ba alamun damuwa ya ce. "Ya yi abin da ya dace ne a matsayin shi na mijinta, bada wata manufa nai maka hakan ba, ba kuma dan na takura auren ka, ko dan auren bai mini ba sam, nasan son Halisa sosai, tun ba yanzu ba, ban kuma damu daka furta gaban kowa kana son ta ba.Alal haƙiƙa nayi haka ne domin na ƙara inganta aurenku, ya kafa tarihi a duniya ba iya family ba, duk macen da mutum ya rena har zuwa matakin duniya ya kuma aureta, batun ace bai san wahalar aure ba wannan gaibu ne da tsagwaron son zuciya,yafi kama da tatsuniyar gizo da ƙoƙi, muje ciki ka ɗauki matarka, Allah ya sanya albarka cikin rayuwar aurenku ya kaɗe fitina" Ya juya cikin gida zuciyarsa cike da mamakin Yaa Sheikh ɗin da kuma rashin ta idanu da ya yi masa. "Baka kyauta ba Malam" ya juya ya dubi Mother a hankali cike da gajiyawa da komai dake faruwa ya girgiza kai ya ce. "Ina son kai ta da kai na ne, shi ne burina" ya yi gaba, daman tuni Umma A'isha ta shige cikin gidan. Mother ta bi bayansu, Abba Hakimi na tsaye kamar yadda Yaa Sheikh yake tsaye ya kalli Mother ya ce. "Kirawo mini ita" Umma A'isha ta ce "Kayi haƙuri Hakimi, kada ka biyewa zuciyar Aliyu data fara sanin mace yanzu,ai masa uzuri" "Kin Allah a yau kuma yanzu sai Aliyu ya ɗauki matar shi sun tare, kada na sake jin bakin ki Aishatul-humaira" ta ce "Allah ya baka haƙuri" lokacin da Mother ta shiga Halisa na kwance akan gado ta rungome, ta ɗauka Abban nata zai so farin cikinta, tana son iyeyenta, danginta She wants to spend some time with her father's family, taji daɗinsu tasan yadda suke amma shi ne zai sanya ƙafa ya yi fatali da farin cikinta? Duk wanda bai son Ahhalinta kamar ita ce baya so, ya nuna Jikinta yake muradi amma banda farin cikinta, a karo na farko taji zafin Yaa Sheikh mijinta, ma riƙnta, uban yaron dake cikinta fiye da kima ta ji sam ba zata iya bari ko yatsarta ya kama ba. Ta yi saurin goge hawayen dake bin fuskarta tana mayar da sautin kukanta, sbd motsin da ta ji, ta miƙe zaune tare da yin ƙasa da kanta. Mother ta nemi waje ta zauna ta ce "I saw that you were crying" ta yi murmushi ta ce "Barci na fara" "You supposed to do that, but not now" Halisa ta ƙara yin murmushin ƙarfin hali tare da yin ƙasa da kanta irin al-kunya nan ta Fulani "Your grandfather is calling you, ki saka hijabi ki fito" A sanyaye ta ce "To" ta miƙe tare da ɗaukan wani hijabi sage green ta saka Kyakkyawar fuskarta ta bayyana wacce ta ƙara haske da cika, ta zura slippers ta nufi Main parlour. Cikin ƙaramar muryarta tai sallama ta nufi tsakiyar parlourn ta zauna ƙasan carpet ta ce "Gani Jon wuro" Ya kalleta ya ce "Tashi ki bi mijinki Halisa" zuciyarta ta buga da ƙarfi tai ƙasa da kanta ta kasa cewa komai, Yaa Sheikh ya jingina da jikin ƙofa idanunsa a kanta, sai yanzu ladamar furta abin da ya ce ta lulluɓe shi, amma a yanzu ko haƙuri ya bayyanar Abba ba zai ji ba, kuma ba zai saurara ba. "Magana nake ki tsaya mini, ba daman an saka muku ido ba? Yanzu an cire tashi ki je Allah ya tsare ya bada ladan aure" hawayen da take maƙalewa ya gangaro zuwa fuskarta cikin Muryar kuka ta ce "Kayi haƙuri nai kuskure Jon wuro ba zan sake ba, ina neman alfarma a gareka ka janye batun na bi wani, ka barni na zauna tare da ku" da sauri Mother da Umma A'isha suka kalli Halisa ba wasa ko sakin layi a cikin maganarta. Abba Hakimi ya ce "Mijinki ne, bana wani ba ra'ayinki shi ne zaki ba, amma ai kina son shi meye dalilin haka?" Ta saki murmushi sosai ta ce "Bana son shi Abba, bana son zama da shi, ina son ya bani ta kardar sakina kamar yadda ya furta" Mother ta ce "Ai ba ai sakin ba, cewa ya yi idan ki ka tafi kuma ai kina nan" ta kalli Mother ta dawo ta kalli Yaa Sheikh ta ce. "Amma ai ya yi niyya? Kuma Ubangiji da ita yake amfani Mother, Yaa Sheikh jikina ya ke so bani ba, ba kuma farin cikina ba, na ɗauka shi da kan shi zai ce naje ga dangina sai naga saɓanin haka, ban san kowa ba sai Hamma Khalil da Hamma El duk da bana jin zan amshi shi matsayin yayana, ba zan zauna da Yaa Sheikh ba, ba zan zauna da shi ba, zanta zama a wajanka Jon wuro zuwa sanda zan haihu ya sakeni nayi idda na samu miji nai aure" Yaa Sheikh ya runtse idanunsa jiri na neman ɗaukan shi, yana hasko rigima a idanunta amma bai hasko wannan tashin hankalin ba, wanda ba zai iya ɗauka ba kuma ba zai jure hakan ba. "Daughter kin yi kuskure, kin fahimci Yaa Sheikh ba daidai ba, kada kiyi amfani da ƙaramar ƙwaƙwalwarki ki datse soyayyar dake tsakaninku, kada ki hau tubalin da zai kai ki zuwa ladama, ita *DAUƊAR GORA* ciki kan shata (Real Smasher)" Halisa ta fashe da kuka ta ce "A lokacin na so shi,kamar bana son kai na, babu abin da nake muradi a duniya sai shi kaɗai a rai na, Mother tana bi jire bani Abbina da yanzu ni ba Matar shi ba ce, kawai yanzu naji ba zan iya zama da shi ba" Mother zatai magana Abba Hakimi ya ɗaga mata hannu ya ce "Ba a shiga sha'anin mata da miji sai kiji kunya, ki bari tabi abin da zuciyarta ta yanke mata" _A decision of the heart, What the heart chooses._ "Allah ya kyauta,ya kawo sauƙi cikin lamarin" cewar Umma A'isha. Abba Hakimi ya ce "Jeki Allah ya yi miki Albarka!" Ta miƙe tsaye zata koma bedroom bai san mene ya faru ba, sai ganin shi ya yi tsaye a gabanta riƙe da hannayenta ya kafeta da jirkitattun idanunsa masu laushi da nuna tsantsar buƙatar miji zuwa ga matar shi. Ya kasa magana sai launin idanunsa daya sauya ƙwarai, zafin zuciyar shi ya fi ƙarfin ya bayyana yadda yake ji a cikinta, tamkar gobara ce ta tashi wani ke ƙara tuttula mata fetur. "Nasan ba gasky bane Zawja" ya faɗa a taushashe cikin wata kalar muryar shi kan shi bai san ya faɗi hakan ba. Ta kalli cikin idanun shi ta ce "Babu ƙarya a irin riƙon da kayi mini, babu kuma wasa a irin darussan daka bani, dan haka ban taɓa ƙarya ba kuma ba zan fara akan ka ba Malam Yaa Sheikh" Ya fesar da numfashi ya kasa magana ya yi ƙoƙarin jawota ya rungome ko zai ji nutsuwa tayi saurin bige hannunsa ta ce. "Ina jin al-kunya sbd shekaru da furfurar dake tare da kai, baka duba halin da zan shiga ba da ace ka sakeni, ka manta da kai ɗaya nayi sabo, dan haka wannan ya zama First and last da zaka ƙara kai hannunka jikina, domin na haramta a gareka, kyautatawa ɗaya zan maka shi ne ɗan ka da zan raina a cikina na kuma shayar da shi nonon da ka ke kwaɗayi" cikin harshen larabci ya ce "Zawja ki fahimta *_IDAN BA KE_* kamar babu Aliyu ne" ta kalle shi sosai ta ce. "Sai wata rana" ta juya da sauri zuwa bedroom ɗinta, kuka na ƙwace mata, Allah ya ji ya gani tana son Abbanta amma dole ya barta ko yasan zafin so da kuma raɗaɗin da take ji na abin da ya yi mata. Yaa Sheikh ya sulale ya zauna saman kujera ya dafe kai da hannu bibbiyu, daman tuni su Mother suka bar wajan. _When all is gone_ A wanann rana da kuma daren zuƙatansu da zuciyoyinsu basu zauna lafiya fa, _The night was long for them, a dark night and the heart was filled with sorrow_ sun rasa ya ya za su yi, _The night that prevented them from sleeping, the love and passion for each other entered their hearts more and more_ Da asuba Yaa Sheikh bai iya jan jam'i ba, sbd zazzaɓin daya rufe shi da wani wahalallan ciwon kai, da ƙyar ya iya zuwa masjid ɗin. Da azumi ya tashi har wajan ƙarfe 12 bai ta shi ba. Misalin 2:45 ya shigo cikin parlourn sanye da shadda cream colour babbar riga da ƴar ciki, ƙafarsa sanye cikin Black Gustavo parent italian leather Tassel Loafers sai ɗaukan idanu takalmin ya ke, hannunsa maƙale da Rolex na Companyn Daytona. Ƙamshin Roja ya sanya Ummul ta ɗago kanta, suka haɗa idanu tayi saurin janye nata, domin ƙarara tashin hankali ya bayyana a fuskar shi, Dattijo da Hajia suka kalli Yaa Sheikh ta ce. "Mai gidana shigo mana kai tsaye" ya dai tsaya ta ƙara cewa "Lafiya dai?" Ya ƙara yin shiru ta gyara zama ta ce "To kaci kan ka, wallahi nafi ƙarfinka sai dai uwarka gata nan" Ummul dai tayi murmushi kuma bata kula Yaa Sheikh ba, alrdy Mother ta sanar mata komai, hakan ya yi mata daɗi duk da abune mai wahala Halisa ta ce dole sai ya rabu da ita, ya ƙarasu ciki ɗauke da Sallama kan akan cinyar Ummul ya gaida kakannin na shi. Shi bai magana ba Ummul ba tai ba, can ta ce "Ɗaga ne da na kawo maka lunch" ya girgiza kai ya ce "Azumi" ta ce "To Allah ya bada lada" a hankali taji gabaɗaya kan shi ya ɗauki zafi sosai ta taɓa kan ta ɗauke hannu ta ce "Baka da lafiya?" Ya ce "Lafiya lou" tai ta kallon shi. Ta cire hiramin ta dinga shafa sumar kan shi tana masa addu'a, a haka taji saukar numfashi shi ta leƙa taga ashe barci yake. Wasa wasa sati guda ya shuɗe, na biyu ya shafe, na uku ya shige sati huɗu cif bai sanya Halisa cikin idanunsa ba, ko gilmawar ta baya gani. Halisa kuma sai ta fahimci baya gidan take fitowa parlourn suyi hira, da zarar taji motsi ko ƙamshin turaren shi take barin wajan. Tana shan wahala amma haka take jurewa cikin dare tayi ta kuka tana riƙe ƙafa, ta faɗa sbd buƙatar mijinta da take, Yaa Sheikh baya bambance Alhamis da Litinin kullum cikin azumi yake,ya rame sai fararen idanunsa da suka ƙara fitowa. Zahrah ce kwance gadon asibiti Jikinta na rawa, na'urar room ɗin sai ƙara take, Surry ta riƙe ta riƙe Muhammad sosai, cikin sauri Mimi da Dr suka shigo ganin ba zai iya ba, ya ƙara kiran wasu likitocin aka nufi emergency da ita, da ƙyar suka shawo kan matsalar. Alhaji Farouk da Mimi suka kalli Dr ta ce "Ban fahimta ba Dr mene ya samu yarinyata?" Ya gyara zama yana zame Glasses ya ce "Bayan hawan jinin da take da shi, ciwon zuciya ya shige ta da ƙarfi, bai kai matakin aiki ba, amma irin shi da wuri yake kisa, domin ganin yarinyar ku ta ci-gaba da rayuwa a duniya ya zama dole ki bata abin da zuciyarta ke so" Kuka ya ƙwacewa Mimi Alhaji Farouk ya ce "Me take so har haka? Idan kuɗi ne akwai komai take so za a siya mata" Mimi tana kuka sosai ta ce "Abin da Zahrah ke so, kuɗi bai isa ya siye shi ba, ko da zaka ƙarar da gabaɗaya dukiyarka ne, ba zaka sama mata Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu ba" Alhaji Farouk ya miƙe ya ce "Dole naje na samu mahaifiyar Yaa Sheikh da Abba Hakimi tun da mahaifin shi baya duniya ya zama dole" Cikin dare wajan ƙarfe 3 Halisa na zaune a saman kujera hannunta riƙe da ice cream wanda Maimoon ta siyo mata a Havilla, ta saka a freezer ya ƙara sanyi tare da ƙanƙara. Ta lumshe idanu tare da siɗe ƙaramin cokalin da baki sanyi na ratsa ta sosai, yana ƙara sanyata cikin wani hali feelings mai tsanani na ta so mata, ta ajjiye ice cream tare da miƙewa tsaye daga ita sai Riga da wando na Pajamas white colour Yaa Sheikh's favorite colour ta sanya Scuff faux-shearling slippers sai ƙamshi take ƙirjinta ya ƙara cika, ta miƙe zata juya zuwa cikin bedroom kenan ta ji an ɗaga ta cak tare da fara tafiya da ita...https://vm.tiktok.com/ZMYJCVDeF/ Ka shiga link ɗin ka faɗi kalma ɗaya mai kyau akan littafin idan ba ke👆🏾08119237616 Ko ba a faɗa ba, tasan shi kaɗai ne zai iya yi mata haka, ta shiga kokawa zata ƙwace kanta amma ta kasa, ta daddage ta fasa ihu ta ce "Wallahi zan maka ihun kwarto idan baka sauke ni ba" bai shirya tunan asirin da take shirin yi masa ba, ya yi saurin dire ta ƙasa yana riƙe da hannayenta, kalmomin da zai mata bayani yake ta harhaɗowa a bakinsa amma ya kasa samun cikakkiyar kalma ko ɗaya, ganinta kusa da shi ba ƙaramin barazana bace ga zuciyar shi da kuma abin da ke addabar shi tsayin satittika. Ya numfasa yana riƙe kan shi gudun kada ya yi abin kunya a gaban ƴar ƙaramar Yarinyar dake neman jan shi a ƙasa ya ce "Zawja ni ne kwarto?" Ta kame fuska tare da ɗauke kai can, ganin yadda muryarta ke tasiri a zuciyar Yaa Sheikh take saukar masa da nutsuwa yasa ta ƙara tsuke ɗan ƙaramin bakinta. A raunace cikin wani sabon yanayi mai wahalar fassaruwa YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU ya furta. "Zawja ƴar fillona come to your husband, why are you doing this to me, am I stranger?" Cikin ƙarfin hali, da rashin nutsuwar Zuciya data gangar jiki ya furta hakan. Halisa ta ƙwace hannunta tana yin nesa da shi taƙi cewa komai, babu alamar tausayi akan fuskarta... Taurin kan yarinyar ya bashi mamaki bai san lokacin data sauya ta zama mai kafiya da naci haɗi da zafin zuciya ba. "Anya kina son rabauta da ribar dake cikin zamantakewar aure Zawja? So ki ke na zama Ayuu!?" Ya yi shiru da nufin ko zata tanka masa amma tai mursisi dole ya tsuguna ya lashe aman da ya yi mai datti da wari, daman tabarmar kunya da hauka ake kwashe ta. "Na yi miki al'ƙawarin idan akan taɓa jikin ki da nake ki ke wannan kumfar bakin, to na haƙure zuwa lokacin da ranki zai fari, bana son ki ƙaura cewa Idanuna, IDAN BA KE ba san ya nake b" sai lokacin ta kalle shi ta ce. "YAA SHEIKH" Ganin kamar da gayya ta faɗi sunan na shi ya sa kawai ya bita da Idanu, yanzu ta dai na bashi mamaki, kallon mara tausayi wacce bata amsar uzuri yake mata. Ta kalle shi ta ce "Ba jikina ne bana so ka taɓa ba, so nake ka haƙura dani na tsayin shekarun da suka rage maka a rayuwa, ka yi zuciya ka bani takardar sakin daka furta kuma ka ayyana a ranka YAA SHEIKH ALIYU" cikin rawar murya YAA SHEIKH ya ce "ƙarya na ke, iya laɓɓa kawai na furta haka, IDAN BA KE babu wata rayuwa da zan iya" dariya ta so kama Halisa amma ta danne tana dafe ƙirji ta ce "Asstagafirullah, Allah na tuba ka manta ƙarya haramun ce?" Bai ƙasa a gwiwa ba wajan furta. "Ni ba Manzo ba, ni ba sahabi ba, ni bawa ne na Allah, a koda yaushe zan iya kauce hanya!" Ta ware hannunta irin "Anyway, is not problem" Ya langwaɓe kai ya ce "Kin yarda IDAN BA KE babu numfashin Aliyu" ta nuna shi da hannu ta ce "Wallahi ba zan koma gidanka ba, idan har ni ce kwanciyar hankalinka to ka shirya tafiya lahira da kwanan kabari" tana faɗin haka ta juya tana kaɗa masa ƙugu wanda suke ƙara sanya YAA SHEIKH cikin wani hali wanda shi kan shi ba zai iya furta ko fasalta yadda ya ke ji ba. Ya zube akan kujera yana dafe kan shi, bakinsa ɗauke da addu'ar samun sassauci da rahamar Ubangiji. Ya miƙe a sanyaye tare da nufar part ɗinsa yana zuwa ya nufi bathroom ya sakarwa kan shi shower da ruwa mai sanyi, ya daɗe tsaye yana mayar da numfashi. Ya ɗaura alwala yana fitowa ya saka Jallabiya Viridian green mai ƙaramin hannu, ya ɗauki hirami ya ɗora a kan shi tare da ɗaukan prayer mat ya shimfiɗa. Sallah ya yi raka'a biyu raka'ar farko ya karanta Fatiha da Surah Kafiroon, ta biyu ya yi Fatiha da Surah Al Ikhlas. Cikin sujjadar ƙarshe ya shiga faɗin. "اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْتَخِيرُكَ بِعِلْمِكَ، وَأسْتَقْدِرُكَ بِقُدْرَتِكَ، وَأَسْألُكَ مِنْ فَضْلِكَ الْعَظِيم، فَإِنَّكَ تَقْدِرُ وَلا أَقْدِر، وَتَعْلَمُ وَلا أَعْلَم، وَأَنْتَ عَلاّمُ الغُيوبِ، اللّهُمَّ إِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ Idan zama da Halisa matsayin matata shi ne alheri - خَيْرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، عَاجِلِهِ وَأَجِلِهِ فَاقْدُرْهُ لِي وَيَسِّرْهُ لِي ثُمَّ بَارِكْ لِي فِيهِ، وَإِنْ كُنْتَ تَعْلَمُ أَنَّ هَذَا اْلأَمْرَ شَرٌ لِي فِي دِينِي وَمَعَاشِي وَعَاقِبَةِ أَمْرِي، فَاصْرِفْهُ وَاصْرِفْنِي عَنْهُ وَاقْدُرْ لِي الْخَيْرَ حَيْثُ كَانَ ثُمَّ أَرْضِنِي بِهِ." Bayan ya kammala Sallar Istihara ɗin ya jingina da jikin gado idanunsa rufe, barci ya ƙaura cewa Idanunsa tare da yi masa hijira, ƙaramar yarinya na son Jan shi a ƙasa ya zama kamar bita zai-zai, bai taɓa mafarkin zata ƙaurace masa har haka ba,bai ɗauka bayan shi zata damu da ganin wasu nata ba, ya ɗauka iya shi ɗaya ya ishe ta a rayuwa. Ya ɗauka ba zata nemi soyayya mai zafi daga gare shi ba, sai gashi tunaninsa ya saɓa zaton shi. Har aka kira Assalatu yana zaune, rabon shi da cin kyakkyawan abinci har ya manya. Ya miƙe yana ɗaukan casbawa tare da yin waje. A harabar gidan yaci karo da Abba Hakimi da kuma Umar-khan da Ishaq-Hakim sun fito zasu nufi Masjid. Suka jera ba tare da kowa ya yi magana ba,cikin takun shi mai kama dana wahainiya, nutsuwa,kamala, kwarjini da tarin Ilhama dake kwance saman fuskar YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU ya shiga wajan liman tare data kabbarar harama, karatu ya fara a sanyaye cikin rashin sautin murya saɓanin da, gabaɗaya suka rasa meke damun shi yana yi yana rafkanwa, bayan ya sallame ya yi sujjada bayan sallama. (Sujjadar ba'adi). Wa'azi ya fara akan gudun duniya da duk wani kayan kyale-kyale dake cikinta. Misalin 10 na safe Abba Hakimi da Mother da kuma Umma A'isha na zaune saman kujera Halisa fito sanye da ƙaton hijabi har ƙasa, ta durƙosa har ƙasa ta gaishe su. "Matar ya ya akai ne?" Ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Jon wuro makaranta nake son na koma Please" ya daɗe yana kallonta yana jajanta lamarin kafin ya ce. "An shige ki da yawa, wanne mataki ki ke kafin ku dawo?" Ta ce "Jss2 zan shiga" ya ce "Tab, yanzu Kinyi girma sai dai a biya ki zana weac da neco, bana jin kuma zaki iya karatun University" Da sauri ta ce "Zan iya Jon wuro, Allah ina da ƙoƙari ko karatun Alkur'anin da ka ke mini haddace shi nake, gashi yanzu ina izu talatin da biyar" ya ce. "Na gamsu, duk da ina mamakin kaifin tunaninki da basirar da Ubangiji ya baki Halisa" Mother tai murmushi ta ce "Duk wanda ya zauna da YAA SHEIKH ai ba zai taɓa zama daƙiƙi ba,balle kuma wanda ya rena" walwalar fuskar Halisa ta ɗauke ta ce "Ai da ƙoƙarina Dada ta haifeni" Mother ta ce "Haka fa" ita dai tai shiru Abba Hakimi ya ce "Tambayi mijinki, shi ne zai baki iznin idan ya amince zan bawa Umar-khan ya yi komai" Tamkar zatai kuka ta ce "Ni bani da wani miji, ka dai na haɗani da kowa don Allah Jon wuro" daga bakin ƙofa aka ce. "Anƙi ɗin, bayan duniya ta gama shaidawa Gadanga shi ne mijinki kuma shi ne gatanki" Jadda ta ƙarasa faɗa tana shigowa ciki, Maimoon ta biyo bayanta. Daga tsaye Jadda ta ce "Halisa ki ke meye ne? Ke kam ba a nonon Khadijah ki sha wannan mugun halin ba, uwarki ba haka take ba, ta san halarci ta san kuma wanda ya yi mata, tun wuri ina baki shawara ki bi mijinki dau da ƙafa, kafin wata can tayi ciki tashi, ni Alkur'an da zai aure mata uku ma da ya kyauta mini, ai lafinki ne da ki ka sake masa jiki yana lugudan da ya yi niyya da shi, har ya banka miki ciki, waya faɗa miki ana yi wa namiji haka? Ai basu da kunya ta wannan ɓangaren kuma tunda kuka fara dole ku ƙare tare, balle namiji kamar Malam wanda ya karanta yaji komai a Muslunci" Wani takaici ya kama Halisa ta ce. "To ya yi auren mana, ni daman ai bana son shi" Jadda ta dungure mata kai ta ce "Laa! Ji tsinanniyar ƙarya, mai ƙarya a ƙona shi a wuta yasin, gashi nan kin cika kin yi fam! Alamar kin son buƙatar mijinki mayya kema ɗin fitinanniyya ki yi ta lalata ɗan jama'a yanzu ki guje shi" ta juya kan Abba Hakimi ta ce "Can fa naci karo da shi, wallahi sai dana zubar masa da ƙwalla, ni na ɗauka ma da wani ɗan ganyen nai karo kai Allah ya sa mu gama da duniya lafiya, wai Malam ne soyayya ta rugurguza shi haka, huhuhu! Ke kam ba zaki taɓa gamawa da duniya salamun ƙaulin ma idan har baki rungomi mijinki da hannu bibbiyu ba, idan ba yara ki ke so kina samun cikinsu akan titi ba" ba wanda ya kulata can ta nisa ta ce. "A to meye ma ruwana, wannan rayuwar kowa yaji da abin da yake gaban shi, Allah ya sa ba wata tsiyar na ce ba, amma dai ƴar mutan Rome kinci amanar malam" Umma A'isha ta ce "Amana kam ta ci" Jadda ta muskuta ta ce "To Ubangiji ya san yadda zai da lamarin, ko kuma kawai ya saki ƴar banza mai zubin zabiya, ni da ƴata ce da tuni na haɗa mutin a gaban kowa zai ɗaga mata nono" ta jinjina kai ta ce "Allah ya san yadda zai da lamarin" Halisa ta haɗe fuska sosai ta ce "Idan auren a hannunki yake yanzu ki sake mini shi, ko ki je ki sanya ya sake ni ki ga idan zan mutu masifaffiyar mata kawai" Jadda tai mitsi mitsi da idanu ta ce "Kiga masifa akan Mai rawani Wlh shi ne azababbe, meye nawa da zan raba haɗin Allah?" Mother ta shiga cikin zan can ta ce. "Rabo da Jadda kin ji daughter, gidan Aliyu ne ba zaki koma ba" Ta kalli Abba Hakimi ta ce "Jon wuro makarantar?" Ya numfasa ya ce "A'a, ba ruwana jeki nemi izini wajan mijinki,kafin ya ce baƙin ciki nake masa" Ta miƙe zuciyarta babu daɗi bata son duk abin da zai sanya ta shiga sabgar shi. Bayan tafiyarta Jadda ta ce "Maryam haƙuri nazo baki, ki daina gani na kamar tsohuwar banza nasan me nake, Yaran da Ubangiji ya azurtaku dasu zaki duba, kada rayuwar su ta ƙare a haka" Mother ta ce. "Ayya Jadda kin yi mini adalci kuma ki fahimci ni, wallahi a yanzu bana son Engineer ko kaɗan, zaman court kawai nake jira ya sawwaƙe mini kuma ya bani ƴaƴana..." Mother ta dinga faɗa ta inda ta shiga bata nan take fita ba. Jadda ta fashe da kuka ta ce. "Azaba, daga nemen taimako sai zagi Maryam?" Dr A'isha data shigo yanzu ta ce. "Babu batun zagi, Gasky ce kawai ya bata raguwar sakin ya je ya yi rayuwa da sauran karuwai" Mother ta kalli Dr A'isha haka kurum kalmar ƙarshe ta ɓata marai har taji zafin Dr A'isha ɗin. "Ya je ya yi rayuwar da sauran karuwai" hausawa sun yi gaskiya da suka ce ba a shiga tsakanin miji da mata, duk lalacewar mijinki dole a kira shi da uban ƴaƴanka, bare kuma _first love_ Jiki a sanyaye Jadda ta fito daga gidan, Engineer dake cikin mota gaban shi ya faɗi ganin yadda mahaifiyar ta shi ta fito, gabaɗaya Ƴan-uwan shi suƙi saka baki cikin matsalar. Dr A'isha ta miƙe ganin Mother bata tanka ta ba, ta nufi bedroom ɗin Halisa ta shiga bata kyakkyawan darasi akan ƊA-NAMIJI ta ɗora ta akan tubalin da zata ka Yaa Sheikh hankali kwance duk ta nunawa Dr A'isha ita bata ra'ayin Yaa Sheikh yanzu, karatu kawai take so. Ta rantse da abin da zai kasheta ba zata koma gidan shi ba, balle auren shi. Dr A'isha ta bata sabuwar waya mai kyau tare da sim, ta buɗe mata komai WhatsApp, Arewabooks, wattpad. Ta nuna mata yadda ake karatun littafin duk ta iya Hausa harda ɗan turanci. Kana ta sakata cikin wani shahararren group na MU MA MATA NE. Ta ƙara yi mata gargaɗin kada ta kuskura ta ƙara barin Yaa Sheikh ya taɓa koda hannunta ne. Kiran Ummul a waya ya sanya Yaa Sheikh shiryawa cikin wata dakakkiyar shadda mai kyau da ɗaukan idanu, fara tas ya ɗora hirami idanunsa maƙale cikin sirirn farin Glasses photochronic and faɗawar da kwayar idanunsa tayi. Kasancewar ranar juma'a ne ya ɗora Alkyabba mara nauyi, ya fito a babban malami mai ɗaukan ƙaddara a ko wanne lokaci da yarda da ita, ba zai iya driving ba haka ya sa Umar-khan ya yi driving nasa zuwa grandparents house ɗin shi. Ya fito a nutse bakinsa ɗauke da zikirin ranar juma'a ya ɗaga idanunsa ganin garin a lullume alamar hadari ne a ƙasa, ya ɗauke yana shigewa ciki. Wacce ya gani zaune a parlourn ya bashi mamaki ainun, yaushe ta zo? da izinin wa ta fito? Ƙarar shi ta kawo wajan Ummul ɗin shi ko ya ya? Ya yi sallama bashi da tabbacin da amsa, amma yana da yaƙinin zata amsa ɗin, kafin ya zauna Ummul ta fito hannunta riƙe da plate na wainar fulawa da lemon kankana, suka haɗa idanu ta ce. "Sai yanzu?" Ya zauna gefenta yana jinjina kai ta ce "Daughter ga wainar nan, ɗan malalen kuma ba a ƙare ba" Halisa ta yi murmushi ta ce "Thank you Ummul ɗina" Maimoon ta ce "Zan ci ni ma" Halisa ta shagwaɓe fuska idanunta cike da ware tana buga ƙafa ta ce. "Ummul kin ganta ko?" Ummul ta ce "Maimoon bar mata, taci tai ƙiba" Yaa Sheikh ya tabbatar gangar jikinsa ce kawai ke tare da shi, amma gabaɗaya tunaninsa, zuciyarsa, ruhinsa yana gare ta, bai taɓa ganin yadda aka so uwa kuma aka tsani ɗan ta ba. Ummul ta juya kan Yaa Sheikh ta ce. "Ina son ka bawa Daughter dama ta koma makaranta" kafin Yaa Sheikh ya yi magana Alhaji Farouk ya faɗo cikin parlourn...Alhaji Farouk bai gama sanin Ummul ba, amma nutsuwarsu da ta zo ɗaya da Yaa Sheikh ya sa kai tsaye ya gano ta, ya yinda da ita Ummul ɗin ganin farko ta wayi fuskar shi sbd kamar da suke da Zahrah, ba tare da nuna wata damuwa ba kasancewar ta wayayyiya ta ɗauke kai daga duban shi. Yadda ya faɗo musu parlour without everyone's permission ba sallama ba komai shi ya ɗan sosa mata ranta. Halisa ma ɗauke idanu tayi haka kawai ta ji zuciyarta na buga Jikinta ya mance murus. Yaa Sheikh bai kalli Alhaji Farouk ba, bai kuma yi mmkin zuwan na shi ba, a irin gane-ganen shi ya gano kusan dalilin zuwan Alhaji Farouk ɗin. Alhaji Farouk ya zube saman carpet bakin shi na rawa ya ce. "Am sorry na shigo without permission, ayi mini afuwa" Ummul ta ce "Ba damuwa,idan har lafiya?" Ya girgiza kai ya ce "wallahi ba lafiya ba Hajiya Ummul-khairy, ina cikin tashin hankali, damuwar da kuɗin da nake da shi bai isa ya siye ta ba, ko ya biya mini ita ba" Ummul tai jim Kafin ta ɗauke numfashi idanunta can akan plasma ta ce "To! Ubangijin al'arshi ya yi mana magani" Alhaji Farouk ya kasa cewa komai, sbd wani irin nauyi da Ummul ta yi masa a cikin idanunsa, wani kwarjininta na musamman ya mamaye shi har ya gaza cewa komai, gabaɗaya kalaman shi suka ɗauke tare da yin hijira daga cikin bakinsa. Ummul ta fuskance shi tana girgiza ƙafa ta ce "Alhaji Farouk ko? Ya akai ne ka same mu cikin uzuri mu ma" Ya goge zufar data yanko masa, Ummul ta kalli Umar-khan daya shigo ta ce "Umar-khan ƙaro mana A.cn nan ko?" Ya ce "To! Ummul!" Alhaji Farouk ya rusuna sosai tare da yin zaman ƴan bori ya ce "Taimako nake nema Hajiya Ummul, ki dobi girman Allah dana Manzon shi, kada ki dubi girman laifin da Zahrah ta wanzo tana aikatawa a gareki, wallahi ke kaɗai ce matakin da zanbi wajan ceto ran ƴata dake gadon asibiti, cikin halin rayuwa ko mutuwa...," Ummul ta tari numfashin shi da cewa "Kamar Alhaji Farouk ya yi makkowa, Ubangiji ke da rayuwa shi ke da mutuwa, kuskure ne haɗa wannan da wani bawa" ya jinjina kai ya ce "Haka ne, na ji na ƙara samun ƙarfin gwiwar faɗa miki komai, na fahimci ba iya ɗanki ke da ilimin addini da sanin Allah da yarda da ƙaddara ba, hadda ke kan ki" Yaa Sheikh gabaɗaya a takure ya ke jinsa, duk kalma ɗaya da ake faɗa har tsakiyar kan shi yake jinta, shi ya sa ya yi baya a hankali tare da yin lamo jikin kujera yana riƙe hannun Ummul. Alhaji Farouk ya ɗora da faɗin "Nasan idan na faɗi abin da yake rai ka, za kuga kamar na zama mara kunya, na sani duk wani uba dole zai so abin da yarinyar shi ke so, irin son nan na mutuwa wanda zai iya kaita lahira, ki kwatanta hakan matsayin ke ce mahaifiyar Zahrah, zaki iya zuba idanu ta mutu akan soyayyar wani babban Malami, masanin addini, a faɗin nahiyar nan tamu ta wajanta baki ɗaya, malamin da yake da nagarta wanda ake sauraran tafsirin shi fiye dana sauran Malaman da muke da su, malamin daya mallaki bankununi adadin wajan biyar, reshen, Kano, Kaduna, Abuja, Katsina da sauran su, wanda ya mallaki kamfanin sarrafa shinkafa domin ra gewa talakawa farashin yadda suke siye wajan wasu, malami na farko da aka samu ya buɗe gidan marayu yake ciyar da su, da kuɗin shi, yake basu karatu, malamin daya raya makarantun tsangayoyi zuwa na zamani, ina nufin YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU" Cak Halisa ta ajjiye wainar data ɗakko da zummar kaiwa bakinta, daman tunda aka kawo bata ci ba, tana ƙoƙarin ci Alhaji Farouk ya shigo. Bayanan shi suka sanya ta kasa ci sai yanzu da take shirin ci ta ji abin da ya nemi tarwatsa mata zuciya da sanya ƙaramar kwakwalwarta cikin halin troma, wani irin masifaffan kishi ya ta so mata, ƙirjinta ya yi mata nauyi, numfashinta ya tsaya cak wanda ya sanya ta shiga kokawar dawo da shi amma abin ya gagara idanunta ya shiga rufewa kamar mai shirin suma, hawaye na fitowa daga cikin idanunta da sukai jajir. A firgice Maimoon data ankara ta ce "Anti Halisa me ne ya sameki, lafiya innalillahi Ummul Yaa Sheikh Anti Halisa suma take wallahi" Yaa Sheikh ya buɗe gajiyayyun Idanunsa wanda kwana biyu barci ya ƙaura ce daga cikinsu, yana yunƙurin ta shi Ummul ta girgiza masa kai tare da yi masa nuni daya koma ya zauna Ya bi umarnin ta, ya zauna yana mai riƙe kan shi, a zuciyar shi tsoro da fargabar abin da ya jefa Zawjan shi cikin wannan yanayin yake, yanzu ƙwayar idanunsa suka hangota lafiya lou yanzu kuma ta rikice kamar wacce ke farfaɗiyya ko wacce Aljanu suka bugar. Ummul ta tallafo Halisa Jikinta tare da amsar ruwa mai sanyi daga wajan Maimoon ta shiga shafa mata a fuska, a hankali ta shiga bata ruwan, Maimoon na murza hannunta zuwa tafin ƙafarta. Duguwar ajjiyar zuciya ta ja a wahale idanunta na buɗewa da ƙyar, wani irin zafi da raɗaɗi take ji a ƙasan zuciyarta wani abu na yi mata yawo. "Sannu Daughter, ƙwarewa ki kai hala?" Maganar Ummul ta ƙara dawo da ita daidai, ta ɗauka it was a dream ganin Alhaji Farouk zaune ya sa ta runtse idanunta muryarta na rawa ta ce. "Zuciyata zafi take Ummul gida zani" ta faɗi hakan ta biyu, tunaninta ko Yaa Sheikh zai tashi hankalinsa har yazo gareta ta sauke masa masifar dake damunta, sai taga ko inda yake bata kallo balle yasan meke damunta, hakan ya ƙara tunzurta wani baƙin ciki ya ƙara ninkuwa sosai fiye da sosai ta fashe da kukan sanin abin da yake damunta. "Mene na kukan kuma?" Ta shagwaɓe fuska tare da basarwa ta ce "Ummul kai na ke ciwo sosai, na ji ba zan iya cin wainar ba" Ummul tai murmushi kawai ita ma ta nuna kamar ba komai ɗin ta ce "Daughter baki dai na kukan ciwo ba, jeki kwanta to" ta kasa cewa komai sai naɗe ƙafa da tayi kawai Ummul ta koma ta zauna, Maimoon kuka ta ɗauke wainar ta fara ci. "Alhaji Farouk ban fahimci zan can ka ba?" Ya numfasa ya ce "Ina nufin ki yarjewa Yaa Sheikh ya auri ƴata Zahrah a karo na farko, ciwon zuciya ne ya kamata,kuma tana matakin ƙarshe don Allah kada soyayyar ɗanki tayi silar mutuwar tilon ƴata da nake da ita a duniya" A wannan karan Halisa zama tayi kamar zararriyya duk sukai banza da ita, idan ta kalli Yaa Sheikh sai taga idanunsa rufe, tana ɗauke idanu yake buɗe na shi ya kafeta da jirkitattun idanunsa masu ɗauke da wutar sonta kamar rai da Ajali. Ummul ta ce "Da zan yi taking revenge akan Zahrah da tuni nayi, kawai bata gabana bata kai na tsaya ɗaukan hukunci kan ta ba, nasha ganin cases kala-kala, bayan kasancewa police ina aiki da hukumar NASA tare da CVI, ina son ka ɗauki wannan matsayin ƙaddara, wanda kuma ance cikar imanin mutum shi ne yarda da ƙaddara, idan ni zan saka Arɗo ya auri Zahrah to har abada ba zan sahale masa ba, domin babu kyautatuwar hakan, dubi abin da ya faru tsakaninta da wanda ya raini Aliyu, amma idan har shi Aliyu ya amince zai aureta to gaka ga shi nan, ba zan hana shi aure ba, domin Ubangiji ya umarci maza da auren mace sama da ɗaya har zuwa huɗu, idan kuma ba zai iya adalci ba, ya auri ɗaya domin ita ce mafi a'ala a gare shi" Umar-khan da Maimoon hadda ita Halisa suka kalli Yaa Sheikh suna jiran jin abin da zai ce Alhaji Farouk ya ce "Ka taimaki addinin Musulunci, ka auri Zahrah ka ɗauka jahadi kayi,ina iya yin komai domin ganin ka amince" ya shiga ƙoƙarin durƙosawa gaban Yaa Sheikh, Yaa Sheikh ya yi saurin kama hannayen Alhaji Farouk ya ce. "إِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تُقْسِطُواْ فِى ٱلْيَتَٰمَىٰ فَٱنكِحُواْ مَا طَابَ لَكُم مِّنَ ٱلنِّسَآءِ مَثْنَىٰ وَثُلَٰثَ وَرُبَٰعَ ۖ فَإِنْ خِفْتُمْ أَلَّا تَعْدِلُواْ فَوَٰحِدَةً أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَٰنُكُمْ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰٓ أَلَّا تَعُولُواْ" Yaa Sheikh ya dubi Alhaji Farouk da kyau ya ce "Dalilin da suke sakawa mutum ya ƙara aure na da yawa, akwai rashin samun mace ta gari, akwai rashin kwanciyar hankalin iyali, akwai rashin gamsuwa da iyali, sai ka ƙara aure idan kaga da cutuwa" ya yi jim kafin ya miƙe tsaye ya ce "Wani matar shi ke buƙatar hakan, akan sake da damar ta, taji yana iƙirarin IDAN BA KE amma ai ba ita ɗaya ba ce a duniyar ko? Wani ƙazamar mace ya haɗu da ita, wani kuma ya bi kyau wajan auren daga baya fahimci kyan yana gushewa ba kuma shi ne fa'ida ba, shi ya sa Manzon Sallallahu alaihi Wasallama ya ce "Mafi cancantar aure shi ne, wacce zaku aura dan nagarta,ko nasaba mafi alheri ita ce mai addini, a wannan gaɓar na amince da auren Zahrah matsayin nagartar da ka ke da ita, ina fatan zata zama macen rufin asiri" Maganar ba iya Halisa ba, har Ummul sai ta daka, tasan da biyun yake maganar amma batun amincewa auren fa? Halisa daɓas! Ta yi Idanunta ƙurr a gefe guda ta ka ɗaita a zuciyarta tana auna zantukan Yaa Sheikh. Alhaji Farouk hawayen farin ciki ya sakko masa ya riƙe hannun Yaa Sheikh ya ce "Na gode, Na gode Allah ya saka da alheri Malam, Allah ya jiƙan magabata" suka jere har waje, suna fita Yaa Sheikh ya dakata tare da fara yiwa Alhaji Farouk magana mai muhimmanci, cike da farsaba da lafazi mai daɗi. Halisa ta rarrafa da ƙyar tare da shigewa wani bedroom tana zuwa tasa key ta murza ta zube a gado tana rusa kukan rashin makama da abin yi, ta rasa abin da ya sanya take kukan kawai ta ji ba zata iya bari ya wulakanta ta ba, bayan da auren shi a kanta, inma zai auren ya tabbatar ya bata divorce paper ɗin ta. Wayarta ta ɗauka ta shiga kiran Dr A'isha tana ɗauka ta fashe da kuka ta ce "Na shiga uku Adda A'isha zuciyata zata buga" Dr A'isha ta ce "Kin san bugawar zuciya kowa? Meke faruwa ma tukun?" Ta sauke ajjiyar zuciya ta ce "Abbana aure zai yi, kuma Zahrah zai aura" Dr A'isha ta rusa wata ashar ta ce "Kut wannan zance ne, This is something that will never happen, ƴar iskar yarinyar zai haɗa muku shimfiɗa, da ita?" Kukan Halisa ya ƙaro sosai fiye da kima ta ce "Allah ni ya bani takardar sakina na ji bana son zama da shi ɗin" Dr A'isha ta ce "Oh no dear, ba haka za ai ba, dole shi zai nemeki da kansa, kada ki taɓa yarda da cewa kin masa laifi kuma ki basa haƙuri, har abada shi zai na baki haƙuri ke macace ke ce wacace ki ke da abin bashi, ina ƙara jan kunnenki kada ki kuskura ki bashi damar da zai riƙe koda hannunki ne, ki jan shi a ƙasa ya zo har inda ki ke" Halisa ta yi sak a lokacin tana jin kamar ba daidai bane wannan zan can na Dr A'isha ta ce "Abbana zan ja a ƙasa? Babbane fa kuma Malami" Dr A'isha ta ja tsaki ta ce "Mtwss ji shirme ko? Shi namiji ba ruwan shi, duk girman shi, duk maluntar shi akan wannan abin dake wajan mace sai ya zama yaro ƙarami saboda da maita, da zarar abin da suke kwaɗayi ya tsofa sai su fara tunanin hanyar da zasu bi su ƙara aure domin ya yin ta gida ya kau, kuma ai laifin na shi ki nuna da gaske bakya ra'ayin shi takardar saki kawai ki ke ya baki" Nan da nan Dr A'isha ta ƙarasa kurɓata raguwar tunanin ƙaramar kwakwalwar Halisa a sanyaye ta ce "Thank you, I'll try my best ganin nai haka" sukai Sallama daga nan Halisa ta kunna network ta shiga WhatsApp kai tsaye grp ɗin MU MA MATA NE ta shiga bayan ta yi sallama ta ce "Don Allah ƴan uwana mata ga muhawara" kasancewar yamma ce ya sa duk manyan matan suna online suka shiga faɗin. "Muna ji" Ta ce "Kana da miji, yana son ka, so irin na mutuwa, sai saɓani ya haɗaku akan ba zaka je kaga dangin mahaifinka ba, bayan tun da aka haifeka baka taɓa ganinsu ba, kuma su ne farin cikin ka, har ya furta cewa idan har ta je to ya yanke auren dake tsakaninsu, ita kuma bata je amma ta dage sai ya saketa, ya bata haƙuri amma taƙi gashi yanzu aure yake shirin ƙarawa, shi ɗin mabuƙaci bashi da haƙuri akan abin da ya ke, don Allah idan ke ce ya zaki?" Da wata number mai username ɗin: Akeela Mrs Akeem. Aka ce _Shir me kawai_ Wata babbar mace harta shige Maganar sai ta dawo ta fara typing ta ce "Kai tsaye zan iya cewa mahaukaciya ce, kuma In sha Allah sai ya ƙara aure,mata wani lokacin basu da tunani" Akeela ta tura emoji na dry tare da yin reply akan maganar Sarah ta ce Akeela😂🤦🏻‍♀️Sarah Mrs Abeedeen Abdul-jabbar Abas wannan ba yi ba ne gasky, idan kuma matsalar ta Halisa ce fa?" Sarah bata bada amsa ba, sai wata mai suna Julde ce ta ce Julde: Ta yi kuskure gasky, ni ma haka na tafka wannan kuskuren har mijina Abu-maleek ya fara masturbation, shi namiji ba a hukunta shi da Wannan akwai hanyoyi na hukunta miji banda wannan, ni ma dai zan so ya ƙara auren ƴar banza taci malafar gidansu" Sarah: ta ce "Bari kawai Julde, ita Halisa ai ba zata aikata haka ba, mijinta ba shi ne babban malamin nan ba?" Da sauri Halisa ta fara typing ta ce. "Laa Wallahi ba ni ba ce, kawai a wani grp na gani shi ne na yi sharing da ku" maganar tai girma aka fara tafka muhawara mai zafi wasu su tsinewa Halisa ba tare da sun sani ba, wasu kuma su goya mata baya akan ƴan uwa su ne komai, miji zai iya barinka banda ƴan uwa. Jiki ba ƙwari tai Offline tana sakin wani sabon kukan a haka har barci ya ɗauke ta. Bayan sallar magriba Yaa Sheikh na zaune a wani haɗaɗɗan parlourn gidansu Ummul da ƙyar ya iya shanye kunun gyaɗar da tayi masa, he lost his appetite. A karo na farko da Ummul ta ce "Yaa Sheikh wannan kasa dace, auren Zahrah?" Ya kalleta idanunsa na rufewa ya rame sosai ya ce "Ya zan Ummul?ke ma kin goya mata baya" Ummul ta ce "Ba baya na goya mata ba, kai na haifa ba ita ba, babu yadda za ai na tilasta Halisa ta dawo wajanka za taga kamar don kai na haifa ba ita ba, zan ƙara faɗa maka kayi kuskure daka hana ta tafiya da kuma furucin da kayi shi ne ta riƙe a ranta har haka" ta jina kai yana son amsar laifin shi ko ta halin ƙaƙa kafin a raunace ya ce "Ban hanata da wani dalili ba Ummul, ina son na zama ni ne silar zuwanta gare su, na kasa jure yadda ake mini hawan ƙawara, ita ɗin ƴar gata ce, tana da Abba, Dada, grandparents ɗinta they are still alive, tana da yaya uwa ɗaya uba ɗaya, she have a siblings kamar su Khalil Maimoon, ni fa? Ke ɗaya nake da ita, Zawja kawai nake gani a idanuna bayanke.." Ummul tai ƙasa da kanta she was trying to hide her tears Sarai ya fahimci me take don haka ya miƙe tsaye zai fita tayi saurin miƙewa ta riƙe hannunshi ta ce "Idan auren Zahrah kana ji shi ne mafita, kuma shi ne tubalin da zai dawo maka da wacce zuciyarka ta buɗe ido a sonta kayi haka, bana son ka auri sbd ba zaka iya adalci ba, kuma kafi kowa sanin hukuncin hakan, ni ɗin dana rage maka na ɗauki nauyin Uwa, Uba, ƴan uwa a gare ka Aliyu, ka lalace sbd mace ka fita hayyacinka bana son ganinka haka, kada ka sake naji labarin ka ɗauki azumi gobe" ganin Ummul na shirin kukan da gaske muryarta na rawa sosai ya shige Jikinta ya rungometa ya ce "Ba zan ba Ummul, amma sai na fi azabtuwa idan har ban azumi ba" ta rungume shi tana shafa kan shi ta ce "Akwai Allah Arɗo, lokaci ya yi da zaka koma Rugar Bello ka amshi kujerar mahaifinka ka gana da ƴan uwanka na can" ya jinjina mata kai ya ce. "Ina shirye-shiryen tafiya aikin hajji, zan fara zuwa Yola ta can sai na shi ge, bana son a sanar da Zawja zan yi tafiya ko barta karatu ne na sahale mata tayi zan yi haji daga gare ta" Ummul ta sake shi ta ce "Haji kuma?" Ya lumshe idanunsa ya ce "Koyarwar Annabi ne, lokacin da matansa suka ɓata masa rai sai ya tattara kayan shi yabar gidan tsayin kwana 40 zuwa arba'in da wani abu" A nan bedroom ɗin Ummul ya kwanta bayan yaje wajan dattijo kan shi a cinyarta tana shafawa tun yana magana a hankali har barci ya ɗauke shi. Ta ƙora masa idanu babu abin da ya bari na mahaifin shi,komai ya ɗauke haƙuri da sanyin hali, da kuma kafiya a soyayya ta ajjiye kan shi saman pillow kana ta fita, cikin dare kamar haɗin baki wajan ƙarfe 3 suka buɗe ƙofa dake duk gidan Ummul ɗin suka kwana ba tare da sanin junansu ba, karon dasu ka yi ya sa Yaa Sheikh ya ɗan ja baya ita kuma ta yi baya zata faɗi sbd tsoro ya saka hannu ya riƙeta tare da dawo da ita dab da shi, suka kalli juna ya zame zai bar wajan tayi saurin shan gabansa kamar yanzu ne komai ke faru ko sunan Zahrah bata ƙaunar a ambata ta ce "Kabani takarda ta" ya harɗe hannu a ƙirji sosai yana ƙare mata kallo bai ce komai ba, bai kuma raɓi inda take ba ta fashe da kukan rainin hankalin shi gabaɗaya tayi kan shi tana zuwa ta faɗa jikinsa tare da zagaye hannayenta a ƙugun shi ta fasa wani irin ihu tana ƙanƙame shi ta ce "Wallahi babu inda zaka sai ka sakeni ba zan ƙara zaman aure da kai ba kona kwana ɗaya.... *Kada ku manta sunan Littafin IDAN BA KE masu cewa labari ya ƙare kawai ja nake you're guys are mistaken.. ni ma ɗin ai na fi na gama ko? Sbd na samu peace of mind na samu cikakken hutu kafin Allah ya a haɗamu a wani bayan Ramadan. Burina kuna karatun da idanun basira, kuna hango daidai da kuskuren dake cikinsa ba wai kawai nishaɗi ba ya haka ne zan fahimci nawa kuskuren..... Mata masu ɗaukan shawarar ko wanne mutane a kiyaye wata shawarar mugunta ce, kuma ba don Allah ake baka ita ba, sadaukarwa ga masu ƙaramin tunani irin na Halisa.https://vm.tiktok.com/ZMYeKp4XV/ Follow my account👆🏾 comment, like, share❤️🫶🏼💋 Yaa Sheikh ya riƙe kan shi daga rungumar da tayi masa, ya rufe idanu yana sauke numfashi a hankali, ji ya yi komai na shi ya sauka daga kan setting, duk yadda gangar jikinsa da zuciyar dake ɗauke da sabon son matar malam a kullum sukai kewar Jikinta, muryar, rigimarta haka ya kame kan shi ba tare da nuna cewa da gaske ya azabtu da rashinta kusa da shi, ya shirya nuna mata ita ɗin kawai ya ke so, ba wani abu data mallaka daga baya ba, zai tabbatar sai ta neme shi da kanta. "Ba zan zauna da kai ba, bana son ka Yaa Sheikh tun da bani ka ke so ba, ba farin cikina ka ke so ba, gangar jikina ka ke muradi" Har lokacin tana riƙe da shi tana kuka kamar ranta zai fita, abu biyu ke mata zafi da ƙona a zuciyarta, yadda ya amince da batun auren Zahrah wanda ko a mafarki bata yarda cewa zai iya ƙara wani auren ba, balle ta yi tunanin zai auri wata aba wai Zahrah? Raguwar maza da raguwar mariƙin daya riƙe Yaa Sheikh ɗin Matsayin ɗan cikin shi, shi ne yanzu ya amince ya amshi raguwar mahaifin shi. Ya ware idanunsa akanta cikin rashin son magana mai tsayi ya ce. "Sake ni Matar Malam!" Tayi saurin sakin shi domin tama manta ta riƙe shin. Ta ce "Ai dan ban sani ba, kasan ba zan taɓa riƙe jikin ka ba" Ya jinjina mata kai kawai tare da juyawa a zuciyar shi ya ce "Matar da duk ita ta lalata dani, da ban ɗanɗani zaƙin ba ina zan damu, ina ganin shaiɗan cin mace ni Aliyu" "Don Allah ka sake ni, zuciyata bugawa zatai muddin naci gaba da sanya ka cikin idanuna matsayin mijin dake aurena, kaje can ka auri raguwar uban riƙon ka" A wannan karan ya kasa shanye maganganun Halisa, yadda take fidda zance kamar wacce aka zaunar tare da yi mata huɗuba. Ya juya bakiɗaya zuwa inda take fuskar shi tayi jajir alamar wannan shi ne karan farko da ranshi ya ɓaci da maganganunta, tai tsaye zuciyarta na bugawa tare da harbawa ganin yadda ya yo kanta babu wasa akan fuskar shi, sai tsoro ya kamata. Yana zuwa ya yi mata rumfa zata ja baya ya saka hannu ya damƙo ƙugunta tare da jawota ya mannata da na shi ƙugun, ta lumshe ido tana fidda numfashi, sbd wani abu daya shiga yi mata yawo mai kama da feelings. Ta nemi ƙwace kanta domin iya turaren rojan daya kama cika ɗakin kaɗai ya isa ya sauya mata lissafi balle kuma yanzu da ƙugunsu dake manne, kwantaccen gemun shi mai laushi kwance a wuyanta yana shafa mata, yanayinta ya sauya ta kasa motsi a hankali cikin nutsuwa yana mai ƙara fahimtar yanayin nata saɓanin ita da bata ga sauyi ko guda tattare da shi ba, Ya goga mata tsinin hancinsa a fatar wuyanta yana nai fesa mata zazzafan numfashi mai ɗauke ƙamshin mouth mint chocolate freshener, ta buɗe ido da ƙyar wanda suka jirkita ta sanya cikin nasa idon kamar yadda yake kallonta. Ya zura hannunsa ta ƙasan ƴar rigar barcin dake cikinta, ya ɗora tafin hannun a saman cikinta ta wajan mara, a hankali yaja ido tare da rufewa numfashinsa ya ɗauke na wani lokaci sbd ɗumin cikinta daya ratsa hannunsa, wata Soyayyar uba da ɗan shi ta bijirowa Yaa Sheikh, ƙaunar abin da ke cikin Halisa ya mamaye dukkan ƙofofin dake zuciyar shi, ɗiya maca ce? Ɗa namiji ne bai sani ba, amma son ko wanne jikinsa ya kama Yaa Sheikh, tare da son uwar Unborn ɗin na shi. Nan da nan Halisa ta birkice ta nemi nutsuwarta ta rasa, bakin neman sakin ya yi shiru ji take tamkar ya jata ya rungome, a zame jikinsa ka ɗan tare da zamewa ya tsuguna akan qwiwoyin shi nutse cikin wani mataccen yanayi duk da yana riƙe kan shi ya ɗora bakinsa a mararta tare da sumbata, wajan zame bakinsa ya sakar mata wani kyakkyawan kisses wanda ya sanya tai saurin kama sumar kan shi, ya dinga addu'a yana tofawa a cikin kafin ya miƙe tsaye, yana miƙewa tayo jikinsa zata rungome ya ja baya yana faɗin "Ki ke cewa me?" Ya faɗa a gajiye yana jan gemunsa, Baƙin ciki da takaicin ya cika ta ya kunna ta da ashana tare da sanya fetur ciki, amma ya barta ita ɗaya tana ƙona kanta. Zafi biyu! Ya ƙaro da ƙyar take buɗe ido ta ce "Nace bana son ka Aliyu!" "Aliyu?" Ya maimaita a zuciyar shi. Is that true ƴar fillon shi ke kiran shi da sunan da ko Abba Hakimi baya faɗa sbd girmama ilimin Ubangiji? Amma ƴar cikin shi ta faɗa gatsal! Hankali kwance. Ta ƙara cewa "Kaje ka auri karuwar uban riƙon naka, ka ɗora daga inda ya tsaya" Da ace Yaa Sheikh na cikin tsarin maza masu dokan matayensu, da babu shakka sai ya lakaɗawa Halisa mugun doka wanda zai dawo da ita daga haukan daya sameta, ya juya yana sauke numfashi har zuciyar shi ta samu nutsuwa daga zafin da tayi dalilin ambaton sunan Allah. Murya can ƙasa irin ta marasa lafiya ɗin nan ya ce "Zan baki, ki tuna mini zuwa safiya" yai shiru ya nisa ya ce. "Ba Zahrah ba, ko mother idan na yi niyya zan aura, tunda ban sha nononta ba, idan ina son mace da zuciya ɗaya to ko wacce ta shahara a karuwanci zan iya aura, da zarar ta tuba ni kuma zan Jahadi, Ina son Zahrah da gaske" Yana faɗin haka ya juya zuwa wajan freezer ya ɗauki Apple da gorar ruwa mai sanyin gaske ya koma bedroom ɗin da yake ciki. Yana barin wajan Halisa ta zube ta dinga kuka kamar ranta zai fita, ashe da gaske son Zahrah yake? Yanzu duk daɗin da Yaa Sheikh ke jiyar da ita Zahrah ce zata samu, su kwana tare?gado ɗaya wata kilama a manne a jikin Abban nata? Ta dinga kokawa da numfashinta tana riƙe ƙirjinta, ita kawai jin abin take kamar mafarki, amma hakan bai dameta ba, indai zai saketa taje ta gana da ƴan uwanta domin tayi al'ƙawarin idan har igiyar auren shi na kanta to babu inda zata, sai manne cinyoyi take kamar wacce hauka ya kama wani mugun son kasance da ɗa namiji ya shige ta ido rufe ta saki kuka ta ce "Mugu" Yaa Sheikh ya ɗaga gorar ruwan duk sanyinsa haka ya zubawa cikinsa bai iya shan Apple ɗin ba ya ajjiye gefe guda, kusan abu ɗaya ke damunsu ya shiga sakarwa kansa shower mai sanyi daga ƙarshe ya fara lafilfilo yana kaiwa Ubangiji kukan shi akan ya sausauta zafin zuciyar Matar Malam ɗin. Ummul ta buɗe ƙofar bedroom ɗin ta shigo bakinta ɗauke da sallama tsaye ta kanshi, yana gyara zaman diamond rolex watch, tai tsaye tana kallon kyakkyawan dattijo ko magidanci da Allah ya bata matsayin ɗa ɗaya tilo, babban mutum masanin addinin Musulunci tsantsa babban likita wanda ya san aikin shi, bai haƙuri da riƙo da ƙaddara a duk sanda ta zo masa, mai tausayi da imani da jinƙan na ƙasa da shi. "Arɗona" ya juya ya kalleta ya nisa ya ce "Sabahul khair Ummul" Ta ce "Yawwa, wani abu ya haɗaka da Daughter?" Kasancewar baya ƙarya kai tsaye ya ce "Rikici ne, akan sakin ne" ta numfasa cike da tausayin Yaa Sheikh ta ce "Anya ba zakai mata abin da take so ba?" Ya dubeta a raunace ya ce "Ummul na saki Zawja?" Ta ce "Na san zafin da zuciyarka ke ciki, Halisa yarinya ce amma ina mmki taurin kai da zafin zuciyarta,bana son na fara jin zafinta wata macan sai an mata sakin take shiga hankalinta, idan sakin ne mafita ya kamata kayi ko ɗaya ne" Ya taka har zuwa wajan Ummul ya riƙe hannunta a taushashe ya ce "Kiyi addu'a, komai zai daidai" "To Allah ya kawo sauƙi cikin lamarin ya kuma daidaita tsakaninku" ya jinjina kai ta ce "Tafiyar ce? Kaje wajan Abba Hakimin?" Ya ce "Zuwa 11:30 zamu ta shi, yanzu zani" ya faɗa yana jin cewa zai kewar ganin koda masifar da take masa, amma ko zai sha wahala itama dole ta sha domin ya fahimci fitinar da cikin Jikinta ya sata. "Allah ya tsare ya kare, ya ƙara maka haƙuri haka lamarin aure yake wani daɗi wani sai an wahala, wanda aka wahala ɗin sai kaga yafi Kwari da inganci" Shi dai kallonta yake harta gama ya juya ya nufi waje sai da ya yi nisa ta ce "Na manta tun safe Maimoon da Daughter suka shige" nan ma ya jinjina mata kai, ya nufi part ɗin Dattijo da Hajia suka gaisa, Alkyabbar jikinsa na ɗaukan idanu yana basa ƙamshi mai daɗin shaƙa yana mai gyara zaman hiraminsa ya ƙarasa harabar gidan ya samu Umar-khan dake tsaye yana jiran shi yana zuwa ya buɗe masa ƙofa yana faɗin "Barka da safiya Yaa Lee" ya rufe idanu ya buɗe alamar ya amsa domin maganar wahala take masa, kai tsaye gidan Abba suka nufa, babu wanda ya yi magana har suka ƙarasa Ishaq-Hakim ya buɗewa Yaa Sheikh Umar-khan ya fito suka nufi ciki A parlour suka samu mother ta saka Halisa a gaba ta inda ta shiga bata nan take fita ba, gabaɗaya haushin Halisa ya kamata bata san haka take da taurin kai ba sai yanzu. Dr A'isha ta ce "Barrister ni banga abin faɗa ba, ba a ga abin da yake mata ba sai ita za a ga laifinta, kuma ita ce mace ita zata zauna da shi tunda bata so ba sai a rabu da ita ta fito da wanda take so ta aura" Mother ta ce "Kenan ke ce ki ke mata huɗuba?" Tai saurin cewa "A'a,nikam ina ruwana meye nawa miji kowa da nashi, bayan itama da wayonta tunda har ciki ne a Jikinta ai ta shige ai mata huɗuba" Daga bakin ƙofa aka ce "A'isha ta shi kibar gidan nan" ta ɗago da sauri suka haɗa idanu da Yaa Sheikh, hantar cikinta ta kaɗa ta tsare shi da kallo kwarjinin shi da cikar kamalar shi da haiba suka cika mata idanu ta ce "Me ka ce?" Ya shigo ciki har inda take zaune da hannu ya nuna mata ƙofa ya ce "Ki bar gurin nan tun kafin na nuna ɗaya ɓangarena, babu ke ba matata" ta ce "Yaa Sheikh ni ka ke cewa haka kamar wata sa'arka? Ni ka ke rabawa da matarka?" Abba Hakimi ya ce "Ta shi ki ke, tunda Yaa Sheikh ya yi magana akwai abin da ki ke" tai ƙwafa tana ficewa daga parlourn. Yaa Sheikh ya nemi waje ya zauna fuska ɗaure idanunsa a ƙasa ba tare daya ƙara kallon kowa ba "Ya akai Aliyu?" Sai a lokacin ya sauka numfashi ya ce "Tafiya zan yi" Abba Hakimi ya ce "Tafiya da gaggawa haka? Har tsayin yaushe?" Ya miƙe yana cewa "kawai sai Allah ya dawo dani, bari na je kada na rasa jirgi" Mother ta ce "Allah ya tsare ya ki ya ye angon Zahrah, muna nan mun fara shirye-shirye yanzu Ummul take sanar mini ai yanzu zakai aure, daman wata rabuwar alheri ce ka samu kyakkyawar mata" Umma A'isha tai murmushi tasan da biyu! Wai anjefi uwar miji da rani, an jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya. Yaa Sheikh ya juya yana cewa "Wajanta zan fara zuwa" Ya fice abin sha da sauri Halisa ta miƙe Mother na kiranta tai banza da ita, tana zuwa ta tsaya Idanunta kaca-kaca da hawaye ta ce "Ka ce na tuna maka, ka sake ni, ko sati ba zan ƙara ba zan samu mijin aure dalilin cikin nan kawai zan jira na haihu" Yaa Sheikh bai damu da Umar-khan da Ishaq-Hakim dake tsaye ba ya riƙo hannunta tare da dawo da ita gaba. Ya tsareta da narkakkun idanunsa ta ɗauke kai a hankali ya jawota jikinsa tare da shigar da ita cikin Alkyabbar shi zata ƙwace ya riƙeta da kyau! Ya ce "Bake na rungome ba, jina na, ƙwan dana zuba miki har ki ka ɗauka da shi zan sallama" ta ɗago zata kalle shi gemun shi yaƙi bata damar haka ta ce "Ɗana dai, daga yau ka daina tunanin kai ne uban shi" shi dry ma ta bashi ya shafa cikinta ya ce "Shi ya sa naga ke ki kai cikin, nutsu muyi magana" tai banza ko wanne second guda sai zuciyarta ta buga na fargabar da gaske wai wajan Zahrah za shi? Ya ce "Haliyserh da gaske baki so na?" Ta ce "Wallahi bana son ka, na tsaneka, ka rabu dani" ya jinjina kai ya ce "Zan miki abin da ki ke so, zan kuma tafi tafiyar da zaki mamaki wacce ba lallai na dawo da rai ba, ki faɗawa abin da zaki haifa ba Mahaifinsa yaƙi babarsa ba, ita mahaifiyar ita taƙi uban, wannan zai zama rungoma ta ƙarshe, ki jiƙa jikin ki, ki sha Haliyserh Ahmad Nuran Sarki, zan je nai sabuwar rayuwa da Zahrah ina fatan alheri" ya jim yana ɗan matseta a ƙirjin shi kafin ya sumbaci goshinta yana zareta daga jikinsa, ya zaro farar Envelope daga jikinsa ya damƙa mata ya ce "Your Divorce paper" yana bata ya shiga mota Umar-khan yaja motar da gudu zuwa airport... Tsammaci abin da baka tsammani, aiki da hankali yafi aiki da kwakwalwa😊Ta dinga juya Envelope ɗin a hannunta Idanunta akan gate tana kallon yadda motar Yaa Sheikh ke ficewa, ji tayi kamar yana tafiya da zuciyarta da ruhinta Jikinta ya yi sanyi wani abu mai kama da faɗuwar gaba ya risketa. Ita ce ta ɓukaci sakin amma sai taji wani baƙin ciki na sakin, kamar yadda ki wacce ƴar mace taje jin baƙin ciki idan an saketa, shikenan ta zama bazawara Yaa Sheikh zai je ya yi rayuwa da Zahrah "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Na shiga uku, wayyo Allah" Ta faɗa tana dafe kanta tare da yin baya zata faɗi Mother tayi saurin tare ta ta ce "Ke lafiyarki ɗaya ki ke shirin suma?" Halisa ta riƙe Mother ta ce "Wallahi ya sake ni, ya sakeni na shiga uku" ta fasa wani ihu tana riƙe Mother. Ita kanta Mother sai da ƙirjinta ya buga tsoro ya kamata, Wanne irin hukunci Yaa Sheikh ya yankewa zuƙatansu? Ta tabbata ya haƙura da Halisa kenan? Ta ce "Saki kuma? innalillahi....," Tama ƙarasa faɗar abin da tayi niyya ganin Halisa kamar zata data iska sbd yadda yake kuka, ya sanya ta jata zuwa cikin parlourn Abba Hakimi yana shirin barin wajan sai ya tsaya ya ce "Lafiya dai?" "Ina fa lafiya, abin da take hauka neman ta samu" Abba Hakimi yai shiru yana nazarin maganar. "Kamarya Maryam?" Mother ta nuna mata Envelope ta ce "He divorced her, Now she is a widow" "Lallai ran Malam ya ɓaci, tunda har ya iya rubuta saki, banso haka ta kasance ba da yabi komai a hankali" Abba Hakimi ya koma ya zauna ya ce "Muga" Mother ta miƙa masa Envelope ɗin, ya amsa yana gama warewa ya ci karo da rubutu kamar haka. _“Ta ya ya ki ke tunanin ni Malam Aliyu Haydar Aliyu zan iya sakin matata Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki? How can i spend my time ba tare da ƴar fillona ba? Taya zan jure ganin rigmar da take mini tana wa wani? Zan ci gaba da rainon ƴata, matata, gimbiyar masarautar Sokoto, Yaci gaba da son Matar Malam na tsayin rayuwa zuwa mutuwa, na barki zuwa lokacin da zaki nemeni da kan ki, ki ɗauka aurar Zahrah mu duka ƙaddararmu ne kece sanadi kuma, One thing shi ne IDAN BA KE ba Yaa Sheikh na ki, Abbanki, Modibbonki na yarje kiyi makaranta ki je garinku idan hakan zai faranta ranki.. Fatan alheri”_ Abba Hakimi ya yi murmushi a ɓoye bayan ya kammala karatun, zuciyar Mother cike da zullumi ta ce "Saki nawa ya yi mata Abba?" "Sakin tsayin rayuwa!" Cewar Abba Hakimi. Ya bawa Mother takardar ta fara karantawa, ta jinjina kai tana sakin ajjiyar zuciya. Umma A'isha ta karanta itama, Dr A'isha data shigo yanzu ta miƙa hannu zata amsa Abba Hakimi ya ce "Aishatul-humaira bani nan" Umma A'isha ta miƙa masa. "Abba mu gani,naga duk kun duba ko?" "Eh, amma ba dole kowa ya gani ba" tai shiru ba don ranta ya so ba. Halisa ta kalli Abba Hakimi ta ce "Da gaske Abbana ya sakeni Jon wuro?" Ta faɗa da ƙyar. "Na ɗauka haka ki ke so?" Ta ɗaga masa kai zuciyarta na zafi da soya. Ya ce "To meye na damuwar?" Ta fashe da kuka mai cin rai sai da tayi mai Isarta babu wanda ya tankata ta ce "Kuma sai ta sakeni da ciki, daman da gaske baya so na? Zai je ya auri karuwa" mother tai murmushi a ɓoye kafin ta ce "me zai sa ya zauna inda aka tsane shi? gashi can wata zata mutu akan son shi, aini naji daɗin haka kina haihuwa sai ki fito da miji musha biki" ta ƙara fashewa da kuka tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinta ta faɗa gado ta mance da cikin Jikinta birgima kawai take akan bed ɗin tana ihu tana tsinewa Zahrah albarka. daga ƙarshe ta fara cilli da komai na bedroom ɗin ta rasa wa zata faɗawa damuwarta waye zai bata shawara mai kyau, Dr A'isha ce mai sonta kawai, kuma ya rabata da ita ta zauna tana ta kuka. Ƙarar wayarta ya tsayar da ita daga kukan da take ganin sunan Dada ya sanya taji zuciyarta ta karaya ta ɗaga wayar murya a dashe ta ce "Hello!" Dada ta ce "Kin kyauta Danejo, Allah ya yi miki Albarka, ko da wasa naga ƙafarki gidan sarauta sai ranki ya ɓaci, idan har sbd haka ki ka aikata abin da ki kai" Cikin kuka ta ce "Hande en boni na lalashe me na yi kuma?" Dada ta ce "Ba ke ba, hatta ni Besty nada iko dani balle ƴar dana haifa, ke ko nauyin furfurar shi ba kiji ba? Shekarunsa? Darajar ilimin addinin shi,ki zubawa idanunki toka sbd baki data ido ki ce wai ya sake ki? Kin san hukuncin macan dake neman saki wajan mijinta? Kin san azaba da tanadin da Allah ya yi musu? Wallahi ba ruwana wannan ba tarbiyyar dana baki ba, akwai wacce ke son lalata mini ke, ko kuma wata ɗabi'a ki ka sauya wacce ban sani ba, ki tuba ki bi Allah" Tunda ta fara magana Halisa ke kuka ta ce "Ya zan yi Dada? Ban taɓa ganin mahaifata ba, ban zauna tare da mahaifina ba ko sau ɗaya ba, ban san ƴan-uwana ba, shi ya fara ɗorani a hanya har naji zan iya masa komai ya gaji ya kai ni" ta saki kuka ta ce "kuma fa baya so na, wai Zahrah zai aura ina laifin ya nemi auren wacce ban sani ba ya san na tsaneta ba, kuma ya yi mini al'ƙawarin ba zai auri kowa ba.....," Dada ta katse ta da faɗin "Tunda shi bashi da hankali kamar ki ko? Besty ni ya yiwa biyayya, ni na shaida masa bana buƙatar zuwanki masarauta, sbd ban manta wahalar dana sha ba, na ce sai naga yadda zamana ya kasance da sauyawar al'amarin zan bashi damar ya kawo ki, umarni na ya bi, ni zaki tsana Danejo ba Abban naki ba, batun Zahrah kuma ke ki ka bawa mijinki lasisin damar kula wata har ya aureta, ni na ji daɗin haka gobe wata mai irin halinki ta kuma, Zahrah kuma daman son shi yake yana aurenta ki kaɗe har ganye sai a fara lissafa miki aure tun yanzu" "Dada don Allah zan zo wajan Mai martaba wallahi zuciyata babu daɗi" Dada dake kan layi ta ce "Kin san Allah babu inda zaki zo, ko kinzo sai na saka Khalil ya dawo dake ko El-bashir" Ta haɗe rai ta ce "Ni ki daina haɗani da wani El-bashir" ran Dada ya sosu da halin Halisa ta ce "Ɗan uwan naki ki ka tsana? Akan wanne dalili" tai shiru domin da kunya ta ce akan Yaa Sheikh ta tsani El-bashir "Zan zo kai lefen Besty ne zaki bayani" kafin tai magana ta kashe kiran "Lefe?" Ta furta a fili kenan aure ya tabbata Yaa Sheikh ya kasa jure fushin zai auri Zahrah mai yasa zai hukunta ta da hakan? Ta ce "Na tsaneka, bana son ka" A can parlour bayan tafiyar Dr A'isha Abba Hakimi ya ce "Koda wasa kada wani ya kuskura ya shaida mata ba saki bane, zuwa lokacin da za ta gaji da kanta" "Ya batun auren Zahrah gasky ne?" Ya ce "Ba wanda zai iya tsayar da Malam, zuciyar shi ba irinta kowa bace, baya son Zahrah amma ba zai iya bari ranta ya salwanta ba, kuma ta rantse idan bai aureta ba zata iya kashe kanta, ya ɗauki kasadar zai yi Jahadi kuma zai riƙe Muhammad ya dawo wajan shi, ya yi masa riƙo da zuciya ɗaya saɓanin yadda Engineer Aliyu ya riƙe shi, zai ramawa kura anniyyarta" "Amma ban ji daɗi ba, bai dace Yaa Sheikh ya auri wacce Engineer ya sani ba" Murmushi kawai Abba Hakimi ya yi ya ce "Me ya sa zaki haramta masa abin da Allah ya a halarta masa? Mata tunaninku da ban yake" ya miƙe tare da ficewa. Zahrah na kwance hannunta ɗaya manne da drip ɗayan kuma jini ke shiga a hankali, ta rame tai baƙi ta fita daga cikin hayyacinta bakinta ya bushe ba kowa ake bari ya shiga inda take ba, Kallo ɗaya zakai mata ka zubar mata da hawayen tausayi, ko nono Muhammad baya samun shi kullum cikin shan madara yake. Dr ya gama duba ta ya juya yana fitowa Mimi ta ce "Dr ya ake ciki?" Ya sauke numfashi ya ce "Kuyi mata addu'a, zuwa lokacin da Allah ya nufa zata tashi idan mai tsayin rai ce" Ta juya ta kalli Alhaji Farouk cikin kuka ta ce "Alhaji kwanakin ka biyu da zuwa Kano, amma babu Yaa Sheikh ba alamar shi, don Allah kayi wani abu kada Zahrah ta mutu akan Soyayya wacce irin Masifaffiyar soyayya ce wannan? Wlh ko a film da labarai na littafai ban taɓa ji ba, Allah ka dubi idanuna kada ka hukunta mini Zahrah da soyayya" "Allah zai shiga lamarin In sha Allah" Mimi na ƙoƙarin magana suka ji ƙamshin turaren Roja ya mamaye wlrd ɗin da suke zaune. Ta ɗago da sauri Idanunta ya sauka akan Yaa Sheikh da Umar-khan sai wani kyakkyawan Bafullatani da kuma Surry. Wai, dole Zahrah ta so Yaa Sheikh mutum bai nagarta da tsantsan addini da nutsuwa da kamewa har haka Sai bazan ƙamshi yake idanunsa cikin white Sunglass wanda ya ɓoye faɗawar na shi Idanun, Farar shadda ce a jikinsa sai ɗaukan idanu take babu Alkyabba dai hirami kafaɗa da kan shi, alamun har ya yi wanka ya sauya kaya a hotel ɗin daya sauka. Mimi da Alhaji Farouk suka miƙe, Alhaji Farouk ya miƙawa Yaa Sheikh sukai subawa a hankali cikin nutsuwa ya ce "Ya mai jiki?" "Jiki sai addu'a Yaa Sheikh" Ya jinjina kai yana duba lokaci kafin ya ce "Allah ya bada lafiya" Umar-khan ya ce "Za mu iya ganinta?" Da sauri Alhaji Farouk ya ce "Eh, In sha Allah muje muje" gabaɗaya ya ruɗe sbd nutsuwar Yaa Sheikh da kwarjinin da ya yi masa a idanu. Jagora sukaiwa Yaa Sheikh har zuwa ƙofar shi kaɗai Dr ya bawa damar shiga. Tana kwace amma sai da zuciyarta tai kyakkyawan bugawa sbd ƙamshin turaren shi wanda ba zata taɓa mancewa da shi ba, ta rufe idanu hawaye na silalowa daga gefen idanunta, sai yaushe zata daina mafarkin shi? Komai na shi gizau yake mata ta kasa jurewa ta amsar ƙaddara. Yana tsaye kanta yana mmkin yadda ta faɗa ƙwarai duk ta lalace, a kallo ɗayan da ya yi mata ya fahimci da gaske zuciyarta tai mugun kamowa da ciwo wanda ba a son irin shi "Ya jiki?" Maganar da tai silar faɗuwar Zahrah daga kan gadon ya yi saurin saka hannu ya taro ta, ta juya sukai idanu biyu wata ajjiyar zuciya mai ƙarfi ta sauke hawaye wani na korar wani, tayi saurin cire drip da jinin da ake ƙara mata, tare da fisge na'urar Oxygen ɗin dake aiki a Jikinta, babu ƙwari a Jikinta amma haka ta miƙe tana zuwa ta faɗa jikinsa ta rungume shi tana sakin wani irin kuka wanda yake nuni da ka tausaya mini ka taimaki rayuwata. Sanin cewa zuciyarta a yanzu matacciya ce, abu kaɗan za ai mata ta lalace yasa ya ɗan daidaita ya shafa kanta kaɗan ba tare da ya ce Komai ba, muryarta a hankali ta ce "Ka taimaki rayuwata ka aureni Malam, ka tausaya mini zuciyata babu daɗi kamar zan mutu" wani irin kuka take gwanin tausayi ya janyeta daga jikinsa tare da zaunar da ita saman gadon ta ce "Saboda Allah, da soyayyar da ka kewa Annabi Muhammad s.a.w" ya kalleta da kyau yana nazartar yanayin kafin ya ce. "Na amince, zan aureki" Ta saki murmushi while hawaye na zuba ta ce "Na gode Allah ya saka da alheri Ubangiji ya ƙara girma" Ya jinjina kai sukai shiru ta kalle shi ta ce "Nasan takura maka akai, ko tausaya mini kayi ba dan kana so na ba ko?" Ya nuna mata pillow ya ce "Huta, barci" ta ce "Nayi barci har na gaji, yanzu bani da wani damuwa daman kai ne damuwata" sai yaji tausayinta, sai yanzu ne yake gane cewa duk wanda yake hauka akan SO! To kawai a rabu da shi, so babban abu ne da kan iya tarwatsa zuciyar mutum murus ya lalata masa rayuwa ya ɗauke masa farin ciki yanzu ya shaida haka. "Matarka? zata amince dani, na maka al'ƙawarin ba zan taɓa janta da faɗa ba ko tayi zan haƙura domin tayi mini komai datai mini halarci har ta amince ka aureni, wlh idan ni ce ita ba zan iya barinka ba, balle ka auri wata ina maka son da Ubangiji kaɗai ya sani kuma shi ne zai zama shaida, kana da kima kwarjini tarin da haiba wacce ba kowa zai iya Fuskantarka da wani shirme, nasan zaka zauna sani bisa takura kayi haƙuri,kai mini adalci ba laifina bane" Ya girgiza mata kai a taushashe cike da kulawa ya ce "Ba takura, ki nutsu zamu zauna gida ɗaya tare" tai murmushi tana ɗan riƙe ƙirjinta. Ya taimaka mata ta kwanta ta ce "Kada ka tafi don Allah" Ya jinjina kai yana tsaye kanta tana kallon shi tare riƙe hannunsa har barci ya ɗauke ta. Fita ya yi, zuwa office ɗin Dr. Dr ya ce "Ko iyayenta basu san tana ɗauke da Cancer ba, wanda kuma munyi scanning yaci ƙarfinta abu ne mai wahala ta tsallake wata biyar a raye a duniya" Yaa Sheikh ya ce "Subuhanallah!" Dr ya ce "Yana da kyau ta ƙare watanni biyar ɗin nan da farin ciki, kada ita kanta tasan cewa akwai Cancer Jikinta hakan zai ƙara taimakawa wajan murmurewar Jikinta" "Ba wani aiki?" Dr ya ce "For now babu, domin taje ƙarshe sai dai fatan samun sauƙi wajan Ubangiji" ya miƙe yana godiya. Daga nan sukai sallama Yaa Sheikh ya nufi Rugar Bello a hanya ya kira Abba Hakimi sukai magana mai ɗan tsayi kana ya kira Ummul daga nan ya ajjiye wayar. Halisa na zaune tana azkar Idanunta ya kumbura sbd kwana tayi tana kuka sai dab da Subhi barci ya ɗauke ta, kasancewar ta saba ta shi yin Sallah ya sa bata makara ba Ta miƙe da ƙyar tana dafe kanta Idanunta na lumshewa sbd barci ga wani irin matsanancin feelings dake damunta ta rasa yadda zatai da rayuwarta, harta mata tsayin lokacin data ɗauka ba tare da Yaa Sheikh ba, she miss his torch, his kiss, his body his everything daya shafe shi amma zafin ranta ya kasa bari ta yarda tai kewar, tana ƙoƙarin kwanciya mother ta buɗe ƙofa ta shigo lokacin wasu masallatan nata sallah ta ce "Barka da safiya Mother" bata amsa ba ta ce "Kije, ki haɗa mana breakfast, ga wanke-wanken ma da mopping" a raunace ta ce "Ina maid ɗin? Bana jin daɗi" ta ce "Allah ya sauwaƙa mai aiki kuma mun sallameta ke zaki koma yin komai" Kamar zatai kuka ta ce "Bari gari ya yi haske to" "Yanzu na ce, kafin Abba Hakimi su tafi kai kuɗin Auren Zahrah" kamar an caka mata wuƙa a zuciya haka taji hawaye ya sakko mata, mother tai waje. Ita kaɗai ta dinga kuka babu mai rarrashi wayarta ta ɗauka da niyyar yiwa Maimoon ko Dr A'isha magana a online sai taga anyi mata magana da prvt number, kamar ba zata shiga ba sai kuma ta buɗe abin data gani ya yi mugun tayar mata da hankali ta dafe cikinta da sauri wanda ya murɗa fitsari ya taho mata, tai downloading picture ɗin Yaa Sheikh ta gani rungome da Zahrah a ɗakin asibiti a ƙasa kuma aka ce. "Mun gode sosai Halisa da shirmanki ya bawa ƙawata damar samun cikar burinta, yanzu Yaa Sheikh na Zahrah ne har abada ki fara kokawar neman mijinki domin yanzu wutsiyyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa, ke da Yaa Sheikh har abada.....," Bata ƙarasa karantawa ba ta nemi ganinta ta rasa ta kuma kasa fahimtar komai ta fasa wata ƙara tana faɗin.."Wallahi ƙarya ki ke, baki isa ki auri abin da na fiso a duniya ba, dole ki rasa kamar yadda ki ka rasa" gabaɗaya Jikinta rawa yake har ya gaza ɗaukan ƙafafuwanta ta sulale ƙasa tare da yin zaman ƴan bori. Wani irin kuka take mai tarwatsa zuciya da sanya mutum cikin damuwa, duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata, hannunta na rawa ta ɗauki wayarta tare da kiran Dr A'isha. Ringing ɗin farko aka ɗauki wayar tare da faɗin. "Hello!" Halisa ta ce "Adda A'isha na shiga uku, ba zan iya ba" Dr A'isha tai murmushi tana kallon ɗaya wayar hannunta kafin ta fita daga inda take ciki, ta nemi bakin gado ta zauna ta ce "Shiga uku dame Halisa?" Cikin shassheƙar kuka murya bata fita sosai ta ce "Da gaske Abbana aure zai yi wallahi, kuma Zahrah zai aura ba zan iya jurewa ba, ina jin kamar zuciyata zatai bindiga" Dr A'isha ta kaɗa ƙafa ta ce "Meye abin damuwa? You need a divorce paper, and you got it, I think you will be happy". Halisa ta dafe ƙirji ta ce "I love my husband, ina son mijina kin san ban tsane shi ba, ba kuma zan iya barin wata ta aure shi ba, yanzu ya zan?" Dr A'isha ta runtse idanunta tana jin kamar wuta Halisa ta watsa mata a ƙirji da ta ce _She loves her husband_ ta kasa cewa Halisa komai ta shiga dannar zuciyarta sbd zafin da tayi.. "Na zama shasha, na rasa meke damuna" Dr A'isha ta ce "It's over, kin yi sake when all is gone, yanzu sai da kibi hanyar da zaki hana Yaa Sheikh ya auri Zahrah, idan ba haka ba kina kallo zai haɗa shimfiɗa da ita" Ta sauke numfashi ta ce "Kin san saki uku ya yi miki, ke da Yaa Sheikh har abada domin rama abin da ya yi miki, shi ne hana shi auren Zahrah" Halisa ta goge idanunta ta ce "Bana jin Abbana zai mini saki har uku, kuma anƙi faɗa mini saki nawa ya yi mini" "Kira ki tambaye shi mana?" Ta girgiza kamar Dr A'isha na gabanta. Jin tayi shiru ya sa Dr A'isha ta ce "Ko ki je inda yake" sai a lokacin ta ce "Ya yi tafiya" "Zuwa ina? Yaushe zai dawo?" Cewar Dr A'isha. A raunace wasu hawayen na biyu mata zuwa saman kuncinta ta ce "Ban sani ba, bani da labarin yaushe zai dawo" Dr A'isha tayi murmushi Idanunta akan mijinta wanda ya shigo daga masallaci kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kai. A hankali ta ce "Ask Abba Hakimi, you'll get the information Catch you later" tai hanging up na kiran. Idanunta kan waya Abubakar ya ce "Sweetheart waya da Subhi yau babu ko azkar?" Ta yi masa kai ka ɗauka bada ita yake ba. Ya ƙara cewa "Dr na" "Abubakar" ya buɗe baki da hanci yana kallonta ɗauke da mamakin yadda ta kira sunan na shi babu ko risinawa ta ce "Dr kin san me ki ke cewa?" Ta ɗago idanunta fes akan shi ta ce. "Nasan kana da labarin ban taɓa yin hauka ba ko?" Ya jinjina mata kai ya ce "Elxty, The way you called my name surprised me" "To, Allahamdulillah tunda sunanka ne Abubakar ɗin" ya ce "Meke damunki ne Dr?" Idanunta ya sauya kala ta ce "Kai ne damuwata Abubakar, domin ka hana ni abin da nake buƙata tsayin shekaru bayan a koda yaushe ina iya mutuwa,ko kafi so na mutum ban bar masu yi mini addu'a ba? Burinka kenan nasan cewa kai ne baka haihuwa fa" Da damuwa ya ce "Ina tauhidinki ya tafi A'isha? Ni zan baki haihuwa?" Ta ce "In a capital letters YES! ka duba Halisa matar malam, shekaru nawa na mata? Gabaɗaya yaushe sukai aure amma yanzu cike ne da ita haihuwa take shirin yi, ni kuma ina zaune a tutar babu" Ya kai hannu zai riƙe ta domin wallahi gani yake kamar wacce Aljanu suka shafa ko wacce kwakwalwarta ta taɓo "Ras nake Abubakar, ina son faɗa maka cewa na gaji ne kawai I'm tired" "Tired of what, Dr?" A fusace cike da kallon wulaƙanci ta ce "Your married, na gaji, na gaji, na gaji wallahi ka sake ni, naje na auri wanda zuciyata ta rayu da son shi, daman aurenka is my destiny i know tun ba yau ba" Ya dafe kai ya ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, ni ki ke faɗawa haka Dr? Kin san abin da kalamanki zasu iya jefani? Kin san tasirunsu cikin zuciyata, kin san son da nake miki, Kada kiyi amfani da jarabtar da muka tsinci kanmu ki cutar da rayuwata, haihuwa da rashinta daga Allah suke, ta yiwu yaran ba alheri bane a garemu shi ya sa Ubangiji bai azurtamu da su ba, shi da kan shi yana cewa yana jin tsananin kunyar wanda bai azurta su da haihuwa ba, ki riƙe ƙaddara ki kuma yarda da ita shi ne cikar imaninki" "Shut up your mouth Abubakar Tijjani Asase, ka haifeni ne? ko malami ka zama da zaka zauna kana faɗa mini Allah ya ce Annabi ya ce, tunaninki ni daƙiƙiyya ce ko? Lemme repeat myself I'm tired I need my divorce paper immediately!" "Wallahi Allah, ba zan sake ki ba, sbd ina son ki IDAN BA KE ki ɗauka rayuwata ta zo ƙarshe ne, ki sani matata ce ke igiyar aurena ke yawo akan ki, da alama baki son rabauta da aljanna ki koma wajan ɗan uwanki Yaa Sheikh ya yi miki darasin dake cikin aure A'isha" Yana kawowa nan ya fice daga cikin bedroom ɗin zuciyar shi babu daɗi. Halisa tunda suka gama waya da Dr A'isha take zube a ƙasa tana auna maganganunta, Hawayen fuskarta yaƙi tsayawa. Ta miƙe da ƙyar jiki a sanyaye ta nufi Main parlour sanye da hijabi Kitchen ta nufa aikin data tarar dai da gabanta ya faɗi, ta ta shi akan wahala aiki koma ba sabon abu bane wajanta, tun a rugar Rome. Zata kunce nagge duk yawansu ta tafi kiwo, ta tatsi nono ta tafi talla ta dawo tayi aikin gidan, amma ƴan watannin da tayi tare da Abbanta Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu Ya sangarta ta, ya bata farin ciki, ya bata tarbiyya, ya kula da ita bata aikin fari dana baƙi sai ɗaukan darasin zazzafar soyayyar shi da karatun da yake mata, ita kanta bata san ya take jin kanta ba, ta manta ita ce Halisa Danejo Rome. Ta dawo amsa sunan Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu, yanzu kuma data dawo Princess shi ne za a haɗata da aiki har haka wanda ta mance yadda ake yin shi. Lallai aure rahama ne, cikar ƙimar mace gidan mijinta. "Mena aikatawa kai na ni Danejo?" Ta yi ta surutu ita ɗaya taci kuka ta ƙoshi she just missed, amma me? Shi ne abin da bata sani ba, tana buƙatar Mentoring kanta a cushe yake. A hankali ta fara wanke-wanken ta gama tas, kana ta gyara kitchen ɗin. Kasancewar an gyara wanke ta saka a inji malkaɗe ta malkaɗa. Gefe guda ta kunna gas ta ɗora ruwan kunnun shinkafa. Ruwa ta zuba cikin pot ɗin ta kawo kwakwa wacce ta goga ta zuba cikin ruwan, kafin ruwan ya rafasa ta koma wajan kullin ƙosan ta haɗa shi. Ta ɗora kasko ta zuba mai daidai yadda zai sha kan ƙosan, ta zuba albasa cikin man ta barshi ya yi zafi sosai. Daidai lokacin ruwan data zuba ya tafaso tare da kwakwa, ta kawo haɗin kullin shinkafar tare da muciya a nutse take zubawa tana damawa har ya yi kauri yadda take so. Ganin bata gama ba ya sanya ta rage gudun gas ɗin man data ɗora, tana gama haɗa kunnun shinkafar ta juye a wani babban flas. Ta goge wajan daya ɓaci ta ajjiye flas ɗin gefe. Ta dawo kan man data ɗora, ta haɗa ƙosan wanda ya sha kayan ƙamshi da ƙwai da tafarnuwa. Is taking long kafin ta gama soya ƙosan, ta ɗauki paper ta saka ƙasan flas sbd gudun gumi ya lalata shi,ta juye tas ta ƙara ɗaukan wata paper ɗin ta rufe saman shi. Ta ajjiye gefe guda. Ta ta fasa tea da ginger da tafarnuwa da sauran kyan ƙamshi da barkono kaɗan. Shi ma ta juye cikin mug ta goge wajan tas, tana gamawa ta koma Main parlour ta share tai mopping ta kunna boner ta saka turare mai ƙamshi sosai ta fesa air-con. Nan da nan parlourn ya ɗauki ƙamshi, a lokacin gabaɗaya Jikinta ciwo yake da ƙyar take buɗe ido ga damuwar zuciya, ga feelings ɗin dake damunta har tsoro abin ke bata, nan da nan za ta jita a jiƙe. Ta shirya breakfast ɗin lokacin goma saura minti biyar cif. Mother ta fito cikin wata green ɗin atamfa ciganvi ɗinkin doguwar riga. Tausayin Halisa ya kamata amma ta share ta ce "Sai yanzu ki ka gama?" Kallon mother kawai tayi ta kasa cewa komai, ta ɗaga ƙafa da ƙyar ta nufi bedroom ɗinta. ko hijabin Jikinta bata cire ba ta kwanta kan gado tare da jan pillow ta rungome, ta rufe idanu sai suffar Yaa Sheikh ta dinga zama kamar magic a Idanunta, ta tuna rungumar da ya yi mata ta ƙarshe sai ta matse ƙafa da ƙyar barci ya ɗauke ta. Wajan azahar barcinta ya yi nisa taji kamar ana motsi a ɗakinta, ta kasa buɗe ido sama-sama kuma wani ƙamshi ke ratsa hancinta yana sauka har ƙasan zuciyarta, ƙamshin da ba zata taɓa manta irin shi ba, idan tai kamar zata farka sai a hura mata iska taji an rungometa tsam a ƙirji, ɗumi na rasata. Ta saki jiki cikin magagin barci ta ce "Abbana" aka shafa kanta ana manna mata baki a wuyanta tare da sakar mata wasu lafiyayyun kisses cikin wata murya mai rauni da shauƙi aka ce "Madadin Abbanki ne" baki ya kai da niyyar kissing nata ta buɗe ido da sauri tana cewa "Modibbo!" Ɓat! Kamar gilmawar walƙiyya ya ɓaci daga cikin bedroom ɗin sai ƙamshin turaren Roja daya bari, cike da zullumi ta miƙe tana kunna hasken ɗakin, abin mamakin bai huce yadda ta ganta naked babu kaya ta juya zuwa kan bed taga kayanta ya she zube a ƙasa. Ta shiga tattaɓa Jikinta da sauri ta ɗauki hijabi ta saka har ƙasa ta saka wani skert tai waje da gudu tana sakin ajjiyar zuciya,sam bata lura da tarin mutanan da suke parlourn ba, kai tsaye tai wajan mother ta ce. "Abbana ya zo?" Mother tai mata kallon baki da hankali ta ce "Waye kuma Abba?" Halisa tai shiru. "Oh! Tsohun mijinki Yaa Sheikh wai?" Ta ɗaga kai da sauri ita burinta ta ji ya zo ɗin. Mother ta ce "Ikon Allah ko shirman naki har kwakwalwarki ya taɓa ne Halisa? Banda haka ina za muga Yaa Sheikh yanzu bayan ya yi tafiya kuma ha yanzu zai dawo ba" Halisa ta ce. "Na ganshi yanzu a bedroom ɗina, na tabbatar shi ne, naji ƙamshin turaren shi har na ce masa Abbana sai kuma ya gudu" Mother ta ce "Ah, ta tabbata kin zauce tsanar shi ce tasa ki ka fara mafarki da shi?" Ta tura baki ta ce "Koma mene ai Abbana ne, ko ya sakeni ai baby zan haifa masa" Umma A'isha ta ce "Haka ne, kuma babyn mai sunan Ummul da Mother" Halisa ta taɓa rai ta ce "Ai na rasa Mother farin ciki take da Abba ya sakeni" Mother ta ƙara sawa ranta cewa Halisa akwai wauta da ƙuruciya a kanta tana son mijinta sosai abu ne kawai ke yawo a kanta. "To ai ni ke nake tayawa murna, farin cikin ki shi ne nawa fa" ta juya kan Umma A'isha ta ce "Ke kaɗai zaki faɗa mini gasky, amma wallahi Modibbo na gani" Ummul dake zaune ita da hajja da Dada da kuma Fulani Atine, da Fulani Balaraba sai Dr A'isha da Yaya Halima da Maimoon da Zeefa. Ummul ta kalli Halisa ta ce "Arɗo ki ka gani, anya ta ya ya?" Ta faɗa tana son tabbatar da abin da take zargi ta ce "Da gaske Ummul naji ƙamshin shi" Ummul a ranta ta ce "Wato ya tuna da layyar zanar shi kenan? Yanzu mata a suffa mai wahalar ganewa" a fili ta ce. "Ki nutsu, gizau ne da saka abu a rai" "Ba kiga kayan lefen Zahrah ba ne?" Sai a lokacin Halisa ta lura da wasu mayan set ɗin akwatuna har set biyar different colours ta dinga kallon kayan, abin ka da wacce ke shirin kaɗan ga damuwa da tai mata yawa, kowa ya juya mata baya, ga rashin cin abinci. Ta runtse idanu bata fahimci baya tayi zata faɗi ba sai taji an kamata an zaunar tare da bata ruwa ta gane cewa suman wani lokacin tayi, kanta a ƙasa ta dinga goge hawaye a takaice. Daga ƙarshe ta miƙe tare da barin wajan. Tana barin wajan Ummul ta ce "Mai ya sa kuke son wahalar da ita, why not a faɗa mata Gasky she's still his wife, look at her condition ba ita ɗaya bace, don't think wani abu zai iya affecting health ɗinsu?" Mother ta ce "Wannan kada ki ji tausayinta ko kaɗan, barta kawai ba abin da zai sameta" Fulani Atine ta ce "Allah sarki akwai ƙuruciya fa, na lura bata kula da Dadarta ba, balle mu" Dada tai murmushi kawai amma yadda taga Danejo ta koma sai duk Jikinta ya yi sanyi. "Sannu da ƙoƙari Ummul, kaya sun yi ma sha Allah Halisa anyi ƙoshi" Yaya Halima ta ce "Wallahi sai son barka, hadda key ɗin mota, ki duba gold necklace ɗin da suke ciki da rings, an narka dukiya" Dr A'isha ta ce "Yanzu an fasa haɗa na wajan Barrister?" Yaya Halima ta ce "Lefen da Barrister ta haɗawa Halisa daban, wannan kuma daga mijinta Aliyu ne kamar yadda Abba Hakimi ya buƙata" Dr A'isha ta jinjina tana son fahimtar mai ya sa Abba Hakimi ya nuna mata an saki Halisa?...Idan bake"Excuse me?" Ummul ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da nufar bedroom ɗin da Halisa ta shiga, Dr A'isha ta bita da kallo tana son fahimtar abin da Ummul take son yi. Ummul na shiga ta samu Halisa zaune bakin gado Idanunta ya yi jajir hannunta ɗaya riƙe da mararta dake mata mahaukacin ciwo,ganin Ummul ya sanya ta saki yanayin fuskar domin Allah ya gani tana son Ummul sosai har cikin ranta. "Ummul da gaske kayan lefen Zahrah ne?" Ummul ta ɓalle murfin gorar data shigo da shi mai ɗan sanyi ta bata ta ce. "Drink" ba tai mata musu ba, domin tana buƙatar ruwan sbd bushewar da maƙoshinta ya yi. Sai da ta shanye fiye da rabi kafin ta ajjiye, ta tura mata plate ɗin wainar fulawa wanda tasa Maimoon ta soya mata, aka saka Attahiru ciki sbd yajin da take so, with egg aka soya da manja. "Eat" Ummul ta furta cikin kulawa sai a lokacin ta ce "Bana jin yunwa Ummul, komai a ƙirji yake tsaya mini" "See you, you can do it maza cinye kiji wani abu" badan ranta ya so ba, ta fara cin wainar fulawar ranta cinye tas ta ƙara shan watermelon juice. Bayan ta dawo nutsuwarta Ummul ta kama hannunta ta ce "Meke damunki Halisa? Mene a ranki share all your feelings with me kinji daughterna" Halisa ta kasa magana sai haɗiyar zuciya, idanunta suka ƙara rikicewa Ummul ta ƙara yarda mugun mugun zafin zuciya ne da Halisa, taurin kai, tare da kafiya da naci. "Talk" hawaye ya shiga silalowa Ummul ta ce "Ok don't cry my dear, take a deep breath". A hankali yaja numfashi kamar yadda Ummul ta ce "breathing down" nan ma ta ƙara saukewa, kamar ƴa da uwa haka Ummul ta jata Jikinta ta rungome, ta fashe da wani matsanancin kuka wanda bata taɓa irinsa ba, ta ƙanƙame Ummul tana shassheƙa Jikinta na rawa, tausayinta ya kama Ummul ta rungometa very tight a Jikinta, ta fahimci Halisa ba soyayyar miji ta rasa ba, hadda ta uwa, da wanda zai zauna da ita yaji ainahin damuwarta, ta rasa soyayyar miji, ta rasa kulawar uwa, ga batun kishiya, ga cikin dake Jikinta ga abubuwan da suke yawo a kanta tare da gurɓata tunaninta. "Ya isa daina kuka haka" Ta ɗagota tana share mata hawayen ta ce "Ya akai?" Cikin rawar murya ta ce "No one's love me, no one's care about me duka sun tsaneni Ummul, ban san meke damuna ba, am a bad gril Ummul" Ummul ta kama hannunta ta ce "Listen, Halisa." Ta nisa kaɗan ta ce "If someone hate you tunani zaki dan me ya sa ya tsaneki? Mene laifinki mai ki ka aikata har ya tsaneki? Idan ki ka fahimta, sai ki fara ta yaya zaki Correcting mistakes naki? By apologies? Or by thinking your future, idan yafiya zaki nema, at anytime zaki iya making mistakes na rayuwa wanda kowa na yi, idan kuma zaki kalli rayuwarki ta gaba dake jiranki, to zaki fara tunanin tayaya zaki kare kanki daga ƙara aikata wannan lafin da ki kai a baya? faɗa mini wanne option ki ka ɗauka?" Halisa was speechless da ƙyar ta ce "Zan yi tunanin gaba" Ummul ta ce "That's my daughter, amma faɗa mini ke ki ka aikata har aka tsaneki ake Publishing naki haka?" Ta marairaice ta ce "Nace bana son Abbana ya sakeni" Ummul ta girgiza kai, tana kallon zallar ƙuruciya duk mai kunya a gaban uwa mahaifiyya ai ba zai ce baya son ɗan data haifa ba, amma ita ko a Jikinta. "Saboda me bakya son Abbanki?" Ta ce "Ummul duk laifin shi ne fa, ya hanani zuwa wajan dangina, kuma ya furta kalmar rabuwa dani ba tare da sanin yadda kalmar zatai tasiri a zuciyata, na yanke shawarar na rama gwargwadon zafin da naji a zuciyata a kan shi, shi ne nace kawai ya sakeni bana son shi, ban san meke damuna ba a lokacin amma komai ƙanƙantar abu zafin shi nake ji a raina, cikin ƙaramin lokaci zuciyata take fusata, amma duk da haka ya sakeni yaje zai auri wata to don Allah Ummul ba dole naji haushi na daina cin abinci ba, na daina dariya da fara'a kuma kullum bana iya barci" Ta jinjina kai irin abin ya ɓata mata ɗin nan ta ce "Duk dare abin ya yi ta yi mini yawo a jiki, marata ta kumbura naji kamar akwai abin da nake so, naji ƙirjina yana ta ƙaiƙayi, sai nayi kuka nake jin daɗin" Ummul understand! Tas ta gane me Halisa ke ji, ba Abin da take buƙata da kewa kamar mijinta ta kuma kasa gane shi kan shi feelings ɗin. Ta gyara zama domin Mentoring nata take son yi da kyau ta ce. "Ki manta ni na haifi Yaa Sheikh, kiyi tunanin ni ce Dadarki shawara zan baki irin ta ƴar da uwa" Ta ɗaga kanta a hankali Ummul ta ce "Kina son Aliyu ko baki son shi da gaske?" Halisa ta sunkuyar da kanta ƙasa kunya ta kamata, tayi abubuwa da yawa wanda Idanunta ya rufe har bata san ta aikata ba, yanzu kuma da wahala ta iya sarrafa kanta akan soyayyar tsohon mijin nata. "Faɗi abin da yake ranki, kada kiyi wasa da damarki daughter" tai ƙasa da kanta taƙi magana, Ummul ta miƙe tsaye ta ce "Ok fine bari naje kada muyi late zuwa Yola" ta faɗa tana yin waje. "To ai ya sakani ko da ina son shi" ta faɗa a sanyaye Idanunta na zubar da hawaye. Ummul ta juya ta kalli Halisa sai ta dawo ta zauna, kafin suyi magana Dr A'isha ta shigo ta nemi waje ta zauna, ba tare da Ummul ta kalli Dr A'isha ba ta ce "The you need something?" Dr A'isha ta girgiza kai ta ce "just to rest" "Ok, am sorry zaki iya bamu waje, You can using the other room" Rai ɓace ta miƙe ta fita, Ummul ta kalli Halisa ta ce "Ba ruwanki daya sake ki, amsa zaki bani" "Ina son shi, yadda nake son Abbana ko Mai martaba bana jinsa haka a raina, yanzu ya manta dani" Ummul tai murmushi ta ce "Your father is your father, matsayin kowa da ban, idan ki kai mini al'ƙawarin zaki sauya na miki al'ƙawarin zan saka Aliyu ya ƙara aurenki ina nufin ya dawo dake" "Ai wallahi nama sauya, ina son Abbana ina son zama da shi fa, da yana nan zai ta rarrashina har nayi barci, kuma ya goya...," Ummul ta katse ta da faɗin. "Enough, sirrine haka zaki zauna da Zahrah kina faɗa mata anything daya ke faruwa matar malam?" Ta ɓata fuska jin sunan Zahrah ta ce "To na daina, amma dai ai mijina ne" ba wasa a fuskar Ummul ta ce "Haka ne, amma aure sirri ne! Ki nemi yafiyar Yaa Sheikh domin bashi kaɗai ba Allah da mala'ikunsa suna fushi dake, kije ki zauna da abokiyar zamanki babu tashin hankali ki nuna kema kina son mijinki duk abin da zai faruwa kada ki yarda tasan faɗa kuke, ko kuna fushi, yanzu kije ki kira shi" Ta marairaice ta ce "Ai bani da number shi, ban san inda yake ba" Ummul pretend! Ta zaro ido ta ce "Au kema? Ai babu wanda ya san duniyar da Yaa Sheikh yake babu wanda yake da number shi, Innalillahi Allah ya sa ba wani abune ya faru ba" Halisa ta gigice ta miƙe zatai waje Ummul ta riƙeta sosai ta ce "Ki bari Abba Hakimi ya dawo, nasan zaki samu wajan shi, da ga yau kada ki kuskura ki ƙara faɗawa wani abin da yake faruwa" ta ce "Adda A'isha kawai nake faɗawa ita take so na, take bani shawarar kada na sake bari Abbana ya taɓa ni" murmushi kawai Ummul tayi tana ganin criminal take ganewa balle ita da take police banda ma zata bada takardar barin aiki. "Ki nutsu kada ki bawa kowa damar shigowa rayuwarki sai wanda ya cancanta, idan naga kina saka damuwa bakya cin abinci to ba ruwana dake" a sanyaye ta ce "Na gode Allah ya saka da alheri" Ummul ta fita tana fita, ta samu sauran a parlour suna ƙara yaba kyan kayan lafen na Halisa, maƙowa da ƴan uwana da sauran abokan arziƙi duk sun shigo. Kaya aka zuba na gani na faɗa duk wanda kayan yasan an narka dukiya. Aka bada tukuici Ummul taƙi amsa sam, Hajja ta amsa ta ce "Ai hakƙine" suka bar gidan. Yaa Sheikh na zaune a babban gidan shi dake ƙasar Makka cikin garin Madina, a hankali ya sauke numfashi idanunsa rufe, tunda yabar gida babu ranar data zama ta banza a gare shi, kullum cikin hukunta kanshi yake da azumi ya ɗauki laifin ya azawa kan shi, so hana ganin laifi, baya layin mazan da so yake rufe musu ido komai girman so zai iya hukunta Matarshi akan laifinta, amma wannan laifin shi da kan shi ya bada ƙofar yi, ya kuma san halin abar shi tun tana ƙarama da zuciya. Ya sauke numfashi yana juya Apple ɗin dake hannunsa bai jimawa da shigowa daga sallar Issha ba. Umar-khan ya shigo bakinsa ɗauke da sallama ya zauna yana faɗin. "Abba ya kira" Ya jinjina kai tare da yin baya ya ɗora ƙafar shi saman table. Ƙamshin turaren Roja wanda ya zauna a jikinsa da kyau yana fita tare da mamaye makaken parlourn na shi, ya faɗaɗa Jallabiyar jikinsa tare da ɗora ƙafarsa saman cinya. Umar-khan kallon Yaa Sheikh ɗin yake yana mamakin abin da yake ɓoyewa. Ringing ɗin waya ya katse shirun Umar-khan ya ce "Ummul ce" Nan ma Yaa Sheikh bai magana ba sai tsare Umar-khan ɗin da ya yi da narkakkun idanunsa, Umar ya bashi wayar ya kara a kunne. "Aliyuna" Ummul ta kira shi a taushashe, ya sauke ajjiyar zuciya yaƙi cewa komai, Umar-khan ya a miƙe tare da barin wajan ganin kamar zamansa ya takura Yaa Sheikh ɗin. Yana fita Yaa Sheikh ya ɗan marairaice ya ce. "Ummul" ta ce "Halisa ko?" Ya lumshe idanu ya buɗe a nutse ya ce "Ya take?" Ta ce "Tana cikin damuwa, na rashinka na lura wani abu na faruwa" ya numfasa da kyau ya ce "Dr A'isha" da mmki Ummul ta ce "Ya akai ka sani?" Ya jima bai ce komai ba sai can ya ce "Na ɗauka ba zaki mamaki ba, ki ɗaukeni matsayin halitta biyu, Mutum da Aljan" tsoro ya kama Ummul ta ce "Mutum da Aljan Aliyu anya wannan rayuwa?" Ya ce "Kada ki mamaki kowa da ƙaddarar shi, ina iya faɗa miki me kike yanzu, tayi yiwu tsari ne daga Ubangiji naji ina son zama haka" "Kenan da gaske Halisa kai ta gani jiya? Layar zana?" Ya yi murmushi mai taushi hannunsa akan dogwan gemunsa yana ja ya ce "Babu ko tantama, ni ne na kasa jurewa" kamar zatai kuka ta ce "Nayi maka magana akan layar zana Arɗo ashe baka ji ba, bayan kasan babu kyau?" Cikin kulawa kamar tana gabansa ya ce "Ummul ko wanne ɗan tara yake bai cika goma ba, ina da ilimi both side, ina arziƙi, ina da kyau ki ɗauka layar zana shi ne dalilin daya sanya ban cika goma ba, na zama tara, amma ni nama manta da ita wannan zuwan bayi na bane, kici gaba da addu'a" Ko ba a faɗa ba yasan kuka take ta kasa cewa komai daga ƙarshe ta kashe wayar. Suna gama waya wani message ya shigo wayar sbd gilmawar notifications, har ya shige sai ya buɗe saƙo ne daga number da bashi da ita ya fara karantawa. _“Aliyu ashe baka haifo ba? Ashe zuciyar kare ce da kai? Ka bani mamaki dana samu labarin ba sakina kayi ba, to wallahi ko zaka mutuwa ba zan komawa aurenka ba, maye wanda ya rako maza duniya ni Halisa Danejo Rome har abada nayi maka nisa kaje can ka zauna da karuwa dan ba abin mamaki bane idan kai ma ka sance haka...I HATE YOU YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU”_ Ya saki wani murmushin manya tare da miƙewa a hankali cikin nutsuwa da kamewa haɗi da tsantsar kamala da addinin daya gama ratsa shi ya turawa number kalma biyu zuwa uku. _“IDAN BA KE”_ shi ne kawai abin da ya rubuta tare da turawa. Tunda ya tsaya a wajan kuma bai motsa ba, sai zufa dake yanko masa all over him hannunsa ɗaya ya dinga rawa, a haka Umar-khan ya riske shi ya dinga kiran sunan shi amma bai tanka ba, bai juyawa ba, zufa bata fasa yanko masa ba. Umar-khan ya ɗauki remote ya kunna karatun Alkur'ani ya nemi waje ya zauna yana kallon sarautar Ubangiji. Halisa na zaune gaban Abba Hakimi yana rusa masa kuka tana faɗin "Don Allah Jon wuro ka yafe mini ka taimaka ka bani number Abbana na kira shi ko sau ɗaya ne" ya numfasa ya ce "Matar sau nawa zan shaida miki bani da number? Amma zan miki al'ƙawari idan kema zaki mini" da sauri ta ce "Wallahi nama yi maka Abbana nake so ka dawo mini dashi" ya ce "Zan saka a lalubo mini number shi, amma ina son ki mayar da hankali ki ƙarasa haddarki saura izu biyar ki kammala kin tsaya wasa, na cike miki form ɗin makarantar "Ibadur-rahman a can zaki ƙarasa za a saka ki ajin hafizan bana zuwa nan da wata uku kin sauke" ta zare ido ta ce "Yanzu sai wata uku zanga Modibbo na shiga uku, ni na haƙura da karatun na haƙura da sokoto bana son kowa bana son komai Abbana nake so" ya ɓata fuska ya ce "Shikenan jeki neme shi" ta riƙe hannunsa ta ce "Shikenan na amince yaushe zan fara zuwa makarantar?" Ya ce "Gobe" a hankali kuka na son ƙwace mata ta ce "Allah ya kaimu" ta miƙe da sauri tayi bedroom ɗinta lokacin Engineer ya faɗo parlourn a gigice kamar an cillo shi. Halisa ta buɗe bedroom ɗin tana sakin kuka ganin bedroom ɗin duhu sosai baƙiƙƙirin ko hannunta bata iya gani yasa taji tsoro ta juya zata fice taji an murza key. Ta buɗe baki zatai magana akai saurin rufe bakin da tattausan hannu mai sanyin gaske hannun duk gargasa, aka fincike hijabin Jikinta zatai ihu ta gudu taji ya haɗata da faffaɗan ƙirjin shi mai cike da suma ta ƙwalla ƙara sbd jin mutum naked babu komai a jikinsa... 08119237616 Paid book*_Sorry for disappointed.. wallahi ban san ydda zan faɗa ba, nayi busy aiki ya yi yawa am trying my best naga na sauke hakƙi amma i couldn't. Kuyi haƙuri bear with me, har gobe har bini IDAN BA KE na kuɗi ne, masu yi mini magana na turo musu daga page kaza zuwa kaza ku saurara, idan buƙata kike ki siya Ubangiji bai hanaki 500 ba.. 08119237616_* Ya riƙeta sosai tare da hanata damar yin wani cikakken surutu. Halisa ta tsorata sosai amma Jikinta ya saki ta lafe jikinsa tana sauke numfashi a hankali, Yaa Sheikh ya jata zuwa bakin bed ya zauna tare da zaunar da ita saman cinyarsa a hankali ya riƙe ƙugunta, ya goga mata tattausan gemunsa mai laushi da santsi. "Waye kai" Ta furta tsoran na barinta ba tare da sanin waye ba, amma haka nan taji ta daina tsorata musamman da taji ƙamshin Abbanta a tattare da mutumin. Duk yadda taso mutumin daya riƙeta ya rungome ya yi magana ƙiyayi, ta luff jikinsa tana sauke numfashi cikin nutsuwa Yaa Sheikh ya zame hijabin Jikinta tare da yin cilli da shi, babu wasu cikakkun kaya a Jikinta duguwar riga ce iya qwiwa, kyawawan cinyoyinta a waje suna ta glowing wanda cikin Jikinta ya ƙara musu gaske. Tsit tayi ta shiga sauke numfashi abin da ke damunta ya shiga tasowa Idanunta ta rufe tana rirriƙe hannunsu dake shafata dasu. "Zaka cutar dani, ka... Ka bari" ta faɗa a rarrafe cikin rawar murya. Bai amsata ba, sai ɓalle bottles ɗin gaban rigar da ya yi, bai tsaya zarewa ba cikin wani irin sabon yanayin daya tsinci kan shi, ya fisge ya cillar. A taushashe cikin harɗewar harshe da ɗaukewar numfashi Cikin rashin ya ce. "Yaa Allah! Wayasubuhanallah, Allahu Akbar" a fili kuma ya ja numfashi tare da sauke shi a wuyanta yana manna mata sajan shi wanda ke ƙara sanyata cikin wani irin yanayi, wanda a ko wanne lokaci zata iya sakar masa kuka idan har bai bata abinda gangar jikinta ke buƙata ba, tuni ta sakar masa ragamar komai. In a romantic style ya zame rigar tare da janta ƙasa shoulders ɗinta suka bayyana, da sauri ta faɗa saman ƙirjinsa ta riƙe ƙugunsa sosai, sbd babu bra a Jikinta haka nan ta samu kanta da jin kunyar wanda ke tare da ita, kuma taji a Jikinta wajan ya zubawa idanu, duk inda yaso kallah gani yake ba ruwansa baya yiwa idanuna shamaki. Ya faɗaɗa fuskarsa da murmushi tare holding nata back fuskarsa a wuyanta yana zuba mata wasu hot kisses wanda ta kasa riƙe kanta ta saki wani sangartaccen kuka ta ce "Waye ne kai? zan faɗawa Abbana tunda mugunta kake mini" Ya fahimci muguntar da take, ya ɗora hannunsa a cikinta wanda ya fara kumbura sukai baya ta faɗa ƙasa, shi kuma ya yi mata rumfa hannunsa dake mararta ya shiga murzawa har ya zame rigar, ta rufe idanu Jikinta ya ɗauki rawa tunaninta wani abu zai mata sai taji saukar softness lips ɗinsa a cikinta ya sumbata, ya ƙara sumbata murya can ƙasa ba tare data san magana ya yi ba ya ce. "Abbie is here, Ammi is here" ya ƙara yi mata wani kisses ɗin a cibiya yana shafa cikin ya ce "Oh God, protect my unborn child" Ya zame jikinsa tare kallon fuskarta da yake ganinta tarwai a idanunsa ita kuma ta lumshe idanunta, ya sumbaci goshin da kuncinta daga nan bata sake sanin meke faruwa ba, sai farkawa tayi taga ƙarfe 5:15 na yamma. Ta farka a tsorace da ƙyar ta iya addu'ar tashi daga barci, ji tayi duka gabɓanta ciwo suke, ta saka hijabi tare da kunna hasken bedroom ɗin ta shiga ƙarewa ɗakin nata kallo babu komai sai ita ɗaya,ta dafe ƙirji ta ce "Ya Allah meke shirin damuna ne? Me ya sa nake ganin Abbana?" Ta dafe kai tana zama bakin kujerar. Mother data buɗe ƙofa ta shigo ta ce "Halisa?" Tai firgigit ta buɗe ido a rarrabe kamar mara gasky ta ce "na.. na'am" "Meke damunki, ɗazo na shigo na sameki kina ta barci zuwana na uku kenan, yanzu kuma ina sallama shiru" Ta juya ta kalli bedroom ta ce "Mother ba kiji ƙamshin Modibbona ba?" Ta saki baki ta ce "Wanne irin ƙamshi ni Maryamu, ƙamshin kuma na Yaa Sheikh bayan kin san baya ƙasar" Ta saki kukan tsoro, shagwaɓa hadda rigima ta ce "shi na gani, yanzu ya shigo muna tare har barci ya ɗaukeni" Mother ta saki tsaki ta ce "Kin fara samun matsala, ki tashi kiyi wanka da sallah kici abinci, ina son duba lafiyarki" Ta goge idanu tare da yin kicin-kicin da rai. "Meye kika haɗa fuska, ba zaki mini wannan sangarta taki da kukan rashin abinyi ba" Ta ƙara haɗa fuska ta ce "Allah ya baki haƙuri, naga dai Abbana Dr ne, kije kawai zai duba ni" Mother ta ce "To sannu ƴar Abba ba kiji kunya ba? Bayan kin gama yi masa ɗiban Albarka, baki duba girman shekarun shi da gemun shi, da ilimin da Allah ya bashi kika watsawa idanunki toka kika ce bakya son shi ya sake ki?" Ta marairaice fuska tana tura baki ta ce "To yanzu na cire tokar shikenan? Nifa ina son Abbana ko ya yi sakinma wallahi ban sako ba" Mother ta saki baki gudun kada ta sake magana, Halisa ta sakar mata layi ta ce "Uhm ki fito ina jira" ta ce "To, amma idan kin san zaki mini wannan allurar wallahi bana so" ita dai Mother ba ta ce komai ba, sai da taje ƙofa zata fita Danejo ta ce "Mother wallahi idan Father yazo ki bisa zama babu miji babbar masifa ce kuma jarrabawa uhm" da sauri Mother ta fice daga cikin bedroom ganin tsakani da Allah ita Halisa shawara take bawa Mother ɗin. Wanka tayi tai sallah tare da yin Istigifari na makarar da tayi, ta shirya cikin wata light blue ɗin abaya mai stones da flowers tana da faɗin wuya hakan yasa rigar ya zauna sosai a ƙirjinta wanda ya ƙara cika da sauyi, babu rama a Jikinta domin kullum ƙara buɗewa take musamman waje biyun nan, da hips da brest ta fuska ne ta fayau Idanun ya faɗa sai dogwan hancinta kawai. Ta fito Main parlour tana rolling vail ɗin abayar hannunta riƙe da waya. Ba kowa a parlourn kai tsaye ta shige kitchen ta samu salad da tumatir da albasa ta haɗe waje guda fal cikin plate, ta zuba white oil da yaji kaɗan ta saka maggi, ta haɗa da lemon tsami yawonta har tsiyaya yake sbd wani irin kwaɗayi daya taso mata, daman ta jima ba taci komai ba, sai abincin da Ummul ta bata. Ta fito da kwaɗon salad ɗin da lemon citta data haɗa ta daka ice ya yi wani irin sanyi na shige misali. Zama tayi saman kujera ba tare data lura da wanda ke zaune ba, hannu baka hannu ƙwarya ta dinga cin salad ɗin, fisgewa taji anyi kamar tai hauka ta ce "Wane mai son ɗaukan zunubin ne" ta faɗa tana miƙewa Idanunta ya sauka akan Khalil Ahmad Sarki ta saki murmushi tana tsalle tare da rungome shi ta ce "Oyoyo my prince my hamma" ya watsa mata harara ya ce "Princess wannan yajin is not good for your health" ta marairaice ta ce "Please Hamma ka bani wallahi ji nake kamar zan amai idan banci ba" Umma A'isha ta ce "Kada ka damu babu abin da zai mata" ya watsa hannu ya ce "daman dai fushin Yaa Lee nake jiye mana" Halisa bata sake cewa komai ba sai cin salad take, tana gamawa ta ɗauki ruwa mai sanyi tasha. "El-bashir karɓo mini ruwan nan" El-bashir dake zaune kusa da Halisa bata sani ba,ya ware idanu ya ce "ki barta mana" cikin tsawa ta ce "Mubasshir ka kawo mini nace ko?" Halisa na tsaka da shan ruwan sanyin wanda take jin daɗin shi taji an ƙwace ta juya da sauri suka haɗa idanu da El-bashir cikin masifa ta ce "Waye kai? Meye haɗinka dani da zakai mini shisshigi cikin lamarina?" El ya kasa ce mata komai sai Dada ce ta ce "Ni zakiwa rashin kunya ba El-bashir ba, kuma ba a taɓa sauya tuwo suna" Halisa ta miƙe duk da taji daɗin ganin mahaifiyarta amma hakan bai hana ɓacin ranta bayyana ba ta ce "Ba zan taɓa son shi tunda baya ƙaunar Abbana ya nemi kashe shi" tana magana faɗin hakan tai bedroom idanunta cike da ƙwalla. Dada ta miƙe zata bita El-bashir ya ce "Please Mom u hve to understand her feelings komai tayi daidai ne, ni ne mai laifi nima kuma bisa kuskure amma dani da ita ba a san wanda yafi son Yaa Lee ba" Dada ta ce "Duk wannan bai zama dalilin da zata wulaƙantaka kuma ta tsaneka ba" Khalil ya ce "Be patient Mom, I'll talk to her tana da zafi da riƙe abu ne" ya lallaɓa Dada ta zauna shi kuma ya nufi wajan Halisa.. Washegari Halisa ta shirya ta nufi makarantar Ibadur-rahman. Zahrah na zaune gefen gado Dr yana ƙara dubata domin yau za a sallameta daga asibiti ya ce "Allahamdulillah jiki da sauƙi, kici gaba da shan magani" tai murmushi ta ce "Thank you Dr, da baka taimaka mini ba, ba zan taɓa samun farin ciki da auren Yaa Sheikh ba, naji daɗi yadda plan ɗinmu na ciwon Cancer ya tafi daidai babu matsala" Dr ya ce "Imagine da gaske ace kina da Cancer" ta ce "Please daina faɗa ban shirya tafiya lahira na bar Yaa Sheikh ba, burina naga ranar aurenmu amma sai nan da wata uku ai thank God an kawo kuɗi dai" Dr ya jinjina kai ya ce "Congratulations, yanzu kin daina sharholiyya kenan?" Ta ce "Har abada babu ni ba ita, daman can tsautsayi ne balle yanzu dana fahimci Yaa Sheikh tsanar da ya yiwa kalmar Zina, sai naji na tsaneta nima, ina son shi kamar zan mutu ina buƙatar soyayyar shi da kulawar shi, wannan dalilin yasa nace ka faɗa masa ina da ciwon Cancer it was all my plans" Surry dake bakin ƙofa riƙe da Muhammad ta dafe ƙirji a ranta ta ce "That's means she's lying to him? ba wani ciwon Cancer" tai murmushi tana girmama ƙarfin son zuciyar Zahrah. ta juya ba tare data shiga ba, Dr ya sallami Zahrah suka koma gida ta fara shirye-shiryen biki a karo na biyu duk safiyar Allah sai ta kira Yaa Sheikh wani lokaci ya ɗaga wani lokaci ya share, tun tana dannewa harta fara yi masa complain shi kuma ya ɗan fara sassauta yanayin sbd condition ɗin da take ciki. A hankali yake tafiya kan shi a ƙasa yana gyara zaman alkyabbar jikinsa fitowar shi kenan daga zaman tattaunawar da sukai akan aikin hajjin da za a fara nan da kwana goma. A yau ɗin kuma yake son barin Madina zuwa Makka, amma yana da muhimman wajan da yake son ya ziyarta ya kaiwa Allah kukan shi, ya kuma karkato da hankalin Saif-wazir zuwa gida. Daga nan masallacin juma'a ya nufa yaja jam'i kana ya yo gida. Umar-khan dake zaune ya ce "Ka samu kira, da saƙwanni" ya jinjina kai idanunsa rufe a taushashe cikin gajiyawa ya ce "Kayi magana ko?" Umar-khan ya ce "Abubuwa da yawa sun ƙare a kamfanin sarrafa shinkafa, munyi magana da Manager Khalil dole za a tura wani Chaina" Yaa Sheikh ya yi shiru ya ware idanu ya ce "El-bashir" Umar-khan ya ce "I don't have his number" da ido kawai Yaa Sheikh ya kalli Umar-khan ya ce, da sauri cikin ladabi ya miƙa masa wayar a hankali kamar mara lafiya ya zuba number El-bashir a wayar ya danna kira tare da saka handsfree. Lokacin El-bashir yana tare da Abba Hakimi da Dada tare da sauran family wayarsa ta fara kaɗa Algaita, ganin sunan da bai taɓa tunani ba da sauri ya ɗauka yana faɗin. "Assalamu alaika" Yadda ya amsa wayar with so much respect yasa sukai tunani Mai martaba ne. Yaa Sheikh ya amsa kafin ya ce "You're alone?" El ya ce "Many people" lokacin Halisa ta shigo hannunta riƙe da Alkur'ani fuskarta rufe da liƙab El-bashir ya ce "Include your wife" Halisa kamar wacce ta fahimta tayi saurin ƙwace wayar Jikinta na rawa ta kara a kunnenta ta ce "Abbana" Ya runtse idanunsa zuciyarsa tai kyakkyawan bugawa gabaɗaya Jikinta ya ɗauki sautin muryarta wacce ya yi kewa da jinta , ya rungume hannayensa a ƙirji, ganin haka ya sanya Umar-khan miƙewa tare da fita yasan yanzu ba lallai ayi maganar kamfanin ba. Yadda taji anyi shiru ta ƙara tabbatarwa Abbanta ne akan layi ta zame wayar daga kunnenta ta ɗora a bakinta ta sakar matsa kiss ta ƙara sakar masa wani kiss ɗin "Muu'ah... Muu'ah" Abba Hakimi ya yi ƙasa da kai, Dada ta miƙe tabar wajan, mother ta saki baki da hanci Umma A'isha dake kakace tayi murmushi kawai, Khalil Ahmad Nuran Sarki ya kalli Halisa yana yabawa rashin ta indonta. Mubasshir El-bashir Ahmad Nuran Sarki ya kalli kyakkyawan ƙanwar ta shi mai tsananin kama da shi, komai nasu iri ɗaya ne so da ƙaunar Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki kuma Halisa Danejo Rome uwa uba Matar Malam Halisa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu ya wanzu a zuciyarsa. Ta buga tsalle tama mance da cikin Jikinta tana sakin dariya hawaye na zubu mata ta fasa ƙara da ihu wanda ya karaɗe parlourn bakiɗaya ta ce "I love You Abbana, I miss you Modibbona, ina sonka Yaa Sheikh ina sonka ina sonka zan cinyeka da soyayya Mijina mai gemu" tuni Khalil ya ɗora Camerar iphone ɗinsa akanta. Yaa Sheikh ya nutse cikin lallausan kujerar da yake yanayin da yake ciki ba zai barshi yayi magana ba, bai sai adadin ke yake ji akan wawta da ƙuruciyar ƴar fillo ba. Ƙit ya kashe wayar yana fesar da numfashi ya faɗaɗa fuskarsa daga kamewa yana jan gemunsa ya ce. "Bbyn Abba, Matar Malam" wayarsa tai haske ya duba. "Check Your WhatsApp" Number Khalil da ita aka turo saƙon. Akwai Wi-Fi gidan yana shiga vedio ya shigo, milk ɗin hijabi idanunsa ya gane masa, ya yi downloading vedion da sauri ya miƙe idanunsa akan Halisa dake tsalle na muryar jin muryarsa ya katse ya kira number Mother tana ɗauka, a karo na farko cikin zafin murya harshensa na riƙewa ya fara faɗa da masifa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, don me za'a barta tana tsalle bayan ansan ba ita ɗaya bace if something happens to her fa? Yana gama faɗan ya kashe wayar ba tare daya bar Mother tayi magana ba. Ta riƙe haɓa ta ce "Yau zafin zuciyar Aliyu Gadanga ya motsa masifa kenan" jikin Halisa ya yi sanyin ganin yadda Yaa Sheikh ya yi mata banza ko dai da gaske bashi bane kamar Yadda El-bashir ya faɗa?... *_3 month later_* Gabaɗaya harabar filin da ake saukar Alkur'anin da bikin hafizan mahaddata a cike yake da manyan baƙi, iyayen yara da ɗaliban saukar. Kimanin ɗalibai 100 ne cif sai hafizai guda 35 sanye suke da fararan hijabi tas sun san rufe fuska da liƙab, hannunsu sanye da safa haka ƙafarsu, wanda sukai saukar kuma milk ɗin hijabi ne a jininsu, makarantar matan aure ce amma ba'a taɓa sauka wacce takai wannan ba acikin shekarar. Ɗaya bayan ɗaya aka dinga kiran sunan hafizan suna karatu daga ƙarshe aka ce "Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" a sanyaye ta miƙe tana ƙara buɗe hijabinta sbd cikinta daya fara tasawa na kimanin wata huɗu zuwa biyar. Yau ta ƙara tabbatarwa Abbanta Yaa Sheikh ya gujeta rana mafi muhimmanci da zai tayata murna amma babu shi a wajan ko wacce mace mijinta na tare da ita, amma banda ita. Tayi ƙasa da murya tana sauke numfashi a hankali cikin sautin murya mai amo! Wanda duk wanda yasan yadda Yaa Sheikh yake ƙira'ar Alkur'ani yaji karatun Halisa zai san cewa rainon shi ce, cikin fidda tajweed da makarijin huruf ta fara karatun cikin suratul Nisâ'i. Wajan ya yi shiru aka shiga tasa Camera a kanta duk da ba a ganin fuskarta wani irin karatu take mai cike da nutsuwa. A hankali ya juya fararen idanunsa akanta yana mai yabawa da karatun nata farin cikin da yake ciki ya ninka nata, shi ne maƙo na musamman da sarkin Kano amma har ya bata Alkur'ani da certificate da allo bata san shi ne ba, tana gama karatun ta saki kuka wanda an ɗauka na farin ciki ne, ita kuma zallar damuwa ke damunta na rashin ganin nata gwanin ko ta ce tsohon mijinta. Aka dinga basu kyaututtuka anan aka Shaida akwai muhawarar Alkur'ani ta ƙasa da ƙasa wacce hadda sunan makarantar a wacce za a fara karawa ta cikin gidan kafin a samu gwarzuwar da zata tsallake matakin ƙarshe. Taro ya tashi Halisa taci kuka ta ƙoshi Mai martaba ya dinga alfahari da Princess haka Dada, Ummul ta rungome Halisa jin hadda zazzaɓi a Jikinta,cikin kuka ta ce "Ummul baya so na da gaske, na shiga uku Ummul zuciyata" Ummul ta ce "kada ki damu kanki, akwai gajiya da zazzaɓi tare da ke" kafin Halisa tayi magana suka ji ance "Assalamu alaikum" ƙamshin turaren Roja ya ƙara bayyana mai sallamar Halisa ta juya da sauri tana cire liƙab ɗin fuskarta sukai idanu huɗu da Yaa Sheikh dake tsaye cikin wata dakakkiyar shadda fara tas ya ɗora Alkyabba mai tsananin kyau da tsada ya fito a Yaa Sheikh ɗin shi. Hawayen fuskarta ya ƙasa tsayawa,Ummul tai murmushi a hankali ya shiga takawa har zuwa inda take tsaye ta haɗe fuska kamar ba ita ke kukan rigima ba, yana zuwa ta juya zata gudu ya saka tattausan hannunsa ya kama nata tare da dawowa da ita baya, a hankali cikin wani kyakkyawan yanayin ya juyawa su Ummul baya yana mai shigar da Halisa cikin Alkyabbar shi ya zagaye ƙugunta da hannunsa duk biyun suka manne da juna, ya ranƙwafa daidai wuyanta ya sumbaci kuncinta da bakinsa mai tsafta tare da hura mata iska a kunne cikin raɗa ya ce. "Congratulations Hafizata.... Ruhin Aliyu" ya faɗa yana lashe gefen kunnenta...Halisa ta ɓata fuska tare da yin kicin-kicin da ranta, Yaa Sheikh ganin idanun jama'a baya kansu ya saka tattausan hannunsa tare da tallafo fuskarta ya ɗora fuskarsa saman nata idanunsa na yawo a fuskarta yana son ta sanya nata idanun cikin nasa, ko ya fahimci rigimar ta yanzu ta mece? Duk da yasan ya yi laifi mai yawa har bai san ta ina zai fara ba?. Yadda gangar Jikinta tayi kewar shi haka zuciyarta, ta kasa jurewa yanayin musamman ƙamshin turaren dake sauya mata yanayin da take ciki. Ta ɗago Idanunta a hankali ta zuba cikin nasa gently ya lumshe nasa gajiyayyun idanun yana jin abu na fisgar shi kamar ya jawota ya rungume na tsayin lokaci Ganin nata ya fara kassara masa jiki da son sauya masa yanayin da yake ciki Ya rufe ido ya buɗe a hankali ya zameta daga jikinsa ba tare da ya ce komai ba ya juya daidai lokacin Umar-khan ya yi parking da mota, kai tsaye ya shiga suka bar wajan da sauri. Tabi motar da kallo tana jin kamar ya tafi da zuciyarta ne, tsoro ya kamata ta shiga addu'ar Allah ya sanya ba tafiya ya sake yi ba a karo na biyu?. "Hankali ya kwanta?" Cewar Mother dake tsaye cikin wata atamfa ta ɗora mayafi akai murmushi Halisa tayi ta ce "Ni daman a kwance yake" Mother ta riƙe baƙi ta ce "Ba shakka, to zan sanar masa kada ya dawo" tayi saurin ɓata fuska ta ce "Allah ya sa ba cewa nayi bana son shi ba" Yaya Halima tayi murmushi ta ce "Faɗa mata dai daughter kisan zaman da zaki da ita" kamar jira Halisa take ta ce "Wallahi Anty Halima duk wanda baya so na da Modibbo na sani, kawai rabuwa nake dasu" Ummul dake tsaye hannunta riƙe da key car tana sanye cikin Abaya wacce kallo ɗaya zakai kasan bata ƙana nan mutane bace, tayi rolling vail a kanta ba zaka taɓa cewa ita ta haifi Yaa Sheikh ba. Ta murmusa ta ce "Rabu dasu Daughter, yau ranar farin cikinki ce, kin zama hafiza, Modibbo ya dawo kuma yau zaki tare a gidan mijinki kekam waya kai ki sa a?" Halisa ta ƙara wajan Ummul ta ce "Ai ina haihuwa sunanki zan saka, kinfi kowa so na, idan Abbana ya kuma yi mini wani cikin sai na saka sunan Abbana mijina Aliyu" "Yau mun shiga uku da mara Kunyar yarinya" cewar Mother. Ummul ta ce "Gold setting ke aiki, let her do" Ummul ta duba agogon dake hannunta ta ce "Ya Allah, bari naje am getting late, sai kunzo" ta kalli Halisa ta ce "Congratulations once again Matar Malam ta zama Malama, your gift is waiting for you" Danejo tayi kyakkyawan murmushi wanda ya ƙara fidda kyanta, tana ƙaunar Ummul na gartar matar ta kai harta shige samun uwar miji kamarta a yanzu sai an bincika. "Allah ya tsare Ummul" Ummul ta murza key tare da tayar da motar cikin nutsuwa take driving harta bar wajan. Yaya Halima ta ce "Matar nan tana birgeni iliminta ya yi rana, tasan yadda ake mu'amala da mutane" mother ta ce "Wallahi" motoci suka shiga zuwa gida domin gabatar da sauran abubuwa tuni an tashi wajan saukar. Baƙin motocin da Halisa ta gani a parking lot ya bata mamaki sai ba ta ce komai ba, ta nufi cikin gidan fuskarta ɗauke da farin ciki tayi zaton zata samu Yaa Sheikh ciki Turus! Tayi ganin Surry riƙe da Muhammad matar da bata taɓa tunanin zata sake ganinta ba, Surry ta miƙe tana faɗin.. "Su ƴar fillo manya, kin zama babar mace kamar ba mai tallan Kindirmo a Rugar Rome ba?" Halisa smiling, ta zauna tana cire hijabin Jikinta fuskarta a sake ta nuna itama ƴar duniya ce ta ce "Kyakkyawan tarihi shi ake tunawa har ayi maka gori akai, masu ta zubar sai dai ya zame mutu tabo na har abar baya" Surry ta shanye maganar ta ce "Haka fa, to ya kike fatan lafiya?" A hankali ta ce "Lafiya ita ke ɓoya, kin dai ga yadda nake, na ɗauka zaki bari sai na haihu ai?" Surry ta cije baki ta ce. "Babu ko kunyata ki ke maganar haihu?" Halisa ta kaɗa ƙafa tana jingina ta ce "Cikin Yaa Sheikh ne fa, na halak ɗan sunna? meye aibu a wannan zamanin ake yawo dana shege ba bare wanda igiyar aure ya baka" tana faɗin hakan ta miƙe zata shige ta ce "Mun kawo amarya ne, naga kamar baki sani ba, ko Yaa Sheikh bai faɗa miki ba, ƙilan abubuwan sun masa yawa ya manta" Halisa takai seconds 20 kafin numfashinta ya daidai a wannan tsaiwar da tayi, ƙirjinta ya buga mararta ta ɗaure sosai. Idanunta ya shiga rufewa jiri na neman ɗaukanta, ta dinga kiran sunan Allah har ta samu daidaito ta maze fuska ɗauke da murmushi ta ce "Ƙaramin abu uzururruka suke sawa a manta ai, yanzu kuma na lallaɓa shi yaje zai huta" har tai gaba ta ce "Ina amaryar ko nace uwar mata inji Jadda nikam ai Mumy zance mata" mamaki ya kusan kashe Surry take zaune, ta ƙara tabbatarwa wuta ba wajan wasan yara bace an ajjiye ƙwarya a burminta. "Akwai event anjima so tana hutawa zuwa lokacin" Halisa ta watsa hannunta sama ta ce "As she wishes" Da ƙyar ta ƙarasa bedroom ɗinta, tana zuwa jiri ya kwasheta cikin sauri Dada dake zaune ita da El suna magana akan yadda zasu faɗawa Halisa baƙon al'amarin. "Danejo, what happened to you Halisa" ina tuni ta fara kokawa da numfashinta dake neman ɗaukewa kamar wata mai Asthma. Dada ta jata Jikinta ta rungume ta zauna bakin gado tana jijjigata tare da kiran sunanta amma ina a tsorace ta ce. "Prince go and call Mother" ya miƙe hannunsa riƙe da sanda sbd ƙafarsa da bata gama ƙwari ba, yana fita ya samu Mother ita da Maimoon tsaye suna magana ya ce "Mom, my Mom is calling you" "Lafiya dai Mubasshir" ya ɗan kalleta ya kalli wajan ya ce "Princess ina nufin Ha..." Bai ƙarasa faɗa ba tayi saurin bawa Maimoon bowl ɗin hannunta ta nufi bedroom ɗin Halisa. El-bashir ya nemi saman kujera zuciyarsa fal tunani akan dalilin daya sanya Yaa Sheikh zai ƙara aure, ya rasa wacce zai aura sai Zahrah yarinyar daya sha ganinta lokacin da ya je raka Mai martaba Oummara. Ya juya ya kalli Maimoon ya ɗan kalli bayanta ya ce "Where's Fattoumah?" Ta ce "Zazzaɓi ke damunta, tana bedroom" A hankali ya ce "call her" Ta juya a zuciyarta tana mmkin miskilanci na El sai wanda ya yi niyya da shi zai magana. Yana zaune hannunsa riƙe da waya yana dannawa ta shigo parlourn bakinta ɗauke da sallama, ya amsa without looking at her "Uncle El gani" ta faɗa a hankali tana riƙe kai, ya ɗaga kai ya kalleta ganin yadda tayi tsaye kamar ana yaƙi ya ce. "Zan rankwashi kan ki,idan ki ka sake ya yi mini tsaye" ta tura baki ya miƙa mata hannu ya ce "Come" Ta kama hannunsa ta zaune gefensa yaji Jikinta zafi ya shafa kanta ya ce "How long?" Ta kalle shi ya ce "the fever" ta ce "Yau ne" ya jinjina kai yana faɗin "Sorry" Tai shiru ba tare da tace komai ba, ya samu kan shi da son jin muryarta ya ce "Fattom ya akai?" Hawaye ya shiga saukar mata ta ce "Mother nake so ta dawo wajan gidanmu, kowa babarsa na tare da su mu daga Grandma sai Father" ya lura abinda ke damunta kenan, yarinyar nada riƙo sosai cikin son kwantar da hankalinta ya ce "Kina son daina damuwa?" Ta ɗaga masa kai ya ce "Ki biyoni nan muje na ajjiyeki har abada" ya faɗa yana nuna mata saitin zuciyar shi. Ta dinga kallon shi ta rashin fahimta ya ce "I love You Fattom, Kinyi ƙarama but I'll manage zan kula dake" kunya ta kamata ta miƙe da gudu tabar wajan ya bita da kallo yana taɓe fuska. Mother dake tsaye ta dinga trying number Yaa Sheikh baya going ta ce "Meke damunta ne wai?" Yarinya rigima tai yawa, ga saurin ficewa daga hayyaci. A raunace Dada ta ce "Ban sani ba, kawai haka ta faɗo" "Ko ta samu labarin auren Yaa Sheikh ne?" Dada ta ce "Anya? Bana jin haka" Ta dubi Halisa dake kwance jikin Dada ƙirjinta na ɗagawa hawaye na bin fuskarta, ta juya babu jimawa ta dawo da ruwa mai sanyi ta buɗe ta shiga shafa mata a fuska zuwa ƙirjinta, taja doguwar ajjiyar zuciya a hankali ta buɗe idanunta ta shiga binsu ɗaya bayan ɗaya ta ce "Da gaske Abbana Ya auri Zahrah?" Dada da Mother suka kalli juna, suka kasa bata amsa ta miƙe zaune hawaye wani na korar wani ta ce "Kuma ya tabbata Abbana ya sakeni? Yanzu nu ba Matar Yaa Sheikh bace na daina amsa sunan Matar Malam, ya auri Zahrah" Idanunta ya ƙara rikicewa Mother ta ce "Wai injiwa? Waye ya ce ya auri Zahrah?" A takaice ta ce "Her friend Surayyerh" Mother tai murmushi ta ce "Yanzu maganar banzayen can ki ka ɗauka? Ko dan ranki ya ɓaci ai ta faɗa ke kuma ki ka yarda mai maimakon ki nuna mata baki damu ba, ko mata uku Yaa Sheikh zai sake aura" Ta runtse idanunta taji jamar zuciyarta ce zata faso sbd yadda take harbawa ta ce "Don Allah Mother ki faɗa mini gasky, wlh zuciyata zata buga ni kaɗai nake son Abbana bana son ko wacce mace ta so shi" Dada ta ce "Da gaske....," Tayi saurin katse Dada da cewa "Maganar aure babu, sun zo kawo wai Muhammad dayi miki murna zama hafiza" wata wahalalliyyar ajjiyar zuciya ta sauke mai nauyi a fili ta ce "Allhamdulillah" Sai tausayinta ya kama Mother domin Halisa na cikin matayen nan masu bala'in kishi wanda yake kusan yin ajalinsu ta ce "Dole ki nuna musu babu abinda ya shafeki, ki tashi yanzu ki wanka mai gyara zata zo a ƙarasa yi Kinga idan akai yau shi ne aka ɗauki wata guda anayi, za'ai miki nut make-up akwai event a gidan Ummul" Ta miƙe tsaye, Dada ta dinga kallonta a ɓoye da yadda kullum cikin Halisar ke sake bayyana kanshi a fili, ya zauna tas wanda ya ƙara mayar da ita babbar kan ɗauka tayi shekaru 20 zuwa saka amma she's still on 17 going to 18. Wanka tayi da wani bath perfume wanda aka kawo mata tun daga Maiduguri, tana fitowa mai gyaran wacce ta kasance matashiyar budurwa ta fara yi mata dilka a jiki nan da nan fatar ta ɗauki glowing, ana gamawa aka saka mata turaren wuta na jiki aka rufeta da wani duvet ya shiga ratsa jikinta, kana ta bata wani ta tsuguna akai ya shigeta da kyau, ta sake yin wani sabon wanka gabaɗaya bedroom ɗauki ƙamshi turaren ya zauna Jikinta, kowa ya ganta sai ya yaba kyan Jikinta, musamman data kasance mai haske. Aka shiga yi mata make-up duk da tace bata so, amma Mother ta tsaya akanta kafin a gama akawo wani farin voyel na mata mai golden ɗin flowers da manyan zane, ana gamawa ta saka kayan riga da skert ne ya kama Jikinta ya yi bala'in kyau, akai mata ɗauri mai steps, Halisa bata yarda da gaske ake event ɗin ba, sai da taga an ɗakko golden ɗin Alkyabba ta mata mai farin zane an saka mata. So ma sha Allah! Ta fito a Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki, ta fito a Halisa Danejo Rome sbd kyanta na Fulani, Ta fito a Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu sbd nutsuwar ilimin data bayyana a jikinta. Make-up artist ɗin ta dinga yi mata vedio da pictures masu a zaɓaɓɓen kyau. Mother ta ce "Ki zauna kada ki fito,sai ma kira ki" ƴar Maiduguri ta shiga bawa Halisa kyakkyawan darasi na aure tana mata bayanin abubuwan da maza suke ƙauna musamman mijinta daya kasance babban malamin addinin Muslunci. Zahrah da mai make-up ɗinta, aka zuba wani eyelashes da eyeshadow ta saka red ɗin lace fitted gown "Wai meye kike haɗa rai?" Ta ce "Naso nasan wanne kaya yarinyar can zata saka ne wallahi" Surry taja tsaki ta ce "Kina da damuwa, yarinyar da bakya gabanta" Zahrah ta ce "Ba zaki fahimta ba, yarinyar kamar ƴar tsana wallahi komai kyau yake mata" Surry ta ƙara jan tsaki ta ce "Madam be yourself". Misalin biyar daidai ba tare da sanin kowa ba motar Halisa ta bar gidan zuwa gidan Ummul, Babban harabar gidan an zuba masa decoration sai ka ɗauka hall ne, yanayin decoration ɗin sai kayi mamaki domin close hall akai mayar da wajan mai maimakon open, Familyn su Ummul da suka kasance manyan mutane wayayyu duk sun zo, Aka rufewa Halisa fuska da hular Alkyabba Ummul ta kama hannunta zuwa wani bedroom ba kowa ciki, ta shiga kiran Yaa Sheikh baya ɗagawa, ta kira Umar-khan shima bai ɗaga ba, tun safe Yaa Sheikh yabar wajan sauka har biyar ina ya yi? Ko ya mance da batun event ɗin?. Tana tsaye sai ga Khalil ya shigo suka gaisa ta ce "Yarima ina Yaa Lee ɗin?" Ya shafa kai ya ce "Yana can ɗaya part ɗin Halisa nazo kira" tai murmushi ta ce "Ok zata zo" Ummul ta ƙara feshe Halisa da perfume wanda Yaa Sheikh yake mahaukacin so, ta jata ta ƙofar baya har zuwa part ɗin da yake ciki. Sai kunya ta kama Halisa Ummul ta harareta ta ce "Ke da Abban naki?" Tai ƙasa da kai, a hankali ta murɗa handle ɗin ƙofar cikin siririyar muryarta ta ce "Assalamu alaika" Yana tsaye a tsakiyar parlourn fitowar shi kenan daga wanka ya shirya cikin shadda fara da Alkyabba wanka ya zuba kyau sosai, saukar muryarta ya sa ya juya a hankali suka haɗa idanu, frm head to toe ya dinga kallonta a ransa ya ce "Mace ta gari" a fili kuma ya ɗan saki fuska tare da ware mata hannu alamun ta zo, kanta a ƙasa ta shiga takawa har zuwa inda yake tana zuwa ya jawota jikinsa yan ɗora kansa a wuyanta ya ce "Amincin Allah ya tabbata ga ruhin Aliyu" ya rungometa sosai daidai lokacin suka ji ƙarara saukar camera akansu ta ko'ina, da hasken vedio, Khalil Ahmad Nuran Sarki, Umar-khan, Ishaq-Hakim, El-bashir Ahmad Nuran Sarki sai wani ɗan uwan Yaa Sheikh wanda bai san da shi ba sai yanzu Mujaheed gabaɗaya sun saka farar shadda da milk ɗin Alkyabba, sai wasu photographers wajan su biyar, Hadda Majeeda photographers mai yiwa sarkin Kano photo, Yaa Sheikh an shammace shi, baya son wanann bidi'ar bai kuma san da ita ba, yana son sakin Halisa sbd vedion da ake musu amma yana tsananin kishin pech ɗin jambakin da aka saka mata, ya ware fararen idanunsa akanta gently ya tallafo haɓarta yana ƙara ranƙwafawa daidai fuskar yana mai rufeta da Alkyabba cikin nutsuwa ya ɗora bakinsa saman nata, su duka suka lumshe idanunsu rabon da suji ɗanɗanon kiss na juna sun manta wata kyakkyawar cafka ya yi wa bakin nata ya shiga kissing nata cikin kwarewa irin ta malamai a ran shi yake jin duk gift ɗin daya ta nada sunyi kaɗan a gareta, ya ƙara janta ya matse ya rungometa sosai kamar za a ƙwace ta... Sarautar's Library Paid book #500 08119237616Latest news On IDAN BA KE.......❤️ There is a prize for the person who comments the most on TICTOK👇🏾 https://vm.tiktok.com/ZMYLLt9QX/ Dan shin da yaji a gemunsa da kuma kwantaccen zagayayyen gashin da ya yi luf saman bakinsa ya sanya ya fahimci kuka take mara sauti, ya zame fuskarsa bayan ya tabbatar ya gama shanye gabaɗaya jambakin da lipstick ɗin dake bakin nata. Da kyawawan idanunsa wanda suka janye ya zuba mata su, ba tare daya rabata da jikinsa ba, ya tallafo haɓarta tare da sanya yatsar hannunsa ya goge mata hawayen yana ƙara ware idanunsa a kanta so yake ya buɗe baki ya furta. "Ya kike? Mene na kuka?" Amma bakinsa ya yi nauyi harshensa ya harɗe, ta kalle shi muryarta na rawa ta ce "Da gaske ka sakeni Modibbo" ya buɗe ido sai kuma ya matse kafaɗarta like "Oh!" Ya tsare ta da idanu, yana son yaga reaction ɗinta ya kuma gani ɗin. Domin gabaɗaya Jikinta ne ya fara rawa hawayen fuskarta ya ƙaro tana neman lalata make-up ɗin wacce tayi masa kyau a idanunsa, but he didn't know tayaya zai ce yaji daɗin kwalliyar ya kuma yaba. Jikinta ya yi sanyi tai ƙasa da kanta tana shassheƙar kuka, yaja baya kaɗan yana zama saman kujera fuska kame ba can ba ya ce. "Ibrahimul-khalil i want to be alone" Khalil ya ce "You want to be alone, or want to be your wife?" Umar-khan ya yi murmushi, yana da matuƙar girmama shekarun mutum, magana indai ta manya ce baya shiga, hakan yasa ya shafa kansa yana mai juyawa.. "Umar-khan ji mana" Khalil ya kira shi yana cewa "Ina zaka? Let's celebrate together Princess jeki zauna close to your husband" Ta tattara Alkyabbar jikinta kanta a ƙasa ta ƙarasa kujerar da yake zaune akai, gently ta zauna kanta daidai kafaɗar shi, babu wanda Yaa Sheikh ya kalla a cikinsu, turaren dake tashi jikin Halisa shi ne babban abinda ya sanya shi cikin wani hali Ya kame tare da riƙe kansa, Khalil ya ce "Drop your head" ta kalle shi a kunya ce ya ce "Ina nufin ki saka kanki a shoulder ɗin shi" Ta juya tare da kallon Abbanta taga ba ita yake kallo ba, gently ta ɗora kan nata, tare da rufe Idanunta ta ɗora hannunta saman nashi, al'amarin dake fin ƙarfinsa ya sanya ya buɗe narkakkun idanunsa ya sauke a kanta yana ɗan ranƙwafa kaɗan daidai lokacin photographers ɗin suka shiga sauke musu pictures kala-kala. Duk irin abinda sukai Yaa Sheikh bai motsa ba, ya sarautar fulanin tashi ta motsa, Halisa ake bawa styles wanda ake ɗaukan photon da shi.. El-bashir ya nufi wajan yana zuwa ya rungome Yaa Sheikh ɗaya gefen kuka ya riƙe Halisa ya ce "One picture please" Akai musu picture, daidai kunnen Yaa Sheikh El ya ce "Abba Tell your wife ta daina fushi da yayanta, ta ƙulla ce ni ni kuma ina son sister ɗita" Sai a lokacin Yaa Sheikh ya yi murmushi yana girgiza kai ya ce "Come Mubasshir" El ya durƙosa gaban Yaa Sheikh, a taushashe ya ce "Kayi rigima, amma ta ƙanwarka yawa gareta kada ka damu" Halisa ta kwaɓe fuska tana marairaice fuska tare da watsawa El wani kallo ya ce "Abba hararata take fa" Yaa Lee ya juya suna haɗa idanu da Halisa ta tura masa baki ya ɗauke kai kawai. Ɗaya bayan ɗaya suka fice daga cikin ɗakin, ya rage daga Halisa sai Yaa Sheikh, ta lura zanan fulawar hannunta yake kallo da kuma jan henna ɗin da Sss henna tayi mata, ta fahimci ya yi masa kyau amma bai san me zai ce ba. "Ya yi kyau ne Modibbo?" Ya lumshe idanu ya buɗe yana ƙara kallon hannunta kafin ya kama ya riƙe cikin nasa, a nutse kuma ya kai hannun bakinsa ya sumbata ya saka yatsun a baki bisa sunna ya tsotsa ya ce "Allhamdulillah" shi ne kawai abinda ya a furta, yana riƙe kan shi. Ya miƙe tsaye yana cewa "Meye kike kallona haka?" Tai ƙasa da kanta nauyin Abban nata ya kamata ta ce "Babu" da hannu ya nuna mata ƙofa ya ce "Go" Bata ji daɗi ba, ta juya cikin sanyin jiki zata fita taji ya rungometa baki ɗaya, numfashinsa na sauka a wuyanta ya hanata juyawa baya buƙatar da kalli cikin idanunsa sun juma a haka cikin muryar da bata san yana da ita ba ya ce "For the make-up" Ya yi kissing wuyanta ya ce "Jazakallah-bil khair Allah ya yi miki Albarka" yana faɗin haka ya juya mata baya, tayi sauri zata sha gabansa da sauri shi ma ya shige bedroom yana murza key tare da ɗaga shaddar jikinsa yana mai ɓoye abinda baya son ta gani. Tayi tsaye tana mamakin abinda yake ɓoyewa ganin bata fahimta yasa ta fita jiki a sanyaye. Tana fita Ummul ta kamata, Halisa ta ce ita sallah zatai yin duniya aka juya tace itafa magriba tayi dole aka rabu da ita, bayan ta idar mai make-up ta ƙara yi mata wata, ta shiryata cikin wani farin lace mai kyau da tsada wannan karan ma hadda Alkyabba. Zahrah na zaune a bayan mota, aci uwar kwalliya ana yauƙi, Surry na zaune kusa da ita, tai kwalliya itama, hannunta riƙe da waya tana duba, kamar daga sama tana shiga I.G taci karo da posting ɗin B.B.C ya buɗe ido da kyau Yaa Sheikh ta gani zaune a kujera sai Halisa dake gefenta ta marairaice fuska shi kuma yana kallon yadda take rigima su duka gabaɗaya sun sha Alkyabba sunyi wani irin kyau wanda baki bai isa ya faɗa ba. Under the posting ɗin aka ce _“Bayan samun jita-jita akan auren Babban malamin nan da matar da bamu sani ba, yau gani ya kori ji, Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu ya auri ƴar gidan Sarkin Sokoto Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki, yayinda suke walimar zama hafiza da tayi a makarantar Ibadur-rahman, Allah ya sanya albarka”_ Zufa ta yankowa Surry kamar ita ce Zahrah ta ce "Zahrah anya baki ɗebo ruwan dafa kanki ba?" Zahrah ta ce "Kamarya?" Ta miƙa mata wayar, Zahrah ta dinga kallon picture ɗin zuciyarta na bugawa sai ta ce "They're lie, ƙarya ne" Surry ta ce "BBC basa posting ba tare da sun tabbatar ba fa, amma bari na duba Twitter ai Prince Khalil nayi" tana shiga Twitter tai searching. Prince Khalil Ahmad Sarki. Sai ga profile ɗinsa ya bayyana tana shiga taga anyi tweet 20 minutes ago, a nan taga pictures kamar hauka na Yaa Sheikh da Halisa. Ya rubuta “Finally, the day, the most most couple's in the world, Mrs....and Mr Congratulations My sister Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki with her handsome husband Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu” A fili Surry ta ce "Tab, ina ruwan saki na dafe" Zahrah ta kasa magana kishi ya mamaye mata zuciya, Surry ko a ƙafarta ta koma ta dinga karanta Retweet na mutane, harda masu cewa Ai Halisa tayi masa ƙarama. Ana haka taga Tweet ɗin El-bashir ya faɗo just now. Photon Halisa da Yaa Sheikh ne ya rubuta. “HML Abba and his wife Princess” El-bashir bai fiya son hayaniya ba, ko a sunansa na profile haka ya saka Ahmad Sarki El. So babu mai gane cewa El-bashir ne da yawa sun ɗauka Mai martaba ne da kan shi. Kuma shi kaf Social media twitter kawai yake. Ana haka El ya ƙara yin twitter rubutu ne a taƙaice ya ce. _“Got Marriage_” Lokacin da suka isa event ɗin ya cika manyan mutane masu yawa kala-kala gasu nan, aka fara walima Halisa na zaune sai fara'a take tana ɗagawa mutane hannu, har zuwa lokacin bata san matsayinta a wajan Yaa Sheikh ba, Zahrah fuska haɗe aka shiga bawa Halisa gift wasu har Zahrah suke bawa sunce itama ta cancanta. Yaa Sheikh yaƙi fitowa yana kwance bedroom yana fama da kanshi. 9 daidai aka tashi Ummul wani diamond ring ta bawa Halisa as a gift, tunda aka fara walimar bata ga Mother dasu Yaya Halima ba da sauransu taga dai Dada sai Fulani Atine da Fulani Balaraba. Ƴan uwan Zahrah duk suna nan. Daga Zahrah har Halisa Ummul ta ce su zauna nan, daga ƙarshe aka ɗauke Halisa aka shiryata cikin lafaya white mai taushi, tai kyau sosai maimakon su tafi gida sai taji mutane sun shigo suna rangaɗa buɗa ta ce "Ummul wai mene naji haka?" Ummul ta ce "Yau ƴar rainon Abba zata tafi gidan Abbanta a fara zaman ibada" Wani tsalle tayi ta rungume Ummul ta ce "Wayyo Allah daɗi, I love you Abbana, Ummul kema ina sonki sosai da kika bani Modibbo" Ummul tai murmushi gabaɗaya bata ɗauketa matsayin mother-in-law ba, kallon uwa take mata hakan ya yi wa Ummul daɗin. Ummul na tsaye wayarta ta fara ringing ganin mai kiran yasa ta ɗaga tana cewa "Ya akai Arɗo?" Cikin gajiyawa ya ce "Ban son fitina, hayaniya ki bari by 11 zan tafi dasu" yana faɗin ya kashe wayar Ummul ta fita ta sanarwar da Hajja, Jadda ta dinga bala'i da ƙyar Yaa Sheikh yaga daidai tunda albarkar mutane ce baya so. Ummul ta dinga yi wa Zahrah faɗa ba tare da tuna laifin da Zahrah tai mata ba, Zahrah tai luff ta zama mage mai kwanciyar ɗaukan rai, kamar ruwa ya cinyeta ta ce "Na gode Ummul, Ni Halisa is like a sister to me daga ɓangarena babu wata matsala Wallahi na miki al'ƙawari" ta ce "Thank you kije yana jira" Mimi daman ta amshi Muhammad Surry kuma ta koma gidan Abba Hakimi, tana fita harabar gidan ta samu Halisa tsaye na buɗe murfin mota, Yaa Sheikh na zaune a gaba fuska haɗe idanunsa akan gate ɗin da aka buɗe, Halisa ta buɗe gidan gaba ta zauna Zahrah taji haushi sosai sai tayi kamar bai dameta ba ta ce "Am sorry sweetheart na barka jira" da sauri Halisa ta ɗago kanta ta kalli Zahrah, domin har yanzu an kasa samun wanda zai sanar mata cewa a yau bayan an tashi daga sauka aka ɗaura auren Zahrah Farouk da Yaa Sheikh, ta ce "Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Oh ashe kece lafiya mana, gidan mijina zani" wani irin kallon kin zama mahaukaciya taiwa Zahrah ta ce "Gidan miji? Wanne miji?" Zahrah tayi murmushi ta ce "Sorry mijinmu, ko ba'a faɗa miki yau aka ɗaura mana aure da Yaa Sheikh my sweetheart ba?" Halisa ta juya ta kalli Yaa Sheikh taga sam basu yake kallo ba, bai ma nuna alamar yaji me suke cewa ba, ta ce "Abba da gaske aure kayi?" Ya juya ya kalleta da kyau kamar ba zai magana ba ya ce "Zan tafi" Zahrah ta gane da ita yake,ta buɗe bayan mota ta shiga, hawaye tuni ya wanke fuskar Halisa ta dinga kallon Yaa Sheikh sai kawai ta buɗe ƙofa ta fita, ganin haka ya buɗe shima ya fito bata shiga gidansu Ummul ba ta nufi gate zata fita, ya yi saurin riƙeta yana cewa. "Ƴar fillo" a hankali taƙi sauraran shi, ta fara ƙoƙarin ƙwace kanta zuwa lokacin ji tayi numfashinta na tsayawa ta jawota ya rungometa tsam a ƙirjinsa ta kasa kuka, sai haɗiyar zuciya Jikinta ya saki, ya durƙosa ya ɗauketa bakiɗaya zuwa mota, ya zauna kana ya zaunar da ita a cinyarsa ya mance da batun Zahrah na motar ya dinga bubbuga kumatunta, ta buɗe ido ta ce "Baka so na, baka so na Abba, aure kayi ka auri Anty Zahrah? Ba zan iya ba zuciyata zata buga, wallahi gwara ka sakeni da gaske akan naga ranar da mijina zai kwanta da wata, mutuwa zan yi idan naga wannan ranar ina son ka Modibbo don Allah kace ba kishiya kayi mini ba" ta ƙare maganar wani gigitaccen kuka na ƙwace mata, Yaa Sheikh was speechless ya kasa cewa komai ya rungometa tsam a ƙirjinsa ya shiga sakar mata kisses masu zafi ta ko'ina, the only thing da zai iya ya kashe bakinta nata shi ne samar mata da nutsuwa idanunsa rufe ya saka hannu ya farka rigar Jikinta ta rabe biyu a hankali ya danna kujerar da yake kai while kissing her ya kwantar da kujerar yana ƙoƙarin zame vest ɗin Jikinta yaji ance "Ka danne mini ƙafata.... 08119237616*_Nimcyluv Writer's Queen 68 _* IDAN BA KE Paid book ₦500 08119237616 Zahrah ta faɗa muryarta na ɗan rawa kamar zatai kuka, Yaa Sheikh ya dafe kansa yana rufe idanu cikin ranshi ya ce "Asstagafirullah Yaa Allah" domin gabaɗaya ya manta Zahrah na bayan motar, ya zame Halisa daga jikinsa tare da duba yadda ya yaga mata riga sai duk kunyar Zahrah ta kama shi domin kamar cin fuska ne, ya ɗan buɗe ido irin Kinga abinda ki ka ja ko? A zahiri kuma ya kame fuska yana riƙe kan shi, yadda Halisa ke jin rikici da rigima yasa sam bai tankata ba, sai kuka take mara sauti. Tana nan jikinsa yana ƙare shigar da ita jikinsa da hannuna ya yiwa motar key tare da nufar gate, wanda tuni gatekeeper ya buɗe masa, ya cilla motar kan titi kai tsaye ya nufi unguwar da haɗaɗɗan gidansa yake. Cikin nutsuwa da ƙwarewa haɗi da tsantsar kamala Yaa Sheikh yake driving motar idanunsa akan titi, yadda hawayenta ke jiƙa masa shaddar jikinsa da ƙirjinsa yasa time to time kawai yake girgiza kai tare da fesar da Iska. He don't know how sad she's, bai kyauta ba, bai kyauta ba, ko wacce nada burin tasan halin da mijinta ke ciki, tana son ta zama guda ɗaya tilo daga ita sai yaranta wajan mijinta, ya sani ya yi kuskure irin babba ɗin nan, Ita ɗin yarinya ce amma a karo na farko ya rasa kalmomin da zai mata bayani dan gane da kishiyar da akai mata rana tsaka. Zahrah tunda tayi ƙasa da kanta bata ɗago ba, sbd abinda ya zo ya tsaya mata a maƙoshi yaƙi tafiya, ƙirjinta ya yi nauyi, suna mota ɗaya ace har Yaa Sheikh ya mance da ita? Ko da ba matarsa bace ita, yana da kyau ya yi mata kara ya daina nuna maitar buƙatar matarsa akan Idanunta me hakan ke nufi? Wata zuciyar ta ce "Alfarma akai miki Zahrah, kada ki zaƙe" ta girgiza kai ɗayar zuciyar ta ce mata "To Amma yanzu ai ke ɗin matarsa ce, kina da hakƙi akan shi ba zaki iya zuba idanu ba, dole ki tashi tsaye" Baya san sun ƙarasu gidan ba, sai taji ya yi parking a parking lot na gidan shi, tare da danna horn Sannan ta dawo daga hayyacinta. Ta buɗe idanu tana kallon mazaunin da yake kai riƙe da Matar Malam, ta buɗe ƙofa tare da fitowa tazo daidai Glasses ɗin tare da yin knocking, slowly ya sauke Glasses ɗin motar, ganinsa tayi jingine da kujerar motar ya ɗan lumshe idanunsa kamar mai jin barci. Ya ware idanun tare da zuba mata su kaɗan alamar "Ya akai?" Ta ce "Am looking for my sister, naga kamar tayi barci ma" Ya jinjina mata kai, nauyinta ya kama shi sbd Halisa dake kwance a ƙirjinsa, ji ya yi tayi shiru hakan yasa ya kalleta, hannunsa dake cikin rigar Halisa take bi da kallo, ya kame fuska yana janye hannunsa daga ƙirjin na Halisa. Tayi murmushi mai ciwo ta ce "Is she okay?" Ya dai yi mata shiru yana kallon yadda haske ya ƙawata harabar gidan nasa tamkar rana, ji ya yi tana kiran sunan Halisa tare da ɗan bubbuga hannunta. "Wake up Sister, we're at home" "Kije, zan tashe ta" Ya faɗa not looking at her, tayi kamar bai dameta ba ta ce "Ok Sweetheart, catch your life" tana faɗin haka ta nufi ƙofar da zata kaita asalin cikin gidan wanda yake ɗauke da Main parlour. Halisa daman akwai gajiya tare da ita, ga zafin da zuciyarta ke mata, ga kewar mijinta da gangar Jikinta take, suna fara tafiya kuma Yaa Sheikh ya fara hura mata iska a fuska da kunne, tare da zura hannunsa cikin rigarta yana shafa cikinta wanda yake jinsa har zuciyarsa, daga nan kuma ya haura da hannun dama wannan dalilin yasa tun kafin su yi nisa barci ya ɗauketa. Ya zareta daga jikinsa yana kallon yadda ta ɓata fuska ko a cikin barci, ya faɗaɗa fuskarsa yana ƙara jinjinawa rigimarta, fitowa ya yi da ita a jininsa bayan ya rufe ƙofar ya nufi cikin gidan, suna zuwa bakin ƙofar parlour Halisa ta ce "Sauke ni" daman ba barci take ba she was pretend kamar barci take ko mene, bai ja batun da tsayi ba ya sauketa, ta ce "Ina ne part ɗina?" Tayi maganar ko inda Yaa Sheikh bata kalla ba, sbd raɗaɗi da baƙin da zuciyarta ke mata, yau ita zatai sharing mijinta da wata banza? wacce bata da tabbacin ko lafiya lou take bata da H.I.V ba. Da hannu ya nuna mata part ɗin dake dama, wanda ƙofar take a rufe, ta juya ta nufi wajan taji ya kaɗa mata key a hankali ya ce "The key" Ba yabo ba fallasa ta amshi key ɗin ta buɗe ƙofar part ɗin, tana shiga ta murza mata key tare da zubewa a baƙin ƙofar tana sakin wani irin kuka mai cin rai. Zahrah tayi wani irin murmushi tare da takawa cike da gwalli ta ƙarasu wajan Yaa Sheikh ta ce "Lafiya lou take kowa?" Tayi maganar tana ƙoƙarin rungome shi da tafiyarsa ta ƙasaita ya matsa yana haurawa saman bene ya ce "Laá adari" ta bisa da idanu ta ce "Ka duba ta mana, bana son damuwa" ya tsaya cak yana kallon Zahrah daga upstairs ɗin bai magana ba, sai jinjina mata kai kawai da ya yi. Ta dubi haɗaɗɗan parlourn wanda gabaɗaya Yaa Sheikh shine ya zuba komai dake parlourn, milk and Brown colours ta buɗe part ɗinta ta shiga, parlour ta fara cin karo da shi, shi ma ya haɗu sosai daga nan kuma sai bedroom , bathroom da kitchen duk akwai a part ɗin kowa, sharp-sharp tayi wanka ta shirya cikin wata nightgown, a hankali ta dubi ƙirjinta koda ta haifi Muhammad ƙirjin bai yi cikar da ake tunani ba, shi yasa batai wasting time na shayar da shi ba, sunan tana shan magani amma har yanzu bata sauya zani ba, ta ɗauki wata bra mai tudu ta saka ƙirjin ya tashi kaɗan ta fesa perfume ta saka slippers tare da fitowa ta haura upstairs part ɗin Yaa Sheikh. Tayi tsaye bakin ƙofar tana riƙe handle ita burinta yau bai shige ta kwanta da Yaa Sheikh, har mafarkin wannan rana take ranar yau kuma ta kasance ranarta domin ita ce amarya. Ta murɗa handle ɗin tare da shiga, wani ƙamshin ya ratsa hancinta ta rufe idanu a hankali ta ce "My sweetheart ɗan gayu I love you Beb" baya parlourn dan haka ta shige cikin bedroom ɗin da taga ƙofar a buɗe, kai tsaye ba tare da sallama ba ta shiga yana zaune saman doguwar kujerar dake kusa da bed ɗin shi, ya ɗora ƙafarsa saman table hannunsa riƙe da gorar ruwa yana tsiyayawa cikin glasses, jikinsa na zubar da ruwa alamar bai jima da fitowa daga shower ba. Ta dinga binsa da kallo, domin wannan shi ne lokaci na farko data ganshi sanye da wata milk armless mai buɗaɗɗen ƙirji, sumar ƙirjinsa luf ɗauke da danshi ruwa, haka gemunsa, ta kalli farar dogwayen ƙafarsa har zuwa cinyarsa, ko'ina na jikinsa kwance da gargasa, shekaruna suka ɓoye sai samartakar shi data bayyana, nutsuwa da kamewar shi a fili. "Ba a shigo mini ba sallama" ta dawo daga kallon maitar da take masa ta ce "Oh My bad, I screwed up" Ya yi mata uzurin domin babu mamaki bata saba ba, ko wanne tsuntsu kukan gidansu yake, wani abun baya blaming nata, a haka a reneta. Bai ce mata komai ba harta nemi waje kusa da shi ta zauna tana cewa "Thank you" Ya ɗaga kai ya kalleta alamar ƙarin bayani ta ce "Yau zan kwana tare dakai, mafarkina zai zama gaskiya, naji daɗi yau Halisa zata bar min kai, we'll spend the night together zamu raya First night ɗinmu" ita kaɗai take magana bai ce komai ba, ta zame ta ɗora kanta a ƙirjinsa ta rungome shi ta ce. "I love You to the rest of my life.....," "Tea" ya katse da faɗin haka, ta ce "Tea kuma?" Ya jinjina kai ya ce "Ban son suger sosai, ki saka honey" gabanta ya faɗi ita kam ai batai zaton haka ba, she don't know how to make tea, ita kunna gas na bata wani iya sosai ba ta ce "Sweetheart tea yanzu? Why not safiya" ya duba time yaga kusan 11 na dare ya zareta daga jikinsa yana miƙewa tsaye ya ce "Good night" Da mamaki ta ce "Night? But I want to sleep on your arms Beb" ya kama hannunta har zuwa baƙin ƙofa murya can ƙasa ya ce "We'll talk tomorrow In sha Allah" hawaye ya cika a Idanunta gashi ta shanye maganin da aka haɗa mata tass ta shirya amsar mijinta da hannu bibbiyu, a sanyaye ta ce "Ban taɓa ganin aure haka ba, at least mu kwana tare koda babu komai tsakani, daman nasan alfarma kayi mini ba so na kake ba, ka tasauyawa halin da nake ciki da bana son ka ba zan nace ka aureni ba" ta saki kukan makircin tana riƙe ƙirjinta ta soma tari tayi kamar ciwonta zai ta shi. "Stop Zahrah" Ta tsaya tana kallonsa ya harɗe hannayensa a ƙirji yana binta da kallo da kayan data saka, bashi da wani feelings ko kaɗan a kanta, amma ya san hakƙinta ne kuma dole Allah zai tambaye shi. Kamar an tilasta masa ya yi magana ya ƙasa da murya ya ce "Me ki ke so?" Da sauri ta ce "You" Ya rufe ido ya buɗe in a romantic style ya ce "Gani" kambala'i yana nufin bai fahimta ba? Ko yaya ne? Wasu hawayen ya taro cikin Idanunta tayi murmushi ta ce "Good night" Zata juya ya kama hannunta sbd shi har ranshi tausayinta yake ji, musamman idan ya tuna watanni biyar suka rage mata a duniya sbd ciwon Cancer babba abune da yake kisa cikin lokaci ƙanƙani, ya ɗan rungometa ta gefe murya ƙasa ya ce "Am not in the mood" kamar jira take ta rungome shi sosai tana sakin kuka wanda duk rabi na kissa ne, ta fahimci hankalinsa baya tare da ita, kamar yadda ta sani haka ne domin gabaɗaya tunaninsa yana ga Matar Malam da kuma halin da take ciki, yana son zuwa ya kwantar da rikicin ta tun kafin safiya tayi ta rikice masa ya kasa fahimta.. "Don Allah sweetheart yau ɗaya, yau kawai ka barni na kwanta tare da kai don..." Sai ta fara tari tana riƙe ƙirjinta tare da ɗauke numfashinta. Yaa Sheikh ya riƙeta tare da janta gefen gado ya kwantar ya ce "Clam down, it's okay" ta jinjina kai tana kallonsa ya ja mata duvet yana miƙewa ta ce "Ina zaka?" Ya nuna mata ƙofa alamar rufewa zai, ƙofar yaje ya rufe, abu biyu sukai haɗe masa, idan bai sha tea ba sam baya jin daɗin, ga tunaninsa yana ga matarsa da cikinsa dake Jikinta. Zahrah kallon sumar kansa kawai take yadda ta kwanta har wuya, gashi ta rabo gida biyu, six packs ɗinsa a murɗe full options. A jikinsa yaji kallonsa take kuma shi ɗin take jira, ya kashe hasken bedroom ɗin ya dawo ya zauna bakin gado yana jingina da frame, yana kwanciya ta dawo kusa da shi tare da ɗora kanta a ƙirjinsa ta ce "Ina son ƙare rayuwata dakai, amma na kusa barin duniyar nan ko yanzu na mutu don Allah kada ka bawa kowa Muhammad ka riƙe shi na bar maka har abada, burina yanzu bai huce na samu farin ciki tare dakai na tsayin lokacin da suka rage mini a duniya" ya saka hannu ya rufe bakin tare da faɗin "Shhhha" Yana zaune har barci ya ɗauketa tana shafa lips ɗinsa da take jin kamar tayi kissing amma ya kame fuska babu dama, gently ya zame jikinsa daga nata tare da miƙewa ya buɗe wani bedroom, haɗaɗɗene sosai a ciki kuma harda bene wanda zai mayar dakai downstairs. A nutse yake taka strais ɗin har ya sauka, ya nufi wata ƙofa tare da saka key ya buɗe, shiru bedroom ɗin sai ƙarar karatun Alkur'ani dake tashi da kuma sanyin a.cn dake ratsa ko'ina, ya duba saman bed ya ga bata kai, harya juya zuwa bathroom ya hangota kwance saman prayer mat ta cure waje guda, ya durƙosa ya saka hannu tare da ɗaukanta bakiɗaya ya cire hijabin har lokacin kayan da tazo dasu ne a Jikinta ko wanka ba tayi, Jikinta zafi zau alamar zazzaɓi ne ke damunta, ya zauna da ita a jininsa ya shiga ƙarasa zame raguwar kayan ya rage daga bra sai under wear a Jikinta, sai kuma cikinta daya fara girma tare da nuna kansa a fili, ya saka hannu ya shafa cikin yana ƙara shigar da ita jikinsa da kyau, idanunsa rufe da suka fara rikicewa ƙamshin turaren Jikinta na rikita shi ga wani laushi da tsantsi da fatar jikin nata ta ƙara, Ɗumin da Halisa daji na shigar ta ya sanya ta ƙara shigewa jikinsa ta luff tana narke fuska cikin magagin barci ta ce "Zan mutu Abbana, ka gujeni ka zaɓi wata, You left me" Ya ɗora fuskarsa a tata yana goga mata tsinin hancinsa a hankali ya yi kissing lips ɗinta with all his heart ya ce "Bbyn Abba, Zawja rigima" Kamar tana jinsa ta tura baki tana ƙara shige masa da kyau, hakan ya ƙara rikita Yaa Sheikh ya kame bakinta ya shiga kissing cikin zafin nawa da kewa, tayi saurin buɗe ido sbd juyawar da abin cikinta ya yi ya daki mararta nan da nan fitsari ya taso mata, kallonsa kawai tayi tare da zare Jikinta ta nufi bathroom, tunda ta shiga bata fito ba har barci ya fara ɗaukan shi. Da Subhi Zahrah ta farka ta shafa taji babu Yaa Sheikh, ƙirjinta ya harba ta miƙe da sauri tana tashi taga ya buɗe ƙofa ya shigo jikinsa kayan jiya ne, amma kamar wanka ya yi gabaɗaya sumar kansa ta kwanta tana zubar da ruwa, bai bari ta kalli cikin idanunsa ba ya shige bathroom ɗin shi, Alwala ya ɗaura tunda ya riga da ya yi wankan da bai niyya ba, ya fito ya ganta tsaye bai ce komai ba, ya shirya cikin ash ɗin Jallabiya mai kyau ya nufi masjid, Zahrah ta koma tare da kwanciya ta ci-gaba da barci. Da ƙyar Halisa tayi sallah sbd ciwon da Jikinta yake, da gajiyar da Abbanta ya tara mata, sai jiya ta ƙara tabbatarwa Yaa Sheikh namiji ne bai nuni tausayi ko ɗaya a gareta ba, sai daya fanshe gabaɗaya kewar daya ɗauka, duka abinda ya tara a jikinsa sai daya juye mata shi, da ƙyar ta samu kanta, ta miƙe da ga kan prayer mat ta nufi kitchen ta kunna gas ta shiga haɗa tea ta yanka albasa da Attahiru, bayan ta kammala dafa tea ɗin da yaji kayan ƙamshi domin komai an zuba mata a kitchen musamman kayan ƙamshi, ta soya lafiyayyan ƙwai da yaji albasa. Ta juye tea ɗin a mug mai ɗan girma ta zuba soyayyan egg ɗin a plate mai faɗi. Kasancewar ya gaji kuma yunwa yake ji sosai yasa 6 daidai ya dawo gidan, mmki ya ƙara kama shi ganin Zahrah kwance ya nufeta yana bubbuga pillow ta buɗe ido ta ce "Sweetheart" a taƙaice ya ce "Kinyi sallah?" Ta ce "What's the time? 10 ya yi" ya buɗe baki ya ce "10? To tashi ki koma part naki idan yyi kiyi sallah" kafin tayi magana yaji ƙamshin Matar Malam ya kawo masa ziyara, yana daga tsaye ya juya suka haɗa idanu sai yaga ta sakar masa murmushi fararan haƙoranta a bayyane, Zahrah dake kan bed ta kalli Halisa batai tunani zata kula Yaa Sheikh a yanzu ba, Halisa ta ajjiye tray ɗin hannunta ta zuba ƙamshin turare daga ita sai wata riga ƙarama sai wando three gaiter cinyoyinta duk a waje ta ɗaure kanta da ribbon, tana zuwa ta rungome Yaa Sheikh tare da yin tsayin ƙafa shi kuma ya riƙe ƙugunta, ta sumbaci cheeks ɗinsa both sides, Idanunta cikin nasa ta ɗora bakinta a nasa tayi kissing ta ce "Sabahul khair حبيبة قلبي" Halisa ta juya ta kalli Zahrah da tayi tsaye ciki da mmkin makircin yarinyar ta ce "Ke bakisan yau rana ta bace?" Halisa marairaccen fuska ta ce "Sorry Anty Zahrah, Abbana yunwa yake ji ba zan iya barinsa haka" Ta saka hannu taja gemun Yaa Sheikh daya kasa cewa komai har lokacin hannunsa yana riƙe da ƙugunta ta ɗan bugi ƙirjinsa ta ce "Abbana shi ne da muna wanka ɗazo a bathroom na ka gudu ko? Bayan ko rama cizon da kayi mini a breast ɗina ban yi ba.....Gabaɗaya Idanun Zahrah ya rufe sbd tashin hankali, ta ƙara buɗe idanunta akan Yaa Sheikh da yaƙi yarda ya kalleta cikin damuwa taja tsaki tare da juyawa tabar ɗakin ko gabanta bata gani ta riƙe ƙirjinta dake mata zafi. Tana fita daga bedroom ɗin Halisa ta zame jikinta daga na Yaa Sheikh tana haɗe fuska tare da yin kicin-kicin da ranta kamar ba ita ta gama kissa da kisisina ba. Ganin zata juya ya riƙo hannunta yana dawo da ita cikin murya mai sanyi ya ce "Baki isa ba" "Kana jin yunwa, kuma aikina ne banda haka babu abinda zan zo nayi" ta faɗa tana ɗauke fuskarta dake tafin hannunsa, ya zame tare da zama saman kujera idanunsa lumshe sbd gabaɗaya ta gama kashe masa jiki garin kurar wata daga bedroom ɗin. Ganin da gaske barin ɗakin za tayi ya sanya Yaa Sheikh haɗe yatsun hannunsa suka bada sauti fuska kame ya ce "Don't leave Haliyserh Sheikh Aliyu haydar Aliyu" muryarsa babu wasa cikinta, ya kuma kame alamun umarni yake bata ba shawara yake nema ba. Ta dawo tare da zubewa a ƙasa wajan ƙafafuwansa ta saki wani irin raunataccen kuka, bai ce mata komai ba domin tana buƙatar kukan har zuciyarta tayi sanyi cikin kuka ta ce "Modibbo ya kake so nayi? Kasan yadda naji dana zo naga Anty Zahrah kwance a gadonka, sabon gadon da ko zama banyi akai ba amma har matarka ta kwanta kenan a jikinka ta kwanta tayi barci" Ya harɗe hannu a ƙirji tare da buɗe ido yana kallon yadda take rigima da rikici wanda zallar kishi ne ya haifar da su. Ta miƙe tsaye, tare da cire rigar Jikinta, ya rage sai bra a Jikinta, tana kuka sosai ta ƙara cire three gaiter ɗin Jikinta nan ma ya rage daga ita sai white lace pat. Tuni idanun Yaa Sheikh ya jirkice ya juye tare da yin ja, wani abu na fisgar shi bai taɓa ganinta zahiri a cikin haske ba sai yau. Duk inda yaso yake cilla idanunsa ya kalla a jikin nata, a ransa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake. Halisa ta juya ta ƙara juyawa ta ce "Ka faɗa mini wacce halitta ce a jigina bata cika ba har kaje ka auri raguwar wasu? Ka faɗa mini dame ta fini har ka aureta ba tare da sani na ba sbd bani da muhimmanci a wajanka, why Abba why me ya sa kasan zafi da raɗaɗin da nake ji a raina kasan yadda kishinki ke barazanar ɗauke rayuwata?" Bata duba cikin Jikinta ba ta durƙoshe a wajanta tana kuka sosai ta ƙara cewa "Ka mayar dani wajan Ummul ni ba zan zauna dakai ba, ba zan iya sharing mijina da wata ba" Ya wani irin kyakkyawan murmushi Yaa Sheikh ya yi wanda ya fidda fararan haƙoransa gently ya miƙe tsaye tare da ƙara sawa inda take ya ce. "Stand up" tayi shiru tana shassheƙar kuka, ya saka hannu ya ɗagota tsaye yana janta zuwa bakin gadon shi ya zauna, tare da zaunar da ita saman cinyarsa ta saka hannu zata ɗauki riga ta saka ya kame hannunsa bakinsa a kunnanta ya ce. "Kinyi kaɗan" ta ƙara ɓata fuska ta ce "Ka sakeni, ai baka marmarin jikina kana da wanda ya fishi, bani rigata" shi dai bai ce komai ba ya rungumeta ta baya yana shafa cikinta ta ce "Abba me ya sa" a taushashe ya ce "Ƙaddara Zawja, ban son rigima" ta juya ta kalle shi ta ce "Au rigima? Wannan abin ka ɗauka matsayin rigima Yaa Sheikh?" Ya dubi cikin idanunta ya numfasa ya ce "Ko wanne bawa yana da zanan ƙaddarar shi a bangon littafin shi wanda aka bashi na tsayin rayuwa...," Ya yi jim yana ɗora kanta a ƙirjinsa ya riƙe hannuwanta ya ce "Yarda da ƙaddara shi ne cikar imani, kinsan zan aureki?" Ta girgiza masa kai ta ce "Amma ina ganinka ai, a barci na" Ya yi murmushi mai kyau ya ce "To auren Zahrah a farko ƙaddara ce, haka yanzu ma, Ubangiji ya umarci mu da auren mata sama da ɗaya idan muna da hali da iko, ya ce idan ba zamuyi adalci ba mu auri ɗaya ita ce mafita a garemu, ki duba suratul Nisâ'i 3 ayat zuwa 4 Hafizata" Ta ce "Meyasa ka ɓoye mini? Meyasa kuma ka gudu ka barni? Meyasa kace ka divorce paper nawa through bashi bane?" Ganin yana ta kallonta ya kasa cewa komai ta ce "I understand,amma kasan ina sonka ko Yaa Sheikh?" Nan ma ya yi mata shiru, bisa dole tayi shiru tasan idan ya yi haka akwai dalili, inma yanayin da yake ji yafi ƙarfinsa,ko kuma abinda yake zuciyarsa yake son faɗa amma ya yi masa nauyi a harshe. Kamar daga sama taji ya ce "Ki bari na gwada miki banbanci a aikace, kin kurar mini mata kinzo kina rikici sunan Breakfast aka kawo, Ya Allah ka dubi bawanka Aliyu" ta tura baki gaba ta ce "to ina ruwana da matarka tazo ta zauna mana, ba wani kurarta da nayi gulma ce kawai" Ya haɗe fuska cikin nutsuwa da kulawa ya ce "Zawja ki tayani yin adalci, yanzu ku biyu ne kowa ni yake buƙata kina da muhimmanci a gareni ki yarda ƙaddara ce auren Zahrah, kin san idan kina haka tsakani da Allah ni zaki jefa a wuta ya zaki dinga tsirara kina ƙulla mini sharri" Ta kalle shi ganin da gaske kuma bai taɓa magana mai tsayin haka ba ta ce "Tom Malam" Yai mata shiru ta ce "Tea ɗin fa?" Ya miƙa mata hannu ta ɗauki cup ta tsiyaya masa ta saka 2spoon na honey kana ta bashi. Cikin nutsuwa yake sha har lokacin tana zaune akan ƙafafuwansa ta ce "Malam ina da tambaya" ya jinjina mata kai ta ce "Wannan zumar meye amfaninta?" Da idanu ya kalleta bai mata amsa ba, ta saka hannu ta fara cin soyayyan egg ɗin, harta manta da batun Zahrah domin ta samu Soyayyar mijinta, abu ɗaya ne ba zata iya jure ganinsu waje guda ba, ta ciro wani zata kai bakin ya kama hannun tare da turawa bakinsa yana ɗan yatsuna fuska, daga cin abinci Yaa Sheikh ya fara juye mata duk da yana iya ƙoƙarin shi wajan ganin bai shiga hakƙin Zahrah ba amma sai ya yi da gaske. Ta miƙe tare da ɗaukan kayan rigarta cikin sauri tabar bedroom ɗin tana masa gwalo ya bita da gajiyayyun Idanunsa. Ya jima a wajan kafin ya miƙe ya wanke bakinsa tas ya nufi bed ɗin shi ya kwanta yana lumshe idanunsa, kwana biyu yana stressed kansa da yawa jiya kuma da zai huta ya ƙarar da Lokacin shi wajan yin ibada da raya sunna ta Manzon Allah. Zahrah tana shiga ɗakinta ta shiga safa da marwa kanta ya ɗaure ta kira number Surry tana ɗagawa ta ce "Surry kina ina?" Ta ce "Gidan surukanki mana" ta ce "Ina son ganinki yanzu pls" Surry ta ce "Rite away Maa" hanging up na kirar sukai, bata tashi a wajan ba sai wajan 9 sbd ciwon da kanta yake mata sosai, tayi wanka tare da Alwala sai a lokacin tayi sallar Subhi kana ta shirya cikin fitted gown na atamfa Holand blue and white tayi mata kyau, duk abinda take bata jin daɗin ranta, gudun kada zuciyarta ya buga da abin da bata shirya gani ba ta nemi waje ta zauna tana chat a wayarta. 12:45 daidai ya shiga sakkowa daga upstairs ɗin sanye da Ash ɗin shadda shampoo sai ɗaukan idanu take ya ɗora hula jaddara hannunsa a baya nutsuwarsa ta bayyana shekarunsa a fili ya dinga bin main parlour ɗin da kallo jin shiru ba motsin kowa sai ƙamshin dake fitowa ba tare da yasan daga ina bane. Fita ya yi zuwa Masjid ɗin dake unguwar a lokacin kuma wata black ɗin mota ta shigo gidan, bai bi takan motar ba ya shige abinsa, Dr A'isha da Surry suka dinga kallon Yaa Sheikh har sai da Surry ta ce "Wannan kallon fa Dr" Dr A'isha ta ce "Na rasa wanne kyau Yaa Lee ke da shi, Ummul nada kyau haka grandparents nasa, but shi ɗin kamar ruwa biyu ne" Surry ta ce "Kin san Fulani nada kyau amma ko? Kuma ita kanta Ummul banji asali bahaushiya ce, ni nutsuwa da kwarjinin shi ke hanani nutsuwa idan yana waje" Dr A'isha ta rufe idanu tana sauke nauyin ta ce "let's go in" Fitowa suka yi tare da shiga ciki, gabaɗaya suka zauna a main parlour Surry ta ɗauki wayarta ta shiga kiran number Zahrah tana ɗagawa ta ce "Ina parlour" ta ajjiye wayar tana bin parlourn da kallo ko'ina birgeta yake, an narka dukiya wacce baki ba zai taɓa iya faɗa ba. Babu jimawa ta fito tana rangaji ganin Dr A'isha kuma yasa tayi turus sai kuma ta zauna tana faɗin "Wlcm" Surry ta ce "Sannu Amaryar Yaa Sheikh, na ɗauka yau ai ba zamu samu ganinki ba sbd soyayya" Zahrah ta ce "Uhm wacce soyayya nayi kwanan baƙin ciki" Surry ta ce "Subuhanallah, bar faɗa" ta ce "Bari kawai, can you imagine a gabana yarinyar nan ke rungome Yaa Sheikh tana faɗin wai ya cije ta ji nayi zuciyata ta buga ƙirjina ya fara zafi" Surry ta dinga dry tana riƙe ciki ta ce "What funny, bar raina Allura, ƙarfe ce wallahi" Kafin suyi magana Halisa ta fito hannunta riƙe da waya, ta kallesu sau ɗaya ta marairaice fuska ta ce "Habibi ƙalbi sai kace baƙi akai shiyasa ka tafi lambu, bari nazo musha lambun soyayya" ta cire wayar ta ɗora a baki tare da manna kiss ta ce "Mu'ah Uban ƴaƴana ga ƴar rainonka nan, ƴar filloka kuma matarka nan zuwa" ta kashe wayar shi dai Yaa Sheikh jinta kawai yake ya kasa fahimtar maganganun nata. Halisa tayi murnar ta ce "Ashe baƙi mukai har haka?" Surry ta ce "Uwar gida ykk?" Ta ce "Ni lafiya nake sai dai Antyna Zahrah kin san ita ce amarya ita ce on duty maybe tasha jiki, kin san Mijina or Surry ba rago bane ya san ta kan soyayya" Zahrah tayi murmushi ta ce "haka ne ƙanwata domin na tabbatar da ƙwarewar shi a jiya" Halisa ta miƙe tsaye tana gyara zaman duguwar rigar Jikinta ta buba farin lace lace da White ɗin flowers, rigar ta zauna mata sosai ga ƴar ƙaramar necklace ɗin wuyanta tayi kyau sosai ta ce "Point of correction Anty a gidan Yaa Sheikh dai nice babba kin san uwar gida, ki faɗa mishi ya mance gajeren wandon shi akan bed ɗin jiya bari naje" tana faɗin hakan tayi gaba Surry ta ce "Wannan yarinya zata iya kashe aure ji magana kamar ana karanta mata?" Zahrah ta ce "Idan kissa ce aini babarta ce a wajan, mu zuba mu gani" Halisa na fitowa wata haɗaɗɗiyar farar mota na shigowa sai ɗaukan idanu take, motar na shigowa wasu motoci guda biyu suka shigo ya zamana baƙin motocin huɗu ne a gidan harda tasu Surry. Halisa ta ƙarasa inda Yaa Sheikh tana murmushi ta ce "Yallaɓai" ya dubeta tare da murmushi wani mutum ya fito daga motar ya ce "The car key" ya amsa tare da jinjina kai alamar godiya, El-bashir da ya yi driving su Dada ya ce. "Abba sabuwar mota kayi ko ni ka siyawa? Wannan motar latest car ce bata jima da zuwa ba" Yaa Sheikh ya shafa gemunsa a taushashe cikin yanayi na riƙe kansa ya ce "Prince guda a siya masa mota?" El ya ce "Please mana Abba wlh nayi broke" Ya juya ya kalli Halisa da take da kallon motar ya kama hannunta tare da damƙa mata key ɗin daidai kunnenta ba tare dasu Dada da mother sun ji ba ya ce "For you Wife, Hadda Alkur'ani gift" Maimoon dake laɓe ta buga tsalle ta ce "Yaa Lee Anty Halisa ka siyawa mota" Ya jinjina kai Maimoon ta buga tsalle ta ce "Wow it's expensive" hawaye ya cika idanun Halisa ta kasa cewa komai, ta kalli motar ta kalli Abbanta ta kalli su Mother, Maimoon tai cikin gida tana kwallawa Dr A'isha kira da Zahrah akan su fito Yaa Sheikh ya siyawa Halisa mota, Halisa ta fashe da kuka ta faɗa jikinsa tana cewa "Thank you Habibi ƙalbi... Thank..." Ta kasa maganar sai kuka, Mother ta ce "Allah ya sa albarka" Dada murmushi kawai tayi tare da yin cikin gidan, El kuma kamar ya zauce sbd haɗuwar motar sai taɓawa yake, ganin ba kowa wajan yasa Yaa Sheikh yayi holding nata back tare da kissing hannunta ya damƙi hannunta ya ɗora daidai ƙirjinsa dake harbawa wajan saitin zuciyar shi a hankali ya yi mata raɗa ya ce "Na baki wannan" ya nuna zuciya ya ce "Virgin gift to my lovely wife, i have never thank you before, Jazakallah-bil khair I will never forget that day, ranar da ki kai mayar da tuzurun Ummul rangaɗeɗan ango.....Ta ɓoye fuskarta sbd kunya while hawaye da kuka na sake cin ƙarfinta, Ita kam a yanzu mene ya rage mata banda cikawa da imani da rabuwa da iyaye lafiya, duk wata Soyayyar miji ta samu. Ya saka hannu ya ɗago kanta data ɓoye a ƙirjin shi ya tsareta da fararen idanunsa masu sauya mata tunani cikin ƙasa da murya ya ce. "Ƴar fillo? Meye?" Ta sunkuyar da kanta ƙasa idan tace a yanzu bata jin nauyin Yaa Sheikh tayi ƙarya sbd kullum cikar zati da haibarsa ƙaruwa take ga wata tarin kamala da Ilhama na cikakken nutsatssen mutum mai tarin ilimin Addini. Muryarta na rawa ta ce "Thank you Abba, Allah ya saka da alheri ya ƙara arziƙi da wadata, ya baka halak a kullum ya rabaka da haramun cikin dukiyarka, Allah ya bamu zuri'a mai albarka masu kulawa damu kamar yadda ka kula da rayuwata" Tunda ta fara magana ya harɗe hannu a ƙirji ya zuba mata idanu, har ranshi yaji daɗin addu'arta ya kuma ya bawa tunaninta, wanda a zamanin yanzu ba ko wacce mace take tsayawa ta yiwa mijinta addu'a kamar haka ba, wasu babu haka ma a lissafin tunaninsu. Ya lumshe idanunsa yana shaƙar iskar dake tashi a wajan take tahowa da ƙamshin Jikinta, rufe idon ya bata damar ƙare masa kallo sosai, sai yanzu ta ƙara gasgatawa Yaa Sheikh ya fita kyau nesa ba kusa ba, shi ɗin cikakken Bafullatani ne, sbd gabaɗaya dangin mahaifinsa Fulanin Yola ne na Usuli kuma Makiyaya, Fari tas farin da kai tsaye ya shige na Fulani yafi kama dana _Half-caste_ ƙwayar idanunsa ba nrml ɓaka bace ba kuma za a ce mata Brown ba, ko ace Blue kamar ta turawa, sauyin ƙwayar idanunsa ya sanya kallon shi ya zama wani irin wanda yafi kama da romantic, He has a round face, da saje wanda ya kewaye and a long beard irin gemun nan mai tsayi na Manyan malamai, labɓansa jajir suke sbd yawan taune su da yake da kuma tea ɗin da yake sha ko liquid abu, hancinsa siriri kuma dugo, sumar kansa yalwataciyyace kamar wacce ya sanya mata dayin sbd rabuwa da tayi kala biyu daga tsakiya zuwa goshinsa tai baƙi sosai sai ƙyalli take, daga tsakiya zuwa wuya kuma tayi jaa yawancin jikinsa gargasa ce, ga ƙirjinsa mai faɗi kamar yana ɗaga ƙarfe kullum yana da tsayi sosai but his ears are big suna da faɗi. Ya saka hannu ya zungureta tayi saurin ɗauke kai tana sauke numfashi ya ce. "Kin wani tisani a gaba" Ta kwaɓe fuska ta ce "to me zan yi bayan ka cika zuciyata da farin ciki" Sai kuma ta ƙara sakin kuka hadda na shagwaɓa da zarar zai kalli Idanunta sai ta ɗauke kai ya kamota gabaɗaya tunda har lokacin El yana can yana duba motar Halisa, ya bata side hug tare da ɗora hannunsa a kafaɗarta ya ce "Dodo na zama?" Ta girgiza kai ta ce "Wallahi Abba haka kurum kunyarka nake ji" ya saka hannu ya dungure mata kai yana girgiza kansa a taushashe ya ce "Allahumma yaá hadiki Zawja" tayi dariya shi kuma ya ɗaga kiran Abba Hakimi tare da nufar mota ya juya ya ganta tsaye da hannu ya nuna mata ta koma cikin gida, ta ɗaga hannu tare dayi masa bye-bye Tana shiga El ya dawo wajan Yaa Sheikh domin bar musu wajan ya yi dama, Yaa Sheikh ya shiga mota yana bawa El car key kafin nan ya yi masa gargaɗi bai son driving na ganganci a haka suka fice daga cikin gidan. Zaune Halisa ta samu Dada da Mother a parlour suna hira, Dr A'isha na danna waya Zahrah na zaune Idanunta akan plasma Surry kuma tana kallon Halisa tana ƙara yaba kyan da Ubangiji ya yi mata, Halisa tayi murmushi ta ce "Sannu da zuwa Dada sannu da zuwa Mother" Mother ta ce "Bana so, sbd farin cikin an siya miki mota ai ko kulamu bakiyi ba" tayi dry tace "Kai Mother wake wasa da kyautar miji? Ba ko wacce mace zata sameta bafa sai wacce ta zama kamilalliyya ta kare kima da mutumcin ta har zuwa gidan miji ba dole na manta daku ba" Maimoon tayi caraf ta ce "Absolutely right Anty Halisa, wallahi irin motar ake yayi kin zama ƴar gaban goshin Yaa Sheikh congratulations Princess" Zahrah ta miƙe zata bar wajan Maimoon ta ƙara cewa "Laa Anty Zahrah ba kije Kinga motar ba" tayi murmushin yaƙe ta ce "Haba mu da muke gida ɗaya ai motar kamar tawa ce ko" Maimoon ta buɗe komai da komai har receipt ɗin ta ce "Kinga kowa iya sunan Princess ɗin sakoto na gani Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu" Halisa ta gyara zama tana ɗan ya tsuna fuska sbd ciwon da cikinta ke mata ta ce "Ke kam Maimoon idan da kara ai motar ta ce" Maimoon ta watsa hannunta sama ta ce "Oh yeahhh" Baƙin ciki ya cika zuciyar Zahrah duk ta inda ta ɓollo amma sai Halisa ta zame, kuma bata taɓa nuna baƙin ciki gabaɗaya ta rasa mafita, ta koma ta zauna gudun kada a gano ace baƙin ciki take. Surry ta ce "Congratulations" Halisa ta miƙe ta ce "Muna zo mana" Maimoon ta miƙe tare da bin bayan Halisa har zuwa haɗaɗɗan part ɗinta, lafiyayyan girkin da tayi ta haɗa a tray ta bawa Maimoon ta ce takai Main parlour, takai ta ƙara ɗaukan wasu ta koma ita kuma tayi Alwala tare da yin sallar Asar kana ta dawo parlourn. Ƙamshi ya dinga ratsa hancin Zahrah yawonta na tsinkewa rabonta da abinci tun jiya ko breakfast ba taci ba, Mother ta ce "Surrayerh kuzo kuci abinci" Zahrah ta girgiza kai ta ce "No thanks" Surry ta kasa jurewa ta ɗauki Spoon ta fara cin fried rice ɗin wacce taji hanta daɗi har ratsa kunnenta yake, Zahrah cikinta ya dinga ƙugi daga ƙarshe tabar wajan tana zuwa ta shiga kiran number Yaa Sheikh amma bai ɗauka ba, sai kawai ta fashe da kuka tana riƙe cikinta ga ciwon kai dake damunta. Bayan sun gama cin abincin Maimoon ta kwashe kayan tas taje ta wanke mata ta gyara kitchen ɗin, Mother taja Halisa har zuwa bedroom ta kalleta ta ce "Ina fata kin daina shirman nan naki" idanunta ya cika da hawaye ta ce "Har yanzu zuciyata zafi take idan na kalli Zahrah wai ita ce kishiyata, Shikenan taci galaba akai na kamar yadda tace zata dawo gashi ta dawo" Mother ta ce "Bata ci ba, amma idan kin bata dama tabbas zata ci, tana mugun son Yaa Sheikh, Yaa Sheikh na mutuwar son ki namiji kuma baya so da ƙaunar mita ko yawan complain a rayuwar shi, kiyi kishi a kansa ba laifi bane, amma kada ki zama mai biyewa matarsa kuna tada masa da hankali, kada ki nuna kishinsa akan idanun Zahrah kiyi kishin daga ke sai shi, ki kyautata masa ki zama mace mai yawan gdy, ki fahimci kuma abinda mijinki yake ƙauna daga gareki......," "Taya zan fahimci me Abbana yake so?" Mother ta haɗe fuska ta ce "How can I know bayan kece yake mijinki, kin gane me nake nufi ki zama mai kula da wajan da tsaftace shi yadda zaki dinga jan hankalinsa da su" Halisa tayi shiru tana tunani kafin ta ce "Kuma zai kwanta da ita? Shi ne abinda ba zan iya jurewa ba wallahi" Mother ta ce "Kada ki zama selfish, idan lokacin kwanaki yazo ta hanaki za kiji daɗi? Ke matarsa ce itama haka, gabaɗaya kuma da hakƙi a wajansa fifita ɗaya daga cikinku zai sanya Yaa Sheikh ya shiga fushin Allah ko kina so ya tashi da shanyewar ɓarin jiki?" Ta girgiza kai Mother ta ce "then support him wajan sauke hakƙin Zahrah domin tana buƙatar shi fiye dake ɗin nan, don Allah Halisa kada kiyi amfani da son da Yaa Sheikh yake miki kice zaki tilasta masa yin wani abun kinji" tayi murmushi mai ciwo sosai ta ce "Mother nasan me nake, ki daina ɗaukana matsayin shasha" taci gaba da yi mata faɗa da nasiha kana ta fara bata wasu bayanan na musamman da perpumes kala-kala. Dr A'isha dauriya take amma bata jin daɗi wanda tazo dominsa kuma ko inda take bai kalla ba gashi yaƙi dawowa cikin gidan, ta miƙe ba tare da sanin kowa ba tabar gidan. Yaa Sheikh yana daga cikin motar ya dinga kallon Hotel ɗin yana mai yin Asstagafirullah acikin ran shi, El ya buɗe masa bayan mota ya sakko da ƙafafuwansa da suke cikin Black Gustavo parent italian leather Tassel Loafers cikin nutsuwa yake tafiya mutane suna binsa da kallo cike da mmkin abinda ya kawo babban malamin cikin hotel ɗin Tahir place, wasu kuma na risinawa suna gaida shi, a haka yabi tabbataccen wajan da aka bashi, ya tsaya a bakin ƙofa El ya yi knocking, not long aka buɗe ana faɗin. "Ko wacce shegiyar ce yau koni ko ita....," Maganar ta tsaya dalilin ganin mutumin da bata taɓa tunanin zata gani ba a rayuwarta, ta murza idanu jiki na rawa ta koma ciki da sauri tare da faɗawa cikin toilet, Yaa Sheikh ya yi sallama bisa tsari na addinin Musulunci tare da saka kan shi cikin ɗakin, ya kalli Saif-wazir dake zaune hannunsa riƙe da kwalbar giya ga madarar sukudayen a ɗaya hannun idanunsa ya yi jajir, gashin kansa ya hargitse ya ɗago kai cikin maye ya ce "You? Sheikh Aliyu haydar Aliyu ko?" El-bashir zai magana Yaa Sheikh ya girgiza masa kai alamar a'a, Saif-wazir ya ce "Are you happy to see me cikin wannan halin? Na zama kamar mahaukaci ko?" Sai kuma ya girgiza kai ya ce "No! Ni ba mahaukaci bane ba zan taɓa zama mahaukaci ba, amma waye babana? Ni ne? A'a kai ne a'a wancan ne.?" Yaa Sheikh ya runtse idanunsa sosai a fili ya ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Asstagafirullah Allah na tuba" Saif-wazir ya yi dariya ya ce "You role my life kai ne ka lalata mini rayuwa ka sanya mahaifina ya kureni Well-done Aliyu" Cikin ɓacin rai Yaa Sheikh ya ɗaga hannu ya zabgawa Saif-wazir mari ya ƙara zabgawa Saif-wazir mari ya ce. "Ka cuci rayuwarka Saifuddeen ka ha'inci Abba Hakimi, ka lalata tarbiyyar daya baka, kai aka kora na fika jin baƙin ciki ban taɓa zama wajan Abba Hakimi da niyyar wani abu, ko dukiya ko dan na raba shi da yaran daya haifa ba..." Ya sauke numfashi idanun Yaa Sheikh har wani ruwa suke sbd ɓacin rai ya ƙara zabgawa Saif-wazir wani marin ya ce. "Na hango soyayyar ɗa da uba a idanun Abba Hakimi nasan baya iya barci sbd rashinka, iyaye na son yaran da suka haifa fiye da yadda yaran ke son kansu, suna son yaransu fiye da yadda suke son kansu, sai kai ɗaya zaka fita zaka a cikin zuri'a ka zama wanke ɗaya" yama kasa magana El duk ya tsorata bai taɓa ganin masifar Yaa Sheikh ba sai yau, daman duk wani Aliyu Masifaffe ne don a haka ma Yaa Sheikh yana riƙe kansa, bai fiya nuna kansa ba, sai dai ya yi ta sauke ajjiyar zuciya fuskarsa tayi jajir sbd masifa kuma babu halin yi. Saif-wazir ya ce "Ka fita ka bar mini ɗaki" Yaa Sheikh cije baki ya shiga danna waya ana ɗauka ya yi magana, kana ya ƙara kiran wata number nan ma ya yi magana ɗaya biyu ya kashe wayar. Yana tsaye a wajan ya kai ya kawo wasu polices suka shigo can kuma sai ga Shugaban ƴan hisba, ya kalli Police ya ce "Take him, ba arresting nasa ba zuwa dawanau" ya juya kan Wani ya ce "Jeka fito da yarinyar" ya nufi toilet ɗin yana turawa ta buɗe yarinyar ta fasa ihu tana faɗin "Don Allah ka rufa mini asiri Wallahi Allah a gida ba a san halina ba, islamiyya zani shi ne nazo nan, Wallahi ba zan sake ba don Allah don Annabi wallahi bana son a sani a gida" Yaa Sheikh don babu dokan mace a tsarin shi da sai ya yi mata doka tas, cikin huci ya ce "Kai ta zuwa Hisba ka binciko iyayenta ina son ganinsu" Da Saif-wazir da yarinyar gabaɗaya aka kame su, Yaa Sheikh ya yi waje tare da shiga mota El-bashir zai shiga ya miƙa masa hannu, jikin El na rawa ya bawa Yaa Sheikh key ɗin yana bashi ya figi motar da gudu yabar El-bashir tsaye a wajan. Daga Halisa har Zahrah an zuba wanka ana jiran dawowar Yaa Sheikh amma har akai sallar Issha bai shigo ba, Zahrah na kwance a ɗakinta Halisa kuma tana Main parlour ta kasa nutsuwa. Jikin tane ya bata kallonta ake ta ɗago kai yanayin yadda taga Yaa Sheikh ta tsorata Jikinta har rawa yake, ta miƙe tsaye ta ce "Sannu da zuwa" yaja waje ya zauna binta da idanu sai da ya gama kallon inda yake so kafin ya sauke numfashi ya ce "Kira Zahrah" tayi jim! Sai kuma cikin sanyin muryar ta ce "To" Ta nufi part ɗin Zahrah tana ƙofa ta tsaya tare da yin sallama, bata damu data amsa ba ta ce "Habibi ƙalbi yana kira" tana faɗin hakan ta juya, ta zame kansa a ƙasa ya riƙe kan da hannu ta tsuguna har ƙasa ta kama ƙafarsa ta cire takalmin, daidai lokacin Zahrah na fitowa ta tsaya tana kallon ikon Allah sai kuma ta nemi waje kusa da Yaa Sheikh ɗin ta zauna ta cewa "Wlcm Sweetheart" bai amsa ba, Halisa ta miƙe ta ajjiye takalmin a gefe ta kama hannun Yaa Sheikh bai mata musu ba ya miƙe ta zame masa Babbar rigar jikinsa tare da cire hiramin, ta kwasa ta haura upstairs ɗin shi. Zahrah ta ce "Ina ta magana shiru ko laifi nayi?" Ta faɗa tana ɗora kanta a kafaɗar shi, bai ce mata komai ba kuma bai hana ta rungume shi ɗin ba, ya ɗaga idanunsa jin ana tafiya suka haɗa idanu da Halisa tayi saurin ɗauke Idanunta sbd kukan data tsaya tayi,ta durƙosa ta tsiyaya masa ruwa mai sanyi a glass cup ta miƙa masa, ya amsa tayi mmkin yadda ya shanye ruwan tas duk da bayan son sanyi, ta ƙara zuba masa Zahrah ta ce "Ya zaki ta bashi ruwa?" Bata kulata ba ta miƙa masa ya kuma shanye ruwan, sai a lokacin ta nemi waje kusa da ƙafafuwanta ta zauna tana zuba ruwa a cup takai bakinta zata sha taji ya ƙwace, ta juya ta kallesa taga ba ita yake kallo ba, sai daya gama tunaninsa da jan ajinsa kafin ya ce. "Ku duka matana ne, Zahrah ke ce babba amma matsayin Matana Zawja ce gaba dake, kuji tsoran Allah ku duka ku zama matan sirri masu haɗuwa su faranta ran mijinsu, wallahi wallahi duk wacce naji ba daidai ba wajanta zan saɓa mata, ni ba mijin littafi bane da zan banbanta wata, ina son zama da ko wacce" ya yi shiru a hankali ya ce "Sai ku raba kwana" gaban Halisa ya faɗi jin batun raba kwana, Zahrah ta ce "2days 2days zaka fara dani tunda ni ce amarya idan kayi kwana biyu sai ka koma wajan Halisa kayi kwana biyu ko Uwar gida?" Halisa tayi murmushi ta ce "Eh" ya harɗe ƙafa ya ce "Allah ya yi muku albarka ku tashi kuje" Halisa kamar jira take ta miƙe tare da shigewa part ɗinta, ya bita da kallo ta gefen idani Zahrah jiki na rawa aka tafi tare da fara shirin tarbar ango Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu. 10:23 ya shiga sakkowa zuwa downstairs cikin wata farar riga Armless mai zif a gaba, ta kama damtsen shi sumar ƙirjinsa a bayyane, sai wando three gaiter shima fari ya tsaya iya cinyarsa ya nufi part ɗin Halisa da nufin yi mata good night hannunsa zube cikin aljihu, key yasa ya buɗe ya lumshe idanunsa sbd wani ƙamshin air-con daya daki hancinsa, ga tsayin A.cn hakan yasa suka haɗu tare da haifar masa da kasala, da ƙyar ya ƙarasa cikin bedroom ɗin ya sameta tsaye a gaban mirrow tana shafa humura a Jikinta ta saka nightgown mai lace ɗin wuya ta tsaya mata iya cinya cikinta ya bayyana sosai domin ya girma ƙirjinta ya cika sun bayyana ta saman wuyan rigar, kai tsaye kuma idanun Yaa Sheikh a ƙirjin ya sauka bai san me zai ce abu ɗaya ya sani idan da abinda yafi ƙauna ga mace bai shige breast ba, suna matuƙar ɗaukan hankalinsa sai yaji kamar da gayya Halisa ta saka rigar, ta amsa masa sallama ba yabo ba fallasa ya jingina domin har ranshi tsoran ƙara sawa ciki yake zai iya yin ɓarna riƙe kanshi kawai yake, kamar ƙaramin yaro ko wani matashin saurayi ya narke murya ya ce "Zanci abinci a sammin" sosai ya bata dariya sai ta haɗe rai ta ce "Abba ka manta wajan Zahrah zaka ita zata baka ai" ya yi ta kallonta da yadda take juya hips tana ƙara shafa humura a ƙirji tare da ɗago su sama, duk yadda ya kame kansa da yadda ya riƙe kanshi da kyau bai san lokacin daya tsinci kansa a gabanta ba, ya tsaya a bayanta tare da saka hannu a......https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL *Follow my Facebook account sbd muhimman abubuwa👆🏾* 👇🏾 follow my account on Arewabooks please https://arewabooks.com/u/nimcyluv Humurar hannunta ya ƙwace tare da kaiwa hancinsa ya shaƙa ya ajjiye da sauri yana rufe idanunsa cikin nutsuwa da yin ƙasa da murya ya ce "Baki da tausayi Zawja" ta haɗe fuska tamau ta juya zuwa parlour yana zaune bai bita ba, ta ƙara dawowa ta shige kitchen lokacin data dawo ya tankwashe ƙafarsa saman gadonta daya sha bedsheet, hannunta riƙe da tray ta tsuguna har ƙasa ta ajjiye murya ba shaƙe ta ce "Ga abincin nan" Ta faɗa tana neman waje gefe ɗaya ba kamar yadda ta saba zama so close to him ba. Ya ɗauki mintuna bai ce komai ba can ya numfasa yana shafa cikinsa domin da gaske yunwar yake ji, ya jima bai ci wani abu mai nauyi ba ya ce "sbd za a sammin abinci ake kame fuska?" Tayi saurin faɗin "Ranka a ɓace ka shigo ɗazo" ya ware fararen idanunsa masu haske da launi yana nuna ƙirjinsa da yatsar shi ya ce "Ni ɗin? Injiwa" Ta girgiza kai ta ce "Nafa gani, na gani a cikin ƙwayar idanunka Malam" Ya ƙura mata idanu shi gani yake kamar ba ƴar fillon shi ba, Zawja matar nan ta shi rigimammiya gabaɗaya sai yaga kamar an sauya masa ita, ya jinjina mata kai yana sakkowa ƙasan carpet ya ce "To, ba haka bane" bata ce komai ba, ta buɗe warmer tare da fito da tuwon samun mita fari tas ta buɗe shi daga cikin leda ta ɗora saman plate, ta ƙara saka masa wani sai da ta saka masa guda uku a plate sai tiriri suke sbd warmer ɗin mai riƙe zafi ce, ta ɗauki wani plate ta zuba masa miyar bushasshiyar kuɓewa wacce taji nama sosai, baya wani cin tuwo sosai amma yadda ƙamshin ke ratsa hancinsa yaji gabaɗaya son cin tuwon ya kama shi. Yana ta kallonta ganin ko inda yake bata gani ta matso da bowl da ruwa, gane nufinta yasa ya wanke hannunsa ciki. Tare dayin bisimillah ya saka yatsun shi huɗu ya gutsiri tuwon ya kai bakinsa, daɗi da ɗonɗanon ya ratsa kunnenshi, Halisa ta koma gefe hannunta riƙe da Hislul Muslim amma sam hankalinta baya kai. Lokaci zuwa lokaci yana juya ya kalleta baya magana idan yana cin abinci ƙa'ida amma yanzu kasa riƙe kansa ya yi cikin kamala ya ce "Haliyserh ce? Ko kowa zonan" ta juya da Idanunta da ya yi ja ta kalle shi ya girgiza kai tare da tsame hannunsa daga abincin ya wanke tas zai kwashe kwanokan ta ce. "Kaje kawai, zan kawai it's my responsibility" Ya dubeta da kyau ya ce "Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce: matanku gonakinku, abin alfaharinku, ababen ɗebe kewa da sanya su nishaɗi, ku taimaka musu, da aikin gida domin ƙara soyayya da wanzar da farin ciki" Ya sauke numfashi yana shafa sumar kansa wacce furfura ta fara fitowa kaɗan kaɗan cikin kamala da sanin ya kamata da tsantsar addinin daya gama ratsa shi ya ce Imam Zainul-abidin (a.s) ya yi nuni da kiyaye hakkin mata da fadinsa: “Kuma hakƙin mata shi ne ka san cewa Allah maɗaukaki ya sanya ta mazauni kuma wurin nutsuwa gare ka, kuma ka san cewa wannan ni’ima ce daga Allah maɗaukaki gare ka, sai ka girmama ta, ka tausaya mata, duk da kuwa hakƙinka a kanta ya fi karfi, amma tana da hakki a kanka na ka tausaya mata domin ita ribacewarka ce. Kuma ka ciyar da ita, ka tufatar da ita, idan ta yi rashin sani da wauta sai ka yafe mata” ta tura ƙaramin bakinta gaba ta ce "Salon ace Malam ya zama mijin ta ce" Kamar ba Yaa Sheikh ba ya saka hannu ya riƙe ƙugunshi cikin son kwantar mata da hankali domin ya fahimci damuwarta ya ce "Lallai ƴar nan, Malaminsu a waje abokinki a gida, a good friends should be helping each other" Ya kwashe kayan zuwa kitchen tana zaune taji ƙarar ruwa ta miƙe tana leƙawa. Tsaye ta ganshi yana wanke plates ɗin tayi saurin cewa "Ka bari don Allah ban saka ba, ni wallahi Abba duk ka ɓata mini kitchen" Ya gama jagwalo gwalon shi ya ajjiye ya kafi Idanunta ya sureta zuwa sama ya nufi kan bed da ita cikin kunnenta ya ce "Nifa ki daina ɗauka wani malami,sbd cutata zaki kwana biyun rowar lemon tsami ake mini" ya hautsinata yana zame rigar ta zuwa ƙasa, tayi saurin riƙe ƙirjinta tana marairaice fuska ta ce "A'a Please, bana son ka shiga fushin Allah kaje wajan matarka kuma mayyarka tana jiranka" muryarta na rawa ta ƙare maganar tana ɗauke kai, ya yarda da batunta amma ai laifinta ne waye ya ce tayi shigar Iskanci ya gani da goga abu a jiki. Ya jingina da jikin prame tare da jawota ya zaunar saman cinyarsa ya kama hannunta tare da binta da kallo kamar mara wayo ya taɓe fuska cikin ƙasa da murya ya ce "kina sane da hakƙin ɗan Ummul da ki ka ɗauka?" "Wanne irin hakƙi kuma Yaa Sheikh?" Ya girgiza kai tare da lumshe kamar mai barci, ta saka hannu ta shiga shafa fuskarsa zuwa lips ɗinsa, ya cafke yatsun ya zura a bakinsa ta ce "Modibbo lafiya?" Ya buɗe idanu da ƙyar ya ce "Ana maganar cuta ina lafiya? Kije Allah ya yafe miki" ya ƙare yana tsotse yatsun da yake ɗauke da zanan henna. "Ba zaka tafi bane" Ya yi mata banza, ya jawota ya rungometa a jikinsa da kyau, hannunsa cikin riga a hankali yake addu'a kuma yana shafa mata tare da hura mata iska a kunne, tayi luff tana riƙe shi gam!. Numfashinta mai zafi ya fara sauka a ƙirjinsa alamar tayi barci cikin nutsuwa ya zameta ya gyara mata kwanciya, tare da ja mata duvet ya sumbaci goshinta tare da cikinta data ɗora hannu akai, bai san ya ya yake ji game da ita, ya kuma kasa fahimtar yadda zai fasalta ko bayyana al'amarin, kalmar Ina son ki tayi ƙanƙanta a gareta, sam! Ta shige hakan, kawai abu ɗaya ya sani aikatawa a bayyane kamar yadda ta zama wani sashe da sashin jikinsa. Ya shafa kanta ganin ta tura baki tare da marairaice fuska kamar ƴar tsana she looks like takeaway. Ya fita bayan yabi kusurwar ɗakin da addu'a kana yaja mata ƙofa ya nufi part ɗin Zahrah yana riƙe kansa tare da kame fuska ya dawo Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu ya fita daga Yaa Sheikh ko kuma malamin Danejo Rome. Zahrah na zaune ta riƙe Jikinta sbd magungunan data sha, gabaɗaya a sama ta sha ga wani magani goran tula mai saukar da ni'ima sai duk ta birkici, ƙamshin turaren Roja ya ruga sallamar Yaa Sheikh zuwa wacce ya yi a kamalance tana ganinsa ta miƙe tsaye fuskarta ɗauke da murmushi ta rungome shi ta ce "Wlcm Sweetheart, har na fara tunanin zuwa gareka" Ya jinjina kai tare da zareta a jikinsa a hankali ya ce "kizo part ɗina" yana faɗin haka ya juya ya fita, sbd turaren dake hautsina kansa amma bai nuna ba, ta ce "Ok I'll be there" Ta ƙara fesa perfume ta shan magani wanda ya sa duk ta lalata kanta, yana zaune ya sauya kaya zuwa na barci ash colour hannunsa riƙe da coffee daya samu an ajjiye masa, ta faɗo ba sallama yaƙi kulata da kanta ta miƙe ta fita ta sake shigowa ɗauke da sallama ya amsa yana miƙewa zuwa bathroom ya yi brush da alwala ta kariya, ya sameta kwance ya kwanta yana kashe hasken ɗakin. Zahrah ta ce "Me ya kake samun Halisa har part ɗinta, amma ni sai nazo naka akwai fa'ida hakan ne?" Bai kalleta ba cikin gajiyawa ya ce "Banda hayaniya please" Ta jawo Jikinta zuwa nasa ta riƙe shi tare da ƙoƙarin haɗe kissing nasa, ya yi saurin zame fuska yana sakar mata murmushi tare da kissing goshinta. Zahrah ta ce sam bata san Wannan ba, ta birkice masa, gabaɗaya gangar jikinsa ta kasa amsar saƙon da take tura masa, yana da biye da ita gudun saɓawa mahalicci da gaske tana tsananin buƙatarsa da kulawarsa gareta, ya yi yaƙi da zuciyarsa bada wasa ba yana kiran sunan Allah a haka ya samu sassauci ya fara kyautata mata, amma sam ya kasa yarda yaji bakinta a nasa. Yaa Sheikh na fita Halisa ta buɗe ido, zuciyarta na bugawa ta riƙe kawai domin wannan daren tabbas zai shiga cikin kundin lissafin ajjiye muhimman abubuwa, zai zama dare mafi tsayi da muni a tare da ita duk wani mai sonta dole ya tausayawa mata, yau Abbanta ne zai kwana tare da wata? Ɗaki ɗaya,gado ɗaya? Maybe na jiki ɗaya. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un" ta furta tana fashe da wani irin kuka mai cin zuciya ko cikakken abinci ta kasa ci yau, taji a ranta idan akwai abinda zai bata matsala acikin aurenta bai shige kishin da take dashi akan Abbanta Yaa Sheikh ba, tayi kuka sosai daga ƙarshe ta miƙe tayi Alwala tare da ɗaukan Alkur'ani sai dai sam bata ganewa kuma bata fahimta, gudun kada tayi saɓo ta ajjiye ta fita zuwa main parlour barci tuni ya ƙauracewa Idanunta, ta zauna a kujera tana kuka ƙasa-ƙasa. Zahrah taga Yaa Sheikh ya tsaya cak bai taɓa ganin abin al'ajabi da almara haka ba, ki da can baya da yake riƙe kansa lafiyayye ne shi, amma yanzu daya nufi hanyar samawa Zahrah nutsuwa sai maɗaukan suka daina ɗaukan sati ta zama tamkar ruwan da tsumma ya jiƙa tare da kwanciya tayi barci irin barcin nan da zakai zaton namiji nakashasshe ne... Sorry For the shortly👏🏽*Follow my Facebook page👇🏾* https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL Ta shi Yaa Sheikh ya yi sbd tsananin kunyar Zahrah daya lulluɓe shi, bai san yadda zata ɗauki al'amarin ba, ya nufi bathroom ɗin shi tare da sakarwa kansa shower, idanunsa lumshe yana kiran sunan Allah maɗaukakin sarki, wanda ya samar da sammai da kassai bakwai, ya wanzar da sirrai a cikinta, ya samar da ƙasa, wacce muke tafiya a kanta, ya halicci mutane da dabbobi da dukkan abin dake da rai. Ya sauke numfashi wannan abu shi ne mafi tsayuwa a ranshi, yana ganin abin al'amara amma wannan ya banbanta, ya kai duban shi ganin yadda yanzu komai ya daidaita kamar ba yanzu ne maɗaukan suke barci ba, ya ƙara sakin ruwa sosai tare da ɗaura alwala ya sanya bathrobe ya fito jikinsa na zubar da ruwa. Zahrah ta dube shi Idanunta cike da hawaye sosai ta ce "Na sani, ba zaka iya ba amma daka sani da baka fara mini abinda zai sanya na samu matsala da tunani na ba, ina jin kamar Allah ya ɗauki raina kafin cikar lokacin da Dr ya faɗa" Ya dubeta lokacin da yake taje gemunsa mai tsafta, kaifin idanunsa a kanta ya sanya ta kasa cewa komai sai kawai ta fashe da kuka na baƙin ciki tana rufe fuskarta. Bai ƙoƙarin hanata ba, yasan da zaifi hakan ga ko wacce mace musamman ita da ga yadda al'amarin ya kasance, zata iya zargin wani abu, duk da zato zunubi ne. Ya shimfiɗa prayer mat bayan ya sanya farar jallabiya tare da tayar da sallah, ya jima yana Sallah tare da addu'ar Allah ya nuna masa manufar sabon wannan al'amarin a cikin maɗaukan shi ya yin barci, kamar yadda ya saba yin gamo da sabbin al'amura cikin rayuwar shi. Har lokacin daya idar kuka take ya dubi agogo a hankali da sauri kuma ya rufe idanu ganin 2 da wani na dare, gently ya miƙe tare da nufar kan gadon ya zauna cikin laushin murya da gajiya da jin kukan nata ya ce "Zahrah" ta ɗago kai ta kalle shi ya numfasa ya ce "Kuka? Name?" "Kafi kowa sanin kukana Yaa Sheikh wallahi...," Ta kasa ƙarasa maganar tana fashewa da kuka sbd ita kaɗai tasan ciwon da mararta yake mata, ya jawota ya rungometa jikinsa ya shafa kanta ya ce "It's okay, ki barwa Allah komai cikin lamuranki, ban san yaya ne ba, ban san matsalar ba kiyi addu'a just pray" ta riƙe shi gam! Numfashinta na fita da ƙyar raɓuwa da take a jikinsa wani tsananin a zaba take ji sbd wutar abinda ke cinta ta ce. "Kayi mini al'ƙawarin farin ciki, ina son samun baby dakai kafin Ubangiji ya ɗauki raina" ya girgiza kai yana ɗan faɗaɗa fuskarsa wacce hakan ya sanya gemunsa motsawa yana gogar fuskarta ya ce. "Idan kina son rahamar Ubangiji da kuma farin ciki ga rayuwarki da mijinki, You should stop lying" kukanta ya tsaya tayi saurin kallonsa ta ce "Ƙarya?" Ya jinjina kai ya ce "Eh, idan za kayi ƙarya don ka samu wani abu, sai Ubangiji ya baka abin kuma ya barka kai da shi daga ƙarshe ya zamana abin bai amfana maka da komai ba" ya numfasa cikin gajiyawa amma ya zama dole ya fahimtar da ita abinda bata sani ba, domin ya lura Empty head ce ya gyara zama cikin tarin nutsuwar shi ya ce "Kin ya ƙarya kina da Cancer, kin manta ni likita ne?" Bakinta na rawa Zahrah ta ce "Ni... Ni.. yaushe?" Ya tsareta da idanunsa masu kaifi wanda ya tilasta mata yin shiru ya ce "Kada Kiyi musu, kowa da baiwar da Ubangiji ya yi masa, haka kowa da naƙasun da yake da shi a rayuwa, na sani na sani, i knew everything da ki ke harding, ban aure don naji tausayinki ba, ban kuma aurenki don ina son ki ba, haka ban aureki don inci zarafin ki ba ni da kai na bani da dalilin aurenki, amma na bar hakan matsayin ƙaddara wacce take zama zanan dutse, duk wayonka, da iliminka, duk na gartar da Ubangiji ya baka sai ya jarabce ka da ƙaddarori masu zafi domin ya gwada imaninka, idan kayi haƙuri ka miƙa lamarin ga Ubangiji sai Allah ya duba ka kuma ya sanya hannu cikin al'amarinka, ke ƙaddara ta ce ke kuma soyayyar da ki ke mini ita ce ƙaddararki" Idanunta ya cika da hawaye kunya ta kamata, Allah da kansa ya ce fazakkir fa'innàl zikkira tamfa'ul mu'uminun. Yaa Sheikh ya ƙara samun ƙarfin gwiwar fahimtar da Zahrah ya tallafo haɓarta yana bin fuskarta da shekaru ya ce "Kin san za a haifeki? Kin san zaki karatu mai zurfi? Kin san zaki haɗu da Father? Kin san zaki samu ciki har huɗu? Kin san zaki haɗu da Saif-wazir? Kin san saki aureni? Kin san zaki haifi Muhammad?" Ta girgiza kai jiki duk a mace ta ce "Ban sani ba" a taushashe yana sakin fuskarta ya ce "Allah ya sani, tun kafin haihuwar ki ya rubuta hakan jikin allon lauhil-mahfuz, allon da baya ƙarya bawa baya shige ƙaddarar shi, baki san ina jin tsananin nauyi da kunyar kai na na auri wacce tayi hulɗa da wanda nake kallo matsayin Uba? Na kanji sauƙi idan na tuna babu haramci, ba ke ba ko Mother zan iya aura idan hakan ya zama ƙaddarar Aliyu!" Ya miƙe tsaye ganin kamar lokacin kiran sallar farko ya yi ya ce "One thing da zan faɗa miki, ki dai na yarda da mutum akwai wanda suna zaune da kai domin su samu abin faɗa akan ka acikin mutane, akwai wanda zasu ya beka bisa raɗin kansu a baya su zageka, akwai wanda su da kansu basu dalilin daya sanya suke tare da kai ba, zaka birgesu har zuciya amma zasu zageka, masu yin hakan kuma Ubangiji ya tana dar musu makoma domin laifin bawa akan bawa saɓo ne mai girma da zunubi, ki tsarkake harshenki daga cin naman mutane ko cin mutuncin su" Ya ƙara sauke numfashi gajiya duk ta bayyana a jikinsa ya ce "Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce: lokacin da aka yi Mi'iraji dani, muka hau sama sai naga wasu mutane da baƙaƙen farata suna yage fuskokinsu da ƙirjinsu, na tsorata da hakan nace Ya ɗan uwana Jibrilu su waye wannan?" Sai ya ce mini "Su ne wanda suke cin naman mutane da cin mutuncinsu su" Anas bin Malik (RA) . Yaa Sheikh bai gushe ba sai daya ƙara bata fatawa da faɗin Ibn Abu Shaiba ya ruwaito shi a cikin Musnaf ɗin sa ya ce Manzon Allah (SAW) yana cewa: “Wanda ya ci mutuncin ɗan uwansa za a yi masa suturar wuta (a Lahira), idan mutum ya yi ba daidai ba kira shi ka sanar masa da kuskuren shi domin ya gyara”. Zahrah Jikinta ya ƙara sanyi sosai gabaɗaya bata san Wannan ba, musamman daya kasance kaf zuri'arsu ilimin ya hudu ya yi musu gurbi a zuciya, Zahrah kuma tazo ta fisu ilimin daman kuma ace abin cikin kwan yafi kwan daɗi, kyan ɗa ya gaji ubansa, kuma ko wanne tsuntsu kukan gidansu yake. Taji ta tsani kanta,kuma ta tsani komai zafin iyayenta da basu kyakkyawan ilimin addini ba ya shigeta. Ta kalli Yaa Sheikh cikin kuka ta ce "Da gaske baka so na?" Bai iya ƙarya ba, kuma baya son farata ba zan faɗa mata gaibu domin taji daɗi ba, sbd yasan babu hakan a ran shi ya ce "Eh, ban san me gaba zata haifar ba kiyi addu'a" ta miƙe tare da faɗawa jikinsa ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi, soyayya masifa ce, musamman Allah ya haɗaka da wanda baya son ka kuma jarrabawa ce, ita kam zata iya cewa Soyayyar Yaa Sheikh ita ce girbin abin data shuka na saɓon Ubangiji tun a duniya. Ya ɗan rarrasheta kana ya koma Bathroom ya wanke jikinsa domin a jininsa yake jin ta ɓata shi ga ɗan abin da ya yi mata. Da sauri ta nufi steps na benen zata yi downstairs ganin Halisa zaune ta riƙe kanta tana kuka ƙasa ƙasa ya sanya Zahrah taka tawa. _"Zahrah think, Kada ki zama abar gori wajan kishiya"_ Zuciyarta ta faɗa mata haka, tayi saurin komawa da baya tare da laɓewa ta kurma ihu ta ce. "Wayyo Allah Yaa Sheikh zan mutu, ka bari wallahi ban saba ba, zaka ka sheni na tuba nayi ladama wayyo bayana Wayyo marata I love you so much sweetheart" Halisa ta firgita tare da miƙewa ta saka hannu ta toshe kunnenta. Ɗan cikinta ya juya ya daki mararta ta fara gani dishi dishi zuciyarta kuma tayi wani kyakkyawan bugawa. Zahrah ta leƙo ganin Halisa cikin wannan yanayin ya sanya ta ƙara sakin wani ihu ta ce. "Yaa Sheikh da gaske kake faɗa mini Halisa bata daɗi? Bata iya komai ba, ka daina faɗa kada taji babu daɗi" ta ƙara yin shiru ta ce "Na gode sosai ban taɓa sanin cewa kafi so na fiye da yadda ka ke son Halisa ba sai yanzu, na gode da kyautar fili da kuma kamfani wayyo i love You so much" Halisa ta gigice ta dinga kiran sunan Allah da karfi tana dafe cikinta, iya tsorata da firgita tayi sosai tun tana kiran sunan Allah daya kawo mata ɗauki har tari yaci ƙarfinta ta kifa tare da buga kanta da jikin kujera. Zahrah was happy ganin Halisa cikin wannan yanayin, and she don't feel anything data aikata, ta juya zuwa bedroom ɗin Yaa Sheikh ta same shi tsaye a gaban mirror ya kafe waje guda tare da riƙe kansa da hannu ɗaya, she hope ace bai ji abinda ta faɗa ba. Ta ƙarasa tare da tafa kafaɗar shi ta ce. "Sweetheart" Ya juya ya kalleta taga idanunsa jajir tayi murmushi sai shi shima ya yi murmushi, gabanta ya faɗi ganin haƙuri guda ɗaya dal a tsakiyar bakinsa, ta juya ta kalli mirrow bata san lokacin da fitsari ya fara zuba daga Jikinta ba, ta cikin madubin taga Rabi jikin aljani rabi jikin Yaa Sheikh ya koma wata suffa mai munin gaske, taji ya taɓa ta ya ce "Fitsari a nan Zahrah?" Ta kasa kallon shi domin ba fitsari ba, wallahi hatta kashi zata iya a wajan ta ƙara kallo cikin madubin, wani razannan ihu! Ta fasa ganin wani narkeken maciji yana yawo, babu addu'a ta fara ihu tana faɗin. "Asstagafirullah no no, what's is that..." Dum! Aka kashe hasken ɗakin ya zama baƙiƙƙirin sululuu kuma taji abu yana ratsawa ta cikin rigarta tare da shigewa cikin wandon jikinta ta ƙara yin wani ihun tana faɗin "Dad, Mimi help wayyo Ya zama Aljani wallahi aljani someone please help me" Sai kuma hasken ɗakin ya dawo ta haɗa zufa Jikinta banda ɓari babu abinda yake. Ta juya taga Yaa Sheikh tsaye a kanta ta girgiza kai sai ya wangale mata haƙuri ɗaya ta miƙewa tana layi zata kifa kafin ta faɗi sai taga babu komai a wajan ganinta ya ɗauke. Yaa Sheikh dake bathroom ya kifa kansa a sick kamar an dasa shi Jikinsa ya jiƙe sosai da zufa sai karkarwa naman jikinsa yake, kamar a mafarki yaji Zahrah ta fasa ihu ya ɗago kansa dake sara masa sosai ya dafe da hannu ɗaya tare da murɗa handle ya bita daga bathroom ɗin, Ya she ya samu Zahrah kanta ya bugu sosai ya ɗagota yana ɗan bubbuga kumatunta domin jin jikinsa yake kamar an masa dokan tsiya, ya ce "Fatymerh?" Ya daɗe kafin ta saki numfashi ta buɗe idanu tana arba da shi ta saka ihu zata gudu ya riƙeta da kyau ya fara mata addu'a ya lura kamar tsoran shi take ko an firgita ta ohhu!? Da taimakon addu'ar ta ɗan dawo hayyacinta sai ta fashe da kuka ta ce "Wallahi gidanmu zani, kashe ni za'ai" da mmki ya ce "kisa? Akan me" tana kuka sosai ta ce "Kawai zani, amma akwai Aljanu a gidanka" ya ɗan yi jim! Sai kuma ya yi ɓoyayyen murmushi ya ce "Gidan Malam guda da Aljanu? Sai dai idan Malam ɗin ne Aljani da kan shi, Kinga tashi muhimmancin addu'a kenan" ta miƙe tana riƙe da shi amma ta kasa kallonsa gani take kamar zata wawulon shi mai haƙuri ɗaya ya ce "Sallah" da sauri ta ce "Nima sallah zan yi" mmki duk ya addabe shi ya yi mata kallon tsaf! Ya ce "La sallah Ala, ban janabati sai kinyi wankan sarki" ta ce "Mene wankan tsarki?.... Afuwa my Special kunji shiru, ku tayani da addu'a kawai Please... Kwana biyu sai a hankali.*_Arewabooks@Nimcyluv 73_* Yaa Sheikh was speechless ya lura da Zahrah bata da ilimi na addini, everything and anything babu, Ilimin addini zero, kula da miji zero, girki zero, shagwaɓa zero, ƙirji zero that's too much to her. Bai ƙara ce mata komai ya ɗauki hiraminsa ya naɗa as asual, kai tsaye downstairs ya nufa bakinsa ɗauke da tasbihi gabaɗaya bai lura da Halisa dake durƙoshe a main parlour ba, walking slowly cike da nutsuwa ya nufi part ɗinta, ganin ƙofar buɗe ya sanya ya shiga bakinsa ɗauke da sallama cikin murya mai tsananin taushi. Babu ita a bedroom ɗin, he was thinking ko tana bathroom tunda daman sallah bata shigeta, daman kuma hakƙinsa zai sauke a matsayinsa na miji. Ya juya tare da buɗe ƙofar da zata fitar da shi daga Main parlour ya nufi compound zuwa masjid. Tun a yanayin tafiyar shi Halisa tasan shi ne kafin kuma ƙamshin turaren shi ya biyo bayan, da ƙyar ta iya ɗago kanta tabi bayansa da kallo zuciyarta babu daɗi Banda duhu babu abinda take gani cikin ƙwayar Idanunta, kuka ya yi mata hijira bata taɓa sanin yinsa Rahma bane sai yanzu. Ta miƙe da ƙyar tana ambaton Allah tasan wayonta bazai fitar da ita, daman kuma ance komai yayi zafi maganinsa Allah. Tana shiga bedroom ɗinta taja ta rufe tare da murza key, bata iya wankan data saba duk Subhi ba, alwala tayi ta sauya duguwar rigar Jikinta zuwa Jallabiya. Bayan ta idar ta jima tana addu'ar samun kusanci da mijinta, duk wani abun sharri mugun ji da mugun gani ya ɗauke idanun abin daga kansu, daga ƙarshe ta nemi Ubangiji ya sassauta mata zafin kishin da take dashi akan Abbanta Yaa Sheikh. Wani irin zafin Yaa Sheikh taji wanda bata san dalili ba, amma maganganun da Zahrah ta faɗa ya tsaya mata suna ta kokawa da ƙarya da gaskiyar dake son gasgata batun nata, tana nan zaune taji ana knocking ƙofar babu mai yin hakan sai shi, taƙi motsawa can cikin taushin murya taji ya ce "Zawja" tayi banza da shi su take ta barshi shi da Zahrah taga inda iya al'amarin nasu zai tsaya, Yaa Sheikh dake tsaye hannunsa riƙe da Casbawa bai jima a Masjid ɗin ba, domin hankalinsa na kan Halisa da abinda yake cikinta, tun a jiya ya fahimci kamar ba daidai take ba, shi ya sa 6:00 daidai ya fito tare da dawowa zuwa duba halin da gabaɗaya matayen nasa suke, Yaa Sheikh ya gyara tsaiwa idanunsa na lumshewa ya ƙara lanƙwasa harshe ya ce "Are you ok Zawja" Still batai magana ba, hakan yasa ya kasa samun nutsuwa ya juya zuwa bedroom ɗin nasa yana shiga ya ɗaga fararen idanunsa suna haɗa idanu da Zahrah ta fasa ihu da sauri muryarsa na harɗewa ya ce "La'ilaha illallah Muhammadur Rasulullah s.a.w" Ya riƙe kansa daga kallonta ya nufi gaban mirrow tare da ɗaukan key ya nufi waje tabi bayansa da sauri suna sauka tayi part ɗinta shi kuma ya tsaya tare da buɗe ƙofar Halisa, yana shiga ya sameta zaune inda tayi sallah hannunta riƙe da Alkur'ani, bai ce komai ya karɓi Alkur'anin tare da ajjiyewa waje guda, kana ya dawo ya ɗauketa cak tayi saurin haɗe fuska ta ce "Meye haka?" He just staring at her face yana hango rigimar gaske ya zauna saman kujerar dake kusa da bed ya yi nishi like he so much tried. Yana sakin fuska ya ce "Tubarkallah, Zawja kada Kiyi lukuta fa" ita da kanta mmkin yadda Jikinta ya buɗe bakiɗaya take tayi ƙiba taban mamaki musamman hips ɗinta wanda yake ƙara tabbatar da girman cikinta. Muryar na rawa gudun shiga hakƙi ta ce "Sabahul khair" Ya kama fuskarta tare da juyo da ita amma sam taƙi yarda ta kalle shi ya yi mata shiru yana saka hannu ta baya tare da rungomota zuwa jikinsa hannunsa yana shafa cikinta daya kumburo sosai a hankali ya manna labɓansa a wuyanta yana goga mata hancinsa, tattausan gemunsa na shafar fatar wuyan nata, tsikar jikinta ya tashi sosai sai da ya gama shafar inda yake so da yake tsole masa idanu kafin yace "Meke faruwa?" Tayi shiru ya sauke numfashi a nutse tare da miƙewa da ita ya ce "don't tell me, but ki saka Allah cikin lamarin ok?" Ya kwantar da ita da ita tare da durƙosawa ya ɗaga rigar Jikinta duk tana binsa da idanu ya sumbaci cikin tare da yin addu'a ya shafa, kafin ya yi magana wayarta ta fara ringing ya dubi wayar haɗaɗɗan pictures ɗinsu ne shi da ita a screen wallpaper. “Hamma El” Yaga an rubuta bai ɗaga ba ya miƙa mata tayi saurin ɗaukan wayar tana kwaɓe fuska cikin rigima da shagwaɓa ta ƴar auta ta ce "Hamma" Ta cikin wayar ya ce "Princess, gani nazo wannan neman rigimar ya yi yawa" ta marairaice fuska tana sakin kuka ta ce "Uhm ni dai a'a" ya kalli harabar gidan Yaa Sheikh banda ƙamshin flowers da kukan tsuntsaye babu abinda kake ji gwanin sha'awa gidan."Ina Compound" tayi saurin cewa "Gani nan" ta goge hawayen idanunta tare da ɗaukan hijabi, ya dubeta da kyau ko'ina na jikinta sheƙi yake musamman fuskarta, a haka zata fita Compound masu aikin duk suna nan, ya miƙe fuska a kame Ya ce "Ki cire tunanin fita Compound" yana faɗin haka ya fita, tayi shiru domin bata gane me hakan yake nufi ba, ta kira El-bashir ta ce ya shigo. Ta fita zuwa main parlour hannunta riƙe da waya a zaune ta samu Yaa Sheikh yana kallon labaran tashar Aljazira, tana nan tsaye El-bashir ya yi sallama ya shigo hannunsa zube cikin wata Marron ɗin Double Breasted suit, ya saka Derby shoe sai ƙamshin Thierry mugler yake,ya yi murmushi dimples ɗinsa irin na Halisa ya bayyana yana ƙoƙarin zubewa gaban Yaa Sheikh ya gaida shi yaji Halisa ta faɗa jikinsa tare da ƙanƙame shi da kyau tana kuka kamar ranta zai fita. A tsorace El ya rungometa yana faɗin "What happened Princess?" Domin ji yake da wani abu ya sameta gwara shi ya same shi, ita kaɗai suke jini ɗaya uwa ɗaya uba ɗaya, banda haka bashi da kowa sai na biyunta Yaa Sheikh. "Am sorry Hamma, kayi haƙuri ba zan sake maka harara dako in kula ba, kai kaɗai zakai mini soyayyar da babu gori cikinta kuma tabbatacciya kayi haƙuri" Shi dariya ma ta bashi, Yaa Sheikh kuma ya kwashe karatun nata tas, bai kalli inda suke ba, idanunsa dai ya yi jajir ainun kamar wanda wutar kishi ke damunsa, El ya shiga ƙoƙarin zameta sbd cikin Jikinta tana kuka ta ce "Please Hamma El ka tafi dani kaji, bana jin daɗi wallahi ai da ba zaka so ka rasa ni ba" yaja hancinta ya ce "Ba gaki ga Abba ba?" Ta maƙale kafaɗa, ya girgiza kai ya ce "Wlh daman Mom tace ba wani abin kirki a kiran ki, rigima ce" Ya zameta yana durƙosawa gaban Yaa Sheikh ya ce "Good morning Abba" Ya jinjina masa kai alamar lafiya fuska kuma sake yana jin El-bashir ya zuciyarsa,sosai yake ƙaunar yaron. Ta ce "Ka zauna mana" Ya harareta ya ce "Ke gidanki ne, ni kuma wajan Abbana nazo" ya gyara zama daidai ƙafafuwan Yaa Sheikh ya ce "I'm starving aban breakfast" tayi wani irin murmushi ta ce "Laa Anty Zahrah ce zatai breakfast maybe ta gama" daidai lokacin Zahrah ta fito cikin kwalliya ta zuba lace Idanunta sun faɗa sunyi zuru-zuru. Ta nemi waje ta zauna tana ɗan yin murmushi tace "A'a baƙo mukai ne?" Idanun El akan plasma bai ce komai ba, Halisa ta ce "Anty Zahrah kin gama breakfast ne?" Ta ɗan saci kallon Yaa Sheikh taga gabaɗaya basu yake kallo ba, ta ce "Ban ba, bana jin daɗi" Halisa ta jima tana kallonta kafin ta ɗauke kai tana faɗin "Allah ya sauwaƙa"kitchen ta nufa ta fara shirya abu mai sauƙi irin very liquid ɗin nan wanda ba zai ja lokaci ba, fried indomie tayi ta saka mata su carrots, onion, da sauran vegetables. Tana da garin kunun tsamiya ta dama kunun tsamiya, kana ta tafasa shayi da zuba ginger da barkono da na'a na'a. Kana ta soya ƙwai tasan ba lallai El ya sha kunun da tayi ba. Tana gamawa tayi wanka ta shirya cikin wata simple light blue ɗin abaya wacce ta fidda shaps ɗinta, ta fito sai ƙamshin turare take. Yaa Sheikh ya kasa riƙe kansa ya dinga satar kallonta har ya ɗora idanunsa a kanta da kyau, wani kasala ya saukar masa musamman da suna haɗa idanu ta tura masa ƙaramin bakinta na tsiwa ya zame idanunsa yana girgiza kai a ransa yake sanya mata albarka. Ta zauna so close to him tare da ɗora kanta a ƙafaɗar hannunta a gemunsa tana ja idanunta akan El-bashir ta ce "Prince the breakfast is ready" Ya miƙe ya ce "Ok Little Our Princess Abba's girl" ya nufi dining room ɗin dake main parlour, Halisa ta juya suka haɗa idanu da Yaa Sheikh taja gemun ta ce "Habibi ƙalbi let's go" ya riƙe hannun nata,ganin idanun Zahrah ya sanya ya saketa ya ce "Part ɗina, cikin freezer Honey" ya yi maganar ba tare daya faɗi ainahin abinda yake so ba, ta fahimta sai ta miƙe ta ce "Okey Yallaɓai" Tana barin wajan Zahrah ta ce "Amma kasan kayi ba daidai ba" a taushashe ya ce "Da?" "Daka riƙe hannunta bayan kasan ranata ce" ya ɗago ya kalleta da kyau, kamar zai shiru sai ya ce "aikin da ki ka kasa tayi,ke zaki breakfast baki ba, ita kuma tayi tazo inda nake ta gaishe ki, kefa? Ko ina kwana babu" Ta ɗauke kai ta ce "Amma ina da niyyar gaisheka" kafin ya yi magana Halisa ta ƙwalla masa kira ta ce "Ɗan babyna Abbana Yaa Sheikh banga zumar ba" Ya miƙe tsaye tare da ajjiye wayar shi ya nufi upstairs, yana zuwa ya sameta durƙoshe gaban freezer yana zuwa ya saka ƙafa ya zungureta bata kallesa ba ta ce "Ina take" a hankali ya ce "Stand up" ta miƙe da ƙyar kafaɗarta ta sake tayi saurin shigewa jikinsa tana "Wayyo Abbana" ya riƙo ƙugunta tare da binta da kallo ya ce "Zaki iya haifar yara 20 anya?" Ta zare ido ta ce "Tab ai na gama daga wannan" "Kidding" ya furta domin shi da gaske zuri'a yake son mai yawa tunda familynsa basu da yawa. Ta ce "Sakeni to" ya kalli ƙirjinta ya kalli bakinta ya ɗauketa ya ɗora saman freezer kafin tayi aune ya fara bata wani cikakken sumbata yana birkitata, yana shafa duk inda yaso baya son yi abin kunya inda yaji abu ya yi masa sai ya fara faɗin.. "Yasubuhanallah! Ya Allah Ma sha Allah" cikin ƙaramin lokaci ya ɗorata akan network duk tana cewa bata so suka hargitse juna, ƙarar da taji yasa tayi saurin dubawa ta zare idanu ganin ya kusa yaga mata gaban riga. Ta sakkowa da sauri yana shirin kamota tayi waje tana maida numfashi, a hanya sukaci karo da Zahrah da take da wayar Yaa Sheikh da ake kira, ta bita da kallo kishi ya mamaye zuciyarta fal! Tana shiga ta samu Yaa Sheikh ya kifa kansa da jikin freezer ta ce "Ana kira" yana yin magana zai fallasa halin da yake ciki, ya miƙe tare da juya mata baya "Are you already?" Ta faɗa tana shirin dawowa gabansa ya yi saurin ɗaga Jallabiyar shi yana shigewa bathroom.... Misalin 5 na yamma motar Yaa Sheikh tayi parking a harabar gidan Abba Hakimi, ya fito yana gyara zaman babbar rigar jikinsa, Halisa ta buɗe ƙofa ta fito sanye cikin duguwar riga kamar kullum ta zumbula hijab, ga liƙab a fuska hadda safar hannu, tana fitowa ta ɗage liƙab ɗin tana haɗe fuska tare da tura baki ya yi murmushi mai sauti cikin kamala ya ce "Yanzu ki ka amsa sunan Matar Malam" Tayi gaba sbd haushin hijabin take ji ga cikin daya fara takura ta, duk ta damu kanta ya kuma ƙara fuskarta ƙiba tayi wata ƙatuwa, ita ta fara shiga cikin gidan bakinta ɗauke da sallama, Abba Hakimi da shigowar shi kenan ya ce "A'a wa nake gani kamar matar?" Ta nemi waje kusa da shi ta zauna ta ce "Ni ce Jon wuro ina yini" ya dinga ya ce "Ma sha Allah,sannu kinji Allah ya bada lafiya" Umma A'isha ta ce "A'a tashi daga nan kada ki danne mini miji, jibi yadda ki ka zama narkekiyya ni ƴar nan" Ta juya tana amsa sallamar Yaa Sheikh ya zauna saman kujera cikin tarin nutsuwar nan na shi ya gaida su. Umma A'isha ta ce "Me kake bata ne? Wannan ƙibar ai ta shige ta hankali" Halisa ta ce "Soyayya yake bani, ke kam matar nan mene damuwarki da ƙiba ta ne?" Abba Hakimi ya ce "Kishi take baki da ita" Mother ta fito ita da Dr A'isha cikin farin ciki ta ce "Oyoyo ga Daughter ma sha Allah, aure ya karɓe ki" ta zauna Halisa ta gaida ita ta ce "Mother wai baki koma gidan Father bane?" Kai tsaye ta ce "Eh, Aku" Tayi murmushi kawai ta ce "Allah sarki Farther tausayi kuke bani ne" Dr A'isha tayi mmkin yadda Halisa taƙi ko kallonta balle ta gaisheta. Abba Hakimi ya ce "A'isha ta samu matsala da mijinta, harta dawo gida" Ya juya ya kalleta fuska haɗe ya ce "Ɗauki tarkacanki ki koma" cewar Yaa Sheikh. Ta ɓata fuska amma sosai taji daɗin jin muryarsa ya buga mata wata gigitacciyar tsawa ya ce "Out immediately" Ta fashe da kuka sosai tare da jan mayafi tayi waje. "Me ya sa?" Yaa Sheikh ya kalli Abba Hakimi rai ɓace ya ce "Shirme tayi, bayan ita ce bata haihuwa ya rufa mata asiri... 08119237616Duka suka bishi da kallo, Mother ta ce "Idan har haka Dr A'isha ta yaudari kanta" Abba Hakimi ya kasa magana, sbd a iya saninsu babu wata hujja data nuna cewa Dr A'isha ce bata haihuwa, a kullum mijinta take nunawa matsayin wanda ke kawo naƙasu kuma likitoci sun ƙara tabbatar da hakan. "Amma a ko wanne lokaci Likitoci sune suke bada tabbaci akan mijinta shi ne baya haihuwa, ya akai reshe ya juye zuwa mujiya?" Umma A'isha ta ƙare tana kallon Yaa Sheikh da alama suna jiran su ji ta bakinsa ne kuma yaja baki ya rufe yaƙi cewa komai, suna da tabbacin kuma ba zai ce komai ɗin ba, na bayan ma daya furta ta kaishi ƙarshe ne. Halisa ta kalli Mother ta ce "Ni dai wallahi yunwa na keji" sai a lokacin Yaa Sheikh ya ɗaga fararen idanunsa tare da kallonta, abincin da taci kafin su taho har mamaki yake, amma yanzu har tana neman wani?. Mother ta ce "Shi yasa gaki nan kamar an zuba yis tubarkallah, me zaki ci" Halisa ta sakko ƙasan carpet tana miƙar da ƙafarta wacce ta kumbura, a nutse ba tare da kowa ya lura ba ya dinga kallon ƙafar dole akwai dalilin kumburin. Ta buɗe baki cikin takurawa irin ta masu juna biyu ta ce "Kawai ni duk abinda kuke da shi a bani zanci" Umma A'isha ta kada baki cikin zulaya ta ce "Bafa Abbanki Yaa Sheikh ke bamu kuɗin cefane ba" kamar jira take ta bata martani da "Mijina bashi da rowa, idan ku kai mini rowa na haifi ɗana haka zaku haɗu da shi" "Da waye zamu haɗu?" Umma A'isha ta sake faɗa, domin Halisa jikar ta ce shi ya sa bata damuwa da sakin zan can nata. "Gwarzon mijina ba irin tsohu na kujera" Sai a lokacin Mother ta sake cewa "Yanzu kuma kan Ubana kika dawo" Ta juya kan Yaa Sheikh ta ce "Malam ka ɗauke matarka duk ta Ishemu" Yaa Sheikh ya ɗan faɗaɗa fuskarsa yana mai yin baya kaɗan ya ce "Wajan Ummul zamu, taci a can" Mother ta riƙe baki ta ce "Kana son faɗa mana Ummul tafi kula maka da Matarka ko?" Ya miƙe tsaye yana shafa fuska zuwa gemunsa, Halisa ta kama jikin kujera ta miƙe tana faɗin "Ai wallahi tafi so na, shi ya sa nake son ɗanta kamar hauka I love you Abbana so much love" tuni ya yi waje ta zura hijabi tana cewa "Kuma ba zan dawo ba sai na haihu" Umma A'isha ta kada baki ta ce "Allah ya raba lafiya, mu ai haka muke so" Abba Hakimi da addu'ar fatan alheri da samun farin ciki na har abada ya bisu, Halisa macace tana son Abbanta bayan kallon miji da take masa, tana masa kallon komai nata shi ya sanya bata riƙe kanta akan soyayyar shi, tana da kaifin baki kamar reza tunaninta kullum kaifafa yak. Yaa Sheikh yana riƙe kansa sbd bai saba ba, kuma halinsa ne haka baya iya bayyana yadda yake ji sai dai ya nuna shi a aikace, jajir tacce ne, ya gode Allah da son da ya kewa Halisa bai rufe masa idanu ya kasa nuna mata kuskurenta a duk sanda tayi ba daidai ba. Yaa Sheikh na fita ya tsaya jingine da jikin motar shi yana shaƙar iskar dake wajan, tafiya yake son yi mai muhimmanci amma baya son barin baya da ƙura, Halisa nada ciki tana tsananin buƙatarsa Zahrah na cikin damuwa da muradin jinsa a jikinta, ya kuma abinda ke faruwa babu wata cikakkiyar fahimta da fuskantar juna tsakanin matan nashi guda biyu! Laifin waye? Nasa? Ko Halisa da take ƙarama kuma uwar gida? Ko kuma Zahrah mai zuwan yanzu data kasance Amarya kuma gaba da Halisa a shekaru. Horn ɗin mota ya dawo da shi cikin tunaninsa ya ware idanun yaci karo da motar Father dake shigowa cikin gidan lokacin kuma Halisa ta fito hannunta riƙe da jakar da Mother ta bata, Yaa Sheikh ya ɗauke idanu yana daidaita kansa da kyau tare da juyawa ya miƙawa Halisa hannu ta kama ya dawo da ita kusa da shi yana amsar liƙab ɗin hannunta zai saka mata ta ce "Modibbo ka barni kamar zan faɗi nake ji" ya riƙeta da sosai ya ɗaura mata daidai kunnenta cikin lallashi ya ce "Dole ki saba Zawja" Mother ta ce "Kinga na manta na baki wannan....," Maganarta ya tsaya lokacin da sukai idanu biyu da Father ya fito daga mota shi da Maimoon, Auta sama sai Zeefa da kuma Jaddada. aka shiga kallon kallo, Father ya yi baƙi ya lalace ya fita hayyacinsa kamar ba mijin nan nata ɗan gayo ba, Jadda baki ya mutu sbd halin da ɗan ta ke ciki, babu jimawa kuma wata motar ta sake shigowa Uncle Haroon da Uncle Bashir ne a ciki. Yaa Sheikh ya juya zai shiga mota Uncle Haroon ya ce "Malam Aliyu ai da ka tsaya ko?" Ya saki hannu motar tare da harɗe hannunsa yana rufe idanu. Mother ta kalli Maimoon da Idanunta ya yi jajir sosai, ta ce. "Are you sick?" Maimoon ta kasa magana ta fashe da kuka tana zubewa a ƙasa tare da riƙe ƙafar Mother, Zeefa da Auta Fattoumah ma sukai elxty what Maimoon did. Kuka suke sosai gwanin ban tausayi, a raunace Father ma ya tsuguna ya ce "Maryama na sani, wallahi na sani kuma hakkinki dana Yaa Sheikh ke bibiyar rayuwata, ban cancanci ki tausayi mini ba idan nayi kamar na haƙura dake sai naji babu wacce nake buƙata a cikin rayuwata sai ke ɗin nan, wallahi Barrister IDAN BA KE na tabbatar rayuwata zata iya salwanta, babbar isharar da Ubangiji ya nuna mini yadda ƴata ga cikina Fattoumah take cewa ta tsaneni, wacce kalar jarrabawa ce wannan" Ya fashe da kuka ganin yadda Mahaifinsu ke kuka ya sanya gabaɗaya ya ran suka sake fashewa da kuka sosai. Ya ƙara riƙe ƙafarta ya ce "I made a mistake, a mistake I can't fix,But let's take this as the determination of the existence of Muhammad, Destiny is the cause, be patient and forgive me for the blessings of God and our children" Tausayi ya kama Mother irin tausayin _Mata zuwa ga mijinta_ Uwa uba yaranta da rayuwarsu ta fara lalacewa. Jadda ta matse hawaye ta ce "Harfa cewa nayi zan ɗaga mishi nono, gashi tun ban ɗaga ba rayuwarsa tana gantali tsakanin duniya da lahira, ni dai an fitar mini zakka a cikin yarana naga Nahwu naga aya akan Aliyu, amma hannunka ba zai taɓa ruɓewa ka yanke ka yar ba, kiji tausayinsa ko ɗan mitsitsi ne ki yafe masa kana ki koma gidansa ku rungumi yaranku" ta kece da kuka sosai ta ce "Wallahi gorin duniya nake jiye musu, a dinga nuna su da baki ana babansu ya yi wa wata cikin shege harta haihuwa" Uncle Haroon ya kada baki ya ce "Sai haƙuri fa" "To ba ya zama dole ba? Haka fa Ubanku ya yi daman ance shi hali ɗan akene ya mutu tare da bar masa mugun gado" Uncle Haroon ya yi shiru Jadda ta ce "Naga duk kun tsare ni da idanu? Ku ɗin nan Ubangiji ne ya taƙaita da kuma ƙarfin addu'a kwarankwasa da a shegu za kuzo duniya, muta ta addu'a kullum ina kuka cikin dare sbd Ubangiji yafi duba zuciyarta har ya shiryu, shi ya sa duk abinda zaka aikata a duniya ka tuna cewa zaka haifa, idan baka haifa ba za'a haifa maka, gado kuma jini yake bi gashi nan Ali ya kwashe Iskancin da ubanku ya yi" "Yanzu ai ba wannan maganar ake ba" Ta kalli Uncle Bashir ta ce "To ita nayi niyya babu ruwanka dani" Engineer Aliyu dai yana tsugune ya ƙara cewa "Ki rungumi ƙaddara ki dawo gareni don Allah, wallahi wallahi Ina son ki IDAN BA KE I can't be..." "Ya Isa, Allah ya yafe mana baki ɗaya" cewar Mother. Ta ɗago Auta Fattoumah ta rungome Idanunta ya yi jajir, Jadda ta ce "A'a bana son mugun abu irin naku na lauyuyi cewa zaki na yafe maka Ali kuma zan koma gidanka" kai tsaye ta ce "Zan koma Albarkacin yarana" Father ya saki Ajjiyar zuciya. Zeefa ta ce "Father ka tashi Mother ta yafe maka" ya miƙe ya dubi Yaa Sheikh ya ce "Ka yafe mini kai ma Aliyu don Allah" Yaa Sheikh ya jinjina kansa kawai yana buɗe ƙofa zai shiga mota. Jadda ta zabga Salati ta ce "Muhammadur Rasulullah s.a.w wa nake gani haka kamar ƴar Fulani wacce aka ce ta sai da nono" "Ni ce" Halisa ta sauke Glasses tana faɗar haka, Jadda ta ce "To baki da lafiya ne naga kin kumbura?" Tayi shiru sai kuma ta ce "Allahamdulillah" "A'a wallahi da sauƙi, ina lafiya a wannan ƙibar kamar anyi miki fanfo, koda yake ai ga Malam nan yasin da ban gane shi ba, kalli yadda kumatu ya zazzago"Halisa ta kai da su Uncle Haroon, Maimoon ta gaida Halisa. Kana Yaa Sheikh ya shiga mota tare da yin key bakinsa ɗauke da tasbihi ya nufi hanyar zuwa wajan Ummul, yana fita motar Umar-khan na shigowa daga wajan aiki bankin Yaa Sheikh. Driving yake a nutse duk da bai wani saba da tuƙan na shi ba, amma ba zai jure ana driving matansa ba. Halisa ta juya ta kalle shi ta ce "Kayi haƙuri Habibi ƙalbi" Ya saka hannu ya kamo nata tare da ɗora a fuskarsa, bai ce komai ba. Ta ce "Ina da kishi bana son ko wacce ta raɓeka Habibi, amma banwa kai na adalci na amince da ƙaddara ko zan mutu don kishi kada ka damu, ina neman alfarma ka bawa Zahrah ƴan cinta na Matarka" Ya sauke numfashi cikin nutsuwa ya ce "Allhamdulillah" ta kalle shi tana jan gemu ta ce "For?" Ya sha corner ya ce "Zawja tayi hankali" tayi kicin-kicin da fuska tana zame hannunta ta ce "Oh da mahaukaciya ka aura" Ya juya ya kalleta sai kawai ya girgiza kai ba tare da ya ce komai ba. Gatekeeper ya buɗe masa gate ya dinga zubawa Yaa Sheikh addu'a neman zama lafiya. Ya shafa Aljanu sai bai ji kuɗi ba, ya amshi jakar hannunta ya buɗe ya ɗakko kuɗi ya bashi. Jakar ya bata ta ce "Kai Habibi ka riƙe mini mana" yana riƙe hannunta zuwa cikin gidan ya ce "Ba mijin novels bane ni" A kusan tare muryarsu ta ratsa parlourn dattijo ya amsa shi da Hajia halisa ta gaishe su ta ce "Wannan tsofaffin kamar tattabaru kullum kuna tare" Dattijo ya ce "Matar Malam gidanku" tayi dariya. Yaa Sheikh ya miƙe tare da nufar part ɗin Ummul, ya yi sallama ta amsa tare da bashi izini tsaye ya sameta gaban wardrobe tana gyara clothes ɗin ta, ya nufeta ta rungume shi sbd baya girma a Idanunta. *Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu* baya jin kan nashi matsayin babba a gareta. Ya tsuguna ya gaidata ya nemi waje ya zauna, kallon da yake tayi mata ne ya sanya ta lura akwai wani abu ta ce "Arɗona ya akai?" A taushashe ya ce "Ki bani labarin Abbi" tayi shiru sai kuma ta zauna ta ce "Na faɗa maka, me kake son ji kuma" Ya kalleta ba tare daya amsa ba ta ce. "Mahaifinka samun kamar shi za a jima, kamar yadda kake cewa Matarka *IDAN BA KE* ba zan iya rayuwa ba, haka yake duban cikin idanuna ya ce "Ummul-khairy kina da haƙuri, Ubangiji ya biya ki, *IDAN BA KE* zan yi rashin wani sashe daga cikin rayuwata" tayi shiru alamar tana jin zafin abin sosai amma ta jure ta ce "Bayan kasancewar shi Arɗon Rugar Bello, shi ɗin ma'abocin shiga jeji ne, har aka yi rashin sa a ya faɗa gidan tururuwa, tunda daga wannan lokacin yake jinya sosai, ya fara gane-gane amma bai faɗa mini ba, daga ƙarshe ko yana gida sai ace an ganshi waje kaza, na share duk ban damu ba, ashe a faɗawa gidan tururuwa da ya yi, ya samu matsala Aljanu suka ratsa jikinsa wanda lokacin daya yana iya fahimta ko jin abinda ba ko zai ji ba, idan na damu sai ya ce meye ne ƴar matana akwai wanda zai maye gurbinki gareni, yana nan zaki samu, wani lokacin cikin dare zai ta shi ya fita jeji babu jimawa sai ya dawo, da safe na sake gani ya dawo mutum biyu kenan, sai ya ce kada na wani damu, mahaifinka har magunguna yake bayarwa ya ɓoye wata laya acan Rugar Bello ya ce kada a taɓa fito da ita sai lokacin da wani jininsa ya ɓukaci jin wani abu daga cikin rayuwarsa" ta goge hawayen idanunta ta ce "Magana ta Gasky ban taɓa ganin mutum kamar mahaifinka ba, nagartar shi ta kai, yana da zafi ƙwarai amma yana da sauƙin kai baya ɗaukan duniya ta zafi, idan na kalleka sai naji kawai shi nake gani baka ɗauki komai nawa ba, baka ari wani abu daga wajena ba amma babu abinda ka bari na Mahaifinka everything" Ya saka hannu ya goge mata hawayen idanunta ya ce "Allah ya yi masa rahama, ina son Abbi kamar yadda nake son Ummul" ta ja hancinsa ta ce "ina tunanin lokaci zuwa Rugar Bello ya yi a fito da layar a duba mene cikinta" Kafin ya yi magana suka ji muryar Halisa Ummul ta ce "Shigo" tana shigowa ta juya zata fita ganin uwa da ɗana zaune saman gado Yaa Sheikh sai narkewa Ummul yake. Ummul ta miƙe ta ce "A'a dawo mana ni tashi zan yi" Halisa ta ce "A'a daman kawai yunwa nake ji" Ummul ta kalli Yaa Sheikh ta ce "Bata ci abinci ba kuka taho?" Yaa Sheikh ya kwanta gadon Ummul yana sauke numfashi ya ce "Ita take cinye abincin gidan fa, ni da Fatymerh bamu da ci" Halisa ta haɗe fuska taƙi cewa komai sbd ganin idanun Ummul, ta ce "Shige ya danna miki wannan ƙafar bari na kawo abinci" ta fita ita kuma ta shigo bedroom ɗin tana zama ya jawo ƙafar ya dinga danna mata, idan ya kalli ƙafar sai ya kalli fuskarta shi kaɗai ya saki murmushi ta ce "Wai Habibi me ka kewa dariya" ya ce "Kalli hancin ki Zawja kamar fanke, Asstagafirullah" ta ɗauki pillow ta cilla masa ya cafe ta ƙara ɗaukan wani ta cilla masa sai kawai ta fashe da kuka ta ce "To waye ya jawo mini idan ba kai ba" ya rungumeta bakiɗaya ya ce "Sorry zo nayi miki waƙa".... Misalin 9 na dare ya shiga sakkowa daga kan upstairs ya nufi part ɗin Zahrah yi mata sai da safe, ya sameta kwance Idanunta yana kallon gefe ɗaya wayarta can nesa da ita, Ya yi sallama ta amsa a hankali tana tashi zaune ya jima tsaye yana kallonta kafin ya zauna kusa da ita cikin taushin murya ya ce "Lafiya" Tayi murmushi kanta ƙasa ta ce "Ya Ummul? jikin Halisa su Abba Hakimi" ya tsora mata idanu yana son gano meke damunta, ganin yaƙi magana ta ce "Nayi abinci ban sani ba ko zaku iya ci" nan ma bai magana ba sai can ya ce "Ina ki ka iya?" Ta ce "Nayi searching by Google" ya jinjina kai ya ce "Come" Ta kalle shi ta ce "Halisa" bai magana ba ya saka hannu ya jawota jikinsa ya rungometa, a tsakanin nan ya lura Zahrah nada haƙuri, kuna da alama haƙurinta shi ne zai taimaketa Allah baya taɓa mutum da mugwayen abubuwa dole ya baka wani abu wanda za ai misali da shi, tabbas tana da haƙuri ya kuma ji tausayinta Halisa kuma zafi gareta ta iya masifa amma tana da saurin yafiya. Ya ƙara rungometa jin ta sauke numfashi a kunnenta ya ce "Fatymerh Zahrah" tayi murmushi sai taga bata damu ta neman komai wajansa ba, a karo na farko wani abu mai kama da SO ya gilma a zuciyarsa game da ita ɗin. Ya ɗago kanta duk ta rame amma tana da kyau sosai itama babu zato taji ya ce...*_Arewabooks@Nimcyluv75_* Ransa ya ji ya ɓaci for no reason ya sauketa daga jikinsa yana miƙewa tsaye hannunsa zube cikin aljihu, slowly ya sauke numfashi trying to control his anger, cikin nutsuwar nan tasa mai jan hankalin mutane gare shi ya shafa kai a hankali ya ce. "Da kin huta, munci abinci" tayi murmushi ta ce "To babu damuwa sai a zubar, daman ba lallai ku iya ci ba" bai kalleta ba ya nufi waje yana faɗin. "Ba kyau albazaranci, ki fito da abinci za a bayar" kai tsaye ya buɗe ƙofa ya yi waje, not too long ya dawo ya sameta a parlour hannunta riƙe da warmer ta miƙa masa ya amsa tare da sake fita, ta na nan tsaye ya ƙara dawowa ya saka key ya rufe gidan. Tayi ta kallonsa jin kamar idanu na yawo a kansa, gently ya juya yana zuba mata idanunsa da yake rufewa sbd tsananin gajiya da son yaji ya samu kansa cikin hutu ko ya yi barci ishasshe. "Need something?" Ta yi ƙasa da kai sbd kwarjinin da ya yi mata, yau ɗin sai ta ganshi yafi kullum cikar zati ta ce "Karatun? Ina nufin wankan da kai magana" ya ƙarasa kamar zai tsaya inda take sai ya dubeta da kyau cikin kulawa ya ce "Zuwa safe, ki kula" "Okey good night sweetheart" tayi part ɗinta, shi kuma ya yi addu'a ya shiga tofawa a ko wanne lungu na parlourn, kafin ya kashe hasken ɗakin. Direct wajanta ya nufa, tun tuni zuciya da gangar jikinsa ke jansa zuwa gare ta, ƙofar a buɗe take ya buɗe bata parlour ya shige bedroom bakinsa ɗauke da sallama cikin sanyin murya. "Wasalamu Alaika Yaa Sheikh" ta faɗa tana miƙewa da ƙyar frm head to toe yake binta da kallo. "Me ciki" Ya faɗa cikin sigar wasa ta ɓata fuska ta ce "Ai dai daga wannan Shikenan, matarka ta haifa maka" Ya saka hannu ya ɗagata yana murmushi ba sosai ba ya ɗorata a gadon ya ce "Lallai yarinya" Ta ce "Abba" Ya kalleta bai amsa ba ta ce "Me ya sa ka ke son ce mini yarinyar bayan kasan yanzu nima uwa zan zama" Sunna ne zama da matarka kayi hira koda baka da ra'ayi ko baka da surutu hakan yasa ya ce "A sbd ke yarinyar ce" ta ɓata fuska sosai ganin haka ya lumshe idanunsa ta ce "Tashi ni yau na yafe kowa ya kwana a bedroom ɗin shi, wlh takura ni ka ke Abba" Ya maƙale kafaɗa yana shafa sumar kansa tare da kwanciya saman cinyar ta ya ce "Ni ba inda zani kawai ki barni ina nan, ina gadinki da killata kuma sannan, na baki kula idan akwai buƙata kenan" ta saki baki jin babban malami kamar Yaa Sheikh yana zage yana rera mata waƙa kafin ta ce komai ya riƙe kumatunta yana girgizawa ya ce "Ko na tafi sai na dawo, sadakin ki sai na kawo zuciya ya nai mini zillo....," Ta tuntsire da dry sosai ta ce "Wow What a nice voice, Habibi kafi mawaƙin murya mai daɗi" bai kulata ba ta ce "Daman ka iya waƙa? Malami guda?" A taƙaice ya ce "Malami Sahabi ne? Ba gashi kin yi dry ba" "Don Allah sake mini kaji." Ya miƙe zaune ya ɗauki ƙafarta ya ɗora saman cinyarsa ya shiga danna mata, yana tsananin jin tausayin mace mai ciki, bare Ƴar fillonsa kuma gudan jininsa. "Tab Yaa Sheikh da waƙa!" Ya kame kansa da kyau ya ce "Ki kula, kada a barbaɗi baki mara saiti" "An gama jarumin, gwarzona mijina aljannata kuma ubana duniyata, I love you so much Modibbona" ya girgiza kai kawai. Ta ƙara cewa "Ina son ka" yaji kalmar har ƙasan zuciyar shi, tsigar jikinsa ta tashi wani abu na fisgar shi musamman da cikin Jikinta ya ƙara sanyawa ta dawo kamar ba ita ba, jikinsa ya saki ya yi baya ya kwanta itama ta kwanta tana ɗora kanta a ƙirjinsa ta danne masa ƙafa da ƙafarta ta ce "Yau ba darasi ne?" A hankali ya ce "Ayu ki ka maidani?" Taja hancinsa ta ce "Kawai na san ɗan Ummul da zalama akan darasin auren, baka da haƙuri" neman magana take da abinda za a fara yi masa surutu akai har ya yi shiru sai ya ce "To nace ki huta yau" Ta ce "Ni kuma ina buƙatar ka yau ɗin nan yanzu ma" Mamakin ƴar rainonsa ya gama cika shi ba ko wacce mace ke tarar mijinta kai tsaye ta ce tana buƙatar shi ba, sbd jan aji da iyayi irin na mata, bayan aure zama ne na dindindin, a koda yaushe miji yana cewa yana buƙatar matarsa rana ɗaya zaki iya warewa ki nemasa koda shi ɗin bai nema ba, hakan zai sanya ya ƙara jin son matarsa ƙwarai da gaske a ran shi. "Baki jin kunya?" Tayi fari da fararen idanunta ta ce "Mene abin kunya, kai da ka ke nema kunya kaji? Kullum kazo da ƴar murya, sai ni zanji nauyi? Kenan na cutar da kai na ko bayan kai mijina ne ni kuma matarka ce" ya fahimci dai shi ɗin take buƙata, daman shima tausayinta ya keji nan da nan ya farke rigar barci tare da cilli da ita, wannan lokacin Halisa ta nunawa *Yana Sheikh* Abbanta ita ma macace ta san kan duniya, ta shayar da shi mamaki yana riƙe kansa amma sai da taso sashi yin abin kunya da zarar yaji bakinsa ya buɗe zai ce "Yasubuhanallah Allahu Akbar". Bayan komai ya daidaita ya rungumeta ya ce "Allah ya yi miki Albarka". Da Subhi kusan tare suka tashi ya yi alwala ya sanya Arabian jallabiya da farar hula kansa, abin mamaki yana zuwa ya samu Zahrah zaune saman ladduma tana kallon sama, suna haɗa idanu ya jinjina mata kai tare da rufe ƙofar ya nufi masjid. Misalin 11:00 Zahrah ta fito kusan a tare kuma suka fito da Halisa wacce take jera breakfast a dining room, suka kalli juna Halisa ta ɗauke tana faɗin "Ina kwana?" "Lafiya lou" ta faɗa tana murmushi ta ƙara da cewa "Sannu da aiki, ya jikin naki da kin kira na tayaki aiki ai" Halisa ta ce "Don my me, zan iya" ƙamshin turaren shi ya bayyanar musu da sakkowar shi, Suka juya kusan a tare wani irin kallon ya kewa Halisa da sauri ya ɗauke kai yana gyara zaman alkyabbar shi, Halisa ta daure bata je gare shi ta rungume shi kamar yadda ta saba ba, duk da cewa girkin ta ne amma babu daɗin yin haka gaban Zahrah. Ya ja kujera tare da zama Zahrah ta ce "Ina kwana?" Ya yi mmki domin bata taɓa gaida shi ba bisa ra'ayin kanta. Ya jinjina mata kai Halisa ta zuba masa breakfast kana ta zubawa kanta, Zahrah ma babu kunya taja plast ta haɗa tea. Shiru wajan ya ɗauka Yaa Sheikh yana lura da yadda Halisa ke gumi sbd azabar yaji, ya dubi abinda ta ke ji ganin bai san mene ba, ya saka hannu ya ƙwace plate ɗin ya tura mata soyayyan ƙosan daya sha kayan ƙamshi da tea mai kauri wanda bai ƙarasa sha ba. Ta ce "Nifa shi na keso" Ya ware gajiyayyun Idanunsa akanta ba tare da ya ce komai ba, ta fahimci shirun nasa ta ce "Ɗan silif ne wallahi daɗi sosai Habibi" ya ajjiye bottle water yana goge bakinsa da tissue ya miƙe yana faɗin. "Duk an gama zuba yawo ciki" kamar jira take ta ce "Wata rana sai na ɗore maka yawon cikin baki" Zahrah duk sai ta zama uncountable kamar wata maid, sosai taji yadda suke wasa da dariyar kamar wa da ƙanwa sun birgeta, she wishes ace ita Yaa Sheikh ya kewa haka. Ta goge Hawayen daya zubu mata a ɓoye. Can ya zauna saman kujera ya ce "Jeki Library ki ɗakko ƙawa'idi guda uku" ta ce "To" tana barin wajan ya ce "Fatymerh Zahrah" ta amsa da "Na'am" da hannu ya ce ta zo. Ta miƙe ta dawo wajansa ya kama hannunta ya ce "Kina lafiya?" Ta amsa da "Allahamdulillah" ya jinjina kai yana riƙe da hannunta har Halisa ta dawo, sosai ta gani amma bata nuna ba ta koma gefensa ta zauna suka sanya shi tsakiya, ya buɗewa Zahrah babin da zai musu, yasan Halisa ta sani amma baya son nuna bambanci itama ya amsa ya buɗe mata. Cikin sanyi da taushin murya ya ce. *Babin raɓewa wanka* Ya yi shiru, cikin nutsuwa ya shiga bayanin kamar yadda ya yi wa Halisa lokacin da suke garin Makkah!. Ya ɗora da faɗin. "Akwai wakan jinin haila, Janaba na jima'i, wankan jinin biƙi, wankan juma'a, wankan shiga garin Makkah, wankan mutuwa, shi ne rabe-raben wanka" sukai shiru baki ɗaya musamman Zahrah ya ɗora da faɗin. "Janaba: Janaba ɗaya ce daga cikin abubuwan da suke wajabta wanka, wanda yake hanyoyin kasantuwa da janaba sune kamar haka; *Fitar Mani* Idan maniyyi ya fita daga mace ko namiji to wanka ya wajaba, amma kafin wankan ya wajaba sai ya zama maniyyin ya fitane ta hanyar jin daɗi, kamar kallo ko wasa ko tabe-tabe ko jingina.., amma idan ya fita ba ta hanyar jin daɗi ba ya fitane ta hanyar wahala, kamar ya taka wuta ko harbin kunama ko kuma wutar lantarki ta ja shi, to wannan wanka bai wajaba a kan shi ba sai da kawai ya yi alwala. Shi wannan fitar maniyyi da ake Magana akan shi ko dai ya fita a farke ko kuma ya fita ana barci, idan ya fita ana farke shine ake maganar an ji dadi ko ba'a ji ba, amma idan ya fita ana barci ne to ba wata maganar jin dadi wanka ya wajaba" Yanayin yadda yake bayanin kaɗai ya isa ka fahimci magana bata dame shi ba, shi ya sa gabaɗaya ko wa'azin shi za'a tura mutum ake jinsa muryarsa mai sanyi ce cikin haiba ya ce "Na biyu, saduwa da iyali idan har an tabbatar miji da mata sun zama turmi da taɓarya babu shakka wanka ya wajabta a gare su, inma namijin ya fitar da maniyyi ko mai fitar ma haka ma macen, idan mutum sai sadu da Iyali sau goma to wanka ɗaya ne ba goma ba.Idan mutum ya sadu da mace kuma yake so ya jinkirta wankan janaba zuwa an jima to abinda zai yi shine ya yi tsarki sai ya yi alwala, domin alwalar tana rage kaifin janaba, sannan kuma tana kara kuzari lokacin da ake so aƙara saduwar. Idan mutum ya sadu da mace sai bai fitar da maniyyi ba wanka ya wajaba akanshi kamar yadda bayani ya gabata, to bayan ya yi wankan sai kuma ya ga maniyyi ya zubo, to anan idan wata sabuwar sha'awace ta fitar da wannan maniyyin wani wankan ya kama shi, amma idan janabar da ya yi wa wankace maniyyinta ya zo yanzu to alwala kawai zai yi" Ya rufe littafin yana amsar ruwan da Zahrah ta miƙa masa ya sha kaɗan ya ajjiye ya ce. "Mu tsaya nan, sai gobe In shaa Allah, kafin nan ga yadda ake wanka" Suka kalle shi ya kame fuska ya ce "Wankan Janaba yana da siffa guda biyu: Akwai siffatul ijza' (ta wadatar), kuma wacce ake kira siffatu kamal' (ta kamala). Wankan Janaba a siffar sa ta kamala shi ne: Idan kazo zaka yi ko za kiyi wanka ga ruwa a gabanka. Farkon abin da zaka fara yi shi ne: zaka karkato bakin mazubin ruwanka, ka wanke hannunka sau uku, sannan sai ka tsoma hannu a cikin ruwan sai ka ɗebo ka wanke gaban ka, a dai-dai lokacin da zaka wanke gaban ka a lokacin zaka kulla niyya ta wankan janaba (Ko waninsa) wanda yake wajibi ne, idan ka wanke gabanka ma'ana kayi tsarki kenan to daga nan kuma sai kayi alwala irin yanda kake alwala ta sallah, abin da duk kake a alwala ta sallah zakayi sai abu ɗaya shi ne wanke ƙafafuwa to wannan zaka kyale shi ba zaka yi shi ba, to daga nan sai ka tsoma hannunka guda biyu a cikin ruwan ba tare da ka ɗebo ruwa ba sai ka murmurza kanka saboda ko wanne gashi da ya buɗe a lokacin da maniyyi yake kokarin fita daga jikinka ya koma yanda yake, don gashin dan Adam yakan buɗe musammam gashin sa na ka, idan ka zuba ruwa a haka na iya haifar maka da ciwon kai ko wani abu daban, bayan haka sai ka ɗebi ruwa a cikin tafin hannun ka ɗaya sai ka zuba a kanka ka tabbatar ya game ko'ina a kanka, ka sake kanfata na biyu ka tabbatar ya game ko'ina a kanka, haka na uku ka tabbatar ya game ko'ina a kanka. To idan kayi wannan sai ka ɗebi ruwa ka game dukkanin jikin ka da shi kana mai farawa da ɓangaren jikin ka na dama kafin na hagu, sannan na hagu ka tabbatar ruwa ya taɓa ko'ina. To idan kayi wannan ne ka kammala,abu na ƙarshe shi ne sai ka wanke kafar ka ta dama sannan kafarka tahagu shine cikon alwalarda ka riga ka faro. Wannan ita ce siffa ta kamala a wankan janaba. In wankan janaba ne haka zakayi, in na haila ne haka za'ayi inma wanka ne na biƙi haka mace zata yi, idan wankan jumu'a ne ma haka za'ayi, wankan idi ma haka zaka yi, banbanci kawai shi ne NIYYA" Halisa ta kama hannunsa ta ce "Allah ya saka da alheri Yaa Sheikh, Allah ya ƙara basira da ilimi mai amfani ya sa matar malam ta ɗauki halin Malam" Ya girgiza mata kai, Zahrah ta goge hawaye a ɓoye ta ce "Thank you so much Sweetheart really appreciate" Ya miƙe tsaye yana gyara zaman alkyabbar da hiramin kan shi ya ce "Allah ya yi muku albarka" Halisa ta miƙe tana maƙalewa gefensa ta ce "Zan raka ka mota" Bai ce komai sukai waje Zahrah ta bisu da idanu, addu'a Halisa ta dinga yi masa kala-kala harda yaji tsoran Allah akan yadda zai taraya dukiyar shi. Kai tsaye Police station ɗin da ya kai Saif-wazir ya nufa, ya cike komai aka bashi beli damar kamar ajjiyar shi ya kai, ya nufi gidan Abba Hakimi lokacin Umar-khan ya shigo tare da iyayen yarinya da hisba suka kama, uwar yarinyar ta dinga kuka kamar ranta zai fita shi ma kan shi Saif-wazir ya yi laushi ko haɗa idanu ba ya yi da *Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu* kai tsaye kuma Yaa Sheikh ɗin ya nuna auren Saif-wazir zai haɗa da yarinyar Abba Hakimi ya amince, suka tsayar da maganar nan da sati mai zuwa ranar juma'a za a ɗaura auren. A nan Abba Hakimi yake shaidawa Yaa Sheikh an bawa Khalil Ahmad Nuran Sarki auren Maimoon domin ya gaji da sintirin da yake daga Sokoto zuwa Kano, don haka rana ɗaya za a ɗaura koda Maimoon bata tare ba. *_3 weeks ago_* Har kawo lokacin babu abinda ya haɗa Zahrah da *Yaa Sheikh* haƙurinta ya ƙara bayyana, bata sake masa maganar komai Halisa cikinta ya girma sosai domin kusan wata na takwas yake ta kusa shiga na tara ta zama babbar mace. Abu ɗaya ke damun Zahrah yadda take yawan mafarkai da jarirai guda uku suna binta suna kuka duk inda tayi suna maƙale da ita ɗaya hannunsa riƙe da almakashi, ɗaya safa, ɗaya kuma da magani duk ta firgita kuma ta kasa faɗawa Yaa Sheikh. Wani lokacin suna zaune zata sabura tana "Don Allah kuyi haƙuri ban sanku ba, ba yara na bane" al'amarin kamar wacce zata zauce. Satin daya kama Yaa Sheikh yaso kai Halisa Sokoto can masarauta amma girman cikinta ya hana shi, ya ɗauketa ya kaita wajan Umma A'isha, Zahrah kuma ya ce ta shirya su je Yola ta nuna bata so ko kamar iyayenta bata ƙaunar ya yi, sai da ya yi mata jan idanu ta amince. Yaa Sheikh da Ummul da kuma Zahrah suka nufi Yola, gaisuwa kawai ke haɗa Ummul da Zahrah suna zuwa suka sauketa a Jimeta. Suka shige Rugar Bello, har inda Layar take Ummul taje ana haƙowa ta buɗe tas taci karo da rubutu kamar haka. *_Kariya ne daga dukkan jinin mai wannan layar, babu shi babu aikata zina, duk inda zina take mu aljanun Arɗon Rugar Bello mun haramtawa jinin Arɗo raɓar inda take, ko ya haɗu da makira wacce ta aikata hakan to mazantakar shi ba zatai aiki ba, matarsa wacce take tsarkakkiya a gare shi ita ce zata same shi, babu mai iya lalata wannan aikin domin wanann layar bata gaskiya ba ce, ta gaskiyar na wajanmu Wannan shaida ce domin ku sani, idan wanda ya mutu zai dawo to lallai mazantakar shi wata rana zatai aiki, idan wanda ya mutu ba zai dawo ba babu shakka shi da wanda ya ke zina ko ya taɓa har abada...... *Note* _Masu magana akan auren Yaa Sheikh da zata ba zai taɓa faruwa a zahiri ba,to wallahi wallahi za kuyi ladama kuma za kuyi kaffara ku saisaita rantsuwarku ni ke da labari na fiku sanin mene zai faru, babu hujjar da zata saka littafi ya ƙare na dinga jansa bisa jin daɗina rubutun nan da wahala ba, komai ma rubuta daman a tsare a yake sai abinda aka cire..... Nayi magana akan wanka na tsagaita bayanin nawa sbd nauyin wata maganar amma ku bincika littafan Fiqhu, ko Umdatul ahhakam_*_Arewabooks@Na'ima Sulaiman Sarauta76_* "So that's the reason?" Ummul ta faɗa a ranta tana ƙara kallon rubutun, Yaa Sheikh ya kalleta kawai, sai kuma ya miƙa mata hannu ta bashi shi ma ya karanta kamar yadda tayi. Sai taga sam bai damu ba, ko dan ba a gane damuwar shi ne ya sanya haka? shi ɗin kaifi ɗaya ne kuma mai wahalar fahimta, wannan magana ce mai matuƙar nauyi Yaa Sheikh kuma ya kasance namiji ba mace ba, bare ta tsaya su tattauna makomar Zahrah take tunani, bata jin yarinyar a ranta amma tana girmama auren dake tsakaninta da Yaa Sheikh ɗin, infact Ummul bata ɗauki Zahrah matsayin,Daughter-in-law ɗin ta ba. Ummul tabi bayan Yaa Sheikh zuwa cikin Rugar Bello domin daga baya ne inda aka ɓoye layar take tana zuwa ta samu Yaa Sheikh shi da Labo suna magana wanda ya wancin maganar Labo ke yinta Yaa Sheikh jinjina kai kawai yake sbd tsananin gajiya, akwai tarin abubuwa a gabansa baya jin zai zauna a Rugar Bello zuwa wani lokaci. Wata Bukka Labo ya nunawa Yaa Sheikh ya durƙosa tare da shiga ciki bakinsa ɗauke da Tasbihi. Ya zauna saman wata tabarmar kaba yana tankwashe ƙafarsa, Ummul ta shigo ta zauna ba jimawa aka kawo musu Kindirmo fal cikin ƙwaya da zafinsa, tsananin daɗin Kindirmon ya sanya Yaa Sheikh rufe idanu ya sha son ran shi a lokacin kewar mahaifinsa da matarsa ne suka lulluɓe zuciyarsa. Ummul ta ce "To ɗan na gada, sai yanzu ka ƙara fitowa matsayin Fulanin Yola Usul kuma cikakke, Fulanin ma ɓangaren makiyaya masu dukiya" Ya dubi Ummul ɗin tasa yana janye ƙwayar ya ce "Fulani da Barebari ba a zama lafiya fa naji" "Wani ya ce maka ni barebari ce?" Ummul ta faɗa tana watsa masa harara ya yi murmushi kawai yana lumshe idanunsa, a wannan daren Yaa Sheikh ya zauna da ƴan uwansa Fulani ya shaida musu baya buƙatar maye gurbin mahaifinsa kawai su kasance masu adalci wa juna, banda ƙyashi da hassada, Yola ita ce mahaifar shi duk da ba a nan aka binne cibiyar shi ba. Washegari suka ƙarasa Rugar Rome, yaso da ƴar fillonsa ya zo idan akwai abin da ba zata manta ba, shi ne rayuwar da tayi a cikin wannan Rugar, da dukkan wanda yake cikinta ba zata manta da su ba. Shatu ta ƙara girma da wayo, Ummul ta tambayi umarnin tafiya da ita aka bata, zo kaga murna wajan Shatu. Zahrah ta share hawayen idanunta ta kalli Mimi ta ce "Baki taɓa zaunar dani kince abin da nake ba daidai ba ne, kina cewa na maida hankali a karatu amma me ya sa ki banbanta mini karatun boko dana addini, baki nuna mini yadda zan samu lahira ba sai ki ka nuna mini yadda zan san duniya, ita ma ta sanni" Ta fashe da kuka sosai numfashinta na riƙewa Idanunta ya yi jajir cikin zaucewa ta ce "Nayi rayuwa irinta dabbobi, na zama jahila na kuma zauna cikin jahilanci, kun cutar da rayuwata tun ina ƙarama da wando da riga na buɗe idanu da sunan sune kaya na, ina 4yrs kuka sani play grp, na san kun sani islamiyya ban san yaushe na daina ba, ban kuma san dalilin daya sanya na daina ba, ina shigar da bata dace ba, ina fita inda nake so kina ganin sauyi a jikina amma baki taɓa cewa fitar da nake bai dace ba....," Yaa Sheikh dake bakin ƙofa shi da mahaifin Zahrah Alhaji Farouk ya ce "Kee!!" Ya faɗa cikin ɗaga sauti, hakan ya sanya ta tsaya da maganarta fuskarta tayi caɓa-caɓa da hawaye ga majina ta ce "Sweetheart ranar wanka ba a ɓoye cibi, duk halin dana shiga she's the reason behind" "Ki fahimta Zahrah, bayin kai na ba ne soyayyar da muke miki ya sanya idanunmu ya rufe bama son damuwarki, bama son duk wani abu da zai baki matsala a rayuwa, tunanina kullum zamu rasaki" Zahrah ta fashe da dariya while kuma hawaye na zuba daga idanunta ta ce "Gaskiyar bahaushe, daman ance ka ƙi naka duniya ta so shi, kaso naka duniya ta ƙi shi, tun banje ko'ina ba ina ganin ishara kala-kala a duniya, Ubangiji ya fara hukuntani da soyayyar wanda bana ran shi, kullum ji nake zuciyata kamar zata fashe naji kamar na bar gidan Yaa Sheikh" Ta girgiza kai ta ce "Soyayyar da nake masa ta rinjayi duk abinda zuciyata ke raya mini, motsin Yaa Sheikh kawai idan naji yana sauƙaƙa mini ƙuncin da kuka jefani da halaka na tsayin shekaru, balle nayi tuzali da fuskarsa sai naji iya hakan kawai ya wadatar dani" Ta miƙe tsaye tare da dawowa wajan Yaa Sheikh ta ce "Ba miji na ɗauke shi ba, ina masa kallon Yayana ne, wanda zai iya tsare mutuncina, ya fito dani daga ranar da kuka sanya ni zuwa inuwa, na gane bambanci mai ilimi da jahili na gode Allah da bai barni na dauwama haka ba, balle na zo duniya a banza na koma a iska" Tas ta goge hawayen idanunta ta ɗauki mayafi ta yafa ta ce "Muje Sweetheart" "Fatymerh Zahrah!" Yaa Sheikh ya furta iya gareta, ta kalle shi sai tayi murmushi ta ce "Wallahi ba zan ƙara kwana a gidan nan ba, kuma daga yau su ɗauka basu taɓa haihuwa ba balle su tuna suna da yarinya kamata, wannan shi ne girban abin da suka shuka" Mimi ta fashe da kuka ta kasa magana ta zube a wajanta ta ce "Ni ɗin wacce irin uwa ce mara lura da tarbiyya me zan faɗawa Ubangiji" "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Alhaji Farouk ya furta, yana cikin masifa goma da ashirin. Ta kama hannun Yaa Sheikh dake tsaye bai tanka musu ba, ya juya ya bita zuwa compound Ummul na zaune cikin mota domin daga nan Airport za su shige, ta dinga kallon Yaa Sheikh da mmki ya shaida mata a nan gida zai bar Zahrah amma ya akai suka fito tare. Zahrah ta saki Yaa Sheikh ya dubeta cikin nutsuwa da tarin kulawa yana ɓoye yanayin da yake ciki ya ce "Iyaye fa?" "Na yafe musu, nima yafiyar Ubangiji nake nema ko zaka dubeni da idanun Rahama ka tuna nima matarka ce ka bani kulawar da nake so" "Ina son barinki nan" ta kalle shi da mmki sai ta ce "Zaka iya barina, amma kana fita zan fita zanje duk inda Allah ya nufa na san ba zan wulaƙanta ba, amma yanzu kai Allah zai tambaya tunda ina ƙarƙashin ka" Ya rasa bakin yi mata bayani ta fashe da kuka sosai ta tsuguna daidai ƙafarsa ta ce "Ni ɗin daman ai ƙaddarar ka ce, amma don Allah kaji tausayina ko zauna dani kulawarka kawai na keso ba wani abu ba" ta ƙara sakin wani raunataccen kuka mai ciwo da cin zuciya ta ce "Tun ina jin haushin Matarka har na dai na, ganin son da ka ke mata na fara son ta ko za kaji tausayina" ya numfasa yana riƙe kansa dake sara masa. "Stand up" ya faɗa a taƙaice. Ta ƙasa miƙewa sbd kukan da yaci ƙarfinta ya saka hannu ya miƙar da ita, tana tashi ta faɗa jikinsa ta ce "Rayuwata bata da amfani Yaa Sheikh nayi ladama, soyayyarka zaka kashe ni" jin numfashinta na fita da ƙyar yana ɗan bata side hug yana bubbuga bayanta alamar rarrashi. Ta shiga sauke ajjiyar zuciya a hankali ya zareta suka nufi mota ya nuna mata gaban mota, shi kuma ya shiga baya kusa da Ummul suka nufi airport. Alhaji Farouk yana tsaye ya zama kamar statue yaji ƙarar notifications yana dubawa yaga an zare kuɗi daga acct ɗinsa kuɗi masu yawan gaske. Kafin ya motsa bank sun kira shi sun bashi tabbacin ya samu hackers sun kwashe masa kuɗi, gumi ya dinga yanko masa yana zubewa wajan. Kafin ya ƙara wani tunani manger kamfanin shi ya masa waya yanzu haka kamfanin ya kama da wuta. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un wayo Allah Allah na tuba Allah ka tausaya mini Allah ka dubi idanuna ka yafe mini" ya dinga faɗa yana fashewa da kuka. Karayar arziƙi ta dimfaro shi..... A hankali yake ware idanunsa akan harabar Orphanage ɗin na shi cikin nutsuwa da tarin kamala ya murza yatsun hannunsa yana duba lokacin tare da tunanin inda Umar-khan ya tsaya, slowly ya ɗago kan shi cikin sa a ya sauke idanunsa akan Umar-khan shi da Hafsat suna hira kamar sun jima da kamuwa da junansu, Ya girgiza kai kawai tare da komawa ya jingina da jigin motar shi. Beeherh ta taho da gudu ta ce "Abbana shi ne tun daga ranar nan baka dawo ba, kuma Mumy bata zo ba?" Ya durƙosa ya ɗauketa yana kallon Kyakkyawar fuskarta ta yarinyarta ga baby hijab a jikinta ta saka hannu ta fara wasa da gemun shi ta ce "Ni yau wajan Mumy zan kwana" Yaa Sheikh ya fesar da numfashi ya ce "Rigima Beeherh,yau za kiga Mumy" daidai lokacin Umar-khan ya ƙarasu Hafsat ta durƙusa ta ce "Ina yini Abba" ya jinjina mata kai yana buɗe bayan mota tare da saka Beeherh ciki, Umar-khan ya shafa kan shi ganin kallon da Yaa Sheikh yake masa. Cikin rawar murya ya ce "Uhm dama....dama...dam" "Mene haɗinku?" Yaa Sheikh ya katse kunyar Umar-khan cikin inda inda ya ce "Yaa Lee ina son Hafsat ne, ina son aurenta idan ka bani dama" Yaa Sheikh ya kalli Hafsat ya ce "Kina son shi?" Ta kasa magana sbd kunya ita duk duniya ta yarda ta kuma amince Yaa Sheikh shi ne babanta domin a wajan shi ta tasu "Uhm" Sanin halinsa tayi saurin cewa "Eh Abba" tana faɗa ta kwasa da gudu tayi ciki. Ya girgiza kai, Umar-khan ya buɗewa Yaa Sheikh mota ya shiga, daman yau gabaɗaya kamfanin shi dake kano ya zaga wanda suke wata jahar ne bai je ba....kafin su zo gida Beeherh tayi barci Halisa dake zaune a parlour da ƙaton ciki haihuwa Yau ko gobe ta miƙe da ƙyar tana riƙe kujera cikin saurinsa ya ƙarasu tare da kwantar da Beeherh ya kama Halisa ya zaunar da ita a ƙasan carpet ya ɗauki pillow ya saka mata ta ɗora ƙafarta tayi murmushi tana jan hancinsa ta ce "Na gode Yallaɓai" Ya zauna yana danna mata ƙafar cikin tsananin so da kulawa wacce kullum take ƙara yawa a zuciyarsa ya lumshe idanunsa jin tayi masa wlcm da zazzafan kisses ɗita tun daga bakinsa har zuwa wuya suka kalli juna ta ce "Sannu da zuwa" Ya jinjina kai sbd ya gaji da gaske, gashi bashi da burin fita wata ƙasar. Ta kalle shi ta ce "Yarinya muka samu?" Ya kalli Beeherh dake barci a nutse ya ce *"Beeherh Sheikh Aliyu haydar Aliyu"* ta ce "Yaa Sheikh mai yara da yawa" Yana shafa cikinta idanunsa tuni ya juye ya ce "Ina son yara, sosai ina son nawa na kai na sama da ashirin" ta zare idanu ta ce "Ashirin tab" Zahrah dake fitowa hannunta riƙe da Azkar ta ce "Haba Uwar gida kada ki zama raguwa mana" Halisa ta ce "Ba wani nan, kiyi masa hanya kawai ya ƙara aure" Yaa Sheikh dai idanunsa a rufe yake ya ce "Kwana biyu na lura Fatymerh Zahrah tafi jin tausayina" Ya miƙe tsaye Halisa ta miƙe suka haura sama suna shiga ta cire masa rigar jikinsa ya jawota ya baya tare da mannata a ƙirjinsa idanunsa rufe yake sauke mata wasu lafiyayyun kisses masu wahalar fassaruwa ya saka hannu ya farke bra ɗin jikinta ya ƙara farke under wear ɗin cak ya ɗauke zuwa toilet ta ce "Mene haka kuma" ya ciji kunnenta ya ce "Wanka zaki mini".... Mother na zaune a parlour hankalinta gabaɗaya baya jikinta ta ce "Maimoon bi bayan Fattoumah" Maimoon ta ce "Mother kin san halin Auta da sanyin jiki daga kai abinci sai ta zauna" Father ya ce "Haba Maimunatu jeki mana" ta miƙe tsaye tana fita Compound El na fitowa daga mota sanye da kayan police ya yi wani irin kyau ta ce "Uncle El da yamma" ya taɓe baki kamar zai shiru ya ce "Ban waje wajan Fattoumah na zo" Maimoon ta ce "Komai Fattoumah idan tayi wari za muji" El ya buɗe mata idanu ya ce "Ke kuma munafuka halinki ɗaya da mijin naki ai" ta rufe baki ta ce "Au kana Nufin Prince Khalil munafiki ne?" Ya mata banza tayi dry kawai ta nufi bakin ƙofar ɗakin gatekeeper ta ce "Baba Fattoumah data kawo maka abinci fita waje tayi ne?" Shiru ba amsa ta ƙara magana shiru, sai kawai ta tura ƙofar wata irin gigitacciyar ƙara wacce ta cika compound ɗin ta fasa hakan ya sanya El fitowa da bindiga a sukwane, da gudu Mother da Father suka fito El-bashir ya ce "Ke lafiya?" Banda rawa da ɓari babu abinda jikinta ke yi ta kasa magana, El ya shiga cikin ɗakin kai tsaye idanunsa ya sauka akan Fattoumah dake kwance an ɗaureta da igiya an rufe bakinta da wani abu, jini na zuba ta ƙasanta alamar fyaɗe akai mata...... *Masu tambayar complete book's ɗina👇🏾* Tsintacciya 500 Uncle ne 400 Sirrin mu 500 Abu maleek 500 Sai na aureta 300 Izzar so 300 The new emir 300 👇🏾 Zain Abeed 1,23 ₦1000 Dare da duhu 1000 Idan ba ke 1000 08119237616👈🏾 kuyi magana WhatsApp.*_Arewabooks@Nimcyluv77_* *Women Adviser* *Elegant online Writer's leader* *Hausa Novelist* *Social media presenter, Ngo, human rights* Follow the link👇🏾 https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL El-bashir was shocked ya kasa motsawa duk da kasancewar shi Namiji, kan shi ya yi wani irin sarawa zuciyarsa na harbawa, idanunsa sukai jajir wani irin ruwa ya kwanta a cikinsu, ya ɗauke kai da sauri daga kan Fattoumah wacce take numfashin wahala. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Ya furta a fili. Cikin sauri kuma ya shiga ciki yana durƙosawa yadda Fattoumah take kallon El-bashir babu ƙifatawa ya ƙara sanyawa El wani irin tashin hankali a fuskar shi aka ajiye masa tabon da har abada ba zai taɓa gogewa ba, his whole body was shaking zufa na yanko masa all over his body. "Fattoumah!" Mother ta kira sunanta a gigice tana ɗora hannu a ƙirji lokacin da El yake kunce igiyar jikinsa tare da zare abin da aka sanya mata a baki. Mother ta saki kuka tana cewa "Allah ya isa, Allah ya isa, Allah ya isa Ubangiji ya saka miki Mamana ko Uban waye shi wallahi sai nayi Shari'a da shi" Ta ƙara sakin wani kukan tana riƙe Maimoon da Zeefa gani take kamar suma haka zai faru da su yanzu. Ta ƙanƙame su a jikinta ta ce "Ya Allah wacce irin rana nake gani yau ni Maryamu, wacce jarrabawa ce me ya sa na aikeki wajan mugu azzalumi Fattoumah, me ki kai masa ya zaɓi ya lalata gobenki da rayuwarki bakiɗaya Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Ya Allah da ganin Wannan ranar gwara mutuwa ta" "Mother ki daina faɗar haka ne ya samu Fattom, me akaiwa Fattom jini ke zuba a jikinta" Zeefa ta faɗa yarinyar ta gigice da ganin ƴar uwarta cikin wannan halin. "Maimoon riƙe Nazeeferh ki tabbatar kin kula ku shiga cikin gidan yanzu" "But Mother" a gigice ta ce "Maimunatu!" Maimoon ta fashe da kuka ta rungome Zeefa suka bar wajan. Father was speechless yana ganin idan akwai wanda Mother za tayi Shari'a da shi to babu makkawa shi ne, domin daman sharri ɗan aike ne, kan me shi yake bi. Faɗin Ubangiji ne, ita zina bashi ce dole ka biya da hannunka, kama ta diìna tû danò. Abin da ya shuka yake girba, kashin kajin daya shafuwa kansa ya shafi yarinyar da bata ji bata gani ba, yarinyar da babu wani kyakkyawan kusanci tsakaninta da shi, tana ƙyamatar duk abin da zai, tayi masa tsana ainun tun akan Yaa Lee, da ƙyar ya samu ya lallaɓa ta dawo yadda suke. Ya saki kuka. "Laifi na ne, it's all my fault kiyi haƙuri Fattoumah" El ya ɗauki Fattoumah ganin yadda take ta razana ta kuma kafe shi da idanu kamar wacce take jira ya taimaketa, bai ji nauyin Mother ko Father ba ya shiga mota tare da ita a jininsa cikin sauri Mother ta nufi gida tana ɗaukan mayafi da key car. Tasan yadda El yake a fusace da wahala ta same shi, Father ya ce "Jirani mu tafi tare" Tayi masa wata muguwar harara tare da yin ƙwafa ta shiga mota tana danna horn ta mance babu gatekeeper babu alamun shi. Bai taɓa jin ladamar abinda ya aikatawa Zahrah ba sai yanzu, kunyar haɗa idanu da duk wani na shi yake uwa uba kuma Mother wacce yake jin babu wacce zai kaita jin zafin abinda ya faru idan akwai bai shige *Prince El-bashir Ahmad Nuran Sarki* ba. Ya jima da fahimtar shaƙuwar dake tsakaninsu ba wai iya haɗuwar jini bane, hadda abin nan da ake kira da _Blind love, first love between heart and heart_. Bai san ya akai ba, kawai ya ganshi ya yi parking a harabar Aminu Kano teaching hospital! Ya buɗe mota muryarsa was shaking ya ce "Nurse, Nurse, Dr" Cikin sauri wasu Nurse's suka zo suna janye da gadon marasa lafiya ganin shi ɗauke da kyakkyawar budurwa or under age baby, Fattoumah. She's 14 yrs old going to 15 amma tana da jikin girma so ma sha Allah, kaf cikinsu tafi kowa fuskar kamala tana da idanu masu sanyi bata son hayaniya, but she's so cute damn cute irin shhhhh ɗin nan.. Tana da kafiya da zuciya hakan yasa suke zaune da El lafiya komai ta ce Uncle ɗina ko tana kuka Mother ta ce ke da waye? Sai ta ce " *UNCLE NE*" Suka amshi Fattoumah daga wajan El wata ta ce "Sir You have to change your clothe ya ɓaci da jini" A dame ya ce "Owk" was what she's sayed to him. Ganin El da police uniform ya sa basu tsaya tambayar police cikin Raped case ɗin ba. In few minutes El ya kira Sergeant ya shaida masa, Sergeant ya kira C.F.P Commissioner of Police. Daga nan ya kira Human rights, wanda suke da haɗin gwiwa da Ahip tare da Ngo. Yana nan tsaye Mother ta ƙarasu a gigice ta ce "Mubasshir Ina Mamana" "Clam down, she'll be fine" ta dafe kai tana kuka ta ce "Mubasshir ina cikin tashin hankali, ace mai gadin gidana the old man ya yi rapping ƴar cikina, mai yasa har yanzu ba a maganin masu fyaɗe ne? Zan tabbatar daga kan Fattom babu wanda ya ƙara aikata fyaɗe a jihar Kano" Ta rushe da kuka ta ce "Ya lalata rayuwar Fattom gobenta nake ji wacce irin jarrabawa ce, mai yasa baƙin halin Ubanta zai sauka kanta?" Ya kama hannunta har zuwa emergency ɗin ya zaunar da ita, ya kasa cewa komai zuciyarsa ta tsaya da aiki ya zama kamar wani statue..... Yaa Sheikh ne ke tafiya cikin kamfanin sarrafa shinkafar shi yana mai lura da komai, cikin nutsuwa yake jinjina kan shi yana sauraran abin da Umar-khan yake faɗa masa. "An kammala komai gobe za a fitar da container goma, kafin zuwan azumi dai zamu fitar da containers kusan 200" he just nodded his head. Silent ringtone ne ke tashi ya zura hannunsa cikin aljihu ya ɗauki wayarsa Samsung ganin sunan wanda ke yawo saman wayar ya sanya ya yi jim yana tunani gently kuma ya yi answering call ɗin yana lumshe gajiyayyun Idanunsa tamkar mai jin barci. Ya kara a kunne. "Mubasshir Ahmad Nuran Sarki" Yaa Sheikh said. Sbd jin El ya yi shiru sai ajjiyar zuciya yake saukewa, a hankali kamar zaiwa Yaa Sheikh kuka ya ce "Abba" "Speak,Son." Cewar Yaa Sheikh yana mai da hankalinsa zuwa ga wayar sbd raunin El daya bayyana ta ciki. "Amma zuciyata babu daɗi, anci mutuncin wacce a keso nake burin aura Abba" Yaa Sheikh ya yi shiru yana jin maganganun ya kasa fahimta. Halin Yaa Sheikh daya sani ya sa El ya ce "My girlfriend was raped" ya ƙara da faɗin "I mean Fattoumah" Ya runtse idanu, yana kiran sunan Allah a zuciyarsa cikin kamala ya ce "Where are you now?" "At hospital, Aminu Kano teaching hospital" ƙit, ya kashe kiran yana juya zuwa harabar kamfanin nasa hannunsa ɗaya riƙe da Alkyabbar jikinsa ɗaya kuma yana shafa gemunsa, Umar-khan ya biyo bayansa da sauri tare da buɗewa Yaa Sheikh bayan mota, shi kuma ya nufi gaban mota tare da yi mata key suka nufi hospital. Cikin ƙaramin lokaci Family suka san abin da yake faruwa, hatta Dada ta bata garin kano al'amarin ya risketa, Abba Hakimi ya dubi Mother ya ce "Ina ne garin su Mai gadin?" Idanunta ya yi jajir ta ce "A Ɗan-batta yake" Ya dubi Ishaq-Hakim ya ce "Amshi Address da komai, na yi magana da police kaje ayi arresting nasa" "To, Abba." Ya fita waje, Yaa Sheikh da kansa ya ƙara duba Fattoumah tare da yi mata ɗinki yadda yake girgiza kai da yadda idanunsa sukai jajir zaka san cewa zuciyar Maza Aliyu ta motsa. "Uhm ba kullum ina faɗa ba ana mini kallon ƴar hau, ƴar guguwa? Kawai ka ɗauki ƙaton banza a gidanka kace wai mai gadi bayan kana da zataran ƴan mata balagaggu a gidan" ba wanda ya kula Jadda ta ƙara cewa "Ga irinta nan, kayi mugun gado ita daman zina rance ce ka fara biya duk akan Zara'u Allah yaga son da na kewa yarinyar nan wallahi da Munari ce ba zan damu ba" Ta fashe da kuka sosai tana matse ƙwalla ta ce "Masifa yanzu Haruna idan babu damuwa kawai ka tattara yaran nan ka riƙe wajanka ina tsoran a ɗirkawa wata ciki a gidan nan, shi ya sa ake son mutum ya aikata abu mai kyau ba komai yake zama ƙaddarar bawa ba, hadda son zuciya, kayiwa ƴar wasu anyiwa taka" "Jadda ki daina wannan maganar" ta miƙe tana kallon Uncle Bashir ta ce "Algungumi gaskiya ce baka son na faɗa ko? ai dama ƙawata Didi na nan tabbas da mun haɗu munci mutunci ko wanne ɗan banza, ai duk tare mukai ƙuruciya tasan halin uban baku club club ba wanda bai sani ba a faɗin jihar Kanon dabon lijeriya" "To Allah ya kyau" "Ya kyauta abin da ya fi haka ai, kawai ya cuci yarinya ni wanda zai aureta nake tunani, mazan yanzu daba kunya gare su ba" "Ko yanzu aka ɗaura mini aure da Faɗimerh na shirya" Jadda ta kalli El ta ce "Allahu Akbar, kun wanda bai damu da duniya ba ko? To ubanwa zai hanaka auren Zara'u" Fitowar Yaa Sheikh daga cikin wani emergency room ya sanya Jadda yin shiru tana kallon Yaa Sheikh wanda ya ƙara cika idanu fiye da baya, bai kula kowa ba ya nufi wani office kai tsaye yana dafe kansa yadda yaga jikin Fattom ya yi ya sanya shi shiga cikin tashin hankali, baya son depression and stress su kama shi, Ya rufe idanu da kyau da sauri ya buɗe ganin yadda yake hasko cin mutuncin da tsohon ya yiwa Fattoumah. Zuciyoyin kowa babu daɗi babu kamar Barrister Maryam da IGP kuma Prince El-bashir Ahmad Nuran Sarki. Tana ganin an gama lalata rayuwa da goben ƴarta, abu ne wanda kan iya zama tabo a zuciyar Fattoumah za kuma taji zafin mahaifinta Father da gaske idan ta san cewa shi ne sila, El yana ganin kamar shi aka ruguzawa rayuwa anci mutunci his fiance, an lalata kima da darajar uwar yaran shi... Halisa na zaune gabaɗaya yau bata jin daɗi ko sallah a zaune take cikinta ya sakko ƙasa sosai tun safen kuma ruwa ke fita a jikinta gudun kada ta tayar da hankalin Yaa Sheikh ya sanya bata gaya masa ba, shima ya lura sai ya kawo rikici ne kawai irin nata domin tun jiya faɗa take ji da shi abu kaɗan zata ce ita ba haka kai ni ka fita ma daga ɗakin kawai, ya kan lallaɓata a samu zama lafiya. A lokutan ya dawo dayin azumi cikin kullum yana lazumtar ko wacce rana gudun faɗawa halaka, baya iya kusantar Halisa sbd condition ɗin ta, Ga Zahrah zero take gare shi baya iya komai. Zahrah dake kallo ta dubi Halisa data ɗan ja tsaki ta ce "Lafiya kike dai ko?" "Uhm lafiya" was abinda ta ce. Wayarta ta ɗauka ta kira Mother tana ta ringing ba a amsa ba, can ta kira ta Maimoon babu jimawa ta ɗaga jin muryarta babu daɗi ya sa cikin dauriya Halisa ta ce "Moon lafiya?" Maimoon ta fashe da kuka ta ce "Mai gadin Gidanmu ne ya yiwa Fattom fyaɗe" Halisa ta miƙe tsaye sai kuma ta ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Wani irin murɗewa mararta tayi, lokacin guda bayanta ya riƙe ta kasa motsawa cikin tashin hankali ta yarda wayar sbd tasowar wani irin masifaffan ciwo mai kama dana mutuwa a firgice ta ce. "La'ilaha illallah Muhammadur Rasulullah S.a.w wayo bayana wayyo Abbana zan mutu" zufa ta shiga yanko mata cikinta ya shiga rawa da ɓari na tsananin ciwo. "Subuhanallah ba dai naƙuda ba Halisa" "Kira mini Abbana mutuwa" Zahrah ta gigice tausayin Halisa ya kamata domin bata mance wahalar data sha lokacin haihuwar Muhammad ba, Halisa na kuka Zahrah na kuka suka rasa yadda za suyi, cikin sa a Zahrah tunani ya faɗo mata har zata kira shi da number sai tayi tunanin idan da number Halisa ta kira zai fi ɗagawa, tana ɗauka ta shiga ɓangaren calls babu wasu kira sai number ɗaya wacce a rana sai ayi waya goma da number babu suna sai Double kisses a jikin number tayi kiran number ba jimawa ya ɗauka, cikin nutsuwa daman kiran nata yake jira jin shiru ya sanya Yaa Sheikh sauke numfashi yana rufe idanunsu tare da lafewa jikin kujera ya ce "Kankanaty" "Ba ita ba ce" Ya zaro idanu sai kuma ya basar ya riƙe kansa da kyau ya ce "Sorry Wife" "It's okay, Halisa wanted to speak with you" "Oh!" Ya ce yana rufe idanu jikinsa ya saki. Ihun! Halisa ya sanya Yaa Sheikh buɗe ido yana furta "Yaa Rasulullah!" Cikin kuka da ciwon dake cinta ta ce "Abbana zan mutu, cikina, marata, bayana babyn zai fito ta baki wayyo Allah na mutuwa zan yi" Ya runtse idanunsa ya miƙe cikin nutsuwa duk da a rikice zuciyarsa take ya ce. "Yi addu'a, Zahrah karɓi waya" Halisa ta ƙara wani kukan da gaske ji take ba zata rayuwa ba. "Wife" Zahrah ta ce "Na'am" ya ce "Can you drive?" "Sure" Ta ce tana riƙe Halisa wacce jikinta ke rawa ta durƙoshe tana yarfe hannunta, kukan Halisa duk ya dagula masa lissafi ya ce "Fito da Zawja ina tunanin motar ta akwai mai maza zuwa Aminu Kano, kiyi driving a nutse" "In sha Allah sweetheart ka kwantar da hankali" ta miƙe zuwa part ɗin Halisa ta ɗakko mata ƙaramin hijab wanda ba zai takura ta ba, itama ta saka hijab da ƙyar ta iya miƙar da Halisa zuwa shiga mota ta sakata a baya, cikin nutsuwa take driving lokaci zuwa lokaci take cewa "Sannu ki dai na kuka" Yaa Sheikh ya nufi labor room ba tare da sanin kowa ba, ya cire kayan jikinsa idanunsa kwance a mararsa wacce ta kumbura yana kallon yadda kayan aikinsa suke numfashi ya ɗauke idanu ya zura wata green riga da hula tare da mars a fuska hannunsa ya saka safa, baya aiki a hospital amma yana da right na shiga duk hospital ɗin da ya yi niyya. Yana fitowa ya samu Police sun dawo ɗauke da tsohon El ya shaƙi wuyan shi yana duka ya ce "Wannan dandatsa ya dace ayi masa" Jadda ta ce "Alkur'an a gutsire tsinanniyar abar uban kowa ya huta" "Kada ku ɗauki doka a hannu fa" "Har abada ba zan huce ba, idan ba nakasta shi nayi ba" Jadda ta zuro kanta ta tsakanin ƴan sandan ta ce "Ka rugurguza mazakutan shi kawai, ɗan hau daga gani daman ya daɗe yana sharholiyya" "Ba haka za ai ba" Cewar Abba Hakimi, ya juya zuwa ga El ya ce "Abokina Mubasshir sake shi" El yana huci ya kalli Abba Hakimi ya ce "But grandfather" "Mubasshir!" Yaa Sheikh ya kira sunan a tsawa ce, cikin sauri El ya saki tsohon har ya juya ya dawo da baya tare da dunƙule hannu ya daki bakin tsohon, abinka da dokan police nan take haƙora biyu suka zube, ya ƙara dunƙule hannu ya daki gaban tsohon ya ƙara dokan gaban wajan kayan aiki wani ihu! Tsohon ya kurma jin kamar an saka almakashi an gutsire abar sbd tsananin azaba cikin azaba ya fice daga world ɗin. "Algungumi tsohon najado, da ƙyar kaga Annabi ai mai kayan ɗan sandan can ɗan gidan sarkin Sokoto ya kyauta, so nayi a cire munafukar abar a zura a leda a dinga shela da ita ana nunawa sbd masu halin ƴan taure irinsa" Mother har lokacin kuka take, Dr A'isha da bata jima da zuwa ba ta dinga bata baki, Yaya Halima kuma bata ƙasar. Ganin Yaa Sheikh cikin kayan aiki na likitoci wanda sukai masa kyau da gaske ya sanya suka dube shi kafin suyi magana ya ɗaga wayar shi da sauri ganin Zahrah na kira, jinjina kai kawai ya yi ya nufi waje. Da hannu ya yiwa Nurse's nuni da gado suka biyo bayan shi janye da gadon yana zuwa Zahrah na fitowa lokacin Halisa ta gama fita daga hayyacinta sunan Allah kawai take ambata, ya ɗauketa da kansa zuwa gadon suna zuwa Mother ta miƙe ta ce "Ya Salam Daughter haihuwar ce" Halisa ta saki kuka ta ce "Mother haka Dadata taji da zata haifan, wallahi ba zan ƙara ciki ba, na gama haihuwa ni na tsani Abbana bana son shi wayyo mutuwa zan" Jadda ta buga tafi ta ce "Ƴar jakar uba lokacin da kike sake jikinki ya luguda ubanwa ya sani, ai shi namiji ba ruwan shi wai azaba ranar haihuwa ake ji daman" Dr A'isha ta miƙe ta ce "Lemme help you" Yadda Halisa keyi dole ta baka tausayi ƙarfinta duk ya ƙare jikinta ya saki abinda ba a son mai haihuwa tayi... Dr A'isha ta dubi Yaa Sheikh dake riƙe da hannun Matar Malam ta ce "Bana jin zata iya haihuwa da kanta.... 08119237616Hannu Yaa Sheikh ya saka yana shafa kan ƴar fillon shi yana mai sauke numfashi da hamdala a ran shi. Idanun Dr A'isha bai hana shi sunkuyawa ya sumbaci goshi da ƙuncin Halisa ba. Bai san mai zai ce da Ubangiji ba sai godiya. Cikin lokacin ƙanƙani ya azurta shi da tarin abubuwan masu yawan gaske! Ita ɗin alheri ce, kyauta ce daga Ubangiji. Ya lumshe idanunsa yana jin abu na kwanciya cikinsu, sautin kukan babyn na ratsa cikin kunnensa. "Allhamdulillah!" Cewar Dr A'isha tana zare babyn daga ƙasan Halisa wacce ta galabaita tare da ficewa daga cikin hayyacinta. Ta riƙe hannu Modibbo da ƙyar naman jikinta duk rawa yake. Yaa Sheikh kasa taɓoka komai ya yi, Dr A'isha ta yanke cibiya tare da goge babyn da zaiton kana ta naɗe cikin showel. "It's a baby girl" Ya jinjina kai, fita tayi daga room ɗin, bayan ta kwantar da babyn a baby bed. Jikin Jadda na rawa ta ce "Ya..ya..ya ya ake ciki" Murmushi Dr A'isha tayi ta ce "Ma sha Allah, she give birth to baby girl" Jadda ta rangaɗa buɗa ta ce "Allahu Akbar, Allahu Akbar kaji yarinya da halin manya Ubangiji ka sanya war haka mu ƙara dawo amsar haihuwa" "Amin Ya Allah, mene tukuci?" Mother wacce farin cikin saukar Halisa lafiya ya rage mata kaso 50 na daga cikin damuwarta ta ce "Tukucin faɗar haihuwar matar malam ai na musamman ne, ki kira mijinta ya zo" Dr A'isha ta wara hannu ta ce "that's good, kawai zan tura account details" "Go ahead" suka saki murmushi. Farin ciki ya mamaye zuciyar gabaɗaya Familyn, haihuwar Halisa ya ƙara zama abu mafi muhimmanci a cikin zuri'ar. Zahrah ita kanta tayi farin ciki domin ta shiga damuwa. Shi da kansa ya tura gadon da take kai zuwa resting room, domin sama mata cikakken hutu. Ya sanarwar da wani Dr ya kawo masa drip da Injection ya sanya mata. Har lokacin bai bawa kowa damar shigowar inda take ba. Yana riƙe da hannunta gam! Yana kallon yadda take barci a wahale numfashi na fita da ƙyar, ya damƙe hannun cikin laushin murya mai cike da tsananin gajiya da nuna farin cikinsa a fili ya ce "Barakallahu fiik Zawja, meu amor! So lucky to have you in my life!" "Ya kamata kaje ka huta, domin kasha ciwo da ya ƙushi, she's so lazy" Ya kalli Dr A'isha sai ya miƙe yana zame hannunsa daga cikin na Halisa, kai ka ɗauka shi ne mai haihuwar, duk yadda yaso riƙe kan shi ya gangara. Yana fitowa Jadda tayi masa ka tana rangaɗa buɗa, ya marairaice domin har tsakiyar kan shi yake ji, baya son takura ko hayaniya zautar da shi suke. "Congratulations Yaa Lee" Ya jinjina kai ba tare daya kalli Umar-khan ba. Dr A'isha ta fito hannunta ɗauke da baby dake barci, Abba Hakimi ya fara amsar ta tare da yi mata addu'a, kana Father sai kuma Umma A'isha. Mother tabi kyakkyawar fuskar yarinyar da kallo, babu inda ta bar Halisa, hatta ƙaramin bakin iri ɗaya ne. Yanayin gashin kanta ne yake kama dana Yaa Sheikh da yatsun hannunta, wani irin sahihin kyau yarinya ke da shi, gata ƙatuwa tubarkallah kamar ba ƴar fari ba. "Daughter ta haifi mai kama da ita" Umma A'isha ta ce "Anya? Kamar ta Malam nake gani shimfiɗe a fuskarta, bakin ne dai na surutu irin na uwarta" "Ni fa Ƴar gidan Modibbo babyn ke mini kama" Dr A'isha ta ce "Sure, They look alike" Mother ta ce "God made her behave like her father" Sai a lokacin Zahrah ta ce "Kuma Halisa nada kyan hali, open heart gare ta" Gabaɗaya sun manta tana wajan, sai kunya ta kama su. Mother ta miƙa mata babyn ta ce "Ga Daughter ɗin taku Zahrah" caraf, Jadda ta ƙwace babyn tana zare idanu ta ce "Allah ya isa, tsakani na dake sai Allah ni ban zan kulaki ba, kowa yasan jinya nazo, to ba zan zuba idani a bawa kishiya ƴar kishiya ba, salon a shafa mata taitanos mu shiga uku, a cuci yarinya ko gama zafin haihuwar bata gama ba" Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa, haihuwa na taruwa a cikin Idanunta. Jadda ta ce "A'a fa bawai magana na faɗa ba, balle a ƙullace ni duniyar ga da babu gasky haka kurum ba za a suɗe mini kurwa ba" "Kiyi haƙuri nifa ba mayya bace" Zahrah ta furta a raunace. "Kaji mafisa ko? Babu dama kayi magana sai a ƙullaceka, to aniyyar ko wanne ɗan ƙaniyya ta bisa duk yadda kaso da kame baki sai an saka ka faɗar zunubi" Daidai lokacin Yaa Sheikh ya fito cikin wata Jallabiya Ash colour mai laushi da santsi, ta kwanta sosai saman farar fatar shi, ya naɗe kan shi da hirami. Yadda fuskarsa ke motsawa tana faɗaɗa zaka fahimci yana cikin farin ciki mara misaltuwa. Ya dubi Zahrah da ta bar wajan tana goge hawaye. "Hufii, to don Allah haka ba yafi ba? Da cewa nayi ta tashi tabar wajan Alkur'an sai ta tsaneni yanzu dana kame baki nayi magana a nutse ba gashi ta fahimta ba, Alsulhu khair!" "Eh gwarai ga sulhu nan" Dr A'isha Said "Lafiya?" Yaa Sheikh ya furta a taushashe ƙamshin turaren shi na Roja ya cika wajan, wanda ya sanya Dr A'isha sauke numfashi a ɓoye tana riƙe kanta. "Matarka ta kura, ta hanata ɗaukan baby" Jadda ta zare idanu tana dafe ƙirji sai kuma tayi shiru ganin yadda Yaa Sheikh ya kafe ta da idanunsa masu tsananin kaifi da sanya mutum shiga cikin nutsuwar shi "Allah ya raya Baby Ubangiji ya sanya albarka" Umma A'isha ta ce "Allah ya sanya kuma matar malam tayi hankali" Sai a lokacin cikin sakin fuska yana jan jikinsa ganin Ummul na zuwa ya furta. "Matana da hankali" Mother ta ce "Ba shakka" Duk abin nan da ake hankalinta na kan Fattoumah ita da Father daya bar wajan yanzu. Idanun da sukai yawa a wajan ya hana Yaa Sheikh rungume Ummul kamar yadda ya saba, a hankali yake binta da idanu wanda take ganin tsananin farin cikin dake cikin su. Suka amsa mata sallamar. Tayi murmushi ta ce "Barrister ya jikin Faɗima? Abu bai yi daɗi ba Ubangiji ya ki yaye ya kuma taƙaita ya bata lafiya" Mother ta ce "Amin Ya Allah" Dr A'isha ta dinga kallon Ummul ganin yadda take komai a waye cikin nutsuwa da kamala, da shigar nan nata wanda ba a rabata da ita Abaya's masu kyau da tsada. "Can Mubasshir ya sameni, ina ga ya manta da na tura resigning letter " Mother ta ce "Ikon Allah, amma ba lokacin barin aikin ne ya yi ba?" "Not at all,There is a reason why I joined the police force, and now I let El-Bashir finish the job". "To Allah ya taimaka" Ummul tayi kyakkyawan murmushi ta ce "Anyi baby kuma, Allah ya raya ya bawa mahaifiyar lafiyar shayarwa" suka amsa da Amin. Ta juya ta kalli Yaa Sheikh ta ce "Arɗo You left your wife alone, and i think she's crying". Bai ce komai ba, bai kuma motsa ba idanunsa akan Jaririyar hannun Ummul, yana jin son yarinyar da komai na wanzuwa a zuciyar shi. Ya juya zuwa Room ɗin da Halisa ke ciki, har lokacin barcin wahala take yana daga bakin ƙofa ya shiga ƙare mata kallo sai kawai ya girgiza kai fararen haƙoransa a bayyane alamar dariyar ya yi mai kyau a fili ya ce "Ƴar kwailar matata" Ya fita zuwa reception Zahrah na ganinsa ta goge hawayen idanunta tana miƙewa tsaye cikin inda inda ta ce "A.... You" ya bita da kallo tayi murmushi ta ce "Congratulations sweetheart, ina maka murna da samun babyn" bai ce mata komai ya kama hannunta zuwa ciki ta ce "Zan koma gida" A hankali ya ce "Zuwa anjima" ta ce "To zan jira nan" ya dubeta da kyau ta ce "I wanted to be alone kawai fresh air nake so" Cikin ɗaga murya ba wasa ya ce "Fatymerh Zahrah!" Sai kawai ta fashe da kuka ta ce "Am sorry, ba zan iya jure abin da Jadda zata faɗa ba, daman Halisa na kawo Thank God ta sauka lafiya zan koma" ya riƙe hannun da kyau ya nufi ciki da ita, sai da suka je corridor ya rungomota jikinsa ya ce "Sorry" "Na kasa jurewa, na jawa kai na mugun tabo, wanda ya sanya na kasa samun soyayyar ƴan uwanka, na kasa samun taka soyayyar balle nayi zaton samun baby tare da kai, lalai na cancanci haka" Ya yi mata shiru yana dai rungume ta ita. "Yaa Sheikh" ta ɗago kanta ya kalleta yana lumshe idanunsa ta ce "Don Allah kada ka barni, nayi al'ƙawarin zama dakai ko ba zan samu farin ciki ba" Ya share mata hawayen ya ce "Ki riƙe Allah" ya faɗa yana zare ta a jikinsa tayi murmushi ta ce "In sha Allah" Haƙurinta yana ƙara bashi yaƙinin tabbas Ubangiji ba zai barta haka ba. "I love You sweetheart" "Wife" ya ce kawai... Har Issha El-bashir bai shigo ba. Walking slowly yake tafiya a world ɗin, hannunsa zube jikin aljihun wandon Camouflage-print cargo trousers sai Sleeveless jersey tank top a jikinsa, idanunsa maƙale da Sunglass black. Yanayin yadda yake tafiya sai sanya kasan jinin Mai martaba Ahmad Nuran ne yake gudana a jikinsa. Fuska a haɗe babu walwala sbd zafin zuciyar da yake ciki. Ya murɗa handle ya shiga suka haɗa idanu da Fattoumah ya ɗauke ido ganin Mother ya yi tsaye zube da aljihu. "Sai haƙuri, Allah ya bi mata kadinta" Ya shafa kai ya ce "Oops it's okay" Ya fito da waya yana dannawa fita Mother tayi a sanyaye Fattoumah ta ce "Uncle" "Angela" El ya furta yana zama tare da kama hannunta ta ce "Kada ka barshi Uncle muguwa ne" Ya runtse idanu yana ayyana azabar da Baba mai gadi ya ganawa Angela ɗin shi. "Ya zan na bar wanda ya san gonata kafin na sani? He most pay" Ganin tana ta kallonsa ya ce "Mene Angela?" "Fitsari zan yi" ya saka hannu ya ɗagota ya ce "Zaki iya takawa?" Ta girgiza kai domin har ɗinki akai mata. Cak ya sunkuceta zuwa toilet, ihu! Ta fasa sbd azabar zafi lokacin da fitsarin zai fita tana kuka sosai jikinta na rawa da ƙyar tayi, sam El bai damu da ganin jikinta ba ya fahimci ita ɗin kawai yake ba wani abu nata ba, ya taimaka mata da wanke wajan tana miƙewa ta shige jikinsa tana sakin wani kuka. Yadda take kukan zaka san wahala take sha, ya riƙe da kyau a jikinsa a hankali yake cewa "Sorry, am sorry Angela" ya ɗauketa zuwa bed ɗin tana kwance a cinyar shi yana waya a hankali ya ce "Oh, ina buƙatar a shige da shi state C.I.D, kafin shiga Court" A tsawa ce ya ce "Zanci Ubanki ɗan iska, kai baka san waye ni ba You hve no idea akan abin da zan aikata" cikin ladabi ya ce "My bad" El-bashir Said "I, El-bashir Ahmad Nuran Sarki ka kula ba wanda zan ɗagawa ƙafa akan matata" ya sauke wayar rai ɓace. "Uncle me ya sa ka ke faɗa?" Ya dubeta yana ƙoƙarin sauke numfashin shi. "Angela zaki aureni" Sosai Fattoumah ta san kalmar aure, sbd wayonta shekarunta kuma sun kai ta sani tayi murmushi tana ɗauke kai. Ya kamo fuskarta yana zare Glasses ɗin idanunsa ya ce "Ba zan iya jira ba, fitar da nayi sai dana tabbatar igiyar aurena ta hau kanki Binta, You're now Mrs El-bashir Ahmad Nuran Sarki, El loves you Angela"..... Halisa ta dinga mamaki wai ita take da yarinya, ita ta haihu, ita ta zama uwa. Sai ta fashe da kuka musamman idan taga babyn na motsi. Da zarar taji ƙamshin turaren Yaa Sheikh take rufe idanu bata mance azabar data sha ba, ita kam gwara first night da wannan azabar ta haihu. Zuciyar Babban malamin babu daɗi yana ta so ya keɓe da ƴar fillonsa amma taƙi yarda. Umma A'isha ta zauna wajanta. A hankali motar shi tayi parking Umar-khan ya fito da sauri ya buɗewa Yaa Sheikh, lokacin 6:45 na safe sanyi na busawa ya Fito cikin kyakkyawar tufa kamala da Ilhama ya ƙara wanzuwa a jikinsa. Cikin tarin nutsuwa yake sanya ƙafar shi ta daba,kana ya maye gurbinta dana hago har ya isa ƙofar Room ɗin. Bakinsa ɗauke da sallama Umma A'isha ta amsa masa, hannunta riƙe da babyn dake kuka sosai yin duniya kuma Halisa taƙi bata nono, da zarar ta bata taji zafi zata cire kuma nonon ya cika sosai. Muryarsa da ƙamshin turaren shi ya sanya Danejo kame fuska Umma A'isha ta amsa tana faɗin. "Allahamdulillah, Ya Zahrah" ya jinjina mata kai yana zama saman kujera daman Umar-khan bai shiga ba, ya shige wajan Mother dake kula da Fattoumah. "Matar Malam riƙe ƴar nan mai azabar kuka, zan duba Faɗimatu" Tayi shiru "Magana nake" nan ma tayiwa. "Kawo ta" Ya faɗa in clam and golden voice. Umma A'isha ta bashi ita yana amsar ya ɗorata a ƙirjinsa yana jijjigata amma taƙi yin shiru. Ƙaramin yatsar shi ne ya sanya mata ta shiga tsotsa ya dinga shafata yana mata karatu a kunne har tayi shiru. "Wannan fushin?" Ya faɗa yana leƙa fuskarta ta tashi zaune ta ce "Amma Abba ai baka kyauta mini ba" ya ware idanu ya ce "To fa, dame?" Ta tura baki gaba ta ce "Baka ce mini haka haihuwar yake ba ai" Ya dawo kusa da ita ya ce "Wanne suna ki ke so?" Ta kalli Jaririyar dake ta tsotsar hannun mahaifinta ta ce "Ummul-khairy" ya tsora mata idanu sai ya zaro zam-zam daga jikinsa ya bawa babyn, kana ta tauna dabinon ajwa ya saka mata, ya yi mata kiran sallah kana ya yi mata huɗuba da Ummul-khairy. Ya ce "Allah ya raya mini Mamana yadda take kama da babarta ka sanya kada tayi rigimarta" Halisa ta ce "A haka dai ka aura daga nan har Rugar Rome" "Eh tana tallan Kindirmo ba" Ta ƙara cewa "Abba nifa na gama haihuwa ba wasa nake ba" Ya dubeta ya ce "Tare mukai komai fa, Na baki ciki, ki kayi rainon shi, kina laulayi ina kulawa dake, a haka fa akace an tsaneni, naƙudar jiya akai mini dukan tsiya" tana ƙoƙarin magana taji ya ɗage rigarta bakiɗaya tare da kafa....*_Arewabooks@Nimcyluv79_* Ihu ta saki ya yi saurin zame bakinsa yana saka hannu ya dungure mata kai, ta marairaice ta ce "Zafi fa, kuma daman...," "Shhhh" ya furta yana ɗora hannu tare da ƙarewa wajan kallo. "Mene wai?" Bai iya magana sosai ba, sai daya haɗiye ruwan daya zuƙa ta ce "Kafa shanye" ya lumshe idanu speaking calmly ya ce "Na sani" "Me ya sa?" Halisa asked Yaa Sheikh ya ce "ƙaya na ciri miki" tayi ta kallonsa tana ganin wayo ita dai kawai ya yi mata Ya zame idanunsa dake yazo a fuskarta tare da ɗaukan bbyn dake kuka ya ɗora mata ita a cinya cikin kasalar data saukar masa ya ce "Feed her" "Ciwo yake fa" Ya dubeta ya ce "Na cire abin ciwon" kafin tayi magana taji ya sakawa bbyn a baki kamar jira take ta cafke. Ta fasa ƙara wacce ta razana Little Ummul. "Wayyo Allah zata cire wayyo Ummul, wayyo Dadata" mmki ya cika Yaa Sheikh. A hankali kuma ta sauke ajjiyar zuciya lokacin da taji ya rungumeta gabaɗaya a jikinta yana kallonta Tana kallon Little. "Thank you, thank you" Ya ce cikin laushin murya ita kuma tayi ƙasa da kanta tana son taji thank you ɗin ta mece ce? Ya riƙe hannunta cikin nasa yana ƙara shigar da ita jikinsa yaja numfashi ya ce. "So lucky to have you in my life, Zawja. Thank you Zawja for sending this amazing present to me…. I loved it and it will always be very special to me, Of all the gifts you have given me, this surprise gift will always be the most special because it came as an unexpected surprise and it will always stay fresh in my memories and my heart" Ya tallafo haɓarta cikin nutsuwa tare da yin copping face ɗinsu. "Can i say you're the best wife ever? Am proud of you Ƴar fillo" "Am also proud of you Habibi ƙalbi, you means alot to me you're the father of my children I love you so much" Ya tsora mata idanu bai san me ya sa a lokuta da dama take karantar zuciyarsa ba, kafin ya faɗi komai ta gama karanta. Ya gode Allah, daya bashi macen rufin asiri "Yaa Sheikh" Ya dubeta bai amsa ba. "I love You" yaji _I love You_ ɗin har ƙasan zuciyar shi, ta ƙara kashe masa jiki tsigar jikinsa ta shiga ta shi tana zubewa. Manna mata sumbata a goshinta cikin kamala irin ta mutanan ƙwarai masu nagarta da sanin hakƙin Iyali tare da zuri'a. Ya furta. "لو كان العتاق يثل كم أحبك، لضمتك بين ذراعي للأبد" "I love you Abbana" Ya fahimci so take ya furta mata wannan kalmar da tayi watanni tana jiran jinta a bakinsa amma ya kasa.. Ya ɗauke kai tare da saka hannu ya ɗauki Little da tayi barci, babu inda tabar babarta har fari da komai hakan ya sa ya ƙara jin son yarinyar na wanzuwa a zuciyarsa. Juya mata baya ya yi. Ta ce "Habibi" yaƙi juyawa. Ta saka hannu taja gemun dan shin da taji a gemunsa kamar an zuba masa ruwa ya sanya ta ce "Abul-khairy ku...." Tayi shiru jin ya juya ya sake rungumeta tare da ɓoye fuskarsa a wuyanta Ta saka hannu ta amshi Little ta ajjiye gefe guda, a ranta take jin kuka yake abin da bai taɓa yi ba, bata taɓa gani ba. Yaƙi yarda ya saketa balle ta kalli hawayen. "Please Habibi stop stop..!" Ya dakatar da ita da faɗin "Princess, my wife. You have given me the biggest blessing of my life. I treasure this moment of being the father of my child. Thank you for gifting me this bundle of joy and happiness" "Thank you, ina jin nafi ko wacce mace dace da miji mai nagarta da sanin hakƙin iyalinsa, miji ba fahimta da shiga cikin lamarina, mijin da soyayyata bata rufe mishi idanu wajan ganar dani kuskure, miskilin mijin da zai sanya ni a gaba da kalamai masu daɗi duk kame kai da miskilancin shi, Thank you Dear Lord" Hawayen daɗi ya shiga fita daga Idanunta jin ya kama hannunta ya zura mata zobe, ta fahimci the best gift daya iya bayarwa shi ne Ring. Wani lokacin ya ce Allah ya yi miki Albarka wacce hakan yake ƙara sanya *Halisa Danejo Rome* cikin wani irin farin ciki mara misaltuwa. So da ƙaunar mijinta *Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu* kuma *Dr Aliyu haydar* ya gama gigita rayuwar *Princess Halisa Ahmad Nuran Sarki* Ya kasa magana ya shiga sauke mata wasu lafiyayyun kisses ta ko'ina ya mance a gadon asibiti take kuma ita ɗin ɗanya ce, jikinta ɗaya ne. "It seems that Little Ummul will have a sister nearby, or in this hospital" Khalil Said yana ƙarasa shigowa cikin room ɗin, daman Umma A'isha da Mother duk suna room ɗin da aka kwantar da Fattoumah. Yaa Sheikh was speechless ya kasa furta komai ya kame fuska da kyau babu alamun wasa, amma fuskar shi ɗauke take da annuri da hasken farin ciki. "Kai Hamma daka tsaya a waje ai" "That's what i was telling him" Khalil ya juya ya kalli El dake tsaye sanye da navy blue na suit ya zuba hannu a aljihu. "Kace mini me? Magaji yaushe ka fara sharri" El ya ce "Goodness, bance maka mata da miji ne ciki ba, ai naga zuwan Abba tun farar Safiyya" Khalil ya watsawa El harara ya ce "Kai yake Abbanka not me, ja jiki" Maimoon dake shigowa hannunta ɗauke da flast wanda Ummul tazo da shi yanzu ta ce "Haka ranar nan ya ce wai rawar kai gareni irin halinmu ɗaya" Khalil ya zaro idanu ya ce "Ni ne mai rawar kai ɗin?" El ya ɗaga hannu zai make Maimoon Khalil ya ce "Kana taɓa mini mata sai jikinka ya faɗa maka dan ubanka" Ƙwafa El-bashir ya yi Ya ce "Wannan yarinyar ficika da ita sai gulma" "Eh babu komai, ficika kuma gata can kwance a gado kaje kaji da kwailar daka kwasa shi ya sa kake ta zarya daga Sokoto zuwa Kano, Kano to outside country" Maimoon taja jiki tare da haɗawa Halisa tea mai kauri sai tiriri yake, ta zuba mata farfesun kayan ciki fal plate "Abba zo muci" caraf ya ce "Waye zai ci abincin me jego kayan ƙazanta" Maimoon ta kwashe da dariya ta ce "Wallahi ko ni ba zan iya ci ba" Mai jiran kaɗan balle wacce aka jefa da kashin kaza, ta saki kuka wanda ya farkar da Little ta ce "Abba wai ni ce ƙazama, kai ma ba za kaci ba" Yaa Sheikh ya lura da gangan Khalil yake son taso masa da rigimar ƴar fillon kafin ya ce komai Ta ce "Ai shi nawa ne, ni tasa ce kuma dan kaji yanzu kafin ku shigo ya saka bakinsa a n...." "Don Allah" Yaa Sheikh ya furta daidai kunnenta yadda ita kaɗai zata ji shi kam ta fasa wannan zancan a gurin nan ai ya banu da Khalil, ga Mubasshir,ga Maimunatu... El ya ɗauki bbyn ya dinga kallon ciki so da ƙauna ya ce "Me za a na ce mata to?" "HALA" cewar Yaa Sheikh yana miƙewa tsaye ganin yadda Halisa tayi kicin-kicin da rai sbd bai ci abinci ba. "Wow suna mai daɗi Hala" Yaa Sheikh ya yi waje abinsa kai tsaye kuma Fattoumah yaje dubawa a nan ya samu labari ashe Tun asuba jirgin su Mai martaba da Dada da su Fulani ya sauka, hadda Yaya Halima. Mai martaba yana can gidan Abba Hakimi. Shi ma daga nan harabar asibitin ya tsaya,yana nan tsaye yana waya yaga shigowar mota ganin ɗaya daga cikin motocinsa ce ya sanya ya ɗan buɗe idanunsa baya ya ajjiye wayar shi daga kiran Umar-khan. Zahrah ta fito sanye da shigar kamala hijabi har ƙasa hannunta riƙe da basket suna haɗa idanu da Yaa Sheikh ta saki murmushi ta ce "Good morning sweetheart" Ya jinjina mata kai har ranshi yake son yaga ya kyautata mata amma ya kasa ta ce "Ya sister Halisa da daughter?" A hankali ya ce "Allahamdulillah, wife" Zahrah ta ce "Bari na shiga,naga kamar fita zakai ko?" Nan ma ya ƙara jinjina kai yana lumshe idanunsa, yana jin zuciyarsa babu daɗi sam da ganin halin da Zahrah take ciki, ya kasa samu kalmomin da zai amfani dasu wajan fahimtar da ita halin da yake ciki, sam wannan kariyar da wasu can Aljanu suka bashi bai ji daɗin ta ba, idan ƴar iska Ubangiji ya ɗora masa Soyayyarra da? Shi aka cutar. rayuwa kenan!. State C.i.d Kai tsaye nan Yaa Sheikh ya sauka Khalil da kan shi ya yi driving nasa sai El wanda yake jin kamar zuciyarsa zata faso idan yaga ɗan iskan tsohon ji yake kamar ya saka bindiga ya harbe banza. Mai kula da sashen bincike da fyaɗe da kan shi yazo wajan Yaa Sheikh bayan sun gaisa ya ce "Kada ka damu Yaa Sheikh, zamu aika shi court daga nan kuma za a yanke masa hukuncin bayan fitar da hujjoji" El ya ce "How long za'a ɗauka kafin zuwa court duk wani fyaɗe kuma wanda yake da aure hukuncin kisa ne fa? A bani dama na harbe ɗan taure" Ya yi murmushi "Clam down prince, zai girbe abinda ya shuka imma irin ya fidda ƴaƴa masu kyau ko akasin haka" dole El ya haƙura. Yaa Sheikh ya koma gida domin ya huta ya samu cikakken tunanin da zai yiwa Zahrah bayani. A can asibiti da mamaki Zahrah ke kallon Mimi da Alhaji Farouk tare da wasu ƴan uwanta. "Zahrah" Mimi ta kira sunanta muryarta na rawa hawaye ya cika mata cikin idanunta. Zahrah ta juya da sauri zata shiga mota, Mimi tabi bayanta cikin rashin sani ta bangaji wata budurwa, budurwar ba tayi ƙasa a gwiwa ba ta saka hannu ta ɗauke Mimi da mari cikin faɗa ta ce "How dare you ahh? Wacce irin banza dabba ce ke kina tafiya kai a sama kamar tinkiya mai yasa talakawa suke haka ne mtwss" wani zafin zuciya ya tasowa Zahrah ta ɗaga hannu zata daki budurwar Ummul ta riƙe hannun tana murmushi "Ummul mahaifiyata da mara fa?" Ummul ta ware idanu ta ce "Oh da gaske? Har kin manta?" Ummul ta ƙara murmushi ta ce "Idan maye ya manta uwar ɗa ba zata mance ba, faɗin Ubangiji ne da kansa, wanda ya zagi uwar wani haka za a zagi tasa, kin mareni kin zageni ba akan idanun ɗana ba, yau gashi an mari mahaifiyarki akan idanunki an kuma ci mutuncin ta, shi ya sa a kullum kake iya bakin ka naso ɗaukan mataki sai na share domin iya son ɗana da Ubangiji ya gwada miki shi kaɗai ya isa ya zame miki ishara, sai dai ba zaki taɓa zama inuwa ɗaya da Aliyu ba, kamar yadda ki ke mafarki nasan ya kasa faɗa miki ko?" A gigice Zahrah ta ce "Don Allah Ummul kiyi haƙuri ki rufa mini asiri kada ki ɗauki fansar abinda nayi miki ta hanyar rabani da Yaa Sheikh ki tausaya mini shi ne kaɗai inuwar da nake jin gina naji daɗi" ta saki kuka sosai. "Babu ruwana Fatimerh, banyi lalacewar da zan raba aure ba, zanan ƙaddarar damu kanmu bamu san da shi ba, shi ne Ubangiji ya yi ikonsa akan haka zai kuma rabaki da Yaa Sheikh cikin ruwan sanyi" Halisa da Umma A'isha da suka fito domin tafiya gida an bata sallama suka tsaya suna kallon ikon Allah. Kowa ya kasa magana, Abin mamakin dake faruwa bai shige dukkan wanda yazo hucewa sai ya juya ya kalli Halisa wasu suna nunata da hannu suna cewa ita ce Ƙarar jiniya suka ji ko ta ina Mother ta ce "Wai meke faruwa ne?" Halisa ta marairaice fuska ta ce "Mother me ya sa ake kallona ne?" Aka buɗe motocin kai tsaye wani ya nufi wajan Halisa Ummul tayi saurin shan gabansa ta ce "What's going on?" Ya fito daga Card ya ce "Ɗan sanda daga hukumar C.I.D Criminal Investigation Division" Ummul ta ce "Ok then, mene ya kawo ku?" Da hannu ya nuna mata Halisa ya ce "To Arrest that young lady behind you...... 08119237616 Paid book ₦500 Complete ₦1000 *_After 3yrs🫣....._*_*Sarautar marubuta 80*_ "Arrest?" Suka haɗa baki wajan faɗa Halisa ta gigice ta riƙe Ummul domin ita take gani kamar mijinta Yaa Sheikh cikin rawar murya ta ce "Wallahi banyi komai ba, me nayi su waye ku?" "Hakan ya ƙara saka mini shakku akan ki"Ya faɗa yana ƙara jinjina kai ba tare da tsoro ko fargaba ba. Ummul ta ce "Excuse me Officer, kasan matar wace da za kayi arresting nata? Akan wanne dalili, me tayi" Ya duba lokaci ya ce "Sorry Madam, kina wasting time ɗina, idan muka ke office ɗinmu zaki ji komai wajan tuhumar mata laifin daya sanya mukai arresting nata" Halisa ta fashe da matsanancin kuka "Ummul, Abba, Mother I don't wanna go to prison" Gabaɗaya ta gigice ta saka kuka, ga jikinta babu ƙwari abinka da ɗanyan jiki irin na masu jego. Mother ta bawa Umma A'isha Hala ita kuma ta riƙe Halisa dake neman fita hayyacinta daman ita bata iya firgita ba yanzu zata zauce. "Babu inda zata ba tare da faɗin dalilin arresting nata ba" Mutumin ya kalleta ya ce. "Ki saurara da maganganunki, ko mutuwa tayi sai mun tafi da gawarta" a ruɗe Mother ta ce "What! Are you at of your sense?" Mothers na gama magana Ummul ta fito da card ɗinta wanda take shirin kai wa. Ta nuna mishi ta ce "I am police officer, nasan kana da matsayi mai girma ba rukuninmu ɗaya ba, amma zan baka mmkin ƙarfin ikon daga sama" "And am ready to be her lawyer" cewar Mother! Cikin tsawa ya ce "Arrest her!" Ya faɗa a tsawa ce cikin zafin rai. hankalin Familyn ya ta shi, Ummul taja gefe tana waya mai matuƙar muhimmanci yadda take wayar zaka san ranta zai ya ɓaci. Mother ta riƙe Halisa, Dada daman kasa cewa komai tayi taja gefe Idanunta cike da hawaye. Cikin sauri Zahrah ta shiga tsakani ta ce "Arrest me first before her, ko tausayi baka da shi mace ta haihu a sallamata yanzu shi ne kake tunanin tafiya da ita Oh My Goodness" "Officer" "Yes Sir!" Wani ya faɗa yana ƙamewa ya miƙa masa hannu ya bashi wayar gallery ya shiga ya fito da photo tare da juya screen ɗin wayar ya nunawa Zahrah ya ce "Yanzu sai ki fahimta" Zahrah ta zare idanu tare da dafe ƙirji cikin sauri ta matsa daga kusa da Halisa tana amsar wayar tare da duba photon da kyau. *Halisa* ce tsaye hannunta riƙe da wuƙa ta cakawa wani mutum. Daga nan ya nuna mata vedion cc.t.v camera. "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Halisa wa kika kashe" a ruɗe Dada ta ce "Kisa?" Halisa wacce numfashinta ya fara gardama ta riƙe Mother da ƙarfi tana girgiza kai idanunta na rufewa sosai cikin kaɗuwa da fitar hayyaci ta ce "Ban kashe kowa, wallahi bani bace banyi kisa ba na shiga uku Ku kira mini Abbana shi yasan ba zan kashe kowa ba" "You're lie. Liar" Zahrah Said tana sakin kuka ta kasa yarda Halisa zata iya kisan kai, amma photon ya nunata komai da komai. Dada ta amshi wayar cikin tsananin tashin hankali tayi baya tana salati ya akai Halisa tayi kisa? Ya akai ta shiga cikin har ta kashe rai mene alaƙarta da wanda ta kashe. Jikinsu ya yi sanyi suka kasa magana banda Ummul dake can tana waya. Ya watsa hannu baya ya ce "So allow me to arrest her" Halisa ta riƙe Mother tana girgiza amma Mother ta kasa komai, ta koma kan Umma ta ce "Wallahi ƙarya suke bani bace ban kashe kowa ba kada su rabani da ƴata kada su rabani da mijina" Wani murmushi Officer ɗin ya yi ya ce. "So that's true daman ance kina da ɗaure gindi a duk wani iskanci da kike, yanzu zamu ga wanda ya tsaya miki zamu kawo ƙarshen barikin ki ƴar ta'adda kawai" Ya miƙa hannu tare da kama nata zai sanya mata handcuff ya ji an fisge hannunsa tare da murɗe shi baya, ya bada sauti. Ya saki ƙara "How dare you torch my sister's body, wanne ɗan iska ne kai waye ya baka damar kama matar *Yaa Sheikh, Ƴar sakin Sokoto* ?" "Ƴar sarkin Sokoto? A information ɗin da aka bayar ance yarinyar a gidan karuwai take da zama" Manyan motoci ne suka shigo cikin asibitin a guje har da ta wasu polices nada ban. Yaa Sheikh ya fito da sauri hankali ta she yana sanye da Jallabiya idanunsa ya yi jajir da alama fitowar ba zata ce wacce ba'a shirya yinta ba. Halisa na ganinsa da raguwar ƙarfinta ta nufe shi ta faɗa jikinsa kamar yarinya taba rufe kuka. Ya rungumeta yana bubbuga bayanta cikin sigar rarrashi. Yadda jiniyar kan shi tayi zai baka mamaki haka tabbatar yana cikin fushi mai zafi, zuciyar ƴan maza Aliyu na kusa, babu batun malunta. "Abba banyi komai ba, kada su tafi dani kada su rabani da kai da Hala ban musu komai ba" Ya runtse idanunsa wanda ruwa ya kwanta cikinsu tsabar zuciya takaicin yadda suka gigita masa mata yafi komai bashi haushi, ya ƙara sanyata jikinsa yana rungumeta da kyau ya kasa magana sun jima haka kafin ya kama hannunta zuwa dalleliyar motar shi ya sanyata a baya, zai juya ta riƙe shi ta ce "Habibi kada ka barni nan" ya watsa jajayen idanunsa akanta ita kanta ta firgita sai taga idanun tamkar bana mutum ba ya yi wani kala-kala yana sauyawa. Ya riƙe hannunta alamar "Relax" yana zame jikinsa tare da juyawa. Kai tsaye wajan Umma A'isha ya nufa ba tare da ya ce komai ba, ita ma ta miƙa masa *HALA SHEIKH ALIYU HAYDAR* Ya amsheta yana jin yadda take wurga ƙafa tare da tsotsar hannu. Motar ya koma ya sanya mata Hala a cinya ta rungumeta sosai tana ganin kamar wani zai rabasu idanunta cike da hawaye ta ce "Modibbo kazo mu gudu Please rabamu za suyi" ya juya mata idanu kai tsaye ta fahimta shi ne *IDAN BA KE* El-bashir Ahmad Nuran Sarki ya riƙe wuyan Officer ɗin ya ce "Akan me zaka yanke hukunci ba bincike" Garbati ya ɗimauce wani ya zo da sauri ya ce "Officer munyi kuskure ashe kama ce kawai suke da juna ba ita bace" Wanda aka kira da Officer kuma shi ne Garbatin cikin In-ina ya ce "Oh! to to ya yi, kuyi haƙuri kamanni ne ba ita ba ce" Ɗaya daga cikin jami'an da suka shigo tare da El ya ce "Babu sunanka cikin list ɗin Officers namu daga ina aka turo ka?" "Sunan shi Garbati Nuhu, ɗan gidan Mai gadin da aka kai Court" gabaɗaya suka kalli Garbati kenan yayi haka ne da nufin su sake mishi Uba? Ta hanyar basaja da kayan ƴan sanda da kuma cin amanar hukuma.. "Fake news ne kenan? What about the vedio mene shirinka?" Yaƙi magana Yaa Sheikh ya kasa jurewa ya kuma kasa lamunta daya rufe idanunsa yadda Garbati ya damƙi Halisa yake gani, cikin zafin nama ya ɗauke shi da kyakkyawan maruka. Ya ce. "Za mu yi masa hukunci irin na addinin musulunci, za a kashe shi ta hanyar jifa ya aikata fyaɗe da auren shi" El wanda zuciyarsa ke kusa ya saka hannu ya naushi Garbati gani yake kamar ubansa yake doka. Garbati ya galabaita ya ce "Wannan shi ne karo na biyar da mahaifina yake fyaɗe, kuma a duk wanda ya aikata a matsayin me gadi ne, da ya yi sai ya gudu imma an kama shi zan saka kayan ƴan sanda na yiwa iyalan yarinyar kashe di a haka har magana ta mutu, hankalina ya tashi lokacin da naji ya yi fyaɗe ga zuri'ar babban Malamin nan da ake faɗa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu. Bana da ikon yi musu bara zana, domin ahhali ne babba, mun shirya sakin labarai a Social media akan cewa Yaa Sheikh bashi da Uba, mu kaga hakan bai ba, sai muka duba yarinyar da kuka fi ƙauna a cikin ahhalin wato Halisa ita matar Yaa Sheikh ɗin, mun san idan muka kamata mukai barazanar kisa gareta dole zaku saki mahaifina, manufar shi ne ana sakin shi zan bar garin da shi" Suka saki salati, Ummul ta dinga girgiza kai. Mother ta ce "Sai inda ƙarfinmu ya ƙare akan Ubanka dole ya baƙunci halira" Bala Tukur ya ce "Shi kenan?" Garbati ya ce "Eh" "Batun dabar da kake kana fashi tare da kashe jama'a, ka mance yarinyar daka nuna musu vedionta tare kuke aiki" Garbati ya Girgiza da lamarin Yaa Sheikh. Kamar mai gani har hanji, daman yana lura da yadda zubin fuskar shi ke sauyawa lokaci zuwa lokaci. "Amma ya naga Halisa a jiki" "kama ce kawai" inji Garbati ya ce "Nima da kamar nayi amfani, haƙiƙa idan Halisa ta ɓata za'a iya kama Fariderh sbd tsananin kama ban taɓa yarda ana iya samun masu kama da juna ki babu haɗin jini ba sai yanzu" Aka tattara su Garbati zuwa Police station. Yaa Sheikh ya juya cikin nutsuwa amma zuciyarsa zafi take ya buɗe bayan mota ya shiga cikin sauri Umar-khan ya shiga shima. Ya dubeta ta shiru ta riƙe Hala sai kuka take gently ya saka hannu ya jawota jikinsa ya riƙeta sosai yana shafa kanta ta sauke ajjiyar zuciya da ƙarfi. For some minutes ya ɗagota suka haɗa idanu cikin kulawa yana tattara dukkan kulawarsa akan ta ya ce "Are you Okey?" Ta ce "Abba ban yi komai ba" Ya jinjina mata kai yana jin abu mai ƙarfi yana fisgar shi akanta. Ya ce "Nutsu, ba wata sauran damuwa, am here, and I'll always be by your side ok?" Ta ɗaga masa kai ya rungumeta ta jinsa ya saka hannu a riga yana shafawa tayi murmushi kawai tasan me yake nufi don haka ta gyara zaman Hala ta shiga feeding nata, har lokacin yana rungume da ita tana ɗago kai yake zaro mata idanu sai ta fahimci a yanzu shi ɗin rabi da rabi ne. Wato *MUTUM DA ALJAN* Sabuwar rigima ta ɓalle domin Umma A'isha cewa tayi gida za a dawo da Halisa shi kuma ya ce sam ba a isa ba, babu mai tafiyar masa da matan shi aure nawa ne ya mutu daga tafiya wankan jego. Halisa taso tafiya domin ta fahimci waye Yaa Sheikh tunda ya sameta ya mayar da ita abinci, ya daina azumi sai na Alhamis da Litinin daya zame masa jinin jiki... A wannan lokacin hankalin El-bashir Ahmad Nuran Sarki dana duk wani makusan cin shi ya tashi, abinda ake ɓoyewa ya fito aka rasa daga gidan wacce jaridan aka samu labarin fyaɗen Matar El-bashir Ahmad Nuran Sarki wato Fattoumah Aliyu. Zan can kuma sai fasuwa yake wasu suna haɗa jijita akan daman can hanyar ƴar iska ce, daga kan Social media, gidan rediyo, gidan t.v Babu wata hujja data nuna daga wajansu maganar ta fita, da abun ya yi tsamari maganar abinda Father ya aikata da Zahrah ta fito harda batun Muhammad. Duk Wannan maganar da abinda yake faruwa Yaa Sheikh yaja baki ya yi shiru, shirun na shi na nufin abubuwa da dama. Hankalin Mai martaba Ahmad Nuran Sarki ya tashi domin ana shirin lalata masa masarauta ne jama'ar garin Sokoto sun fara surutu akai. Sati na zagayowa aka sha shagalin sunan Halisa Yarinya ta ci sunan *Ummul-khairy Sheikh Aliyu haydar* ana kiranta da *Hala* bayan sallar zhur aka ɗaura auren *Umar-khan Abba Hakimi, da Hafsat Sheikh Aliyu Haydar* sai kuma *Prince Khalil Ahmad Nuran Sarki da Maimunatu Aliyu* Tare dana *Saifuddeen Abba Hakimi* Sosai aka sha shagali farin ciki wajan angwayen ba a magana, kada ma Khalil Yaji labari he can't believe wai yau ya auri Maimoon. El burinsa daman a sallami Fattoumah domin ƙasar zai bari da ita, duk da kwaɗayin Mai martaba na son yin murabus ya dan ƙawa El kujerar mulkin amma ya rufe idanu yaƙi sam, daga ƙarshe ma ya ce baya so shi yafi ƙaunar siyasa. Shiru babban makami ne shirun da Yaa Sheikh ya yi da wanda ya sanya El ya yi ya tayar da hankalin Fulani Atine domin ita ce wacce ta fitar da bayanan komai zuwa gidan jaridar da ba a son da zaman su ba, suka fara haɗa shi a twitter ya shiga jerin news ɗin da yake trending. Sai gashi ta fito tana surutai akan ko basu ga abin bane sun ɗauka wasa ne sai abu ya tabbata ta zare ta zama zautacciyya ta dinga tunawa kanta asiri abu yaci tura Mai martaba ya ce a dangana da ita zuwa gidan mahaukata. _*After 3 week's*_ Saukar su kenan daga airport Ummul da kanta ta zo ɗaukan su ta amshi Hala ta ce "Ma sha Allah, takwara tafi iyayenta kyau" Halisa ta ce "Kai Ummul kada dai ki ce yanzu ita kike so" Ummul tayi murmushi ta ce "Babu laifi idan nayi haka, a daina kwasar mata sanyi fa kusan weather ya sauya, ayi sanyi ai zafi daga haka damuna zata sauka" Yaa Sheikh yana tsaye a tsayin satin ukun zaka ɗauka shekara ɗaya ne, domin fatar shi ya sauya ya ƙara haske saje da gemu sun ƙara ƙawata fuskar ya daina aikin komai sai na wa'azi wanda ake sakawa a gidan redio da t.v yanzu, yana ji da gidan maruyansa. Ta dube shi ta ce "Me kuke ci a Sokoto ne?" "Laa ai satinmu ɗaya a can muka shige Makkah" Ummul ta riƙe baki ta ce "Ikon Allah ba gaya dangi" Suka shiga mota ita take jansu da kanta Halisa na baya shi kuma yana gaba rungome da Hala wacce Ubangiji ya sanya masa ƙaunarta yana jinya tana ta tsotsar hannun shi alamar nono take buƙata. "Idan zaka zauna da Zahrah to ba kayi mata adalci ba, naga tausayi na neman ya sanya ka shiga hakƙinta" Halisa tayi shiru domin a zaman da sukai ta fahimci haƙurin Zahrah daman wani lokacin akwai huɗubar ƙawaye. "Ummul..." "Aliyu" Yadda ta kiran sunan zaka san babu sauƙi a sanyaye yana shafa kan Hala da yake cike da suma ya ce "Kiyi haƙuri" Gani ya yi ta ɗauki hanyar gidansa mai makon na grandparents nasa, suna shiga suka samu Jadda riƙe da Apple tana ci ga jakar kayanta a gefe, Zahrah wacce ta rame sosai sbd tsananin buƙatar namiji ta miƙe ta ce "Wlcm Sweetheart" tayi ƙasa da kai ganin Ummul Jadda ta ce. "Daɗi miji, kin bi miji kullum cikin dare ya danneki kamar ayu babu mmki yanzu ya ƙara ɗirka miki wani cikin.... 08119237616 Paid book aji tsoran Allah an ga mana magana ina sane fa! Kawai duk abinda kafi ƙarfin shi babu batun tsayawa ɓata baki akai*Da wasu suka biya da wanda suke karantawa Free 🤣 aje arewabooks ayi following acct ɗina, har girma ake taɓa Allah wadai da masu fitar da book ba haka da masu karantawa matsayin free, to ina naga lokacin surutun hakan ma🤣 typing da ƙyar sbd busy, ku shiga link ɗin kai tsaye👇🏾ku danna following* https://www.arewabooks.com/notifications "To ai gwara nayi cikin dana zauna zaman gulma" Jadda tayi mitsi mitsi da idanu ta ce "Azaba, daga maganar alheri sai gasa magana to ai babu laifi don kin samu ciki da ki zauna hoto kamar wannan fa?" Ta nuna Zahrah kafin ta girgiza kai cikin takaici ta ce "Ga waccar ƴan banzar mai mugun hali ita fa ta dinga zuƙa matarka can watannin baya akan ta tsaneka" Halisa ta nemi waje ta zauna, Yaa Sheikh ya haura upstairs cikin nutsuwa tun a hanya ya fara zame Alkyabbar jikinsa sbd tsananin gajiya kuma tayi masa nauyi a jiki. Zahrah ta bishi da kallo tana son shi a ko wacce daƙiƙa yana ƙaruwa a zuciyarta, balle yanzu daya ƙara sauya ya riƙe kan shi haibarsa kullum ƙara bayyana ga cikar kamala. Jadda ta gyara zama tana ƙara saka Apple bakinta ta ce "Ina baku labari babu kalar wulaƙanci da tijarar da Likitan nan A'isha take kowa bata yiwa mijinta ba, wai baya haihuwa dake shi sauna ne ya tsaya yana biyewa Iskancin mace banda abinsa ba sai kawai ya saki ƴar kazan uba ta kama gabanta ba, mata nawa ne a duniya ba suyi aure ba suke jiran mazan shiru" Zahrah ko a jikinta, Ummul kuma tana riƙe da Hala wacce ta farka tana wurga hannu da ƙafa. Halisa ta mayar da hankalinta akan zancan Jadda amma zaka ɗauka maganar bai dameta ba, sbd yadda ta mayar da hankalinta zuwa ga plasma. Jadda ta girgiza kai irin zance na cinta ɗin nan. Ta ce "tijara kala-kala tayi ina baku labari, ashe burinta ta kashe auren, ta auri mijinku malam kinji rashin amana shi yasa amana tayi ƙaranci duk yadda Matar Malam ta yarda da ita amma zata aure mata miji, haka ta dinga zugaki dake kema rainon fulani ce kika biye mata, Allah dai ya yi mijinta ba zai wulaƙanta ba, kuma babu rabon ku zama ku uku ashe ita ce bata haihuwa, yanzu dai tana can ta fita hayyacina mijin kuma kamar maye yana nan riƙe da ita kamar takalmi a hammata" Cikin alhini ta ƙara girgiza kai ta ce "To ni dai bance komai ba, yanzu ma ba wani abu nace ba, amma dai ta kusa cin amana" Babu wanda ya kulata, Halisa kishi ya motsa Idanunta ya ya yi jajir domin gani take har yanzu Dr A'isha tana bibiyar Yaa Sheikh shi kuma ya san komai ya ɓoye. "Riƙe ta nan wannan dai ba tayi halin me suna ba, rigimarta yawa ne da ita" Jadda ta karkace ta ce "Azaba, Ƴar Fulani ce fa ta haifeta sai abinda kika gani" "Ke wai miye damuwarki ne? Me Fulani sukai miki? Kina zaune a gidan Bafullatani kina masa rashin kirki, kada ki manta me gidan Bafullatani ne mahaifinsa haka, matarsa haka jinin fulani ke yawo a jikinmu and we're proud to be Fulani" Jadda ta riƙe baki ta juya ta kalli Ummul wacce ta ɗauke kai kamar wacce bata san mene yake faruwa ranta fes kuma da abinda Halisa tayi. "Zagina kike fa?" Halisa ta rungume Hala a jikinta tana jin kamar ma ta wurgar da ita sbd haushin ubanta ya shafe ta ta ce "Zagi ko Gasky, wallahi sai na haɗaki da Aljanu cikin dare suyi maganinki" kus Jadda tayi ta kasa gwaggwaran motsi. Zahrah da magana bata dameta ba ta miƙe tsaye tare da nufar kitchen ta haɗuwa Ummul kayan motsa baki ta ce. "Sannu da hanya Ummul" Ummul tayi murmushi ta ce "Yawwa Zahrah, ai bana jin zanci komai tafiya zan yi" "Tun yanzu Ummul" Ummul ta ce "Eh, kira mini Aliyu" Zahrah ta nufi upstairs Ummul ta bita da kallon tausayi. Fitowar shi daga wanka kenan ya zura Jallabiya mai sauƙin nauyi sbd garin ya ɗan yi ɗumi ga heater data ƙara gasa bedroom ɗin. Ruwa na zuba daga sumar gashinsa ya zube a gefen lafiyayyan gadon shi yana lumshe gajiyayyun Idanunsa masu nauyin gaske. Da sallama ta shigo ya amsa cikin murya mara sauti. Tsayawa tayi tana kallon shi ya cika mata idanu ainun tama kasa ƙara sawa. Idanunsa a rufe amma yana jin idanu na yawo a jikinsa alamun ana kallon shi, speaking calmly ya ce. "Baki sanni bane" Tayi murmushi tana ɗauke kai ta ce "Farin sani na, kawai You have changed" Ya miƙa mata hannu alamar ta zo, ta ƙarasa zata zauna nesa da shi ya jawota sukai kusa ta ce "Sannu da zuwa ya hanya?" Ya yi shiru. "Ya kuka baro mutanan sakkwatawan Shehu?" Calmly ya ce "Fatymerh Zahrah" ta amsa da "Na'am Abul-khairy" "Am sorry" ta ware idanu ta ce "For?" Ya saketa yana miƙewa tsaye ta bisa da kallo haka kurum ƙirjinta ya shiga bugawa da ƙarfi "Mene ya faru?" "Babu" ya bata amsa a taƙaice yana zura D&G couples slippers ta ce "Amma ban haƙurin na mene?" He just nods his head and quickly leave the room. Ta dinga bin bayansa da kallo. It's been 7mnts but till now nothing change, she loves him so much but all these times he rejected her love because he didn't like her. So what exactly he meant by saying sorry to her and har yanzu yana tare da ita something fishy! Ta zube akan ƙafafuwanta kuka na fargaba ta kufce mata, tana so da ƙaunar shi tana masifar jin shi a ranta amma Soyayyar *Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu* ƙaddara ce kuma jarrabawa! Ta ƙara yarda ba komai mutum yake so ba, azaba da soyayya babban abu ne Allah ya haɗata da soyayyar *Yaa Sheikh* sbd tarin laifukan data akaita. Bata iya barci kullum da ciwon mara take kwana kuma take tashi tun sha'awa na damunta har ta kawo lokacin da zata iya cewa bata ma jin sha'awar ta ɗauke ta kuma tafi bakiɗaya. A zaune ya samu Ummul ita da Halisa da tayi wanka ta yiwa Hala ta sauya musu shiga sukai kyau sosai daga Hala har babarta ya ɗan saci kallonta ganin ta haɗe fuska. Ya nemi waje ya zauna cikin nutsuwa yaja idanunsa ya lumshe yana ɗan jan gemunsa. "Aliyu!" Ya ware idanu gabansa har faɗuwa yake duk sanda Ummul ta kira shi da sunan da yake mancewa shi ne asalin sunansa. "Na'am" ya amsa ganin kamar akwai abinda zasu tattauna yasa Halisa ɗaukan Hala ta nufi bedroom ɗin da Jadda ta shiga. "Nasan kasan me kake kana da tsoran Allah, so ka ƙara sanya tsoran Allah cikin lamarinka, tuni zan maka Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce: Fazakkir fa'innàl zikkira tamfa'ul mu'uminun" Tayi jim ta ce "Ku tunatar domin tunatarwa tana amfanar mumini, na ɗauka kana son Zahrah shi ya sanya na zuba maka idanu naga kudun ruwanka, koda kana sonta zama kai da ita cutarwa ne, babbar soyayyar da zaka nunawa Zahrah shi ne ka haɗata da wani mai nagarta ka bashi aurenta, ita macace bata da kowa taci abinci ta kwanta dole akwai matsala saɓanin kai da kke namiji shekaru. Ko wacce daƙiƙa da mintuna idan suka shige basa dawowa, rashin dawowar na nufin abubuwa da dama ciki hadda lokaci,idan kayi amfani da lokaci a gurbin daya dace ba, idan ƙarin auren ka ke buƙata babu mai hanaka idan ma huɗu zaka zuba Aliyu" Ya dubeta da sauri ta ce "Ai Allah ya baka aron rai da damar yin mata huɗu ku? Amma kada ka zauna da matar da ba zaka amfana mata da komai ba, itama haka. Kada wannan tausayin ya yi gabala akan gasky ka saketa ka saki Zahrah Aliyu domin ta samu ƴancinta na cikakkiyar mace" ras! Gaban Zahrah ya faɗi komai suke faɗa a kunnenta. Tama kasa kuka sai a lokacin ta fahimci kuka rahama ne, zuciyarta ta dinga ɗagawa tasa hannu ta dafe ƙirjinta dake bugawa, sunan Allah kawai take ambata wanda yanzu har a zame mata abin ambato a kullum. "Kaji me na ce?" "In sha Allah" ya ce a sanyaye ta miƙe tsaye shima ya miƙe yana ɗaukan key car ta bisa da kallo domin tasan waye Yaa Sheikh ta kuma san ɗanta farin sani. "Kayi fushi dani ne Arɗo?" Ya ɗan marairaice fuska wanda ya saba yi a gabanta ta ce "Sannu fa" Ya gane me take nufi ya nufeta tare da shigewa jikinta Ummul ta sauke numfashi a yanzu a rayuwa ita babu abinda take so da ƙauna kamar Yaa Sheikh shi ne komai nata, shi yasa baya girma a Idanunta akan shi kuma taƙi amincewa da tayi aure. Babu wanda yake iya Fuskantar Yaa Sheikh da niyyar yi masa faɗa sbd ana ganin yasan kome bayan a rayuwar nan babu wanda baya buƙatar Mentoring. Ta shafa kan shi ta ce "Allah ya yi maka Albarka da zuri'ar ka" ta rufe idanu tana jin ƙaunar Ummul har ran shi. "Best mother ever, my best friend" ta dungure masa kai kamar yadda ya kewa Halisa ta ce "Ni ce Best friend ɗin?" Ya ɗan yi murmushi sukai waje ta ce "No thank you, ni da nake a mota zan je gida yanzu In sha Allah" "Allah ya tsare" ta ce "Amin". A nutse take driving har ta fice daga cikin makeken gidan na Yaa Sheikh. Ya yi shiru yana bin green flowers ɗin da suke wajan, bai shiga cikin gidan ba ya nufi gidan gonar shi wanda yake ɓangare guda a cikin gidan shi, tattabarun shi na ganinsa suka fara sakkowa ya nemi waje ya zauna ya zura ƙafar shi cikin ruwa yana watsa abinci kifaye suka taso sama. Baya ɗaya daga cikin wanda suke son ƙarin aure, matar shi ta wadatar da shi da komai, ba raga masa ba, abinci, kulawa, biyayya tana ɗauke buƙatar shi a koda yaushe tana bashi farin cikin da shi kan shi yake mamaki. Halisa ta dubi Jadda dake cewa "Ai Danta A'isha ba tayi ba, babu mamaki shi Malam ɗin ya san komai yaƙi faɗa miki, ke kuma daɗi miji kina baje masa ƙafa yana allan dungure a ciki sai fa ya kai ki ya baro ya ɗirka miki ciki, ki tashi mai kwanika ga goyo ga ciki, yo shi meye ruwan shi? Namiji ai sam bai da kunya daman tunda naga yana azumi kullum nasan babu lafiya" Tayi ƙasa da murya ta ce "Don ma ya haɗu da fitinanniyya irin shi duk sun zama ƴan iska suna sharholiyya a gaban jariri" sosai Halisa ta jita amma tai burus. Daga Zahrah har Halisa babu wanda ya sake ganin Yaa Sheikh. Ta samu Hala ba tayi rigimar data saba ba, dinner ta haɗa mai kyau tayi Alwala da sallah kana ta shirya ta baza turare. Tana zaune a parlourn dake part ɗinta tana feeding Hala ƙamshin turaren Roja ya bayyanar da zuwan shi kafin kamilalliyyar muryarsa ta bayyana cikin nutsuwa ya shigo ta amsa sallamar babu yabo babu fallasa. Kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke kai kawai ya yi mmki domin ko Hala na bayanta tana barci yana shigowa take tashi ta nufesa shi kuma ya rungumesu bakiɗaya. Ya zauna kusa da ita speaking calmly ya ce "Madam yunwa na keji" Tayi shiru ya kalleta da kyau Idanun Hala ya sauka akan mahaifinta ta dinga bin duk inda yabi da fuskar shi daya tabbatar shi take kallo ya saka hannu ya ɗauketa. "Malam ba kaga nono nake bata ba?" Not looking at her ya ce "Ni sai na sha" Ta haɗe fuska ta ce "Ko Dr A'isha ba" maganar ta dake shi ya kalleta sai bai ce komai ya lura rigima take ji. Ta ce "Ni dai duk ƴar iskar da take kula mini miji wallahi ban yafe ba" nan ma yaƙi kulata sai kawai ta fashe da kuka sosai ta ce "Ka auri Zahrah ban sani ba, shi ne yanzu wata banza can Dr A'isha take kulaka bayan da nata miji" Shi abin dry ya bashi ya kwantar da Hala a gefensa ya saka hannu ya damƙo Halisa tayi ƙara ya jawota da ƙarfi ya matseta a jikinsa idanunsa rufe ya fara farke wuyan rigar Jikinta ya ce "Yarinya tsiwa ki ke ji ko?" Ta girgiza kai ta ce "Ni fa bance komai ba" Idanunsa ya yi jajir ya rufe bakinta ta hanyar zura nasa ciki ɗif tayi kisses ɗin bakinta yake kamar zautacce kana ganinsa kasan daman ya jima haƙuri kawai yake sai daya gama huɗu mata jiki tun kafin aje babban masauki ta fara ƙoƙarin guduwa kullum ji take kamar ana ƙarawa Abban nata ƙarfi ya miƙe yana cire Jallabiya tare da ɗaukan Hala wacce ke tsotsar hannu bata san duniyar sharholiyyar da ake ba, ya kwantar da ita akan bed ɗin kana ya sunkuci Halisa har tsakiyar gadonta.... Washegari da safe suna zaune suna breakfast Jadda sai kwasar farfesu take Yaa Sheikh a hankali yake shan kunun gyaɗar dake masa daɗi wanda indai bashi ya sha da safe ba baya jin daɗi. Halisa ta kasa haƙuri ta ce "Abba" ya ɗago gajiyayyun Idanunsa ya watsa mata ta ce "Sau biyu ina zuwa duba Zahrah ina ganin part ɗin a rufe fatan lafiya?" Jadda ta ce "Ban taɓa ganin yadda kishiya ke damuwa da kishiya ba sai a wannan gidan kamar wanda aka haifa ciki ɗaya" Yaa Sheikh ya yi shiru sbd ba ɗabi'ar shi bace yin magana idan yana cin abinci gabaɗaya yanzu ne ma bakin nasa ya buɗe. "Modibbo" Ya ajjiye cup ɗin hannunsa tare da ɗaukan tissue ya goge bakinsa cikin kamala ya ce "Zan duba" "Wanne dubawa gata nan ta fito, ke ƴar nan lafiya? Wanna akwatin fa" Halisa ta miƙe tsaye ganin Zahrah janye da manyan akwati ta dinga dubanta ta ce "Tafiya zaki ne" tayi murmushi ta ce "Eh" ta ƙara duba akwatin ta ce "To ina zaki har haka kayan nan sun yi yawa fa" "Tafiyar har abada" Halisa ta kalli Yaa Sheikh da yake kallon Zahrah kenan taji me suka faɗa jiya? "Abba me yake faruwa ne, ina Zahrah zata?" Zahrah ta ce "Zan bar miki mijinki ne Halisa" a ruɗe ta ce "To amma ai bance wani abu ba, babu abinda ya haɗa mu" "Ƙaddara ta haɗa Halisa, kuma ita zata raba yanzu" Hawayen da take ɓoyewa ta zube gaban Yaa ta saki wani irin kuka ta ce "Ina son ka Aliyu, ina son Yaa Sheikh son ni kai na ban san adadin shi ba, wlh idan zan kwana na yini ban isa na faɗa abinda na keji a raina ba, duk mijin da zan aura ba zan iya yi masa biyayya ba zan zauna da igiyar auren wani amma soyayyarka ce a raina, don Allah don Annabi ka bani takardar saki,ka sakeni don Allah kamar yadda Ummul ta buƙata" Halisa ta riƙe Yaa Sheikh tana girgiza kai cikin kuka sosai ta ce "Kada ka saketa Abba, kada rabamu Abba ina son ta ina son zama da ita don Allah Habibi kada ka saki Zahrah I'll talk to her" Yaa Sheikh ya rasa ta ina zai fara ya saka hannu ya ɗago Zahrah idanunsa sunyi jajir Zahrah kuka Halisa kuka, Jadda na gefe tana zare idanu. A hankali ya tallafo fuskarta Zahrah yana kuma riƙe da Halisa ya ce "Ko wanne bawa akwai ƙaddarar shi, kada ki sare ina son zama dake, Ummul na son ki zauna dani amma zamu cutar da ke" Ya yi shiru ya ce "Wani sirrin idan Allah ya ɓoye zai fi kyau a rufe babu buƙatar faɗa, ina jinki har raina wani abun ba alheri bane a rayuwarmu amma idanunmu su rufe ki koma ga Allah, zai baki miji wanda ya fini" Tayi murmushi amma wani irin zafi zuciyarta ke mata ta ce "Na fahimta, amma a ko wanne zuciyata zata iya bugawa kawo yanzu nasan ciwo ya gama lalata zuciyata, Alfarma ɗaya nake so kayi mini" Ya riƙe fuskarta ya ce "Me kike so Fatymerh Zahrah?" "Sau ɗaya kawai, sau ɗaya kiss me hug me as goodbye" Halisa ta runtse idanunta a hankali ta sulale tabar wajan Jadda tuni tayi waje tana bawa maids ɗin gidan labari. Ya dubeta ta ce "Please kiss me, please Yaa Sheikh kiss me.... 08119237616Kamata Yaa Sheikh ya yi ya riƙe And he gave her a nice little kiss, some minutes ya zareta jikinsa numfashinta har riƙewa yake sbd yadda ƙamshin Roja ya shiga hancinta a ƴan minutes ɗin da tayi a jikinsa ji tayi komai ya tsaya mata. Ya kama hannunta zuwa waje can compound Jadda na ganinsu tayi ƙasa da murya ta kalli mai bawa flowers ruwa cikin nutsuwa ta ce "To ita wannan lokacin ita ce mai jawo manyan akwatinan tana cewa a saketa, ɗayar kuma zaka ganta kamar zabiya don fari mai ƴar jaririya ita ce take kukan kada ya saketa fa" Shi dai kallonta yake ta ƙara karkacewa tana ƙasa da murya ta ce "Duk yadda akai ta fahimci baya son ta ne, shi kuma kasan miskilanci gare shi ba zai taɓa cewa komai ba, jiya fa suka dawo daga Madina ina kyautata zaton ya ƙara sakar mata wani cikin ne domin farin nata bana lafiya ne ba" Duk abinda take faɗa kai tsaye yake shigewa kunnen Yaa Sheikh ko inda take bai kalla ba, ya nufi motar shi mai baƙin glasses ya buɗewa Zahrah ya fahimci bata hayyacinta. Tana shiga ya saka aka zuba kayanta a bayan mota shi kuma ya shiga mazaunin driver. Cikin nutsuwa yake driving yana jin yadda take kuka amma ya kasa cewa komai, kukan shi ne sauƙi ga zuciyarta. Dab da gidan Abba Hakimi ya gangara gefen titi tare da yin parking ya kashe motar, ya sauke numfashi cikin kulawa da son kwantar mata da hankali ya ce "Stop crying Fatymerh Zahrah!" Ta kalle shi ta ce "Me ya sa? Ban san ranata da daina kuka ba Yaa Sheikh naso na ƙare rayuwata ne bakiɗaya da kai kuda baka kusanci inda nake ba" Ya kalleta da kyau baya son bayyana sirrin shi ga kowa kamar yadda ya riƙe sirrinta ga matar shi Halisa har yanzu bata san bai kusanci Zahrah ba, ya ƙudiri niyyar ba zata sani ba ɗin. "Ki ɗauka hukunci ne daga Ubangiji, kada ki yarda zuciya ta ɗebeki yarda da ƙaddara Zahrah" Ta jinjina kai ta ce "I believed in fate, but my destiny is too hard My heart aches and I want to die and rest in this life" "Come here" ta ƙarasa kusa da shi very close to him. Ya riƙeta ya ce "Repeat after me" Ta jinjina kai, tana share Hawayen Idanunta amma kukan yaƙi tsayawa. Yaa Sheikh was speechless sun jima a haka kafin cikin nutsuwa yana riƙe kan shi ya ce "ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﻋَﺒْﺪُﻙَ، ﺍﺑْﻦُ ﻋَﺒْﺪِﻙَ، ﺍﺑْﻦُ ﺃَﻣَﺘِﻚَ، ﻧَﺎﺻِﻴَﺘِﻲ ﺑِﻴَﺪِﻙَ، ﻣَﺎﺽٍ ﻓِﻲَّ ﺣُﻜْﻤُﻚَ، ﻋَﺪْﻝٌ ﻓِﻲَّ ﻗَﻀَﺎﺅُﻙَ، ﺃَﺳْﺄَﻟُﻚَ ﺑِﻜُﻞِّ ﺍﺳْﻢٍ ﻫُﻮَ ﻟَﻚَ ﺳَﻤَّﻴْﺖَ ﺑِﻪِ ﻧَﻔْﺴَﻚَ، ﺃَﻭْ ﺃَﻧْﺰَﻟْﺘَﻪُ ﻓِﻲ ﻛِﺘَﺎﺑِﻚَ، ﺃَﻭْ ﻋَﻠَّﻤْﺘَﻪُ ﺃَﺣَﺪًﺍ ﻣِﻦْ ﺧَﻠْﻘِﻚَ، ﺃَﻭِ ﺍﺳْﺘَﺄْﺛَﺮْﺕَ ﺑِﻪِ ﻓِﻲ ﻋِﻠْﻢِ ﺍﻟْﻐَﻴْﺐِ ﻋِﻨْﺪَﻙَ، ﺃَﻥْ ﺗَﺠْﻌَﻞَ ﺍﻟْﻘُﺮْﺁﻥَ ﺭَﺑِﻴﻊَ ﻗَﻠْﺒِﻲ، ﻭَﻧُﻮﺭَ ﺻَﺪْﺭِﻱ، ﻭَﺟَﻠَﺎﺀَ ﺣُﺰْﻧِﻲ، ﻭَﺫَﻫَﺎﺏَ ﻫَﻤِّﻲ” Yana faɗa tana faɗa ta sauke numfashi cikin nutsuwa ta ce "Thank you" "No!" Ta dube shi cikin rashin fahimta ya ɗauke idanu ya ce "I have to thank you, for understanding me" kamar anyi forcing nasa to talk ya ce. "Yola?" Ta jinjina masa sai kuma ta ce "Eh gida zani, nama ji Daddy ya sai da gidan" "Zaki amince dani? Na aurar dake?" Tayi ƙasa da kanta kafin ta ce "Zan so na baka wannan damar, amma ba zan sake aure ba. *NA GAMA AURE* zan riƙe yarona Muhammad In sha Allah zuwa sanda Ubangiji zai amshi rayuwata" maganar ya shiga Yaa Sheikh. Sai kawai ya yi shiru tare da yiwa motar key ya nufi gidan Abba Hakimi, Umma A'isha ta nuna Zahrah ɗaki kafin gobe ta shige Yola, Yaa Sheikh ya zauna wajan Abba Hakimi suka ɗan tattauna da har Umar-khan ya shigo shi da Hafsat dake laulayi tana ganin Abban nata Yaa Sheikh ta sunkuya ta gaishe shi kai kawai ya jinjina mata. Abba Hakimi da yake matsayin suriki ya ce "Hasfat Sheikh Aliyu fatan lafiya kuke?" Ta sunkuyar da kanta ta ce "Lafiya lou Abba" Yaa Sheikh yana gidan har sallar Issha suna ta magana da Abba Hakimi can kuma Abba Hakimi ya kira wani a waya. Zahrah ta kalli Abba Hakimi dake cewa. "Kiyi haƙuri amma na biye Malam ina da yaƙinin ya yi miki zaɓi na alheri ki amince, an ɗaura aurenki da Saifuddeen ga sadakin ki" Idanunta ya cika da hawaye ta ce "Ba komai Abba, Yaa Sheikh ya yi mini komai yasa na san wace ni ya bani ilimi sanadin shi na zama mace komar kowa Allah yasa zaɓin shi ne ya zama alheri a gare ni" Abba Hakimi ya miƙe yana faɗin "Allah ya yi miki Albarka Zahrah, mun yi magana da Alhaji Farouk mahaifinki ya amince idan ba damuwa ba sai kin koma ba za a kawo miki Muhammad ɗin" Tayi godiya Yaa Sheikh miƙe yasan kawo yanzu Halisa hankalinta ya ta shi ta ce "Na gode sosai" Yana yin waje abin shi ya ce "Ki ɗauke ni like a brother to you komai ki ke so come to me, happy marriage life" ya yi waje abin shi ta bisa da kallo zuciyarta nayin wani zafi. Lokacin daya isa gida Jadda ta jima da yin barci, direct part ɗinsa ya nufa ya cire Jallabiya ya yi wanka ya sauya kaya zuwa white Pajamas riga da wanda sai ƙamshin Roja yake yana jin zuciyarsa ta rage nauyi sbd hakƙin Zahrah daya sauke, daman bata da iddar shi wannan dalilin ya sanya ya ɗaura mata aure da Saifuddeen wanda shi da kan shi ya amince. Steps ɗin benen yake takawa zuwa downstairs a haka ya nufi part ɗin Madam Halisa ya murɗa handle bakin shi ɗauke da sallama, bashi da tabbacin tana parlour sai ta shige bedroom ya sameta tsaye gaban wardrobe,tana ƙoƙarin sanya night gown cak taji an ɗage ta sama, ta zaro kumburarrun Idanunta waje ta ce "Habibi kaya zan saka" yana kwantar da ita tare da rufeta da ƙirjin shi yana goga mata fuska a wuyanta yana shaƙar ƙamshi murya can ciki ya ce "No need" ta riƙe shi ta ce "Please mana, kuma.....," "Zawja tsarin iyali?" Ya faɗa yana ƙara taɓa gefen hannunta. Ta ce "Sbd Hala na saka, kuma kasan yanayinka Habibi" ya yi ta kallonta idanunsa sun yi jajir jijiyoyin kansa duk sun fito sai huci yake ya tsareta da manyan idanunsa a hankali ya saketa tare da miƙewa zai fita ta diro daga kan bed ɗin tare da shan gabansa ta ce "Ka fahimce ni Please Habibi bada wata manufa nayi haka ba" ya saka hannu tare da matsar da ita gefe, ta ƙara yin gaba zata riƙe shi ya buga mata wata kyakkyawar tsawa cikin faɗa ya ce "Move!" Taja jikinta wanda yake ta rawa da ɓari bata taɓa jin tsawar daya shigeta irin wannan ba, sanadin haka ya tayar da Hala ta saka kuka kafin ta ƙarasa yaje ya ɗauke yarinyar shi tare da bar mata ɗakin. Kuka ta dinga yi hankalinta ya tashi bata taɓa hango masifar Yaa Sheikh a ƙwayar idanunsa kamar yanzu ba, ta jima tana kuka wajan ƙarfe 12 ta miƙe ta nufi upstairs ta samu ƙofar shi a rufe, ta dinga knocking yana jinta ya share. Yaa Sheikh ya daɗe bai shiga ɓacin rai irin wannan ba, yana so da ƙaunar zuri'a mai yawa da kuma albarka amma ace tun a haihuwar fari mace tayi tsarin iyali me hakan ke nufi? Ya dubi Hala Sheikh Aliyu haydar dake ta sukur-sukur a ƙirjinsa ta ƙiyin barci da alama nono take buƙata, ya shafa kan yarinyar dake cike da suma gwanin sha'awa kamar ya tsokanota ta saka kuka tana shura ƙafa, ya shiga jijjigata amma fir Hala taƙi yin shiru zam-zam ya ɗauka ya bata ta sha sosai yarinyar akwai kuka kamar mahaifiyarta. Ya sanyata a kafaɗa ta shiga tsotsar fatar wajan murmushi mai laushi ya yi ya ce "I love you Hala, and i so much love your mother amma halinku ɗaya, mene laifi don ta sake yin ciki bani nake bata ƙwayayen ba? Ni ban gaji ba sai ita?" Tayi masa ƙuri da manyan fararen idanunta kamar mai fahimtar mai yake cewa a haka suka raba dare da ƙyar tayi barci tana tsotsar lips ɗin shi kamar ta samu nono ya rungumeta yana ƙara jin soyayyar mahaifiyarta a ran shi ya kasa barci kamar yadda Halisa ta kasa. Da azuba tana farkawa Idanunta ya sauka akan Hala tayi mmkin yadda aka sauya mata wajan kwanciya domin a ƙasa barci ya ɗauke ta dab da Subhi yanzu kuma ta ganta akan gado. Sallah tayi ta goya Hala ta shiga kitchen ta haɗa breakfast, tana gamawa ta yiwa Hala wanka ta shiryata ba jimawa barci ya ɗauke ta itama tayaya wanka ta shirya tsaf cikin wani green lace mai kyau ta murza ɗauri. Ta samu Jadda a parlour tana shan tea ta haura upstairs, tayi sallama ya amshi murya can ƙasa yana zaune saman kujera ya ɗora ƙafa idanunsa sanye cikin glasses hannunsa riƙe da azkar sai laptop a gefe da mug ɗin coffee ta tsokana ta ce "Mrng Habibi" ya amsa a ciki ta ce "Breakfast is ready" ya yi mata banza. Abu kamar wasa har tsayin sati Yaa Sheikh ya ɗauke mata huta tsakanin shi da ita gaisuwa idan ya tabbatar lafiya take sai ya ɗauke hala. Tuni Jadda ta gudu tace ba zata iya da masifar shiru ba. A kwana na goma ta same shi kwance ya lumshe idanunsa dawowar shi kenan daga duba banks da Companies ɗin shi da gidan marayu. Ya ƙarasa gidan Abba Hakimi ya duba Umma A'isha dake zazzaɓi ya samu Zahrah ta ɗan kwantar da hankalinta. Yana jinta yaƙi magana ta daddage ta fasa masa ihu aka tare da birgima, bai san mene ya faru ba sai ganinsa shi ya yi riƙe da ita yana jijjigata ya ɗauka aljanu take. "Ke lafiya Zawja?" "Abba ka mayar dani gida tunda baka so na baka ƙaunata ka juya mini baya, na baka haƙuri nace na cire in-plan ɗin" yaja jiki ya kalleta da kyau ya ce. "Zawja ni ne baki so, tunda baki son bani zuri'a daga gareki" tana kuka sosai ta ce "Kayi haƙuri Habibi ba zan sake ba, surutu ne bana so kada a ganni da wani cikin nayi maka al'ƙawari haihuwa har sai lokacin da Ubangiji zai tsayar da ita daga gareni" Ya kalleta kawai daman tuni ya huce domin sunyi magana da Ummul kawai ya rabu da ita ne yaga gudun ruwanta. Ta dinga kuka ya ce "Meye?" "Baka kuya mini baya ba ƴarka kawai ka sani" Ya sakko daga kan kujerar ya juya mata baya ya ce "Hau" ta maƙale kafaɗa ya ce "Ai baki isa ba, ga bayan nan dole ki hau" taƙi ya ɗauketa ya sata suka zagaya wajan kana ya sauketa. "Me ka ke so?" Ya girgiza mata kai ta ce "Kana nufin babu? Abba kwana goma bama tare fa?" Ya buɗe baki zai magana tayi saurin haɗe bakinsu ta shiga bashi wani kyakkyawan kisses a wannan lokaci sai da Halisa ta goge gabaɗaya fushin Yaa Sheikh ta ƙara bashi mmki domin ta gama gane lagwan shi. *2 months later* Mai gadin su Fattoumah aka yanke masa hukuncin jifa kamar yadda addini ya faɗa, ɗan shi kuma aka yanke masa hukumcin zaman kaso akan amfani da kayan soja da tuhumar shi kan siyar da miyagun kwayoyi. Ɓangaren Fulani Atine hauka sai abinda ya ƙaro babu sauƙi cikin lamarin. Dada na fama cikin wata huɗu, Maimoon da Hafsat duk cike gare su haka matar Saifuddeen.. a lokacin Zeefa ta samu miji itama aka sanya aurenta. Rayuwa taiwa kowa daɗi banda Surayyerh dake faman neman miji idanu rufe amma bata samu ba, gabaɗaya samarin sun gudu taƙi amfani da damar da Ubangiji ya bata tun tana da lokaci taƙi amfani da shawarar mahaifiyarta. Ummul ta riƙe Shatu wajanta tana kula da komai nata taƙi yin aure duk har zuciyar Yaa Sheikh yana son yaga mahaifiyar ta shi da aure amma ya kasa furta mata. El tunda ya ɗauke Fattoumah Angela ba'a ƙara jin motsin shi ba. Ta dubi cikin gerden ɗin da ya ya yi mata kyau sosai a hankali ta ɗaga kanta zuwa gefe wajan wani ruwa taga an saka. *_Happy 1 year Anniversary_* Ta ƙara juyawa zuwa wani wajan da aka saka _*To My wife Zawja*_ ta dubi ƙaton zanan heart ɗin gently ta taka zuwa ƴar rumfa mai kujeru guda biyu an saka cake a tsakiya da ƙaton frame na picture nasu su biyu an rubuta. _*"OUMU-HALA*_ Marrying you was the smartest thing I ever did, happy 1 year Anniversary Zawja"_*IDAN BA KE 83 End*_ O Allah, I have greatly wronged myself and no one forgives sins but You. So, grant me forgiveness and have mercy on me. Surely, you are Forgiving, Merciful. My biggest Fans i no words to thank you, ban sani ba amma kullum masoya ƙaruwa suke, Ba zan saka *IDAN BA KE* cikin tops popular book's ba, but i can say zai iya zama The best book among the other's, godiya ga *Paid grp 1* godiya ga *Paid grp 2* special thanks to *My special grp* girmamawa ta musamman ga *Arewabooks* Nimcyluv sarauta loves you always forever ever. _Special thanks to these people who are important to me_ NASIR NID, FAUZIYYA D SULAIMAN BRIGHT PENS, Sauran marubutan da suka bibiyeni a wannan littafin kuna da yawa i can't list them thank you all. Thank you my parents thanks for support and care rabbi ya saka muku da alheri. 🤣 Ƴan wasa na ina godiya Uncle Sheikh Aliyu ina tsoran haɗuwa da kai serious, Brother Bashir Mubasshir, Ummul🥰 and the rest Sorry Khalil🏃🏼‍♀️. _Oh! I almost frgt to thank my people those who read my book as free nasan soyayya ce ba zance ban yafe ba amma littafin kuɗi ne ga duk wanda ya yi niyyar biya contact me 08119237616. Ƙofa a buɗe take ga abinda aka yi kuskure, yabawa, jinjinawa, sharhi yadda kuka ji daɗin labarin da gyaran ban ɗaukewa kowa ba am ready to accept my mistakes👏🏻_ Complete Book 1 2 ga mai so dubu ɗaya 1k. This page dedicated to my husband much much love ❤️❤️❤️❤️❤️ Ta juya da sauri domin ba ƙaramin surprising nata ya yi, idanunta cike da ƙwalla da kuma soyayyar mijinta ta riƙe Yaa Sheikh ta ce "Yaa Allah, i so much love you Habiba you're the best husband ever Allah ya ƙara maka arziƙi da wadata ya taimake ka" ya holding nata back yana sakin murmushi mai kyau idanunsa lumshe ya ɗauki wayarsa tare jawota jikinsa sosai ya yi musu selpie. Hala nada shekara ɗaya ciff a duniya Halisa ta kuma samun wani cikin a wannan lokacin farin cikin Yaa Sheikh har yafi na baya, Ummul ta kalli Yaa Sheikh daya fito daga ɗakin grandpa ɗin shi ta ce "Ku barni mini Hala mana, sbd yayeta dole za tayi" Ya kasa cewa komai domin ba ƙaramin nauyi ya ke ji ba, ganin yanayinsa ya sa ta ce "Ina Halisar fa?" "Tana wajan Mubasshir waje" Ummul ta buɗe ido ta ce "Yau kuma, yaushe yazo da Fattoumah?" Yana yin waje tare da covering jikinsa da Alkyabbar jikinsa ya ce "Uhm maybe yau ko?" "Ok kirata muji" ya nufi waje tun daga nesa ya hango hasken fatar jikinta domin shigar sabon cikin ya sanya tayi wani irin fari kamar wacce jini ya ƙarewa.. da idanu ya kalleta ta miƙe tsaye tana kallon Fattoumah ta ce "Mijina na kira, ke kam Hamma El ya lalata miki tarbiyya" El dake jingine jikin mota Hala na riƙe gemunsa yaji maganar Halisa sama-sama ya ce "Angela me princess take cewa?" Fattoumah tayi murmushi ta ce "Cewa tayi yaushe zaka sama mini kamar Hala?" Ta faɗa tana kashe masa idanu ɗaya. Ya girgiza mata kai ya ce "Bayan ajjiyar da nayi tun watan daya shige wani kuma ki ke so? Don't worry I'll give you more" "Kasan kuna kama da Hala? Dama kawai abar mana" El ya ce "Rufa mini asiri Angela daga Abba Sheikh har Princess babu mai iya bayar da Hala wannan yarinyar kamar gold, kuma maganar kama ai ba abin mmki bane ni da babarta kamar twins haka muke wajan kama da juna, Hala kuma kamar su ɗaya da babarta that's means mu uku muna kama da juna" Fattoumah dariya tayi tana shigewa cikin gida wajan Ummul El Yabi bayanta yana zuwa Halisa ta ce "Prince ɗan muga Hala zan saka mata ring" bai kawo komai a ran shi ba ya miƙa mata ita ya shige ciki, yana shiga Yaa Sheikh ya kama hannu matar shi zuwa mota ya jasu har zuwa airport a hanya ya kira Umar-khan suka haɗu ya bashi key ɗin motar Umar-khan na tsaye shi da Hafsat da Jaririyarta mai suna Ajimal har jirgin su Yaa Sheikh ya lula sama zuwa gari mai albarka Madinatul-munauwara. A vip suke _very important people_ suna shiga ya zame Alkyabbar jikinsa ya ajjiye gefe yana lumshe idanunsa tare da jan numfashi sai yanzu abin ya bashi dariya da kunya sun gudu da ƴar su sbd kasa su barta wajan Ummul. "Habibi ƙalbi naji kunyar Ummul" "Uhm" ya ce yana kallonta kafin a hankali ya miƙa mata hannu ya ce "Zo kiji" ta kwantar da Hala a kan wata kujera ta ƙarasa wajansa suka kalli cikin idanun juna, ba zata iya cewa ga abinda Idanunta ya hango mata ba, tana karantar kallon shi, ko shirun shi amma yau abubuwan da suke gilmawa a cikin idanunsa daban suke. "Shekarar ki nawa ne?" Tambayar ta bata baki sosai kafin ta ɗaga Idanunta sama alamar tunani ta daki ƙirjin shi ta ce "I think 18 going to 19 what happing?" Ya girgiza kai ya ce "No! kin zama big Mama Zawja" tayi dry sosai tana kama gemunsa tare da kitsawa ta ce "Ba dole ba, ina samun kwanciyar hankali, soyayyar miji kulawa ka romantic style naka kala-kala" ya zura hannunsa a ƙirjinta yana sauke wani zazzafan numfashi idanunsa ya jirkice ya tura kan shi a wuyanta tare da manna lips ɗinsa ya shiga bin fatar wajan da tongue ɗin shi. "Modibbo" Ta zame fuskar shi da ƙyar ya watsa mata idanu ta ce "I love you Modibbona" ya runtse idanu ya buɗe yasan bata san tasirin da I love you ɗinta ke da shi a zuciyarsa shi ne a sanya kullum take narkar masa da zuciya da hakan. "Tsoho ki ke so?" "Bana kallon tsofan kyakkyawan saurayi nake kallo" ya jinjina mata kai tare da kafe ta da kallo. "Wannan kallon fa?" Ya riƙe kafaɗunta cikin nutsuwa ta sarƙewar murya ya ce "Shekaruna 37 cif, shekarunki 19 lokacin cika she 40yrs kina 22 ba za kiga tsofana da furfurana ki juya mini bay...," Bakinta da yaji cikin nasa tayi masa wata kyakkyawar sumbata yasa ya ƙarasa haɗiye sauran maganar a zuciyarsa. Sai da tayi kisses nasa da kyau kafin ta ce "Har abada, gaban abada idan zan rayu to dakai ne" Ya lumshe ya girgiza "I feel empty without you IDAN BA KE Just..." Sai kawai ya rungumeta a ƙirjinsa yana shafa cikinta ɗumin cikin na ratsa hannunsa farin ciki sosai yake ciki za'a ƙara haifa masa Baby. Sai dare jirginsu ya sauka haɗaɗɗun motoci suka zo ɗaukan shi, har gidan shi aka kai shi daren ranar basu runtsa ba gefe guda aka ajjiye Hala suka kwashi soyayya mai cike da tsafta. YAA SHEIKH bakinsa baya iya furta abubuwan da yake ji game da Halisa Danejo Rome, gangar jikinsa ita ke fansar bakinsa hakan yasa yake ƙara shigewa zuciyar Halisa a ko wanne lokaci,ko wacce daƙiƙa ko wanne harbawar seconds. Faɗan su baya ɗorewa domin Halisa ta gama gane waye mijinta duk son da yake mata ta nayin ba daidai ba zai rufe idanu ya yi mata faɗa tas, idan kuma ta ce kawai ya mayar da ita gida a lokacin zan sakko daga dokin zuciyar tare da accepting apologies ɗin ta, ta hanyar sauke mata mazantakar shi. Ɗaliban shi na ISLAMIC UNIVERSITY OF MADINA. Sukai farin ciki sosai domin suna ƙaunar lecture ɗin shi, yana nan da kame kan shi fuska kame Kullum ya ƙara daddako cikikar kamala kwarjini ba a magana. Rayuwa ta dinga juyawa ci-gaba ya dinga zuwa ta ko'ina, a haka har Halisa ta ƙara haihuwar kyakkyawar yarinya sak mai kama da ita, idan Yaa Sheikh ya kalli Halisa ya kalli Hala ya kalli Rohna mamaki yake gabaɗaya kamannin Zawja suka ɗauka lallai ya amince Ƴar fillo ta fishi fitina da ƙwazo. Da shi da wata bahaushiya suka dinga kulawa da Halisa har ta samu cikakken wata biyu. A wannan lokacin ne kuma aka fara azumi. Ana gobe sallah tarihi ya maimaita kan shi domin kiran gaggawa suka samu daga ƙasa Nigeria an kuma ƙi faɗa musu abinda yake faruwa. Babban tashin hankalin Yaa Sheikh bai shige yadda yake kiran Ummul wayar a kashe a haka har suka dira a Nigeria. Lokacin biyu ga sallah Halisa ta samu tayi Oummara a karo na biyu hajji ne Allah bai bata iko ba. Yaa Sheikh ya dubi idanun El-bashir da yazo ɗaukan su a airport, sosai ya firgita da yanayin El. Ya kasa jurewa ya ce "Mene ya faru Mubasshir?" Da sauri El-bashir ya rungume Yaa Sheikh yana sakin ajjiyar zuciya. Maimoon wacce ita tayi namijin ƙoƙarin bayanta goye da Ajimal ta amshi Rohna Shatu ta amshi Hala wacce ta fara dabo Yarinyar gwanin sha'awa tayi ƙiba sosai sai tayi kamar haifaffiyar Makka ɗin. Halisa ta kasa fahimta tunaninta ya tsaya duk yadda taso ta fahimci abinda yake faruwa ta kasa ganewa. Da ƙyar El ya yi driving har zuwa gida tun a ƙofar gida ƙirjin Yaa Sheikh ya buga sbd cikar mutane. Ganin Yaa Sheikh ya dawo musu da mutuwar sabuwa fil! A zuƙatan su Umar-khan, Ishaq-Hakim, Saif-wazir suka rungume Yaa bakiɗaya suna kuka sosai domin yanzu shi suke kallo matsayin Uba. Mother, Dr A'isha da Yaya Halima duk suka zagaye shi tare da zuba masa idanu ya rasa mene ke faruwa da shi, ko a ba'a faɗa ba kai tsaye ya fahimci cewa Abba Hakimi gone, he's no more, he pasted away! That's means Halisa's grandpa babu shi baya nan a raye a wannan duniya. Ya zame jiki da ƙyar kai tsaye part ɗinsa na gidan Ya nufa jiri na kwasar shi luuu ya yi Ummul dake zaune daman ta san za ayi haka tayi saurin riƙe shi, gabaɗaya jikinsa rawa yake ya rungume Ummul sosai ya hanata motsi lokaci ɗaya zazzafan zazzaɓi ya rufe shi, Shi ɗaya tal a duniya ya kewa kallon Uba majin gina tun yana yaro a ƙasa matsayin rarrafe Abba Hakimi ya fifita shi fiye da yaran daya haifa. Tsayin kwana uku babu mai zuwa wajan Yaa Sheikh ya yi tawakkali amma shirun bayin kan shi bane, jama'ar dake kan shi suka rufe masa baki baya ko tari sai kallo da idanu. Lokacin daya dawo daidai abinda ya fara tambaya shi ne mene ya faru? Aka shaida masa ciwon ciki ne farat ɗaya bayan ya ɗauki sahur da asuba kafin Assalatu rai ya yi halin shi. Yaa Sheikh ya tattara gabaɗaya dukiyar Abba Hakimi akaiwa yaran shi rabon gado. Tun daga ranar suka ɗauki Yaa Sheikh matsayin Uba yadda su kewa Abba Hakimi kallon Uba haka suke masa. Ya tsaya tsayin daka akansu har tsayin shekaru huɗu lokacin yana da shekara 40 ciff, yaransu biyar Hala, Rohna, Huda, sai namiji Aka sanya masa sunan Abba Hakimi suna ce masa Hakimi sai ƙaramin su Taujid. Huda da Hakimi tagwaye aka haife su, kwanakina take zubawa sosai duk shekara sai ciki abin ya dameta amma fur Yaa ya rufe idanu ya ce Allah ya hore masa idan ma duk wata zata haihu dole ta dage da gyara. Zahrah duk daga kan Muhammad bata sake samun haihuwa ba data samu cikin zai zube baya zama, haka ya riƙe Muhammad ya yi wayo sosai. Umar-khan da Hafsat a tsayin shekara shida ɗin nan yaransu biyu, haka Maimoon da Khalil, El-bashir Ahmad Nuran Sarki da Fattoumah Aliyu ɗan su ɗaya mai sunan mai martaba a yanzu kuma shi ne Sarkin Sokoto. Arziƙin Yaa Sheikh ya ninka haka bisa jajircewa da taimako. *20 year's later* Gidan cike yake Hala da Rohna sai kuka suke kamar ransu zai fita Hala ta ƙanƙame mahaifinta tana cewa "Abbi ban so, ban son auren kada a rabani daku na fasa auren" kuka take sosai Yaa Sheikh yana ƙaunar yarinyar shi ƙwarai komai nata na Halisa ne shi yasa yake jinta daban a zuciyarsa. Ya rungumeta yana bubbuga bayanta shekarun shi 60 cif ya zama babba mutum wanda ake kwatance da shi a hankali ya ce "Sorry Mamana, sorry" ta girgiza kai tana riƙe shi Rohna kuma Halisa ta riƙe tana cewa "Mami ki ce Abbi kada ya basu mu" school mate ɗinsu sai vedio suke musu haka photographers abin ya zama wani extraordinary. Mother da Dr A'isha suna kallon ikon Allah basu taɓa sanin haka Yaa Sheikh yake ƙaunar yaransa ba sai yanzu. Daga gefe guda aka saki tsaki mai kyau Hakimi ya juya zuwa ga ɗan yaron da ba zai shige 16yrs ba, baƙi ne shi sosai har sheƙi yake gabaɗaya shi ne ya banbanta a cikinsu ba zaka taɓa cewa daga cikin Halisa ya fito ba, shi ne last born nata. Labɓansa jajaye ne tas haka idanunsa farare ne gabaɗaya jikinsa zanan tattoo ne ra'ayin shi ya bambanta da duka sauran yaran. Ya ƙara jan tsaki yana saka hannu tare da har gitsa sumar kan shi wacce ta zama irinta Yaa Sheikh kala biyu. Hakimi ya ce "Abraham what exactly wrong with you?" Ya ɗaga manyan idanunsa yana miƙewa tsaye tare da bada faɗi idanunsa na lumshewa kamar mai jin barci a hankali speaking calmly ya ce "I don't know what exactly wrong with me, wannan ihun yana gab da fasa mini kai Please Hakimi do something i need to rest duk an cika mana gida da ihu kamar gidan mutuwa" Hakimi ya ce "Yaron nan baka da hankali, Big sister's naka suna kukan rabuwa da Mami da Abbi damu kanmu amma kana zancan iska" Abraham ya watsa hannu tare da buɗe ido sai ka ɗauka shi ne babba ya ce "And so what? Na faɗawa Abbi yaran nan ba zasu iya zaman aure ba, dani ya yi wa ta gidan ubanwa zan zauna ina kuka" Hakimi yabi ƙaramin ƙanin nasu da idanu yana mmkin faɗin ran yaron har tsoro yake bashi. Abraham rai ɓace ya saka hannu ya fisge Hala daga jikin Yaa Sheikh daidai lokacin angwayen suka shigo jin abinda ke faruwa. Idanun Abraham har wani ruwa ruwa ne yake kwanciya cikinsu ya kalli Junaid-Ali ya ce "Brother take your wife ta dame mu" Junaid-Ali ya yi murmushi ya ɗauke Hala cak tana zunduma ihu ya yi waje da abar shi. Haka ya ƙara fisgo Rohna ya damƙawa Abuturab ya ce "And you too take your wife" shi ma ya riƙe Rohna yaran sunyi mugun shaƙuwa da iyayensu sosai. Huda kuka take sosai na rabuwa da ƴan uwanta haka Hakimi idanunsa ya yi jajir banda uban tafiya Abraham ko a jikinsa sai ma riƙe kan shi da ya yi da hannu bibbiyu sbd juyawa yake baya ƙaunar hayaniya. Halisa ta juya zuwa bedroom ta dinga kukan rabuwa da yaranta tausayinsu ya kamata. Yaa Sheikh ya haura upstairs. Sauran ƴan bikin suka shiga mota zuwa rakiyar amare. Yana daga kwance ya miƙe zumbur yana jan lafiyayyan tsaki ya ce "Ni meye nawa laifin da ba za a yi mini aure ba?" "Kai yanzu idan akai maka auren kayi me?" Ya girgiza kai kawai yana jin tambayar rainin hankalin da Hakimi yake masa. Ya haura upstairs zuwa part ɗinsa har ya juya ya ce "And don't forget wallahi babbar mace nake so In sha Allah irin 40 to above ɗin nan ko 50" yana faɗin haka ya shige part ɗinsa yana taune lips. Surry har yanzu babu mijin aure, Jadda nan tsofa ya gama cin ƙarfinta Ummul daman bata zo bikin ba sbd bata ƙasar bakiɗaya. Shigowa ya yi ƙamshin Roja ya shiga hancinta ta ɗago suka kalli juna idanunta a kumbure ya yi murmushi yana zare Glasses ɗin idanunsa ya ce "Mene ya samu Mami ne?" Ta kwaɓe fuska ta ce "Are questing me? Bayan an rabani da yarana" ya jawota jikinsa ya ce "Oh! Sangartar Abraham ya yi yawa zo muje na baki wasu ƙwayayen haihuwar yanzu ki ƙinƙishi" Ya bugi ƙirjinsa ta ce "Ina tausayin Rohna" "Ni Hala" ta kalle shi ta ce "Hala gaba take da Rohna fa?" Ya rungumeta yana zame hannunta daga riƙe fuskar shi ya ɗauketa yana cewa "Mamana halinki ta ɗauka, mijinta zai sha barbaɗa da surutun ba a tambayeta ba amma bata da juriya kamar ki that's why" ta lumshe idanu ta ce "Thank you Abba, ka gama yi mini komai I love you" Ya yi mata rumfa sosai ya ce "Ni ne da godiya, kin bani Mamana, Kin bani Khadijah, kin bani Mother Maryama (Huda) da Abba Hakimi, ga auta Ibrahimul-khalil Abraham, kin zame mini komai kin mamaye mini gida da zuri'a masu Albarka, *IDAN BA KE* that's means babu YAA SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU" ya rufe idanu ta ce "Allahamdulillah, Allah na gode daka bani miji kamar Yaa Sheikh i love You Habibi ƙalbi" Idanun Yaa Sheikh ya yi jajir bakinsa ya shiga rawa ya faɗa buga kan shi, Halisa ta tsaya kallon ikon Allah cikin sarƙewar harshe da wata In-ina ya ce "I.... I... I...." Wasu irin hawaye Masu zafi suka sakko daga cikin idanunsa yana matseta kamar zai rabata gida biyu cikin In-ina ya ce "I.... I.... Lov...love... I love You" dam! Zuciyarta ta bada sauti sbd tasirin kalmar tunda suke sai yau ya ce mata I love you, ya yi murmushi itama tayi murmushi ta gama fahimtar a yanzu ba Yaa Sheikh ɗinta bane kawai ya juye zuwa MUTUM DA ALJAN tana ganin yadda jikinsa ke murɗewa kamar wani maciji ya ƙara ɗaga murya ya ce "I love you Zawja" yana faɗa yana rungumeta sosai ta ce "Allahamdulillah" tana faɗa ya ce "I love you Haliyserh Sheikh Aliyu haydar Aliyu I love ƴar fillo,I love you Danejo I so much love you princess Queen of my heart IDAN BA KE ba Sheikh Aliyu haydar Aliyu Allahamdulillah" "Abraham laɓe ka kewa su Abbi" ya kame fuska hannunsa riƙe da iphone system zai kaiwa Yaa Sheikh ya duba masa wani abu shi ne ya kai bakin ƙofa yaji ana I love you. Ya juyawa har ya je bakin ƙofa ya ce "Yaa Hakimi can i ask you?" Hakimi ya ce "Sure, go ahead I'm listening" Abraham ya ce "A cikin mata wace tafi iya soyayya irin romantic love ɗin nan" Hakimi ya ce "Wannan sai dai Malamai ai sune suka san kan soyayya" Abraham ya ce "Ohh! I'll catch you MALAMA malama zan aura" Hakimi ya juya yana cewa "Sannu *MIJIN MALAMA* (Upcoming book). _Allahamdulillah. Nan na kawo ƙarshen littafin IDAN BA KE Book 1&2 Ya Allah ka sanya littafin ya zama hujja gareni ba hujja akai na ba, Ya ka datar damu duniya da lahira Ubangiji kaga manufarmu ka sanya mu gane gasky ka kuma shiryemu kada ka barmu da iyawarmu, dabararmu wayonmu ka sanya mu amsa tambayoyin da duk za'ayi mana😭👏🏻_ MEENA VIP GROUP HAUSA NOVEL DOCUMENT for more information contact on +234 7014979567 WhatsApp ONLY