Ajininsa yake 3-01
Posted by ANaM Dorayi on 06:55 PM, 19-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.
.Duba da yawan makaranta Hausa yasanyamu
fadada hanyar sadarwar mu daga whatsapp zuwa
bude blog, daga bisani sai nafahimci kamar da
yawanmu vamufiyason shiga blog ba, Bansan
dalilin hakanba, sakamakon yawan korafe korafe
dake riskata yasanyani yin nazari wace hanyace
ke da sauki bayan wannan, karshe dai natino
face book, sakamakon haka muka yanke
shawarar bude page a facebook din duk domin
fadada hanyoyin sadarwarmu wadda ba dan
komai mukeva sai dan jin dadinku,insha Allahu
Labarinmu nagaba zai kasance ta hanyoyi Uku,
:-Whatssap. 08139787515
:-Blog Anamdorayi.mywapblog.com
Saikuma ...
:-Face book.. https://mbasic.facebook.com/
HAUSA-Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%
2CPAGE_ID10%2C7370123473
Hakan amma bazai tabbatuba sai da hadin
kanku..
Dan haka inna bukatar 20,Like a group din kafin
mu sanya littafi na gaba..
Naku har kullum
ANaM Dorayi
--------------------------------------------------------;------------------
Ya koma rigingine ya kwanta, ya rasa dalilin da
yasa Nusaiba ta tinkare shi da wadannan
maganganun banzan. So take ta hada shi da
iyayensa ko me? Idan kuma ta gaji ne, ai bai yi
mata tirke ba. Iyakar ta Alh. Basheer ya ce ya
aje masa komai na sa, sai me? Daran nan
Nusaiba bata yi barci ba, gaban Ubangiji ta
gurfana kamar yadda ta saba kai kukanta. Allah
ya za6a mata alkhairi. Haka kuma tayi kukan
bakin ciki yau ita da mijin auranta take cacar
baki. Lallai rayuwa shirin Allah ce, amma ko a
mafarki bata ta6a tunanin hakan ba a rayuwar
ta. A kodayaushe zuciyar ta na shirya mata
kyakkyawar rayuwa da jin dadi tare da
gamsashshiyar soyayya ga duk mijin da ta aura.
A kunnan ta aka yi kiran sallar farko, ciwon kai
ya ce ga shi nan irin wanda bata ta6a jin irin sa
ba. Da kyar ta sallaci asuba. Ta jawo filo ta jefa
bisa sallayar ta kwanta. Dora kan ta, ke da wuya
ta ji fitar Naseer kamar da gudu. Ta tashi zaune
tana sauraron buga kofar falon sasn su Abba.
Ta mike ta fito kofar falonsu a gwame. Tayi waje
can sasan su Umma. Naseer ta ji yana
fadin,"Zarah ba lfy, yanzu Inna tayo waya inje
maza-maza. Kafun su Abba su gama salati, ya
fice. Ta koma daki da saurin ta, ta dauko hijab
ta suro jakar hannu.don ta tabbata haka Naseer
ya fita babu ko sisi ajikinsa. Ta fito, ta iske su
Umma ma tsaye suke a waje, ya tafi ya bar su.
Makullin motar ta na cikin jakar ta bude ta
dauko,"Umma zo mu bi shi a wannan motar."
Ta ce,"Ba ni so ki na yawon nan Nusaiba, cikin
ki ya tsufa." Abba ya ce,"Gari bai k'arasa waye
ba ma, kun tafi ku 2 mata a mota? Gara ku bari
gari ya waye sosai." Ta ce,"Ba komai Abba, Allah
zai tsare. Umma zo mu je yanzun garin zai
waye." Umma ta shiga suka rankaya. Malam
Balarabe na tayi masu addu'a. Hajaran majaran!
Suka iske Naseer da Inna, domin ance jaririryar
ta mutu a ciki, sbd haka Likitar za ta yi iya
kokarinta su fito da ita, idan kuma abin ya
faskara, aiki za su yi mata. Nusaiba ta nemi
waje ta zauna jinin ta ya k'ara hawa, kan ta
kamar ya tsage, sbd tsabar ciwo. Bayan kusan
minti 40. Likitan ta fito ta ce, maza-maza su je
su biya kudin aiki. Ta mika wa Naseer takarda,
hannunsa na rawa ya rike ya duba. Dubu 35 zai
biya. Umma ta ce,"Ka fito da kudi ko ko? Ya
girgiza kai,"Sai na koma gida, kuma ina jin kudin
da ke gidan dubu 10 ne kawai, banki kuma ba
su fito ba, ya za'ayi kenan? Ya tambaya
hankalin sa tashe. Kafin Umma ta ce wani abu
Nusaiba ta miko rafar kudi, ga wasu yi maza
kaje ka biya. Ya bi tada kallo kafin yasa hannu
ya kar6i kudi ya kwasa da gudu ya nufi wajen
biya.
(Allah sarki baiwar Allah, Allah yahadamu da
mata masu tausayinmu da kaunarmu)
Duba da yawan makaranta Hausa yasanyamu
fadada hanyar sadarwar mu daga whatsapp
zuwa bude blog, daga bisani sai nafahimci
kamar da yawanmu vamufiyason shiga blog ba,
Bansan dalilin hakanba, sakamakon yawan
korafe korafe dake riskata yasanyani yin nazari
wace hanyace ke da sauki bayan wannan,
karshe dai natino face book, sakamakon haka
muka yanke shawarar bude page a facebook din
duk domin fadada hanyoyin sadarwarmu wadda
ba dan komai mukeva sai dan jin dadinku,insha
Allahu Labarinmu nagaba zai kasance ta hanyoyi
Uku,
:-Whatssap. 08139787515
:-Blog Anamdorayi.mywapblog.com
Saikuma ...
:-Face book.. https://mbasic.facebook.com/
HAUSA-Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%
2CPAGE_ID10%2C7370123473
Hakan amma bazai tabbatuba sai da hadin
kanku..
Dan haka inna bukatar 20,Like a group din kafin
mu sanya littafi na gaba..
Naku har kullum
ANaM Dorayi
Nusaiba fa duk ta rude, ta k'ara rikicewa
musamman yadda ta ga Nosis na shiga suna
fita. Likitoci 2 ke kan ta, suna ta k'ara kokarin
su, domin ba sa son ayi mata aikin. Allah da
ikonsa kuwa Likitan da aka kira, yayi nasarar
ciro matacciyar jaririyar, sai dai Zarah nan take
numfashin ta ya dauke. Ba ta ba dalilinta,
komai ya daina aiki a jikinta. Suka yi caa kanta,
latsa nan, gwada can. Amma ba alamar motsi.
Likita ya tura a dauko (Oxygen). Su Nusaiba na
tsaye. Nos din ta fito da gudu, jim kadan ta
dawo da shi da shige dakin. Zuciyar Nusaiba ta
soma bugawa, ta nufin dakin tana fadin,"Shi
kenan Antina! Su Umma suka rirriko ta, su ma
kukan suke yi. Inna ta ce,"Zo ki zauna Nusaiba,
kin ga ba ke kadai bace. Ki kwantar da
hankalinki, ki yi mata addu'a. Tana shiru.
Naseer na iso wajen, bai yarda da yanayin daya
gansu ba. Ga Nusaiba na kuka tana ta fadin,"Shi
kenan Antina." Ya ce,"Menene Umma? "Ba
komai, ji ka ka gaya ma su ka biya kudin." Ya
tsura wa Nusaiba ido, duk ta fita hayyacinta, ya
ce,"Ki yi shiru mana." Ta ja hijabi ta rufe fuska,
sannan ya wuce, ta biyo bayan sa. Yana isowa
kofar. Likitin na fitowa. Ya mika masa takarda
da siri,"Doctor an biya kudin,"Ya ce,"O.K, ka rike
risit din za'a maida ma ku da kudin ku, an riga
an ciro Bebin. Ita ma uwar sai dai ku yi
hakuri.... Nusaiba ba ta gama jin bayayin ba, ta
yanke jiki ta fadi, nan take ta hau fizga. Gaba
daya suka yi caa kanta har da Likitan. Abin
kamar bugun jinnu, duk gabobinta sun sandare,
idanuwa sun kakkafe, baki kumfa. Likita ya ce, a
kai ta ofishin sa. Naseer ya dauke cak! Ya kai ta
ofishin, ya kwantar bisa dan gadon su.
Su Umma ne biye da shi kamar za su yi hauka
saboda tashin hankali. Shi kansa Naseer hawaye
ne ke sauka bisa kuncinsa. Likita ya miko masa
takarda,"Sa min hannu nan, dole a cire abinda
ke cikin ta, don tsira da rayukansu." Bai jira
Naseer ya gama sa hannun ba, ya fice da
saurinsa. Jim kadan wasu Nosis suka shigo da
gadon daukan maras lafiya, dukkan su da kayan
dakin tiyata a jikin su. Irin kayan suka sanya wa
Nusaiba, suka maida ta gadon da suka zo dashi,
suka gara ta dakin tiyata. A tsakar wurin Naseer
ya zube ya kame kan sa hannu 2, ya rasa
duniyar da yake." Me zan gani yau? Inna-lillahi-
wa"Inna-ilaihir-raji'un! Umma ce tayi karfin hali
ta kar6i waya hannu Inna, ta kira Malam
Balarabe,"Mallam ka yi maza ka zo, abubuwa
sun rinca6e, daga Zarah har Nusaiba ba mu san
halin da suke ciki ba. A zaton da mu ke yi ma
dai Zarah babu ita. Nusaiba kuwa yanzu suka
wuce tiyata da ita." Hankalin sa yayi
mummunan tashi, salati yake yana k'arawa, har
ya rufe gida, ya kama hanya. A mota ya kira
Alh. Basheer ya labarta masa halin da suka wayi
gari da shi. Subhanalillahi! Babu 6ata lkc suka
baro Kaduna. Malam Balarabe na isa. Shi
Malama Umar ya iso. Yadda suka same su
zazzaune haka su ma suka nemi wuri suka
zauna. Naseer na nan dunkule a kasa. Malam
Umar bai ko shaida shi ba, sai da ya jima a
wajen. Ya tashi ya matsa gun sa ya tsugunna ya
dago kan sa,"Naseer! Tashi daga k'asan nan, zo
nan ka zauna." Ya kamo shi ya taso da kyar,
suka zauna bisa kujera, yana rungume da
kafadar sa. M.Balarabe shi ma ya taso, ya
tsugunna gabn su ya ce,"Sun bada gawar ne?
Ya girgiza kai, hawaye suka kara kubce masa, ya
ce,"Sun ce ba mutuwa tayi ba, doguwar suma
ce, shine suka sa mata (Oxygen)Gaba dayan su
suka sauke numfashi, suka yi hamdala ga Allah,
tare da addu'ar Ubangiji ya ba su lafiya. Kamar
wucewar minti goma da zuwan su Abba. Likita
ya fito, duk suka mike suka nufi gun sa,"Yaya
Likita? Yayi dan murmushi,"An yi nasara,"Bebi,
na nan lafiya lau, shi da uwar sa. Za'a fito da su
nan bada dadewa ba. Kowa sai hamdala. Umma
da Inna suka rungume juna. Duk da haka
hankalin Naseer bai kwanta ba, so yake ya
gansu da idon sa, ya tabbatar da lafiya lau
suke. An ba su izinin ganin Zarah na minti 5r.
Haka suka yi tsaye gaban gadon suna mata
kallon tausayi. Inna ta fara barin dakin ta dawo
wajen ta zauna, tayi shiru hawaye na tsitaya,
babu abinda za ta iya yi, komai Allah yayi, dai-
dai ne. "Yan mintoci bayan fitowar su daga
wajen Zarah, aka kawo ma su Bebin da aka ciro
wa Nusaiba. Bebi ne katon gaske jajur da shi,
sannan babu abinda ya bambata shi da Ameer.
Illa girma daya fi shi. Kowa yasa masa albarka,
suka mika wa Babansa. Ya zura masa ido kamar
ya lashe shi so da kaunar Bebin suka kama
zuciyar sa. Kwalla suka cika idanun sa,"Allah ka
raya mi shi." Ya fadi a ransa..
A lokaci guda daran jiya ya fado masa, nan da
nan ya mike ya ba Umma Bebi, ya fice da sauri
ya sami wata kwana, ya hade kai da bango.
Babu abinda ke yawo cikin ransa, sai
maganganun daya cacca6awa Nusaiba, a idonsa
yake ganin lokacin da ta miko masa rafar kudi,
duk a tunanin take ganin halin da ta shiga.
Wanda komai zai iya faruwa da ita. "Da mutuwa
tayi da shi kenan, ta tafi ta bar ni da hakkinta a
wuya na?" Ya fashe da kuka sosai, irin wanda
bai ta6a yinsa a rayuwar sa ba. Ji yayi an kamo
shi,"Malam Umar ne,"Haba Naseer, ka yi hkr
mana, ka roki Allah ya ba su lafiya. Wannan
koke-koken ai ba su da amfani. An san ka na
cikin tashin hankali, amma jurewa za ka yi, ka
zama namiji. Zo mu je, yanzu za mu tafi, don a
samu a bizne jaririyar wajen Zarah. Yi hkr d'an
gidan Inna." Ya goge masa fuska, ya riko
hannun sa suka dawo. Yarinyar na lullube cikin
zani, ya nuna wa Naseer ita, yayi jim, yana
kallon ta, sannan ta dauke kai. Ya matsa kusa
da Abba ya ce,"Ka zo da waya?" Ya ce,"Ga ta, ai
na riga na gaya wa su Alhj, suna tafe." Ya
ce,"To shi kenan, bari in kira Sageer." Ya kar6i
waya, ya matsa gefe,ya kira duk wanda yake
son kira, sannan ya maida wa Abba wayarsa,
suka dauki shatan tasi ta maida su gida. Suna
bada baya. Su Alh. Basheer na isowa. Abinka da
asibitin Shika, sai suka rasa ina za su dosa, don
haka ya kira wayar Naseer. Tana ta bugawa,
amma da yake tana gida, babu mai dauka. Ya
kira ta Abba, su kuma sun riga sun kusa gida,
saboda haka Malam Umar yabasu lambar Inna,
suka kira. Naseer ya fita ya nemo inda motar su
tayi fakin. Yana isa wajen. Ummi ta fara kwalla.
Yana neman tsugunnawa. Alhjn yayi sauri ya
kamo shi,"Sannu Naseer ya fargaba? Ya ce,"Mun
gode Allah." Ya ce,"Malam Balarabe ya ce ashe
doguwar suma Zara tayi ko? Ya amsa da kai? Ya
dan rungumo kafadar sa,"Ka yi hakuri kaji? Allah
zai ba su lafiya." Ya gyada kai, ya dubi Ummi
suka gaisa, sannan yayi masu jagora zuwa inda
suke, suna tafe yana maida masu yadda abin ya
faru. Bayan sun gaisa da su Umma. An jajanta
wa juna, sai Alh.Basheer ya nemi ganin Likita.
Abn ka ga mai kudi, nan da nan ya sami duk
abubuwan daya bukata watau daki na
musamman da likita shi ma na musamman. Kan
ka ce kwabo, an hada Zarah da Nusaiba waje
daya, an zuba masu komai na bukuta. Ummi na
rike da Bebi, yana to son a zuba masa abinci a
bakin sa. Da yake akwai kayayyakin Zarah,
ruwan zafi kuma tana da zuma da dabino sbd
tana yawan cin dabino, sai Inna ta kawo, duk
Ummi ta ba shi, sannan ta dan kada zuma a
ruwan dumi, ta cika masa ciki, nan da nan ya
koma barci. Ganin hankali ya dan kwanta. Inna
ta ce Naseer ya koma gida yayi wanka, daga nan
ya kwaso wa Bevi kaya da ita Nusaiban. Yana
fitowa su Sageer na shigowa shi da Fa'iza, dole
ya sake komawa, suka gaida su Umma. Ya kawo
masu Bebi suka gan shi. Wucewar 'yan mintoci
15 ya karbi mukullin motar Nusaiba, tunda ga
Sageer zai tuka a maida ta gida. Sun yi fakin
kofar gida, suka yi sallama suka tafi, ba tare da
sun tsaya wani surutu ba, domin Naseer baya
ma son yin magana.
Yana shiga gida, ya tu6e kayan jikin sa, ya zaro
sauran kudin da suka rage cikin rafar da
Nusaiba ta ba shi. Ya zauna bakin gado ya zura
masu ido, jim kadan ya sauke numfashi, ya aje
su bisa filo. Ya wuce bayi ya sakarwa kan sa
ruwa. Bayan yayi wanka, ya kimtsa ya kawo
wayoyinsa da kudade ya zuba aljihu. Ya fito ya
nufi dakin Nusaiba.
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
Gaban hoton ta ya tsaya ya k'are mata kalo ba
tare da ya san me zuciyar sa ke sakawa ba.
Wadirof ya bude, ya d'ebo riga da Zani kala 5r.
Yayi tsaye yana tunanin a ina zai ga kayan Bebi,
tunda bai ta6a siyowa ya ce mata ga shi ba?
Abinda ya yanke shawara shine ya shiga kanti,
ya siyo. Wata zuciya kuma ta ce masa "Kai dai
dudduba." Yana gama tunanin sa, ya nufi
akwatuna ya fara budewa, abn ya ba shi
mamaki, domin setin nan kaf kayan Bebi ne ciki
a mak'are. Yayi shiru duk al'ajabi ya ishe shi, ya
nemo jaka ya debi kaya iya dibar sa, kayan
shafe-shafe, su pampas da setin bahon wanka,
wanda komai na bukatar wankan Bebi. Akwai
shi a ciki. Ya loda kaya a but, ya sallami Abba
ya koma asibiti. Yana shigowa da kaya niki-niki,
ya iske Zarah ta farfado, sai faman kuka take yi,
sbd jin abin daya faru da Nusaiba. Su Umma na
ta bata hkr. Ganin Naseer ya shigo, dukkan su
suka fita waje.Ya matsa wajen ta ya zauna gefen
gadon, da sauri ta fado masa ta sake 6arkewa
da kuka. Idanuwan sa suka cike da kwalla, ya
kasa cewa uffan tsawon lokaci. Sannan ya
dagota, ya share mata hawaye ya ce,"Ya isa
haka. Ya jikin? "Yayi sauki. Ashe abinda ya faru
kenan? Ya ce,"To yaya za'ayi? Allah ya ba ku
lafiya." Kwalla suka sake zubo mata ta
ce,"Amin.", Na ga Bebin mu kamar Ameer ne
aka dawo mana da shi." Yayi dan murmushi,"Shi
ne ma, domin shi ma sunan za'a maida masa."
Ta ce,"Yayi dai-dai." Suka k'ura wa Nusaiba ido,
a lkc guda kuma suka kalli juna ya ce,"Allah
yasaa ita ma ta farfado. Lafiya, kamar yadda ki
ka tashi." Ta ce,"Amin yayana." Ta wuce da
kanta kirjin sa, tayi ajiyar zuciya, ya sumbaci
tsakar kanta, sannan ya gaya mata su Sageer
sun zo shi da Fa'iza. Suna gaishe su." Ta dago a
hankali ya taimaka mata ta kwanta tana
fadin,"Muna amsawa." Ta bi shi d kallo, ta ci
gaba da cewa,"Na san ba ka ci komai ba
yayana, ka hada Tea mana ka sha." Ya kada
kai,"Ban jin yunwa Zarah." Ta ce,"Ai kai ba za ka
ji ya ba, amma tana nan tana cin ka." Yayi dan
murmushi ya ja ha6arta, ya ce,"Hankalina bai
gama kwanciya bane Zarah, sai na ga
farfadowar yarinyar nan." Ta dan lumshe ido, ta
bude wani dadi ta ji ya ratsa, ta miko yatsun ta,
ya rike ta.. Ta ce,"Insha Allahu lafiya lau za ta
farfado. Kar ka ka zauna da yunwa yayanmu, za
ta iya yi ma illa." Ya sumbaci, yatsun ya ce,"Shi
kenan, zan sha yanzu." Umma tayi sallama, ya
mike da sauri yana amsawa, ita ma maganar
abincin tayi masa, sannan ta bude jakar kayan
daya kawo, ta debo wa Yaro kaya, ta dauke shi
suka fice. Anan ya hada Tea ya dawo bisa kujera
gaban Zarah yana sha, suna hirar Nusaiba.
Bayan sallar la'asar. Alh. Basheer ya ce shi zai
koma. Ummi ma ta ce me za ta tsaya yi, tunda
ga su Umma ga Inna? Haka suka wuce, duk ba
su ga farfadowar Nusaiba ba, idan Allah ya kai
rai gobe, za su dawo. Bebi kuwa na lkie da
Zarah. Naseer ya tasa su yana ta fama kallon
abin sa, son sa na k'ara kwarara jikin jinin sa da
bargonsa suna kashe jijiyo har bisa fatar sa.
Karfe 9n dare ya baro Shika. Zarah tare da Bebi
ta kwana, ko ya motsa, ita ake mika wa ruwan
dimi ta ba shi, duk da jikin ta babu kwari sosai.
Shi kuwa Naseer kasa runtsawa yayi, saboda
tsabar tunanin abubuwan daya aikata wa
Nusaiba, wadanda a yau yake ganin suna so su
zame masa da na sani. Lokacin sallar asubahi ya
yi, ya tashi ya je yayi alwala, ya bada farali. Da
kansa ya shiga kicin, ya shirya duk abubuwan
da yake son tafiya da su asibiti. Yayi wanka, ya
kimtsa. Karfe 7 saura kwata, ya dauki hanyar
Shika. Karfe 8:30 Nusaiba ta farfado da surutai
tare da sambatun da babu wanda yake fahintar
me take fadi.Likita ya ce ba damuwa, za ta
wartsake nan bada dadewa ba. Suna fa jin dadi,
musamman Naseer da zuciyar sa ke cike da
zullumi. Ko su Alh.Basheer da suka zo, sun yi
farin ciki kwarai, anan suka iske su Malam
Balarabe da Malam Umar. Shi yake gaya masu
cewa Bebi sunan marigayi watau Iliyas ya ci.
Wasa-wasa Nusaiba ta kai har dare bata gane
kowa, sai sambatu. Likita dai sai kara basu
hakuri yake yi, yana jadadda ma su za ta
warware. Amma haka suka kwana da ita, ba
barci. Surutai babu ma'ana. Abinda yafi basu
tsoro, shine yadda harshen ta ya karye, tana
magana kamar wacce ta sami matsalar
shanyewar gefen jiki. Da safe kowa ya zo da
kuzarin sa, turus! Yake yi, saboda abin akwai
ban tausayi, ballatanta da idanuwan ta suka
bud'e waras! Tana kallon kowa, amma bata
sanin ko waye. Murna fa ta koma wa kowa ciki,
domin al'amarin Nusaiba k'ara gaba yake yi,
abin tamkar tabin hankali. Kwana 3 kenan. Da
sassafe ta tashi da wani kuka mai tsuma zuciya
da ban tausayi, babu abinda take kira, sai
"Antina! Alhali ga Antin ta tana tallafe da ita. Ita
ma kukan take yi, tana fadin,"Ga ni fa nan
amarya, ba mutuwa na yi ba."Ta tsura mata ido
zuru! Shi kan sa kallon mai ban tsoro ne, sbd
idanuwan a juye suke, duk sun firfito waje.
Zarah ta sake fadin,"Kin ganni? Ni ce amarya,
ban mutu ba. Ki daina cewa za ki mike da gudu,
kin ga (Operation) aka yi miki. Duba ki gani, kin
ga Bebin mu? Ga Umma ga Inna. Yanzu yayan
mu ma suna tafe. Ki na son ganin su ko? Ta
girgiza kai, ta ce da karfi,"Antina ta mutu na ce!
Wayyo Abba na, sun kashe Antina! Da gudu
Zarah ta bar dakin, ta zube barandar waje, ta
fasa kuka. Kwatsam! Sai ga su Ummi, tun daga
nan suna jin ihun ta, tana kwala wa Abbanta
kira. Ummi bata son lkcn da ta watsar da
kayayyakin hannun ta ba, suka fada dakin. Su
Umma na rirrike da ita. Alh.Basheer yayi azama
ya rungumota,"Ga ni Nusaiba, ga ni, ki yi shiru."
Amma kara fadi take,"Abba na ka zo sun kashe
min Antina! Hankalin sa yayi mummunan tashi,
ya dubi su Umma."Ina Doctor ne wai? Ta
ce,"Sun zo har su 4. Nosis sun zuba magunguna
cikin karin ruwar nan, sun mata allurai, har
yanzu barci ya ki zuwa." Alh.Basheer yayi waje,
ya nufi ofishin likitan daya dauka na
musamman, cikin zafinsa ya shiga, a tsaye ya
fara fadin. "Wai me ke faruwa ne Doctor? Ban
gane condition din yarinya ta ba! Shi ma ya
mike cikin sanyin murya ya ce,"Cool down Alhj,
zauna." "No I can't sit Doctor! Kullum yarinya sai
k'ara rikicewa take! Why? Wai ba anan ku ka yi
mata tiyata ba ne? Ya ce,"Alhj babu wata
maganar an ta6o mata wata jijiya. Infact, aikin
ta bai shafi ko'ina a jikinta ba, sai inda Bebi
yake. Ka zauna mu yi magana, Please! Da kyar
ya zauna, shi ma Lkita ya zauna." Dama kai na
ke jiran zuwan ka mu yi magana. Nusaiba ta
fada cikin matsananciyar damuwa, wacce har ta
sanya ta fizge-fizge, alhalin tana da ciki. Babbar
matsalar ce ga mai ciki idan ta sami kan ta a irin
wannan yanayin, domin ya kan kai a rasa su
duka. Shine za ka ga mutan kauye da suka
jahilci abin sai su ce bugun jinin ne, maimakon a
hanzarta kawo ta asibiti, don daukan matakin
gaggawa, sai a shiga hayaki da shafe-shafen
turaren aljanu. Daga karshe ka ga an rasa uwa
da Da. Abinda na ke so ka gane anan, damuwa
babu abinda bata haifarwa, amma ina son ku
natsu, za mu bicike da kyau, mu gano aininhin
abinda ke damunta. A halin yanzun muna
Expecting comma ta shiga, abinda muke magana
kenan da sauran Doctor." Alhj fa bai
yarda."Wannan ba comma bace, ta6in hankali
ne, sbd haka idan ku yi bincike a kwakwalwarta,
ko nawa ne zan kashe! Ya ce,"Wannan duk ba
matsala, yanzu zan rubutu gwaje-gwaje da
hotunan da za'ayi. Idan an rubuta kudaden, sai
aje a biya." Rubuta min, in je a biya kudin."
Yana zaune Likita ya rubuta duk binciken da
za'ayo. Tare suka fito, ya hada shida Yaron da
zai raka shi ofisoshin da za su rubuta kudaden.
Al'amarin Nusaiba kuwa ta rikita kowa, kuka
kawai suke yi. Shi kan sa Bebin kukan yake
tsalawa, yana jin yunwa, amma ta hana su yi
'yan dabara a lika shi, ya sha nono. Naseer ya
doso wajen, tun daga Nesa ya tsinkari muryar
ta. Da gudun sa ya karaso, yana tambayar
Zarah! "Me ya faru?, Murya na rawa ta
ce,"Nusaiba ta rikice Kai tsaye ya shiga dakin, ya
zube jakar da ke hannunsa, ya nufi gunta yana
fadin,"Ya haka Umma? Duk suka dare, suka ba
shi wuri, tana kyallo ido ta gan shi, ta zaburo
tana mika masa hannu, "Abba na! Abba na, ina
ta nemanka za su kashe ni? Bai san lkcn daya
rungumota ba,"Menene? Iye? Ba ki san akwai
ciwo a jikin ki ba? Allah da ikon sa, shiru tayi,
tana ajiyar zuciya,"Kai na ke ta kira Abba na, ka
ki zuwa, kai ma ba ka so na ne? Idanuwansa
suka cika da kwalla. Kowa yayi waje yana share
hawaye. Ya jima kafin ya ce,"Ai gani na zo, me
aka yi? Wa ya sanya min ke kuka? Ta zura masa
ido ta ce,"Antina suka kashe min, shine suka zo
ni ma suka danne ni, za su kashe." An ce miki
Antinki bata mutu ba, tsaya ki gan ta. Zarah! Ya
kira ta. Ta shigo, ya jawo hannayensu ya
hada,"Kin gan ta? Antinki ce. Ta fizge hannunta,
ta saka ihu,"Ba ita bace! Allah ba ita
bace,"Antina ta mutu
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
Ya rufe bakinta ya ce,"Shi kenan na ce, shi
kenan ba ita bace." Zarah ta yi sauri ta fice.
Sannan tayi shiru. Ya dube ta ya ce,"Abinda ki
ke yi, ba shi da kyau, ki na jin Bebin mu na
kuka, kin ki bashi nono, me ki ke nufi? Ta
ce,"Abba na ina naga Bebi kuma? Ga shi can a
waje, yana kuka."Ta ta6e baki ta ce,"Ban haihu
ba, Antina ce ta mutu. Ya kamo ha6arta ya
ce,"Dube ni, ki saurara da kyau, za ki ji kukan
Bebi. A kawo shi ya sha? Tayi shiru, tana
kallonsa. Ya sake kiran Zarah, ya ce ta kawo
Bebi,. Ta zo da shi a shawul, ya kar6e shi, ta
tsaya tana kallonta! Ya ce,"Yauwa, dube shi ki
gani." Kyakkyawan kallo tai masa! Ya ce,"Yauwa,
dube shi ki gani, kyakkyawa da shi." Ta leko ta
dube shi,"Abba na wannan k'aton Yaron ai ya
girme ni." Ya ce,"Ban son shirme, ba shi ki gani,
idan bai sha ba, ki min duka." Ya dora mata shi
bisa jikinta, ta 6allo wa Zarah harara, sannan ta
dubi Naseer,"Abba na ka ce wa matar nan ta
fita, ban son ganin ta. Munafuka kawai, duk
sune suka kashe Antina." Hawaye suka kawo wa
Zarah, ta juya ta fita. Ya ce,"To ta fita, ba shi ya
sha. Ta ciro ta ba shi, ya kama sai tsotsa yake
yi, bawan Allah ya sha kuka, shi yasa bai jima
ba, barci ya kwashe shi. Naseeer yayi zuru,
yana kallon su, tsabar tausayinta yake ji, kamar
ya ce wayyo Allah. Ta ce,"Abba na ka daina
kallo na mana." Ya ce, "Ah! Ai kowa dole in kalle
ki, tunda ina son ki, kin zama abar kallona. Ko
kuwa? Ta sadda kai, tana dan murmushi. Ya dan
k'ara matso ta, ya ce,"Kin ga har yayi barci, to
ke ma ya kamata ki kwanta ki yi barcin, ki huta
ko?Ta yi hamma mai tsawo, yana rufe da
bakinta, kafin ta ce,
"Barci?"
Kin ga ni ban son shirmen nan na ce.
Kawo Bebin a kwantar da shi, ke ma ki kwanta
ki gani."
Ta ce,"Bar shi kawai, ya yi min dadin rikewa."
Hirar su kawai suke yi, abin ya ba kowa mmk,
har Alh.Basheer ya gama zirga-zirgar sa, ya
dawo. Ummi ce ta mayar masa da yadda aka yi,
ta yi shiru ta natsu.
Ya shigo dakin a hankali Naseer ya mike yana
masa sannu da zuwa, da ta fasa wata irin k'ara,
gaba dayan su gigicewa suka yi.
Naseer bai san lkcn daya koma gun ta
ba,"Menene? Idanuwanta rufe tana fadin,"Ban
son ganin sa! Ban son ganinsa!! Munafiki
ne.............
Ya rufe bakin ta, yayin da Alh.Basheer yayi waje
da sauri. Naseer ya ce,"Ban son abinda ki ke yi
Nusaiba, gaskiya ni ma zan tafi." Ta ce,"Na
daina Abba." Ta ci gaba da surutu k'asa-
k'asa,"Munafikin banza, munafikin wofi, ya wani
shigo wa mutane ko kunya." Yayi shiru, ya
kyaleta, kwalla suka zubo masa, ya share.
Wannan al'amari da me yayi kama? Kuma fa
duk shine sila ko?
Ya tambayi kan sa. Wasu hawayen sharshar!
Suka fito, ya sake gogewa. Alhj kuwa yana tare
da su Ummi, shi ma sai da ya share kwalla,
sannan ya mayar da yadda suka yi da Likita,
kuma nan ba jimawa, za so zo su tafi da ita
dakin hoto.
Jama'a sun sha Zagi da tsinuwa lkcn da aka zo
daukan ta, har da Naseer din da yake fada aji,
ya zama munafiki, tunda yana gani zai kyale a
tafi a kashe ta.
Dole Likita yasa aka kawo masa wata allura, da
kan sa ya zurkud'a mata.
Take nan ta wuce luuuu....!!!
Ba rai, ba dalilinsa.
Sannan da masu daukan ta suka gara ta wajen
hoto.Har aka dawo da ita, bata sani ba, nan
suka bar ta tana ta barci. Hankalin kam ba a
kwance yake ba. 'Yan dubiya na ta zuwa gaishe
ta, amma tana barci, da yawa daga cikin su
daga Kaduna suke zuwa. Haka Antin Jordan
kodayaushe sai ta bugo ta tambayi jikinta. Bizar
ta kawai take jira a gama, ta kamo hanya.
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Sakamakon duk gwaje-gwajen da aka yi mata
suka fito. Likita ya kira Alhj ofishinsa, shi kuma
ya kira Naseer, domin mijinta ne, hakkinsa ne
ya san halin da matar sa ke ciki. Kowanne ya ja
kujera ya zauna gaban Likita.
Shi kuma ya firfito da sakamako, ya ci gaba da
bayani."A gaba daya binciken da mu ka yi, babu
wata matsala a tattare da ita. Kwakwalwarta
lafiya lau, zuciya ma haka, k'oda lafiya lau, haka
jirin ta lafiya yake.
Saboda haka abin nan dana fara gaya maka
Alhj, shi din dai za mu ci gaba da kula da ita
akan shi."
Alhj ya ce,"Yanzu ka na nufin tsabar damuwa ce
ta jefa ta a wannan yanayin? Ya ce,"Kar ka yi
mamaki, damuwa tana sanya hawan jini, kuma
babu ga mai juna biyu.
Saboda haka za mu ci gaba da bata taimakon
daya dace, sannan daga wajen ku a matsayin ku
na iyaye da mijin ta, rarrashi ne kawai. A ring'a
lalla6ata, a kodayaushe, hanklinta ya zamana a
kwance yake tare da samun isashshen barci.
Insha Allah za ta warware, sai kun yi
mamaki."Alhj ya munfusa, ya dubi Naseer,"Ka ji
ko? Wannan aikin ka ne, ko dama kai kadai take
son gani, mu duk mun zama munafukai. Don
Allah ka yi hakuri da ita, sannan a rink'a had'a
mata da addu'a.
Idanuwansa cike da hawaye ya amsa,"Ya zama
dole Abba, Allah ya taimake mu."
Duk suka amsa da Amin."
Tun lkcn aka bar wa Naseer ragamar komai
ahanununsa, kowa ya koma gida, sai dai su zo
akai-akai su duba ta, shi ma ta, taga, idan har
idan ta 2, idan kuwa har ka ga wanin Naseer a
kusa da ita, tabbaci hakika barci take yi.
Zarah ma an sallame ta, ta koma gida, amma
kodayaushe zuciyar na asibitin, shi yasa bata iya
daurewa kullum ne sai ta zo, koda za ta wuni a
waje tana lek'en taga tare da renon Ameer.
Haka Likitocin ta ke iyakar kokarin su ba dare,
ba rana akan ta.
Magana ce ta kudi. Alh.Basheer kuwa ya saki
komai ya dace ayi mata, komai tsadar magani.
Shi kuwa d'an gogon, bai gajiya da yi mata
hidima, shi ne cin ta, shine shan ta. Kullum
yana like da ita, suna hiar shirme, domin kuwa
shirme ce, yanzun nan za'ayi magana dai-dai,
lkc guda sai ta ya6o shirmenta. Babu abinda ya
dame ta.Idan dare yayi kuwa tana barci, zama
yake bisa kujera ya zura mata ido, yana yi mata
addu'o'i. Idan ya tuna da bayanin Likita kuwa,
hawaye yake zubdawa sosai, domin ya tabbata
shi ya tara maya damuwar sa ta jefa ta wannan
mawuyacin halin.A haka so da k'aunar Nusaiba
suka zauna kwarai da gaske cikin zuciyarsa, har
yana mamakin kan sa."
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~Sabon
shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
Kwanan ta 11 yau, ya gama kintsa Ameer, ya
kwantar da shi cikin (Net) din sa. Ya dube ta,
tana ta lissafin zucci, ya ce,"Za ki sha Tin ne
kafin ki kwanta? Ta ce,"Had'o Abba." Ya had'o
mata dai-dai wanda ta saba sha. Ya zo da shi
bakin gadon, ya zauna. Ya debo a cokali ya
ce,"Ungo, sha 'yar gidan Abbanta." Ta dube shi,
tayi murmushi," Miss you."Dariya ta ba shi, ya
ce"Za ki fara ko? Ai ni fushi na ke da ke."Me na
yi Abba na? Ya mika mata, ta kur6e ya
ce,"Batan kin kori kowa, mutane na son ganin
ki, amma kin hana, me yasa?
Hmm... Abba na kullum ina raba ka, amma ba
ka ji.
Me za'ayi da munafukai? Ya ce,"Na fa hana ki
ce musu munafukai. Haka dazu ki ka cewa
Umma, sa'ar ki ce?
Ta dan 6ata rai, tayi shiru, ya miko mata Tea ta
ki kar6a. Ya aje cokali ya dago ha6arta."Fushi ki
ka yi? Da ni ki ke fushi, shi kenan bari in zo in
tafi." Ta ce,"Yanzu saboda Allah Abba duk
wanda ya nuna baya so na, ba munafiki bane?
Yanzu dubi yadda ka ke k'aunar Naseer, amma
k'iri-k'iri ya nuna min, baya so na, yayi ta
wulakanta ni. Saboda Allah Abba me zan kira shi
ba munafiki ba, tunda ya munafunce ka."
Tunda ta soma mgn, gabn sa ya yanke ya fad'i,
yayi sukuiti duk jikin sa ya mutu, ya rasa me zai
ce? Ta zura masa ido, ta ci ga,"Abba ai dai ka
san na maka biyayya da ka ce min shi ka za6a
min, ban maka musu ba ko, Amma ka san Allah,
shi baya so na, wannan cikin na jiki na ma, ya
ce da shi zan koma gidanmu, baya so. Na ce ai
ban je da d'a gidan sa ba, ko fan fadi gaskiya
ba?
Hankalin Naseer fa ya yi mummunan tashi, ya
tabbata wata rana a surutanta za ta iya fadi a
gaban kowa. Idanunwan suka kad'a, ya aje Tea
bisa dirowa ya rufe.Ya kamo kafadunta 2, suka
yi wa juna zuru kafin ya ce,"Wannan maganar
bata dace ki na fadar ta ba 'yar gidan Abbanta.
Naseer masoyin ki ne, ni ya gaya min yana son
ki kwarai da gaske."
Ta girgiza kai,"Na rantse da girman Allah, karya
yake maka Abba. Naseer munafiki ne, ina gaya
maka maganar nan, ka yarda da ni Abba." Ya
sake ta ya kama kai.
Ta bi shi da kallo ta ce,"Mamaki ma ka ke yi?
Kai har yanzu ba ka san mutane ba, ka na dai
kallo aka kashe Antina, me za'ayi?
Yayi hucin zafi ya ce,"Duk na ji, amma kin san
abinda na ke son ki da shi ?
Ki kyale maganar nan, kar ki gaya wa kowa, ni
zan yi maganin abin. Kin yarda?
"ka dai gaya masa, idan na haihu zan aje Yaron,
shi zai maida shi cikin lemon
gwangw........................
Ya like bakinta,"Nusaiba na ce ki bar maganar
nan, zan fa tafi abi na." Ta ce,"Yi hakuri." To kin
yarda ba za ki gaya wa kowa ba? Na yarda,
amma ka san Allah, ka yi hankali da wad'annan
mahaukatan da suke zuwa 6arayi ne."
Yayi shiru yana kallonta, duk ta dagula masa
lissafi." Ba ni Tin mana." Ya dauko ya ci gaba da
bata, sai zuba masa surutu take, shi kuwa bakin
sa ya mutu har ta yi barci.
Yayi tagumi bisa kujera, ya rasa abinda ke masa
dadi.Ta dai ce ta yarda ne kawai, ba za ta sake
fadi ba, amma abin maras hankali, ai ba'a sirri
da shi. Dan saukin ta ma, bata kula kowa sai
shi. Daran nan bai runtsa ba saboda tunani.
Safiyar yau kuma daga ya ce, bude baki ayi
burosh, shi ke nan ta fasa kuka. Yayi rarrashin
dunuya, ta k'i yin shiru, ta k'i kuma mgn, a
haka ta shafe sama da mintu 30 ita da kan ta ta
yi shiru. Ta gyara kwanciya, ya sanya mata ido,
tana ta ajiyar zuciya, har barci ya sace ta.
A lokacin shi kuma ya fara na shi hawayen da
kyar ya iya tsaida su, saboda tsabar tausayinta.
Ko me yasa ta kuka?
Oho!
Ya tambayi kan sa, ya ba kan sa amsa.
Idanuwan sa suka kara ja, kamar garwashin
wuta, dama ga rashin barcin da bai yi ba jiya.
Yana nan zaune zuru, ya ji motsin Ameer, shi
ma ya farka. Ya tashi ya zuba masa ruwan dimi
a fida ya zuba glucose ya karkada, sannan ya
dauko shi suka fito waje, ya zauna a kujera yana
ba shi har ya shanye. Idon sa 2, amma baya
kuka, yana ta 'yan wasannin sa. Naseer na taya
shi.
Muryar Alhj kawai ya ji yana masa sallama, ya
dago da sauri yana amsawa. Tare suke da Ummi
da Antin Jordan. Ya mike yana masu sannu da
zuwa. AntIn Jordan ta kar6i Bebi tana
fadin,"Sannu Naseer, don kai ne abin gaisarwa.
Yaro duk ya rame." Yana murmushi ya
tsugunna, ya gaishe su.Alhj ya ce,"Mutuniyar
barci ta ke yi ne? Ya ce,"Eh. Ummi ta ce,"Yauwa
mun yi sa'a, shigo Fatima ki gan ta."Suka
dungoma cikin dakin, shiru suka yi suna kallon
ta kawai, don kar su yi surutu ta farka. Sun
kusa minti 10 a tsaye, sannan suka fito dan
koridon. Naseer ya baza darduma, suka
zazzauna. Ya koma gefe ya zauna, suka ci gaba
da tambayar sa yanayin jikin na ta?
Ya ce,"Da sauki, an gode Allah, amma ko dazu
ta sha kuka, kuma ta k'i magana, abinda ma ya
sa ta barci ke nan."
Antin Jordan ta goge kwalla, ta dubi
Alhj,"Gaskiya yaya idan babu wani ci gaba a fita
da ita waje kawai." Ya ce,"Wannan maganar na
rai na, akwai iiya kwanakin da na dibarwa
Likitocin nan din ne, idan sungaza, zan dauke
ta."
Ta ce,"Wannan tashin hankali da yawa yake." Ya
ce,"Jarabci ne, mun gode Allah, muna rok'onsa
sauki.
Kai Naseer ka yi ta hakuri, ka ji?
Ya ce,"Hak'uri na mu ne duka Abba."
Haka suka kasance tare, jama'a na ta zuwa
kamar kullum. Koda ta farka. Naseer ne kawai
ya shiga, ya kai mata Bebi. Allah da ikon sa
babu kuka, sai hira kamar ma ba ita ta sharari
kukan dazu ba.
Yayi mata burosh, ya bata Tea, ta sha. Abin
yana ta 6a Antin Jordan mmk har ta
tambaya,"Yanzu ina shiga, sai ta fara Ihu?,
Ummi ta ce,"Ko za ki gwada ne?
"Don daukan alhaki? Na gan ta ta taga, ya isa.
Allah ya yaye mata."
Ta ce,"Amin. Kwananta 7 ta koma Jordan.
Ranar da ta tafi, ranar Kausar ta iso da mijinta.
Bata 6ata lokaci ba, ta fadawa dakin, kanta ta yi
ta rungume ta sa kuka. Wani ihun da Nusaiba ta
yi, dole ta sake ta, tana kallo, jiki na rawa. Ta
runtse ido, tana zagi tana fadin.
"Ban son ganin su. Ban son ganin su! Naseer ya
rirrike ta. Mijin Kausar ya fito da ita, me za ta yi
ba kuka ba. Haka ta fada jikin Ummi, tayi ma
isar ta. Naseer kuwa da kyar ya shawo kan
Nusaiba tayi shiru, ta daina zage-zage. Ba
karamin Huashi Kausar ta bata ba, sbd ta6a tan
da tayi.Yini guda masifar da ta rink'a yi
kenan,"Wata munafuka ta zo ta cakume ni za ta
kashe ni! Sai bayan la'asar tayi barci. Kausar ta
je gun ta, tayi mata addu'o'i. Hawaye na zuba.
Da yamma lilis suka koma Kaduna.
Haka Kausar ta tafi da bak'in ciki, a duk lkcn da
ta tuna hawaye, ke zubar mata.
(Allah sarki Nusaiba
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 3-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:53 PM, 20-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
To shi kenan ya wuce." Ya kamo ha6ar ta, yi
dariya,"Yi dariya 'yar gidan Abba!
Ta fado kirjinsa, tana murmushi.
Ya rungume ta, ya runtse ido, wasu kwalla suka
yi masa caa, fadi yake a ransa, "Son ki ya kama
ni Nusaiba, ki yafe min don Allah.". (Hhhhhhh,
Anzo gurin, ammafaaaa...uhm! Maji ma gani)
Bai ko san ta kici-kicin tashi ba, sai da ya ji tana
kira,"Abba!
Ka shake ni!
Ya hanzarta sakin ta, yana goge kwallah. Ta bi shi
da kallo,"Wash!
Ka wani matse ni Abba, ai sai in mutu."Ya tashi
ya bata wuri, ya shige bayi ba tare da ya ce
komai ba.
Jim kadan ya fito, ya wanke fuskarsa, kwance ya
same ta, ya matsa gabanta ya ce,"Hirar ta isa
haka, ki yi barci ki huta." Ta amsa da ka, ya
duk'o ya sumbace ta, ya ja mata mayafi. Ya ja
kujera ya zauna, ya sauke numfashi,"Allah ka ga
iya kokarin da na ke yi. Allah ka taimake ni
yarinyar nan ta sami lafiya.
Ta ce,"Ka kwanta mana Abba." Ya ce,"Zan
kwanta, ke dai yi barcin ki." Ta rufe ido.
Tare da gyara kwanciya.
Da asuba ya fito bayi da alwalar sa, ya shimfida
sallaya, yayi sallah. Ya jima yana addu'o'i kafin
ya jiyo motsin ta.
Ya waigo yana kallon ta, ta tashi zaune, tayi mika
tana salati. Ta kalli can, ta kalli nan, bai ce da ita
k'ala ba.
Ta k'ura wa Bebin da ke barci cikin (Net)
ido.
Ta dago kai ta dube shi, suka yi ido 4.
Yayi murmushi, ya ce,"Kin ta shi?
Fashewa tayi da kuka, ya taso da sauri ya zauna
gefen ta."
Nusaiba, ke Nusaiba, za ki fara koke-koken nan
ko?
Tayi shiru tana tunaniin Antin ta.
Hawaye na ta ambaliya.
Ya rik'o ta, ta kwace jikin ta, kuka take tana
k'arawa.
Ya ce a ran sa,"Na shiga 3, yau kuma da kukan ta
tashi." Ya matso, ta matsa. Ya ce,"Ni Nusaiba, ni
ki ke gudu? Bata kalle shi ba, balle ta ce wani
abu. Ya sake matsowa, ta matsa. Ya ce,"Shi
kenan, bari in yi tafiya ta, in tafi ko? Ta amsa eh,
da kai. Ya ce,"Tabd'i! Da magana yau,"Cikin
ransa.Ya rasa yadda zai yi, dole ya sa mata ido,
tayi ta kuka. Can kuma ta tashi ta fito koridon ta
zauna, bisa kujera. Shi ma ya biyo ta nan ya
zauna, yana gadin ta.
Jim kada ya ji kukan Ameer.
Ya mike ya ce da ita,"Ga Ameer can ya tashi, in
kawo shi ya sha? Ta kyale, bai ma ishe ta kallo
ba, ya shige ciki ya dauko shi, ya tsugunna
gabanta,"Yauwa, 'yar gidan Abbanta kenan, dubi
Bebin mu kuka yake yana jin yunwa, dan ba shi
ya sha." Ta dauke kai, tamkar bada ita yake
magana ba.
Abu fa ya gagara, dole ya dauko wa Ameer fida
ya tura masa, yayi ta tsotson ruwa da
glucose.
Kullum karfe 7 nan take masu. Alh.Basheer suna
nan zaune kuwa, sai ga su.
Naseer ne ya fara hango su, ya mike ya nufo
su.
Su ma tsayawa suka yi cak, ganin Nusaiba a
zaune wajen.
"Yaya dai? Alh.Basheer ya tambaye shi, yayin da
Ummi ta kar6i Ameer a hannun sa.
Ya ce,"Ai yau ko Ameer ta k'i ba shi nono.
Kuka kawai take yi,"Ya ce,"Likita ya zo?
Ya ce,"Ka tsaya nan, kai kuma koma gun ta, bari
in nemo Likitan." Ya koma wajen ta.
Alhj ya zaga ya wuce, ita kuwa Ummi ta
lafe.
Jimawa kadan suka dawo da Likita. Abin ya ba
Naseer mamaki daya ga Lkita ya zo, ya tsaya
gabanta bata zage shi ba.
Ya ce,"Nusaiba, tashi mu shiga ciki, mu yi wata
magana." Kai tsaye ta mike ta wuce. Naseer ya
saki baki, shi ma ya taso ya biyo su. Ta zauna
bakin gado, ya jawo kujera ya zauna ya
ce,"Kukan me ki ke yi?
Ta ce,"Antina ta mutu ko?Ya ce,"An gaya miki
bata mutu ba, Antin ki na gida." Ta runtse ido
wasu hawayen suka tsunke mata, ta sa hannu ta
share. Ya ce,"An ce kin ki ba Bebin ki nono,
saboda me? Haka za muyi da ke saboda Allah?
Ta dube shi da kyau ta ce,"Doctor ka yi min wani
taimako don Allah, lambar Abba na zan ba, ka
kira min shi." Idanuwan Naseer suka k'ara yo
waje, ya koma da baya da baya ya fito waje. Shi
kuwa Likita k'ara tsura mata ido, ya ce,"Abban
ki? Ta ce, eh. Ya ce,"Ina zuwa." Ya leka yayi kiran
Alhj da hannu. Ya taso daga inda yake zaune ya
zo. Likita ya kamo hannun sa, ya shigo da shi a
hankali. Kan ta na duke ya ce,"Wannan Abban
naki ki ke nema? Tana yo ido hudu da shi, ta
mike hawayenta suka yawaita, ta ce,"Abba! Wani
tsananin farin ciki ya kama Alhj, dole kwalla suka
cika idon sa, ya ce,"Bebin Abba! Ta rugo da gudu
ta rungume shi. Tuni Ummi ta fado dakin ta hade
su ta rungume, kuka suke saboda murna. Haka
Naseer ke sharar kwalla. Amma ya rasa abinda
zuciyar sa ke sakawa game da wannan al'amari.
Tabbas Nusaiba ta warke, to me zai biyo baya?
Da alamun zai shiga magana, yanayin da ta
nuna. Yayi ta maza ya shigo. Alhj Basheer ya
rungume shi, suna wa juna barka. Likita ya fita,
ya bar su cikin farin ciki da murna maras
misaltuwa.Bayan sun natsa. Ummi ta dubeta,
duk ta rame ta ce,"Sannu Nusaiba, Ubangiji Allah
ya k'ara karewa." Ta ce,"Amin. Ta miko mata
Bebi ta ce,"Kin ga Bebin da aka ciro miki? Ta dan
dube shi, tayi murmushi , ta dauke ido,"Na gan
shi Ummi ta. Kwalla suka taru fal a idonta, ta
kasa shanye su, sai da suka zubo. Abban ya
rungomu kafadunta, ya ce,"Yi hakuri daina kuka,
komai ya wuce Insha-Allah." Ya ce,"Allah ya
yarda Abba. Bari in yi sallah." Ta mike ta wuce
bayi ta jima bisa sallaya, tana yi wa Allah godiya
daya dawo mata da rayuwarta dai-dai. Ta dawo
gefen gado ta zauna kusa da Abban ta. Ya jawo
ta jikin sa, ta dan numfasa ta ce,"Abba lokaci yayi
da zan gaya maka wata magana, ina fatan za ka
gafarce ni." Naseer na jin haka, ya mike ya bar
dakin. Abba ya ce,"Babu komai Bebina, gaya min,
me ke da mun ki? Ummi ta sa masu ido tana
kallo. Ta k'ara gyara zama ta ce,"Na san za ka yi
mamaki, idan na gaya maka cewa tun aure na da
Naseer, babu kwanciyar hankali tsakani na da
shi. Ai kuwa Alh ya sha mamaki, ba shi da kadai
ba har Ummi da take zaune. Ya kara dubanta,
baki sake, ya tambaya, "Saboda me? Ta
ce,"Abinda na fahinta,"Abba, shine ya kar6i aure
na ne kawai don ka cika masa ido, ba zai iya ce
maka a'a ba. Amma a hakakin gaskiya Naseer
baya so na, kuma ya nuna min kiyayya, ba don
Antyna na tsaye ba, ina ganin wuyar da zan sha,
ba 'yar k'arama bace.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Shi yasa na ke son ta, domin tayi min komai,
kuma tayi iyakar kokarinta wajen jawo hankalinsa
zuwa gare ni, sai dai haka bata samu ba, saboda
babu sona a zuciyar sa." Ransa ya 6aci kwarai, ya
ce,"Me yasa tuntuni ba ki gaya min ba? Ta
ce,"Saboda kai ne Abba. Ba na son wani tashin
hankali ya shiga tsakanin ku. Kuma ina ganin ai
ya girmama ka ne, tunda ya kasa fitowa fili ya
nuna maka baya so na. Shi yasa na yi ta kokarin
zama da shi shekara daya da rabi, sai da Allah ya
kawo rabon wannan Yaron, sannan ya shiga daki
na. Daga baya na yi tunanin bai kamata mu
zauna muna cutar da juna ba, shi yana jin haushi
na, ni ma ina jin na shi. Sai na same shi a daran
da wannan abin zai faru, na yi masa magana.
Abba cewa yayi idan na k'ure shi, zai 6atacciya,
dole in koma gidan mu, har d'an baya so, ya bar
mana...................!!! Tana shiru. Ummi ta
cafe,"Ina, inda kuma yayi karya kenan. Ai ba mu
kai masa ke da Da ba." Alh.Basheer yayi shiru,
zuciyar sa na tafasa, abin kamar a mafarki yake
ganin sa, domin ko alama bai ta6a mafarkin
Naseer zai ci amanar sa haka ba. Ya dubi Ummi
ya ce,"Har hada mata kayan ta mu tafi." Ta mike
tana fadin,"Ashe ga damuwar da ta kusan hallaka
rayuwarki Nusaiba, kenan. Yayi wa kan sa. Kuma
sai Allah yayi miki sakayya." Nusaiba ta kada
kai,"Ba haka bane Ummi ta, ba laifin sa bane,
kar ki manta soyayya, gamon jini ce, laifin sa 1,
shine daya danki amanar da ba zai iya rikewa
ba."Alhj ya ce,"Duk laifin iyayen sa............ Tayi
saurin katse shi."A'a Abba, iyayen Naseer ba su
da laifi kuma ina mai tabbatar maku yadda ya
yaudare ku, haka ya yaudare su. Ba su san komai
ba a game da zaman mu. Sun rike ni tamkar 'yar
cikin su. Idan na ce ga abinda su kai min, na yi
masu karya, sai Allah ya tambaye ni. Abba, rokon
da zan maka daya ne, don Allah, don son Annabi
kar ka k'ullaci kowa akan maganar nan, ni ce
baya so, to ka dauki 'yar ka. Ai shikenan, an
gama magana." Ya ce,"Haka ne Nusaiba, ki yi
hkr, ni ma na gane kuskure na, ni na jawo miki
duk abinda ya same ki." Ta ce,"Ban ta6a ba ka
laifi ba Abba, ba kuma zan ta6a ba ka ba. Ai kai
alheri ka k'ulla, sai dai ka san a wannan zamanin
ba kowa yake son ayi masa za6in abinda ya
kamace shi a ruywar sa ba. Ya fi son abinda
ra'ayinsa ya ba shi. Ka ga kuskuren da aka samu.
Ina alfari da kai Abba na, kuma ko a yanzu ka
sake za6a min miji. Wallahi zan aure shi. Bai san
lkcn da ya rungume ta, ya fara kwalla ba. Haka
Ummi ke ta share hawaye, tana sawa Nusaiba
albarka. Ta mike ta shiga hada kaya. Hayaniyar
hama'a suka jiwo gaba daya jama'ar Naseer ne.
Zarah ma kayan barci ne ajikin ta, ta dora zani ta
sa hijabi. Suka doro cikin dakin. Zarah na
fadin,"Amarya!Ta zaburo da gudu, "Antina! Suka
rungume juna, sun sha kuka, sai da Umma ta
raba su ita ma, ta rungume ta. Daga nan ta
matsa ta gaida kowa. Su Malam Balarabe, Malam
Umar. Ya gaisa da Sageer da amayar sa. Bayan
an gama gaishe-gaishe. Malam Balarabe yasa aka
yi addu'a, kowa ya shafa. Aanan suka lura babu
Naseer tun shigowar su. Inna ta fara
magana,"Jama'a wai ina dan Inna ne? Malam
Umar ya ce,"Kai wai dama babu Naseer a wajen
nan? Sageer ya amsa,"Ai kuwa baya wajen nan,
tunda muka zo? Malam Balarabe ya ce,"Ah to ina
ya je? Ya fadi, yana kallon Alh.Basheer. Ya
ce,"Gaskiya ban san inda ya je ba. Kuma dama
ina son ganin ka, idan ba za ka damu ba." Ya
ce,"Bismillah Alhj, ba damuwa." Suka fito waje,
yayin da Zarah da Nusaiba ke like da juna suna
maida yadda abubuwa suka faru. Alh.Basheer ya
kebe da M.Balarabe, ya kwashe bayanin da
Nusaiba tayi masa kaf, ya gaya masa. Tun da ya
soma magana, gaba daya jijiyoyin jikin Malam
Balarane suka tsinke, jiri ya fara dibar sa. Allah
yasa a zaune suke, da babu abinda zai hana shi
faduwa. Tabbas ya san Naseer baya son auran
nan, aka yi shi, amma ko alama bai ta6a sanin
rashin mutunci da wulakancin da ya rinka
aikatawa ba. Ya jima kafin ya ce,"Alhj wannan
magana ta ban kunya, kuma Wallahi tallahi ban
san komai a game da zancan ba. Nusaiba bata
nuna mana ba, balle ta furta da bakin ta. Don
girman Allah ka yi hakuri Alhj. Ya ce,"Ai magana
ta k'are, tunda baya son ta, ni ina son abata
kuma zan tafi da ita, ba tare da 6ata lkc ba.
Amma D'a, ban sako mata shi cikin gara ba, sbd
haka nan za ta aje shi ko ya kashe ko ya bar shi
da rai, duk ya rage nasa. A karshe, ka gaya masa
na gode. Allah ya saka da alkhairi. Kan
M.Balarane yayi gingirinn! Kunya kamar ya nutse
kasa. Idanuwan sa suka cika da kwalla, ya rasa
me zai ce wa Alhj? Kawai sai ya juya ya dawo
dakin, gaban kowa ya daga murya ya
ce,"Nusaiba, don me za ki min haka???Akan me
za ki zauna sama da shekaru 2 cikin wulakanci da
bak'in ciki, amma muna tare, ki kasa gaya min?
Ba ki min adalci ba Nusaiba, domin da kin gaya
min da tuni na yanke hukunci, sai dai ya nemi
wani uban, ba ni ba! Kowa yayi tsuru-tsuru.
Nusaiba kuwa tuni ta fara kuka. Ya matsa gadabn
Ummi ya tsugunna." Hajiya ki yi wa girman Allah,
ki yi hakuri. D'a ne ka haife shi ba ka haifi halin
sa ba. Ko alama ban san halin da suke ciki da
matar sa ba. Ga mahaifiyar sa nan a zaune, ko
ita da ke zama tare da su munafikin Yaron nan
bai ta6a barin ta gane wani abu ba, balle ni da
ban zama cikin gida. Maganar tafiya da Nusaiba
kuwa kun yi dai-dai, domin ko ni ne hakan zan
yi. Saboda haka kowa yayi shaida. Ni Balarabe na
tsame hannu na akan komai daya shafi Naseer,
duk abinda ya ga dama yayi rayuwa
ce................ Ya fashe da kuka, jikin kowa yayi
sanyi, matan da ke wajen ma tuni suka soma
taya shi, musamman Umma da ta ji abin kamar
saukar aradu. Sageer ma waje yayi kirjin sa na
bugawa, ga ranar da yake jin tsoron zuwanta,
kullum yana gaya wa Naseer. Amma kunnuwansa
iskar duniya ta dode masa su. M.Umar da Alhj
suka riko M.Balarabe,"Ka yi shiru haka,"Malam
Balarabe, kar zuciya ya kwashe ka, ka yi masa
baki." Ya dube su ya ce,"Ni Naseer yayi wa tijara
haka, Babu komai, rayuwa ce!Ya dubi Umma ya
ce gaba,"Ke dauko masa D'ansa mu tafi, ki kai
masa kayansa, idan ya ga dama ya jefa shi bola!
Malam Umar ya ce,"A' ba'a yi haka bane, duk ku
zauna a sasanta magana. Ai in rai ya 6aci, hankali
ke nemo shi. Alhj ka yi hakuri, mu zauna da
Naseer mu ji ta bakin sa, don girman Allah kar ku
yanke hukunci kai tsaye haka." Alhj ya kada
kai,"Ban k'i taka ba. Amma Naseer ya riga ya
k'are magana, sai dai hukuncin daya yanke ne
ban yarda da shi ba, d'a kan ba na mu bane, na
shi ne. Don haka anan za'a bar shi. Iya magana
kenan." Malam Balarabe ya ce,"Magana tayi dai-
dai Alhj, ku bar masa shi, ya san uwar da za ta
shayar masa D'an shi. Ki dauko shi mu tafi, na
gaya miki, idan kuma ki na nan, ni na wuce! Yayi
waje. Malam Umar ya bi shi. Umma ta dubi
Ummi, ta ce,"Don girman Allah Hajiya kar ku yi
wa Yaron nan haka, shi bai san komai ba, ku
tausaya masa." Tayi shiru, ta rasa me za ta ce?
Yadda Alhj ya fusato, babu mai sa shi dukan
D'an nan. Haka Zarah ta rike Nusaiba,"Amarya
kar ki ta fi, don Allah ki taimake ni. Idan ki ka
tafi da wa zan zauna? Suka k'ara fashewa da
kuka. Ita dai Fa'iza ba baki, sai ido. Bata fahimce
komai ba, take ta faman kuka. Alhj ya fice ya bar
su nan, suna ta faman magiya. Jim kadan ya
dawo tare da Likita. Shi dai ya ga ana ta koke-
koke, a zaton sa duk na murna ne, yayi abbuwan
da zai yi, ya gama ya ba su sallama tare da
takardar magunguna da za ta ci gaba da sha na
tsawon kwana 7.Alhj da kansa ya rink'a dibar
kaya yana kaiwa cikin mota, har ya kwashe su
duka. Ya kamo hannun Nusaiba, ya wuce da ita.
Ummi ta biyo bayan su, suka bar Umma da jariri
bisa gado, yana ta faman barci. Ta k'ara fasa
kuka. Inna ta kamota tana rarrashi. Haka Zarah
ke durk'ushe, hannu 2 bisa kai.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Daga inda Naseer ke 6oye, yana hango su Alhj
suka zo suka wuce a moTa. Yasa hannu ya goge
hawayen da ke kuncinsa. Jimawa kadan ya hangi
su Umma. Inna na dauke da Ameer, suka shiga
motar da ta kawo su. Direba ya ja suka bar
asibitin. Wasu hawayen suka sake zubo masa,
yayi kamar ya hadiyi zuciya ya mutu. Ya nufi inda
ya aje motar sa, ya shiga haka ya dawo gida,
baya gani wuri sosai. Ya rasa inda zai je, sai yayi
fakin kofar shago, ya shiga ya sallami su Abbas
ya ce duk su tafi gida. Ya kulle kansa ciki, ya rasa
abinda ke masa dadi a duniya. Cikin gidansu
kuwa kamar anyi mutuwa, shiru ba ka jin motsin
kowa. Jim kadan Zarah ta fito da jakar kayan ta,
ta lallabo zuwa sasan su Umma. Ta leko a
hankali, ta ga babu kowa, ta cire takalmanta ta
wuce sadaf-sadaf kamar 6arauniya. Tayi waje kan
ta tsaye tayi gidan su. Inna ta zura mata ido,
kafin ta ce,"Ke kuma fa? Ta shige uwar daki da
gudu. Inna ta biyota,"Na ce ke kuma fa? Kin
shige da gudu. Menene na ce? Ta ce,"Allah Inna
ni ma ba zan zauna ba. Haba ai wulakancin yayi
yawa, ko alama yayana baya jin magana. Ta
balbaleta da fada,"Laifin waye? Ai duk ku na
sane, aka rasa wacce za ta gaya wa manya, don
ayi maganin abin, sai yanzu da zance ya lalace,
za ki ce Naseer ne baya jin magana? Maza dauko
jakar nan, ki koma inda ki ka fito, tun kafin
Babanki ya k'araso gidan nan, ya sameki." Ta
6arke da kuka, tana fadin,"Ba inda za ni Inna,
idan har na koma gidan nan, to yayana ya dawo
da Nusaiba. Kuma ku matsa min ku gani. Wallahi
tafiya ta zan yi." Inna tasa mata ido tallafe da
baki. "Ki ka ce me? Lallai wuyanki ya isa yanka,
to zan ji idan kke ki ka haife mu." Ta yi zamanta
bakin gado, har Inna ta gama babatun ta, ta
fice." Na rantse da Allah ba zan koma ba, ya je
ya ci kan sa a gidan, tunda shi ba'a gaya masa
ya ji." Koda Malam Umar ya dawo, babu yadda
ya iya yi da ita, ya gama fadansa da barazanarsa
ko gezau zuciyar Zarah bata yi ba, kuma ta
rantse ta maya, muddin suka bari ta bar nan, ba
za su sake ganin ta ba. Shi yasa da ta dauko jaka
ta fito. Inna ta dauko muciya ta kora ta daki, ta
ce,"Koma daki marasa kunya, idan Naseer din ya
zo ya dauke ki! Ta maida jaka ta yi zamanta cikin
dacin rai da takaici tare da tausayin Nusaiba da
karamin goyonta.
Sageer ma da ke zaune a dakinsa, babu abinda
ya fi damun sa irin dan karamin yaron da aka
aje. Alhalin bai san komai ba. Fa'iza ta
ce,"Yakamata ku taimaka wa yaron nan a maida
shi wajen Maman shi,"Wallahi shi ne abin
tausayi, ba ka ji yadda na ke ji ba, kamar inyi
tsuntsu kai shi wajen ta." Ya ce,"Shirun nan da ki
ka ga nayi. Ameer kawai na ke tunani." Yayi
hucin zafi, ya dauko waya daga aljihu ya nemo
lambar Naseer. Ta dan jima tana bugawa kafin ya
dauka, ya ce,"Ka na ina ne? Murya dishe ya
amsa,"Shago." "To ina zuwa." Ya kashe waya, ya
dubi Fa'iza,"Wai yana shago, bari in je in same
shi." Ta ce,"To ba za ka dan ci komai ba? Ya kada
kai, bari dai in je in dawo. Ya fice, tana fadin a
dawo lafiya. Ya kwankwasa kofar shagon, ya zo
ya bude, suka koma ciki tare. Daga kallon Naseer
kawai. Sageer ya gane yayi nadama, gaba daya
ya jeme ya fita hayya cin sa. Ya dube shi a
sanyaye ya ce,"Ka ga irin abubuwan da na ke
gaya maka ko? Yanzu ina ribar wannan abu?
Kullum ina gaya maka yi wa iyaye biyayya ibada
ce, duk kuma mai yin sa ba zai ta6a ganin 6acin
rai ba. Amma Naseer na ka ji, ni ban san abinda
ke damun ka ba. Dan yaro jariri an ajiye maka
shi, ina amfanin sa? Iyayen ka na ta kuka saboda
kai, wacce irin masifa ce wannan? Ka farka daga
bacci Naseer, kai ba yaro ba ne."Ya dube shi
kwalla suka zubo ya ce,"Ban san abinda zan ce
ba Sageer, domin ni kaina na san mai laifi ne,
saboda haka duk hukuncin da aka yanke min,
yayi dai-dai. Sai dai babu wanda ya san cewa na
dade da yin nadama, sannan in na ce ba son
Nusaiba yanzu, na yiwa raina karya. Shi ya sa na
dage ba dare ba rana wajen kula da ita tare da
rokon Allah ya bata lafiya, don in samu in nemi
gafarar ta, na kuma nuna mata iya so da kaunar
da na ke mata yanzu. Allah da ikonsa sai ta sami
sauki, hankalinta ya dawo jikin ta, a lokacin da
iyayen ta ke wajen, sannan bata 6ata lokaci ba,
ta zayyane masu komai. Ka yarda da ni Sageer?
Ka taimake ni, domin ni yanzu ban san yadda zan
yi ba." Sageer yayi shiru, yana kada kai
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Tabbas ya yarda da maganganun Naseer, saboda
yana daya cikin masu mmkin yadda Naseer ya
rinka kula tare da ririta Nusaiba, sai dai a lokacin
ya dauka saboda halin da ta shiga ne, kuma bata
son kowa ya kusance ta, sai shi. Ya nisa kafin ya
ce,"Yanzu tinkarar Abban, tashin hankali ne ba
karami ba, kuma dole ne aje a same shi, tunda
shine jigon komai. Abin yi shine, ka taso mu je
wajen sa, ayi ta ta kare ko kashe mu zai yi." Ya
kada kai,"Gaskiya Sageer ba zan iya ba.ka je kai
kadai tukuna, ni na fi kowa sanin halin Abba." Ya
ce,"Shi ke nan. Za ka jira ni a anan din ne? Je ka
dawo ina jira. Ungo key din mota don ka yi sauri.
Ya kar6a ya fito a sukwane, ya fada mota, yayi
gidan su Naseer. Yayi sallama falon Abba, a
lokacin Umma tana goya Ameer ta fito ta siyo
masa madarar jarirai, bayan ta nemi Zarah ta
rasa a cikin gidan, don bar mata ajiyar yaron
kafin ta dawo. Shi yasa zuciyan Abba ke kara
tafarfasa, ya sani babu makawa ita ma tafiyar ta
ta yi. Da kyar ya amsa sallamar Sageer. Ya shigo
a darare, ya nemi gefe ya makure, ya ce,"Sannu
Abba." Ya ce,"Me aka yi Sageer? Ya ce,"Abba
Naseer ne................Ya dakatar da shi da
hannun sa kafin ya ce,"Tashi ka tafi! Sannan idan
ka je, ka gaya masa ita ma wacce yake son ta tafi
abinta, saboda haka ya zo ya kwashe kayan sa,
ta bar min gidana in huta." Ya tashi ya durk'usa
Abba................Ya runtse idanuwansa,"Sageer ina
ganin mutuncinka, don Allah, don son Annabi ka
tashi ka tafi. In dai akan maganar abokinka ne,
na riga na datse magana, na yi rantsuwa Naseer
ba zai sake sani kaffara ba. Saboda haka ka je ka
gaya masa, shi 'yantacce ne, kar ya dami kan sa.
Tashi, kanzil ban ka kara fadi ba, idan har ni ina
isa in gaya maka. Idan kuma ban isa ba, to
kacigaba da zama. Sageer ya shiga 3, Abba ya
daddaure shi, ga magana bakin sa babu damar
fadi, yana ji, yana gani, ya tashi ya fice. Yayi
tsaye jikin mota ya rasa tudun dafawa. Ga wata
sabuwa, kuma ita ma Zarah ta yi gaba. Duk da
dai yana ganin na ta mai sauke ni, amma ba
dadi ace ita ma tana gidan su.Ya fi minti 5r a
tsaye, sannan ya bude mota zai shiga. Ya hango
Umma tafe. Ya tar6e yana mata sannu da Zuwa.
Ta amsa za ta wuce cikin gida, ya ce,"Umma ku
taimaki ni Naseer na cikin wani hali, komai za iya
faruwa da shi. Ta ce,"Shine me? Sai aka ce
karshen Umma ya zo? Ya ce,"Ba haka ba ne
Umma. Wallahi Naseer yayi nadama, tun ranar
da ta sami kan ta cikin wannan yanayin, kuma ba
shi da wani buri daya wuce idan ta ji sauki, ya
bata hkr akan abinda yayi mata. Sai kuma aka
sami akasi, komai ya yamutse. Ta yi dan
murmushin takaici ta ce,"Yaro man kaza. To
yanzu da ka zo nan ka na ta dogon bayani, akwai
Nusaiba a nan ne? Tana fa Kaduna, a gaban Ka
Babanta ya dauke ta. Ba sai ya je can ba, ya roke
ta. Menene abin zafi? Ya durk'usa bisa guiwa, ya
ce,"Ku yi wa girman Allah Umma ku yafe masa,
ke ma kin san duk abinda ki ka fadi, ba zai yuwa
ba. Sai da goyon bayan ku." Yana sa aya Abba na
tsayawa kofar zauran, bai ce wa Umma komai
ba, ta wuce cikin gida. Shi ma ya bi bayan ta.
Sageer ya sauke numfashi, ya tashi ya fito ya
tafi.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Yana shiga shagon zama kawai yayi, ganin haka
Naseer din ma yayi shiru, ya san babu nasara.
Sun dau minti goma a haka, kafin Sageer ya
ce,"Wai Zara ma ta tafi gidan su."Ya dube shi da
sauri." Me na yimata ita kuma? Kashe ni suke so
su yi ko? Shi kenan." Ya goge kwalla. Wayar sa ta
hau bugawa, da kyar ya dauka. Yakubu ne ke
kiran sa. Ya rasa ta yadda zai yi ya dauka. Ya
dubi Sageer, ya ce,"Zo mu je gidan Yakubu." Ya
tashi suka tafi. Ya maida masa bayanin komai.
Yakubu yayi masa fada kamar zai ari baki, shi
kansa ba karamar kunya ya ji ba lokacin da Alhj
ya kira wayarsa, yana gaya masa Naseer ya ci
amanarsa. Duk da haka yayi masa alkawarin
shiga maganar, sai inda karfin sa ya kare. Shi
kuwa Naseer B ana maganar, yana kallon kowa a
dage, zuciyar sa gwanin haske, har yana addu'ar
kada Allah yasa su shirya. Amma bisa fuskar sa,
ya fi kowa nuna damuwa kamar yayi kuka. Daga
gidan Yakubu, wajen Zarah suka iso, misalin
karfe 1 na rana. Sun shigo gidan. Inna na kwashe
abinci cikin kula. Ta daga ido ta dube su, tana
amsa sallamar su. Gaban ta ya yanke ya fadi,
ganin yadda Naseer yayi wanu duhu lokaci guda.
Ta ce,"Dan Inna! An gaishe ka da aiki. Ku shiga
gani nan zuwa." Ya wuce simi-simi. Sageer ya bi
bayan sa, suna zaune. Inna ta gama abinda take
yi a kicin, ta bi su dakin. Zarah ta leko daga bayi
ta ga Inna, ta shige sai ta sadado ta aje buta, ta
suri hijabin Inna dake shanye bisa igiya ta yi waje
ta bar unguwar. "Sannu dan Inna, ka sha aiki
Wallahi, ya gajiya? , Ya sunkuyar da kai Sageer ya
ce,"Inna kuskure ne, kin kuma san ajizanci irin na
Dan-adam. Amma a yau ya gane, har ya
tuba........ Ta katse shi, tuban mazuru? Sau nawa
Naseer ke cewa ya tuba a gidan na ma kawai,
wanda na sani? Ai ba zan iya fadi ba. Yanzu wa
gari ya waya? Babu abinda ba mu gaya maka ba
D'an Inna, tun kafin ayi auran nan. Bayan anyi
kuma, ba mu fasa ba, sai dai in kafar ka bata
shigo da kai gidan nan ba, amma ba ka ji. A
fuska lafiya lau ka ke, halin ne kawai ka kasa
gyara shi, su yi dai-dai da fuskar ka. Me yasa? A
yanzu wa ka ke ganin zai iya tunkar Alhj? Babu
abinda za mu iya gaya masa, ya yarda, saboda
ka riga ka rushe ginin tun ranar zane. Naseer ya
ce,"To Inna shi kenan, haka za'a sa ido, auran ya
kare kenan? Ta ce, "Eh mana, ta riga ta gayawa
Babanta ba ka son ta, wa ka ke zaton zai je ya
ce, karya ne? Ya ce,"Gaskiya Inna ban yarda ba,
na san ana zuwa biko Inna. Sai dai in ba za ki je
min ba ne kawai
Ta yi dan murmushin dole ta ce,"Dan Inna
manya, ga laifi, ga saurin tuba. To shi kenan, ka
bari Baban na ku ya dawo, za mu san yadda za'a
yi." Ya numfasa ya ce,"Wai ita ma Zarah don ta
kara min hawan jini shine ta bar gida ko? Ina
take, sai ta ci dan banzan duka yau, in ni sa'an
ta ne, za ta gaya min." Dariya suke da Inna da
Sageer, kafin Inna ta ce,"Yanzu ta shiga bayi, za
ta yi alwala ta yi sallah." "Ina nan ina jiran ta ta
fito,." Inna ta mike,"Bari in kawo maku abinci
Sageer. To Inna. Sageer ya amsa. Ta fice,"Sageer
ya ce, "Na ciro maka wayar Rediyon can ne?, Me
zan yi da ita? Dukan mana harka mance? Tsaki
yayi ya dauke kai. Inna ta shigo da abinci ta
ce,"Ka fa ci. Sageer ka matsa ma sa ya ci. Ya
ce,"Ai zai ci Inna." Ta yi waje ta koma daki. Shiru-
shiru Zarah ta ki fitowa daga bayi. Inna ta fito da
wannan mamakin, tana tambayar kanta,"Ita
wannan zaman me take yi a bayi?" Tana sa aya,
ta aje ido bisa buta a gefe. Ta leko dakin ta
ce,"An gama dukan?" To ai ban ji kuka ba, bata
daku ba kenan." Suna dariya ya ce,"Ai bata shigo
ba Inna.." Ta gintse fara'a ya ce,"Ban gane ba?
Ga shi ta aje butar a waje. Ta juya ta fito tana
kwala mata kira, yayin da dukkansu suka aje
cokula suka fito. Kamar wasa, babu Zarah acikin
gidan. Mamaki ya ishi Inna. Ta kama baki, tana
kallon igiya babu hijabin da ta shanya. Sageer ya
ce,"Wai ita Zarah da gaske take yi? Inna tayi
shiru abin ya girmi shekarun ta. Naseer ya
numfasa ya ce,"Inna ki gaya mata, idan ta ji ina
asibiti kar ta sake ta zo guna. Zo mu je Sageer.
Ya yi waje. Sageer ya ce,"Inna ki ce Allah ya bata
hakuri. Sai anjima." Da kyar ta iya amsawa,"Allah
ya ba mu alkhairi." Shi ma ya wuce. Inna ta ja
kujera ta zauna, yau na ga zamani ni A'isha. Kiri-
kiri yarinya ta ban kunya? Suna tafe a mota
Sageer, ya ce,"Yanzu ina muka nufa? Ya
ce,"Gidan za ni, duk ayi ta ta kare, idan ma
yankana ni za su yi, su yanka. Ba shi kenan ba?
Idan kowa yayi min, ai bai kamata Zarah ta yi
min ba. Duk saboda wa na shiga wannan halin?
Ba saboda sonta ba ne? Duk ba ta ga hakan ba."
Ya furta. Sageer yayi shiru domin ya lura abokin
sa ya zare gaba daya, kar ya tofa wani abu, ya
kara masa zafi. Ya ci uban birki a kofar gidan, ya
fito yayi cikib gida, bai ko saurari Sageer ba. Sai
dai yana shigowa ciki ya tsinkayi Ameer na ta
tsala kuka. Nan da nan ya yi turus, guiwa sa ta
kwa6e, a salu6e yai sallama falon. Umma na
kokarin goya Ameer a lkcn Abba kuwa na zaune
gefe iya wuya yake. Kuma yana ji da kowa, duk
wanda ya kuskura yi masa wata magana akan
Naseer. Yana shigowa. Abba ya mike ya debi
takalman sa ya bar gidan. Naseer ya bi shi da
kallo, ya kasa cewa da shi komai, har Umma ta
gama goyon, ta sa hannu ta dauke gwangwanin
(Prisso-cream) din da ta siyo ta dora bisa firij, ta
dauki fidar ta yi waje. Ita ma ya bi ta da kallo,
sannan ya bi bayanta. Tana famfo tana wanke
fidar da soso da omo. Ya bi ta, ya tsaya a gefen
ta ya sanyaya murya,"Umma!Ji ta yi tamkar ya
watsa mata wuta. Ranta ya ci gaba da k'una
kamar ta rufe shi da dukan fitar hankali. Ya
durk'usa ya mika hannayen sa gaba gare ta.
Idanuwansa dauke da kwalla. "Umma, ki yi wa
girman Allah ki amsa min. Umma ki dube ni ki
saurari rokona. Na yi laifi Umma, amma tuni na
gane kuskure na, ku ba ni dama ta karshe
Umma. Da yardar Allah ba zan sake saba maku
ba, Umma ki taimake ni." Ta gama dauraye fida,
ta yarfe ruwan, ta juya ta koma daki tana
daddaure su yadda suke. Naseer ya nemi wuri
nan ya zanau dirshan! Sageer ya matso zai masa
magana, yayi sauri ya riga shi." Je ka gidan abin
ka Sageer. Na gode." Ya yi dan jim, yana kallon
sa,"Ka ta fi na ce, babu komai, sai mun hadu."
Ya numfasa ya ce,"Shi kenan, Allah shi kyauta."
Ya juya ya fice, ba tare da Naseer ya sake cewa
wani abu ba. Nan yayi ta zama har ya tuno, bai
yi sallah ba. Yayi alwala a nan famfon, ya wucce
sasan su, yayi Sallah a falo ya ci gaba da zama
nan bisa sallaya. Babu abinda zuciyarsa bata saka
masa ba. Zarah kuwa bata dowa ba, sai bayan
sallar la'asar, ba shakkar komai. Ta yi sallama ta
shigi ta wuce Inna a tsakar gida ta shigo daki.
Inna ta tafa hannu ta ce,"Da izinin wa ki ka bar
gidan nan? Ina kuma ki ka je? Kai tsaye ta
amsa,"Inna ai na gaya maku ba zan koma ba. Kin
zaci wasa na ke yi ko? Ta ce,"To ba kuwa zama a
gidan nan ba, bari baban na ki ya shigo. Na lura
so ki ke ki kawowa mutane raini. Ta juya ya bar
dakin. Zarah ta matsa inda kulolin abinci ke aje,
ta buda ta zuba ta hau ci. Karfe 5 M.Umar ya
shigo gida, Inna ta feshe shi. Ya jinjina kai ya
ce,"Wai Zarah da na sani ki ke fadi? Ta ce,"Ka na
wasi-wasi kenan? Shiga tana nan a daki." Tunda
ya baro dakinsa yake balbala masifa har cikin
dakin."Ki hada kayan ki, ki koma inda ki ka fito!
Ta ki motsi, M.Umar har da barazara duka,
amma ko alama Zarah bata motsa ba, sai sharar
kwalla take yi. M.Umar ya cika da al'ajabi, yana
haki, ya koma dakin sa. Inna ta yi zuru tana
kallon sabon salo. Fadi take cikin ranta,"Zarah ta
kangare." Haka kowa ya kwana a wannan dare.
Babu barcin kirki.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Washe gari bayan sallar asuba. Nusaiba ke zaune
bisa gado, tunani bisa tunani. Tun jiya take cikin
wannan yanayin. Musamman da ga Abbanta ba
shi cikin sukuni kuma tun isowarsu gida, babu
inda ya sake fita. Tashin hankalinta ya k'ara
tsananta, tun daga lkcn da ta ga nononta ya cika,
har ya fara tsiyayewa a banza. Bakin takaicin
dake cinta kenan, a halin yanzu bisa gado, ta
rasa inda za ta tsoma ran ta, ta ji sanyi sbd
tunanin dan kyakkyawan dan ta. Ta tabbata yana
can yana kukan neman nono, ga shi nan yana
zubewa a iska. Farkewa ta yi da kuka, sbd
tausayin rayuwar da Naseer ya je fasu ita fa dan
ta,. Ji ta yi an riko ta. Muryar Umminta ke
fadin,"Nusaiba! Daina kuka, ki yi hkr. Ta fado
jikin Ummi ta rungume ta. Ummi ta shafa kanta
ta ce,"Ki yi shiru na ce. Allah ne ya kaddaro miki
wannan al'amari. Yanzu dago fuskar ki ki ji. Ta
dago, Ummi ta sa hannu ta share mata hawaye,
kafin ta ce,"Abinda na ke so da ke Nusaiba, ki yi
hakuri mu je a dauko yaron nan.Bawan Allah ne
shi, bai da laifin komai. Sannan shayar da shi da
za ki yi, shine yake sanya shakuwar uwa da
danta, soyayya tare da jin kai.Ki sani Nusaiba
Ubangiji ne kadai ya san dubun ladan da uwa
take samu tun daga daukan ciki, haihuwa, raino
tare da bada tarbiya, ga 'ya'yan da Allah ya
bata,kar ki bari wannan gara6asar ta wuce ki
Nusaiba. Ki dauko dan ki ya shaku da ke, ya san
cewa ke ce mahaifiyar sa.
Ta yadda zai ji kan ki, a cikin zuciyar sa, idan
Allah ya raya shi. Na yiwa Abban ki magana, na
rarrashe shi, na kuma yi nasara, ya amince,
yanzu yardar ki na zo nema, domin ya ce shi ba
zai matsa miki ba, duk abinda ki ka za6a shi
za'ayi.
Shi kuma Naseer din muna nan muna jiran sa, ya
kawo miki takardar ki.
Yanzu me ki ka ce?
Ta goge kwallan da suka dararo mata, ta ce,"Ki je
ki dauko shi Ummi, babu komai."
Ta tallafo fuskarta ta ce,"Yayi kyau. Allah yayi
miki albarka.
Amma ki tashi ki shirya Direba zai kai mu, don ki
kintso kayan ku a natsa.
Tashi ki daina kuka, ba na son ki na damuwa, kin
kuma san Abbanki hankalin sa ba zai kwanta
ba.
Ta goge hawayenta sarai,. Umma ta kama ta ta
riko, ta raka ta hanyar bayi, sannan ta fice ita
ma, don shiryawa.
Abban ke kwance a falon sama bisa kujera, shi
kadai yake kallon silin yana lissafon halayyar Dan-
adam mai abin mamaki.
Nusaiba ta shigo cikin shirin tafiya.
Kamar mai ciwo yake kwance, bai motsa ba har
ta zo gun sa, yana kallon ta.
Ta tsugunna ta kwanto kanta jikinsa, ta yi
shiru.
Ya daka kanta ya ce,"Bebina, ki je ki dauko dan
ki, ki shayar da shi.
Allah zai ba ki lada, kin ji?Ta amsa da kai. Ya
ce,"Mike ku tafi, na ga Ummin ki ta gama
shiryawa.
Allah ya kiyaye hanya." Ta ce,"Amin Abba na." Ta
mike ta wuce ya bi ta da kalllo, ta kai kofa, ta
waigo suka hada ido, yayi dan murmushi yana
mata (bye-bye) da hannu.
Ita ma ta yi masa, sannan ta sauka, lkcn karfe
7:30am. Ummi ta matsa mata ta dan ci kayan
karin safe.
Karfe 8 Direba ya dauko su, suka damk'i
hanya.
Karfe 8 din dai-dai. Naseer ya shigo falon,
Umma, don gaishe su ko ba za su amsa masa
ba.
Umman kadai ke falon,
tana ta faman gyangyadi.
Da alama Ameer ya sami barci, domin cikin dare
yana ta jin kukan sa.
Bata kalle shi ba, ya durk'usa gaban ta, ya
ce,"Umma ina kwana?
Kamar za ta kyale shi, sai wata zuciya ta ce,
amsa.
Bata kalle shi ba ta ce, lafiya.
Farin ciki ya lullube shi, ya ce,"Na gode
Umma.."
Ta kyale shi.
Yayi dan jim yana kallonta, kafin ya ce,"Umma
ina Abba?
A fusace ta dube shi, ta yi masa tsawa,"Ga shi
nan a baya na a goye!
Tabatacce maras kunya.
Ka sake zuwa ka tambaye ni, ina Abba ya ke, sai
na ci mutuncin ka!
Yasa hannu ya dafa guiwoyinta ya ce,"Yi hakuRi
Ummana, ba zan sake ba.Dama Zarah ce ta ce
ba za ta dawo ba, sai Nusaiba ta dawo, shine
nace ko za ki sa baki ta yi hkr ta dawo kafin a
shawo kan Alhj?
Kai tsaye ta dube shi, tsakar ido ta ce,"Ban
zuwa." Kar mu yi haka dake Ummana. Wallahi na
yi nadamar abinda ya faru, ku sa ke ba ni dama
ku gani zan rike Nusaiba iya rayuwata.
Ta dube shi a dage ta ce,"Bakin alkami ya riga ya
bushe maka Naseer, domin jiya da daddare su
M.Umar da M.Lawar sun zo. Amma Abbanka ka
ya rantse, ya masu, babu ruwan sa a cikin
maganar ka.
Haka ni ma bai lamunce min ba.
Saboda haka ka makara, dabara kuma ta rage wa
mai shiga rijiya. Ina fatan ka gamsu. Yayi zuru
kafin, ya numfasa ya dube ta ido sun kawo
kwalla.
"Shi kenan Umma, na gode. Abinda na ke son ki
rokin min Abba, shine, don Allah yayi hkr, idan
na gaishe shi ya rinka amsawa. Ni zan fita, ga
wannan koda Ameer yana bukatar wani abu." Ya
ciro dubu 2, ya aje bisa hannun kujera ya tashi
ya fice.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 9 ta gota kadan Jeep din su Hajiya Zulai ta
yi fakin kofar gidan su Naseer. Suka fito Ummi na
rike da hannun Nusaiba. Ummi ta yi sallama
tsakar gida. Umma ta amsa daga falo, a lkcn
kuwa ta kammala shirya Ameer tsaf!Yana ta
tashin kamshin hoda. Bata dauki murya sosai ba,
don haka ta ce,"Maraba, ku shigo mana." Ummi
ta yaye labule. Umma ta mike baki har
kunne,"Hajiya!
Ah!
Nusaiba!
Sannun ku da zuwa."
Suka zauna a kujera Umma ta mikawa Ummi
Ameer, ta karbe shi. Sai ta wuce firj za ta dauko
kayan sha.
"Dama kin bar shi, kin san safiya ce." Duk da
haka ta kawo da Jus din kananan kwali da kufuna
2.
Bayan sun gaisa, Umma ta tambayi Alhj? Sai
Ummi ta ci gaba da cewa,"Ba wani abu ya kawo
mu ba.
Ameer mu ka zo tafiya da shi, ya zauna wajen
uwar sa ta shayar da shi. Ko dama 6acin rai ne
yasa aka aje shi."
Kwalla suka cika idanuwan Umma ta ce,"Gaskiya
ne kuwa, na ji dadi, domin a gaba daya wannan
al'amari Ameer shine abin tausayi.
Shi kuma wancan sakaran, ai kyale shi ya gasu,
duk da cewar ya ce yayi nadama." Ummi ta yi
dan murmushi ta ce,"Ai ba'a soyayya dole, mu
ma mun san haka shi yasa Alhj ya ce a gaya
masa, tana jiran takardarta, ko zuwa jibi. Insha-
Allah za mu turo mota akwashe kayan ta a dauki
motar ta."
Umma ta goge kwalla ta ce,"Ba laifi, ki yi hkr
Nusaiba kin ji? Allah ya amfana miki dan ki. Ta
dan sadda kai ta ce,"Ba komai Umma.
Idan kuma na yi miki wani laifi, ki yafe min." Ta
girgiza kai,"Baba abinda ki ka yi min Nusaiba,
Allah yayi miki albarka."
Ta ce,"Amin." Ummi ta ce,"To bari mu je, za ta
debi wasu kayan kafin a zo kwashewa." Umma ta
ce,"To bari in kawo maku wani makullin, ya fita
da na hannun sa."Nusaiba ta ce,"Ina Antina
Umma?
Ta ce,"Ita ma ta tafi."
Suka dubi juna, kafin Ummi ta tambaya,"Saboda
me?------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 3-03
Posted by ANaM Dorayi on 11:46 PM, 21-Nov-15
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Fa ce,"Ita ma ba za ta zauna ba.
Sai Nusaiba ta dawo.
Kin ga ya 6ata 2 kenan, sai wani gyaran
Allah.
Nusaiba ta dafa kirji ido waje, sun kawo kwalla,
ta dubi Ummi ta ce,"Me yasa Antina za ta yi
haka? Ai ni ba zan ta6a dawowa ba, yakamata
yayi ta gane wamman.
Ummi mu je in debi kayan, mu wuce wajen
ta."
Suka mike, Umma ta kawo makulli. Nusaiba ta
debi kayayyakin da take son diba. Abubuwan
dake firj din ta duk ta kwaso ta kaiwa Umma.
Bayan Direba ya zuba kaya a mota, suka sallami
Umma suka rabu suna daga wa juna hannu.
Babu Abinda zata yi, Nusaiba ta hana ta tafiya,
babi abinda za ta iya yi.
Duk iya kaunar da take wa Nusaiba data zauna
dakinta, dole ta
kyale.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Babban abin godiya ma shine, da suka tausayawa
baWan Allah suka zo da kan su suka dauke
shi.
Shi yasa take ta yi wa Allah godiya, ba 6ata lkc ta
kira wayar Abba a kasuwa, ta shaida masa. Ba
karamin farin ciki yayi ba, domin rabon sa da
fara'a tin asubahin jiya. Sai kuwa yau da aka ce
su Hjy sun zo da kan su sun dauki Ameer.
Cikin gidan su Zarah su kai sallama yanzu. Inna
ta amsa. Ta leko daga dakin Malam Umar. Ah!
Nusaiba! Maraba. Fit Zarah ta fito daga dakin
Inna, baki har kunne,"Amarya! Antina." Zarah ta
matso suka rungume juna." Kin dawo ko amarya?
Ta daga ta dube ta,"Haba Antina, zo mu je daga
cikin in gan ki."Ta kama hannunta suka shige
daki. Inna ta ce,"Ke Hajiya shigo nan, kafin su
gama ganawar. Ina fatan dai na dawo mata da
amaryarta ne, mu huta." Bata ce komai ba, suka
shige, tana 'yar dariya.
Nusaiba ta dubi Zarah,"Me yasa haka Antina? Bai
kamata ki yi wa yayanki haka ba." Ta ce,"Ni kuwa
a waje na hakan ya kamata, domin ciwon 'Ya
mace, duk na 'Ya mace ne. Na kuma shaku dake
amarya tafiyar ki za ki ta jefa ni cikin wani yanayi
na dacin rai."
Ta dafa kafadar ta, ta ce,"Kin fadi
gaskiya,"Antina, kuma na san ki ni nuna min
iyakar kaunar da ba duka mace za ta nuna wa
abokiyat zamanta wannan kaunar ba.
Allah ne ya kaddaro zan sami Ameer, amma ke
ce sila Antina.
Ban mancewa har ta kai ki ga rasa na ki cikin.
Ina so ki sani Naseer, yana da halayya masu
kyau, yana da kula tare da tsare hakki, ni ce
kawai da bai so yake nuna min banbanci.Bai
damu da ni ba, balle ya kula da hakkoki na. Kar
ki damu Antina, ba laifin yayanki ba ne. Allah ne
bai sa masa soyayyata ba, saboda haka na ke
rokon ki idan ya zo daukan ki, ki yarda ki bi shi,
domin ke ce rayuwar sa.
Ke yake so, da ya ke yake ra'ayin zaman aure.
Abin alfaharin ki ne a wannan zamanin da ki ka
sami miji kamar Naseer, mai tsayuwa akan
alkawarin soyayya. A karshe ina son ki sani, har
karshen rayuwata ba zan ta6a mancewa da ke ba
Antina. Hasalima dole wata rana Ameer wajen ki
zai dawo, kin ga har yanzu mu na tare ke nan.
Kin hakura ko?
Abinda ya fi ba Zarah mmk, shine ashe Nusaiba
na sane da abinda ya faru kafin Naseer ya shiga
dakin ta. Gaskiya Nusaiba mai hakuri ce, irin
wanda sai an sha bincike kafin a sami irin sa. Ta
zura mata ido cike da kwallan tausayi. Allah na
ganin bata son rabuwa da amaryar ta.
Nusaiba ta kamo hannun ta, ta dora bisa kan
ta,"Ki yi min Alkawarin Antina, a yau za ki koma
dakin ki, ba gobe ba, kin ji? Ta goce da kuka,
suka rungume juna, haka wahayen ya kubce wa
Nusaiba,"Za ki koma ko? Ta dago ta goge kwalla
ta ce,"Zan koma Amarya, amma kema ina rokon
ki idan a an dai-daita da su Abba, don Allah kar
ki kafe ki ce ba za ki dawo ba.Ta yi dan
murmushi, ta ce,"Shi ke nan, bari mu zo mu tafi,
sai mun yi waya, shi kenan na ji, alkawarin za ki
min kamar yadda na yi miki." Ta yi dan jim, kafin
ta ce,"Ai ba laifi na bane Antina, ke ma ba za ki
yarda in zauna inda ba'a so na ba."
Ta kada
kai.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Da ke nan amarya, amma yanzu ina mai tabbatar
miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya min da
bakin sa ba, ni na yi imanin yana son ki, ba ki ga
yadda ya fita hayayyacin sa ba, lkcn da lalura ta
kama ki kuma ya kula da ke yadda
yakamata.
Ta ce,"Anitina ki na so ki gyara yayanki ne kawai,
amma ni na san tausayine irin na musulunci. Kin
san musulmi mai imani ya kan tausayawa dan-
uwansa a lkcn daya shiga wani hali.
A bar maganar nan Antina, ki yi min addu'ar
Allah ya zaba min abinda ya fi zama
alkhairi."
Ta numfasa, hannun ta bisa kafadar ta,"Zan miki
amarya. Allah yasa alkhairin a gidan yayanmu
yake."
Ta mike tana dan murmushi, ta fito ba tare da ta
ce komai ba, sbd bata son maimaita zancan.
Dakin da su Ummi suke, suka yi sallama. Inna na
rike da Ameer.
Zarah ta nufi gun sa, ta dauka, Ummi ta ce,"Zo
nan. Ta wuce wajen ta da Bebi a hannun ta, ta
tsugunna gefenta, ta dafa kafadar ta, ta ce,"
Zarah ba'a wasa da aure, hkr za ki yi ki koma
dakin ki kinji?Kan ta sunkuye tana dan ta6a
kuncin Ameer, ta amsa da kai, sannan ta
ce,"Wallahi Ummi Naseer ya gane kuskuren sa,
tun jiya yake kuka, yana bin mutane ya samu aje
masa biko. Abban sa ne ke fushi da shi, ya ki
bada hadin kai.
Don Allah Ummi, ku yafe masa ku bar amarya ta
dawo."
Ta ce,"Babu abinda Innar ki bata fada ba yanzu,
amma Naseer ya riga ya rushe katangarsa.
Alhj na da saukin kai, sai dai idan ka ta6i shi,
nan ne za ka gane ma yana da zafi.
Saboda haka ku taya mu addu'a. Allah yayi masa
zabi." Zarah ta yi shiru idunwanta suka kawo
kwalla. Ummi ta mike, ta ce,"Allah yasa mu
gana." Duk suka tashi suna fadin Amin.
Har mota suka rako su, sannan Zarah ta mikawa
Ummi yaron. Ta dubi Nusaiba, kowacce hawaye
ya zo mata, suka rungume juna. Da sauri Nusaiba
ta shige mota, haka ita ma Zarah ta ruga cikin
gida, bata son ganin tafiyar Nusaiba.
Hawayen ta suka yawaita, tana sharewa, wasu na
sauka. Direba ya damki hanya. Nusaiba ta yi
shiru cikin mota, ta sak'a wannan, ta kwance
wancan a game da maganganun Zarah. Tabbas
su Abba sun gaya mata Naseer yayi dawainiya da
ita sosai a cikin kwanakin nan 50 da ta samu
kanta a wani yanayi.Sai dai babu wanda zai
tantace me Naseer ke nufi cikin ransa? Ko ita ma
Zarah hasashe ta yi, domin da bakinta ta ce bai
fito fili ya gaya mata ba.
A cikin tunanin ne ta ji Ummi na fadin,"Ke ba shi
nono ya sha, ya
farka."------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Ta dube su firgigi. Ummi na masa mika tana
cewa ka sha barci ko? Nusaiba ta mika ruwa aka
ba shi, sannan ta karbe shi, ta mika masa nono
ya kama yana sha.
Nan da nan so da kaunar sa suka kara shiga
zuciyar ta har bata san lkcn da fa kura masa ido
ba.
Karo na farko da ta tantance kamanin
danta.
Tamkar Ameer na farko. Haka kuma hoton
Naseer take gani zahiri bisa cinyoyinta. Tsigar
jikinta ta tashi yar!
Saboda kyan surar yaron nan, musamman daya
buda ido tar!
Yana dube-duben sa.
Ya sha sosai. Ta juya shi daya gefen, nan ma ya
sha mai isar sa. Bai koma barci ba. Ummi ta
karbe shi, ta ci gaba da renon mai gida.
Jimawa kadan Kausar ta kira wayar Ummi, ta
mika wa Nusaiba ta ce,"Ungo Kausar ce." Ta
kar6a da saurinta, ta danna O.K."
"Hello."
Ta ce,"Hello Nusaiba ya karfin jiki?
Alhamdulillahi."
Ta ce,"Ya maganar Bebi ne? kin san Allah jiya ban
yi barci ba." Ta ce,"Bisa hanyar komawa gida
muke yanzu, mun je an dauko shi.Ta nisa ta
ce,"Better. Ai ni ba zan iya ba, ka aje a jariri, ai
ka cuce shi.
Shi me ya sani? Ta yi dan murmushi,"Kausar
kenan."
Ta ce,"Tare ku ke da Ummi ko? Bari in yi shiru,
idan kin kebe, kya kira ni. Ku sauka lafiya." Ta ce
amin. Ta kashe waya.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sun iso gida 2 rana. Alhj na falon kasa. Suna
isowa Ameer yasa a kafada ya haye sama, yana
fadin "Ku hayo sama in gan ku."
Suka haye suka bar Direba na shigo da kaya.
Mariya na taya shi. Bayan sun natsa a
zaune.
Alhj ya dube su ya ce,"Bayan tafiyar ku. Yakubu
ya zo min da maganar Naseeer, haka shima
M.Balarabe ya kira ni a waya, kodayake yana min
godiya ne akan dauko Ameer da aka yi, har ya ce
zai zo musamman yayi min godiya.
Nace ya bar shi kawai, ta wayar ma ya wadatar,
na kuma ji dadi. To koma dai menene, ban son
mutane su dame ni akan maganar nan.
Lokacin da zan ba Naseer 'ya ta ban yi shawara
da kowa ba.
Shi yasa ban son kowa ya sanya min baki, duk
hukuncin da na yanke. Na riga na yanke shi.
Saboda haka na kira wayar Fatima, na gaya mata
za kikoma Jordan, ni zan kar6ar miki takardarki ki
a wajen Naseer.
Ina fatan hakan yayi dai-dai.
Idan kuma akwai gyara ina jin ku?
Ummi ta ce,"Zabin Nusaiba ne, me ki ka gani? Ta
ce,"Hakan ya ma fi Abba na.
Hankalina zai fi kwanciya."
Ya ce,"To shi kenan.
Insha Allahu nan da kwana 3 za ki bar kasar
nan.
Allah ya kawo miki mai son ki, ki aura."
Ummi ta ce,"Amin."Sun jima suna hira nan, kafin
Nusaiba ta dawo dakinta, duk bata da kuzari a
jikinta, ita kanta bata san dalilin ba. Ta dan
kwanta don ta huta. Sai ga Ummi da Ameer ya
sake tashi barci.
Ta kar6e shi. Ummi ta fice.
Bayan ya gama sha tashinfidar da shi, ita ma ta
kwanta tana fuskartar shi. Rike yatsun sa ta yi
tana dan kada su, tana murmushin jin dadi. Sai
da ta ci abincin rana, sannan ta kira Kausar suka
kebe. Ita ma Kausar din ta goyi bayan Alhj akan
komawar Nusaiba Jordan, domin a ganin ta zatafi
samun
nutsuwa.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Al'amarin Naseer kuwa, bayan ya baro wajen
Yakubu, don jin yadda suka yi da Alhj, ransa 6ace
ya isa gidan su Zarah.
An riga anyi sallar la'asar. Yana shiga Inna ta yi
masa albishir da cewa su Nusaiba sun zo, sun
dauki Ameer. Take nan yayi wa Ubangiji sujada,
yayi godiya gare shi, sbd tsabar tausayin da
Ameer ke ba shi.
Nan da nan wani yanki na 6acin ran sa ya goge.
Sai da ya natsa. Inna ta sake fadin,"Sannan su zo
nan sun rarrashi Zarah, ta ce za ta koma, nan
ma kai take jira, dama kuma ko ba ka zo ba, ni
zan maida ta anjima." Ya numfasa, kaunar
Nusaiba ta k'ara shigarsa.
Yarinya mai hankali, haka kawai ya tsaneta. Ko
me yasa? Ya karkada kai ya ce,"Inna na gode.
Ina Zaran take? Ta zo mu tafi." Ta ce,"Tana nan a
ciki tana jin ka." Ya mike daga inda yake zaune,
ya shiga dakin. Tana zaune bisa kujera, jakarta
na aje gefe.
Ya tsaya kan ta ya ce,"Sai na miki dukan
musulunci tukuna, bari ki gani." Ya nad'e gefen
rigar sa, ya tsula mata." Ni ki ke ba wuya ko? Ta
6alla masa harara. Ya mammare kuncinta.
Idanuwanta suka kawo kwalla, sbd Nusaiba da ta
fado mata rai.
Ya tsugunna ya kama kunnuwan sa 2, ,"Na tuba."
Ya zura mata ido, tana share kwalla," In dai
amarya ce, ki kwantar da hankalin ki. Insha Allah
za ta dawo. Taso mu tafi." Bata tanka masa ba,
ta mike tana ci gaba da share fuska, ya dauki
jakar tayo waje, ya biyo ta.
Inna tana zaune, suka sallame ta, ta k'ara jajja
masu kunni, suka tafi.
Ko cikn mota ta k'i magana, ya dubeta, yayi d'an
murmushi,"Zarah manya,
yanzu ke ma ko tausayina ba kya ji, ina ku ke so
in sa raina?
Ta yamutsa fuska, a karo na farko, ta ce da
shi.
Oho?
Ai dama wanda bai ji bari bari ba, zai ji hoho!
In banda son kai ma, wa ka ke zaton zai tausaya
maka?Ya ce,"Ke mana sanyin raina. Ina ganin ai
saboda ke hakan ta kasance, sbd sonki kadai na
aje wa zuciya ta. Bai kamata ki juya min baya ba,
idan duka duniya sun dora min laifi.
Kalaman sa suka sa jikinta yayi sanyi, ta yi dan
shiru kafin ta ce,"Na san haka yayana, amma
lokacin da kowa ke gaya maka gaskiya, bai dace
ka ki daukar maganar na gaba da kai ba.
Yanzu ina amfanin abinda ya faru? Ya kamo
hannunta ya ce,"Wallahi babu, ban ta6a gane ni
ba ni da wayau ba, sai wannan karon Zarah. Abin
kamar almara na ke ganin sa."
Ta ce,"To yanzu menene abin yi? Ya ce,"Gaskiya
ban sani ba, domin Yakubu ya je, amma Alhj ya
ce mai kama da ni ma bai son gani, balle ya ji
wata magana akan bikon Nusaiba.
A karshe ya ce masa ya riga ya soke ni a rayuwar
sa.
Kin ji bayanin Alhj, sbd haka ni ban da wata
dabara."
Ta yi tagumi, kafin ta ce,"Tabd'i!
Kai yanzu in tambaye ka tsakanin da Allah, ka na
son amarya ta dawo? Ya dube ta ya ce,"D'ari
bisa d'ari na zuciyata ke kaunar Nusaiba ta
dawo, sbd ta yi min abinda ba zan ta6a mancewa
da ita ba a rayuwa."
Ta ce,"To ka gwada wannan dabarar ka gani. Ka
ajiye wani tura mutante wajen sa, ka tafi da kan
ka, ka ce masa, sai ka ga abinda ya ture wa buzu
nadi.!Duk wata bak'ar magana da wulak'anci, ka
jure shi, da kansa zai hakura, yana ji, yana gani
zai sakar maka 'yar."
Yayi d'an murmushi,"Zarah ke nan, bai saurari
manya ba ma, sai ni uban laifi? To zan gwada.
Amma ni kunya ma na ke ji mu hada ido da shi."
Lallai ba sokake ta dawo ba, kunya ai murje ta
ake yi." An gama Zarah,"Allah yasa amarya ta
dawo, ko don in huta da ciwon kai."
Ta 6allo masa harara, ya dube ta yayi
murmushi,"Ai kin ga na dan sami sauki, ko
hararar na rinka sha ta isheni jin dadi." Ta d'an
buge shi a kafada,"Allah za ka sani yayana."
Ya take birki a kofar gida, ta dauko jaka a kujerar
baya, ta fito ta riga shiga gida. A falon Umma ya
isketa.
Umma na mata fada. Ya zauna gefe ya
ce,"Umma sun zo sun kar6i Ameer ko?
Cikin rashin kulawa ta ce,"Sun zo."
Ya ce,"An gode ma su."
Ta yi biris da shi ta ci gaba da mgnr ta da Zarah.
Jimawa kadan ta koma sasan su, ta yi share-
share da goge-goge.
Har dakin Nusaiba ta gyara shi, ta goge zuciyarta
na saka mata lallai amarya za ta dawo da zarar
Naseer ya je da kan shi.
Kwana 3 kenan Naseer ya kasa zuwa Kaduna, sbd
kunya da jin nauyin Alhj. Yau kan Zarah har kuka
tayi masa, tana hada shi da Allah da Manzon
sa.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Yayi shiri tsaf!
Ya biya ya dauki Sageer suka danki hanya. Gida
suka fara zuwa. Mai gadi ya ce ma su babu kowa
cikin gidan, duk sun yi tafiya.Daga can ofis suka
nufa, sakataransa ya gaya masa Alhj ya tafi
Abuja.
Kai abinda babu sa'a. Haka suka dawo jiki babu
kwari tare da mamakin ina za su je kuma gaba
dayan su har da Nusaiba?
Koda suka dawo irin tambayar da Zarah ta rink'a
yi kenan.
Har ta k"arawa Naseer haushi ya ce,"Wai ina zan
sani ne Zarah da ki ka dame ni da tambayar
nan?
Haba!
Yayi tsaki, ya tashi ya bar mata gidan, don sai su
yi
fada.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 10 na safiya su Alh. Basheer na filin jirgin.
An gama bincike, an tantance Nusaiba da Ameer
tare da kayayyakin ta. Suka yi sallma da su
Ummi, ta wuce tana hawaye sabeda Ameer bisa
kafadarta, hannunta daya yana kan Beby. Sai dai
jirgin da za su shiga, sai sun dan jira shi, ya
gama hutawa.
Kamar yadda aka bada sanarwa.
Duk fasinjojin da ake tantance su, na zaune falon,
kafin a ba su umurnin shiga jirgi. Nusaiba ta zo
ta zauna kusa da wata mata.
Ita ma rungume take da Bebi cikin shawul, ga
wata yarinya a tsaye gaban ta, za ta kai shekaru
4.
Tana zama, ba ta yi aune ba, ta ga yarinyar nan
a gabanta, tana ta6a Ameer,"Bebi! Mamanta ta
juyo tana murmushi ta ce,"Husna ba kya ji ko?
Ba na ce ki tsaya waje daya ba? Ta ce," Umma
kin ga Bebi mai kyau? Zo ki gan shi."
Suka fara dariya.
Nusaiba ta ce,"In ba ki shi ne ku hada da na ku?
Ta ce,"Eh.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Ya sunan shi? Ta ce,"Ameer, ke ya sunan ku? Ta
ce,"Adnan.
Mamanta ta ce,"Oh ni, kin ji dadin halinki
Husna."
Ko a jikin ta, sai k'ara kwanciya take jikin
Nusaiba, tana wasa da kuncin
Ameer.------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Tun daga nan hira ta goce tsakanin Maman
Husna da Nusaiba.
Kamar minti 15, aka sanarwa fasinjoji. Su wuce
su shiga jirgi.
Tare suka sa6a yara suka wuce, ita fa Husna bata
yarda ba, son Ameer take yi, don haka Nusaiba
ta kamawa jaka tana bin ta da gudu.(First class)
dukkan su za su zauna, sbd haka ga kujerar
Nusaiba, ga ta su. Adnan da Manan sa. Su dai ba
su yi sukuni ba. Sai da barci ya kwashe Husna.
Sun sauka lafiya, ga 'yan tarbar 'yan uwan su
nan fululu kowa na jira. Nusaiba ta dudduba,
bata hango Antinan ba, haka Maman Husna ke
fadin,"Husna kin ga Abbanki bai zo ba ko?
Tana rufe baki ta yana kira,"Husna! Ta kwace
hannun ta, ta bi 6angaran da ta hango shi."
Abba!
Karo na farko da Nusaiba ta dubi Abban Husna,
sam bata gaskanta idanuwan ta ba. Ta kara
duban sa da kyau, babu ko shakkar Ibrahim
ne.
Jikin ta duk yayi la'asar saboda al'ajabin sake
haduwar ta da Ibrahim, wanda tuni ta mance da
shi a duniya. Suna tafe Maman Husna na
fadin,"Sai yaushe ke nan?
Ta ce,"Ai ina hada layi na, za ki ji kira na. Ai ba
zan yi wasa da lambar da ki ka ba ni ba, dole ne
in kira Husna."
Suka yi dariya. Nusaiba yanke tabi wani
6angare,"Bari in jira su Antina a nan. Ta ce,"Ah!
Ba za ki sallama da Husnar ta ki ba." Ta ce kyale
ta, ta ga Abban ta, ta mance da ni." To shi
kenan, sai na ji ki." Ta wuce inda su Husna ke
tsaye da Abban ta, duk da cukuikuye shi, ta hana
shi sukuni.
Babban yaron dake tare da shi, ya rugo ya
rungume Maman su, shi ma zai kai shekara 6 ko
5 da rabi. Nusaiba na tsaye duk ta kosa Antinta
su zo.......Ta bar wajen. Don bata son Ibrahim ya
gan ta, kawai ji tayi Husna na rikota tana
fadin,"Zo ka gan shi Abba, Bebi mai kyau."
Gabanta ya fadi, ta waigo cikin tsarguwa, suna
hada ido da Abban Husna ya ji kamar zai fadi,
sbd faduwar gaba. Bai san lkcn da yayi zuru, ya
zuba mata ido ba.
Ta shiga dan yake, tana wa Husna magana,"Ke
wai ba mun yi sallama tun a jirgi ba?
Tsayuwayar Maman Husna wajen yasa Ibrahim ya
dawo duniyar daya tafi, yayin da Husna ke
fadin,"Abba na zai ga Bebi mai kyau.
Ka gan shi? Suka fara dariya, ya kar6e shi ya dan
daga sama ya ce,"Good day handsome Bebi!
Yayin da Nusaiba ta juya tana tambyara sunan
yayan Husna, ya ce,"Imran." Ta
ce,"Uhnmm..............Sunanka da dadi." Husna ta
ce,"Ni ma sunana da dadi. Ta kama habarta ta
ce,"Sosai ma, ke mai babban suna ma ba'a fadi,
shi yaya ake kiran ki Husna."
Dadi ya kamata har da yi wa Imran gwalo.
Ibrahin ya numfasa, ya dubi matar sa ya
ce,"Gaskiya wannan haduwa tana da ban mmk.
Ai dole ayi dalla-dalla. Wannan ita ce,"Nusaiban
da na ta6a ba ki labari. Nusaiba ga Madan din
na Sakina." Mamaki ya kama Maman Husna, take
nan kishi ya kulle ta. Ta dan daure fuskata ta
ce,"Ka ce min wacce ta kusan zarar min da
kai.
Nusaiba ma ta gyara fuska, ta ce,"Ki bar
maganar nan Maman Husna ta riga ta wuce." Ya
ce,"Sai zumunci ko? Yana da kyau, ina fatan kin
bata adires, kafin ta koma, za ta kawo mana
Ziyara."Sakina ta gyada kai tana yamutse
fuska,."Na dai bata lambar waya."
"Mts, ina ganin ya kamata mu wuce Abban
Husna, na fara gajiya wallahi."
Ya ce ,"Tunda ba'a zo daukan ki ba, why not ba
za ki bi mu, mu sauke ki gida ba? Sakina ta
kauda kai yayin da Nusaiba ke 'yar dariya, tana
fadin,"Ku bar shi Allah na gode. Ai na san za su
zo."
Ta mika hannu ta kar6i Ameer a hannun sa.
Ya maida hannaye aljihu, ya numfasa, amma bai
iya cewa komai ba.
Ta shashshafa kan su Husna ta ce,"Sai anjima ko
Husna!? "Bye-bye Bebi, sai ka zo gidan mu." Suka
yi sallama da Sakina, ba wata walwala a fuskarta,
ganin haka Ibrahim yayi gaba rike da hannayen
yaran sa.
Sakinta ta bi bayan su cike da kishin babu gaira
babu dalili.
Nusaiba na nan tsaye, duk takaicin al'amarin ya
dameta ta, kamar minti 5 da wucewar su.
Antinta ta iso,"Allah sarki Nusaiba, sorry,"Wallahi
sharrin mota ne, cak ta tsaya mana a titi da kyar
Direba ya gyara."
Yaranta mata duga guda 4, suka yayyame ta,
kowa son ya dauki Bebi yake yi.
Babu 6ata lkc. Direba ya kwashe kaya suka
rankya.
Tunda daga mota, har gida Antin Jordan ke
balbala tsiya akan abinda ya faru.
Dakin ta daban, aka ware mata ita da Bebin ta,
bayan an gama duk kayaniyar ganin juna har da
maigidan ya tofa na sa albarkacin bakin sa.
Sai dai nasihohi yayi mata akan ta aje hankalinta
waje daya, kar ta sa wa ranta damuwa.Daki ta
koma ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallolinta.
Gefen gado ta zauna tana tanunanin yanayin da
suka hadu da Sakina, fara'a kamar gonar
auduga, amma tashi guda ta sauya fuska, saboda
mijinta ya nuna ya santa.
Ta yi dan murmushi, ta ce,"Allah sarki Antina,
alkhairin Allah ya kai miki."
Ta sa hannu ta jawo jakar Bebi, ta daukko lambar
da Sakinta ta bata a rubuce, ta sa hannu ta
yayyaga, tana fadi a ranta,"Sa ran ki a inuwa
Maman Husna, kullum ni da mijinki haduwar
[Aiport] ce, rabuwar (Airport)." Ta matse a
hannun ta, ta wuce bayi ta watsa (Dosbin).
-----------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Washe gari da wuri Naseer ya nufi Kaduna. Shi
kadai kuma ya tafi, wannan karon zuciyar sa ta
bushe, matar sa kawai yake son ta dawo.
Shi yasa ya kwashe duk wani tunanin dake ran sa
a game dake ran sa a game da tinkarar Alhj.
Yayi fakin, ya fito kai tsaye falon yayi
sallama.
Mariya dake goge-goge, ta amsa sannan, ta
durk'usa ta gaishe shi ya ce,"Hau sama ki kira
min Ummi." Ta ce,"Tana ma kicin, bari na kira
ta."
Ya zauna Mariya ta wuce. Jin kadan ta dawo ta
ce,"Ga ta nan zuwa." Ya share minti 5 nan, kafin
Ummi ta iso falon.
Ya mike kai sunkuye ya ce,"Sannu Ummi." Bata
tanka masa ba, ta wuce ta haye sama. Yayi tsaye
nan kirjin sa na harbawa.Bai sake ganin kowa ba,
wucewar minti 30 har ya gaji da tsayuwa ya
koma ya zauna.
Can Alh.Basheer ya tinkaro falon.
Ummi na rike da jakar sa suna maganganun
su.
Naseer ya kuma mikewa yayi tsaye irin na marasa
gaskiya. Ko inda yake Alhj bai kalla ba, jakarsa ya
karba. Ummi ta ce," A dawo lafiya." Ya ce,"Amin."
Ya fice.
Ummi na ta wuce kicin, ta ci gaba da hidimomin
ta.
Naseer yayi kamar ya nutse a kasa, jiki babu
kwari ya biyo bayan Alhj, amma kafin ya
karaso.
Alhj ya shiga mota. Deriba ya tayar. Haka ya
tsaya kamar dolo, yana kallo aka bude get.
Motar ta fice. Ya wuce ya shiga ta sa, ya bi bayan
sa.
Ofis ya ga sun nufa, shi ma ya bi su. Yana zuwa
zai wuce sakatare, ya ce,"Alhj ya ce ka dan jira
shi a nan tukuna."
Ya ce,"To." Ya zauna.
Shi kansa sakataran dauke da mamaki yake,
domin bai ta6a yi wa Naseer iso ba wajen
Alhj.
Yana nan zaune Alhjn ya kira waya, ya bada
izinin Naseer ya shigo.
Ya mike ya tura kofa, ya sjiga Alhjn na ta aikin sa
bisa (Laptop), bai ko kalle shi ba. Ya duka ya
gaishe shi, ya amsa a dakile.
Yayi shiru, haka shima Alhjn bai dube shi
ba.
A haka ya daure ya fara magana,"Abba, na san
babu abinda zan gaya maka wanda zai faranta
maka rai, amma duk da haka ina mai gurfanar
da kai na gare ka a matsayin mai laifi.Ka yanke
min duk hukuncin da ya dace dani, wanda zai
sanyaya maka rai, har ka huce ka ban Nusaiba,
in koma da ita.
Da sunan Allah na ke wannan rokon Abba, ka
taimake ni don son Manzon mu.
Yayi shiru. Shi kuwa Alhj sai a aikinsa yake
yi.
Kamar ba zai tanka ba, wucewar mintoci, kafin ya
ce,"Ka na iya tafiya, zan neme ka."
Ya durk'usa guiwa 2 ya ce,"To shi kenan, na gode
Abba.
Kuma ina k'ara neman afuwa akan kuskuran da
na yi.
Ka gafarce ni Abba."
Ya ce,"Ka je zan neme ka na ce."
Ya mike yana fadin,"Na gode, a tashi lafiya."
Bai amsa masa ba ya fice.
Alhaji ya sauke numfashi, ya dafe goshinsa, bai
san dalilin da yasa son Naseer yayi masa yawa a
zuciya ba, duk lokacin da ya gan shi kaunar sa
karuwa take.
Dole ce tasa ya yanke hukuncin nan, saboda ya
kar6o wa Nusaiba 'yancinta.
Ofishin su Yakubu Naseer ya nufa, can bargar
dawakai, amma wurin na kulle babu kowa, sai
mai ba dawaki abinci.
Bai tsaya 6ata lkc ba, ya damko hanyar dawowa
gida, yana tafe wasi-wasi ne fal cikin ransa, wata
zuciyar na saka masa zai yi wuya Nusiba ta dawo,
wata kuma na tabbatar masa za ta dawo ne,
tunda ya ce zai neme ka.,
Ai kai d'an gaban goshin sa ne. Daya iso shago,
ya tsaya wajen Sageer.
Bai dawo gida ba, sai karfe 1,abu na farko sada
fara gani, shine babu motar Nusaiba dake lullu6e
a wajen.
Gabnsa ya fadi, ya fito da sauri ya fada cikin
gida.
Zarah na zaune a barndar sasan su, tana ta
faman goge kwalla."Menene wai?
Ban ga motar Nusaiba ba a waje!
Murya na rawa ta ce,"An kwashe kayanta, ka ga
shi kenan ta faru, ta k'are, tuntuni na ke gaya
maka, ka je ka k'i................
Ya katse ta da masifa,"Don Allah isa haka, kar ki
kara 6ata min rai!
Ko yanzu daga ina na ke? Ya ce zai neme ni? Ai
shi kenan tunda baya son ta dawo!
Ya nemi waje nan ya zauna dabas, ya cire hula
zufa ta keto masa.
Zara bata iya kara komai ba, ta ma tashi ta bar
wajen.
Umma na jin sa, kanzil ba ta ce da shi ba.
Bayan sallar la'asar, yana kwance dakin sa ya
rasa abinda ke masa dadi, kamar an kwaso son
Nusaiba an kara cusa masa cikin zuciya, sannan a
'yan kwananin nan da bai ga Ameer ba, duk
kewarsa ta ishe shi.Gaba daya abubuwan sun
dagule masa, domin ya sani ba za su ta6a
daidaitawa da Abbansa ba, muddin Nusaiba bata
dawo cikin gidan nan. Ya runtse ido, ya dafe kai
kamar ya kwarma ihu. Zumbur ya mike ya
kwashi makullai, ya fice ko Zarah bata sani ba,
ya fada mota. Ya sake yi wa Kaduna tsinke. Yana
zuwa. Sakatare ya ce Alhj ya tashi.
Yana kokarin fitowa daga get. Motar Yakubu na
shigowa. Suka tsaya kowa ya fito gaba dayan su,
babu mai walwala a fuska. Yakubu ya fara
magana,"Ko ka ji abinda ya faru?" Ya ce,"Na
me ? Ya ce,"Na rufe (Dabai Riders) mana.
Alhj ya rufe kulob, yadda yake gaya min ma ya
sa dawakan a kasuwa har an samu masu siya."
Salati Naseer ya fara yi, kafin ya ce,"Saboda me?
Ya numfasa ya ce,"Wallahi ban sani ba, amma
tun faruwar wannan al'amarin na ku hankalin
Alhj a tashe yake. Iyaka kokari na, akan ya sauya
shawara, amma ya ce ra'ayin sa ne.."
Naseer ya k'ara tarus! Idanuwan sa suka kawo
kwalla, ya ce,"Yakubu ban san yadda zan yi ba,
dazun nan na zo na yi magiya gun sa, ya ce in je
zai neme ni, wai ina zuwa gida. Na tarar an
kwashe kayan Nusaiba kaf. Lambarta ba'a
samu.
Kuma ni na san rufe kulob din nan, duk baya
rasa nasaba da matsalar nan, wata kila yana
ganin ta dalililin Polo ya hadu da ni.Ban san abin
yi ba Yakubu? Ya ce,"Gaskiya ne. Magana kan ta
gama lalacewa. Ka san komai Alhj zai iya yi
saboda Nusaiba, kar ka manta ita ce 'yar sa
kawai. Sannan duk abinda ya faru, kai ka jawa
kanka, domin ba karamar asara ka yi ba. Sai ka
yi addu'a Allah ya sa hakan shine alkhairi. Gida
ka nufa?
Ya kada kai,"Ina nan sai na ga abinda ya turewa
buzu nad'i. Yakubu ya ce,"To sai ka
dawo,"Goodluck." Na gode." Naseer ya fice, shi
kuma ya karaso wajen sakatare, ya aje abubuwan
daya zo da su.
Gidan Naseer ya nufa. Alhj na tare da baki. Yayi
sallama ta gaishe su. Alhj ya bi shi da kallo. Ya ce
"Dama na zo ganin ka ne, bari in jira ka." Ganin
mutane a wajen yasa ya amsa." To ina
zuwa."Naseer ya fita, motar sa ya zauna yayi ta ji
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajinisa Yake3-04
Posted by ANaM Dorayi on 05:24 AM, 23-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Zan yafe maka komai, ya wuce har abada, amma
sai ka kawo min takardar Nusaiba."Kansa cikin
giuwa, ya girgiza kai, ya ce,"Ba zan iya ba Abba,
ka yi hkr." Ya ce,"Wannan ba hukunci na ba
ne.Nusaiba ce ta buk'ata ta kuma bar min
sallahu jiya kafin su wuce Jordan.." Ji yayi
numfashinsa ya shake gaba daya, yana neman
faduwa.
Ya kasa motsi, balle ya ce wani abu. Ya ci gaba
da cewa,"Na ba ka nan da jibi ka zomin da
takardar, daga nan zan maka bayanan wasu
abubuwa da suka kamata ka sani.
Ka na iya tafiya dare yana k'ar yi." Ya dago
idanuwa jajur! Ya ce,"Ummi ku taimake ni, ku ba
ni lambar ta mu yi magana, na san zata saurare
ni. Amma a raba auran a haka, abin babu
dadi.."Abba ya ba shi amsa,"Ban son dogon nace
Naseer, raina k'ara 6aci yake yi. Kwanciyar
hankalin na da kai shine ka kawo min takardar
Nusaiba. Yadda ba ka so, haka ita ma bata so,
shi kenan magana ta k'are babu lallai babu
tilas."
Ya sunkuyar da kai, yayi shiru. Ummi ta
ce,"Yakamata ka tafi, dare ya fara yi Naseer,
muna sauraronka."Yayi wawan ajiyar zuciya, ya
mike da kyar ya ce da su,"Sai da safe,gaba daya
suka amsa,"Allah ya kai mu, a gaida mutan
gidan."Bai k'ara komai ba, ya sakko a hankali ya
tafi.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Karfe 11 dare, ya shigo gida,. Zarah na zaune a
falo ta ci uban tagumi, ya turo kofar ya shigo." Ta
mike tsaye da sauri ta tarbe shi."
Yayana!
Kai kuwa ina ka shiga yau?
Bai tanka ba, ya wuce kujera ya zauna, ta bi shi
hannun kujerar ita ma ta zauna. Ganin yayi zuru-
zuru, yasa tausayinsa ya rufe ta.
Ta nunfasa ta ce,"Ina ka je yayana? Ya
ce,"Kaduna na koma." Ya aka yi to? Ya mayar
mata da abubuwan da Alhj ya ce,yayi shiru ta
rasa ta cewa. Ya kwanto da kan sa bisa
cinyoyinta, shi ma ya yi shirun Ta dafa kan sa ta
ce,"Kai yanzu me ka shawarta."Ya ce,"Na hukara
Zarah. Allah na gani na yi ikayar kokarina. Abinda
ya fi damuna maganganun da Alhj yayi. Ba
k'aramin dafa min jiki suka yi ba, sbd a zahiri
Alhj masoyina ne.Sai kin ga yadda ya cika hotuna
na a falonsa, kya rantse da Allah ni ne dan masu
gidan.
Ni dai na yi abin kunya, ban san ta yadda zan yi
in wanke kai na ba."
Ta ce,"Gaskiya ne, amma duk da haka ka tuntubi
su Umma ka ji ko za ta ce wani abu." Ya mike ya
wuce bayi, yayi wanka ya ji sanyi a jikin sa,
sannan ya kwanta.
Zarah na k'ara kwantar masa da hankali.
Da safe ya shiga wajen su Umma ya gaishe
su.
Abba bai amsa ba, ya tashi ya koma cikin
daki.
Daga can yana jin duk bayayin da yake wa
Umma.
Yana gamawa ta ce.
"To ne menene nawa a ciki? Duk abinda ka ga ya
dace, ka yi, tunda wannan 'ya ba ta mu bace,
k'arewa ma ka ce bata k'asar.
Ka ga da gaske Abbanta ya ke yi." Yayi dan jim
kafin ya mike, ya bar falon.
Umma ta bi shi da kallo, tausayin sa ya dan
kama ta, ta kada kai ta ce,"Kai ka jawo wa kan
ka."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sati 1 Naseer yayi yana sintiri Kaduna, wai ko ya
sanmi sauyin baki daga Alh.Basheer, amma sam
babu.
Yau daya je ma. Alhj cewa yayi yau ce rana ta
karshe daya ba shi, idan bai kawo takardar ba, to
kar ya sake zuwa gun sa, kuma duk abinda ya
biyo baya, kar ya ce yayi masa wulakanci.
Babu yadda zai yi, a daren ya rubuta takarda,
saki 1 ya sa a ambulan ya rufe.
Washe gari ya isa gida, ya sami Alhj yana shirin
fita.Bayan sun gaisa Alhj, na kallo irin ramar da
Naseer din yayi. Ummi ta zo suka gaisa. Yasa
hannun aljihu ya ciro ambulan, ya tsugunna ya
mika wa Alhj. Ya kar6a, ya buda, ya karanta, bai
ko karasa ba, ya rufe saboda irin lausasan
kalaman da ke cikin takardar.
Ya dube shi ya ce,"Magana ta kare Naseer, kuma
duniya da lahira na yafe maka abinda ka yi min.
Son ka a cikin jini na yake, na rantse da Allah ba
zan iya cire shi ba, saboda haka ka saki jikin ka,
kai da na ne.
Magana ta 2, ita ce,"Gida da motocin da na ba
ka, mallakin ka ne, ba na bukatar su. Abinda na
ke son ka da shi ne, ka dauki Zarah ku koma can
da zama.
Wannan umurni ne a matsayin na Babanka."Gaba
daya tsigar jikinsa suka tashi yar! Idanuwansa
suka kawo kwalla.
Ya zamo daga kujera ya ce,"Na gode Abba. Allah
ya saka da alkhairi."
Ya ce,"Koma ka zauna. Yanzu yaushe za ka
kammala karatun ka? Ya sunkuyar da kai, kunya
ta rufe shi, ya rasa me zai ce? Da kyar ya daure
ya ce,"Ai dama ban fara ba."
Da mamakinsa ya maimaita ,"Ba ka fara ba? To
da ka ce min ka na zuwa?
Ya sunkuyar da kai, kamar ya ratsa kujera ya
shige. Alhj yayi dan murmushi ya ce,"Allah da iko
yake, yanzu yaushe za ka fara? Kidimewa tasa ya
ce,"Gobe." Ummi ta ce,"Gobo kuwa? Ba dai gobe-
gobe ba, ai kuma sai an sake nema ko? Ko kuwa
ka na da "(Admission) ne a hannun ka?
Ya girgiza kai,"A'a.Duk sun lura a daburce yake,
saboda haka Alhj ya ce,"Shi ke nan, ka je ka yi
duk abinda ya kamata, idan ka sami ( Admission)
din ka kawo min." Ya ce,"To na gode Abba."
Ya kosa ya tashi saboda tsarguwa, zufa ce kawai
ke kwararo masa cikin riga.
Yana samu aka sallame shi, jikin sa na rawa yayi
godiya, ya fice.
Alhj ya dubi Ummi ya ce,"Kawai Allah ne ya dora
min son yaron nan, ba don haka ba, inda na ke
ma idan aka ce ya zo da kudi ba zai zo ba."
Ta ce,"Ya za'ayi, ga kuma zuri'a a tsakani, dole a
rage wani abin." Ya numfasa yana kada ambulan,
sannan ya mika mata,"Karanta ki ji bayanan dake
ciki." Ta kar6a ta karanta, ta yi dan murmushi ta
ce,"Allah sarki da alama ya saduda Alhj."
Ya ce,"Kyale ni da shi dai."
Ta ce,"Na kyale."
Kowa ya ji abinda Alhj yayi, sai ya sanya masa
albarka.
A hakikanin gaskiya Alh.Basheer mutum ne
wanda ba'a samun su a wannan zamanin, sai an
shekara ana bincike cikin mutanen kirkin da ake
wa zaton suna da halin mutan da can. Karshen
soyayya Alh.Basheer ya nuna wa, Naseer shi yasa
Naseer din ke k'ara nadama kan nadama, so da
kaunar Nusaiba ke k'ara dabaibaye
zuciyarsa.
Kewar ta ke jefa shi.
Nisan tunanin ta musamman lukutan daya samu
a asibiti yana jinyarta.Ya kan rink'a ganin kamar
wata sabuwar rayuwar soyayya ce suka yi a
tsakanin su, wacce yake mafarkin ci gaba da irin
ta.
Malam Balarabe kuwa kalaman godiya sun kare a
bakin sa.
Washe gari daya tafi Kaduna, ba tare da sanin
kowa ba, don nuna girmamawa ga Alh. Basheer.
Tabbas ya nuna halin girman, dole a jinjina masa.
Haka shi ma Alhjn ya roke shi akan ya daina
fushi da Naseer, tunda ya tuba, to ya kamata ya
karbi tuban sa, sbd fushin sa tamkar dafi ne a
gare shi.
Malam Balarabe ya amince, yayi farin ciki ya
kuma zubda kwallan bakin cikin rabuwar auran
Naseer da Nusaiba.
Ba 6angaran su Malam Balarabe kadai bakin cikin
rabuwan auran ya dama ba, ita kan ta uwar
gayyar, yau ta tsinci kanta cikin wani yanayin da
bata gane masa ba, a tun lokacin da sako ya zo
mata ta waya daga Nijeriya cewar ta fara iddar
ta.
Zaune take dirshan bisa gado, ta takure kanta,
tunanin yayi mata yawa.
Tana tambayar kan ta, ita kuma haka Allah ya
kaddaro mata? Mutuwar aure ita ce matsala ta
farko da ke ci mata tuwo a kwarya, a
rayuwarta.
Ta tsani, ace anyi aure ya mutu, sai ga shi yau ya
tabbata akan ta.
"Kaddara!
Ta fada a ranta hawaye, suka kubce.
Ta dawo tana zargin kan ta,"Watakila Naseer ya
so ya gaya mata wata magana lkcn da ta wayi
gari ta gan shi tare da ita asibitin, amma ta ki ba
shi dama.
Yi hakuri ki ba Bebinmu nono. Haba 'yar gidan
Abba."
Tabbas rarrashin ta yake yi, amma ta dauke kai,
ta nuna bata san abinda take yi ba.
Alhalin ta warke, hankalin ta ya dawo jikinta.
Da kenan amarya, amma, a yanzu ina mai
tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya
min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son
ki.
Ba ki ga yadda ya fita hayyacin sa ba.
Lokacin da lalura ta kama ki, kuma ya kula dake
yadda ya kamata!
Ta toshe kunnuwanta ta daga kai.
Idanuwanta tamau a rintse, hawaye suka ci gaba
da sauka.
Istaharar ta ta tabbata gaskiya.
Bata sami isashen barci ba, sbd a yanzu take
tunanin ya kamata ace ta ba Naseer dama shi da
ita sun yi magana.
Yanayin daya suka kwana ita da Naseer, domin a
ranar suka koma Hanwa. Yayi sintiri a sashin ta
iya yadda ya ishe shi, wanda a da bai ta6a shiga
cikinsa ba. Tun Zarah na taya shi sintirin, har ta
hakura ta sakar masa. Daga ranar ya daukar wa
kan sa alkawarin zama lafiya da kowa, zuwa
k'arshen rayuwarsa.
Idan ba shi gida, yana shagon dinki ne, daya
samu Abba ya fara amsa gaisuwar sa, kuma bin
sa yake sau da kafa.
Komai bai zartarwa sai abinda ya ce. Haka yake
bin Alhj, bai ketare umurinin sa. A haka aka
share watanin 2. Mamakin sa 1 shine. Alhj ya ki
dawo da wasan Polo, shi kuma yana jin nauyin yi
masa magana.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
A 'yan tsakanin ne. Fa'iza ta haihu da namiji
k'aton gaske mai kama da Babansa. Ranar suna,
ya rada masa Mohammad. Zarah gidan sunan ta
wuni duk da ta wayi gari baya jin dadi.
Tun daga ranar jikinta ya k'i yi mata dadi,
tsoro ya fara kamata, sbd fargaba daukan
ciki.
Lalurar ta ta fara bata tsoro.
Lalai kuwa, abinda take wa tsoron ne ya
samu.
Shi kan sa Naseer tausayi take ba shi, shi yasa
wannan karon murnar sa raggiya ce.
Zarah na tsakiyar laulayi, aka biya kudin
jarrabawar (External)
Naseer ya biya duka WAEC da NECO.
Daga nan Sageer ya shawarce shi daya fada
makarantun bada (Lesson), don ya k'ara wanke
masa kwakwalwa.
Babu musu, ya nema ya shiga guda 2, yana
zuwa.
Ranar da za'a kai Zarah daurin mahaifa, ranar ce
suke da jarabawar farko. Hankalin Naseer ba'a
kwance yake ba, babu yadda zai yi.
Haka nan ya hakura suka tafi tare da su.
Umma da Inna Sageer ya kai su a Jeep din
sa.
Shi ya tafi jarabawar sa da Civic.A saukake yayi
jarabawar sa, duk da ba shi cikin nutsuwa, babu
tambayar da ta gagare shi amsawa.
Yana tashi ya wuce asibiti abin sa, ya duba
Zaraha, sannan ya dawo shago yayi ayyukansa.
Can yake zama su ci su yi hira, zuwa karfe 9 ya
dawo gida.
Zaman sa shi kadai yana kara taso masa da
kewar Nusaiba, a lkc irin wannan can baya, duk
da ta san baya maraba da ita cikin dakin sa, ta
kan shigo har ta tambaye shi ko yana da bukatar
wani abu.
Shi yasa ya dauki filo ya nufi sashin ta cikin dakin
barcinta, ya jefa pilo bisa kafet ya kwanta.
Nan ya kasance wajen barcinsa, kodayaushe,
yana laluben inda zai ji motsinta.
Watannin 3 sakamakon jarabawarsa ta fito.
Allah da ikon sa gaba daya sakamakon Naseer
masu kyau ne.
Yayi matukar sa'a.
Allah ya kubutar da shi daga sharrin hukumar
jarabawa da yanzu abin yake neman zama
kasuwanci.
Ko ma ince ya zama din."
Magidanci na fama da kansa, duk da haka ya
dage da karma-karma ya biya zunzurutin kudi,
sai jarabawa ta fito, ace yaro bai ci ba, alhali da
kokarin sa da komai.
Sannan ya dage wajen neman taimakon
makarantun (Lesson), tunda daman makarantun
gwamnati sai a hankali.
Ba duka (Syllabus) ake (Covering) , ba, balle yaro
ya san makamar jarabawarsa.
Allah ya sawwake.
Ilimi ya zama wahala ga 'ya'yanmu talakawa.Shi
kam Naseer yayi sa'a kamar yadda Allah ya
halicce shi, shi mai sa'a ne a rayuwarsa.
Da rawar jikinsa ya kai wa Alh. Basheer takardun
ya gani.
Yayi murna kwarai, daga nan ya shiga neman
makaranta, don samun (Admission).
Sageer na taimaka masa.
Ba jimawa ba, ya sami Poly ta hannun Sageer
din, Babu kudin kirki a hannunsa a wannan 'yan
tsakanin, sbd zaman Zarah a asibiti.
Ya zauna yana tunanin yadda za'ayi.
Ba tare daya takurawa kowa ba.
Abin mamaki yana zuwa Kaduna, ya nuna wa
Alhj,("Admission) din, kamar yadda ya umurce
shi, cewar da ya samu ya kawo masa ya
gani.
Take nan ya ware dubu 50 ya ba shi, ya ce ya je
yayi hidimar makaranta.
Allah mai iko.
Tun daga ofid har ya dawo gida, godiya yake wa
Alhj cikin ransa.
Ya kawo wa Abbansa, suka sa albarka shi da
Umma, balle Zarah da take jin tausayin sa, sbd
hidimar da yake sha a asibiti, ga kuma makaranta
ta kunno kai.
Lallai Alhj ba karamin taimako yayi ma su
ba.
Ciki lafiya, ba ka lafiya, ya kama karatun sa a
(Poly Computer Science) yake karantawa, kamar
almara yake ganin abin.
Lokacin kuwa cikin Zarah ya shiga wata 7.
Zullumi ya ishi kowa, musamman ita mai dauke
da cikin.
Kusan kullun da ciwon mara take kwana.
Bata dai yin magana ne kawai.
Saboda ciwon ba wai ya tsananta ba ne.
Sati 2 da fara karatunsa, abinda ake gudun ya
faru.
Ta haifi da namiji.
Aka sanya shi a kwalba kwana 7. Ya ce ga garin
ku nan kuma shi ya ci sunan Alhaji, watau
Mohammad Basheeeeeeeeeeeeerrr
rrrr!!!!!.......
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Labarin haihuwar Zarah har Jordan, amma da
aka ce ya koma. Jikin Nusaiba yayi sanyi, ta dubi
Ameer yana ta rarrafen sa, yayi k'atob gasket,
dauki da nishi jajur, ga suma baka wulik! Kamar
kan Babansa.
Tausayin Antinta ya kama ta, ta yi tagumi ta ce a
ranta,"Allah sarki Antina." Ta numfasa, Ameer ya
rarrafo gun ta, ya dafa ta ya mike, ta sa hannun
ta dauke shi ta rungume.
Tabbas ta sani dole Naseer ya sa Ameer a
ransa.
Ta k'ara matse shi jikin ta, tunanin ta wai ace
Naseer ya tada k'ayar baya, dan sa yake so a ba
shi. Abinda ba zai samu ba kenan, yadda ta
shaku da Ameer.
Ai mai raba ta da shi, sai wanda ya bata shi. Ta
yi dai yi masu addu'ar Allah ya ba su mai
albarka."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
BAYAN SHEKARA DAYA
Shekara guda da rushe(DABAI RIBERS),sauran
kolub-kolub din wasannin polo sai kawo wa
Naseer takardun gayyata suke, suna neman ya
koma kungiyoyinsu.
Gayyata har da Ghana, Kamaru, Benin Republic,
da sauran kasashen makwafta, wadanda suka
san Naseer, suka kuma san irin rawar daya taka a
wasan tsern Polo.
Amma sam ya ki amsa kiransu, duk da ya san
dumbin alkhairin da zai samu a can. Sam-sam
zuciyarsa ta fita daga wasan Polo tunda Alh.
Basheer ya bar harkar.Hakan ya gaya wa Yakubu
ranar da ya same shi da wata takarda da ta zo ta
hannun sa daga Sakkwato. Magana ta kawo
magana, suna hira tsakanin Yakubun da
Alhj.
Shi kuma yake ba shi labari.
Saboda haka Alh.Basheer ya kira Naseer yayi
masa magana. Baya ketare umurinin Alhjn,
amma wannan karon Naseer kad'a kai yai ya
ce,"Abba karatuna ya fi min wannan wasan,
kuma ban jin zan iya wasa da wani (Polo club) a
halin yanzu.
Alhj ya bi shi da kallo, tsaf ya kasa ganeme yake
nufi.
Yayi dan murmushi ya ce,"Shi kenan tunda ka
kawo zancen karatu. Allah ya bada sa'a."Ya
ce"Amin. Alh.Basheer ya dade yana nazarin
maganganun Naseer kuma yana tausaya masa,
domin ya saba da Polo.
Yana sha'awarsa, bugu da k'ari wasan Polo A
JININSA YAKE.Abinda kuwa daka saba da shi zai yi
wuya ya fice maka a rai, sai dole. Alhjn bai yanke
hukunci ba, tukuna, amma yana nan yana nazari
a kai.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Al'amarin Nusaiba kuwa a birnin Jordan, ba yabo,
ba fallasa a yanayin jikinta. Ta kasa samun
natsuwa a ranta, saboda yawan zancen aure da
Antin Jordan ke yi mata, tunda Ameer yayi wayau
sosai, yana gudun sa ko'ina gwanin
sha'awa.
Kullum amsar ta ita ce bata da wani bazawari
tsayayye ko a Nijeriya, balle kuma a nan Jordan
da babu wanda ta sani kasancewar ba fita take yi
ba.Idan ba (Shopping) ba tare da yaran gidan da
Direba. Ta damu kwarai domin ba ta san dalilin
da yasa Antin ta damu da yin sabon aurenna
taba. Shekara 1 kacal da mutuwar auranta.
A yammacin yau (Shopping) din za su da yaran
gidan.
Kowace ta shirya cikin dogayen kaya kala daban-
daban.
Direba ya aje su katuwar (Super market) din da
suke saba zuwa.
Suka shige kowa, yayi na sa wuri, yana neman
abinda yake so.
Nusaiba na jaye da Ameer cikin kwandon
Shopping din ta saka shi, don kar ya rink'a bata
wahala, yana gudu, tana kamo shi.
Bata ko lura da mutumin dake tsaye 6angarn
kayan abincin yara ba, sai da ta ji yana
fad'in,"Ameer!
Haka ka yi girma?
Ta waigo da sauri ta dube shi.
Ibrahim ne ke wasa da habar Ameer.
Bai kalle ta ba, ya ci gaba da cewa,"Ka ba Husna
kewa, kullum maganar ka take."
Ameer washe baki yake yana dariya.
Ita kuwa Nusaiba jikinta rawa ya dauka, ta tsura
masa ido.
A hankali ya dago, ya dube ta yayi dan murmushi
ya ce,"Hajiya Nusaiba."
Ta yi yake, tana fadin a ranta, "Ibrahim ko maye
ne?Kafin ta ce ,"Ya ku ke? Ina su Husna da
Mamanta? Ya ce,"Lafiya lau suke.
Amma ba ki da kirki? Ta gyara fuska,"Da aka yi
me?
Shekara 1 ki na garin nan, ki kasa kawo mana
ziyara, ba ki yi alkawari ba.
Sakin ta ce min ta ba ki (Phone Number), amma
ba ki kira ba." Lambar ce ta 6ace. Ka gaida min
Husna."
Ta fadi tana tura keken (Shopping) tana ci gaba
da kiran yara,"Sumayya ina ku ke? Ku zo mu tafi!
Ya dan sauke numfashi, ya biyo ta a hankali.
Suka hadu da yaran a wata kwana,"Anti ba mu
gama ba,"Inji babbar cikin su Sumayyah.
Dai-dai Ibrahim na tsayuwa wajen.
Ta ce,"Gaskiya ba zan jira ku ba, gobe Direba ya
sake kawo ku." Yayi fit yasa masu baki,"Haba
Anti, bai kamata ba, ki kyale su su gama."
Duk suka bi shi da kallo.
Ya juya kan sa,"Ga Sumayyah ko? Ke fa? Ya nuna
mai bi mata, ta ce,"Khadija."
Ke fa? Ta ce,"Mahadiyya." Ya duka ya kamo 'yar
kamar ,"Ke fa? Ta ce,"Zainab." Ya runtse ido ya
ce"Wash! Uwa da magani. Sannu Husna.
Mahadiyya ta cafe,"Ba husna sunanta ba ZEE
AFLAN! Ta kai mata duka, suka kwashe mata da
dariya. Takaici ya ishi Nusaiba, ta tura keke ta yi
gaba.Ta bar shi yana rabon fada, wa ya radawa
uwa ta ZEE AFLAM? Lalai ba zai sha (Ice-cream)
ba yau."Mahadiyya ta ce,"Ba ni bace. Anti
Sumayyah ce."
Ya kada kai,"Ba ki kyauta ba.
To ku tsaya in tambaye ku, yaushe Anti Nusaiba
ta zo nan? Sumayya ta ce,"Ta dade, tun Ameer
na jariri." Baban Ameer yana nan garin ne? Ta
ce,"A'a yana Nijeriya." Wai ko ba za ku zo mu tafi
ba ne?
Yau na ga yara.
Nusaiba ta leko tana kiran su.
Sumayya ta wuce da saurarinta. Khadija ta biyo
bayanta. Ya kamo hannayen su. Zainab tana
tambayar sa,"Kai ya sunan ka? Ya dube ta ya
ce,"Suna na mai son Anti."
Suka kwashe da dariya,"Wannan suna, ban ta6a
jin irin sa ba."
Inji Mahadiyya,"Ya ce,"Ga shi yau kin ji. Ko a gida
aka tambaye ki, ki ce mai son Anti, sunana."
Ta ce,"To."
Ya debo kwalayen cakulet 2 da biskit 2, ya mika
ma su. Suka yi godiya.
Wajen biyan kudi, suka same su, duk cin
maganin Nusaiba sai da Ibrahim ya biya
kudin.
Suka shiga mota, yana tsaye yana tunanin ta
yaya zai binciko gaskiyar lamarin? Sun bada baya
kadan, ya manta bai ma tambayi inda gidan su
yake ba.
Ya zabura da sauri, ya fada motar shi, ya bi
bayan su.
A haka a hankali yake bin su.
Nusaiba na jin Mahadiyya na tambayar su,"Kun
san sunan mutumin nan? "Wai mai son
Anti."
Gabanta ya fadi, ta zaro ido.
Sumayya ta ce,"Ah lallai ma wannan.
Antin Nusaiba, wai kin san shi ne? Ta ce,"Ina fa
na shan shi, ku da ganin mutum kun tsaya ku na
surutu da shi." Ta ce,"Anti ba ki san shi ba, shine
ya san sunan ki da na Ameer? Ta ce,"To saura in
ji maganar a bakin Anti, sai na murje bakin
yarinya." Sumayayya ta kwa6e fuska, ta dubi 'yan
uwanta, suka kama dariya,
suna toshe baki.A haka suka iso gida, yana biye
da su. Yana kallo suka shiga get, yana kallo duk
suka wuce cikin gida.
Farin cikin ya kama shi, domin ya san mai
gidan.
Injiniya Ahmad Kaita.
Abokin ogan sa ne a ofis, kuma yana aiki da
(Internet Global Services Jordan) ne."
Suna da manya rassa a Potugal, Iraq, Swedan,.
Hedikwatarsu na birnin New-York. Hamdala yayi,
sannan yayi ribas ya koma, farin cikin zuciyar sa
ya dawo sabo ful!
Washe gari karfe 9, yana (Internet Globar
Services). Ofishin Injinya Ahamd Kaita.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
a
Bai sha wahalar ganin sa ba, saboda dama sun
saba gaisawa idan ya zo wajen ogan sa.
Bayan sun gaisa, yayi masa bayanin abinda ke
tafe da shi. Nan take dadi ya kama Injiniya,
domin ya san Ibrahim mutumin kirki ne, ogansa
ma na yabon sa.
Nan take yayi maraba da shi, ya kuma ba shi
kati, ya ce idan ya zo ya kira wannan
lambar.
Yayi godiya, ya fito.
Ofishinsu ya wuce yana mai murna da farin ciki,
babu abinda yake hangowa, sai an daura auran
sa da Nusaiba.
Wai! Yaya zai ji ranat? Yayi sauri ya dafe kirji,
dadi zai kashe shi.
Injiniya na koma wa gidan kan sa ya kira
Nusaiba, ya gaya mata anjima za ta yi bako,
kuma yana rokon ta, don Allah ta ba shi hadin
kai, domin mutumin kirki ne.
Ta amsa da to.
Ta koma dakin ta, ta yi iya tunanin ta, amma ta
kasa gano mai neman dama mata lissafi. Su
Sumayya da sun rantse sun maya ba su gayaea
Ibrahim gidan su ba, balle ya san mai gidan.
To ko hadin Injiniya ne? Ta tambayi kan ta. Ta
runtse ido takaicin duniya ya isheta.Dan ta
karami, an dame ta da maganar aure.
Ita kuma ba shine a gaban ta ba, tana son
isashen lokaci, don kula da dan ta.
Ta sallaci isha'i. Bayan cin abinci.
Wankan ma ta ki yi, balle ta gyara jikinta.
Yadda take tun safe, haka take zaune tana tana
jiran ta ga dan rigimar dake neman auranta.
Bata gama tunanin ta ba.
Zainab ta zo da gudu ta gaya mata sako, inji
Abbanta.
Ta kura wa Ameer ido dake barci, sannan ta
wuce ta fito.
Zuwa karamin falo, inda aka ce bakon yake.
Kai,"Inna-lillahi"Wa-Inna-ilahir-raji'un!
Haka ta fada lkcn da ta yi ido 4 da Ibrahim.
Ya ce,"Dole ki yi salati, kin ga mayaeb zai cinye
ki."
Ta ce,"Saboda Allah menene na bn diddigi? Ya
girgiza kai,"Ba ki ma sani ba?
Lallai yau ne na gane cewa da hadin bakin ki
Abba ya hana ni auran ki."
Ta dan yamutsa fuska,"Allah ne,Abba bai isa ya
hana ka ba."
Kin di ni baki Nusaiba, kuma hakan yana k'ara
min son ki.
Wannan karon da alamun nasara, ki dubi tsawon
tazarar dake tsakanin Najeriya da Jordan, amma
Allah ya ce je ki Nusaiba mijin ki na can." Ta yi
dan murmushi, ta rasa me za ta ce da shi."
Ba karamin dadi murmushi ta yasa shi ba.
Ya dan langwabar da kai, ya sake fadin,"Kamar
an fama min gyambo Nusaiba, tun ranar da na
sake ganin ki tare da Sakina, kodayaushe sai mun
yi hirar Ameer ni da Husna, shi yasa har yanzu
bata mance da shi ba.
Da gangan ki ka batar da lambar da Sakina ta ba
ki, saboda ba kya son in san komai game da ke?
Ta ce,"Tabbas haka ne, na kuma kar6i lambar ta
ne kafin in san ko ita wace ce, da na zo na sani,
sai na kiyayi kai na, saboda tunanin me zai je ya
dawo?
Ya jinjina kai,"Kin yi gaskiya, amma da yake
Ibrahim mai sa'a ne sai ga shi abinda ya je, ya
dawo din.
Ko ba haka ba? Saura a ban dama, ayi ta ta
kare"
Ta ce,"Yaro na karami ne, ban ko yaye shi ba, da
dai............
Ya katse ta,"Ki na nufin Ameer? Je ki ji yadda yayi
suna a gida na, balle kuma ki kawo min shi, gaba
daya zai zama da na.Ta ce,"Ban tsara masa
hakan ba."
Ko?
Ta ce,"Tabbas."
Yayi dan shiru, kafin ya ce,"Ba kya so na dai ke
nan."
Ta ce,"Ban fad'a ba."
Ya ce,"Idan ba haka ba,"Ameer ne kawai zai
hana ki k'i aure na? Ta nisa kafin ta ce,"Har da
matarka, domin na lura Sakina na son ka da
yawa, bai kamata in shiga tsakanin ku ba.
Mun yi hira sosai da ita a jirgi, amma ka na
zuwa, ka nuna mata ka sanni, shi ke nan ta
sauya min fuska.
Ka ji dalilin yaga lambar da ta bani, don ba na
son tashin hankali."
Hankalinsa ya tashi kwarai, ya ce,"Ba ki fahimce
ta ba ne Nusaiba.......
Ta ce,"Haka ne Wallahi, ai ka ga lokacin ba ta ma
san halin da na ke ciki ba.
Ta ganni da Bebi, ba ita ba, kai kan ka ka yi
zaton ina gidan mijina.
Quite O.K a lokacin ba mu rabu ba, sai daga
baya.
To ina ga ace ga shi za ka aure ni?
"Babu abinda zai faru. Haka Sakina take, bata iya
rufe kishin ta, amma bata da fada, idan ku ka
fahime juna za ki gane tana da hakuri."
Ta ce,"Na ji."
In turo kenan?
"Ai na gaya maka ba yanzu na shirya yin aure
ba."
Ya runtse ido, dafe da goshi ya ce,"Nusaiba ba
kya so na.
Please!
Ki je ki yi shawara, abinda ki ke fadi ba hujja
bace."
Ya bata tausayi kwarai, amma gaskiya ba za ta
iya aure yanzu ba, shi yasa haka suka tashi hirar
babu fahimtar juna, kowannan su ya koma cike
da tunani.Musamman Ibrahim da yake ganin
Nusaiba na son ta yi wasa da rayuwarsa, bayan
ya lashi takobin wannan karon, sai ya ga abinda
zai ture wa buzu nadi."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Abubuwa da dama suke damun Nusaiba, ta kan
ji kamar ta tsero ta bar k'asar, domin Injiniya da
Antina sun tasa ta gaba, akan zancan Ibrahim,
kamar yadda shi kan sa ya addabe ta da
zuwa.
A hak'ik'anin gaskiya tana tunanin Istaharar ta,
kuma tana aji a jikin ta akwai maganar da Naseer
yake son gaya mata, dama ce kai bata ba shi
ba.
A wannan gwagwarmayar suka shafe shekarar
har ta yaye Ameer, yana neman wata 6 da
yaye.
Ibrahim bai hakura ba, ita kuma bata sakar masa
ba.
Anti kam har ta yi fushi ta daina yi mata
magana, kamar yadda Injiniya ya sa ido, abinda
ya sa a ransa shine wata kila Ibrahim din ne bata
so.
Shi kuwa Ibrahim har su Husna ya kwaso ya
kawo mata tabbacin cewa Sakina ta sani
kenan.
Wannan bai dami Nusaiba ba, domin bata san
irin bala in da ya sha a gida ba, akan hakan.
Ta fara riga ta ga duniya, babu wata yaudar da
Da namiji zai nuna mata.
Idan gaskiya ne, ya ce zai kai ta gun Sakinar
mana?
Bai ta6a gigi ba, sai dai ya kwaso mata su
Husna.
Kwatsam! Sai ga Alh. Basheer a Jordan, ba zato
ba tsammani. Kai murna a wajen Nusaiba, kamar
ta zuba ruka k'asa ta sha.Tana kewar sa sosai,
tunda ya zo take like da shi.
Shi kuwa Ameer ke zuciyar sa, ji yake kamar in
zai koma ya wuce da shi, ya zauna gidan sa.
Yaron yayi saurin girma kamar ba dan shekara 2
da watanni ba.
Suna zaune dare ya fara yi ga Injiniya ga
Antinta.
"Alhaji ya tambaya,"Wai 'yar gidan ta ku bata
fidda wani ba? Jin haka yasa Nusaiba ta tashi ta
bar falon.
Injiniya ya ce,"Ai mu Nusaiba ba mu san inda ta
dosa ba."
Kamar yaya?
Ya ce,"Wani yaro ke son ta kamar zai yi
hauka,
amma ba ka ga yadda take wahalar da shi
ba.
Ni Wallahi tausayi yake ba ni.
Yana da mata da 'ya'ya'yen sa 3.
Ibrahim sunansa, yana aiki da (Nijeriyan Embasy)
, yaro mai hankali, amma ta ki ba shi goyon
baya."
Ya ce,"Ibrahim?
Ni kuwa kamar na san sunan nan?
Anya kuwa ba yaron nan ba ne daya so auran ta
da?
Fatima ta ce,"Oho,"Nusaiba wani bayani za ta
zauna ta yi.
Yarinya da ka fara magana, sai kuka.
Ni dai yara suke gaya min wai a (Super market)
suka hadu, amma sun ga kamar dama can ya
san ta.
Ya ce,"Lalai Ibrahim din da na ke magana
ne.
Kuma da akwai alamun tana son sa, ni ne na
cusa mata Zancen Naseer.
To me yasa yanzu ba za ta aure shi ba?
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
----------------------------------------------------------------------------------------------
Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100
Ajinisa Yake3-05
Posted by ANaM Dorayi on 11:43 AM, 25-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Ta ce,"Ba zai wuce wannan yaron da ta
kwallafawa rai ba.
Ta shaku da Ameer ko alama bata son a raba su.
Ameer kuwa dole ya koma gidan ubansa, sanin
kan ta ne ba zai kyale mata shi ba.
Alh. Basheer yayi shiru, Injiniya ke fadin,"Nusaiba
manya,
abubuwanta dariya suke ban, na ga yadda za'ayi
wannan al'amari."
Alh. Ya ce,"Ku kyale ta, zan yi maganin
abin."Suka saki wannan shafin, suka kama wani,
dare yayi Alhj ya tafi masaukin sa.
Yana tunani tare ba tare da yayi wa Nusaiba
maganar Ibrham ba.
Koda dama bisa hanya yake, harkokinsa ne, suka
kawo shi, hanya ta ratso da shi nan.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Yana zaune cikin ofis a gida Nijeriya, misalin 11
rana.
Naseer yayi sallama ya shigo.
Ya amsa,"Lafiya lau.
Ya jikin na Zarah?
Ya ce,"An gode Allah.
Wannan karon dai Likita ya ce dole ta huta daga
wannan, saboda mahaifar ta ta yi rauni da
yawa.
Ya dan kada kai,"Ayya, gaskiya ya kamata ta
huta, saboda lafiyar ta, ayi hakuri da abinda
Allah ya kaddaro."
Ya ce,"Haka ne.
Dama tun jiya na zo in nuna maka Result.
Ya fito na kammala Diploma." Ya washe
baki,"Ah!
Lallai abin ba wuya a wurin Allah."
Yasa hannu ya kar6i takardu, ya duba,"Kai!
First class!
Gaskiya takardun sun yi kyau.
Yana 'yar dariya ya shafi keya, ya ce,"Sun ba ni
(Adimission ABU), Direct.
Next month za'a fara Rigistireshon.
Alhj ya miko masa hannu,"Congrat! Kai na ji
dadi., Allah ya bada sa'a."
Amin."
Ya fadi bakin sa ya ki rufuwa, ganin yadda Alhj
ke murna.
Ya mike yana fadin,"Zan koma Abba, na gaishe
ka."
Ya ce,"To na gode.
Zan tura ma da sako(Acconut) din ka, ba yawa,
sai ayi Rijistireshon ko?
Ya tsugunna yayi godiya.Alhjn ya jawo dirowa,
ya dauko farar ambulan ya mika masa,"Wannan
ma sakon ka ne."
Cikin mamaki yasa hannu ya kar6a ya kara
godiya ya fice.
Yana shiga mota da rawar jiki, ya buda
ambulan, don ganin me ke cikin su? Wasu
zaradan hotunan Ameer, ya rinka zarowa daya
bayan daya guda 24 kala-kala. Wasu tun yana
dan wata 4 a zaune, wasu yana rarrafe, da
yawa a tsaye yake.
Ya zura wa hotuna ido, kamar ya sume, saboda
doki da farin ciki.
Ya sumbata, ya rungume ya ma rasa inda zai
aje su.
Take nan ya kira wayar Zarah,"Kin ga yadda
Ameer dina yayi girma?
Ta ce,"A ina ka gan shi?
Hotunansa Abba ya zo min da shu, sai kin ga
yaron Zarah, kamar dan larabawa."
Ta ce,"Ka na ta sa min rai, yayana ka kawo min
in gani mana."
Ya ce,"Ki jira, yanzu zan baro Kaduna."
Ta ce,"Allah ya tsare."
Ya ce,"Amin.
Ya kashe waya.
Ya bi hoton hannun sa da kallo, can ya sauke
numfashi, ya sake sumbatar sa, sannan yayi wa
mota key, ya ya wuce.
Yana isa Zariya. Su Umma ya fara kai wa
hotuna suka gani.
Umma ta dauki daya.
Ya kai wa Inna ita ma ta za6i na ta.
Daga nan ya cilla Shika ya kai wa Zarah.
Wai ta ga hotuna kamar ta dauko Ameer yayi
motsi a gaban su.
Nan ya bar mata 2.
Fitowar sa asibiti a hanya ya shiga shagon sai da
(Gift) da (Frem) na sa Hotuna ya siyo kanana
guda 24.
Gaba daya hotunan sai da ya sa su cikin frem
har da na wajen su Umma da Inna.
Sageer an ba shi.
Yakubu ma, ya samu har da dakin Hajiyar
sa.Naseer B ma ya ce yana so a ba shi. Naseer
kamar zai hauka ce, saboda son Ameer. Bayan
kwana 2 daya koma Kaduna. Haka ya ga hoton
bisa tebur din Alhj gaba dayan firem din mai
kyan gaske.
Ba k'aramin dadi ya ji ba.
Shi yasa ya k'ara kaimi wajen addu'ar sa.
Allah ya dai-daita auran sa da Nusaibansa.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sati 3 tsakani, cikin Zarah ya k'i zama, wannan
karon ko wata 7 bai kai ba, watan sa 6. Dole aka
bi shawarar Likitan nan take aka juya mata
mahaifa, don ta huta da wahala, domin ba
k'aramar wuya take ci ba kafin ta haihu, ban da
jinin da take zubdawa.
Yaya za ta yi?
Haka Allah ya kaddaro.
Ubangiji yasa kaffara ce. Bayan ta gagije, lafiya
ta zauna mata sai Naseer ya neman mata F.C.E.
Ta samu a saukake, shi ya gama mata komai ta
fara karatu.
English/Islamic.
Asabar da lahadi ya fita da ita koyon mota, tun
tana tsoro har ta kware.
Cikin sati na 3, ita ke kai kan ta makaranta. Shi
ke nan ya sakar mata (Honda Civic) din sa.
Shi yana amfani da Jeep kawai.
Kasancewar Sageer zai tafi sabis din sa bana, sai
shagon dinkin sa yayi rauni. Ba sosai yake zama
ba, su Abbas ne kula masa da shi.
Idan ya taso makaranta yake zama ko ranakun
da babu karatu.
Kusan ace hankalin Naseer kwance yake, amma
Allah kadai yasan abinda ke damunsa a
dangane da son dawowa da Nusaiba gidan
sa.Ba shi da bakin magana ne kawai, ko kuma
mu ce babu wanda zai kai wa kukan sa balle a
share masa hawaye. Shi yasa wani lokacin za ka
gan shi a rame, wani lokacin kuma babu laifi.
Bayan wata 2 da dawowar Alh. Basheer Jordan
yana ta binciken halin da Nusaiba suke ciki da
Ibrahim.
Babu wani sauyi, kodayaushe nuna masa take
ba za ta aure shi ba, shine dai ya k'i hak'ura.
Jin haka yasa Alh.Basheer ya ce maza-maza ta
dawo gida Nijeriya ta yi aure anan.
Ta shiga shirin kaya, cikin bak'in ciki da 6acin rai
har ta rink'a jin kamar ta cewa Ibrahim ya fito,
don ta san tabbas Ibrahim na tsananin sonta.
Amma da ta tuna abinda Sakina ta yi mata a
filin jirgi, sai ta yi turus!
A tunanin ta da kyar Sakina za ta bar ta sakewa
gidan Ibrahim.
Saboda haka ta watsar da maganar Ibrahim, ta
ci gaba da shirinta ko gaya masa bata yi ba.
Ana gobe za ta dawo.
Alh. Basheer ya kira Naseer ya same shi a ofis.
Yana zaune, yayi shiru yana jiran ya ji dalilin
kiransa.
Alhj ya dan gyara fuska ya ce,"Gobe Nusaiba za
ta dawo maka da Ameer, saboda ta sami miji za
ta yi aure.
Shine nace zan gaya maka, idan sun iso, ka zo
ka kar6i abin ka, ka sa shi makaranta, tunda da
bakin sa.
K'iris ya rage ba'a zare ran Naseer ba, daga
inda yake zaune, domin ilahirin kwakwalwarsa
sa ta daina aiki.Yayi zugudun, kai sunkuye, bai
motsa ba, balle ya ce wani abu.
Alh. Basheer ya zura masa ido, jim kafin ya sake
fadin.
"Ka na iya tafiya, dama shi kenan sak'on, da
zarar sun iso, zan kira ka a waya."
Ya dago ya dube shi, ido cike da kwalla, sun
kada jajur, bakin sa dauke da magana, sai dai
ya kasa furtawa, sai ya ce to kawai.
Da kyar ya mike ya nufi kofa.
Alhj ya bi shi da kallo.
Goge hawaye yake da bayan hannu.
Yasa kofa zai buda. Alhajin ya kira shi.
Ya waigo a gigice, yana amsawa.
Yayi jim kafin ya ce,"Don Allah ka gaida min
Malama Balarabe da kyau."
Ya hadiye miyau, ya ce,"Zai ji Insha-Allahu."
Ya buda, kofa ya fice.
Ya shigo gida karfe 7 na magariba.
Kwanciya yayi a dakin sa ya rasa abinda ke
masa dadi a duniya.
Zarah ta yi tambayar duniya, ya kyale ta.
Ta yi mita har ta gaji, bata samu wata amsa ba,
duk ranta yayi mata k'unci.
Cikin dare ta farka, ba shi cikin dakin."
Ta fito ta biyo shi, yana falo zaune cikin duhu,
sai da ta kunna fitila sannan ta gan shi.
Ta matsa gaban sa ta ce,"Ikon Allah, watau
yayana she akwai wani lokaci da zai zo, wanda
ba dole ba ne in san me ke damunka? Gaskiya
ne..............
Ya katse ta,"Zarah ba wata magana bace. Ameer
ne za'a dawo min da shi. Nusaiba za ta yi
aure."
Ta numfasa ta koma dirshan ta zauna kafin ta
ce,"Amma yaya ka na da abin mamaki.
Nusaiba za ta yi aure, ba dole ta dawo maka da
danka ba?
Menene abin damuwa a nan? Yayi mata wani
mugun kallon da bai ta6a yi mata irin sa ba, ya
ce
"Babu!
Rok'ona gun ki shi ne ki koma ki sha barcin ki.
Please and Please!Ta bi shi da kallo, bata ma
san me ke bata mamaki ba.
Ta buda baki za ta yi magana, ya kwarara mata
tsawa,"Ki tashi na ce ko? Ban son jin komai
nace!
Idanuwanta suka cika da hawaye, ta tashi da
gudu ta nufi.
Sashin ta kuka kala-kala ta rink'a yi, kamar
yadda tunanin ta yake kala-kala. Lallai son
Nusaiba ya zauna masa, ko kuwa don yana
ganin ita bata aje masa da ba ne, shi yasa ya
fara yi mata kwakwazo?
To ai daga Allah ne, kuma bata bakin cikin
soyayyar sa da Nusaiba.
Me yasa zai juya mata baya yau? Kafin safiya,
idanuwanta sun kunbura.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Naseer na kallon ta, tana shirin tafiya
makaranta. Ransa ya k'ara 6aci. Tana ta wanke-
wanke a kicin ya biyo ta, bayan ta ya rungume,
ya sumbace ta, ya rada mata,"I'm sorry.
Jini na ne ya hau, kar ki yi fushi da ni sweet
Zarah."
Ta runtse ido, hawaye suka zubo, ya juyo ta ya
share su."
Ya isa haka, ai ya wuce ko? La66anta na rawa
ta ce,"Yayana ba na bakin ciki. Ko ka fara son
Nusaiba, kuma ina maku murna idan da za'a ce
gidan nan za ta dawo.
Amma menene na yi min ihu saboda na fadi
gaskiya? Saboda ban aje maka da ba ko?
Nan da nan idanuwan sa suka kada,"Kin san
abinda ki ke fadi kuwa Zarah? Kin maida ni jahili
kenan, ban san Allah ba? Ya juya mata baya,
ban ta6a zaton wannan maganar ba daga gare
ki Zarah."Take nan ta amsa laifinta, sai dai ka
fin ta mik'a hannu, ta kamo na sa, yayi waje ya
bar kicin din. Tana kokarin biyo shi, ta ji tashin
motar sa. Tana fitowa wajen Mai gadi na rufe
get, ya riga ya fice.
Ta koma falo ta zauna, tana mai nadamar
furucin ta.
Daga ita har Naseer babu wanda ya fahimci
karatun ranar. Shi kam Naseer caji 2 ke kan sa,
shi yasa ya kashe wayayinsa, baya son magana
da kowa.
Bai dawo gida ba sai bayan issha, yana shigowa
falo, ya ji ta a jikinsa, kiris ya rage ta kada shi.
Mafarin daya rike ta sosai kenan.
Ta ce,"Yayana na tuba. Allah na tuba ba zan
sake ba."
Yayi ajiyar zuciya mai karfi, ya kamo hannunta,
suka zauna.
Ya dube ta ya ce,"Magana makamanciyar
wannan kar ki sake min ita, idan ki na son farin
ciki na a duniya."
Ta kama kunuwanta 2, ta ce,"Ba zan sake ba
yayana."
Ya jawo kafadar ta, ta kwanto masa,"Ya wuce,
shi kenan."
Ta ce,"To yaya su Nusaiba, sun iso?
Ya ce,"Ni wayoyina ma kulle suke tun safe, ba
na son ya kira ni, so ban san halin da suke ciki
ba."
Ta ce,"Hakuri za ka yi yayana, su gani suke har
yanzu ba ka son ta ne."
Yayi shiru ya rasa me zai ce?
Ta dan dube shi.
"Zo mu ci abinci ko?
Ya ja hancin ta, ya ce,"Sure."
Suka tashi suka nufi tebur don cin abinci."A dai-
dai wannan lokaci Alh.Basheer da Nusaiba tare
da Ameer suka shigo gida.
Alhj ya dauko su daga filin jirgi.
Ummi ta tar6e su, murna kamar su lashe juna.
Duk da Ameer bai santa ba, ya saki jikinsa da
ita sosai.
Da yake shi ba mai bakunta ba ne.
Bayan sun ci abinci, an yi masa wanka yai barci,
ita ma ta kintsa, ta tafi kiran Abbanta, yana
falonsa kwance labarai yake kallo.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Tana shigowa ya tashi zaune yana fadin,"Zo nan
'yar albarka."
Tana murmushi ta zo gun sa ta zauna.
Ya ce,"Yauwa.
Magana za mu yi.
Kin tuna alkawarin da ki kai min a asibiti?
Ta dube shi,"Wane alkawari Abba?
Ya ce,"Lokacin da rigamar auran ki da Naseer ta
taso.
Ina ganin laifina ne, amma ki ka ce a'a, kuma
ko nan gaba na sake za6a miki wani mijin, za ki
aure shi.
Kin tuna?
Ta kada kai, ta ce,"Na tuna Abba."
To za ki iya ciki min shi?
Ta dan yi shiru, kafin ta ce,"Zan cika Abba na,
umurnin ka kawai na ke jira."
Ya rungumo kafadar ta ya ce,"Allah yayi miki
albarka.
Kafin nan na riga na gaya wa Naseer za ki dawo
masa da Ameer.
So kafin ya zo, ki tsaya ki duba wannan
takardar, wasika ce daga mijin da na sami miki."
Ina fatan za ki aje hankalin ki waje daya."
Ya sa hannu kasan filon kujera ya dauko
amblun, ya mika mata ta amsa jiki ba kwari.
Tashi ki je ki karanta, ki yi nazari akai, kafin
Allah ya kai mu gobe inji ta bakin ki."
Ta mike ta wuce babu wani ishashen kuzari a
jikinta.
Ameer ta tsurawa ido, ta fashe da kuka.
Shi ke nan za'a raba ta da shi.
Rayuwa kenan, abinda ya kamata ita da
Babansa su ba shi tarbiyar da ta tace
Hakan ba zai samu ba ko? Ta tambayi kanta,
gocewa ta sake yi da kuka.
Can wata zuciya ta ce,"Ba ga Antin ki ba? Ai za
ta iya rike miki shi tsakani da Allah. Ta goge
hawaye, ta ce,"Haka ne. Na san Antina za ta
iya."
Ta ci gaba da share hawayen, tana ajiyar zuciya.
Ta dauko ambulan din dake gefe ta jujjuya ta,
sannan ta farke ta, ta warware ta fara
karantawa, "Gaisuwa irin ta addinin Islama.
Kafin na ce dake komai, ina mai neman gafarar
tarin laifin da na yi miki. Da ace ki na cikin
hankalin ki a lokacin da na ke tare da ke a
asibiti. Da kin tabbatar da cewa na tuba, na
kuma fad'a cikin kaunar ki, son ki ya kama ni, a
lokacin da zaman mu tare ya zo k'arshe. SAKI
DAYA na yi miki ya ke ma'abociyar hakuri.
Amma ki sani, a duk bagun numfashin da zuciya
ta za ta yi a duniya, tare da bikon soyayyarki.
Da ace zan sake samun wata dama ta auran ki,
na yi rantsuwa da wanda ya halicce ni, zan
nuna miki za6i na gari Abba yayi miki. A karshe
ina addu'ar Allah ya raya mana Ameer, rayuwa
mai kyau cikin addinin musulunci. Mai son
kiNaseer Iliyas Balarabe!
Bata gaskanta idon ta ba, balle ta yarda da
abinda ta gani a rubuce. Ta sake maimaitawa.
Ta tsaya kasake tana sauke Numfashi. Me ke
cikin ranta wanda bata tantance shi ba? Kamar
farin ciki ne ya kamata, to me yasa hawaye ke
neman kubcewa?
-----------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Gaba daya ta kidime. Ta sake duba takardar
bisa sunan mai ita Naseer Iliyas Balarabe! Ta
cicci6o Ameer ta rungume shi tana fadin,"Tare
za mu koma gidan Babanka! Allah na yafe
masa! Da kyar ta sami barcin kirki. Da safe ta
tafi gaida Alhjn, tun daga fuskarta ya shaida
tana cikin walwala, ba kamar dawowar ta jiya
ba. Bayan sun gaisa, ya ce,"Kin ga sak'on? Ta
amsa da kai, tana d'an murmushi. Ya dan dago
habarta, ya ce,"To yaya? Ya fito bazawarin? Ta
fado jikin sa ta kudundune fuska,"Kai Abba! Ya
fasje da dariya,"Shi ke nan, na bari, to tashi ki
ji." Ta mike ya ce,"Na san anjima zai zo, sai da
ba shi da labarin komai, illa Ameer da zai
dauka. Za'a ci kwalliya ko? Ta tashi da gudu, ta
bar dakin. Ya kama dariya yana kwanciya bisa
kujera,"Bebin Abba kenan 'yar albarka.," Karfe 9
da rabi Naseer ya iso gidan su, don gaida iyayen
sa kamar yadda ya saba duk ranar asabar da
lahadi. Yana shigowa. Malam Balarabe ya hau
fada,"Kai menene dalilin kulle wayoyin ka.
Alh.Basheer na ta neman ka tun jiya, bai same
ka ba? Ya ce,"Uhm.............Ba su da caji ne. Ya
ce,"Amma kai k'aryar ka ko hanyar masallaci
bata sani ba Idan babu Nepa, ba akwai jenareto
ba? Yayi shiru." Watau abin zai dawo ko? Da
sauri ya ce,"A'a Abba! Ya ce,"To mike maza!
Yana neman ka." Ya mike yana fadin,"Sai na
dawo. "Umma ce kadai ta amsa mashi. Ya wuce
babu kuzari.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sha daya yana ofis din Alhj ko zama bai yi ba,
yace ya ke can gida ya dauke shi, an riga an
gama kimtsa kayansa. Tafe yake kawai, amma
ko alama baya son ganin Nusaiba, kar kwadayin
dawo da ita ya taso masa. A haka ya iso. Yayi ta
maza yayi sallama falon. Ummi ke zaune a falon
ta yi masa sannu da zuwa, ya tsugunna ya
gaishe ta. Ta kira Mariya, ta ce ta kira Nusaiba,
ita kuma ta haye sama abin ta. Yayi zuru a
zaune kirjinsa na duka. Mariya ta kawo masa
tiran kayan motsa baki. Bai ta6a komai ba, wani
lafiyayyen kamshi ya doki hancinsa. Ya ware ido
saitin kofa. Zuwa can Nusaiba ta ratso rike da
hannun. Ameer. Ya zura masa ido, ashe ma
kadan ya gani, kyan Ameer a hoto. Jikin sa ya
dauki rawa. Nusaiba ta daki zuciyar sa sosai. Bai
daina kallon su ba har suka iso tsakar falon, tayi
masa sannu da zuwa. Baki sake ya amsa. Ta
zauna ta dubi Ameer ta ce,"Ga Abba." Ya kura
mata ido ya ce,"Abba? Ta yi dan
murmushi,"Babanka ne, je ka." Ta tura shi ya
nufo Naseer. Mikewa yayi ya tarbe shi, ya
rungume, "Oyoyo Abba na! Ya jima da shi a
kirjin sa, kafin suka zauna, ya dora shi bisa
cinyoyinsa, suka bi juna da kallo.
Ya ce,"Ka sanni? Ya girgiza kai. Ya ce,"Baba ne.
Ka ce Baba inji? Ya ce,"Baba." Ya sumbace shi a
dukkan kuncin sa. Sannan ya dubi Nusaiba,
suka hada ido, yayi dan murmushi, ya ce,"Kun
dawo lafiya? Ta ce,"Lafiya lau, ya su Antina da
su Umma? Ya ce,"Lafiyar su lau, sun ce a gaishe
ki." Ta ce,"Ina amsawa." Suka yi shiru na dan
lokaci, kafin suka sake kallon juna. Kowa yayi
murmushi, ya dauke ido. Naseer ya kama
yatsun Ameer ya hau kadawa, ya rasa abinda
zai ce. Ameer ne ya katse shirun,"Baba, wai tare
za mu tafi? Ya tallafo kuncin sa ya ce,"A'a za ka
zauna tare da Mama tukuna ko? Ka na so? Ya
kada kai,"Ni zan bi ka." Ya kwanto jikin sa ya
lafe. Ya k'ara rungume shi, ya dubi Nuasaiba,
murmushi kawai take yi kafin ta ce,"Yaro ya san
gaskiya." Ya ce,"Wace gaskiya? Ai kyan sa ya
zauna tare da ke in rink'a zuwa ina ganin sa."
Ta ce,"A gidan wani? Ya 6ata fuska ya ce,"Anan
gidan na ke nufi, idan son samu ne, mu kasance
yana ganin mu tare kowane lokaci, shi zai
taimaka ya san mu ne iyayen sa. Ta dan kada
kai,"To ai kuma ba zama na zo yi ba gidan.
Matsalar kenan." Ya sauke numfashi yayi shiru,
ba don shi da abin fadi ba. Ta ci gaba da
cewa,"Yanzu za ku tafi a fito da kayayyakin??
Ya dan kalle ta, kin kosa ne mu tafi? Ban ce ba,
ayi hakuri." Haka hirar ta ci gaba su kamo nan,
su kamo can, alamun babu natsuwa a tattare
da Naseer. Sun sami awa 2 tare. Ya kwaso
kayan Ameer ya taho da shi, hankalin sa tashe.
A Zariya kowa na murnar ganin Ameer, shi ta
shi ragaggiya ce, sbd zullumin sun kusa rabuwa
da Nusaiba kwata-kwata sai wata k'addara za ta
hado su Shi yasa kodayaushe yana Kaduna tare
da Ameer wai yana kawo mata shi ne ta gan
shi. Dariya take yi, ta ce ta gode."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sati 2 suka wuce Naseer na lilo tsakanin Kaduna
da Zariya. A yau da la'asar ya isa bayan barin sa
makaranta ya sa Ameer a mota suka zo. Suna
tare da Nusaiba a waje suna shan iska.
Alh.Basheer ya dawo, Naseer ya nufe shi suka
gaisa daga nan Alhjn ya ce,"Yauwa tunda ga ka,
shi kenan sai ka kai wa Malam Balarabe katin
daurin auran Kanwar ta ka, wani satin." Naseer
ya dask'are nan, har Alhj ya dauko jakar sa a
mota ya buda, ya debo katuna." Ungo guda 10
ka ba shi. Haka kuma ga na ka nan, in za ka ba
Friend din ka ne, in ba ka Twenty? Kamar ya
ce,"A'a." Sai wata zuciya ta hana shi, ya ce,"Toh
Alhj." Ya mika masa guda 30. Yasa hannu ya
kar6a.
Bayan sun yi sallama da Alhj, ya wuce ciki gida,
ran sa 6ace, ya koma gun Nusaiba,"Me za ki
6oye min? Ashe Next week ne auran ki shine ko
ki gaya min? Ni na isa in hana ne? Baki sake ta
ce,"Shirin gaya maka na ke yi, sai Abba ya dawo
ka tashi. Ayi hakuri. Ya suri Ameer,"Mu mun
tafi. Allah ya bada zaman lafiya." Ya wuce ya
bar ta zaune tana masa dariya. Yana zuwa, ya
watsa katuna bayan mota, suka tafi. Iya wuya
yake yau. Duk wanda ya ta6a shi, zai ji masifa,
gida ya wuce da katunan bai kai wa Abba na shi
ba. Yana zaune. Zarah da Ameer kadai ke
hidimarsu cikin gidan Baya ko fahimce shi ba,
suna kici ita da dan lelwn ta, suna girki. Yayi
nisa a tunanin sa, kamar ya hadiye zuciya, don
haushi. Me zai ci da katuna, banda ya banka wa
'yan iska wuta? Ya zabura a fusace ya fado
kicin, babu magana ya hau bincike, ya 6aro
mata da kayan cikin dirowar sama. Tayi tsaue
tana fadi,"Yayana me ka ke nema? Ashana." Ta
ga ya dauka, yai waje. Ta jefar da ludayi, ta
biyo shi,"Yayana me za ka yi da ashana? Ya
buda mota ya kwaso katuna, ya aje k'asa. Kafin
ya kyasta ashanar ta kwashe su. Ya kama da
karfin yana fadi,"Ki saki na ce ko? Ta dade bata
yi auran ba, idan har sai mun je masu daurin
aure! Ya fizzge iya rabon sa, ya watsar kasa, ya
kyasta ashana. Ya cinna, yayin da Zarah ta buda
ambulan, don ganin takardun da yake rawar
jikin konawa? Kati ta gani ta zaro shi ta karanta.
Dada masa duka ta yi a tsakar baya, yana duke
yana cinna wuta, ta fadi da karfi,"Kai yaya na
da kai ne! Duba ka gani,"Naseer Iliyas Balarabe
aka sa! Ya mike ya fige katin a hannun ta, ya
karanta. Gaba daya jikinsa yayi la'asar, ya zura
mata ido, sannan ya dafe goshi, duk kunya ta
kama shi. Ta ce,"Komai ba ka bincike, sai ka
yanke hukunci." Ya rungumo ta, hayaki yayi
sama, ta ce,"Ga dai sauran nan na cin wuta." Ya
sake ta ya hau tsalle yana kashewa, tana masa
dariya, duk da haka wasu sun k'one, wasu
kuma sun yi dameji. Ya kwaso yana nuna
mata,"Ni yanzu yaya zan yi? Katunan nan har
da Abba? Ta yamutsa fuska, ta dubi Ameer dake
tsaye gefenta, ta ce,"Mu ina ruwanmu ko
sweetyna? Ya amsa da kai, yana dariya. Ta
mik'a masa hannu,"Come on give me five! Ya
bata hannu, suka kashe. Ta sure shi, ta ce,"Zo
mu tafi abin mu, kar abincin mu ya kone. Baban
ka ya zare! Ya kawo mata wawura, ta kwasa da
gudu. T-shirt da wandon dake jikin ta ya bata
damar gudu sosai. Ameer dariya yake yana
murna. Kicin ya iske su suna ta yi masa
dariya."Don Allah ki aje girkin nan, ki zo ki raka
ni." Ta kama k'ugu, ta tambayi Ameer,,"Mu
muka ce ya konawa Abba kati?
Ya girgiza kai,"A'a, ta dube shi ta nuna shi da
ludayi,"Ka ji ko? Saboda haka ba ruwan mu." Ya
matso ya manne da jikinta,"Don Allah ki daina
wasa, ki zo mu tafi."Ta k'are masa kallo kafin ta
ce,"Jira ni ina zuwa." Ya sumbace ta, saboda
Ameer yayi waje. Ta sauke numfashi, ta
ce,"Allah na gode maka amarya za ta dawo." Ta
sauke girki ta kashe (Cooker), ko dama sitiyu ce,
ta rage mata. Daki ta je ta dora (After dress)
akan kayan jikin ta, ta yafo mayanin ta fito, ta
kulle gida. Ta same su a mota. Suka tafi Ameer
na bisa cinyoyin ta. Shi kuwa waya ya dauko ya
kira Sageer a Bauchi."Banza, ka na can za'a sha
shagali! Shagalin me? Amaryar Zarah za ta
dawo." Ah haba don Allah? Komai yayi dai-dai
kenan." Ya ce,"Walllahi ni ban ma san Abban na
ta ya hakura ba, kati kawai ya ba ni dazu." Cikin
murna ya ce,"Congrats. Insha Allahu zan zo a
daura da ni, wannan dole ne. Yaushe ne? Next
week,"Ai kuwa zan zo da yardar Allah." Suka yi
sallama ya aje waya. Ya dubi Zarah,"Ya ce, yana
gaishe ki." Ina ansawa. Amma ba ka gaya masa
ka zare ba, har ka kona katunan." Ya dunkule
hannu ya dora bisa kuncinta. Allah zan kwashe
miki hakora, ki kiyaye ni!
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Ya kuwa kama, ya danna masa cizo, ya janye da
sauri yana dariya. Su ma suna yi masa. Ya shafa
kan Ameer ya ce,"Ta koya ma mugunta ko? Ya
lafe a kirjin ta, suka kwakume juna. Naseer ya
sha mamaki da suka kai wa su Abba ragowar
katin da suka rage masu kyau guda 15. Malam
Balarabe ya ce idan ya na son k'ari ya zo ya ba
shi. Kunshi 1 ya fito da su, wani samfu daban
kuma bugun Malam Balarabe. Abin ya daure wa
Nasrr kai, ya ce,"Ni fa ban gane ba? Umma ta
ce,"Ai ba za ka gane ba, domin Abbanka da Alhj
sun barka cikin duhu. Amma tun ranar da ka zo
da Ameer gidan nan. Alhjn ya gaya wa Malam
cewaR Nusaiba za ta dawo." Ya shagwa6e
fuska,"Saboda Allah ya za'a min haka? Da na
mutu fa kafin lokacin saboda damuwa? Zarah ta
ce,"Sai a rufe ka mu ci sadaka. Ya harare ta.
Umma na fadin, gaya masa dai Zarah. Take nan
ta ba su labarin abinda yayi dazu. Me za su yi
ba dariya ba. Koda ya je Kaduna dariya suka
rinka yi masa, musamman Nusaiba. Shirye-
shirye ya kankama. Da yawa mutane ba sun san
Nusaiba bata gidan Naseer ba, sai da suka sake
ganin kati, musamman jama'ar Alhj. Ranar
juma'a da daddare Sageer ya iso, don haka da
shi aka daura aure. Washe gari karfe 1 da rabi
na rana.
Antin Jordan ta dubi Naseer ta ce,"Lalai kai mai
sa'a ne, ka yi wa Allah godiya, domin yayi maka
baiwa." Ya sunkuyar da kai,"Na gode Anti." Ya
wuce ta bi shi da kallo. Ibrahim ya fado mata,
tausayin sa ya kamata. Ranar daya zo Injinya na
masa bayanin hukuncin da Alhj ya yanke har ya
bar wajen, fadi yake,"Ai dama na san Abba baya
so na. Wannan karon ma har da Nusaiba, tunda
ta iya barin k'asar nan, ba tare da sani na ba."
Ta girgiza kai, ta ce a ranta,"Matar mutum
kabarin sa." A ranar Nusaiba ta tare su Kausar
suka rako ta. Suna shigowa Zarah ta kar6e ta,
suka rungume juna, ta kamo ta zuwa sashinta.
Kausar na ta fama da tsohin cikin ta, ta ya6e
bakin gado. Naseer ya shigo, bayan sun gama
cin abincin, suna shirin komawa. Ya ce,"To ga
motar can sun shawo man sun dawo." Kausar ta
ce,"Na ga ka na rawar jiki ne Jah-Jah, sai wani
korarmu ka ke, ni fa ina nan an sai jibi zan
koma." Ya ce,"Ga Jah-Jah nan a gaban ki, kin yi
wani turus, in za ki kai jibin? Aka kwashe da
dariya. Ta ce,"Anan gidan kuwa." Ya ce,"Ina,
taso maza in lalla6a ki in sa a mota, kar ki caza
min aiki. Ina angwancina, ace in taso asibiti zan
kai ki." Ta ce,"Gaskiya ne, ba laifin ka ba ne,
tana ji ta yi shiru, shi yasa ka ke kara fadi. Ta
na shiru. Antin Jordan ta shigo.
"Kausar cicci6o mana, sai da nace ki yi zaman ki
gida, ki ka ki." Simi-simi Naseer ya fice. Kausar
ta ce,"Ya ka tsere? Dawo mana mu ci gaba. Ka
na Angwanci ko? Ya waigo a bakin kofa, ya amsa
da kai, ya wuce yana dariya. Duk an watse.
Kowa ya koma muhalinsa. Ba ango kadai ba,
hatta Ameer yana murnar ganin Maman sa a
cikin gidan, yayi ta tsalle-tsallensa ya bi can, ya
bi nan. Amma yana cin abinci. Zarah ta yi masa
wanka, gadon ta ya haye yayi barcin, bai nemi
Maman sa ba. Tana zaune misalin 9, nazarin
litattafanta take yi. Naseer ya shigo. Ta dube shi
tana. Murmushi,"Ango kenan. Kamshin nan yayi
Wallahi." Ya tsugunna ya dada mata duka a
baya,"Ba kya ji ko? Ta ce,"Na kai ka rashin ji? Ya
ciji kunnanta, ta shafi wajen, ta ce,"Amarya na
jiran ka, tashi mu je in raka ka." Ta aje littafi ta
kamo hannun sa, ya mike ya rungumo kafadar
ta, suka fito zuwa sashin amrya. Ta turo kafar
tare da sallama ta shiga. Amarya ta sha ado, sai
wanda ya gani. Zarah ta ce,"Kai amarya, ai sai
yayan mu ya mance sunansa." Ta sunkuyar da
kai,"Antina kin dame ni tun dazu." Ta ce,"To
babu ruwana, ga shi nan na kawo shi amana,
gobe in an ga ya susuce, ke ce." Ta kama baki
tana 'yar dariya. Ya kamo kunnanta,"Shi yasa
nace ba kya jin, zo ki wuce." Yana rike da
kunnan ya kai ta kofa, suna dariya. Ta tsaya ta
ce,"Amarya ya kore ni, sai da safe kenan."Ita dai
ta kasa magana, sai dariya. Zarah ta ja kofa."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Ya tsaya ya k'are mata kallo, sannan ya sauke
numfashi. Ya tako a hankali ya tsugunna
gabanta, suka dubi juna, ta dan kauda kai, tana
murmushi. A natse ya kwantar da kan sa bisa
kafafuwanta, ya nisa yayi dan shiru. Haka ita
ma take kallon sa idanuwanta suka kawo kwalla.
Bata san lkcn da ta dora kan ta bisa bayan sa
ba. Sun jima shiru haka kafin ya ce,"Na gode
Allah, na sake gode masa daya nuna min
wannan rana. Haka kuma na gode wa Abba
daya sake mallaka min ke. Na yi kuskure gare ki
Nusaiba wanda baya misaltuwa, ba na kuma
son tuna su. Ki yafe min Nusaiba. Ta
ce,"Tuntuni na yafe maka yayanmu. Ya wuce."
Ya dago ya ce,"Na gode." Kin san wani abu? Ta
kada kai. Ya lalibo aljihunsa ya dauko kudi, ya
kamo hannun ta ya dora mata, ta ce "Na
menene? Kudin ki ne, canjin ki dubu 15 da ki ka
ba ni a asibiti. Ta saki baki tana kallon sa,"Kai
yayanmu, shekara 2 da rabi? Ya sake kwantar
da kan sa, ya ce,"Ba zan ta6a mancewa da su
ba Nusaiba, domin daga ranar da ki ka miko
min su. Allah ya manna min son ki a raina. A
lkcn ba wai ba ni da su ba ne, amma ba su da
amfani, tunda ban san yadda zan yi in ciro su
ba. Alhalin ina matukar bukatar su. Da gaggawa.
Kin min abinda ba zan ta6a mancewa da ke ba
rayuwa, kin taimake ni a lkcn da na wulak'anta
ki na.......... Ta rufe bakin sa."Na ce ya wuce
yayan mu, ka daina tunawa."
Ya dube ta ido cike da kwalla,"Kar ki yi
kokwanto Nusaba, Ina son ki! Ina son ki!! Ina
son ki Nusaiba!!!
Ta ce ,"Na sani." To kice kina so na in ji, ko sau
1 ne."
Ta yi dan murmushi ta ce, "Ina son ka yayan
mu.
Ga kuma kudin ka har canji na bar ma ka."
Yahayo shimfidar sosai, ya ce,"Kin saye baki na
ke nan? Ta yi 'yar dariya,"Na siya."
To me ki ke sha'awar sha? Ta
ce,"Uhm.......Cock, irin mai dan inabin nan. Ka
gane ai? Ya tsura mata ido, tana masa dariya.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Zaman lafiya mai ban sha'awa ga kowa ya dore
a gidan Naseer. Hankalinsa kwance, ba shi da
matsala. Ya k'are Digirinsa. Shine gwarzon
shekara, wanda ya fito da ajin farko a fanni da
yake karanta, sannan ajin farko cikin jerin
wadanda suka zo na farko a sauran kwasa-
kwasai a wannan shekara.
Don haka yana daya daga cikin masu rubuta
jarabawar tantance masu tafiya Turai don karo
ilimi tare da tallafin gwamnati. Kowa yayi masa
murna. Shi kan sa ganin abin yake kamar a
mafarki. Allah yayi gaskiya ya ce tashi in
taimake ka.
Tabbas hake ne, Naseer ya ga Zahiri.
A Kaduna suka rubuta jarabawa 'yan makwanni
tsakani sakamo ya fito.
Naseer ya haye ya ci Nasarar tafita Ingila.
Shirye-shirye ya kankama a lokacin cikin Nusaiba
ya fara tsufa, domin kuwa ya shiga wata na 7.
Ranar da zai tafi daren kasa barci yayi, saboda
tunanin shekara 1 ba zai ga iyalansa ba,
wad'anda ya riga ya aje su cikin ransa, baya son
kasancewa da kowa sai su.
A duk inda yake. Allah.Allah yake ya yi yadawo
gida, saboda tsabar son da yake musu.
Amma babu yadda zai yi, yana son ci gaba kuma
a yanzu ya tauna dadin karatu ya dandana ya
gane fa'idar sa. Kan dole ya dake zuciyar sa.
Washe gari karfe 8 na dare jirgi ya cilla da su
birnin Sarauniya. Sun kama karatu gadan-gadan,
amma kodayaushe cikin waya suke da iyalansa.
A haka watan haihuwar Nusaiba ya tsaya.
Umma ta sa ido sosai a kan ta, babu ranar da
bata zuwa Hanwa. Allah da ikonsa da safe ta
fara nakuda, ga shi Zarah na da jarabawa kuma
ta karshe ce, don kammala NCE din ta. Duk da
haka ta hada kayan haihuwa ta wuce da
Nusaiba asibiti.
Sai da ta tabbtar an shiga da ita dakin haihuwa
kafin ta kira Umma ta gaya mata asibitin da
suke.
Nan take Umma ta watsar da abinda take, ta
biyo hanya.
Tana isowa 8 dai-dai, sannan Zarah ta bar mata
Ameer, ta wuce jarabawa, ta iske an shiga, sai
da ta sha surutu, ta samu aka ba ta fefar.
Da namiji Nusaiba ta sake Haifa, lafiya lau daga
ita har Bebin.
Umma da Ameer na murna. Nan da nan ta kira
wayar Ummi, ta shaida mata ta sake sabon
ango....
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajinisa Yake3-06
Posted by ANaM Dorayi on 12:04 PM, 25-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Suka yi farin ciki. Ta lallatsa ta nemo lambar
Naseer.
Suna gaisuwa, kudinta suka kare.
Tir!
Haushi ya kama ta, sai ga shi ya kira,"Menene
Umma?
Ta ce,"Ka yi Da. Nusaiba ta haihu yanzu." Farin
ciki kamar yayi tsuntsu ya baro Ingila." Ina take
Umma? Ta ce,"Ai tana ciki ba su riga sun fito da
su ba, amma sun ce lafiya kalau suke ita da
Bebin."
Alhamdu-lillah! Allah ya amfana mana." Ta
ce,"Amin. Haka ya kasance cikin doki, kamar
yadda Zarah ke makaranta cikin zakuwa da son
ta koma wajen Nusaiba.
Kafin yamma gidan su ya cika da baki 'yan barka,
angon karni kuwa ya ki barin mai jego sakat da
waya, shi so yake ji kukan Bebi, "Bebi kuma ya ki
yin kukan.
Barcin sa kawai yake kwasa.
Ranar suna, yaro ya ci sunan Alhj. Haka kuwa
suke kiran sa(Alhaji) Ya ci gaba da girma tamkar
Ameer, shi yasa idan Naseer ya rufe ido, baya
ganin kowa illah 'ya'yan sa, tamakar 'yan 2.
Watanni 3 bayan haihuwar ta. Alh.Basheer zai tafi
harkokinsa Turai, ya wuce wa Naseer da hotunan
dan sa, ya gan shi. Hankalinsa ya kwanta. Ya cire
na Ameer daga firem ya zira wanda suke su 2.
An ci gaba, renan Naseer Jah-Jah. Shi kansa yana
mamakin kansa.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Kwanci tashi, shekara ta zagayo. Naseer ya dawo
cikin iyalansa, kamar yadda yake so. Bayan ya
huta sati 1. Alhj ya kira shi suka tafi bargar
dawakansa. Abin ya ba shi mamaki, irin
dawakan da ya gani suna harbin iska.
Sake da baki ya dubi Alhj yace "Abba za'a fara
wasa ne? Ya dafa shi ya ce,"Haka na ke zato,
idan na sami amincewar Jah-Jah."
Bakin sa har kunne ya ce,"Abba in dora sirdi in
hau? Yayi murmushi ,"Why not."
Ya kira mai kula da wajen, ya ce,"Je kawo sirdi."
Nan da nan ya dora Naseer ya haye jikin sa na
rawa ya zagaye bargar dawakan.
Kamar kar ya sauka, dokin yayi masa dadi."
Abba yaushe za'a fara? Ya ce,"Yau da yamma
za'a fara a tisaye, sannan akwai club guda 3 da
na ba takardar gayyata wasan sada zumunci.
DABAI ta dawo sabuwa."
Ya ce,"Insha- Allah kuma gagara gasar masu
gasa." Ya kamo shi suka nufo mota yana
fadin,"Akwai wani kokari da na ke maka, amma
ba zan gaya maka ko menene ba, sai Allah ya
tabbatar da abin, za ka ji.
Ka ci gaba da addu'a.
Allah za6a mafi alkhairi." Ya dan rankwafa ya
ce,"To Abba, na gode.
Allah ya saka da alkhairi."
Wasa ya kankama. (DABAI RIDERS) ta dawo
duniyar tseran Polo. Tutar Naseer Jah-Jah ta yi
sama ta neman ta wuce yadda take da can
baya.
Watannin 9 yana ketawa cikin kungiyoyin Polo,
yana ba su mamaki.
Kwatsam!
Abinda Alhj ke masa kokari ya samu. Ba wani
abuba ne, illa samun shiga shaharrariyar
kungiyar wasan Polo ta kasar Potugal.
Naseer fa kamar yayi hauka, don murna.
Haka Malam Balarabe, bai san abinda zai ce da
Alh.Basheer ba.
Kamar yadda aka bukace shi, daya iso 15 ga
wata, haka yayi sallama da kowa suka tafi tare
da Alhjn.
Sun gwada shi, sun ga iya kwarewar sa a zahiri
ko dama Alhj ya sha kai masu SD filet din
wasaninsa na gida da waje.
Kwarai sun gamsu da wasan Naseer, kuma da
alamun za'a samu da shi. Can Alhj ya baro shi
yana fafatawa cikin turawa.
A lokacin ne ya k'ara tabbatar cewa komai in ka
na da ilimi ya fi tafiya dai-dai, musamman a
wannan zamani.
An bashi gida da motar hawa. Naseer ya
kasance ba shi da wata matsala sai ta kewar
iyalan sa.
Ita ma sun kusa magance ta.
Cikin watanni 2 takardun zamansa dindin a
Potugal suka kamala, ya sami izinin shigowa da
iyalansa. Babu son kai. Zarah ce ta fara zuwa a
matsayin ta, ta babba. Ameer yayi kukan son
biyo ta, amma ina makaranta, ta hana.
Wai! Wa ya gane min Zarah a Potugal?
Ta shakata kwarai tsawon wata 1, ta koma
Nusaiba ta damk'o hanya. Haka suka kasance
suna yi wata guda-guda babu matsala balle
tashin hankali. Kowacce ta zo Naseer yana jin
dadin kasancewar tare da ita, bisa adalci da
tsoron Allah.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Shekara 5 Naseer yayi karfi sosai a k'asar
Potugal a fagen tseren Polo. Yayi farin jini kwarai
da gaske, kowa na son shi. Sau da yawa wasu
kungiyoyin na kawo masa cafka ta hanyar ninka
masa abinda yake samu, amma ya kauda kai,
saboda Alh.Basheer. Domin a halin yanzu arziki
sai dai ya ba wani, bai ma san iya wadanda
suke cin gajiyar sa ba a gida Najeriya.
Duk shekara idan ya je hutu. Bayan dawowa ba
tare daya buda wata cibiyar siye da siyarwa ya
zuba matasa sun samun abinci ba. Hatta Naseer
B dan hassada, ya saduda ya nemi gafara, ya
dawo yana cin arzikin da Allah yayi wa Naseer.
Yayi farin jini ba na wasa ba a Potugal, domin
har tallace-tallace yake wa manyan kamafoni ta
hanyar sana'arsa.
Ba kananan dololi yake kamawa ba, kowacce
talla yayi. A 'yan shekarun nan biyar. Nusaiba ta
hada 'ya'yanta 4 a gidan Naseer, 2 maza, 2
mata.
Hakika hankalin Naseer a kwance yake, kuma
Alhj ya lura karfi sosai a club din sa, tseren
dawaki sai dai ya ba 'yan baya tirenin. Saboda
haka yayi iya yin sa wajen Injiniya Ahmad Kaita
ta hannun sa ya samar masa a aikin yi ta
6angaran karatun da yayi, don kar ya tafi a
banza.
Allah mai ko! Takarda kawai aka ba Naseer ya je
inta-biyu ofishin(Internet Globl Services) reshen
Potugal, take nan suka yarda da takardunsa. Ya
sami shiga aiki. Duk da haka bai bar Polo ba,
amma ya zama na manya, wanda ake son tafiya
da shi, musamman a gagarumin wasan duniya.
A farkon wannan watan Zarah ce ke da zuwa
Potugal, a filin jirgi ya je ya dauko ta. Suka shiga
harkokin su kamar yadda suka saba. Zarah na
nason ziyartar Singafo da Malesiya, don haka
washe gari suka wuce suka kwana 4. Kwana
bibbiyu a kowace k'asa. Sun ci gaba da hutawa
a Potugal.
Sati 2 dai-dai da zuwanta, ciwon ciki mai
tsananin gaske ya murda. Zarah kamar ba za ta
yi rai ba. Naseer ya gaggauta kai ta asibiti.
Babu 6ata lokaci ta ga Likita ya bata kwararrran
bincike. Allah da iko tare da yin yadda yaso.
Wai Zarah ciki gare ta na sati 2 a wajen mahifa.
Naseer yayi wa Likitan ta bayanin matsalarta.
Nan da nan aka buda bakin mahaifa aka maida
cikin mazaunin sa. Ta sami kulawa sosai a
asibitin har ta wartsake.
Yayin da Naseer tuni yayi waya gida, ya shaida
masu halin da ake ciki. Kowa ya sha mamaki.
Shi yasa tana murmurewa ta fara amsa
wayayinsa masu gaishe ta, musamman Nusaiba
da ta kan bugu sau 3 zuwa 4 a rana. Mafarin
zamanta a Potugal kenan tana samun taimakon
daya kamata.
Anyi wa yara hutu. Nusaiba ta aje su wajen
Umma, ta zo duba Antinta, sati 2 ta koma gida.
Sannu a hankali cikinta ya wuce wata 7, ya shiga
na 8 kuma Bebi lafiya lau, kowa na ta murna,
musamman Naseer da yake tausaya wa Zarah.
Rashin da, ga ta ita ma ita kadai wajen iyayen
ta. Satin da za ta shiga wata na 9, jini ya goce
kamar famfo.
Da kyar suka tsaida jinin suka shiga binciken
mai ya kawo hakan.
Ai da gudu Likita yasa aka gara ta tiyata, bai yi
bayanin komai ba, sai da ya ciro k'aton Bebin
namji, sannan yayi mata duk abinda ya ga ya
dace, don tsira da lafiyar ta.
Daga Bisani ya kira Naseer ofishinsa yake gaya
masa matsalar da Zarah ta samu. Mahaifarta ta
fashe gaba daya, wanda dole ya kasance ya
fitar da ita baki daya, hakan shine wajibi a gare
ta, don zaman lafiyar ta.
Kuka ne kadai Naseer bai yi ba, amma ilahirin
hankalinsa ya tashi. Gani yake yi kamar ma cire
mahaifar, zai iya jawo mata wata matsalar, sai
da likita yayi masa bayani sosai, sannan ya
gamsu. Yayi addu'ar Allah ya k'ara mata lafiya,
ya kuma bar mata abinda aka samu, ita ma ta
rink'a ganin abin ta.
Ko gida Najeriya hankalin su ba kwance yake ba,
duk Nusaiba ta k'osa a kammala mata biza ta
tafi.
Bayan kwana 3 kuwa ta isa Potugal.
Antin tana a kwamce, duk ta rame ta dushe,
bata san lkcn da ta fara zubda hawaye ba.
Ga Bebi kato, gwanin sha'awa kuma duk 'ya'yan
Naseer da shi suke kama, har matan.
Nan ta zauna tare da Bebi (Aliyu), zuwa lkcn da
Zarah ta yi sarai, tsawon kwana 12 a asibiti,
kafin Likita ya bata sallama suka dawo gida.
Sai da Zarah ta yi 40, ita da Aliyunta, sai k'ara
murjewa suke, ita dai Zarah ta ki sakin jinkinta
dashi, gani take kamar shi ma mutuwar zai yi.
Sun dawo gida Najeriya yana da kwana 45, gaba
dayan su da Naseer.
Gagarumar walima ya shirya, bata wasa ba,
'yan uwa da abokan arziki suka taru, aka taya
juna murnar samun Aliyu tare da fatan Allah ya
raya shi cikin danginsa, rayuwar Islama. Sati 1
Naseer yayi ya dawo Potugal.
Tun Zaran na fidda rai da Aliyu, tana ganin yau
zai mutu ko gobe har ta zo ta saki jikinta,
zuciyar ta ta zauna waje daya ta daina ba Aliyu
mutuwa. Watansa 9 kenan yayi girman mamaki,
da kan shi yake mikewa tsaye, yana nema cira
k'afa yayi tafiya.
Yana kuwa shan ja wajen 'yan uwan sa suna son
yayi tafiya dole.
Rayuwar su mai dadi suke sha, tare da abokan
huldar shi, domin a halin yanzu Sageer yana
lakcarin a nan (State Poly) da yaransa 3. Kausar
na da 2. Zumunxin su kodayaushe k'ara k'arfi
yake tare da k'aruwar arziki. Ko Zarah ta gyara
gidan su dai-dai gwargwado tare da taimakon
Naseer. A cikin su da iyayen su babu wanda bai
keta hazo ba, ya sauke faralinsa. Komai maka
Allah shekaruna mikawa hada da tarindaukaka.
Naseer ke zaune shi kadai bisa kujeran alfarma
a farfajiyar bayan gidansa. Yayi shiru ya
zunduma taunan baya, har ya zo kan rayuwar
da yake cikin ta a halin yanzu.
Ya dubi tafkeken gidan sa a birnin Potugal,
mallakar sa wanda ya zuba makudan daloli ya
siya. Babu abinda ke ransa, sai dumbin godiya
ga Ubangiji da yayi masa baiwar da ba kowa ke
samun irin ta ba.
Sannan ya mallaka masa ingantattun mata na
nunuwa a fadin duniya.Zarah idan ya tuna irin
baiwar da Allah yayi mata na kaifin hankali da
sanin yakamata, ya tuna ita ta fara gaya masa
rayuwa shirin Allah ce, bai kamata Dan-adam
yana alkawari a hurumin da ba nasa ba, sai ya
ji son ta ya shafe ko'ina a jikin sa, yana neman
zautar da shi.
Nusaiba matar da yake wa yak'inin sa'a ce a
gare shi, Allah ne yayi masa arziki daga gare ta,
'ya'ya da dukiya tare da fice a duniya. In dai
ana maganar wasan Polo, duk masoya wasan
sun san da Naseer Jah-Jah.
Shi yasa idan ya dube ta, haka kawai ya kan ji
hawaye sun cika idanuwansa, sbd tsabar
tausayin kan sa, da ace ya rasa ta akan wautar
banza. Son ta ruwa ne, ya aje wa ransa, don ko
ya fadi, shi kansa yana ganin karya yake yi.
Yayi mika, take nan kewar su ta kama shi,
domin babu ko dayan su a tare da shi. Zarah
na jarabawar karshe ta kamala B-ed din ta.
Nusaiba kuwa ta na watan haihuwa ta 6.
Ita kadayaushe ta fi son haihuwa a gida. Gaba
daya hankalin sa ya koma gun sun, daren nan
ya kasa barci. Kamar wasa zuciyar sa ta rasa
sukuni, ba shiri ya nemi hutun shekara.
Bai hada sati ba, ya baro Potugal, sai ganin sa
suka yi kwatsam!
-----------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
'Ya'yan sa suka baibaye shi, tun isowar sa har
la'asar yana tare da su. Direba yayi kiran su
lkcn Islamiyya, kowanne ya fito cikin shiri, ya
shiga mota. Direba ya wuce da su. Zarah ta idar
da Sallah, ta fito babban falo ta iske Nusaiba
zaune tana kallo.
Kusa da ita ta zauna tana fadin,"Ki na nan ki na
kallon fadace-fadacen nan da ya ki ci ya
kicinyewa." Ta ce,"Ke dai bari, ai ni wannan
fadan na k'asashen larabawan nan tsoro yake
ba ni." Zarah ta ce, ke me kika fahimta daga
gare shi?
Ta ce,"Karshen duniya mana. Dama ance idan
zamani ya zo karshe, alamun har da 6arkewar
rikicin k'asashen gabas ta tsakiya. Yanzu dubi
k'asashe nawa ke rigima, ana kashe su, kamar
ana kashe kiyashi, tsakanin mu a musulmi
kenan."
Zarah ta tallafe kunci ta ce,"Wannan rayuwa
tana firgita ni, me mu2m ya kamata yayi, banda
ya kadaita Allah, yayi masa ibada, sannan idan
ya ci, ya bada sadaka, don neman karshe mai
kyau? Ta ce,"Wallahi kuwa Antina, musamman
na mu mata da aka ce mun fi yawa a gidan
wuta.
Biyayyar aure ce matsalar mu komai muka yi
gidan miji lada ne. Amma sai ki ga abin ya
gagara.
Kar ma ace miki akwai abokiyar zama, abin ya fi
kazanta.
Sai ki ga mace ta mance cewar akwai hikimomi
da yawa cikin auren mace fiya da daya shi yasa
Ubangiji ya halasta shi.
Haka kawai ta dauki bakin kishi ta dorawa
kanta, daga nan ne za ta fadawa hallaka.
Allah ya kiyashe mu.
Zarah ta kamo hannun ta, suka runtse,"Kin yi
gaskiya amarya, shi yasa na ke wa Allah godiya
da yasa ke ce abokiyar zama na." Ta yi
murmushi,"Ni din Antina? Na fi kowa farin cikin
samunki. Allah ya k'ara hada kan mu, ta yadda
yayanmu zai ci gaba da samun kwanciyar
hankali.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Tafi suka ji ana yi ta bayan su.
Duk suka waigo,yayan na su ne a tsaye yana jin
su. Ya zagayo suna dariya ya tsaya gaban su, ya
ce,"To a matsa min in zauna." Suka ware ya
zauna tsakiyar su." Allah ya kamaku, ashe zama
ku ke kuna gumalta ko? Zarah ta kama baki,
"Lah!
Allah mai halitta, jaba ta dubi bakin mijinta.
Gulmar me kuma a mu ka yi ta ka?
Ya kamo kunneta. Nusaiba na kwasar dariya, ya
ce,"Ita jabar 6ata dubin ta ba ne? Ta ce,"Oho."
Ya k'ara murdawa, ta yi k'ara. Nusaiba ta kamo
na shi ta ce,"Allah sakar min Antina, ko ni ma in
cire na ka. "Ya saki ya dube ta,"I see, kun hada
kai ko?
O.k, yayi kyau, ke ba zan ta6a ba, kin zama
yangwam!
Amma ke, za mu hadu."
Duk suka yi dariya.
Ya rungumo kafadansu ya sake fadin,"Allah ya
yi maku albarka, kun zama abin alfahari na, kun
zama jigon rayuwa ta.
Na kuma gane rayuwa shirin Ubangiji ce,
mutane da yawa suna samun dama, amma sai
su ki amafi da da damar har ta wuce su, daga
baya su zo suna cizon yatsa.
Allah ya ba mu ikon amafin da damar mu."
Suka nisa suka amsa da Amin.
Kowacce ta dora kanta bisa kafadar gefen sa.
Suka yi shiru na 'yan dakikai.
Cikin shirun ne suka ji kamar suatin T.V, a wani
sashi na gidan. Naseer ya ce ,"Wai ba duka
yaran nan sun taifi makaranta ba?.
Eh mana."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Ya mike yana fadin,"Ga sautin (Game) can ina j?
Duk suka mike suka bi shi sashin yara. Ameer
ne ya kuke yana buga Game na tseren Polo,
sautin T.V ya rage can k'asa, yi yake kamar zai
tashi sama, sbd kwaikwayon yadda dawakan ke
gudu. Naseer ya lalla6o ya cafke kunnansa, a
tsorace ya waigo manyan idanuwan nan na sa.
Suka kara yo waje tamkar Naseer a zamanin da
yake shagalinsa a filin sukuwa.
Bai tanka masa ba, yai ta jan kunnan sa har
falo, sai su Zarah ke ta faman salati suna
fadin,"Amma dai Ameer Allah ya shirye ka!
Ya tsaya ya k'are masa kallo, kafin ya ce,"Kai ne
babba, amma babban kwabo? Kullum da kai ake
complain! To zan kwashe Game din tunda shi ke
hana ka zuwa makaranta! Yayi sukuiti yana
kumbura.
Nusaiba ta zungure shi, "Maras kunya, sai anyi
magana, ya rink'a cika yana hura hanci, wa ka fi
zuciya? Come on wuce ka dau ko jaka Lado ya
kai ka! Zarah ta kamo shi,"Wuce mu je, ka
dauko jakar, kai ba ka ganin kannin ka sun tafi?
Ta raka shi ya dauko jaka. Nusaiba na ta fada,
ta fita ta kira Lado Direba, yasa shi a mota zai
wuce da shi."
Nusaiba ta zauna kusa da Naseer ta ce,"Ameer
sai addu, ace yaro baya maida hankali a karatu.
Sai game din tsiya? Shi yasa ban so ka kawo
masu wannan sabin Game din ba."
Ya ce,"Zai bari ne." Zarah ta dawo ta zauna inda
ta tashi,"Ameer kenan an dai tafi ana ta
kunci,"Nusaiba ta ce,"Ai kin ji Babansa ya ce zai
bari ne, amma complain din Ameer yayi yawa,
ko makarantar kuka suke da rashin maida
hankalinsa, ga masifa, ni na rasa irin sa."
Ya ce,"Ni kuwa in na kalle shi, dariya yake ba
ni." Kin ji ko Antina? Ta ce,"Ya dai kamata ka sa
baki, ka yi masa fada sosai, kafin ka bar garin
nan, kila ya fi jin na ka. Ameer yan aikin gidan
nan bai kyale ba, haka 'yan kanninsa. Aliyu
kadai bakin sa ke ceton sa da yake duk gautan
ja ne.
Baba na da Alhaji kuwa, sai dai su yi kuka su
share hawaye, balle kuma 'yan matan."
Ya kama kai, ya ce,"Wayyo Abba na, duk
wannan laifin shi kadai? Wai ba yarinta bace?
Nusaiba ta ce,Yarinta? Me yasa............
Ya katseta,"Ya isa! A yimin shut up nace! Rashin
jin nan fa kowa yayi shi, ke kin yi, ke ma kin yi.
Ni ma na yi."
Nusaiba ta ce,"Oho, ashe abin gado ne, ta
6angaranka, amma mu ba muyi rashin jin kin
zuwa makaranta ba."
Yayi 'yar dariya ya ce,"Yan rainin wayau, kun
cika ni da , kamar ban san sirrin kowacce ba."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Zarah ta gyara zama ta ce,"Ai sai ka
fadi"Yalla6ai, mu na ji." Ya dube ta, ya ce,"Ke fa
kullum ki na like bayan taga, ki na zuba ihu,
hawaye sharaf-sharaf, majina har baki. Da an
tambaye ki menene? Sai ki ce kudin (Break) dina
ne suka 6ace."
Ya fadi yana kwaikwayon muryart har da
shashshekar kuka.
Ya juya kan Nusaiba,"Ke kuma ai Abba ya gaya
min da zarar Direba ya fito da mota, zai kai ki
makaranta, sai ki ce kashi ki ke ji."
Ni din?
Zarah ta ce,"Ke ma ki ka tsaya tambayar sa. Ta
figo filon kujera. Nusaiba ma ta dauko na ta,
suka rufe shi da duka.
Me zai yi ba dariya ba, yana fadin,"Mugaye,
k'arya na yi.........?
Na kwashe 'yan biro na da takarduna na bar
gidan, don ba zan iya ceton Naseer ba.
Tsokanar fada A JININ SA YAKE!!! ,
saboda haka ALHAMDU-LILLAH, na gaji da
shari"a.
Idan kuma akwai ma iyawa, to Bismillah!
Jah-Jah na can yana dakuwa a hannun zaratan
matan sa.."
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
afuwan bakujini da wuriba sakamakon wayata
tadan samu matsala, daga bayakuma nadanyi
rashim lafiya, your prayer is needed pls
Zaharaddeen Shomar
Whatspp 08168575100